[8/10, 12:36 AM] ‪+234 806 890 2943‬: ❣ *KHALEED MY BLOOD*❣


         _NA_
_*FATIMA KHALID NASHUKA*_



*Bismillahir ramanir rahim*



1⃣

Axaune yak'e cikin riga da wando, jikin wata bishiya yayi tagumi saka makon rashin aikinyi da yagama makaranta be samuba ga abubuwa sunmishi yawa saboda shine babba a gurin iyayansa, dama su uku suka haifa khaleed shine nafarko sai aysha sai autarsu umaima suna xaune a grn zaria awani unguwa da'ake cewa hanwa, sunan mahaifiyarsu safiyya mahaifinsu kuma Abubakar suna zaune cikin rufin asiri, "assalamu'alaikum" umaima ce tayi sallama ummansu ta amsa tace
"umaima daga ina haka?"
tace "umma naje gidansu baseera" "hakane yau alhamis ba mak'aranta "ummu ina yaya khaleed yake" umma tace
"yafita bai dawoba ai khaleed dan albarka ne fatana Allah ya bashi abunda yake nema".

Umaima tace "Ameen umma bari naje koxan ganshi" toh sekin dawo xata juya kenan sega khaleed yayi sallama ummansu ta amsa cikin murmushi umaima taje dagudu ta rungumeshi tace "ya khaleed dama gunka xanje"
yace "to yar kanwata gani akwai lbr ne?" tace
"dama zancene kazo ka koyamin home work din da'aka bamu a school"
yace "to bari nayi magana da ummana" umma tajuyo tana kallonshi tace "ya akayi ne yace
"umma dama ina zaune acanne sega senator hassan zai wuce yace naxo shine yace ya akayi nake zaune anan gurin shine nace mishi wlh nagama karatu amma bansamu aikin ba haryanxu har nagaji da nema shine yace insha Allah zai sanamun aiki nakawo CV na Wato takarduna" nandanan umma tayi murmushin farincikinta yafito fili tamushi addu'ar dacewa tace bari abbanku ya dawo sai a sanar dashi shima yasa Albarka" ai lokaci guda Umaima taji wani mugun💃🏻 dadii acikin ranta saboda son da takeyiwa Khalid.



*FATEEY YAR MUTAN ZAZZAU*😍
[8/10, 12:36 AM] ‪+234 806 890 2943‬: ❣ *KHALEED MY BLOOD* ❣


*NA*
*FATIMA KHALID NASHUKA*



2⃣



Khalid yamike yana cewa "da umma bari mushiga ciki da yar rigimata"
tace "to"
harzai wuce yace "umma wai ina Aysha ne naga ban gantaba?"
umma tace
"kamanta tatafi hadda"
yace "au hakane shiyasa nikesan Aysha akwai san karatu" umma tayi murmushi
nan sukashige daki khalid yanata koyawa umaima home work can sega aysha tayi sallama ummansu ta amsa tace "Aysha kin dawo?"
tayi murmushi tace "umma na dawo ya khalid fa?"

umma tace "yana ciki" Aysha tace "umma umaima fa duk suna tare?"
nan aysha tawoce ciki tayi sallama ya khalid ya amsa yace "sis kin dawo?"
tace "eh" yace
"ya karatun?"
tace "Alhamdulillah" yace "Aysha yau ina cikin farin ciki"
Aysha ta washe baki tace "ya khalid kasamu aikin ne?"
"Eh insha allah inasa ranhaka".

nan aysha tadunga murna tanama yayannasu fatan dacewa nan kuma sukadinga hira yanda aysha zataci gaba d karatunta Aysha yanzu tagama js3 tace "yaya wani makaranta xakasani"
yace "duk wanda kikeso"
tace  "Allah yaya?" "Allah kuwa my sweet sis" tayi dariyan jin dadi auta umaima tashagwabe fuska tace "yaya nifa?" yace
"Allah sarki autar umma bari kigama wanda kikezuwa sekishiga wanda kikeso nanta tarungume khalid tana murna khalid yanata murmushi dan babu abinda yafiso irin farin cikin yan'uwanshi nan sukajiyo muryan abbansu nakiran autar umma aiko dagudu umaima taje ta rungume Abbansu nan khalid suka fito yana dariya Abba yace "khalid wannan dariyanfa kafin yayi magana umma tarigashi da cewa........


FATEEY YAR MUTAN ZAZZAU
[8/10, 12:36 AM] ‪+234 806 890 2943‬: ❣KHALEED MY BLOOD ❣


NA

FATIMA KHALEED NASHUKA


3⃣

umma tayi murmushi tace
"Abban khalid yau duk muna cikin farin ciki saboda insha Allahu khalid yakusa cinma nasara"
Abba yayi murmushi yace "nise murna kukeyi kunki gayamun abunda kefaruwa"
umma tace
"khalid dai yak'usa cinma nasara"
abba yace
"kufadamin mana" nan umma tagayawa Abba duk yanda khalid sukayi da senator hassan Abba yayi matukar farin ciki dajin wannan labarin nan yayiwa khalid murna da addu'ar samun nasara khalid yace "ranan monday yace nasameshi a office" abba yace
"Allah ya kaimu lfy" duk suka amsa da ameen.

khalid yawuce daki yana duba takardunshi abba yacewa umma "wlh shiyasa kullun nik'e alfahari dasamun khalid a matsayin danmu saboda da natsuwarshi"
umma tayi murmushi tace "shiyasa nima kullun nake kara godewa allah"
Abba yace "sekuma mutayashi da addu'ar Allah yasa yadace Allah kuma ya bashi mace tagari" umma ta amsa da ameen.

nan sega khalid yafito yace "umma Abba bari naje gurin kakus kodayakema aysha umaima kuxomuje"
sukace "to ya khalid" nan sukama iyayansu sallama suka wuce sunacewa kugaida maman mahaifiyar Abubakar ce asalin su dukansu mutanen zaria ne shi Abubakar su biyu mamansu ta haifa Abubakar ne babba se zainab me bimishi duk sunyi karatun arabic da kuma na boko seda Abubakar yagama makaranta bai samu aiki ba ga mamansu ita daya ke wahala dasu sakamakon tunda aka haifa zainab mahaifinsu ya rasu Abubakar dayaga bai samu aiki ba seyafada kasuwanci yana sayo kaya daga kano xuwa zaria ita kuma zainab tayi aure ta auri wani me irin sana'ar Abubakar, yanada rufin asiri sosai allah ya basu yara hudu  suka sa mishi Abdullahi sena biyun sunan yayanta Abubakar sena uku fadila se auta maryam shikuma lokacin Allah yahada Abubakar da safiyya taxo hutu gurin yar'uwarta dake kusa dasu daganan suka kulla soyayya har Allah ya kaisuga aure.

bayan khalid sunje gidansu kakus, kakus tafito tana cewa "khalid kune a tafe" yace "eh kakus" sukashiga cikin wadataccen falonta suka gaisheta kakus tace "amma naji dadin zuwanku khalid yace "Allah koh matas"
kakus tace
"Allah kuwa" umaima tace "kakus nizansha ruwa" kakus tace "nine zan ibo miki ruwa sede karkisha"
 khalid yamike yanacewa "aiko sai tasha tunda da yayanta suketafe" yabude firji yadauko ruwa yabama umaima tace "yawwa ya khalid nagode wanda kuma bai baniba setayi shiru"
kakus tace "karashe mana mara kunya" aysha tace "ke kakus kincika fada"
kaka tace "nayi" khalid yace "kunji ku kyale kakus tasha nazo nacemata xanyo mata kishiyane shine kishinta yamotso" nan kakus tace "Allah ya kyauta kishin waxanyi mutumin dako aikinyi bai dashi bare naji haushin za'aragemin kudin cefane" nan khalid yayi murmushi yace "da kenan amma niyanxu insha Allah ganinama inbaki wasaba seya xamemiki aiki"
kakus tace "ban ganeba nan khalid yashedawa kakus abundake faruwa kakus tayi murna sosai tamushi addu'ar dacewa.


*FATEEY YAR MUTAN ZAZZAU* ?
[8/10, 12:36 AM] ‪+234 806 890 2943‬: ❣ *KHALEED MY BLOOD*❣

     
         *NA*

*FATIMA KHALEED NASHUKA*


4⃣


nansuka cigaba d hira ya khalid yace "kakus zamu wuce" tace
"harzaku tafi"
khalid yace "eh mata sonake muje gidan mummyn fadila" wato zainab kanwar mahaifinsu nan kakus tace "sekun dawo ku gaidata" khalid yace "zataji insha allah"
nan suka fito suka tafi ahanya sai hira suke da kanninshi cikin nishadi da k'aunar juba suna zuwa gidan mummyn fadila sukayi sallama sukashiga da gudu fadila ta rungume khalid tana cewa "oyoyo ya khalid" mummynsu tafito tana cewa "khalid kune tafe?" yace "mune mummy" su Aysha suka gaida mummy se lokacin fadila tayiwa Aysha magana Aysha tayi banxa daita tace "sai yanxu kikaganni kin kyaleni"
nan fadila tayi dariya tace "haba frnd kar'aji kanmu mana"
mummy tace "ai munriga munji tuntuni" Aysha tace "aiko bazaku jiba".


nan sukashige ciki fadila taja hannun Aysha suka wuce daki khalid yakara gaida mummy tace "khalid yasu aunty safiyya da Abbanku?" yace
"duk suna lfy"
 tace "umaima ko magana?"
 umaima tace "mummy ina abunda kikace xaki kawomin?"
mummy tayi murmushi tace "ashe abunna ranki umaima"
umaima tayi dariya khalid yace "ai autar namu bata mantuwa"
 mummy tace "aiko  nagani"
 nan khalid yake gayawa mummy insha Allah yakusa samun aiki mummy murna sosai dajin wannan labarin khalid yace "mummy bari mutafi gida saboda yamma tayi" mummy tace "tom kunako waya da abokinka"?
khalid yace
"daxuma mungaisa Abdullahi anacan ana fama da karatu acan sudan"
nan mummy taje ta daukowa umaima sweet dayawa tabata khalid yamike yawuce dakin fadila.

yana cewa to iyayen surutu zamu tafi Aysha da fadila sukayi dariya Aysha tace
"frnd dauko kayan da kikace mummy tasiya mana fadila tace "ok"
nan tadauk'o kayan k'walliya da mayuka masu kyau Aysha tace "frnd yaushe fatima zata dawo ne?" fadila tace
"wlh semunyi waya da'ita".
 k'awarsuce fatima yarinyan babban Aminin Abbansu Aysha ne dasuke zaune duk anan zaria taje hutune kano gurin yayanta dake aure acan nan suka fito parlou suka sami mummy da umaima daketa fama da sweet khalid yace "mummy zamu wuce" mummy tace "ku gaida mutan gidan khalid"
"Zasuji insha allah nan suka tafi Aysha nama mummy godiyan kayan da tasiya mata umaima tace "mummy nifa?" mummy tace "zan sai miki amma bayanxuba kinji auta"
 umaima tayi shiru tana sonyin kuka  khalid yace
"Sis karkiyi kuka zan siyamiki kinji" tace "yawwa ya khalid kuma karka siyawa Aysha kaji" yace "naji"
mummy tace "to rigimammiya nan" khalid yajasu suka fita fadila nacewa Aysha semun hadu a hadda Aysha tace "ok" nansuka taho gida dayake duk unguwa dayane.



FATEEY YAR MUTAN ZAZZAU 😍
[8/10, 12:36 AM] ‪+234 806 890 2943‬: ❣KHALEED MY BLOOD ❣



NA

FATIMA KHALEED NASHUKA


6⃣


Nan khalid yawuce comfanyn senator hasan yana xuwa ya gawani suka gaisa yace "dan allah nazo gurin senator hasan ne" semutumin yace "ok kokaine khalid, khalid yace" eh nine "semutumin yace" ok dama senator yace inkaxo akaika office khalid yace "ok nan suka shiga khalid yayi sallama senator hasan ya amsa yace" shigo mana khalid ya shigo yaxauna ya gaida senator cikin girmamawa ya amsa cikin sakin fuska yace "inga CV naka din khalid yamika mishi bayan yaduba yace" ok shikenan ka dawo gobe kamar wannan lokacen khalid yace "ok nagode allah ya kara girma senator hasan" ya amsa da ameen khalid yamike yawuce gida.


Yana xuwa gida yayi sallama umma ta amsa cikin murmushi tace "harka dawo yace" eh umma na dawo? "tace sannu da xuwa khalid yace" ywwa umma wanki kikeyi tace "eh khalid" khalid yace "umma ina aysha tabarki kina wanki umma tace" na aiketa gidan su mummyn fadila khalid yace "ok umma takalli khalid tace" ya kuwa andace khalid yayi murmushi yace "insha Allah kuwa umma yace na dawo gobe? umma tace" Allah ya kaimu lafiya khalid ya amsa da ameen nan khalid yace "umma bari natayaki wankin nan khalid yashiga dakinshi yacanxo kaya suna wankin suna hira har suka gama nan aysha tayi sallama ummansu ta amsa tace" aysha kin dawo aysha tace "na dawo umma tace ta gode tana kuma gaidake umma tace" ina amsawa nima na gode "khalid yace" sis kin dawo aysha tace "eh yaya kaima ka dawo andace kuwa khalid yace" insha Allah munasa ranhaka aysha tace" Allah yasa duk suka amsa da ameen.


Nan aysha tace "umma nabiya ta gidan su fatima ummansu tace min insha Allah ran juma'a zata dawo umma tayi murmushi tace Allah ya kaimu aysha ta amsa da ameen umma khalid yace" waike sis kin damu da wannan fatima, aysha tace "wallahi ya khalid munasan junanmu nida fatima yace" to ai seku auri miji daya aysha tayi dariya tace "wallahi ya khalid dazamu samu wandaxe auremu tare damunji dadi nan khalid yayi murmushi yace" to ai seku nema "aysha tace ya khalid wai kaiko  budurwa baka da'ita ne khalid yayi murmushinsa mekara masa kyau yace" sis aini bantaba soyayya ba bare budurwa aysha tayi dariya tace" ya khalid Allah yanunamin matarka yakuma yimata murmushi danshi khalid bama abocin dariya bane ko magana bayasan yinta sosai inkaji hiransa toda yan'uwanshi ne.


suna xaune sega umaima tashigo da gudu ta rungume umma taje ta rungume ya khalid da aysha khalid yace "autar umma kin dawo umaima tace" eh ya khalid aysha tace "auta tsaraba nafa umaima taciro sweet a schl bag dinta tace ganaki ya khalid ganaka tamikawa umma tace" umma ganaki umma tace "nade ijemiki saboda anjima nan zakice nabiyaki sweet dinki umaima tace" yau nabarmiki umma "umma tace" hakade jeki cire kayan khalid yace "kixo muci abinci tace" toh ya khalid yace "yau anbaki home work ne a school tace" aa yace "ok aysha abinci aysha tace" ya khalid banjin yinwa yace "ok nan abba yayi sallama ummansu ta amsa tace tana cewa sannu da zuwa abban khalid abba yace" ywwa sannu d aiki nan su aysha sukace sannu daxu abba ya amsa yana dariya abba ya kalli khalid yace "harka dawo khalid yace tunda xuwa abba? abba yace" to ya kukayi khalid yace "abba yace gobe in Allah ya kaimu na dawo abba yace" Allah ya kaimu lfy khalid ya amsa da ameen abba.



FATEEY YAR MUTAN ZAZZAU?
[8/10, 12:36 AM] ‪+234 806 890 2943‬: ❣KHALEED MY BLOOD ❣


NA


FATIMA KHALEED NASHUKA



7⃣



Nan abba ya wuce cikin dakinshi umaima nacewa "abba yau meka suyomin" abba yayi dariya yace "haba auta daga dawo wata kuma ni yau kaka kade namawa siyayya bandake zaki rakani koh nakai mata" umaima tayi narai narai da ido tanasan yin kuka abba yace "haba auta dan yau nasiyawa kaka tsaraba bandake shine xakiyi kuka" to amma" abba ita kakan nan bata tsufaba mezatayi da sweet inbanda ita kwadayayyiyace" duk suka kwashe da dariya aysha tace "hakane autar umma" au aysha hardake za'aringa mawa uwata tsiya "umma ta amsa da" aisena gawa maman tadena baku komi nata"abba yace zakusani nan abba yacirowa umaima sweet ta amsa tana tsalle "abba nagode" umma tace "auyanxo nan abba ya shige ciki umma tabishi su khalid kuma suka cigaba da hiransu cikin jin dadi" umaima aysha kutashi kunje kukwanta nima kwanciya zanje nayi saboda gobe insha Allahu da wuri xan fita "nan suka miki suna cewa" to ya khalid seda safe "allah ya kaimu lfy suka amsa" da ameen yaya "shima khalid ya wuce cikin nashi daki umma kuma ana can wajen abba.


Washe gari dawuri khalid ya shirya kamar yau yaje ya gaida iyayansu nan yaxo gurin su umaima su kace" yaya har kafito "eh har xan wuce nan umaima tace" yaya nima nashirya mutafi tunda hanya school din mune yace "mutafi yama su sallama suka wuce


a hanya se hiransu sukeyi umaima taji nakira sunanta tawaiga setaga baseera kawarta har kin fito baseera tace" eh nan ta gaida ya khalid yaya khalid ya amsa cikin sakin fuska yace baseera kuna kokarikuwa tace "eh yaya munayi" duk wanda tafi kokari ita zanseyawa wani abun mekyau duk suka amsa da cewa nine yaya yace "aide xamu gani togashi nan mun kawo school dinku khalid yaciro kudi yace" in kunfito beark kosayi sweet "suka amsa suna godiya suka shige school khalid shima ya wuce

 yana xuwa kaitsaye yawuce office din senator hasan yayi noking aka mishi ixinin shiga khalid yayi sallama senator hasan ya amsa yace" harkaxo khalid yace "yagaida senator ya amsa cikin sakin fuska nan senator yacewa khalid" naduba CV naka din kuma naga kanada hazaka dan haka wannan comfany tadaukeka a matsayin ma'aikacinta nan khalid yasaki wani irin murmushi me karama face dinshi kyau khalid yayiwa senator godiya sosai da addu'ar samun nasara senator ya amsa cikin jin dadin addu'ar da khalid yamishi yace "kana iya fara zuwa aiki gobe" khalid ya amsa da Allah shikaimu lafiya yamiki yana kara godiya" ya fito a hanya khalid se murna yakeyi kowa yaganshi yasan yana cikin farin ciki 😀


khalid yana shiga gida yahango umma a tsakar gida yaje ya rungumeta yana dariya umma" tace karka karyanifa tunda kai baka girma khalid ya kara rungumeta yana cigaba da dariya yana cewa "umma andace" umma tadagoshi cikin murna tana tana fadin alhamdulilla allah mun gode maka abba ya amsa da "Allah abun godiya" khalid ya juyo ya rungume abba ya murna abba yace" koban a fadaminba nasan andace "umma tace" kwarai kuwa abba yace alhamdulilla "nan suka tayashi murna da fatan cigaba dasamun nasara duniya da lahira ya amsa da ameen iyayena shiyasa nake alfari da samunku a matsayin iyaye kamar yadda kuke alfahari da samuna a matsayin danku nan khalid yace" bari naje gidan kakus da gidan mummy su amsa da Allah ya tsare nan umma tabashi yasako ya kaiwa kaka ya amsa ya fita


yana xuwa gidan kaka yayi sallama kaka da amsa yashige ciki bata polaur tace shigo ganinan khalid yashige bedroom din kaka ya taddata atsaye tana ciro kaya dan zata fita ne khalid ya rungume kaka yana din "yau naxama angon gaske mebada kudin cefane za'aringa kishina koh" kaka tace "yau naga ja'irin yaro nasan karisani khalid yasaki kaka yana dariya yace" haba kakus danna rungumeki kebaki iya soyayya ba kefa ya kamata ki rungumeni kina murna koda yake tsoron mijinki be iya soyayya ba shiyasa "kaka tace" niko mijina ya iya soyayya "khalid yayi dariya yace" dama andaukeni aikin ne nace bari naxo na sanar da uwargida" kaka ta Washe baki tace "kai amma nayi murna Allah yasanya alkhairi yasa afara a sa'a"khalid ya amsa ameen matas ina xakijene naga kina shiryawa" zanje gidan su yarinyan kawata rahama ne barka ta haihu "khalid yace" ok barito nima natafi dan zanje gidan mummy ne gawannan sakon inji ummata" kaka ta amsa tana godiya khalid Allah ya baka mata tagari irin safiyya" wato ummanshi, khalid yace ameen kakus nina wuce tace "kagaida umma ka kace mata na gode Allah ya kara arxiki kakuma gaida zainab din" yace "toh matas zasuji insha Allah yamata sallama ya wuce yana xuwa gidan su mummy yayi sallama yashige mummy na kichin tafiti tace" khalid kaine tafe "
yace" eh mummy? "
nan suka gaisa yace" yace mummy andaukeni aikin" mummy ta washe baki tace alhamdulilla nayi murna kwarai Allah yasa a fara a sa'a ya kuma tsareka da sharrin makiya" khalid ya amsa da ameen mummy nan yace umma nagai dake "tace" nima ina gaida da yayan "khalid ya mike yace" mummy bari nawuce kigaidamin da sis fadila d maryam mummy tace "maryam ana school fadila kuma tare da aysha sukaje amso dinkinsu dana fatima bikin kawarsu ranan saturday" khalid yace "ok kigaidata abdullahi yakusa dawowa koh" mummy tace insha Allah "Allah ya kawoshi lafiya" mummy ta amsa "ameen khalid ya fara tafiya zesa takalmanshi sega fadila ta rungumeshi tana cewa" good afternoon bros" khalid yace "afternoon sis ya kk" tace qalau yace" hakun dawo tace "eh?"
yace ina aysha yawuce gida ok fadila tace" bros kaga dinkina yayi kyau" khalid yace" sosai ma sis yadaga yanagani dogowan rigace dinkin gwon mummy tace "ina na fatima" yana gun aysha "khalid yace" sis barina wuce gayican anfara kiran sallama" fadila tace "ok bye bros" mummy na wuce.



FATEEY YAR MUTAN ZAZZAU 💃
[8/10, 12:36 AM] ‪+234 806 890 2943‬: ❣KHALEED MY BLOOD ❣



NA


FATIMA KHALEED NASHUKA


8⃣


Khalid yana fitowa yawuce sallama bayan yafito wuce gida yana shiga aysha taxo da gudu tana dariya ta rungumeshi yaya nayi murna da umma ta gayamiki khalid yace "hakane sis ngd ina auta" aysha tace " wanka takeyi shiyasa kajita shiru" ok nan khalid yace "umma na dawo" tace sannu daxuwa yasu maman da zainab "duk suna lfy sunce a gaidake" ina amsawa "sega umaima da gudu ta rungume khalid tana washe baki khalid yace" auta kin fito "tace eh yaya ina cikin farin ciki" yace "tnx sis" yawwa ya khalid to yaushe xamuje sayo kayan kwalliya "khalid yayi dariya yace" nan da kwanaki "su aysha da umma sukayi dariya aysha tace" to koh aikin ya fara zuwane bare asiya miki kayan mekeup din "umaima tayi banxa dasu ta wuce khalid yabita yana cewa" haba my sweet sis aikin san zan siya miki koh kirabu dasu aysha kinji "umaima tayi dariya tace to yaya" tajuya tanawa su aysha dariya 😀

khalid yace" kunci abincin ne "sukace aikai muke jira yaya" ok kuzo muje.


yaune takama tuesday ranan da khalid zefara zuwa aiki tunda ya dawo sallah bekoma barciba ya dauko alkur'ani megirma yana karantawa cikin voice dinshi medadin sauraro sewajen 6:30 ya rufe alkur'anin yacire kaya ya shige wanka yana fitowa yatsane jikinshi yaduko vaslin medadin kamshi yashafa yana gamawa ya dauko kayanshi ringa ce orage color dawandon jins yasaka ya dauko kum yataje gashinsa yadauko turaren shi medadin kamshi ya fesa nan yadau kamshi gashi kayan sunyimishi matukar kyau a jiki yana fitowa ya wuce gurin umma saboda abba yatafi gurin gaisuwa ya gaida umma ta amsa su aysha suka gaidashi bayan sun gama bearkfast ne khalid yace "umma zan tafi" umma tace "to khalid nasihata itace khalid duk inda kake karike gaskiya da amana duk wanda yarikesu wallahi bejin kunya a rayuwarshi baruwanka dashiga harkan da baruwanka dama kai bamesan shiga harkan wani bane inkasamu Allah inkarasa kasama zuciyarka Allah ya so hakan, duk a inda kake karike mutuncin kanka da mutuncin kanka ina rokanma Allah ya albarkaceka ya albarkaci rayuwarka da sauran yan'uwanka Allah ya kareka a duk inda kake ya dauraka akan makiyanka ya axurtaka da mace ta gari ya baka yara masu albarka Allah yasa kafara aikin a sa'a" khalid d kanninshi suka amsa da ameen ameen umma khalid ya mike yace "umma na tafi" toh Allah yatsare "ya amsa da ameen umma.


Khalid yana xuwa ya wuce office din senator yayi noking daga ciki akace yes khalid ya shiga yace" good morning sir "senator yace" morning y kk khalid ya amsa "fine ok yanxu bara nakira wanda zenunana office dinka" nan senator yakira waya se gawani saurayi ya shigo suka gaisa da khalid senator yace "wannan ne sabon ma'aikacinmu zaka nuna mishi office dinshi" saurayi ya amsa "ok sir nan suka fito ya nunawa khalid office dinshi khalid ya zauna tare dama saurayin godiya saurayin yace" nima a nan nake aiki sunana hamisu dafatan zamu xama frnd "khalid yayi murmushi ya ok ba damuwa" nan sucigaba da hira hamisu nagayawa khalid yanayin tsarin gurin.



FATEEY YAR MUTAN ZAZZAU 😜
[8/10, 12:36 AM] ‪+234 806 890 2943‬: ❣KHALEED MY BLOOD ❣



NA


FATIMA KHALEED NASHUKA


9⃣


Bayan khalid da a bokinsa hamisu sungama tattaunawa suka fita xuwa sallah bayan sunfito khalid yakuma office yaci gaba da aikinsa har time din tashi yayi yama hamisu sallama ya wuce gida khalid


 yana shiga yayi sallama umaima taje rungumeshi tana mishi sannu da xuwa khalid yace "umma sannu da gida umma ta amsa yawwa khalid ka dawo" eh umma na dawo "aysha ma ta mishi sannu da dawo nan ya wuce dakinshi yayi wanka ya fito yaje yanacin abinci yana basu labarin gurin aikinsa har abba ya shigo yace" khalid kadawo "eh abba na dawo" sannu da dawowa ywwa "toh ya gurin aikin naka" lfy qalau abba "abba ma yayima khalid nasiha meshiga jiki sosai khalid yace" abba nagode Allah ya kara nisan kwana "abba ya amsa" da ameen 👏🏻


Yau ne takama juma'a aysha suna zaune da yayansu bayan ya dawo daga office yace" aysha bari naje waje tace "toh yaya khalid yazo zefita kenan sega fatima tashigo da gudu tana kiran besti din ta aysha kawai tabige khalid tafada kanshi tamike da sauri bata tsaya bashi hakuri ba sobada ita burin fatima taje taga bestin ta har zata wuce khalid riko mata hannu yana cewa "kebakisan kin bigenina" bane fatima tace "kai bakasan damutun a hanya bane baka bani hanya ba 😏khalid yace" lallaima yarinyan nan ina wasa dakene "fatima tace" dama ina nasanka bare har wasa yashiga tsakaninmu nidan Allah kasakeni naje inda xani "khalid yace" amma yarinya bakisanniba "fatima ta fincike hannunta xata wuce khalid ya kara tareta yace" baza kishigaba tunda ba gidan kuba ne fatima tace "aikai gidan kune" khalid ya kwalo ido 😳yace "ke 👉🏻wai ke kinsanni kuwa" fatima tace "yaxa ayi nashuka dan Allah malam kabani hanya na wuce" khalid ya kuma cewa "bafa xaki wuce ba tunda ba gidan kubane" fatima tace" wai kai halan gidan kune xaka dameni daba gidan gidan mubane toh inso kake kaji toh gidan mune semene 😏nide yar mutan zazzau nace kai amma fatima da karfin hali take.


ai khalid tsayawa yayi kawai yana kallon ikon Allah da irin karfin hali na fatima fatima tace "malam kabani hanya na wuce bawai katsaya tunaniba" aysha ce tajiyo kamar muryan ya khalid da besti dinta nata lekowa ta hango kuwa sune.



FATEEY YAR MUTAN ZAZZAU 💃
[8/10, 12:36 AM] ‪+234 806 890 2943‬: ❣KHALEED MY BLOOD ❣



NA


FATIMA KHALEED NASHUKA



🔟


Aysha nazuwa fatima ta hangota suka rungume juna aysha tana cewa "besti ashe kin dawo ni naji murya kamar naki ashe kece" fatima tace "nice besti dawowata kenan nataho naganki shine wannan ya hanani wucewa yau gidan mune shine aishi gidan sune" aysha ta zaro ido 😳tace "besti yaya khalid nefa.

fatima tace" yayanki dakike gayamin "


aysha" ta amsa da "eh besti" fatima tace shine zehanani shiga "aysha tace" toh bashi hakuri mana besti "fatima tace toh tunda besti tace nabaka hakuri to ai sekai hakuri" khalid kuwa ko magana besakeba ya wuce.

bayan sun shiga gida fatima tace "besti kinsan kuwa yanda mukayi da yayanki" aysha tace "aa ni ina daki naji hayaniya kamar muryanki dana ya khalid shinefa naleko" nan fatima ta kwashe komi ta gayawa aysha, aysha ko me xatayi inba dariya ba nan suka cigaba da hira fatima tace "amma yayanki ninya nayi natureshi nawuce" aysha tace "lallema besti yayan namu" tace "Allah de yasoshi" fatima tace "ya maganan bikin karima gobe ne koh" aysha ta amsa "da gobe ne yau zamuje gidan saboda za'ayi walima ankonki nan da umma tasaya miki harmun amso dinkin" fatima tayi tsalle ta rugume aysha tana cewa "amma besti nagode wa umma tanama ina dabanje nagaida taba natsaya magana" aysha tace "taje gidan kakus ita da auta" abba fa "shima yafita" ok kinga besti zamuje gidan su fadila dan batasan na dawo ba "aysha tace" ok bari nadauko hijabina semuje naba yaya key din kar umma ta dawo bamu nan.



FATEEY YAR MUTAN ZAZZAU 😜
[8/10, 12:36 AM] ‪+234 806 890 2943‬: ❣KHALEED MY BLOOD ❣



NA

FATIMA KHALEED NASHUKA


1⃣2⃣


Umma yanxu zamutafi gidan su karima ne wajan walimarta daga nan muyi lalle "toh waxe baku kudin lallen"   "ai umma a bokan ango ne suke badawa" "baruwanku da kula kulan samari kunji koh " toh umma semun dawo" Allah ya tsare "suka amsa da ameen umma suka fito a waje suka gamu da ya khalid zeshigo gida" fadila ne tace yaya barka da rana"  "ywwa barka sis ya kike ya mummy hope tana lafiya" lafiya qalau "ok ina zukujene haka zamu gidan su karima ne" sekun dawo" toh yaya ai baka bamu kudin kashewaba "toh gashi" yaba fadila 200 aysha mahaka sewuce "fadila tace yaya fatima baka bataba" toh ance miki ita tana sone koh bakiga koh gaidani batayiba wannan yarinyan kamar niba yayanta bane amma sotake tarenani senayi maganinta tukunna amma gashi kibata saboda abba" "nibanaso tunda ban rokekaba wai kai seka ringama mutane magana isa isa kamar kaika haifesu" 😏"keni kike gayawa magana zakisani yarinya.


"toh nasani" sis ban kudina soory yaya zamuyi mata fada" ai kubarta daganan gurin abbanta zan wuce nagaya mishi duk abunda take mini" ai fatima najin haka ta zaro ido 😳 "haba yaya khalid aikaine tun rannan seka dinga hararata amma dan Allah kayi hakuri bazan karaba" 😟khalid yaji dadi a cikin xuciyarshi dan yasamo hanyan daxe cimma wata buri tashi cikin sauki, "khalid yace aa baride nagaya mishi seya gayamiki matsayi na a gurinki" nan ta shiga rokosa Allah yayi hakuri tatuba, khalid yayi kamar besan tana yiba "ganin haka yasa fatima tamatso tarikewa khalid hannu tana bashi hakuri," khalid yace kutafi inda xakuje ni daga nanma nafasa shiga gidan gurin abba zan wuce yajuya yafara tafiya,


fatima naganin haka tatafi da gudu ta fada jikin khalid tana kuka tana bashi hakuri shikowa seda yaji wani irin shock a jikinsa, "kinyarda ni yayanki ne baxaki kara mun rashin kunya ba" "eh yaya nayarda "in kika karafa" kagayawa abban "ok shikenan ya wuce seki sakenko kinwani rirrikeni kaman zaki koma ciki" fatima tasakeshi takoma wurinsu aysha dase dariya suke musu "wallahi kunji yanda kirjina ke dukan uku uku kunsan abba bashi dawasa wallahi seya zaneni" sukasa dariya suka wuce, shikuwa khalid tunranda ya fara ganin fatima yaji ya fara santa besan ta kara renashi ne shiyasa yaki gaya mata da ganin ta mishi karama da yawa, bayan sunje gidan biki karima toxo da gudu ta rungumesu "yaushe kika dawo teema" yau na dawo" nan suka cigaba da ganawa da frnd din su na school

nan ango yakira amarya yace taxo ita da kawayanta tagaya musu suka fito suna xuwa suka fara gasawa tunda suka fito wani daga cikin a bokan ango ke kallon fatima har fatima ta fara tsarguwa tacemawa aysha "besti bari nashiga ciki naji kaina nadanmun ciwo" xata wuce kenan abokin angon ya taho "yace yaxaki shige gida banyan bamu gama magana ba.



FATEEY YAR MUTAN ZAZZAU 💃
[8/10, 12:37 AM] ‪+234 806 890 2943‬: ❣KHALEED MY BLOOD ❣



NA


FATIMA KHALEED NASHUKA


1⃣3⃣


"nikabani hanya nawuce banjin dadi ne  " ayya Allah ya kara lafiya amma dan Allah kidan aramin lokaci kadan yanxu zaki tayi" ok badamuwa "suka koma gefe," nide sunana Adam ina zaune a nan can tundun wada dama wallahi tunda naganki naji kiyimin shine nakesan kagayamin gidanku saboda naxo can nasameki "ok nide ban isa fara zanceba dan haka kayi hakuri.


" haba yaxakimin haka dan Allah sena jiraki" fatima takwasa da gudu tayi gida, adam ya wuce gurin sauran abokansu bayan sungama magana da sukayima juna sallama zasuwuce adam ya kira karima "dan Allah wancan kawar taku nakeso fatima amma tace karnaje gidan su" ok bari nakirama aysha" aysha nazowa adam yace" malama aysha karima tagaya miki komiko" eh " yawwa to dan Allah yaxa ayi toh bari nabaka addiress dinmu" ok nagode sosai aysha senaxo" badamuwa" nan ta wuce ciki take gayawa fadila abun dake faruwa sukaje suka samu fatima suka dinga mata tsaya bayan sun gama walimar ammusu lalle suka taho gida suna zuwa.


nan fadila ta wuce gida fatima ma ta wuce gida aysha ma tana zuwa gida "tace umma nadawo mun dawo" "toh sannunku daxuwa yawwa umma "kinga lalle na" aiko yayi kyau" yaya khalid ya fito daga dakinshi "sis kun dawo" eh yaya "umma anjima karkiji ance ana kirana kiyi mamaki wani ne sunan sa adam wai zezo nakaishi gidan su fatima ne" khalid yaji gabanshi yayi wani mugun fadi "kan umma tayi magana khalid yace ubanwa yabiki izinin mishi kwatance au dama aure kukeso bari zan sami abba da maganan" " umma tace toh kai daga tayi magana setacema aure sukeso" toh ni umma saurayin fatima nefa" ok ita kenan kenan kesan auren toh shikenan zanyi magana da abba" umma tace "wai kai khalid meke damunka ne haka gaba daya kawani tada hankalinka"  umma wallahi fatima ba xata aure shiba" yamaxo kofar gidan ya gani" umma de tsayawa kawai tayi tana kallon ikon Allah takuma gane zallan kishi kedawainiya da khalid.


umma tayi murmushi sekuma "tace wai kai khalid ina ruwanka daga yarinya tasamu meso sekaringa wannan tada hankalinka haka" shikenan umma nasan abunda zanyi" karkaje kahana mata samari zuwa gurin ta" aysha de kawai ta tsaya tana kallon ikon Allah a xuciyarta takecewa wai me yaya yake nufine kode yafara san besti ne wallahi dako nayi murna.


FATEEY YAR MUTAN ZAZZAU 😜
[8/10, 12:37 AM] ‪+234 806 890 2943‬: *❣KHALEED MY BLOOD ❣*


*NA*


*FATIMA KHALEED NASHUKA*


1⃣5⃣


Khalid yatsaya yana kallon yanda umma kefada akan abunda bata saniba, "dan Allah umma kiyi hakuri wallahi ba abunda kike nufibane ya kaini hasalima alkhairi ne ya kaini" wani irin alkhairi bayan daga aysha tace wani yana nan xuwa takaishi wurin fatima sekahau fada tunda ga babanta" khalid yayi murmushi "umma aide kinsan babban wah uba ne kuma niki zomushiga daga ciki dan Allah kiji abunda ya kaini" umma tashige ciki khalid ya bita suka zauna "umma damade kinsan cewa duk duniya abba bashi da aminin da ya wuce mishi abbn fatima kuma nasan ko aure natashiyi shizan nema da maganan kamun abba kuma abba zeyi farin ciki da hakan saboda zega tun yana duniya munsa abba shima mahaifin mune kowani irin damuwar mu zamu gayamishi" kwarai kuwa nima nayi murna da kafahimci hakan amma yanxu ya akayi


"umma naje nagaya mishi cewa ina neman aure ne shi nakesan yashige min gaba dan koh abba besaniba" 😳khalid yaushe kafara neman auren a ina budurwar take da bantaba jin labarin taba nasan koni bansaniba aysha zata sani kuma babu wanda ya tabamin labarin a cikin"eh umma hakane yarinyan ma yarkine" wata yartawa" umma fatima mana" fatima yaushe kuka fara soyayya waushema ta dawo garin da harkuka fahimci juna" kodaya umma dan ita kanta batasan ina santa ba nikuma tsakani da Allah nike santa shiyasa naje nasamu abba da maganan" au ita fatima batasaniba shine zakaje kama abubakar maganan dan ya tilasta mata toh wallahi khalid kasani muddin fatima tace batasanka bame mata auren dole tunda haka akeyi bakaje kanemi SO a wurin yarinya ba kajeka fayama abbanta saboda in tace bataso a tilasta mata to baka isaba


"toh umma in tace bata sona fah ita wancan wawan takeso shikuma ya rigani zuwa shiyasa narigashi zuwa saboda nasan koh ya turo abba zece ammata miji" au dahaka kadogara to kuwa kayi aikin banza" umma kawai kitayani da addu'ar dakikasa yimin kowani lokaci.


"ai dama ina maka nakuma nagayama" toh shikenan umma kideyi addu'ar Allah ya xabi abunda zezama mana alkhairi gabaki dayanmu" ameen ameen seka tashi katafi" khalid yana fita dakisa ya wuce ya fa gado yana tunanin idan teema tace bata sanshi yaxeyi gashi umma tace bame mata auren dole shikuwa yazeyi ya Allah kadubi wannan bawa naka kazaba min abunda zezema alkhairi a gareni.


can kuwa abbn fatima yakira abbn khalid yace in ya dawo daga wurin aiki yanasan ganinsa haka koh akayi abba na dawowa daga aiki gidan ya wuce yana zuwa yakira abban fatima a waya yace ya shigo yashiga suka gaisa da umman fatima sannan ya wuce wurin abba bayan sungama gaisawa suka dan taba hira abba yayi gyaran murya "dama abubakar wani abun farin ciki ne yasa memu kuma ni nayi matukar farin ciki da jin abun ina kuma addu'ar Allah yasa hakan yaxama alkhairi dama dana khalid ne yazomun dawani magana me dadi nacewa yanasan a nemamasa aure shine yazo ya sameni daxu" abba yayi murmushi "toh ashe dan naka ya girma" au ashe daukan yaro kuke mishi mutumin da a kalla ya kusa shekara talatin" toh aina yartake zakaje nemamasa auren" ai abun tuwo na maina ne dan yar gida za ayi kanwarsa ce yarka kuma fatima Allah yasa za abamu" abba nan da nan fara arsa tagaru "inde yata naso toh ni banda matsala senace Allah ya sanya alkhairi" nan suka cigaba da tattaunawa daga karke abba yamike yana cewa ni zan wuce gida abba yamika ya rakoshi suka fito yama umma sallama suka fito waje nan suka kara sallama abba ya taho gida zuciyarsa cike da farin ciki mara musal tuwa.



FATEEY YAR MUTAN ZAZZAU 💃
[8/10, 12:37 AM] ‪+234 806 890 2943‬: *❣KHALEED MY BLOOD ❣*


*NA*


*FATIMA KHALEED NASHUKA*


1⃣6⃣


Abba yana tafe yana murmushi jiyake kaman Allah ya mishi bushara da gidan aljanna dan dama ya dade yana tunanin hakan ya tabbata dahaka har ya isa gida yana shiga gida yayi sallama umma ta amsa "umman umaima yau ina cikin farin ciki mara musaltuwa nayi murna da wannan rana da Allah ya kawomu" murmushi umma itama tayi "wannan wace ranane abban khalid har tasaka wannan murna

" mushiga ciki tukunna" suka shige daki nan abba ya gayawa umma duk abunda ya faru tsakaninsa da amininsa "alhamdulilla niyi farin ciki tunranda khalid ya sanar dani amma waini fatima tasani kuwa" ai babanta yace suje sudedeta kansu sedai muce Allah ya hada mana kawunansu ya tabbatar mana da alkhairi da keciki ya kuma karemu sharrin dake cikinsa" umma ta amsa da ameen.


"nasan kinsan abunda ke faruwa tsakanina da teema sis nasan best frnd din kine dan Allah kitayani lalla bata" yaya karkaji komi insha Allahu besti takace amma yaya aiba yanxu zakayi aure ba dan kaga bamu kare karatunmu ba" eh sis nima bayanxu nakesan auren ba saboda inasan nagina gurin zama kuma ni hasalima teema tamun karama yanxu shekarunta sunyi kadan dayin aure yanxu sekun gama school tukunna lokacin tanada 20 year kinga aita girma koh" um yaya kenan wai dama kana san besti ne yaushe kakamu haka" khalid yayi murmushi "sis kinsan tunranda nafara ganin ta nashi ta burgeni sosai kawai inna kwanta senayita markinta koh office naje senayita tunaninta ke danaga abun nasan sani dena aiki sosai sena nemi shawarar hamisu kawai yace nagaya mata ni kuma kinsan bansan raini shiyasa kai tsaye nagayawa babanta saura ita oganniyar tawa Allah yasa ta yarda" insha Allahu yaya besti xata yarda kace ranan zamu kwashi shoki 💃


"da bikinwa zaki kwashi shoki lallai ma yarinya nide yanxu maye abunyi Allah yasa tayi saurin fahimta" kai yaya gaba daya nalora besti nasan saka kazama mara 🙊ke mekikesan cewa nizaki cewa mara kunya" aa yaya banufina ba kenan naga gaba daya lokaci daya kacanza kuma yaya har kana iya zuwa kasamu babanta da zancen" toh sis inban sameshiba waxan samu bagashi sun gane da gaske nakeba" um hakane yaya wai ya khalid kuna kuwa waya da yaya abdullahi kuwa " sosai ma harshi nagayawa zancen my teema yace munma yakusa dawowa cikin watan nan insha Allahu yana hanya" ok Allah ya dawo dashi lafiya wallahi yaya nakosa ya dawo" baki kaini kosawaba" khalid yace sis bari naje gidan su fatima zumujema tare.



FATEEY YAR MUTAN ZAZZAU 💃
[8/10, 12:37 AM] ‪+234 806 890 2943‬: *❣KHALEED MY BLOOD ❣*


*NA*


*FATIMA KHALEED NASHUKA*


1⃣8⃣


A hanya khalid ya gayawa aysha yanda sukafi da teema "yaya ai tagayamin" au kece abokiyar shawarar "eh mana yaya duk duniya besti bata da kawan da ta wuceni dagani se fadila" ok toh kin gayamata tasoni koh "aa nace mata tatsaya taduba alkawarin da tayiwa wani inyaso kai seta baka hakuri tunda kai dan uwanta ne zaka fahimce ta" khalid da sauri ya kalli aysha "au sis dama duk kaunar da kike nunamin na karyane kece zaki gayawa yarinyan da duk duniya babu macen da tamun sai ita cewa tabarni" kan aysha tayi magana khalid ya fizge hannunsa cikin nata yafara tafiya sauri sauri aysha koh abun mamaki yabata shiko yaya wani irin so yakema fatima haka

da gudu tabishi yana ce mishi ya jirata amma ina khalid kojinta bayayi a haka har suka kai gida khalid sallama kawai yayi ya wuce dakinsa dan umma naciki aysha tana shigowa ta wuce dakin umma zatonta can khalid ya wuce tana shiga tayi sallama "har kun dawo ina yayanku" umma nima shina biyo nasha nan ya shigo "ya akayi kuka rabu batare kuka dawo ba" eh umma tare muka dawo shi yarigani shigo wane "seki duba dakinsa" aysha da gudu tayi dakin khalid tana shiga tasameshi kwance a gado aysha tamatsa wajansa "yaya katsaya kaji komi zance maka" mezaki cemin bayan da kanki kika gayamin cewa kince teema tabarni a tsawace yake maganan kitashi ki fita kina jina "yaya wallahi bahaka bane nifa dawasa nake maka amma gaba daya kawani tada hankalinka" tuni khalid yaji wani dadi a ransa ya juyo ya kalli aysha "amma sis bakida kirki gaba daya kinsa hankalina yatashi amma karki kara min irin wasannan" shikenan yaya ya wuce Allah ya baka besti "ameen ameen sis yanxu naji magana.


fatima haka tawuni cikin tunani cande tayankewa kanta mafuta washe gari sunje school sun hadu da aysha da fadila dama aysha taba fadila labari bakaramin murna fadila tayi ba" matar yaya kinzo "fadila bansan haka banzama matar ba kuzomu wuce class" ok bayan antashi aysha tace "kuzomuje gidan mu nabaku wani abu" tab lallema besti ni naje gidanku wallahi bazaniba naje umma taganni kuma kilama yaya yana gida "dalla me umma zata muki kuma yaya yana gurin aikinsa" oho koma zakice wallahi bazani gidanku ba nide se anjima fadila zomu wuce "au haka zakuyi min bakomi" kekuma besti ai dama nasan kinasan yaya "😳waya gaya miki dan nace bazani gidanku ba" toh meye najin kunyan umma aide kawai naga noki san yaya yakamaki "eh naji komi zakice mude mun wuce" su fatima suka taho suna hira fadila tamata sallama ta shige gida fatima taci gaba da tafiya tana zuwa gida tayi sallama umma sannu da gida yawwa kin dawo "eh umma bari nashiga nayi wanka.

bayan fatima ta kimza taci a binci ne umma tashigo dakinta" fatima dama sonake muyi mana kinga khalid dan aminin babanki ne kuma khalid mutumne me mutunci da sanin darajan manya gashi da ibada atakaicede in nace miki khalid bashi da wani abu banyi karya ba dan haka ina baki shawara a matsayina na mahaifiyarki kiyarda da auren khalid koba komi yaranki zasuyi murna da zaba musu uba nagari" shikenan umma insha Allahu zanyi amfani da abun da kika gayamin "yawwa fatima Allah ya miki albarka ya kuma zabi abunda xexama alkhairi" ameen ameen umma.


FATEEY YAR MUTAN ZAZZAU 💃
[8/10, 12:37 AM] ‪+234 806 890 2943‬: *❣KHALEED MY BLOOD ❣*


*NA*


*FATIMA KHALEED NASHUKA*


1⃣9⃣



Bayan kwana biyu dayin haka khalid yaxo gidan su fatima yashiga suka gaisa da umma "umma fatima nan" eh tana dakinta kashiga "toh" khalid yashiga dakin fatima a zaune yasameta tana game da wayan umma yayi sallama ta amsa "anban izini nashigo" seda kashigo zaka nemi izini "ai umma tabani izinin shigowa nasan tasan bawata matsala ne tace na shigo saboda naga dana shigo daga dakin nan ta fito kinga kuwa da ace tasan baki cikin shiri zatace bari ta gaya miki" um haka ne "dan Allah kixo palour din abba ina jiranki kiji my teema" ok ganinan zowa" khalid ya juya ya fita fatima ta dauko hijab fabi bayan shi.

bayan tashiga ta zauna batace komiba "my teema ba gaisuwa" au anyini lafiya "seda naroka" toh ya hakuri "shikenan dama kinsan yau nace miki zan dawo koh to gashi Allah ya dawo dani yanzu dai kenake jira naji ra'ayinki Allah yasa nayi dace da wannan rana" um nide Allah ya zabi abunda xexama alkhairi "ok inna fahimceki kin amince" um "waike baki magana ne sai um" itade fatima shiru tayi mishi "shikenan my teema Allah ya tabbatar mana da alkhairi" can kasa ta amsa da ameen "shikenan nikinsan bazuwa tadi zaringa yiba kinga yanzu baki isa soyayya ba dama nayi magana ne dan kisani dan haka kimeda han kalinki a karatunki Allah kuma ya bada sa'a" ameen" shikenan nizan wuce Allah ya shige mana gaba "ameen


Khalid ya fito yama umma sallama ya wuce yana zuwa gida ya gayawa umma duk yanda sukayi umma tayi murna tare da fatan Allah ya xabi abunda zaizama alkhairi" ameen umma Allah ya kara girma

gaba daya family dinsu kowa yasan lamari khalid da fatima, fatima ne zaune a school tare da aminan ta "wallahi kunsan wani abu" sekin fadi "um wallahi dazu aunty nafisa takirani a wayan umma take gayamin cewa wai abba nan zuwa wannan saurayin nawa na can kano shine narasa yazanyi" ita ba tasan da zancen yaya bane "eh bata saniba umma tace setazo sesuyi zancen kuma wai gobe zaizo" shikenan Allah ya kawoshi lafiya seki gaya mishi komi "wallahi kunyan gaya mishi zanji wallahi seda yace namishi alkawari kuma namishi danni banyi zatan haka ze faruba

" toh yanzu yazanyi "karki damu besti" insha Allahu ba abunda ze faru" shikenan bari naje gida sena gayawa umma "ok kuzo mukoma class" suka mike suka wuce class bayan antashi kowa ya wuce gida bayan fatima tagama kimtsawa taje tasanar da umma komi "shikenan fatima Allah ya kawoshi lafiya ammade khalid bazezo goben ba koh kinga bazeji dadi ba kumashi inyazo kisanar dashi komi da kanki kinga inna fara gaya mishi ze iya cewa wannan shirinmune kinga kuma zega kaman wulakanci kika mishi kuma wula kanci ba dadi haka.


FATEEY YAR MUTAN ZAZZAU
[8/10, 12:37 AM] ‪+234 806 890 2943‬: *❣KHALEED MY BLOOD ❣*


*NA*


*FATIMA KHALEED NASHUKA*


2⃣0⃣


Yau ne takama rannan da abba zezo fatima tashirya mishi abinci kala kala natarba itama tashirya tsaf can wajan 10 :30am ya sauka a garin ZAZZAU GARIN ILIMI da kwatance da kwatance har yakawo unguwan su fatima yana xuwa ya kirata a waya dan aunty nafisa tabashi number din umma bayan ya kirata yagaya mata inda yake ta gayawa umma tafita can ta hangoshi tunda ya hangota yake sako mata murmushi ta karisa "barka da isowa" yawwa barkanki "toh muje koh" um yanda kikace "suka kariso gida suna shigowa fatima ta kaishi wajan umma

bayan sun gama gaisawa umma ta kalli fatima" kikaishi palour din abba "toh umma" nan suka karisa fatima ta zauna suka gaisa ta tan biyeshi iyayansa da yan'uwansa "duk suna lafiya kema nasameku lafiya" lafiya qalau "ok" nan suka cigaba dahira fatima ta mike ta gabatar mishi da abinci abba yaci abinci ya cika cikinsa yanata mata santi fatima koh se murmushi take masa bayan ya gama ne suka ciki gaba da hira "fatima ya maganan mu shiyasa nataso nazu dan dan nakara tabbatar miki da inanan ina jira kuma kigane cewa narike alkawari Allah yasa kema haka gurinki" fatima tadanyi shiru nawasu lokuta "abba baxan boyema komi ba saboda tsakanina da kai ba yaudara" hakane fatima "ina jinki" kan fatima tayi magana wayar abba ta fara neman agaji "bari nadaga waya fatima oga ne kekirana" ba damuwa "abba ya daga waya can ya ije ya kalli fatima" dan Allah fatima kiyi hakuri wallahi banso hakan ba naso yau mu fahimci juna sosai amma yanxu oga kegayamin cewa yana nemana da gaggawa kinga dole nawuce yanxu


haba abba kabari mukarisa maganan mu mana "wallahi fatima dole natafi yanzu amma insha Allah next week ina hanya" abba yamike suka fito ya kalli fatima "umma fa" fatima ta leka ciki bata gantaba tafito "au ankirata nan makociyarmu zata haihu bari nakirata" aa kibarta intazo kicemata na wuce kinga sauri nike" suka fito daga kan da fatima zatayi suka hada ido da khalid shikuma abba yana mata sallama zeshiga mota yashige mota fatima tana mishi fatan Allah ya saukeshi lafiya.


bayan tafiyan abba fatima da gudu tashiga ciki khalid ya biyota "teema waye wancan naganku tare" um um yaya dama um a kano yake "saurayin kine kenan" um amma da "yanxu gunwa yazo" um guna "haryanxu kenan kuna soyayya" um aa "toh tsaya kiji fatima cikin tsawa khalid ke magana wallahi baki isa kina tsayawa da kowa ba nine mijinki ni daya duniya da lahira insha Allahu fatima kisan hakan" ya juya ya fita fatima ta koma gefe tana sauke ijiyan zuciya tana haka sega umma tashigo "au fatima ina kikabar bakon" um umma ai ya tafi "har ya tafi" eh umma nan ta gaya mata yanda sukayi amma batace khalid ya gansuba

shikuwa gogan naku yana zuwa gida ya fada gado yana tunani yanxu dama fatima nada saurayi dole yasan abunyi ita kuwa fatima gaba daya takasa samun natsuwa bataji dadi ba da bata gayawa ya khalid komi ba.


FATEEY YAR MUTAN ZAZZAU

Download Books Here