Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 67
       By
Gentle Lady💃🏽



Tace indai wannan ne karkisamu damuwa indai akwai shegun to komai kikeso zakisamu aidama tsiyar abu rashin kudi gashi kanagani Abu yafikarfin ka

Amman idan akwai kudi hmmm komai kikeso zaki iyah tambayarsa kidairike sharadansa nazuwa wajensa sannan  kuma duk abunda kikagani adajin tsapappene kar wani karambani yajaki kitaba Tam

Rukayya tace nikam mezantaba Kawata ??? Tayi maganar tanarike habar gemunta tace nifa ko acikin kaset naga boka jikina har ciccira yakeyi saboda tsoro ballantana kuma inga wannan da idona"" tabdi kedai kawai muje

Asma "u tace waikina nufin yanxun??? Hmmm kinsan kowacce kasa yake kuwa??? Rukayya tace shinbama kasar nan yakeba???

Asma "u tace babbar magana aiyafi karfin zama anan kenan cikin arha zakisamu komai tobari kiji taraba yake
Rukayya tawaro ido tace tarabadai tarabadai wacce nakeji anafada???

Asma" u tace kawaimakuwa itah"" rukayya tabuga tagumi tace Toni tayama zanje taraba nidabantaba zuwaba???

Asma"u tace nima kaini akayi gashikema zankaiki bake daya zakiba dazakice kinbace hanya"  rukayya tace bazaki ganebane"" taya zansanarda Muhammad zantafi taraba??? Wlh bazai narniba""

Asma" u tace Amman ke bahwanyace inbanda haka tayazaki sanarda miji ainahin inda zakije barikiji dazaran kinkaida kudin kamar anasaura kwana uku kicemasa Na gaiyaceki biki garinmu Kanwata za ayi aure wacce take hannun yayar mamana  kaduna take

Kinga kwana biyu zakicemasa dazaran munje muyi abunda yakaimu mudawo koyakika ganie
Rukayya tace kinkawo shawara maikyau Amman Anya zaibarni naje waniguri inyi kwana biyu??? Asma"u tace barikai aiyanzu yanda yakeson fateema wlh koda wata daya zakiyi bakidawo ba bazaiwani damu sosaiba

Rukayya tayi shiru sannan tace kinga inayin wani dashi kuma jibi za ayi kwasa tawace inaganin kawai saimu tafi tace shikenan dazaran kudin sunshigo hannunki saiki kirani kiyimun magana"" tace shikenan sukai sallama tawuce gida

Allah yasa Muhammad baidawoba da sadade takoma dakinta danko sallama batayiba ko Fateema batasan dafitar tata

Illaikuwa tana karbar kwasarta tasanarda Muhammad zataje garinsu kawarta Asma u kanwarta za ayiwa aure yace shikenan kwana nawa zakuyi tace biyu nakeji yace shikenan yadauki dubu hamsin yabata yace tayiwa Amarya sayayya tayi murna sosai dama tana tunanin kudinta kamar bazasu isah ba""

Washe gari tashirya dama tasanarda Asma "u Fateema tayimata Allah yakiyaye tace Ameen"" aranta kuwa tace hmmm bakisan wannan tafiyar ta kibace ta musamman
  Tanafita tayi gidan Asma "u tasameta hartashirya itakawai takejirah tanazuwa suka wuce dayake tasha suka shiga motar bawai jirgi bane basu suka kai taraba ba saikusan goshin magrib

Rukayya tace itakam tagaji susamu gurin kwana"" Asma u tace nifa duk nazo garin nan gidan wata magajiya nake kama hayar daki kinsan hotel akwai tsada idankuma kinada kudi isassu saimuje

Rukayya tace sujedai gidan magajiyar suhuta kafin magrib hakan kuwa akayi sukaje cen dama tunda bajimawa sukeyiba dakin magajiyar takebasu Dan ita ma tana dai dagacikin costomomin *hatsabibin boka* duk wacce tsautsayi ya Kaita fadawa hannunta hardai idan taga kinaja anasamun kudi akarkashinki haka zatakai sunanki wajensa atsafeki akafeki gidan tayanda bazakisake dagawa wurinba harsai idan kinmutu

Duk wacce akaiwa auren dole tagudu kokuwa tsautsayi ya afka kanta tayi ciki kafin aure idan tagudu daga GIdan uwayenta tashiga  duniya

Tahaduda tambai yarduniya tokuwa tazama nama"" akwai wani kwalli datake bawa yaranta suna shafawa Wanda takarbo wajen *hatsabibin boka* muddin suka shafashi dasunyi ido hudu dakai tosaidai wani kariyar Allah idankuma harkasoma harka dasu bazakataba bariba

Danduk kakwanta dayaranta bazatasake jindadin mu amala dakowacce maceba"" takenta kuwa yaranta bawai saida dare sukefita kasuwancinsu ba
.sunazuwa kasuwanni dakuma manyan kantuna inda sukasan manyan attajirai sunazuwa hakazalika sunazuwa bikin manyan yankasuwa

Dakuma gamnoni kodakuwa ba agaiyacesuba saisunje Kuma ba ahanasu shiga kodakuwa basuda ticket din shiga

Suna zaune sunazuba firarsu rukayya tamike danjin ansoma kirah asma"u tace inakuma zakije?? Takalleta da mamaki tace banganeba sallah zanyi bake kikace da anyi sallah zamu wuceba

Asmau da magajiya suka bushe da dariya magajiya takalli asmau tace wannan dai sabuwar zuwaceko??? Asmau tace ah wlh bakigantaba sai ahankali

Takalli asmau tace inasharudan da nafadamaki kafinma muzonan??? Ita rukayya sam tamanta
Tace kash wlh namanta Kawata"" Asma u tace akwai aikikuwa wlh idan kikai kuskure baburuwana dake dashine dannafada maki duka dokokinsa kikace kinji kinganie

Rukayya ta marairaice fuska tace yazakice haka aikinsan daban mantaba bazance namantaba waye baya mantuwa aduniya

Asmau tace kowa yanayi Amman inaso Kituna da abudaya wlh *hatsabibin boka* baya yafiya duk kikai masa laifi babu imani zaihukuntaki danhaka kikama kanki mufita lafiya kodai ince kekifita danni qalau zanfita

Rukayya tace tonima ai idankuma  harwani abu zaisameni ai anyi ba ayiba kenan ina amfanin badi barai"" kedai kawai kisake sanardani zankiyaye asmau takalli magajiya wacce taketa busar dariya itama tadarasuka tafa sannan tasake korawa rukayya bayani
 Ana kare sallah suka kama hanyar kauyenda yake  bakin hanyarda zata sadasu  da dajinda yake aka saukardasu suka kama hanya harsuka iso fadarsa dajin dai yana nan kamardai yanda su lubcy sukazo saidai akwai wasu sauye sauye


Danyanzu duhuwa tayiwa wajen yawa kaikobakin dajin ka iso dole katsorata gabadaya yanzu yatsafe dajin kogonda yakecikima yanzu koda kazoma baka ganinsa tayama zaka iyah shiga dajinda yake dauke damiyagun namun jeji da abubuwan firgitarwa

Kafin kakaima tsakiyar dajin kagama yawo saidai uwarka tahaifi wani""" haduranda sukecikin jejen bazasu faduba saidaikayi kokarin hana kanka zuwa gurin

Abudayane zaitserar dakai idan yasan dama wajensa zakazo kodahakan ma saidai katsaya bakin jejin karufe idonkaa saikakirah sunansa takezakaji anyi sama dakai karka kuskurah kuma kabude idonka   idankuma kabude

Namun jejin dakuma miyagun gungun aljanu masucin naman bil adama sune zasuyi kalaci  danamanka yaga yaga za aimaka tayanda kowane guntun naman jikinka bazaiwuce tsoka dayaba""

Dakaji iska talafa bakamar sanda aka surekuba saikabude idonka take zakaganka kabayyana agaban *hatsabibin boka* idankuma zakubar dajinma hakane anan zakurufe idonku saikuji ansake sunkutarku koda zakubude ido kuganku bakin dajin daganan saikuwuce abunku

Asmau tasanarda rukayya yanda zasuyi kuma tace karta kuskurah  tabude idonta rufe idonsu keda wuya sukaji ansunkuceku anyi sama

Sauran kadan rukayya ta kwamtsa ihu"suna bacewa bakagansu ko inaba saicikin babbar fadar *hatsabibin boka*

Naga sauyi sosai awajen gakuma kayan alatunan tako ina saikuma tarin kayan tsafinsa rukayya tanayin ido hudu dashi jikinta yasoma rawa

Asma u itace tasoma koramasa jawabi kafin yace tayi shiru yasan komaiketafe dasu

Yamaida dubansa wajen rukayya yace mekikeso ayimata??? Tace sonakeyi asaka fitina datashin hankali atsakaninsu banaso tabargidan farat daya yan uwansa zasu iyah zargina

Itakuma inaso kowa yatsaneta harta mutanen unguwarmu saita gammace mutuwarta akan rayuwarta yayanda take takama dasu suma surika gudunta

Daka karshe idantagama wulakanta saiyasaketà alokacin duka yan unguwa dama ta ishesu sai kafitarda duka soyayarta azuciyar mijina

Bayan tagama korah jawabi *hatsabibin boka* yakece dawata mugunyar dariya tamkar jakiii nakuka yace wannan babu abunda yafishi sauki awajenmu

Shanruwa ma zaifishi wahala"" yace menene amaryarki tafiso ayanzu??? Rukayya tayi shiru alamun tana nazari 🤔sannan  tace agwaluma da gwaiba

Yagirgiza kai yace bashiba"" tayi shiru dagabisani tace mangwaro  gaudee yace todashi za ayimata maganin

Rukayya tace to Amman inaza asamu mangaro ayanzu tunda balokacinsa bane *hatsabibin boka* yace wannan aikin mune banakuba dazaran kunkai gida zakisamu mangwaron ajakarki saikibata tasha


Zamusamu mujiya dakuma makauniyar jaba da itah za ahada ayimata maganie yandakikasàn mujiya hakazata koma cikin al ummah ke mujiyamà saitafita gata dankuwa zatarika fitarda wàñi wari Wanda makotankuma saisungaji da doyin sannan zamubaki wata laya kijefa amasai

Dazaran kinyi wannan aikinki yagama







Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 68
       By
Gentle Lady💃🏽


 Maganin wannan layar kuwa dazaran kishiyarki tabuda baki daniyar yin magana wa mijinki wani mugun doyi zaiji kamar ya surnana hancinsa acikin shadda""  rukayya batasan sanda tayi dariyaba cikin jindadi tace tomenene ladar aikinka ??? Batareda ya kalletaba yace yar uwarki tasani saita sanardake tajuya daniyar yiwa Asma u tambaya yadaka mata tsawa wacce tahargitsamata kwanya yace ba anan zakiyi maganaba kibari saikun bar nan kubacemun daganie

Atsawace yayi maganar asmau tace saikirufe idonki rukayya dajikinta yaketa faman rawa tayi saurin rufe idonta saikuma akasuresu saibakin dajin

Ai rukayya. Tanabude idonta taganta bakin dajin tayanka dagudu daniyar komawa cikin dajin dantafirgita tuncikin fadar bokan saida Asma u tayi saurin riketa  tajata dasauri sukabar wajen zuwa bakin hanya

Dakyar sukasamu motarda tamiyardasu  gidan magajiya rukayya saida taganta gidan tasoma saukarda numfashi  ko abinci batatsaya ciba takwanta barcin wahala yasureta su magajiya sai dariya suke Dan asmau tafadamata yanda sukayi da rukayya

Washe gari kasuwar garin sukaje tasiye dabbobin ta aikamasu dasu tacewa rukayya kinga yanda zakiyi duk lokacinda kikasake dawowa rukayya ta kwalalo ido tace wa???😳 Badainiba aiduk Wanda kikagani lafirah kaishi akayi wlh nishegen tsorone dani ni inama tsammanin sanda yadakamun tsawar nan anyama basuma nayiba?? 🤔

Gaskiya inhar aikin nan yayi aini shikenan banida  wani buri aduniya indai tabarmun gidan to mezai miyardani"" ?? Asmau tace akwai kuwa Kawata kinmanta akan kishiyarki kawai akayi aiki to idankuma yasake auro wata anan gabafa??? Rukayya tanisa tace kumafa hakane Amman anya zan iyah zuwanidaya wlh natsorata sosai bantaba shiga tashin hankali irin wannan ba"'  Asma"u tace nafarkone aibazaki  sake jinhakanba

Tace shikenan garin suka sake kwana washe gari sukadawo gida "" saida tahuta gidan asmau sannan tawuce gida da sallamarta Tashiga gidan tasamu fateema zaune tanashan iska da itah da muktar Dan gwaggo takarbi faruq ..

Tana ganinta tasaki fara a la Anty sannu dazuwa wlh yanzun nan nakezancenki araina inatunanin kokin taso"" kujerah taja tazauna tanacire hijab tace wlh kuwa tunsafe mukataho yazaman gidan

Fateema tace babuwani dadi gashi abban faruq anturashi wajen wani aiki jiya Amman inajin gobe zaidawo duk zaman gidan ya isheni gashi ban tambaya ba dasainashiga makota

Rukayya tace Karma kisoma bakigani nikaina baburuwana dashiga makota yanzufa duniyar nan mutum akekiyo ba dabba ba

 Fateema tace aibama zanfitaba"" rukayya tasaka hannu cikin Jakarta saikuwa ga mangwaro guda biyu tafitar tanacewa ga abunda kikafiso nasiyomaki ai fateema tanayin ido hudu damangwaro yawunta suka tsinke""  abunkada maiciki tanakarba batawankeba babu maganar bisimillah kawai takama gabtar mangwaro

Wani shu umin murmushi rukayya tasaki aranta tace taki takare fateema "" nantake tashanye dayan tadauko dayan tafasa sai muktar yaceshima sai tasammasa takilla tabashi kamar rukayya tahana saikuma takyale dankar fateema tadauka akwai wani abun

Ta sake gabtar mangwaro tana lunshe ido saboda dadi tace wai Anty ina kikasamu mangwaro alhalin yanzun balokacinsa bane???

Rukayya tadauko bokiti tace baridai inkara maki dankarki fadi tana dariya tace bafa santi nakeyiba kumama koda santin nayi aibalaifi kinkuwaji yanda mangwaron nan yakeda zaki???

Rukayya tace inazansani aikinsan nibanashan mangworo"" fateema tace hakane naman ta wlh hartashanye mangwaron bata ahamoba tacewa rukayya dakinsani deyawa kika siyomun

Tace ayya wlh nima akan hanya naganshi sauranshikawai danasan kina sonsa sosai nacewa driver yatsaya dakyarma nasamu yatsaya""

Fateema tace Allah sarki nagode Anty"" rukayya mikewa tayi tace baridai indan mike kafata kafin la asar barci nakeji wlh fateema tace tosaikin tashi tawuce dakinta tana murmushi

Washe gari tundasafe tajefa layar acikin masansu tazuba ruwa yabiruwa yafada cikin shaddar dadare koda Muhammad yadawo fateema tayi barci baiko kalli kofar dakintaba yashige bangarensa

Rukayya tana ganinsa tahau tsallen murna washegari dasafe tanadaki saiga fateema tashigo tana yakunar fuska tasamu guri tazauna tagaida itah ta amsa dasakin fuska

Saikuma tayi shiru rukayya tace yadai maman faruq??? Kamar tayi kuka tace Anty ashejiya abban faruq yadawo Amman baitasheniba

Rukayya tace ah watakil  yalurah kinajin Da din barcinne"" tanisa Anty aibahakan yasababa sai idan yanzune zaisauya""

Rukayya tace toki kirashi mana"" nimadai jiyan banganshiba saidasafe danaga kaya afalo nasan yadawo

Fateema tace wlh nakirashi yafisau ashirin yaki dagawa bansan laifinda naimasaba"" rukayya tace kisake gwadawa dai haka fateema tayita gwadawa hartagaji takoma dakinta

Yinin ranar takasa cin komai harwashe gari kwanadaya rak hartasoma ramewa"" tana tsaka datunani kawai saiga Muhammad yafado dakin dasauri takalleshi kamar zatayi kuka

Yanayinda taganshi yamatukar furgitata kafin tamike yahau dukanta batasan hawaba batasan saukaba tuntana yunkurawa daniyar tatashi tagudu hartakasa tayi kwance shikuma gabadaya bayagani yasa kafa yahalbeta  aruwan cikinta wata mugunyar karar wahala tasaki take jini yasoma fita takafafunta Muhammad baikyaletaba saida yaga bata numfashi sannan yayarda bulalar yafitaa fuuuuu

Saida yafita rukayya tasadado taga aika aikarda yayi damakuwa tanaganin zuwansa tashige dakinta ganin tanamasa magana yawuceta fuuuu dariya tasheke  da itah tace inakuma soyayyar take ayanzu???

Muktar yana gefe yana kuka yanakirah amma rukayya tadaka masa tsawa tace munafuki rufewa mutane baki"  muktar yasake bare bakinsa yacigaba dawani kukan saida tasake katsamasa tsawa wacce tafirgitashi shima atake yaja zuciya numfashinsa yai sama

Ta sake bushewa da dariya sannan tafita tadibo ruwa ta yayyafamusu kusan taresuka far fado muktar yashige jikin fateema yana kuka

Fateema bayan tagama nazarin abunda yafaru da itah Wanda take gani tamkar mafarki"" tasake fashewa da kuka"" mai tsuma zuciya

Takalli rukayya tace Anty me yake shirin faruwa danine haka?? menaiwa Muhammad yayimun wannan dukan kamardai Wanda bashida imani??

Rukayya tace waikina nufin shine yadakeki?? Toyanibanji shigowarsaba fateema tace wlh shine Anty

Rukayya tace kekuwa laifin mekikai masa??? Tace wanne irin laifi Anty wlh banyimasa komaiba"" rukayya tace to Allah ya kyauta tawuce abunta fateema tabita da kallon mamaki kamar bataga halinda take cikiba ""

Rukayya tanafita  takirah asmau tanadauka tace yee Kawata aikifa yanakyau"" asmau tace  banafada makiba

Tace ainagani yau Muhammad yalakadawa Yar iska shegen duka inajifa kamar tayima bari"" asmau tace toyanzu tana ina??? Rukayya tamere baki tace tanadakinta kwance inda yabarta

Asma u tace yazakiyi haka aizatayi saurin zarginki banafadamaki dakissa akehadawaba yanzu kidauketa kuje asibiti dagacen kicema ayimata wankin Mara idan akwai sauran Matsiyacin yayo waje""

Rukayya tace toshikenan dasauri takoma dakin tasamu fateema tasake suma"  fita tayi dasauri tasamu Dan tax dataimakon wata makociyarsu aka kai fateema asivibiti

Likita yatambayi menene yayi sanadin zubewar cikin??? Rukayya tace aifaduwa tayi Amman ayimata wankin Mara karyazama ciwo ajikinta"" alokacin har anjona mata Karin ruwa

Suna nan harkusan la asar lokacin fateema tafarfado Amman bata bude idontaba"" tanata tunanin wannan lamarin""" kwananta uku asiviti Muhammad bailekoba gashi likitoci sunbar zuwa gurinda take kaibartasuma har wadanda sukejinya daki daya duk sun sauya daki

Aladole tasallami kanta tafito duk Dan adaidaitan da tatara baya tsayawa gashi jikinta baiyi kwariba tana tafiya tana tsayawa tana hutawa hartakai gida

Gashi tafiyace mainisa ajigace takarasa gidan tashige dakinta tafadi kwance tafasheda kuka muktar ne taji yadafata tadago takalleshi duk yayi damau damau cikin kashi tasake fashewa da kuka maitsuma zuciya saida tayi mai isarta tahakurah dankanta

Dakyar tatashi tashiga kichin dinta tasulala taliya sukaci bayan tawankemasa jikinsa haryanzu bataji duriyar rukayyabà Ashe tana makota tabar muktar shikadai cikin gidan

Wasa wasa fateema abusai gabayake batajin sanyi wajenkowa saiwajen rukayya danyanzu saitakwashe watadaya batasaka Muhammad a idontaba

Duk ranarda abun yacizoshi zaizo yayimata shegen duka gabada ya yan uwansama sundauke kafarsu daga gidan

Gashi tanada zurfin ciki ballantana takirah tasanarda su Anty hasana halinda takeciki saidai ciwo yayita cinta ahankali""


Kwanaki sunata tafiya sati haka watanni haka shekaru haka fateema ta lalace tayi bakiii kirin wacce takefara"" alokacin muktar shekaransa shida aduniya yayi wayo sosai hakazalika shine kawai kedan kwantarwà fateema dahankali

Watarana dadare tanakwance zafii yadameta tatashi tawatsa ruwa tadauro alwala"tanashirin kwanciya saiga Muhammad yafado kamar dagasama

Tatsorata daganinsa dantasan babu abunda zaikawoshi dakinta idandai badukanta zaiyiba






Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠



Chapter 70
       By
Gentle Lady💃🏽


Yanisa yana kallonta yace kikwantarda hankalinki yata nine nan zankwatomaki yancinki"" tayi saurin kallonsa tace taya baba aikuma aikingama aiyagama""
Yace ninasan yanda zanyi zanmiyar mata da abunda taimaki"" inhar kin amince dahakan"??? Taja majina tana kallonsa tace idan har nayarda amiyar mata da abunda tamun menene banbancina da itah???

Tanisa ninabarta da Wanda yayi rana dakuma faduwarta koda nayarda amayarmata tunda babu aure tsakanina da Muhammad aikin banzane nikawai nabarta da mahaliccinta indai duniyace aigata ga duniyar niyauma zanwuce garinmu danba kinciki zai iyah kasheni anan idan inatunoshi

Malamin yayi murmushi yace hakane yata dama nayi tunanin hakan Amman tundakince  kinbarta  da Allah bariga Allah yafi" yagyara zama Amman kitsaya kikwana biyu akwai taimakonda zanbaki kafin kitafi""

Tashare hawaye tace kayi hakuri baba niyau gida zantafi"" banason sake kwana garidaya dashi malamin yace dolefa kiyi hakuri dantafiya bata samekiba. Kinkuwasan abunda ketare dake barta mijinki ko yan uwanki idan kikaje babuwanda zaikalleki dankuwa abunda yake ajikinki kokinfita babu mai motarda zaidauke ki kinkosan bazakije gida akafaba

Fateema tayi shiru kamar mai tunanin wani Abu saikuma tace shikenan zata zauna"" tundaga ranar malamin yasomayimata  rubutu tanasha dawani garin maganie"" dayayiwa hadi da habbatus sauda da turaren miski dawadansu kalolin turare yahada dazuma farar saka akadama daruwan zanzan kullum dasafe saisunsha chokali daya

Da itah da mukhar harnatsawon sati daya""  bayan sati daya saigashi tasoma wani irin a mai baki kirin da gudajin mangwaro aciki hakashima muktar ammanshi bayawa sosai danshi baici dayawaba yanayin cizawa daya yaji tsami saiya Yar

Abunda tagani yanzu shine yasake tabbatarmata da gaskiyar lamarin"" saida tasake kwana biyu malamin yayimata kudin motar saida zata tafi tarambayesu sunansu

Matar tace sunanta khadija mijinta kuma ibraheem ta sake yimasu godiya harwajen shiga mota yasa aka Kaita tundasuka shiga motar tashiga duniyar tunani harsuka kawo kano

Tahau Dan adaidaita zuwa unguwarsu koda tashigo duk yawanci suna masallaci wajen sallar magrib dasallama  tashiga gidan tasamu matar Yaya garba tana kada miya

Ta amsa sallamarta tataso taga kowacece tanaganinta tace yarbaba !! Kece da magribar  nan lafiyadai??? Saikawai fateema tafashe dakuka tafada jikinta

Tace yau nabani nidiyar mutum biyu jikar mutun hudu menene kuma yafaru yarbaba"" ??? Fateema batace komaiba taci gaba dakukanta anahaka garba yashigo dasallama yayi tsaye yana kallonsu yace kukan wanakeji kamar yarbaba???

Bilkisu tace wlh itace malam niduk ta tayarmun dahankali "" jinta ambaci sunan yarbaba garba yazoda sauri shima yahau tambayarta jikinsa harrawa yakeyi danyana tsoron ace abunda mahaifiyarsa tayiwa mahaifiyar fateema shine aka sake maimaitawa

Fateema yanda taga hankalinsu yatashi saijikinta yayi  sanyi anan take sanardasu  aurenta yamutu sukai tambayar duniya tafadamusu meyafaru haryasaketa tace laifi tayimasa takisanar dasu komai harsuka gaji sukasamata ido

Dakin ta tashare takoma ciki washe gari su hasana sukazo suma babuyanda basuyiba Amman bandakuka datakemasu idan sun matsamata da tambaya dole suka kyaleta garba yaso yaje yola din

Fateema tace karyaje tunda saki uku yamata menene amfanin zuwan tunda koyahakurah bakomawa zatayiba

Aranta tace aikoda akwai sauran igiyar aurena dashi bazan komaba ballantana komai yakwabe yace shikenan

Ahakan tacigaba darainon cikinta haryafito batafirah dakowa inba muktar ba"" gashi ciwo yanacinta gayawan tunani"" cikinta yana shiga wata tara tasanarda matar  garba in Allah yasauketa lafiya intahaifi mace khadija takeso asamata idankuma namijine ibraheem

Bilkisu tace banda abunki kibari saikinsauka mana saikifadawa yayanku"" murmushi tayi Wanda rabonta dayin irinsa andade tace inaso komenene nahaifa asakashi islamiyya inaso yayi karatun sosai kullum maganarta kenan

Ranar wata juma" a cikin dare tatashi da nakuda muktar ne yasheka yana bugawa su balkisu kofa dama bawani barci mainauyi takeyiba dasauri ta mike tafito waje

Dakin tashiga dasauri tarufo kofa  fateema tayi matukar galabaita tafita hayyacinta saikusan asuba tahaihu

Kojuyowa batayi taga abunda tahaifaba raiyayi halinsa bilkisu taduka tadauki Yar tayankemata cibi tawanketa tagyara wajen garba yanakofa tsaye da muktar yana kuka

Saifita take tana dawowa tadaicemasu ansauka ansamu mace Amman batasanardasu. Yarbaba tarasuba saida tagyara wajen tashirya jaririyar takuramato ido yarinya tamkar uwarta babu abunda yarabasu
Hawayen tausayinta ne suka sauko akan fuskarta Allah Sarki kekuma taki jarabawar kenan fita tayi tabasu yarinyar takoma takimtsa fateema

Fuskarta  tayi haske fayau tamkar tana murmushi kamar kayi magana ta amsa rayuwa kenan "" rayuwa bawani abubace dazaran anzaremaka  rayuwa takomai takare

Duk kwanbonka komai kudinka saifa kadandani mutuwa menene abun dagawar ??? Dazaran anzaremaka rai yanda kasan mutum mutumi haka zaka koma shikenan taka kuma takare babu sauran jindadi masu bururruka aduniya Allah yasa mucika da imani Ameen

Tadade dakin sannan tafito garba yace yamai gejon tana lafiyadai ko ??? Tagyada masa kai kawai alokacin hawayenda take boyewa suka karasa sauko wa takauce idonta danta goge Amman haryagani dasauri yashiga dakin tana kwance inda tahaihu ahankali yataka zuwa inda take yaduka yashafo fuskarta yace Allah Akbar Allah yasa kinyi kyakkyawar tafiya yatofa mata addua sannan yamike alokacin ansoma Kiran asuba

Yakarbi yarinyar yayimata huduba da sunanda mahaifiyarta tace yamikawa  bilkisu yakalli muktar yace muje kayi alwala muwuce masallaci bamusu yawuce yayi alwala shima yayi sukatafi masallaci

Bayan an idar yasanarda liman akayi sanarwa za ayi za na izarta da karfe goma muktar baisan meyake faruwaba saida yaga mutane sunsoma cika gidan sannan hankalinsa yatashi yatambayi garba meyake faruwa ne

Bawani boye boye yasanarda shi yayi tsammanin zaiyi kuka saiyaji kawai yace Allah yajikanta yamatukar bashi mamaki gashidai karamin yaro taredashi akai mata sallah har aka Kaita makwancinta

Tundaga ranar rainon khadija yadawo hannun  muktar  dayake matar garba yaranta biyu duk mazane batasake haihuwaba daga garesu madara akarika bawa khadija

Allah yarayata tuntana karama she gen wayo ne da itah makaran tarsu daya da muktar kowakuma yadakarmasa Kanwa kowaye saiya rama mata bayaso yaga kukanta kokadan

Shikeyimata wanka da kwalliya akanta yakoyi kalaba danbaya kaita wajen kitso tunda yakaita sodaya yace masu kitson mugayene kwarai suke kitsawa  danmugunta "" shikuma ahankali yakemata anayi anashan minti kuma bata kuka

Tana primary 2 yagama makarantar yashiga babbar makaranta soyayya maikarfice atsakaninsu shine uwarta shine ubanta ko yayan inna balki suka daketa bayajin kunyar kowa zairama mata

Sannu kan hankali tanazuwa boko tanazuwa islamiyya Amman tafi bada karfi islamiyya datadawo boko tawuce islamiyya sai magrib ake tashinsu idankuma ranarda ba bokone karfe bakwai nasafe sukezuwa sai magrib

Tun tana yarshekara biyar takai hizif hudu kuma dazaran anyimata karatu nantake take daukesa akanta lokutta dai sunata tafiya khadija tanasake girma"" tanagama primary shikuma yanashiga ss 3 " tashiga itakuma jss 1 alokacin tanada shekara goma shabiyu"" yana gama secondary skull yashiga bayero university"" alokacin khadija takusan sauka alokacinne suka hadu da labila tadawo kano dazama saita shiga islamiyyar su waje daya suke zama Allah yahada soyayyar su waje daya saigashi kuma ashema makotane soyayarsu tayi nisa sosai kullum zakagansu tare alokacin muktar bagida yake kwanaba cen makaranta yake kwana idankuma bakaratu yakanshiga gari yayi aikin karfi yayiwa khadijar sa siyayya "" tuni tabashi labarin sahibarta dasuka hadu duk yakirah waya maganarta kenan sahibar ta"" su gwaggo hasana da Husaina duk sun hayayyafà kowace yaranta biyar duk sungirma Amman muktar shine babba  sai yayan uncle garba sulaiman da dahiru suma suna bayero

Tana ss1 muktar yatafi kasar waje waje karatu dansosai yanaso yayi ilimi yazama maikudi bayason kanwarsa tayi kuka anan gaba Amman ranarda zaitafiii tasha kuka dakyar tabarshi yatafi

Tundayaje baidawoba saida yakwashe shekara biyu  anyimasu walimar sauka dukda khadija tadade dasauka ba ayi walimarba akace sai ansamu kamar mutum dari duk dahaka sai aka kaita ajin hadda alokacin yazo yaga khadijarsa tasake girma kyanta yasake fitowa kamanninsu da mahaifiyarta yasake bayyana tana ss 2 lokacin suna shirin shiga ss 3 bangaren karatun islamiyya kuma hartakusa hardace alkur ani

Muktar baramin dadi yajiba yanda kanwarsa tazama hafiza suna zaune tana rubuta wani hadisi acikin littafinta muktar yakurah mata ido yanata faman murmushi

Ajikinta taji kamar ana kallonta tadago saisukai ido hudu itama murmushin tasakar masa tace Yayana meyafaru??? Murmushin yasakeyi yace idan ina kallonki nakan tunoda mahaifiyarmu

Kamanninku daya saidai kawai kindarata haske kadan dakuma wushiryar da kikeda itah bayan wannan bakuda banbanci hatta Dan abun nan naki dimpull tanadashi akowanne saitin kumatunta

Yanisa please Kanwata karkisa soyyya acikin rayuwarki kamar yanda nadade inasanardake mom tace tanaso kiyi karatun islamiyayya sosai yanisa banason kibiyewa abokai dannasan yanzu a skull kananun yarama zakagansu suna soyayya

Hawayene suka sauko akan fuskar khadija take muktar yarude yataso daga kan kujerar yaduka gabanta habarta yadago yace kuka farincikina

Maganatane tabata maki rai ¿kaita girgiza tace bahaka bane Yayana natunoda mom ne inama nima nayi rayuwa da itah inji diminta kamaryanda kowa yakejin dimin mahaifiyarsa

Kuka tafashe dashi maikarfi muktar baisan sanda shima yafashe dakukanba labila shigowarta Kenan tanufo dakin tajisu suna kuka duk dabaya yabata hakanne baisa taga fuskarsaba saida sukai mai isarsu sannan muktar yayi karfin halin soma lallashinta ganin zaimike labila tayi saurin juyawa tafita batareda sungantaba

Kwanansa biyu yakoma baisake dawowaba sai lokacinda khadija akaimasu walimar haddace al Qur ani

Dalilinda yasaka labila tacewa Usman sunan mahaifiyarta akasamata dan kawai taji yangidan suna cemata sapna wannan sunan kuma muktar ne yalakaba matashi yanajin dadin sunan idan khadija tace saboda mene bayakiran sunanta saiyace ai sunan umma ne to itama hakan tasanarda labila  shine tarike

A Takaicedai wannan shine ainahin tarihin rayuwarta dakuma tushenta babukuma Wanda yasan wuyarda maman khadija tasha sai muktar danbaimanta komaiba shiyasa yakeganin anyama zaiyarda yabawa wani khadija???

*KYAWON TAFIYA DAWOWA*







Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 69
       By
Gentle Lady💃🏽



Tasoma jadabaya"" tanabashi hakuri hannunsa yadorah akan labbansa yace shitt alamar tayimasa shiru takekuwa tarufe bakinta hantar cikinta tana kaduwa

Kusa da itah yakarasa yajaye zaninda yake jikinta yajata akan gado yasoma wasada itah tamkar bayacikin hayyacinsa"" Sam yaubayajin haushi dakuma warinta kodan yana cikin matsananciyar bukatane oho

Fateema Sam tamanta awace duniyar suke duk abunda Muhammad yayi mata tamantashi awan nan daren ashedai darabon khadija atsakaninsu domin rabon khadija ne yatasheshi abarci haka kurum yaji yana bukatar kwanciya damace

Wajen rukayya yasoma zuwa saiyasamu tana al ada dayake wani baya haihuwar danwani harzai koma daki yaji bazai iyaba kawai yatunkari dakin fateema saigashi baiji komaiba harsaida yagama biyan bukatarsa

Aizunbur yamike kamar Wanda yayi mantuwa kawai yakalleta  itama shitake kallo tana murmushi tsaki yaja yawuce abunshi abun ma saiyabata tsoro anya dadyn faruq kansa daya kuwa mikewa tayi ta tsarkake kanta tadawo takwanta

Tundaga ranar batasake sakashi acikin idontaba har aka kwashe wata uku talurah lallai cikine da itah""  gashi batajin dadi saiyawan ciwon ciki yaudai takudurah aranta zata sameshi tànemi izinin zuwa asiviti danciwon cikin yana matsanta mata""

Tana dakon jiranshi harbarci yadan figeta cen tafarka dasauri tasuri hijab dinta tasaka tafita zuwa dakinsa taturah da sallama saikuwa tasamu dakin bude tayi hamdala takutsa kai tareda sallama

Suna zaune dashi da rukayya sunacin naman kaji rukayya saizuba masa shagwaba takeyi shikuma kamar zaimaida itah ciki saboda soyayya""

Bakisake fateema take kallonsu Dan sallamarda tayima abakinta tamakale ganin yanda suke soyewa. Amman kullum rukayya cemata takeyi itakanta muhammad yadaina kwana da itah yadaina sake mata fuska "" wasu hawaye masu zafine suka sauko akan fuskarta

Muryar Muhammad taji yadaka mata tsawa kewacce  irin jakace zaki shigomun  daki cikin irin wannan yanayin kuma kiyimun tsaye akai

Fateema tagoge hawayenta  taduka kanta nakasa tace kayi hakuri nakatsemaku jindadinku wlh banda lafiyane kwana biyu shine nakeso intambayeka gobe zanje inga likita

Yace bazakiba tashi kibacemun daganie"" takalleshi cikin mamaki tace Muhammad bafa wasa nake yiba katausayamun mana damezanji dawulakancin da kakemun koda ciwonda ke jikina???

Afusace yamike yace watoma ninakemaki wulakanci??? Lallai yarinyar nan kinsamu damar rainani dankawai inasake maki fuska tokarshen walakanci kije gidanku nasakeki saki biyu kimaza maza kifitarmun gida kafin nakirga goma

Kwatakwata neman hawayenta tayi tarasa saitayi murmushin takaici tace nagode Muhammad balaifinka bane Nice dalaifi da nanace saina aureka

Babuyanda Yayana baiyiba Amman nace saikai Amman kasani babu inda zanje sainayi idda
Kafinma tarufe bakinta yace agidan ubanwa zakiyi iddar

Tamike ahasale tace agidan uban Yayana kuma babu inda zanje sainayi idda"" yace wlh bazakiyi idda agidanaba ke kijema na iyarda sauran sakin sai inga inda zakiyi iddar tunda ba uwarkice tabani gidan ba

Fateema tace wlh karkasake zagarmun uwa yace idankuma nasakefa "" tace sai inrama ai uwarka bafin uwata tayiba kafin tarufe baki yadaga hannu zaimareta

Tarike hannun tace Karka sake wlh barganin kadakeni ada nakyaleka dajarar soyayyace dakuma aurenka dayake kaina yanzu Kuma babu kodaya danhaka bazanji takaicin ramawaba

Ta sake masa hannu tacije lebonta nakasa zanbarmaka gidanka Amman kasani bazantaba yafemakaba bantaba cutar kowaba nikuma duk Wanda yacutardani bazan yafeshiba wannan alkawarine tanakaiwa  nan tawuce abunta Sam kuka yabacewa idonta

Zatafita yace dawo dawo ko kallonsa batayiba yafada dakinta yadauko muktar yana barcinsa yajawoshi kamar Wanda yadauko kayan wankii


Tana kiciniyar bude kofa yace wazakibarwà wannan shegen dannaki tajuyo afusace tace shegen ubansa aibadashi nazoba danhaka babu inda zanidashi inkaga dama kabarshi yamutu tafita dasauri tabanko kofa

Tanafita yajefo muktar waje yarufe kofar gidansa kukanda yakwantsane yasakata waigowa dagudu tadawo tarun gumeshi tahau rarrashinsa gabadaya unguwar tayi tsit kukan karnuka kawai kakeji yanatashi

Tashi tayi tagoye muktar abayanta dukda babu zanie tasoma tafita gabadaya tsoro yafita ranta tayi tafiya  mainisa  hartabar unguwarsu sosai haryanzu kowa batahadu dashiba "" muktar haryakoma barciii gashi tagaji dole tasamu wani wuri tarabe tacire dankwalin kwanta tashinfida takwantardà muktar  tazauna saiyanzu tasamu damar yinkuka

Tasoma kuka maidan sautiii tsayin min tuna kamar ashirin taga anyadomata fitila maihaske hannu tasaka takare fuskarta tacigaba da kukanta

Ahankali mai fitilar yatako kusa da inda take yakashe fitilar yadan rage tsawo yana dubanta yace baiwar Allah mutum ko aljan???

Batareda takalleshiba tace inaruwanka karabudani"" kaje kayi abunda yake gabanka"" yanisa naji Amman amatsayinki Na mace mai rauni baidace inganki anan ba kuma inkyaleki nimafa inada Yaya kamarki  bazanso nima Yayana susamu Kansu a irin wannan yanayinba inaso suma ataimakesu

Tace gawanda kebukatar taimako ko??? Toni bana bukatar taimakonka"" kabarni Dan Allah tasake fashewa da kuka""
Mutumen ya murmusa yace shikenan tunda bakyaso Amman bazan bar yaron  nan wajen nan ba kinga gidana cen dasafe saikishiga maidakina tabakishi yayi maganar kawai yadauki muktar

Tabishi da kallo komotsi batayiba bayan tafiyar sada jimawa saigashi taredawa ta mata alamu sun nuna matarsace yace kinganta nan yayinuni da Fateema

Matar takaraso wajenta tace haba baiwar Allah kitaso mana kinkosan karfenawa yanzu??? Itakanta matar muryanta ta maibarcice dagaji mijinne yatasheta babu musu kuwa tamike tabi matar hargidan dakinda suka kwantarda muktar nan suka nunamata sukaimata saida safe

Itakuwa babu maganar barci a idonta harsafe bayan tayi sallah tana lazumie saiga matar tashigo dakayan kari tagaida itah sannan ta ajemata tace kisamu kici malam zaiyi magana dake tace to

Duk datasan bazata iyah cin komaiba"" tatashi muktar yayi alwala yayi sallah sannan tabashi abun kari yaci bayan haske yagama mamaye gari rana takunno kai saiga matar tasake dawowa wajenta tace kitaso yana kirah bamusu tamike tabi bayan matar""

Harwani daki tasameshi zaune saman buzunsa gatarin littafai nan agabansa dakuma  allo da Qur ani tasamu gefe tazauna kanta yanakasa tagaidashi

Ya amsa cikin sakin fuska duk kunya takama fateema data tuno yanda sukaidashi jiyan yakatsemata shirunta yace yarinya hakika nalurah kamar kinacikin damuwa

Tunjiya la akarida yanda naganki dayaro acikin dare kuma cikin wannan muguwar shiyar'" inaso kisanardani abunda yafito dake daga gida

Shiru tayi nayan dakiku sannan tasanar dashi""komai yace wa iyazubillah Allah yakaremu dasharrin shaidan yata wannan mugun asirine akaimaki domin arabaki da mijinki

Gaban fateema yabada rasss dasauriii tadago kanta idanuwanta sunakawo kwalla tace asiri kuma baba??? Tomena tarewa wani dahar yakeso yashiga tsakanina da farincikina????

Yace yata abubuwa dayawa alabarinki kincemun matarsa bata taba haihuwaba??? Fateema tagyada kai yanisa kekuma gashi kinyi harbiyu ba mamaki itace dawan nan aikin

Fateema tayi shiru tana nazari ta tuna jiya dadare datasamesu dakinsa duk abunda akeyi rukayya kotado kanta batayiba saicin nama takeyi  abuntaa fateema tashare hawaye tace bashakka idankuma hakane Anty tacutarda rayuwata tafashe dakuka

Saida matar malamin tasoma rarrashinta tanabata bakii







Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠



Chapter 72
      By
Gentle Lady💃🏽





Tundaga muktar har khadija babu Wanda yaruntsa harsafe khadija takwana kuka kafin safe wani zazzafan zazzabine yakamata jikinta yagashe kamar wuta

Sallar asuba kanta dakyar tayi gashi jiya bataci abinciba"" dasafe inna takawo mata abun karinta tatasheta tace takoshi

Babuyanda inna batayiba Amman takici dataga zatadameta tace zataci inna tanafita tasake gyara kwanciya""  tana nan kwance har azahar muktar baishigo dakinba

Inna tasake kawo abincin rana tasamu nasafen bataciba"" ta ajemata tafita dakin muktar tayi saita sameshi zaifito kenan yana ganinta yadansaki ransa yagaida itah

Ta amsa tace idan zaka iyah rarrashin sarkin zuciyar cen kaje wlh yaukoruwa batasha ba rabonta da abinci tunjiya dasafe babu yanda banyi da itah dasafe ba tanuna masa kaga karinta nasafe yanzu danakai narana nadaukoshi

Yayi shiru sannan yace shikenan yajuya zuwa dakinta koda yaturah kofa idonta rufe yake yataka harbakin gadon yazauna yakuramata ido

Yasan tasan shine dangashinan idanuwanta sunsoma zubarda kwalla duk da arufe suke" sunanta yakirah bata amsaba"" baidamuba yace kitashi kici abinci

Nandinma banza taimasa yaturah hannunsa daniyar yatasarda itah mugun zafinda yaji shiyasa yacire hannunsa dasauri batareda yayi niyaba

Cikin tashin hankali yace khadija bakida lafiya Daman??? Meyasa baki sanardaniba duk arude yake maganar dasauri yafita yacewa innah kishirya ta yanzu zandawo da doctor yadubata yafita dasauri yana dauko waya cikin aljihunsa

Abokinsa Abubakar yakirah yasanardashi yana kano yanzu haka yanason ganinsa "" yace toyasameshi gida danyanzu Hutu yake yace toganinan tafe

Yanagama wayar yatari Dan adaidaita zuwa gidan sa bayan yakirasa yace yakaraso saiyafito motarsa sukashiga zuwa gidan

Yashiga yasanarda innah zaishigoda doctor tace to saida yashiga yasamu khadija kwance yagirgiza kansa sannan yafita"""

Yashigoda Abubakar din yagaida innah sanan sukashiga dakin "" yataba jikinta dazafi sosai sannan ya aunata"" haryagama abunda yakeyi muktar yana kallonsa

Yatashi tsaye yana kallon muktar yace me akaimata halan???  Muktar yace mefa akaimata doctor mekedamunta??? Yanisa yawan tunanine yahaifar mata da damuwa gakuma kirjinta yanazafii

Tunyaushe rabonta da abinci?? Jiki asanyaye yace jiya" yace mujeto asiyomata magani dole aimata allurar barci domin tasamu barci ko damuwar zataragu

Yace tomuje yayi maganar yana kallon khadijar taresukaje dashi akasiyo maganin da allurar yabiya sukaje inda masu fura damun injin yasiyamata suka wuce gida

Dakyar yasamu tasha furar sanann akaimata allurah takwanta  yanunamasa yanda zatasha maganin idan tafarka yayimasa godiya yarakashi bakin motarsa sundade suna firah sannan yatafi hankalin muktar duk yana wajen khadija

Kodayakoma yasamu tayi barci kusa da itah yazauna yabuga tagumie yana kallonta"" wasu hawayene suka saukomasa yasadan yatsansa yataresu

Yana nan har akayi la asar yatafi masallaci yadawo yazauna ba itah tafarkaba saigoshin magrib yataimaka mata tawatsa ruwa tayi sallah taci abinci tasha maganie takoma takwanta

Sallamar labila sukajiyo tsakar gidan tagaida innah sannan tafada dakin tanakiran sahib bata rufe bakiba sukai ido hudu da muktar yasake tsuke fuskar  nan

Itama saita dauke kanta tace inawuni bai amsaba itama batadamuba saman gadon tahau tace meyasameki sahiba???

Khadija saman kafarta tahau saitafashe dakuka nantake labila tafara kukan tace me akaimaki sahiba??? dan Allah kiyi shiru

Muktar yanazaune yanakallon ikon Allah"" innace taji kukan yayi yawa tashigo tozakufara sana ar takuba kuyiwa Allah kuyishiru

Kojinta basuyiba itama tsaye tayi tasaki baki kamardai yanda muktar yayi tsayin mintuna goma khadija tayi shiru saikuma takoma rarrashin labila sahiba kiyi shiru kinji kar zazzabi yakamaki

Saida tagama rarrashinta sannan tace inayan tafiya??? Da murmushi tayi maganar labila tace tunjiya naso inkawomaki da dare  harzanfito sainaji raina abace nakoma daki nayita kuka jiya wlh banruntsaba zazzabi yarufeni

Yanzun Karin ruwama akaciremun tanunawa khadija hannunta tace inatashi nacewa hajiya kinzo tacemun ah ah shine nataso ingako lafiya

Khadija tasaki wani kayatacceñ murmushi tana kallon labila tace sahiba lafiyata qalau Nima rashin ganinkine yahaifarmuñ da damuwa Amman yanzu tunda naganki Alhamdulillah

Tace nima wlh sainaji nawarke taresuka sakarwa juna murmushii"" muktar yamike jin ansoma kiran sallah yafita baicedasu komaiba


Aransa yana tunanin wannan wace irin soyayya ce sukewa junansu aidole khadija tace tanason baban labila Kuma batai laifiba   Amman anya nizan iyah barinta ta aureshi??? Nifa tsoron matan yanzu nakeyi dawan nan tunanin yatafi masallaci

Inna ma fita tayi domin tayi sallah suma sukayo alwala sukai sallah anan suka zauna sunata labari yawancin firarsu duk akan karatunsune na islamiyya har innah tagama abincin  dare sukaci gabadayansu sunware tamkar basuyi ciwoba""
Muktar yadawo yasamesu suna tafirah yadade bakin kofar yana saurarensu basu ganshiba dan hankalinsu baya nan juyawa yayi yabar kofar dakin

Saikusan karfe Tara labila tayi gida saida sahiba tarakata sannan tadawo tanashigowa gidan tasha toka zuwa dakinta batajima dazamaba

Saiga muktar saman gadon yazauna yana kallonta yace sapna kenan wannan fushin duk ni akeyiwa ko??? Gashi kinware tunda kinga kawarki Amman tana tafiya kinkoma kina fushi

Dadago da sirarun hawayenta tace Yayana ciwona azuciyata yake bawai afuskaba nayi kokarin boye damuwa tane saboda labila muddin tasan inacikin damuwa zata matsane saina sanarda itah menene damuwata dakuma silar damuwar

Idanhar nasanarda itah Kaine kake fushidani wlh bazata sake kallonka da mutunciba"" ninasan labila batunyauba danhaka nake boye damuwata duk lokacinda muke tare

Yanisa yanzu khadija ninake fushidake??? Kodai kece kike fushidani"" hawayenda suke kan fuskarta suka karasa saukowa yace please nifa bakuka nace kiyimunba "" tace Yayana taya zanyi mushidakai Kaine ubana kuma Kaine uwata
Kasharemun hawayenda uwayena ne yakamata su shafemun banida wani babban farinciki aduniya Wanda yawuce inga nafaranta maka rai

Yayi murmushi khadija kenan aiyanzu banada wannan kimar tunda har nahanaki soyayya Amman kikayi dama bayada mata dadan sauki Amman khadija mai matafa kuma harya manyanta

Gyara zama tayi tana fuskantarsa tace Yayana duk da bansan dalilinka nafurta hakanba nasan kasan wannan baharamun bane

Shimai mata baza a aureshiba tosabodame??? Koshidin bamutum bane??? Kasani mata sun linka maza sosai idankowanne namiji mata daya zai aurah sauran matan kumafa wazai auresu???

Yayana idan kai aure nan gaba kana bukatar kari kaima saiwacce kakeso tace batasonka tunda kaima kanada mata"" shinzaka saki uwar yayankane saboda kanason Karin aure???

Idan kasaketa ka auri waccen kasake ra ayin karawani aurenfa??? Aganina mai mata bashida wata illarda za ace aurensa bazai yiyuba sai idan ansan shidin ba nagartaccen mutum bane tanisa banyimaka wannan maganarba waidan kabarni Na auri dadyn labila

Tundahar bakasonsa wlh nahakurah dashi zansanarda labila kayimun wani mijin kokuma inbika cen kagama bangantaba ballantana  inji damuwa Amman Yayana nasan kanada dalilin fadin haka
Dan Allah kasanardani meye dalilinka






Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠



chapter 71
       By
Gentle Lady💃🏽





Wayar taketa kallo tana murmushi"" saiga kirah yasoma shigowa  cikin kira ar sudes tuni khadija talunshe idonta saboda jindadin karatun tanabinsa ahankali harkiran yakatse

akasake kirah saiyanzu tabude idonta tadauko wayar saitaga ansa hubbina takwalalo ido tace hubbina kuma batasan harta dauki wayarba tanacewa hubbina sai asaitin kunnensa saitaji yace Na am

Wata irin kunya takamata kamar tanitse cikin kasa muryarsa taji yace khadija menaji kinkirani dashi yanzu???

 Duk tabi ta daburce tace dad sorry wlh banice nasakashi awayarba sahibace tasaka namanta sainakirah Ashe harnadauka kaji dakyar takeyin naganar kamar wacce akasaka dole

Murmushi yadanyi maisauti yace nikuwa naji dadi danaji kinkirani hakan"" hannu tasaka tarufe fuakarta  tace kayi hakuri yace aibalaifi kikayiba khadija

Tace harka kaine saikuma tarufe bakinta da alamu batasan sanda maganar tafitoba"" yace ah konadawo ne bakigaji da ganinaba??? Tace sai anjima dad

Dariya yayi maidan sautiii yace kunya kikejine??? Kamar yana ganinta tanoke fuska tareda daga kanta yace isowata kenan harzan soma aiki nacebari nafarajin muryarki"" murmushi tayi tace tokayi aikinka lafiya dad "mungode batajirah mezaiceba taka she wayar"" yabi wayar dakallo yayi murmushi

Khadija sunagama wayar wani farincikine yalullubeta marar misaltuwa tadade tanajin soyyarsa cikin ranta Allah yakaddara shine mijinta

Kullum Usman saiyakirah khadija Amman baitaba kiranta idan haryana kusa da lubabatu Sam batasan meyake faruwaba tsayin sati daya sannan yakoma kano yasanarda malam garba khadija ta amince..

Yace shikenan yabashi kwana biyu zaikirah muktar yasanardashi komai yace saiya fadamashi"" hakan kuwa akayi bayan kwana biyu yakirah muktar.

Tana fara ringing yadauka tareda sallama  malam garba ya amsa muktar yace kawu inawuni yace lafiya  kalau ya karatu

Muktar yace karatu Alhandulillah"" yace to Allah yabada sa a yabada abunda akaje nema yace ameeen  muktar yace kawu ina sapna??? Yace kaima kasan tana islamiyya ni nadawo gidane indan watsaruwa saboda zafie

Muktar yace kagaidamun inna " yace tana amsawa"  daganan saikuma shiru yabiyo baya  muktar takawarda shi run yace kawu ko akwai maganane???

Yanisa ah kam muktar akwai magana mai mahimmanci akan khadija shine dalilinda yasakama nakiraka"" jinya ambaci khadija yasaka yasaka muktar yabar abunda yakeyi yatattara hankalinsa duka yana saurarenshi

Yace inajinka Allah yasadai lafiya  yace qalaune insha Allah yayidan  jinkiri sannan yace watarana ina kasuwa saiga mahaifin Kawar khadija labila kaganeta aiko???

Cikin kosawa yajimeyafaru yace ah nagane" yacigaba yazone akan batun khadijar daganan yakwashe abunda sukai dashi yafadamsa haryanda sukai da khadija tace ta amince

Yana rufe bakinsa muktar yamike tsaye yace ai wannan zancen banzane kawu nawa khadija take dahartasan wata Abu wai soyayya bazata aureshiba!!!

Kawu yace dakata muktar baikamata kahana yarinyar nan cika alkawarinda tadaukarwa kawartaba"" tace daina maganar wani alkwari kawu kawai kacemasa auren nan bazai yiyuba yayanta yace bayaso

Idankuma bazaku iyah sanardashiba nimai iyah fadamasane haba kwata kwata  nawa khadijar take 18years fa" Kuma tarasa wazataso sai Wanda yakeda mata !! Never

Malam garba yanisa yace tonidai bansan yazanyi makaba  Amman gaskiya zak asani jinkunyar bawan Allah nan tundaga kano yataso

Muktar yace Allah yasa daga saudiya yazo kawu ban yarda Kanwata ta auri mai mataba!! Malam yace to Allah yakyauta sai anjima

Yakashe wayar yanakallon innah yace Dama hakan nayiwagudu shiyasa nacemasa yabari saina sanarda yayanta

Kinji yanda yaceko??? Innah tace lallashinsa zakayi ai saiyayi hakuri Amman magana tagaskiya yarinyar nan tanasonsa "" ninalurah dahakan tunkafin yace yanasonta

Malam yayi shiru yana nazari cenyanisa yace to tundashi yakeda kanwarsa yace bayaso ahakurah mana nibanaso inyi karambani inajin tsoron maimaita tarihi duk da banada laifi

Innah tace to Allah yazaba mana abunda yafi zama aikhairi malam ya amsa da Ameen bangaren muktar kuwa sunagama wayar yakasa zama jikinsa harwani ciccirah yakeyi anyama zai iyah sake kwana a kasar nan karfa yanacen kawu yayiwa khadija aure

Kuma wai baban labila mai mata ai bazaitaba yiyuwaba "" dasauri yasoma hada kayanshi sai filin jirgi

Koda jirginsu yasauka takwas nadare masallaci yafara zuwa yafara ramakon salloli sannan yatari Dan adaidaita zuwa gida

Suna tsakar gida sunacin abinci dayake yanayin zafine saman babbar tabar marnan suke saidai sukaji sallamar sa dagasama

Malam garba yadago da mamaki yana kallonsa lallai abun yayi tsamari suka amsa masa sallama yaduka yagaidasu baiko kalli gunda khadija takeba yatashi yakoma bangaren dakunansu""  yashige dakinsa

Tuni murnar dakuma farincikin fuskarta yagushe takalli innah kamar zatayi kuka mikewa tayi zuwa dakin dasauri da sallama tashiga

Yana kwance saman gado yakurawa silin dakin ido ahankali tataka indayake taduka muryanta tana rawa tace yaya halan bakaganniba???

Atsawace yatashi zaune yace naganki sapna mekikeso inyimaki???? Take hawaye suka jikamata fuska tace wani laifin nayimaka Yayana???

Yadallah mata harara yace kebakisan ma abunda kikaiba tunyaushe nake Jan kunnenki akan karkisake kiyi soyayya??

Asheni bansaniba ihunake bayan hari" nawakike khadija dahar zakice waikinason wani kuma bama saurayiba maimata??? Kinsan sarai natsani mai mata bazantaba bari ki auri mai mataba kodakuwa mazan  duniya sunkare


Tanaduke hawaye sunabin kumatunta batacemasa komaiba haryakai karshe cikin sanyin murya tace Yayana baban sahiba tane fa baikamata kajerah shi cikin sahun marasa nagartar mazajeba

Yadaga mata hannu rufemun baki nalurah kedin bakida hankali tokisani gobe gobe dake zankoma sainaga karyar rashin kunya kuma shima zankirashi inji dalilinsa duk matan dasuke kasarnan yarasa wazai ce yanaso ya aurah saike zatayi magana yace kiyimun shiru tashi kibar nan banason ganinki

Cikin muryar kuka tace nidin ya muktar??? Cikin tsawa yace kifita nace tsawarda yayimata cikin wata murya wacce itah kanta batasanshi da itaba

Dasauri tamike tarufe bakinta saboda kuka dagudu tafita tafada dakinta saman gado takwanta tasoma kuka maicinrai meyasa nabata maka rai meyasa??? Danasan hakan zaikona makarai bazantaba bari son dad yashiga zuciyataba

Su inna sai kallo kallo suke  sukalli  kofa sukalli juna"" sunsan koda sunshiga dakin muktar bazaitaba saurarensuba"" Dan idan yahau dokin zuciya bamai saukardashi







Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠



chapter 73
      By
Gentle Lady💃🏽




Yayi shiru daga bisani yace khadija tace na am Yayana " yace kinsan bazanso abunda zai cutardake bako??? Tagyada kanta yanisa tundakike bakisan labarin mahaifiyar  muba

Babu Wanda tasanar mawa kisani bayanni kinada wani yayan"" dasauri tadago tace Yaya kuma a ina?? Yanisa mu uku mahaifiyar mu tahaifa

Nima naji wannan ne lokacinda zamubar garin mahaifinmu tanasanarda wani malami alokacin ban fuskanci labarin sosaiba  bayan nagirma nasake komawa yola

Da mamaki takalleshi duk da inayaro banwani sha wahalar gane gidansaba Amman da tambaya da yake malamine sainayi dace tunda nasan unguwar awajen gwaggo hasana na tambaya

Nasameshi yatsufa sosai baima ganeniba saida nayimasa bayani yanisa kwana na daya agarin hargidan mahaifinnawa natafi Amman baigane niba

Naso sosai nasan inda Dan uwana yake duk Wanda natambaya saiyace babu faruq agidan malamin shine yasanardani labarinda  mahaifiyarmu tasanar dashi

Yanisa anan yakwashe komai yafada mata"" duk irin wahalarda tasha dayanda malamin yacemasa asirine akai mata komai baiboye mataba

Yanakai karshen labarin khadija tafasheda kuka baiyi kokarin hanataba saida tayi mai isarta dankanta tashare hawayenta

Yace wannan dalilinne yasaka banaso ki auri maimata Dan bazanso kema hakan tafaru dakeba"" khadija tadago jajayen idanunta takalleshi tace nagane Yayana Amman inaso kasani babu Wanda zaiwuce kaddararsa

Kataba tunanin za ahaifeni???? Duk da kiyayyarda mahaifinmu yakeyiwa mamana dayake akwai rabon saina shigo duniya gashi anhaifeni

Ya muktar kaddarata rubutacciyace bakada ikon sauyata inhar Allah yarubuto nima zansha wahala babu makawa hanawarka bazai kareni dakomaiba""

Kataba tunanin zan iya auren marar matar dagabaya yasake aurowata wacce zatayi nasanin fitana gidan??? Shifa Allah ba aimasa wayo baka isah ka karkare abunda yake arubuceba  tunfil azal

Baikamata kayiwa kowacce mace kallon hakaba Dan idanharkayi tonima wani mai irin hangenka dawannan zai kalleni

Kasani ba arasa nakwarai acikin al ummah komai lalacewar zamani zakasamu akwai nagartattuñ mutane acikinsu

Tanisa abunda kawai yakamata  kayi kace Allah yakare maka kanwarka daga fadawa hannun irin wadan nan azzaluman  matan"" kuma kabawa kanwarka makami wato ilimin Islam Wanda kowayake takama dashi

Dashi zata iyah kare kanta Allah yashiga tsakaninta damiyagun mutane kumani bana zargin mom wlh baruwanta halinsu daya da labila

Idanhar tanada wani mugun hali da awajen yarta zamugani Dan duk Wanda yatsotsi nono bazai yarba kamar yanda naji anafada

Nikuwa nace wannan zancen burr ne inji tusa saunawa uwa take haihuwar Yaya Amman babu Wanda yagadota wani lokacin maishegen fada saita haifi salihar yarinya

Wani lokacin saliha saita haifi masifaffiya danhaka masucewa waisu bazasu auri yayan masifaffuba bawai halin uwar zaku dubaba nayar dankowa da halinsa

Muktar yanisa yana kallon agogon hannunsa yace dare yayi kikwanta kihuta"" kai tagyadamasa tace nagode kaima kasamu kakwanta nasan jiya bakai barciba

Murmushi yasaki maidan sautii yace ya akai kikasan banyi barciba??? Itama murmushin tayi tace gashinan inagani a idanuwanka

Yamike yadauko mata maganinta yace aikece kikajamun kinfita kina kuka badole hankalina yatashiba"""  tace ayimun afuwa duk laifin nan dai nawane baice komaiba yabata maganin tasha yayi mata saida safe yakoma dakinsa yadade yaana nazarin maganganunta kafin yayi alwala yana sanarda Allah yazabawa kanwarsa abunda yafizama alkhairi arayuwarta
Washe gari dasafe yana dakinta zaune suna firah saiga wayarta tasoma ringing jikinta yasoma rawa dantasan shine jiya silent tasaka wayar bayan fitar muktar  tadauko wajen miss call ashirin tayi mamaki sosai"" saitacireta silent saiyanzu gashi yakirah

Tanakallon wayar tana kallon yayanta yalurah da itah saiyashare yace wayar waye take ringing tsuru tayi alamun rashin gaskiya tace dama dama wayar sahibace tamanta da itah

Dakagan yanda take magana. Kasan batada gaskiya yayi murmushi yace tokidauka kice batakusa dawayar mana"" tadan sosa kanta tace ah ah kawai barta idan yagaji zaidaina kirah kowaye

Wayar hartakatse akasake kirah muktar yamika hannu yadauko wayar yaduba hubbina yaga anrubuta yadaga ido yakalleta saita done kanta yace kinganima inaganin kamar saurayintane yake kirah

Shirudai tayi batace komaiba hartakusa katsewa yadauka tareda sallama dayan bangaren aka amsa "" yace barka dasafiya yace yauwa Dan Allah Khadija nake nema

Muktar yadaga kai sukasake yin ido hudu tasosa kanta kamar wacce zatayi kuka"" yace togata nan tafe yakashe wayar baiko kalletaba yafita rike dawayar

Jikin khadija Yakama rawa tace yaunabani mekuma yakawoshi yanxu??? Saileken kofa takeyi""
Muktar da murmushi kwance afuskarsa yakarasa wajenda Usman yake tundaga nesa yaga matukar kamarda sukeyi da labila kuma tamkarma bai isah haihuwartaba""

Shima yana ganinsa yasaki fara a kafin yakawo inda yake haryasameshi yabashiy hannu suka gaisa "" daganan suka karasa kusa da motarsa

Suka sake gaisawa yace yan america saukar yaushe bayan malam yacemun bakanan"" sosai Usman yayiwa muktar kwarjini a ido Sam yakasa daga idonsa sama yakalleshi""

Yace shekaranjiya nazo"" yace toya hanya inafatar dai lafiya?? Yace ah lafiya kawune yakirani yasanardani sakonka

Usman yatari nunfashinsa yace Allah yasadai yayan namu ya amince"??? Wata kunyace ta sake kama muktar yace ah gaskiya lokacinda naji Sam banyi Na am ba dalilinda yasaka nataso aranar kenan

Nazone daniyar natafi da itah dankawai nace banyardaba saiyarinya tazubemun balafiya jiyama saida tasha allurah Usman yace subhanalillahi yayanmu meyasa zakaimana haka

Muktar yace dad inada nawa dalilin saboda nayi alkawarin Kanwata bazata auri Wanda yakeda mataba saboda shine silar dayasa mukarasa mahaifiyar mu yanisa

Amman sapna tayimun gamsasshen bayani kuma nayarda dahakan yanzu danaganka yasake nisawa yadago yakalli Usman kamar zaiyi kuka yace wlh inason Kanwata sosai itace kawai take debemun kewar mahaifiyarmu

Banaso tashiga tashin hankali da matsatsin rayuwa" yasanne kansa nidama banda natauyemata hakkinta bazantaba bari tayi aureba

Danba zanso wani yacutarda itaba"" Usman yamurmusa yadafa kafadarsa yace nagane abunda kakenufi kuma nagamsu nayimaka alkawarin babu abunda zaisameta inasonta sosai bawai son wasaba dasanina kaima kasan bazantaba bari wani yacutarda itah ba

Muktar yanisa shikenan Allah yazaba mana abunda yafizama alkhairi usman yace Ameen"" muktar yace bari nakiramaka itah

Yayi maganar yanashirin juyawa Usman yasake basa hannu suka gaisa sannan yawuce aransa yanacewa  ashedai baban labila haka yake bashida girman kai""

Usman kanshi yaga saukin kan muktar"" yanashiga gidan innah tace wai inakaje naga khadija sai tsautsauniya take"" murmushi yayi yace innah dadyn labila ne yazo"" yayi maganar yana shiga dakin yace kishirya yana jiranki ya ajemata wayar akan dago harzaifita tace Yayana tsayawa yayi batareda yajiyoba tace nidai banason fita bakafadamashi  gobe zamutafi dakaiba

Adarare takeyin maganar yajuyo dafuskarsa wajenta dauke da murmushi yace inazanje dake  kiyitamun kuka ainalurah soyayyarku hartayi nisako

Tace wlh ah ah ya muktar yace hakane shiyasa naga kinyi serving din numbersa da hubbina

Kafin tace wlh banice nasaba yace karkibata masa lokaci yanajiranki Amman karkidade yawuce abunsa"" murmushi tayi mayafinta kawai tadauko tasaka tasa talkamanta tafito tana leke waiko zataga ya muktar innakuwa sai dariya takemata

Tafito dasauri tafita"" tunda yahangota yasoma aikomata dawani kyakkyawan murmushi Wanda itakanta bazata iyah daukarsaba akarancin shekarunta jitayima kamar kafafuwanta suna hardemata tuni tasanne kanta kasa











Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠



Chapter 74
      By
Gentle Lady💃🏽



Ahankali tataka harzuwa wajenda yake tsaye shikuwa haryanzu baidauke idonsa daga kantaba tafiyarta tamkar dawisu natsuwarta kalamanta komai natadai yana matukar burgeshi

Ko amafarki baitaba tunanin wai zaitaba soyayya dawataba saigashi kwatsam ya afka kogin so kuma yayi nitso tayanda baxai iyah fitaba

Da tsadadden murmushinta Wanda yake matukar dimautarda Usman tayi sallama dakyar ya tattaro sauran natsuwarsa wajen amsa mata sallamarta

 Tace inawuni dad"" yadan gyara tsayuwa sanann yace lafiya qalau mom" dasauri tadago takalleshi batareda tayi maganaba"" yadaga mata gira yace yes indai bazaki  kirani Usman ba nikuma mom zandinga kiranki dashi

Bakinta tadafe 🙊Dan Allah dad karufamun asiri dawanne bakin zankiraka aikuwa danayi rashin kunya takai karshen maganar tana kallon kasa

Murmushi yayi maidan sautii yasake gyara tsayuwarsa yace yayammu yace bakida lfy??? Kaita gyadamasa yace shine jiya akaki daga wayata wlh duk hankalina yatashi inata tunanin kobabu  lafiya

 Shiru tayi cikin tsokana yace khadija meyake damunki?? Shiru taimasa saida yasake tambayarta tace bakomaifa dad

Yace badaikiso insani ai yayanmu yafadamun"" baima karasa rufe bakinba tace nashiga uku mekuma yafadamaka???

Yanda tayi maganar tanaware ido tayi matukar burge Usman yasoma dariya haryana tafawa"" ido takuramasa talangwashe kai sai murmushi takeyi gaskiya dad kyakkyawane inama nice yafara aure danasan nahuce takaicin soyayya indai nasameshi

Yatsagaita da dariyar yana kallonta Sam batasanma yana kallontaba saida yakada yatsunsa sukai kara sannan tadan zaburah

Tanoke kanta tana Sosa kai alamar jinkunya sosai taji kunya dayakamata haka tana kallonsa""

Murmushi ya sakeyi yace toyajikin naki inafatardai kinji sauki??? Tasake gyada kanta yalurah sosai khadija tanada matukar  kunya "" ganin firar tasu kamar atakure take saiyace tunda batada lafiya takoma gida shizai wuce wajen hajiya

Tace masa to Allah yakiyaye hanya"" tawuce gidan tsaye yake yana kallonta harta shige "" yasaukarda sassanyar ajiyar zuciya""  motarsa yabude yadauko siyayyarda yayi mata yabawa yaro yashigar matadasu

Yashiga  motar sa yawuce "" koda yashiga gidan hajiya lokacin suke break yana yin sallama abdulmajeed yataso dasauri yarungumeshi yana gaidashi

Yashafa  kansa cikin  fara a yace katashi lafiya??? Kaiyagyada masa yace Amman jiya Anty saida akamata allurah yace dagaske?? Amman ba afadamun ba

Yayi maganar yana karasawa saman dinner yagaida hajiya ta amsa cikin sakin fuska  labila ma tagaidashi ya amsa yayimata yajiki tace taji sauki sosai"" dama bawani ciwo bane hajiyace tatashi hankalinta  hajiya tace yaunaji lalata nicema natashi hankalin nawa bayan kukanda kikaitayi kinacewa akiramaki dad"" dariya labila tayi tace aini bansan Yar tsohuwar nan tanasonaba sai ranar""

Abdul majeed yace tafisona danni idan nagirma mota zansiya mata!" Suka kwashe da dariya labila tace sannu sarkin soyayya kaikuma mezakayi da tsohuwa??? Kowa yana yayin sabon jinie
???

Yace nidai inason abuta tunda tanafita dani unguwa"" sukasake darawa "" hajiya tace kai maigidana kyaleta zauna kaci abincinka"" karka makara kara labila sai anjima kadan zata tafi""


Usman yace tonima asammun abincin banci komaiba wlh anayin sallar asuba nataso"" labilace tasoma zubamasa ""

Hajiya tace kaikuma lafiyarka wannan uban sammako???  Yakarbi cup din tea daga hannun  labila yace hajiya wannan tambaya hakafa??? mutum yanada uwa sukutum agari atambayeshi danyayi sammako danyaganta""

Konayi laifine yayi maganar yana kallon labila tace inafa laifi dadyna ai zumuncine kasamu lada maitarin yawa

Hajiya tamere baki tace saikuje kufadawa wani badai niba kadaisan abunda yakawoka"" 'Usman yakurba tea yana dariya ciki ciki  yace hajiya gaskiyar kenan

Yajuya wajen Abdul majeed kaiyi sauri kashanye inkaika dagacen inwuce yau wlh aikine dani office din nan"" hajiyadai batace komaiba""

Labila tace dad bazakaje wajen sahiba taba batada lafiya"fa"  ashagwabe tayi maganar abdul yayi kududum yace me dady zaiyi wajen kawarki

Yakalli Usman yace nima jiya ai abokina baida lafiya Amman bakaje ganinsaba sai Kawar Anty"" kamar zaiyi kuka""

Usman yashafa kansa yace aibaka fadamunba danaje ko yarona maza dauko jakarka muje"" Abdul majeed yaruga shikuma yamike

Labila tabishi da kallo tace kai daddy yanzun bazakaba kabari driver yakaishi mana kaisaikaje"" yakalleta yana murmushi yace Ashe yayanta yazo???

Tace yakirakane""" daidai fitowar Abdul yamikamasa jakar yagoyamashi itah yace cen nafara zuwa ai"" yakai karshen maganar yana kallon hajiya takasan ido yana dariya kasa kasa

Murmushi kawai tayi tana girgiza kai yace mujeko nagoyamaka"" yarike hannunsa mujeto daddy"" yace haba Abdul aikanajirah nagama magana da hajiyata ko

Yakalloshi da sauri hajiyarka??? Wlh hajiyatace"" yace najito hajiyarka"" yayimasu sai anjima sukai masa Allah yakiyaye yawuce yana dariyar Abdul majeed


Da dare muktar yasanarda kawu ya amince khadija ta auri dadyn labila bakaramin jindadi yayiba""" yayita sakamasa albarka washe gari Yakama hanyarsa yakoma skull

Usman yanadan zuwa kano akai akai"" haryanzu uwar gayyar batasanda komaiba gefe daya sunfara zana jarabar karewa balaifi sunawaya duk da haryanzu batasakin jiki suyi  firah""

Usman yaturoda magabatanshi anzauna akayanka sadaki yabiya ansaka rana wata biyu"" kenan bayan sati biyu da kammala jarabawarsu





Aisha✍🏼
Copied By
HAYATU BABA ZUBAIRU
        (admin
   Arewa hausa novels
       Novels villa
     Duniyan novels
   Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
          And
Cool novel, makeup and cooking)

      WHATSAPP NO:
    +2347039625239
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠



Chapter 76
        By
Gentle Lady💃🏽
 


Bayan motar tatsaya inda ake ajiyeta driver yafito yabude masa kofa Amman Sam hankalinsa baya jikinsa" saida yakirah sunansa sannan yafarga""

Yadan murja idon sa kamar Wanda yayi barcii"" dauko kayansa yayi da card din yama driver saida safe"" yawuce cikin gida jiki asanyaye

Koda yashiga bata falon kasa yasaukarda wata gajiyayyar ajiyar zuciya"" Allah yasama tayi barci sai inbari saigobe nikuwa abun ma dariya yabani to aikogoben kafada abunda kake gudu zaifaru bafasashi za aiba kaidai kawai kafada musam makomarmu

Ahankali yasoma hawan step din baima tsaya hawan na uraba zuwa sama tadaukeshi tsawon lokaci kafin yakai"" bangarensa yanakaiwa lubabatu tana kawowa dantayi mamaki yau yadawo dawuri

Dan tunda yahadu da khadija baya dawowa saiwajen karfe Tara alokacinne yake kiranta danbadama yayi agaban uwarguba! Au sorry🙊 uwargida tunda labila tace basuyardaba tasanie

Yana ganinta yatattaro sauran natsuwarsa yasamu yasakar mata lallausan murmushi itama tamiyar masa da martanin murmushinsa """

Tace sannu dazuwa yauwa yagidan yyi maganar yana turah kofar dakinsa tabishi abaya "" tace gida saitarin kadaici ai kwanan nan nakeson  naje yawon kasa dani da su sajida"" yace ko??? Tace eh yamere baki baice komaiba

Tace bakace komaiba"" yana rage kayan jikinsa yace Toni menene nawa ??? Da inaso dabanaso inhar kinaso saikinyi ra ayinki nasanma kina fadamunne dankar naga bakyanan Amman banda haka watarana aisaidai nabuda ido bangankiba""""

Maganarsa saima tabata dariya ganin tana dariya kamar wacce kare yaciza yakalleta baki bude yace wannan dariyar haka kumafa???

Tatsagaita da dariyar tace tomekuma nayi dankawai nayi dariya??? Yace bakiyi komaiba Amman kisani ire iren  wan nan dariyar batada kyau acikin addini manzon Allah yace tana kashe zuciya tanakuma rage imani"  jibifa harda hawaye kike shaidanne yakee irin wan nan dariyar"""

Take annurin fuskar lubcy yagushe tace kana nufin nidin shaidance???? Yakwalalo ido yace wani banfadaba baza aji mutuwar sarki abakinaba""

Karki karagaba kifada Allah yabaki hakuri bahakan nake nufiba yadauki towel dinsa yashige bandaki yarufo kofa anan yabarta sai nanata maganarsa take aranta

Haryafito batako motsaba""" yana taje sumar kansa' yadan kalleta tajikin miro yaga yanayinta yasauya"" takowa yayi kusa da itah  yazauna yana kallonta yace uwargidan Usman badai maganar da nayi dazuce tasosa rankiba????

Saurin kawarda damuwarta tayi takirkiro murmushi la bakomai dankawai kasanarda ni gaskiya dannakiyaye gaba

Aini nagode Allah dayahadani dimiji irinka wasu mazan zasuga matansu suna aikata badaidaiba Amman saisu kyalesu kodan kada ran matar yabaci kodan wani Abu
Tace nagode kashirya abincinka yana jiranka"""yamike bari nashirya amma kafin Naci abinci akwai wani albishir dazan baki

Nantake lubabatu tawashe baki tace toshikenan bari nakawo abincin nan"" tayi maganar tana mikewa tasauka waje bayan yashirya yazauna jiranta saigashi tashigo dauke da tiren abincin ta aje kasa""" cikin zumudi tacemasa tofadamun"""

Yace yanzu kuwa""  hannunta yajawo zuwa saman gadon yace zauna bamusu kuwa tazauna""yana fuskan tarta yace albishirinki

Tace goro fari kalkal"" ya murmusa Usman dinki yasamu wacce zai aurah!!! Kamar saukar aradu haka taji maganar batayi saurin saita natsuwarta ba cikin tashin hankali Wanda batasan yabayyana afuskar taba tace ban ban banfahimcekaba wane Usman din????

Yace kinada wani Usman dinne bayan wannan Wanda yake gabanki??? yakalleta damamaki ganin yanda har idonta yasauya"" yace yadai lubabatu kobakiji dadin furucinaba ne??? Kefa kike matsamun kullum akan nanemi mata na aurah inaki kinmanta harfushi kikeyi idan nace nida aure har abada yalokaci daya nafadamaki abunda nai tunanin zaisanyaki nishadi saikuma naga sabanin hakan???

Saiyanzu lubabatu tasan taso tabka kuskure  dayake yarduniyace ta iyah tsara magana "" tayi saurin boye damuwarta takirkiro murmushi tace wlh nafika jindadin wannan ranar abunda yasa kaga nashiga damuwa inatausayin Kane dakuma kaina danakasa  biyawa mijina da bukatarsa tsayin shekaru

Tanisa inajin tsoron Karka auro wacce zatazo ta tayarmaka da hankali narantse danaga tashin hankalinka nagwammace naga mutuwata!!!!

Wani dadine ya lullube Usman baisan sanda yamannata jikinsaba yana sakamata albarka"" tace bakomai dadyn Abdul"" nidai fatana Allah yabaka wacce zatadauki  nauyin lalurarka kamar yanda kakeso Allah yabaka tagarii yace ameeen ameeen kamardai yanda yabani ke

Ta murmusa wanne gari yarinyar take??? batareda fargabar komaiba yacemata kano"" aranta tace munafuki 🙄yanzu dama zuwanda yake kano soyayya yake"" kafin tatambayi sunanta yacigaba sunanta khadija marainiyace
tace Allah sarki Allah yajikan iyaye yace Ameen jiki asanyaye

Tace inafatardai yan uwanta sunyarda dankar ayimana kamar nasauran dakanema saimunsarai da aure saikuma Abu ya lalace""

Yace  ah ah sukam bazasuyi hakaba"" kafin tayi magana yadauko card din duka yamika mata yanacewa  sauran kwana biyar daurin auren

Saura kadan lubabatu takundumo ashar"" takarbi card din jikinta harrawa yakeyi takurawa card din ido kamar maisabuwar makanta"""

Ga rubutu nan taryen taryen takaici baibarta karasa karantawaba"" tamika masa " Yace harkin kare??? Tace ah Allah yasanya alkhairi yace Ameen"" yakarbi katin""

Yace saikiyi list din abunda kikeso duka zanje dakaina insiyomaki"" dakayan dazakici biki"" tace habadai dawainiyar tayi yawa ai" gana fatenda amare zasuyi kuma gahidimarsu aisaina karamaka nauyi

Nadaigode babu abunda nanema narasa agidan nan"" yamurmusa nasanda haka Amman nasan baxaki rasa abunda kikesoba

Tace wlh bakomai saidai kayanda kawai za a baiwa yanbiki""" yamike daga saman gadon yace barma maganarsu nidagayau nakashe taron biki agidana

Damacen banaso Dan bidia ce kece kike kafewa saikinyi kuma dagakarshe kafin awatse sai anyimaki sata kidawo kinafada bance kigayyaci kowaba

Idankuma Mace takawo kanta nasa aka koreta karkiga laifina

Tace waishi wannan wanne irin tsarine yazodashi meyake nufi dahakan??? Ko anyisata aini akaiwa bashiba

Yazauna yasoma cin abincinsa baidamu data yardaba kobata yardaba danshi yasan matakinda zaidauka maigadi zaifadawa karyabar kowa yashiga gidan koda kuwa lubabatu ce tazo dakanta

Haryagama cin abinsa tana zaune saida yagama tamike zatadauki kayan yace xakidawo ko??? Tace meyafaru kana bukatar wani abune???

Yalangwashe kai kamar karamin yaro yalumshe ido yabude alamar ah""
Murmushi tayi tace tome kakeso??? Yace goron albishir dina mana"" kuma kinsan abunda nafi bukata ayanzu"" tagane inda maganarsa tadosa tace ayya gashi inafashin sallah""" yace kash!!! Tokitaimaka koyan dubarune kiyimun Dan Allah"""

Tace please baban Abdul wlh harda Dan zazzabi nakeji kafin zuwankane nadansha maganie kabari basaura kwana biyarba aini namatsuma  amaryar nan tazo nahuta

Yayi dariya lallaima matar nan watakan harma gajiya kikai dani saikace wani maye"""😾 tana dariya itama tace kafadi sunanka aikai mayene Amman bamaicin mutaneba mayen........😂😂😂


Bata karasaba tasoma dariya yace najidai Amman babu Wanda yasan dahakan saike bayanke bawanda zaiganni yace inada lalurah saifa idan kece kika sanarda kawayenki

Tarike baki waceni dazanbude sirrina agun wasu banzayen kawaye"" ai idan nafada watama saita kwacemun kai""" yace kedai fadi ainasan kumata tunaninku ragaggene dazaran kunhadu waku waku mata zakuta bararda zance

Kuyita fadin sirrin mijinku mijinki koda katuwar loma yake wajen cin abinci baidace wata tasan yanda yakecin abinciba

Shimadayake bakomaiba ballantana abunda akeso yatsaya dagake saishi waihar kina iyah sanarda wasu kawayenki bakyako jin kunya waike wautarki aimatane yan uwanki

Allah yasanda hakan Amman ya la anci matarda take barbada sirrin mijinta gawasu mutanen"" haba Yar uwa lubabatu ma tasanda haka tana boyewa bata taba sanarda kawayentaba toballaike wacce bahalinku daya da lubabatu ba

Kodai kiyarda dahakan kidaina fadawa kowa sirrin mijinki kokuma muce lubabatu ma tafiki wlh"" karkimanta anason mace maikunya

Duk matarda batada kunya da itah da dabbobi daya saboda sune suke yawo tsirara suyi komai agaban kowa basajin kunya







Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




chapter 75
       By
Gentle Lady💃🏽




Ranadai akace bata karya saidai uwar diya taji kunya"" komai nisan dare gari zaiwaye watarana jariri zaizama ango koba hakaba??? 🤔


Su khadija sun kammala jarabawar su cikin sa a Usman dakansa yahado mata kayan lefe Amman baizo dashi gidan ba ranarda yadawo Dubai gidan hajiya yasauka anan yabar kayan

Saida yasake kwana sannan yakoma kaduna"" hajiya dakanta tasamu wasu makota aka kai kayan lefen tareda labila Dan itah hannu biyuce tana wajen dad kuma tanawajen kawarta

Kayanda aka tirkawa khadija kainiban taba ganin lefenda yayi yawansa dakuma kyansaba komai akwai aciki babuce kawai babu kananun kaya kuwa gasunan kamar kazanta"" nikuwa nace sa kananan kaya aisai khadija Amman su agwagwa koda sun saka jemewa zasuyi baridai kartajiyoni🙆🏿

Komai nacikin lefen dakagansu kasan sundace dawacce akasiya dominta""" labila taji dadi dangodiyar da taiwa dadynta tamkarma itace aka kawowa kayan"" masu ganin lefe kowa yazo saiyarike baki bangaren awarwaro dakuma kayan kwalliya abunsai Wanda yaganie masu karatu nabarmaku wannan aranku kukiyasta yanda kayan zasu kasance

Danni idan nace zantsaya fadinsu bashakka zankwana ina bayyanamaku kyan kayan Amman bangamaba dannikaina kayan sun matukar burgeni kamardai ace lubcy tagansu wink😜

Yanganin lefe dayan tsegumi hade dayan gulma duka sungama gani sunkama gabansu""" gwaggo husaina ce tadauki nauyin dauko maigyaran jiki asoma gyaramasu Yar su

Tunranarda aka kawo lefe tadauketa itama labila takwashe kayanta takoma gidan gwaggo Husaina danbataso tayi nisa da sahibarta

Zuwan Usman biyu Amman baya ganinta Dan gwaggo Husaina tahanata fita ko ina"" saidai labila takezuwa idan sakone takarbo yanason ganinta sosai Amman yazaiyi

Saidai suyi waya kuma batawani magana musamman idan labila tanakusa saitayita  zungurarta""" yauma suna zaune an dama mata gumba tanasha labila tanagefe tana game jefi jefi tanayi mata mita waime takejirah haryanzu batashanye ba kinsanfa akwai wani tsimin yanajiranki

Ta wullamata harara kamar tayi kuka tace wlh sahiba bakyasona kinsan kuwa yanda abun nan yake??? Ta aje wayar tana kallonta tace so kai aibandama karnayi barin baki sainace nafi dadyna sonki wlh

Sahiba nasan zakice badadi ko??? Aibarashin dadinsa zaki dubaba amfaninda zaimaki"" tundahar gwaggo tabaki nasan yanada amfani shan nashi awajenki tagyara zama kenifa sonake kisiye zuciyarsa banaso yasake kallon kowa agabansa faceke

Takarasa maganar tana dariya Khadija takaimata duka tagoce tana dariya""" khadija tace waike meyasa kike hakane kokadan ke bakyataya mom dina kishi""

Labila tace kishinme ai itah batada kishi kinga mukuwa munadashi Dan Munasonsa fiye da kammu"" itah dai labila tasan inda maganganunta suka dosa sautari tanayin nazarin hakan cewa mahaifiyarta batason dadynta dakuwa tanasonsa bazata taba cutardashiba

Kodakuwa taga abun cutarwa zata iyah taremasa karyasameshi danhaka tuni tacire lubabatu cikin sahun masoyan Usman tajerata acikin makiyansa

Sukuma wautarta sukegani kodan bata tashi hannun mom dintaba shiyasa batajin haushi"" kowanne da abunda yake sakawa aransa

Wayar khadija ce tasoma ringing"" gabadaya suka maida hankalinsu"" wajenda wayar take kara"" my everything sukagani rubuce akan fuskar wayar

Khadija ta harari labila tace aitunranar naso nayimaki  magana"" labila tace to aiyanzu kinyi kidauka kartatsinke""" kuma kifadamasa munazuba idofa haryanzu baikawo mana invitation ba""

Khadija tawaro ido🙄🙄 tace nicema zanfada ??? Wlh saidaikuwà kar agayyaci kowa damadai walima kawai zamuyi koda baki kyafada

Kafin tagama maganar harkiran yakatse wani yasake shigowa
Labila tace kidauka mana karta katse""" saida tasake ballamata harara sannan tadauki wayar tadauka takara akunne tareda sallama"" daya bangaren aka amsa kema amincin Allah ya tabbata agareki ma abociya kyakkyawar fuska"

Wani farda ido tayi""" bakisake kafin tayi magana yace amaryata kina wani abune??? Tadaga kai takalli labila sannan tagirgiza kai"" kamar yana ganinta

Saida yasake tambayarta sanann tace ah ah maganar kanta tamkar tanayimata wuya"" gabadaya muryanta takashe masa jiki"" yace khadija maganar invitation dinku"" naturo akawo maki dan  gaskiya bazansamu damar shigowa gobe ba aiki yayimun yawa""  cen kasan makoshi ta amsa dato"" yace hmm yanzu hardake wajen yimun rowar ganin kyakkyawan murmushinki

Dariya tadanyi marar sauti tace yihakuri wlh balaifina bane "" yasake gyara zama danyanajin dadin muryanta "" yace towaye???

Taballawa labila harara tace sahiba ce"" labila tayi saurin rufemata baki"" tanagirgiza kai"" yace labilar ko"" Deejaarh!

Aranta tace ya salam talumshe idonta yanayin yanda yakirah sunanta yasaukarmata dawata muguwar kasala"" cikin sanyi murya tace umm

Yace Amman deejaarh meyasa zaki biyemasu kinkuwasan halinda nashiga narashin ganinki??? Wlh jinakeyi kamar zanmutu kinkuwaji yanda kirjina yake bugawa dakina kusadani dazakijiwo sautinsa""

Idanuwanta alumshe suke maganganunsa sunashiga cikin kofofin jininta"" jintayi shiru yasaka yace Deejarh"" sannu ahankali tabude idonta tadorasu akan labila anya dad yasan metakeji idan yakirata da wannan sunan

Jitakeyi  aduniya kaf babu Wanda yafishi iyah kiran sunanta "" yasake kiran sunanta cikin wani salon murya Wanda shikanshi baisan yanada itah ba"" tabangaren Usman idanuwansa harsun rikide saboda chananin sha awarda take damunsa kwana shidan dasuka rage bikinsu ganiyake tamkarma shekara shidane

Saiyaga lokaci yadaina gudu kwanaki ganinta yakandan ragemasa damuwa Amman yanzu tsawon wata dasati uku baisakata"" a idonsaba saidai kawai awaya kuma koshi batadauka saitajamasa rai kokuma duk kunyace

Yacigaba please Deejarh kitaimaka zanzo gobe saikifito naganki koda bazaki dadeba"" aranta tace nima inason ganinka"" dad inajima kamar nayi kuka rashin ganinka"" jinshirun yayi tsayi yace Deejarh bakice komaiba idan bazansamu ganinkiba kidaure kifurtamun kalmarda zata ragemun kewarki"""

tsuru tayi kamar wacce tai karya "" yace kobaxaki iyah ba??? Tace nifa dad kunya nakeji"" labila mikewa tayi tarankwashe ta akai tafita dagudu"" saida khadija tasaki kara

Dasauri Usman yamike yana tambayarta lafiya??? Tayisaurin saita kanta bakomai kafata nadanbuge"" yace ayya sannu amaryata

Kunya takeji idan yanakiranta dawan nan sunan"" hannutasaka tarufe fuskarta"" yace yadai amaryata kunya kikejine??? Tace umm tanagyada kai

Yace ainakusa rabaki dawan nan kunyar"" watakunyar ce yasake jefata aciki"" yana kallon agogo yace kingama lokacin sallah yayi"" Amman bakifadamun kalma kodayaba

Shiru tayi"" yace please ! Kokinaso inzo yanzu kokifada koyanzun nataho"" ido taware tace darefa yayi

Yace toki fadamun"" ahankali tafurta I
L
O
V
E

You
Tayi saurin kashe wayar taboye kanta ajiki filo" bangaren Usman wani dadi yaji yakalli wayar yanasakin murmushi kamar yana kallon fuskar Khadija

Tashi yayi yasallami ma aikatan sukayi haramar sallah"" bashi yafitoba"" sai bayan isha"" i

Khadija kam tana kwance tundasuka gama waya dayake tana fashin sallah batayi yunkurin tashiba harbarci yadauketa awajen

Usman ne bayan mota Muhammad yana tukashi zuwagida hannunsa katin daurin auren sune da khadija yau yakeson sanarda lubabatu maganar aurensa saboda yasan halin magulmata shiyasama baibawa kowaba danyasan muddin yarabashi tokota halin yayama saitasamu labari

Jinginawa yayi jikin kujerah yalumshe idonsa tundayake baitabajin fargabar sanarda lubabatu yanason kara aureba saiyau kirjinsa saibugawa yake

Sunakawo wa kofar gidan yasakejin gabansa yafadiii dasaurii yasoma furta innalillahi wa inna ilaihir rajiun  حسبنا الله ونعم الو كيل





Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠




Chapter 78
       By
Gentle Lady 💃🏽



Yasake kecewa da dariya yace yakike kuka kizama jaruma mana aikinsan nibana magana biyu kijirah kafin tashigo gidan munsan yanda zamuyi ai akwai bakaken aljanu dakuma masu shan jijin bil adama

Hayyanul zairi yayi tafiya kasar iraqi na aikeshi nemomun wadansu kayan danakeso nayi tsafi dasu"" zaidaukeshi tsayin wata kafin yadawo dankuwa dajinda zaishiga yanada hadarin gaske bartashi aljani saboda akwai miyagun dabbobi masu cin naman aljanu acen idankuma mutum yasake  tsautsayi yakaishi cen saidai uwarsa tahaifi wani

Inason Gina fadata acen saboda wani dalili"" dayana nan tuni aikinki yagama danhaka saiki jirah kafin yadawo yanakai karshen maganar yadafa tsapappen zakinsa take yabace dashi da zakin lubabatu saida tazaburah tamiyarda madubin mazauninsa

Tagumi tabuga aranta tace anya wannan bokan baihada iri da aljanuba??? Nidai naga abunnashi saigaba gaba yakeyi yanzukuma waifada za aginamasa a Iraqi lallai wani Abun sai matsafa

Hmmm yanzun inaji inaganidai Usman saiya auro wannan shegiyar yarinyar"" tayi shiru aikuwa inyasan wata baisan wataba bakin zuciyarsa zan kulle tayanda zaiyita masifa da mutane baburuwa koni tashafeni Amman saina lalata  wannan auren badai Saurah kwana biyarba hmm ayimuganie to

Mikewa tayi tabude drawer tadauko wata Yar battar karfe tafita zuwa kitchen takunna gas takara battar karfen ajikin wutar tasoma daukar zafii saida tayi zafiii rau sannan takulle bakin battar takoma daki tana murmushin mugunta

Lokacinda wannan abun yafaru Usman yadade dayin barcii acikin barcinsa yasomajin ransa yabacii zunbur yamike yakalli agogon dakinsa asuba takusa tsaki yasoma yi kamar Wanda akaiwa laifi

Jiyakeyi tamkar yarufe kansa daduka"" yarasa yazaiyi hannuwa yasaka yadafe kansa yanakiran innalillahi ahankali yadan samu natsuwa yasakeyin addua Yakoma yakwanta danbarci yakeji

Washe gari lubabatu batamasan sanda yafitaba wajen aiki kuwa gabadaya suka rasa gane kansa koda maganar arxiki kaimasa saiyamiyar maka datatsiya

Idankuma kadameshi da surutu yahauka da masifa kamardai Wanda kare yaciza yanazaune akan kujera yakurawa tarin takardunda  suke gabansa ido kamar maitunanin wani Abu gabadaya jinkansa yake kamar banashiba

zuciyarsa sai tururi takeyi kamar hayaki"" wayarsa yadauko yakuramata ido yaukwanansu biyu basuyi waya da khadija  ba tunranarda yaji ransa yabaci yaji bayason kiranta lambar yakamo yana kallo kamar zaikirah

Yacigaba da jujjuya wayar cenyadanna kirah tayita ringing hartakatse ba adaukaba nantake yaji ransa yabaci yasake kirah

Khadija tana zaune tareda labila tanayin karatun suratul bakarah labila tana saurarenta saboda walimarda za aimata sai Amarya tayi karatu

Shine takeson labila taduba mata duk da tasan bata mantaba wayarta tana hannun labilar sanda yakirah dayake bata ringing sosai bata daukaba..

Dakiran yasake shigowa garin takatse kiran Ashe tadauka kuma hankalinta bawajen wayar yakeba Sam batamasan tadaukaba
.
Shikuma usman yanaganin andauka haryabuda baki daniyar sakin magana yajiyo zazzakar muryar khadija tana karatu.

Wata irin sassanyar ni imace yaji tasauka azuciyarsa tuni yanemi damuwarsa yarasa"" aitake yasoma record yasaka Hans free

Idanunsa yalumshe tamkar maijin barcii harcikin kopofin jininsa muryar khadija take shiga tsayin wajen mintuna ashirin barci maidadi yayi awon gaba dashii

Cen cikin barcinsa yakejin ana helo dad kanajina maryar labilace tatasheshi baimasan yayi barcinba tashi yayi"" yayimika tareda hamma lahaula walakuwati illah billah

Save din recodin din yayi sanann yasake kirah danwasai yakejinsa kamar ancire masa dukkan damuwarda keransa

Tanasoma ringing labila tadauka da sallama ya amsa yanasake lumshe idonsa tace dady barka dahutawa ya aikin??? Yace Alhamdulillah ina khadija??takai kallonta  wajenda khadija take tace gatanan yanzun mukagama karatu zamufita raba invitation ne"" yace saiyanzu zakufara rabawa??? Tace ah ah tunjiya muka fara dare yayi saimuka dawo gida Dan akwai mutane dayawa wadanda yakamata mugayyata

Yace shikenan tokarna tsaidaku saikundawo kikula kinji yarlele"" tace to daddy nagode"" yanaso yace tabawa khadija kuma yakasa danhar yanzu yanajin Dan nauyin labilar

Takatsemasa tunani dacewa dad gasahibar tayi maganar tana mikamata wayar  takarba itakuma tafita dantalurah inhar gabantane sahiba bata iyah wata firah dashi

 takara akunnenta kafin tayi magana yace amincin Allah yatabbata agareki hasken zuciyata"" wani daddadan sanyine yaratsa kofofin sadarwarda ke kaisako ga zuciyarta talunshe ido tanamai saukarda ajiyar zuciyar wacce Usman yajita

Tare dakai ma aboci fara a dakwarjinie"" wani dadiyaji marar misaltuwa waima anya khadijarsace tafurta masa wannan Kalmar??? Kafin yagama tunani tace inafatar kanacikin koshin lafiya???

Sumar kansa yashafo yace INA lafiya fatar kema haka??? Tabude idonta ahankali tana kallon ko far dakin tace idan nacemaka haka nayi karya hubbyna

Wayyo dadi kasheni kusan Usman sumar zaune yayi"" cikin kasalarlar murya yace meyake damunki Deejarh Na??? Tanisa akwai wani Abu dazaidameni aduniyar nan inatareda gwarzon namijie kawaidai kaunarka dakuma kewarka sune sukataru suka dameni azuciyata

Harnakejima tamkar narasa wani muhimmin bangare ajikina"" yagyara zamansa yanalaso busassun labbansa haryanzu idonsa kullesuke dantsabar yanda yake jin dadin firar jiyakema tamkar asararin samaniya yake yawo

Deejarh yakirah sunanta akaro nafarko ta amsa na am hubbyna"" yaja ajiyar zuciya yace waidagaske bamafarki nakeyiba??? Tarausayarda kai tace kamarya hubby ???

Yamurmusa wlh jinakeyi tamkar inawata duniyarda babuwani mahakuli acikinta face nidake bantaba tsintar kaina atsantsan soyayya irin wannan ba"" waidama haka soyake da dadi hakika nasake yarda soyayya tafi Zuma dadi inhar mafarki nakeyi banafatar nafarka daga wannan daddadan mafarkin harkarshen rayuwata

Inaso incigaba dajin wadandan dadadan kalamanki sunamatukar sanyaya manie zuciya""" khadija tadan kishingida tace kokadan masoyina ba mafarki kakeyiba a farke kake kabude idonka zakaganni akusa da zuciyarka indai har kalamaina suna sanyaka nishadi nikuma bazangajiba wajen furtamaka su harsaisun cika duk wani bango dake zuciyarka

Nikaina bansan soyanada dadiba saida nayidace da ma aboci soyayya irinka hakika ninasan nayi dace samunka agareni babbar nasarace inarokon Allah yasake mallakamun kai hasken zuciyata

Usman bakin nanfa yakirufuwa wai Ashe Usman ya iya soyayya??? Abunda baiyiba koda budurwarsa ta mafarki yanaji ajikinsa kamar yanzune zaiyi auren soyayya

Matarsa ta mafarki ya auretane saboda yanajin tausayinta akan abunda matar ubanta takemata "" haka sauran matansa daya aurah azahiri yanasonsune kawai danbukatar sha awarsa lubabatu kuwa jiyakeyi kamar adolene ya aureta

Soyayya tagaskiya kuma kwaya daya tak babu macenda yadamkawa itah sai khadijar sa"" tsayin lokutanda suka dauka labila tanashigowa khadija tacemasa zasufita

Yayimasu Allah yakiyaye tareda kafuzza masu dadi tanakashe wayar tadafe kirjinta labila tahauyimata dariya tace inafatardai bakimanta ko kalma dayaba

Harara takaimata taçe wlh kinbani aiki sahiba bakiji kunyarda najiba"" labila tazauna tana fuskantarta tace haba khadija mijinkinefa Wanda zaki aurah wllh ajiye kunya zakiyi agefe kirungumi mijinki idankuma bakiyiba kinaji kinaganie kunya tacutardake kinga tashi muje abarwannan darasin saigobe

Khadija tamike sukafita suncewa inna suntafi tayimasu adawo lafiya






Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 77
       By
Gentle Lady💃🏽




Anason mace mai kunya hausawa sunacewa kunya adon yammata"" mace ballagaza itace batada kunya

Nidai shawarda zanbaki Yar uwa inhar mijinki yazama irin haka kokuma akasin hakan kisamu kuwarware matsalarku atsakaninku batareda kunyiwa juna tonon asiriba

Danwannan babu abunda yafishi zama tonon asiri "" shinwaima idan kinfadawa wata tanada maganinda. Zatabakine ??? Ninasan babu abunda zatacemaki saidai tace kiyi hakuri shine kawai

Shawarda zanbayar itace idan mijinki yakasance kinkasa biyamasa bukatarsa ta auratayya tokirika hadamasa da dubaru wadanda kikasan basu sabawa addiniba zaki iyah yin koma mene danyasamu gamsuwa ajikinki saidai banda waje daya Wanda Allah yamana iyaka dashi wato bayagamutum

Koya mijinki yakai kolokuwar bukata inhar yanuna maki yinhakan karkiyarda Amman bayan nan ko  inane halal ne "" idankuma bukatarsa tawuce duk wata dabara dazaki masa tokibarsa yayi aure

Karkuma kitada hankalinki idan kikaga ya auro wacce take iyah hakuri da bukatarsa"" karkiga laifinsa bashine yayi kansaba haka Allah yagadamar yinsa saiki tausaya masa

Idankuma baida halin auren Yar uwa inkinada hali kibashi kudi yayi bawai faduwa kikaiba sakamakon aikinki yana wajen Allah" idankuma bakida hali kema tosaiki bashi shawara yarika hadawa da azzumie domin kare kansa daga fadawa ga aikata zina
 Manzon Allah yanacewa awani hadishi dayake kwadai tarwa akan aure"

وقال صلى الله ءليه وسلم يا معشر الشباب من استطاع منكم الباءة فليتزوج فإنه أغض للبصر وأحصن للفدرخ ومن لم يستطع فعليه بالصوم فإنه وجاء رواه البخاري ومسلم
manzon Allah tsira da amincin Allah sutabbata agareshi yanacewa yaku taron samari masu iko daga cikinku tosuyi aure ma ana wadanda sukeda kudin auren kuma sunkai munzalin yin auren sunada bukatar mata "" cewashi aure yanakarewa daga ganie dakuma sha awa
" Wanda kuma bashida iko ma ana baida halinyin auren kokuma idan yayi auren bazai iyah daukar dukkanin hakkin matarba sai manzon Allah yace nahoreshi dayayi azumie sabodashi kariyace

Wannan hadishin basamariba harmai mata zai iyah aikidashi inhar yaga yakusa fadawa ga aikata zina

 Yar uwa saikibashi shawara yafara azumie kema zaki iyah tayashi kinga yasamu ladabiyu galadar azumie kuma galadar kiyaye kansa dadi biyu kenan

Idankuma kece dayawan bukata shikuma bayada shima zai iyah wasadake danyaragemaki kamardai shidin saikuma kikara da hakuri idankuma kinji bazaki iyaba zaikaiki ga hakala saikisameshi kuzauna kifadamasa karkiboye komai

Tsakaninku kuwarware matsalarku idan baida lafiyane saiyanemi maganie idankuma haka Allah yayishi saiya sauwake maki kisamu daidaike kuyi rabuwar mutunci Amman gaskiya indai harzaki iyah hakuri tohakurin zaifi zakici ribarsa agobe kiyama Allah yasa mudace

Lubabatu tace wlh bayabon kaiba nikaina idan naji masu sakin baki sunafadawa wasu matan sirrin gidajensu haushi sukeban saikuma kaga wadanda sukafisu wayo subasa fadar nasu saidai su saurari naka

Usman yace aishine rashin hankalin nagode Allah da matata batacikin ire iren wadan nan matan"" nikuwa nace Allah yasa masu karatun wannan labarin basacikin wadan nan matan

Idankuma kinayi tokinji dagayau saikigyara rawarki kisauya taku wadanda kuma basuyi aurenba sukiyaye dangaba yayimasu amfanie

Zaki iyah turawa wata domin takaru kema kin isarda sako Allah yasa muzama masu rike sirrinmu Ameen

Lubabatu tamatsu tabar dakin danfayau tashiga rudanie

Tayakuna fuska nidai zankwanta kakula dakanka""" yace shikenan Allah yasauwake konazo natayaki barcin???

Tayi saurin cewa ah ah nagode nahutardakai saida safe tayi maganar tana bude kofa"" yace tosaida safe tafita taturo kofa"" wai wata sabuwa lubabatu harda gudu gudu take hadawa jitakeyi kamarma tazama iska takai kanta wajen  *hatsabibin boka* tanashiga dakinta sauran kadan tafadi garin mugun saurinta""
Takulle kofa tafada dakinta wajen drawer tadauko akwatin tabude tafitoda karamin madubin sai walwalniya  yakeyi tashafa cikinsa jikinta yana rawa tareda kiran sunan *hatsabibin boka* muryanta tanarawa kamar maikuka

Daka ganta kasan tanacikin tashin hankali shafawarta keda wuya saiga wani duhu gabadaya ya mamaye dakin abunda bata saba ganiba gabadaya dakin yayi baki kirin wutar dakin tadauke bataganin kotafin hannunta

Wani tashin hankali tasake shiga al amarinda yasoma saukarmata da faduwar gaba lallai wanann matar kilanta wajen boka takaishi shine abunda lubabatu tasoma rayawa aranta

Batagama tunaniba haske yasoma samuwa acikin dakin sannu ahankali haryagama mamaye dakin saiga *hatsabibin boka* yabayyana asaman tsafaffen zakie ido hudu kawai lubabatu tayi dazakin tasaki fitsari daga zaune ganinhakan yasaka *hatsabibin boka* yatintsire da dariya kamar bazai dainaba

Zuwa dakiku ashirin yatsuke fuskarsa tamkar Wanda baitaba dariyaba saiga idanuwansa masu munin gaske sunkoma koraye shar yasoma wani irin hucii kamar mesa hucinsa haryana fesowa lubabatu

Cikin tashin hankali tace yakai wannan hatsabibin matsafi kasani yauban kirakaba saida mummunan labari saiga hawaye sharrr akan kumatunta suna zarya

Tacigaba waini Usman zai ha inta??? Haryatashi aure baisanarda niba??? Sai anasaurah kwana biyar waiyama akai aikinda kaimasa baikama wannan shegiyar yarinyar ba

Haryanxu bokan kallonta kawai yakeyi baice uffanba saida takai karshen maganarta sannan yabushe da dariya yace wannan ranar batada sa a gareki

Tunkafin kisanardani gabadaya aljanuna sunce bazasu iyah jayayya dawan nan yarinyarba sanadinda yasaka kikaga batakishiba aljaninda yake yin wannan aikin yakasa shiga jikinta

Hasalima yanzun yanacen yanajinya sanadin rauninda yasameshi dayaso rike hannunta"" kozaisamu kafar shiga jikinta

Cikin rudani lubabatu tace nashiga uku boka wannan kuma wace irin hatsabibiyar yarinyace???

Wajen wane irin boka takaini Wanda yakeyiñ aikinda yagagari aljanunka su shafeta???

*hatsabibin boka* yasake kecewa da dariya yace nikaina yau banacikin yanayi maidadi lokacinda kika kiranie ina karkashin kurkukuna dayake kasan kasa"" ina ganawa wata aljana azaba!!!

Cikin lubabatu yaduri ruwa kamar tazunduma dagudu yacigaba kirankine yasaka nahau dokina nazo gareki kisani wanann yarinyar tasha banban da irin matanda mijinki yake soyayya dasu

Wannan takere duk wani tunaninki saboda hafizace kuma tanada yawan ibada narantsemaki da karfin tsafina dana gadà kaka da kakaññi babu wani aljani aduniya daya isah yatunkareta haryashiga jikinta batareda yakone kurmus ba yamutu

Kebarta mutuwama ko tokarsa ba azasamuba!!! Take lubabatu tasoma yarfe zufa tace togaskiya banaso ya auri wannan yarinyar danmuddin tashigo gidana zatayi wuyar fita "" kaiyagirgiza yace babu makawa saiya aureta!!!

Saidai kiyi hakuri idan akai auren kisake kirana kafin lokacin ninasan hanyarda zanbi domin mukasheta danwanann muddin tana raye tosaitaga karshenki

Lubabatu tadafe kirji tace wlh saidai naga karshenta Dan ubanta tafashe dakuka"" yanzun dole saitashigo gidan???

Yace tabbas kimadaina barnar hawayenki babu abunda zai gagari *hatsabibin boka* idankuwa har akwai wani aiki dazai gagareni tonikuwa banchan chanchi akirani *hatsabibin boka* ba

Kikwantarda hankalinki kamar tsumma aranda"😆😆😆" tace wane irin kwanciyar hankali zanyi bayan anashirin kawomun annoba!!

Waikunjitafa🙄 wai annoba! Bayankuma itace annobar😕



Masu karatu kuyi hakuri da iyah abunda kukesamu baidace kuna rainawaba inama laifina inayin wannan kullum karfa kumanta inada aikinyi bawai zaman remote nakeyiba kurika hakuri daduk abunda kukasamu kunsan typing dinnan kansa wuyane dashiii bawai yawan typing ba Allah yasa kuna amfani da abunda kuke karantawa

Idankuma kawai dannishadinku kuke karantawa babu amfanin inrika bata lokacina😒






Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠




Chapter 79
      By
Gentle Lady💃🏽



Akwana atashi hasarar mai rai yaune ake daurah auren khadija"" kawu shine yazama waliyin khadija Dan muktar yace wlh bazasu je yola ba aibadole sai anje wajensa za aiwa kanwarsa aureba tundahar yace shibayada wadansu yaya tosuma sunmanta dashi kamar yanda yamanta dasu

Duk da bahakan kawu yasoba Amman yakyale babban masallacin jumua dayake kano bayan antashi sallar jumua akadaurah auren
          *Usman Adam yunus* &
          *khadija Muhammad*


Akan sadaki dubu talatin kamardai yanda khadija tace akarba dan samun albarkar aure"" tunda aka daurah auren Usman yasomajin wani irin farinciki acikin ransa""

Waiyau khadija tazama mallakinsa Abdul saitsiya yakemasa danshima baya kasar yana minna dashi da iyalinsa acen yakoma dazama da iyalinsa bikinne yasa sukazo  farincikinda Usman yakeciki bazai faduba mai karatu ka kwatantashi aranka"" Usman yanacikin dakakkiyar shadda fara saol tasha aikin wuta da babbar rigarsa"" takalmansa hularsa agogonda yake daure akan hannunsa komai iri dayane  muktar ne tareda abokansa suka karasa sukabashi hannu sukagaisa sunatayashi murna
Daurin aurensa yatara dubban jama a anci abinci tareda abubuwan sha kamar gabanza akesamosu naman kajikuwa kamar suyi magana

Anagama daurin aure suka kwasa  da abokansa  saigidan hajiya"" huuuu nikam naceyau nasan baza agane labila ba""

Da la asar za agudanarda walima makarantarsu khadija  gidan hajiya yacika da yan uwa da abokan arxiki ko inakaduba mutanene gasunan kowa kaganshi yanacikin farinciki " kubrah matazo tunjiya da faruq kubrah yayanta uku yanzu suma sungirma tubarkalla"

Bari muleka gidan Amarya muganie tundaga zaure nasomajiyo kamshin turare dagaji kaima kasan hadaddiyar Amarya ce agidan waiwai masha Allah yanda naga khadija badan naganta tareda labila ba dabazan ganetaba" muktar kansa dayaganta bakinsa kinrufuwa yayi saboda ganin yanda kanwarsa takoma tamkar tauraruwa duk inda tawurga saimutane sunjuya"" tayi kyau matuka zanen lallinta yabada ma ana sosai gidayacika dayanbiki masu cinye shinkafar mutane😝

Hayaniya nasomaji awaje naduba naga kosuwaye mezanganiey😳 taron yan group din Haneefa Usman ne wato zangon labarai"" su rabie da Aisha harture fateema  Ali sukeyi saboda zumudi

Bayansukuma zugar su kausar luv" ne Jidda Aliyuu" Haneefa Usman" hafsat m Sharif" fateema zuhurah " fateema Shuwa"rahmaluv" naanyluv" jameela muhd Ali"  Shafa atu Umar maryam Lele Style"" Aisha iliya"" Anty Jidda billy baby"" ummu fauzan " kaikai wadansu digaya Nagano sun lunka nafarkon danabiyu idan manatsaya rubuta sunansu aikuwa sai nacika safin harma inbude wani shafin🙄

Gefe guda nakoma nadauko wata takardar nasoma rubuta sunayen wadanda sukaje✍🏼 naany rabie Aisha sune nafarko sanann sauran sukabiyo baya saida nacika shafi bakwai najinjina wanann karartasu nalinke takarda Na ajeta dazaran munkai amarya zandankata gahannun lubabatu domin tayimasu kyauta maitsoka tukuicin murnarda suka tayata wacce bataji sunantaba kuma taje yawan people baisa nagantaba saitamun magana akwai sauran takarda daya😂😂

Gabadaya suncika gidan nikam nace anyakuwa wadan nan duk angayyacesu🤔 inajikamar akwai gayyar sodii labila tarasa inama zata sakasu danjin dadi takaisu babban falon gidan hajiya tajido masu abinci sukaita narkaa nikam koruwa banshaba!!😑

Baridai muleka bangaren Amarya" au sorry uwargida muga wainarda aketoyawa acen""  tunda nashigo unguwar najita tsit tamkar ba biki akeyiba nakarasa wajen maigadi domin yabudemun kofa yace alhaji Usman yace ko kuda sukazo kar abarsu sushiga harsai ankawo Amarya

Nayi murmushi nace kowayacemaka??? Yace ah kowafa nace kirashidai kaji nikam nasan bazai hanani shigaba idan baniba babu mai iyah dannar kirjin lubabatu babumusu yaciro waya zaikirashi Na kaikaici idonsa nakude gidan saidai yajuyo baiganniba "" tunda nashiga gidan naji shiru nace wayyo labila tayiwa makota bakinciki dayanzu sunanan sunadibar gara

Nayita kwada sallama najishiru nahaye harbangaren lubabatu tunkafin inturah kofa nakejin kukanta baki narike yaufa akeyinta uwargida nakuka

Kwance take kasa sairusar kukatake takeyi tun lokacinda Usman yashirya yacemata yatafiii tayi zaune tana kallon agogo tanata addua Allah yasama yayi hadari yamutu ubankowa yàhuta

Nikuwa nace cenkigani atukunyarki 😕in Allah yaso qalau zaikai tunda taji biyu tabuga tasan andaurah aikuwa tafado kasan gado tayita rusar kuka gashi Usman yahana kawayenta shigowa dansaida sukazo maigadi yace babuwacce zatashiga

Saida suka kirah lubcy tazo dakanta yace ogane yabada wannan umurnin takirashi awaya yace shine yabayar dolensu suka koma tadau alwashin saitasa *hatsabibin boka* yayiwa wannan khadijar kisan gilla mutuwa mafi muni acikin kowacce kalar mutuwa

Gawartama bataso asamu ballantana aimata sallah tundatake babu wacce tataba sakata adamuwa tazubarda hawayenta sama dawannan amaryar aibasaida tsafiba takissa  kawaima saita fitarda itah kuma bazata huceba muddin khadija tana numfashi adoron kasa saitaga karshenta!!!

Nikam bakin kofa natsaya ganin har anyi la asar nasan yanzun haka antafi walimar sallah nagabatar sannan nawuce alokacin lubabatu barcin wahala yashureta""


Harabar babbar islamiyyar tacika makil abokan kasuwancin Usman dakuma yan uwansa tarin masoya dakuma makota tarin malaman makarantar dakuma manyan malamanda aka gayyata wajen ba masaukar tsintsiya bayan anbude taro da addua akakirah Amarya labilace tatake mata baya sanye take cikin atamfa mairatsin bakii daja sai babban hijab dinta harkasa tasaka safa hannu dakafa gakuma likaf babu hanya ko daya dayayi Saura ajikinta  takarasa wajen malamin takarbi lasifikar tasoma karatu gabadaya wajen yayi shiru

Usman baisan sanda yafurta Alhamdulillah har takare karatu takoma mazauninta Usman baisaniba saida babban malaminsu yafara wa azi akan zamantakewar aure

Aure rahamane ba karama bawani bangarene najin dadi rayuwa duk Wanda yatakashi yaji dadi sosai "" Allah ne yace ayi aure domin rahamace bakarama yayimana

Allah yanacewa
 (فانكحو اماطاب لكم من النساء مثنى وثلاث ورباع فإن خفتم ألا تعدلوا فواحدة أوما ملكت أيمانكم)

Ku auri mataye  wadanda aka halartamaku aurensu daga cikinku   Ku auri biyu ko uku ko hudu idankuma kunsan bazaku iyah yin adalciba atsakaninsu toku auri daya ko abunda dayanku ya mallaka ma ana kuyanga suratul nisa i

domin aure yazama rahama agaremu Allah yacewa annabin rahama "

(ولقد أرسلنارسلا من قبلك وخعلنا له‍م أزواجا وذرية)
Mun aikoda manzanni gabaninka mukasanya  mata dakuma zuria agaresu suratul ra adi

Aure wata bbbar rahamace dakuma jindadin rayuwa agaremu kamar yanda Allah yakece awata aya datake cikin suratul rum

(ومن آياته أن خلق لكم من أنفسكم أزواجا لتسكنوا إليه‍اوجعل بينكم مودة ورحمة إن فى ذلك لآيات لقوم يتفكرون

Acikin wata aya anhalittamaku mata ku auresu  domin kunatsu da itah matar   kuma akasanya kauna dasoyaya atsakaninku dakuma rahama 

mace idan tayi aure alokacin tacika Rabin addininta sauran saitayi biyayya gamijinta yake wanann Amarya kisani aljannarki tana karkashin tafin mijinki nasihardà zanyimaki Anan shine ki kiyaye hakkokan mijinki idan kikaji ance hakki toyasafi komai dakomai abunda yarataya awuyanki ke Amarya 

Manzon Allah yanacewa awani hadisi"  إذادعا الرجل إمرأته إلى فرشه فلم تاته لعنته‍ا  الملاعكة
 حتى تصبح
Idan miji yakira matarsa zuwaga shinfidarsa  idan batazoba "" mala"iku zasuyita la antarta hargari yawaye

Tokunji mata dayawa yanzukuwa masu gudun mazajensu bazasuy kirguba""


Kiyiwa mijinki biyayyya duk abunda yasaki jikinki yanarawa kije kigabardashi cikin dadin rai""

Manzon Rahma yanacewa acikin wani hadisi  لوكنت آمرا أحدا أن يسجد لأحد لأمرت المرأة أن تسجد لزوجها" رواه الترمذي"

Daza a umurci wani yayi sujada gawani  lallai daza a umurci mace tayiwa mijinta sujada

Acikin wani hadisi manzon Allah yanacewa duk matarda tafita gidan mijinta batareda izinin mujintaba tanacikin tsinuwar Allah da la antarsa hartadawo gidanta  kukama tanemi yafiyar mijinta ma ana tanemi gafararsa yayafemata

yake wanann Amarya nahoreki darike sirrin mijinki kisanI ke sitrace gamijinki baidace kibayyanawa wata sirrin mujinkiba koya kike da itah

Kikasance mai tattausan lafazi agareshi karkisake muryarki takere tashi awajen magana karkirika magana dashi kamarwani yaronki Dan asabe nafadamaka magi yakare babu daddawa gishirima sauran nagobe haba Yar uwa ahakañ tayakikeso kisamu rahama ""

 kizama maikwalliya dakuma kyalkyali kullum aganki tsaf dakinkima yayita kamshii  kizama maitsafta karkibar bakinki yanadoyi ansha miyar kuka tsami gaye Dan matsitsi dasauransu

 Ba ahanaki cinkomaiba Amman dazaran kinci lokacinda zakije bangaren maigida saiki tsabtacesu karkijemasa baki yana hamami kamar shaddar Masai

Idankika gyara kekanki zakifijin dadi""kirika aske gashin  gabanki dana hammata duk inda kikasan wata dauda zata makale kiwanke wlh wata saikuga gashin hammatarta kamar iccen kwakwa natabbàta  wata kwararriyar maikitso zata iyah kitsashi har asamasa ribon

yake wannan amarya inahoronki dakarki sake kibudabaki kicewa mijinkii  yasakeki!!

Manzon Allah yanacewa duk ranarda  mata tacewa mijinta yasaketa batareda wañi daliliba Allah yaharamta mata jin kamshin aljanna aljannama bazataji kamshintàbà ballanta tasaran shigarta Allah yakiyashemu


Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠



Chapter 80
      By
Gentle Lady💃🏽


 Karkisake kibar kawarki tazauna maki kangado " gadonda mijinki yake kwanciya kuraya sunnar ma aiki wata shibgegiyar katuwa tadosana duwawunta inda yake kwanciya batako jinkunya"" inbanda lalacewar zamani mezaikaiki dakin kwanan kawarki??? Koda kinje wajenta kikwahe falo mana kofalon asamarwa maigida kujerah ta musamman  ko yaranki karkibari surika zama akanta""

Haka kwanonda yakecin abinci kokuma cup dinda yakeshanruwa karkibari wata takafamiki baki inda yazamana mijinkima idan zaisha ruwa awajen zaikafa nasa yadace komai namijinki yazama dabanne danakowa

Yake wannan Amarya kisani tubalinki shine gidan mijinki yadace agareki duk inda kikaje karkisaki jiki awajen face kinadakin mijinki kiji aranki koda gidankune bazaki sakeba bisaga dakinki

Kizauna dayan uwansa lafiya dakuma makotanki idankinada abokiyar zama kidauketa tamkar Yar uwarki karkizama cikin sakarkarun matannan masu shegen kishin tsiya sudai bashason koya dagasu sai yayansu"" ramin kurah kenan

Idan kikace haka tokinyi kamaice ceniya da kurar kenan"" kirike abubuwa guda shida wadanda zanfadamaki

1 Ibada
2 tsabta
3 iya magana
4 rike sirri
5 hakuri
6 iyah abinci

Dadai sauransu inhar kika rike wadan nan zakici ribar zaman aure anan zandakata dankuwa idan nace  zanfadi fa idodan aure dakuma hakkokansa zamukwana muwuni banfadi ko kwataba inayiwa wannan Amarya da agonta fatan samun zaman lafiya dakuma zuriya dayiba ma assalam

Daganan yamikawa wani malami yatashi yasoma dajawabin godiya duk abunda zanfada malam yarigada ya fadeshi inarokon Allah yasa kowa yayi amfani da abunda yasaurara kuma yayi aiki dashi "" Ameen munayiwa dalibarmu kuma malamarmu fatan samun zaman lafiya dakuma kwanciyar hankali agidan mijinta Allah yasa ace kara da akayi Allah yakauda fitinardake tsakaninsu Allah kakore shaidan atsakaninsu Allah yabasu Yaya nagari "
Subhana kallahumma  wabihamdika ash"hadu anla ilaha illah anta astagfiruka wa atubu ilaika

Daganan akabaiwa  wani malamin yabude taro da addua"" akasoma raba takeaway"" kowa Yakama gabansa saifatan Allah yabasu zaman lafiya

Sunakomawa gida akasoma shirye shirye"" kai Amarya su gwaggo hasana suka haushirya Khadija tuni labila tagama shirya kayanta"""  anagama sallar magrib akafito da itah muktar dakinsa yashige yanata kuka kamar karamin yaro

Hakan yakasa khadija tasoma kuka itama dakyar akafitarda itah gidan su inna masunkara datasu nasihar labila motarsu daya da khadija sukahau hanyar kaduna

Sai wajajen karfe takwas sukakai duk da gudunda sukeyi harcikin mota banda kuka babu abunda khadija takeyi har akakai gidan maidagi yahangame masu kofar gidan motoci sukafara shiga gabadaya saida harabar tacika labila tayimasu jagorah hawa nahudu gabaya ansauya tsarin bangaren komai sabo hul akazuba gashi wajen yasha fentii sai kyalli yakeyi"" Amarya tashiga dakafar dama tareda addua

Bayan tazauna sannan akataso gabadaya zuwa bangaren lubabatu balaifi tayi wanka tashirya Amman dazaran kacika kallonta  zakasan tasha kuka tun nan labila Tasha jinin jikinta

Dantunda sukashigo gidan tasan dadynta baibari akayi taroba sugwaggo hassana sukabata amanar Amarya Dan marainiyace takarba kuwa hannu  biyu akaimasu nasiha daganan suka rankaya bangaren Amarya

Akasoma kallon dukiyarda aka narkamata kai abun saiwanda yaganie"" Usman baishigo gidanba sai wajen goma hawanabiyu yatsaya Dan nan yamaida kayansa yarage kayan jikinsa yawatsa ruwa yayi sallah yanamai nuna godiyarsa ga Allah dabaiwarda yayimasa

Ranar kwanan farinciki yayi washegari tundasafe lubabatu tasa akahadawa dangin Amarya abun karinsu saihada hadatake taware kamar ba itaba"" dangin khadija sunata yaba halayyar maman labila

Anan sukaci abincin rana sannan sukasake gyarawa Amarya bangarenta  dazasu wuce sukasake yimata nasiha tanakuka sukarabu labila takoma rarrashi haka akawatse hardare khadija batasakeba

Suna zaune falonta bayan isha I"" Usman yaturo kofa yashigo da sallamarsa labila tagaidashi sannan tamike tabasu waje

Falon kasa tasauka takunna kallo tana zaune lubabatu tasauko sosai tayi mama kin ganinta danbatasan sanda tazo gidanba kokuwa tareda Amarya tazo oho

Labila tagaida itah ta amsa cikin sakin fuska tace yaushe kikazo??? Batareda takalletaba tace jiya aitare nazo dayan kawo Amarya

Lubabatu tagyada kai batasake cewa komaiba tamiyarda hankalinta wajen kallon

Usman ahankali yataka harsaman kujerah yazauna"" khadija gabanta yasoma dukan uku uku hannu yasaka yadago habarta saiyaga hawaye cikin muryansa maisanyi yace meyasaki kuka Deejarh na??? Kodai su inna ne dasuka tafi suka barki??? Kamar yace tasake fashewa dakukan yajawota jikinsa yasoma lallashinta haba Deejarh na kedaya kamata kiyi farinciki wannan baranar kukabace gidankifa kikazo karkimanta kinatareda annurin zuciyarki

Kukanki zaisakani adamuwa Dan Allah kidaina yimun asarar hawayenkin nan masu matukar tsada"" shiru tayi saidai tanajan ajiyar zuciya sannu sannu saboda kukanda tayi"" yace kokefa idankuma kikasake yin kuka nima zantayaki kintaba ganin kukan babban mutum??? Dariya tasoma tasake shigewa jikinsa tana girgiza kai"" shima dariyar yayi yace toyau zakiganie inhar nasakejin kukanki nima zanbude bakina harmakota sujiyo

Dariya takamayi tanaboye fuskarta cikin rigarsa murmushi yakeyi sosai yace kinci abinci kuwa??? Kai ta gyada yace banyardaba yanaji cikinki yadame??? Yayi maganar yanashafo Dan lafaffen cikinta

Tace wlh naci dasahiba kuma banajin yunwa"" yace kintabbata tasake gyada kai yace shikenan kitashi kishirya saiki kwanta kihuta nasan haryanzu gajiyar biki bata fita jikinkiba zanturo labilar saiku kwanta tare hamdala tayi acikin ranta tace to

Jayeta yayi daga jikinsa yadago dafuskarta yana kallo duk da tasaukarda  kwayar idonta kasa cen kasan makoshi yace Deejarh Na kinyi matukar kyau jinakeyi kamar intasaki gaba inyita kallonki hargari yawaye. Bana gajiya dakallon kyakkyawar fuskarki

Idanuwanta talumshe dukkansu wani yanayi suka samu Kansu aciki Usman karamin bakinta kawai yaketa kallo sosai danbakinta yana burgeshi

Baisan sanda yamanna labbansa akan nataba""" sosai kirjin khadija yacigaba da bugawa Amman batayi kokarin hanashiba Yajima sosai yana sunbatarta ganin yakusa rasa natsuwarsa yanashirin wuce gona da iri

Yabaiwa kansa hakuri saida ya tattaro sauran jarumtarsa sanann ya iyah raba kansa dajikinta mikewa yayi dasauri haryakai bakin kofa sanann yacemata saida safe dakyar muryansa takefita

Khadija batace komaiba haryabar dakin tadade zaune awajen sanann tamike tawuce dakin tasoma rage kayan jikinta tawatsa ruwa tadauro alwala tana fitowa tasamu labila hartayi shirin kwanciya darduma tashinfida suka soma karatu

Saiwajen daya saurah suka kwanta""" kowanne zuciyarsa fariii nikam nace banda mutum daya saida suka kwanta khadija tasoma tunanin abunda yafaru dazu wani nishadine taji yakamata filo tajawo takankame jitakeyi tamkar Usman ne aga banta bangaren Usman ma hakane danko abinci baiciba yadade yana tunani kafin barci yakwasheshi

Washe gari anayin asalatu Usman saida yafara tashinsu sannan yawuce masallaci dayan aikin gidan tunda sukai sallah basu komaba sukasoma karatu da azkar din safe

Saida haske yafito sukagyara dakin dakuma falon suka kunna turaren wuta nantake gidan yagameda kamshi"".
Sukai wanka sukazauna sunafirah Usman yashigo dakin"""


Labila tagaidashi ya amsa cikin sakin fuska yatambayeta yasuka kwana tace lafiya qalau fita tayi tasauka kasa tasamu har lubabatu tagama hadawa kowa abunda zaici gefedaya tazauna bayan tagaisheta

Tacigaba dalatsa wayarta"" bayan fitar labila kusa da khadija yazauna tagaidashi ya amsa yacemata ya bakunta??? Tace babu hannuntà yariko yace tataso suci abinci bamusu tamike sukafito

Tunda sukasauko taga mom din labila tayisaurin cirehannunta jikin nashi shima baiyi kokarin hanataba sunakaiwa harkasa taduka tace mom inakwana

lubabatu ta amsa bayabo bafallasa
Lafiya kalau Amarya yakwanan bakunta??? Tace alhamdulillah Usman yajamata kujerah yanuna mata tazauna sannan shima yazauna lubabatu tazauna gefe sunsakashi tsakiya kenan sai lokacin labila tataso tazauna kusa da khadija tature nata gefe tasoma cin dankalin dakecikin farantin khadija suka kalli juna tasakarmata murmushi tace bisimillah

Usman baice komaiba sai lubabatu tace labila menene haka baganaki nanba yazakisaka mata hannu anata saikace warinki

Labila hannunta ta tsantsame acikin plate din tana kallon Usman tace dad inaji kamar bakasanarda mom yanake da wannanba??? Tayi nuni da khadijar batajira mezaiceba tacigaba

Tanamai kallonta mom wannan kawatace ko agida tare mukecin abinci anandinma tare zamuci inasonta fiye da kaina "" wlh koruwa banyarda sahibata tashaba saitaredani

Idankuma ba za abari naci tareda itah ba to itama bazataciba saidai muje mugirka namu ta mike sahiba tashi muje"" khadija takalleta kamar zatayi kuka Sam bataji dadin abunda tayiba wannan yanuna tana zargin mamantane

Usman ne yakalleta yace haba labila meyasa kikeyin haka??? Tace tomenayi dad daganafadi gaskiya nibana iyah cin komai saitareda itah

Yace shikenan zauna kuci yakalli lubabatu wacce tasaki bakii hangaga tana kallonta yace kiyi hakuri kibarsu surikaci tare"" tasaki murmushi bakomai dadyn Abdul nibandamuba abunda yasama nayi magana naga kamar baidace taci abinci da matar ubantaba bansan kawarta bane
Tunda hakan tafiso aishikenan nimeye nawà aciki





Aisha✍🏼.
[3/12, 7:32 AM] Adam yunus: [3/11, 7:51 PM] 1man: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 81
       By
Gentle Lady💃🏽


Yasaki murmushi babu uwargida sarautar mata"" sosai taji dadin wannan sunan dansaida tadan dara har hakoranta  suka bayyana "" labila bata koma kantaba tacigaba dacin abincinta

Waifa abunda yasaka tayi hakan waikoda lubabatu tanada niyar sakawa khadija wani abun dole tafasa inhar batason abun yashafi yarta

Illaikuwa kamar komai lubabatu take kitsawa azuciyarta tamkar suna shawarane tareda zuciyar labila dankuwa tayi alwashin dazaran khadija tasaki jiki dacin abincinta guba zatazuba mata taci idan tamutu saitasa *hatsabibin boka* yarufe bakin kowa tayanda babu Wanda zai tuhumeta tagama yanke wannan shawarar saigashi labila tawargaza

Tagefen ido take watsamata harara tayanda itah kawai takeganie wacce akeyi dominta"" lubabatu tarasa wace irin yatahaifa wacce batason cigabanta itah tanayin komai saboda tasama masu gata Amman labila bataganie

Anacewa idan kasabawa iyayenka zakahaifi kaima Wanda zaimaka fiyedasu itakam bataiwa mahaifiyarta katsalandar cikin al amurranta ko maganie tasamu mom dinta tasakawa dad bata fadamasa Dan abun baima dametaba

Watarana ma agabanta sai mom dinta suyita firah da kawayenta yanda tamallake  dadynsu Amman batajin komai kuma bata tabaji aranta zata tonawa mahaifiyarta asiriba

Saigashi itah tahaifi yarda takenema tatona mata asiri wai anyama bamusayarta akamun danaje wajen scanning ba???  Dakamar wuya yarinya kamar haihuwar hafiza komai nata saitasaka Allah yace"" saiyanzu  tagano dalilinda yasaka Usman yace yabarwa amayarsa sama kenan labilace tace bazata zauna nanba shegiyar yarinya dukta batamun shirina dole boka yakasa yinkomai lallai idan suna tare babu yanda zanyi inkasheta hmm baridai akwana biyu intuntubi *hatsabibin boka* hartacinye dankalinta bata fargaba saida tayita lalabar plate taji wayam""

bayan sun kammala tare suka mike zuwa bangaren khadija  anan sukabar Usman sunashiga khadija tasha toka takoma gefe tazauna takauda kai daga wajen labila

Dama labila tasan sai anyihakan kusa da itah tazauna tariko hannunta khadija tatureta kinga malama kirabu danie

Murmushi labila tayi tarike kunnenta tace tuba nake small mom"""  khadija tasoyin dariya Amman takanne tace banason wasa yanzu balokacin wasabane

Labila saudari inasanardake muhimmancin uwa Amman bakyaji ahakan kikeso inzauna gidanku??? Gaskiya idan bazaki dainaba wlh zamubata dake kibarni narikacin abincina nikadai mana ko anfadamaki wani abunne zaisameni idaan naci nidaya???

Baidace kinazargin mahaifiyar kiba  kizama mai kyakkyawar fahimta gakowa saikiga hakan yazama alkhairi agareki

Labila hawaye tasoma sharewa tanason khadija kodon fadamata gaskiya datakeyi subasusan komaiba itakanta tanason mamanta

Tanaso tazama uwa tagari tuntana karama datafahimci halin uwarta takeyimata nasiha Amman kamar cewatakeyi tacigaba

Tundatake bata tabaganin mom dinta tadorah goshi akasaba dasunan sallah ashedai shiriya wata rahamace da Allah kesanyawa azukatan bayinsa

Yashiryarda Wanda yaso kuma lokacinda yagadama"" yafitarda matacce cikin rayayye yakuma fitarda rayayye acikin matacce samun kanka dakayi acikin shiriya ba dubarar kabace  bakada wata dubara

Tamatso hawayenta Allah kaganarda màhaifiyàà gaskiya "" kukanta yasaka jikin khadija yayisanyi tajikamar itace silar kukan nata

Ta sassautodà murya tàce sahiba maganganuna  sunkona maki raine??? Kiyihakuri  bàdasoñ zuciya nafadi hakanba

Nafadane saboda inajin tsoron gobe kiyama atuhumeki akan rashin kyautatawa mahaifiyarki dabakyayi komai lalacewar mahaifiya mahaifiyarkice

Kodakuwa kinga tanayin abunda baidaceba saikiyita yimata nasiha kinayi kinayi sannu kan hankali saitagane gaskiya kinga kinsamu lada kuma kin kyautatawa mahaifiyarki "" ballantana babu abunda mahaifiyarki takeyi namuni wlh naji ta sake shiga raina hakurinta dasanin yakamarta kallifa yanda ta tarbi yan uwana hannu bibbiyu yanzu irin wannan matar kikabari akayomata kishiya???

Saiyanzu nake zargin kaina anya banshigo huruminda banawaba??? Banaso nayi sanadin shiga tsakanin masoya irin haka sukadai sukasan irin sonda sukewa junansu meyasa tunfarko bakisanarda niba sahiba

Labila takalleta da mamaki ganin itama kukan tasoma tace wlh indai akan mamana kike zubarda hawayenki kimadaina karkiyi hasararsu

 Kuma naji nasiharki zankiyaye Amman kisani nangaba dakanki zakigano abunda ninake hangowa kumani bazarginta nakeyiba yazan yi inzargi uwata kawaidai saboda nasabacin abinci dakene haka zalika wlh banajin dadin abinci indai nidaya nakeci

Cin abinci cikin taro yafi dadi gakuma kara dankon zumunta dakuma soyayya ko agidan hajiya kinaganie indai nikadai zanci abinci tokuwa bazanci komaiba

Amman idan kinga zantakura maki agidan mijinki kiyi hakuri zuwa gobe zandauki kayana inkoma kano inbarki da masoyanki kiyi hakuri dabata maki raidanayi tamike tsaye dasauri khadija tajawota tarungumeta tanakuka yazakice haka sahiba wlh bazan iyah zamaba idan bana ganinki Dan Allah kidaina cewa zakitafi dagayau bazansake yimaki maganaba komai kikace nafahinceki yanzu Amman kiyi hakuri kinji"" jayeta tayi ajikinta tace tonidai kukan ya isah kar daddy yaga idonki yayi ja yadauka dukanki nayie

Khadija cikin kukan tasoma dariya""" tace kaisahiba dukadai kamar jaririya""" tarausayarda kai ato nasan yanda dad yakesonki dazaran yaga idonki yayi jajir bama zainemi ba asiba zaihauni da duka

khadija tace kai sahiba da abun dariya kike wlh Hamma tayi tace nifa barci nakejin zandan kwanta inhuta"" labila taharareta  tace nikuma dabanajin barcin intsaya gadinki koyaya""

Khadija tarike kugu tace kohakan kikayi aibaki fadiba tunda nikikayiwa"labila tace hakafa Amman bazanyibaa  dannima barcin nakeji Amman bari nasaka kaset danazo dashi insaurara harbarci yasureni tayi maganar tanabude Jakarta faifan CD tadauko takunna DVD tasaka Kaset din aka soma da  bisimillah complete Qur"an ne tundaga bakara. Har nasi kira ar sudes gabadaya saman kujerun falon suka kwanta sunkashe kunne suna saurare harbarci yasuresu

 lubabatu datake  bangarenta tuni tasoma jintashin karatun tamkarma abangarenta akeyin karatun

Aranta tace waime wadan nan mutanen suke nufi??? Zasumiyarmun dagida makarantar islamiyya ko masallaci to wlh dasake yanzu ana wannan karatun yama za ayi ta iyah kiran *hatsabibin boka* taja tsaki ninasan duk iskancin labilane""" tashi tayi tasauko kasa danyafi Dan dama dama bakajin karatun sosai

Su labila tuni barci yayi awon gaba dasu sai biyu saurah suka farka sukasakeyin wanka sukai alwala suka gabatarda sallah"" bayan sunshirya suka sauka kasa"" daidai shigowar Usman gidan yakurawa Khadija ido danba karamin kyau tayiba  yadine ajikinta irin mai rawar nan anyimasa doguwar Riga sama yadan matse kasakuma saiyabude takama gashinta duka baya tanannadeshi da dankwali tayanda ko silin gashinta ba aganie kodaya"""

Bawata kwalliya tayi sosaiba manbaki kawaine tasaka sai powder Amman tayi kyau fuskarta tafito tayi haske"" kallonda yake jifanta dashi tuni taji ajikinta bayan sun zauna tadago ahankali tayimasa sannu dazuwa ya amsa labila ma taimasa ya amsa yamasu yazaman gidan sukace Alhamdulillah

Yawuce hawa nabiyu kamar yace khadija tabishi Amman bazai iyah ba bayan yawuce labila tahau zungurarta harsaida yahaye tace waike haka su gwaggo suka koyamaki mijinki yadawo yakwaso gajiya ananma zakiyimasa sannu dazuwa??? Wlh koki gyara ko in tattara inbar maki gidan"" talangwashe kai toyazanyi sahiba???/ au bakimasan mezakiyiba tashi zakiyi kije kihadamasa ruwan wanka idan baicire kayaba kitayashi ke inhar takama kiyimasa wankan saikiyimasa menene bamijinki bane aituni khadija tarufe fuska tace wlh baxan iyah ba sahiba

Labila tace tosaiki zauna tajuyamata baya"" Khadija tayi shiru ganin labila taki ko kallonta yasaka tatashi tace tonatafi tawaigo taballamata  harara tace kimaxauna tamurguda mata baki khadija tagirgiza kai kawai tawuce zuwa saman kamar kazarda kwai yafashewa aciki

Kofar dakin tayi tsaye tana tunanin shiga daga karshe kawai tayanke shawarar shiga. Idonta arufe waikarta sameshi yacire kayansa da sallama tashiga shikam abumma saiyaso bashi dariya yana kwance saman kujerah dakayan jikinsa danyana shiga yazube akan kujerar ya amsa mata sallamarta saikuma tayi tsaye kallonta yakeyi tundaga sama harkasa yalumshe idonsa ahankali yace kikaraso mana!! Dakaji muryarsa kasan dakyar yatattaro haruffan yayimata magana







Aisha✍🏼
[3/11, 7:52 PM] 1man: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 82
       By
Gentle Lady💃🏽



Ahankali tatako inda yake Amman bata zaunaba hannunta yajawo yayi mata mazauni akan cinyarsa kanta yanakasa tana wasa dayatsunta

Yadago fuskarta ahankali yace Deejarh na meyasa bakason kallona ne kodai fuskata tsoro take baki??? Kara sanne kanta tayi tana girgiza kai yace nibanji mekika ceba magana zakiyi"" ahankali tace ah ah"" yace inhakane saiki dago ki kalleni

Ahankali tadago takalleshi idanuwansu suka sarke Dana juna kowanne zuciyarsa bugawa takeyi kamar ganga""" dasauri khadija tasanne kanta bata iyah jimirin kallon cikin idonsa yanayimata kwarjini sosai sake dago fuskarta yayi wannan karon idanuwanta alumshe suke  hakan yabawa Usman damar sunbatar labbanta

Yadaukesu tsayin mintuna ashirin yana wasa da itah ko bihim bataceba kuma batayi yunkurin hanashiba dankansa  yagaji yasaketa yajingina kansa saman kujerar yana maida numfashi"""

Haryanzu tana nan indatake sai saukarda ajiyar zuciya take ahankali"" yadade kwance saidayaji yasamu natsuwa sannan yadago akasakalance yace kinci abinci kuwa??? Kaitagirgiza alamar ah ah

Yace to tashi kihadamun ruwan nayi wanka kobashi kikazo tayaniba"" batace komaiba tamike zuwa toilet din tayi addua sannan tashiga tahadamashi""  ruwan tanacikin toilet din bata fitoba harya gama cire kayansa"" yasameta toilet din

Yace waiharkin hada shine bakizo kinfadamunba kika tsaya anan kodai wankan zaki tayanie??? Cikin zolaya yayi maganar

Aikuwa zumut tafito tace ah ah ba amfanie a aje ruwane abayan gida afita saboda shaidanun aljanu sunayin wanka aciki kaikuma idan kashigo bakaganin sauyin komai saikayi wanka dasu hakan yanajawo safuwar jinnu dakuma cututtuka da shaidanun aljanu kan iyah jefar mutum dasu

Kaiyagyada alamar yagamsu """ yashiga ciki tareda addua yarufe ko far wajenda yake ajiye kaya tabude tarasa kalar kayanda zata daukar masa shiru tayi tana nazari

Wadansu kananun kaya taciromasa jar rigace da bakin wando ""  rigar tanada dogon hannu tayita juya kayan waikomadai bayason kananun kaya??? Farar singlet tadora masa

Saikuma ta aje tafesamasu tirare wayarsa tadauko tashiga massage tayi rubutu ta aje saman kayan tafita falon tazauna jiransa

Bayan yafito wanka baisameta dakinba yaga kayanda taciromasa wayarsa dayagani da haske yadauka

Bansan irin kayanda kakesoba nafitomaka dawan nan idan basuyiba saika sauya"" murmushi yayi ya aje wayar yashirya yasaka kayan rabonsa dayasaka kananun kaya haryamanta"" yataje sumarsa yagyara dankaramin sajensa saiyafito a Usman dinsa

Murmushi yayi lokacinda yakalli madubi yagirgiza kai wayarsa yadauka yasaka agefen aljihunsa nawando yasa daya abaya sannan yafito

Tunda taji kamshin turarensa tadago kanta tadauka baisaka kayanba saitaganshi sanye cikin kayan yayi masifar kyau tayanda khadija takasa boye kunyarta takuramasa ido cen kasan makoshi tace masha Allah tsarki yatabbata ga ubangijinda yahalitta wannan surar"" tsaye Usman yayi agabanta yasaka hannunsa daya acikin aljihunsa yana sakarmata murmushi

Jinkamshinsa"" gab da itah yasaka tadawo daga duniyar tunaninda taje""yace Deejarh na nayimaki kyaune??? tagyada kai saiyanzu tadanji kunya murmushi yayi yashafi gefen fuskarta yace muje muci abinci yunwa nakeji batace komaiba suka jerah zuwa kasa

Lubabatu da labila suna zaune saman dinner sukawai sukejirah kusan tare suka kallesu yanda sukajero sunyi kyau Sundace dajuna Usman yadawo kamar danshekara ashirin dabiyar

Wani mugun kishi lubabatu taji waidama haka Usman yakeda kyau??bata taba ganin shigarda taburgetaba  irin wannan
Harsuka karaso batasan sun kawoba saida khadija tace mata inayini"" tace uyum lafiya  qalau Amarya anyinie lafiya qalau tace sannan suka zauna lubabatu tazuba wakowa saita hadewa labila da khadija sukasoma cin abincin labila kam dadi kamar yakasheta kobakomai tasan yanzu dadyn ta yasamu matarda yadade yana nema kuma insha Allah babu abunda zaisamu sahiba"" wajen yayi shiru bakajin motsin komai sai karar cokullah kowa da abunda yake sakawa aransa"" bayan sun kammala"" Usman yamike yana kallon agogon hannunsa yakalli lubabatu yace yau Abdul zaikoma tundazu inataredashi yanzun ma nadawone inyi wanka saboda zafie

Tace habadai harzasu koma bazasu jirah suyimana ko sati dayaba??? Yace kinsan akwai aiki sosai idan zaiwuce zaikawo madam kugaisa nizanje kano yanzu"" tace to Allah yakiyaye yakalli khadija yace kina bukatar wani abun??? Kaita girgiza alamar ah ah yace shikenan sainadawo tace adawo lafiya Allah yakiyaye yace Ameen sannan yawuce

Labila tahau zungurarta tana nokewa saboda lubabatu tana wajen abun yabawa labila haushi ta mike taja hannunta saida takai bakin kofar tace saiki wuce khadija takalleta saitaga tana harararta tasakai tafita itakuma tajuya takoma cikin falon tazauna tana kallon wayarta kamar batayi komaiba

Lubabatu kuwa binta kawai takeyi dakallon mamaki watoma itah yarinyar tanada kunya dakuma kawaici yartane batasanshiba lallai dole taraba tsakaninsu wanann shegiyar abotar dole abarta"" 🙄

Usman yana bude mota zaishiga yahangota tajikin glass murmushi yasaki danyasan aikin labilane Dan indai Dan khadija yanda takeda kunya bazata iyah tasowa agaban lubabatu ba

Tanakawo wa wajen yasoma dariyarta ganin ta shake kamar zatayi kuka yanzu idan takoma dawanne ido zata kalli mom itah gata marar kunya hardawani zuwa rakiyar mijie

Yace menene Deejarh na??? Tace bakomai motar yabude yace tashigo ciki babu musu tashiga yace naga kamar ranki abace kokinazuwa inje dake???

Murmushi tayi tace sokakeyi Yayana yadakeni??? Yace akan mezaidakeki bayankuma kinataredani

Tace tabdi wlh bakasan halinshiba aizaice yaushe aka kawonie harnafara yawo idan kaje kakarbomun wayana wajen inna namanta bandaukotaba"" yace shikenan yasunbaceta akumatu yace sainadawo tace adawo lafiya tafita tarufemasa motar tana tsaye saida taga wucewarsa tajuya tàkoma  fàlon kanta yanakasa tashiga da sallama

Labila ce ta amsa cikin jindadi kusa da itah tazauna idonta haryanzu yana kasa abunyabawa labila dariya tahau yimata dariya saida taga alamar zatayi kuka sannan tadaina tace sorry small mom bazansakeba ayimun murmushi mana

Khadija takaimata duka tagoce sukahau dariya lubabatu tanagefe tana kallonsu mikewa tayi tace labila kizo inason ganinki tawuce zuwa sama

Labila takalleta takalli Khadija  batace komaiba harkusan tsayin min tuna goma da tafiyarta sannan khadija tace waiba kiranki mom tayiba naga bakida niyar tashi

Tanisa sannan ta mike tace tashi muje"" harararta tayi tace bangane intaso mujeba kikasan kiranda mahaifiyarki takemaki kijemana kinsan akwai sirri tsakanin uwa daya""

Labila tace tonidai idan bazakiba nima zamana zanyi"" khadija tace au ashefa badadi tokizauna Amman wlh nima duk kikasake cewa inje wajen daddy idanhar batare zamujeba nima bazaniba tamurguda mata bakie

Labila tawaro ido tasan khadija zata aikata hakan tace rufamun asiri nidanakeso asamamun Kanwa barito naje nidai tawuce  tana dariya""" khadija tace Allah yashiryaki sahiba

Da sallama tashiga ban garen lubabatu tana saman kujerah ta amsa sallamar kasa tazauna tacemata ganie lubabatu tayi murmushi  tace saiyanzu saiyanzu uwartaki tabaki izinin zuwa tundazufa nakiraki

Kanta yanakasa tace karki daukarwa kanki wani hakkin wandama yake kanki ya isheki ni sahiba batahanani zuwaba hasalima banyi niyar zuwaba itah tasakani dole

Danbakyau kisamu mutum biyu sunafirah batareda kinnemi izinin ganin dayanba kijadaya agefe wani abuñ zaitaba zuciyarsa
Haryayi tunanin kodai maganarsa za ayi lubabatu tamere baki tace wannan kuma kutashafa  tayi shiru nayan dakiku sannan tace labila inaso kifadamun mewannan yarinyar tafini dashi dakike sonta nibakya sona karfa kimanta Nice nahaifeki duk wani Wanda zakiso yasoki bayana yake

Labila tayi murmushi tace kwarai mom nasanda haka nima inasonki irin sonda ya takeyiwa nahaifiyarta halayenkine banaso saboda sun kasance ababen kyama

Kinsan makomar Wanda yakashe musulmi kuwa??? Bayankuma alhakin daddy dakike dauka idan harxaki watsarda miyagun halayyarki wlh zanbaki mamaki  danzandawo tamkar kare agaban sugabanta

Lubabatu tamurmusa tace ke yarinya ce labila haryanzu kuruciya tana cinki nifa gatane nakeyimaku amatsayina Na mahaifiyarku banaso kobayan ran mahaifinku Ku tagayyara

Labila takalleta da mamaki tace kekintaba tunanin mutuwarki???  Gaban lubabatu yabada rasss hartaruntse idonta

Kokintaba tunanin wannan dukiyarda dady yatara bazata kareba??? Ai ahaifi da da arzikinsa yafi amutu abarmasa gado duniyar nan dakike ganie bafa matabbata bace koshi bokan naki yafadamaki shibazai mutuba wlh boka makaryacine mom yanaso yabatardakene dake dashi idan har kuka mutu Baku tubaba wutace makomarku kiwatsarda duka abunda yabaki kidogara ga Allah shine zaibaki duk abunda kikeso

Afusace lubabatu tamike tayanka mata mari tace rufemun baki shashasha wacce batasan maisontaba tunkafin. Ahaifeki nakejin irin wannan wa azin ga malamanda suka keceki awajen karatu Amman kokadan baiyi aiki akainaba sai wanann maganar taki kedabanda bokana harma za ahaifeki kekanki darajarsa kikeci wlh

Labila tadago cikin kuka tace wlh karyane nibabu wani kazami mushiriki daya isah inci darajarsa shaidan kawai inna kintata daidai dadyna bama cikin hayyacinsa ya aurekiba kaico ni labila meyasa mahaifiyata tazama haka daga ina matsalar take???


Lubabatu tace tashi kibacemun  daganie kuma nasan duk take takenki wato ke gamai Kawa?? Nibabu ruwana da kawancenku idankuma baki fita sabgataba harke zansa agama dake dannalurah kinashigarmun hanci nagaji da abunda kikeyi kinsoma shiga huruminda banakiba

Labila tasaki murmushin takaici tace kisa yakasheni mom saimuga idan agurinshi rayuwata take nikoda mutuwa nayi wlh banda takaici me akeyi dawannan kazamar duniyar maitattareda da dauda da kazantar masu halayya irin taku dake da bokan naku sainaganie idan kudin zaku gujewa mutuwa "" ta mike hartakai bakin kofa tace kiyi hakuri mom banason muryana tana zarta taki awajen magana kigafarceni Allah yaganardake gaskiya tabude ko far tafita anan tabar lubcy tsaye rayuwarta intayi dubu tabaciii kirjinta kamar zai balle kofar dakin takulle tawuce kuryar dasauri danfa dole *hatsabibin boka* yasan matakinda zaidauka akanta






Aisha✍🏼
[3/11, 7:52 PM] 1man: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




chapter 83
       By
Gentle Lady💃🏽




Dasauri takarasa wajenda ta ajiye akwatin madubinta tadauko tafito dashi tashafa tareda kiran sunan *hatsabibin boka* saigashi haske yayi tartsi saigashi ya bayyana saman kujerarsa idanuwa jajir lubabatu tasoma magana

Haba boka waimeyasa hakan Ashe akwai lokacinda zanga irin wannan ranar yata tacikina tana nema tafi karfina??? *hatsabibin boka* yakece dawata mahaukaciyar dariya yace babu abunda banganiba acikin madubin tsafie na kisani wannan aikin bakaramin aikibane dole kirabasu indai kinaso kiga karshen wannan yarinyar

Cikin damuwa tace yazanyi inrabasu boka??? Kaima kasan labila idan tanason mutum bazata taba barinsaba dama batasan shirina akantaba dasauki Amman yanzun bazata taba yarda inrabasuba

Yasake kecewa da dariya yace cikin sauki zakirabasu tace taya kenan boka??? Yamurmusa kicewa mijinki yakamata suje yawon shakatawa kodan sumore amarcinsu tunda kinlurah Amarya kunya takeji bazata sake jikinta ananba

Lubabatu taware ido tace habadai idan nayihaka anya banyi wautaba??? Wata razanannar tsawa yadakamata yace nifa ba amusu danie dazaran nace ayi kaza kar atsaya yimun musu idankuma bahakaba narantse dagirman tsafina bazanji tausayinkiba wajen nunamaki kuskurenki

Tuni jikin lubabatu yahau kyarma kamar mazariii tadukadda kanta tubanake yakai wannan gawurtaccen boka man tawa nayi Amman zankiyaye gaba

Batareda ya sauraretaba yace idan kin aikata bayan suntafi saiki nemenie yabace battt yaufa lubabatu tabatawa boka raiii jitake gabadaya duniyar tayi mata zafie kamar wutaa jin Kamar ana kwada sallama yasaka tamiyarda komai tashiga toilet tawanko fuskarta tadan goga powder tafesa turare sannan tabude kofa tafita matar Abdul ce tana ganinta tasaki fara a tace karaso mana

Hauwa u"" koda yake nayi fushi tunsanda kikazo sunan Abdul bakisake zuwaba karasawa tayi cikin falon tazauna tana dariya tace haba Anty luba kinsan balaifina bane wlh tunsanda mukaje minna bansake dawowa nan ba dadyn ameer ne kawai yake zuwa koshi bayawuce kwana daya kema kinsan danazo aidole inzo nandin saboda ke

Lubcy tace hakane ina yaranki ainasan yanzu kinyi haihuwa biyar ko??? Hauwau tarike baki tace lala Anty luba kebakiyi biyarba saini kanwarki"" lubabatu tayi dariya tace aimu munbarmaku bakiga Dan autana yagirmaba


Hauwa u tace inazanganshi labila kawai naganie ai"" nima haihuwana uku biyu mata daya namiji Asiya kausar sai Muhammad inakiranshi ameer dansunan babane"" lubabatu tace masha Allah Allah yarayamana su tace Ameen bari nasa akawomaki ruwa"""

Ah ah dakinbarsu labila tabani ruwa wlh tundazufa mukazo su asiyama sunakasa nabarsu"" tace shikenan ya minnar???
Tanacire mayafinta tace Alhamdulillah ai inasaran kwanan nan zandawo garin nan nagaji dazaman cen bansan kowaba saidai makota ko anawani Abu saidai kaji labari nacemasa yayi aure kawai saiyaje da amaryarsa  nikuma inzauna dani da Yayana

Kallon wata marar wayo lubcy taimata tace lallai Hauwa wasu suna gudun kishiya kekuma harnemanta kikeyi??? Tace to menene Anty luba arzikinefa ai abun farincikin kine mijinki yakara aure alamun kunada wadatar zuci kenan ni wlh koda hudu zaiyi inaso kowafa da halinta zata zauna nasandai duk inda zaije yazagayo  kaina zaidawo dannice uwargida kingakuwa girmana bazai taba faduwaba kobayan raina za adinga yabamun insamu kyakkyawan shaidu aduniya yafi inmutu inbarwa Yayana abun fada

Tuni lubcy tadauke wuta kardai hauwau tasan abunda nake aikatawa??? Takatse mata tunani dacewa amaryarki taburgeni wlh gata karamar yarinya zakuji dadin zama dajunanku dannalurah saitayi hakuri

Lubabatu tace hakane kam wlh ai inata addua dadyn labila yayi dace kinsan matan yanzu sai ahankali watama kina zamanki lafiya damijinki dazaran tashigo saitatashi rabaki dashi

Matanda yake aurah duka banakwarai bane Amman wannan kam ina tunanin andace!" Hauwau tace hakane dadyn ameer yasanardani ai Allah yasake shiga tsakaninmu da mugayen mutane lubcy tace Ameen

Mikewa Hauwa tayi lubcy tace waiharzakiyi me??? Tana yafa mayafinta tace tafita mana kinsanfa jirgi bazai jiramuba dole mujirashi dalokacin tashinsa yayi zaitashi tace hakane tamike turarukka dakayan shafawa tahado mata suka sauko kasan sun samesu sunata firah kamar dama sunsaba dajunansu duk Asiya tace kunga har mom tafito tonidai Anty kibamu number muyi chat

Labila tace wlh bata chat saidai kuyi waya kuma banama tunanin tazoda wayar inaji tamantata agida saidai inbaki tawa

Tace shikenan suka karbi number labila lokacin har su lubcy sun kawo wajensu tare sukai masu rakiya harkofa saida sukaga tashin motarsu sannan sukadawo

Daki suka wuce kaitsaye danyin sallar la asar bayan sungama sukai zamansu adakin"" lubabatu Sam takasa jinta daidai tun abunda tayi yazama dole tasake kiran boka tabashi hakuri hakan kuwa akayi tasake kiransa tabashi hakuri yace ya yafemata Amman kartasake aikata irin wannan kuskuren tace tagode zatakiyaye

Yace nasan abunda kike tsoro kisani babu abunda zaishiga tsakaninsu duk abunda yakefaruwa dasauran matansa itama aikin yashafeta muddin yayi niyar hada shinfida da itah zaisamukansa yana kyamarta saboda warinda zatarikayi kamar mushe

Dazaran sunbar kasarnan zakiga laya a inda nasaba aikowa a ajiye maki kije kisamu wajenda kikasan kullum sai anyi dahuwar abinci tundaga safe hardare"" saiki tona murhun kisaka layar karkibari kowa yaganki dazaran kinyi haka kingama komai

Yanda kikasan zafin wuta idan kikaje kusa da itah haka jikinsu zaiyi zafiii dazaran sun kusanci junansu zasuji kamar zasukama dawutaa dole su nisanci juna tahakan hankalinta zaitashi tadaina samun lokacinda zatazauna tayi addua saboda tunani alokacinne zamucika aikinmu akanta. Wayyo dadi tuni dadi yalullube lubcy tahauyimasa godiya yace maganar labila tabarkomai ahannunsa shiyasan yanda zaiyiii

Tayi masa godiya tace zaiga sako aranar ta siye dabbobin ta aikamasa"" cikin kwana biyu tasamarmasu biza dakomai dantasan inhar cewa tai sutafi labila tana iyah cewa saitabisu wannan dalilin yasaka taiwa tufkar hanciii







Aisha✍🏼
[3/12, 9:24 AM] 1man: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠



Chapter 84
       By
Gentle Lady💃🏽




Zaune suke dadare suna cin abinci lubabatu tace nikuwa yau akwai maganarda nakeso muyi dakai""" yakalleta yace Allah yasadai lafiya ??? Tarausayarda kai tana kallon khadija cikin fara a tace insha Allah baridai mukarasa cin abincin"" yace nidai kifadamun yanzu kinsanni da zumudi kamar sabon angwo gabadaya suka kwashe da dariya harsu labila""


Yace tokokunga laifina ninafison idan za afadamun Abu kawai afada yanzu kafin mugama bakisan iyah jaye jayenda zuciyata zatayiba""" adaure afadamun

Cikin siririyar muryanta tace daddy kasanfa ba amfanie ana cin abinci ana magana kamar bakabawa abincin mahimmanciba""" yakalleta gaskiyarkifa Deejarh tobari mugama yayi maganar yana kallon lubabatu murmushi kawai tayi tacigaba dacin  abincinta

Aranta tace wannan hartasoma tafi labila iyah yi shi abincin harsai anyiwani girmamasa 🙄"" tsaki tayi aranta tacigaba dacin abincinta""  bayan sungama  sannan yakalleta yace karfa kice naciga zanzari nasan duk abunda zaifito bakin nan naki alkhairine murmushi tasaki har hakoranta suka fito tace ko???

Yace koma zakice ainidanake dake nasan haliinki fiye dake kanki""" labila kam murmushi tayi aranta tace kadaisan Wanda kasani  amman babu Wanda yasan halin mom sai Allah nda yahalicceta"""

Tace hakane abunda yake gefenta tadauko Tamika masa tana murmushi shima murmushin yakeyi taredakuma mamakin  menene aciki???

Tagane abunda yakenufi tace kabuda kaganie mana""" bamusu yabude biza ce tazuwa Dubai

Baki sake yake kallonta yace biza naganie??? Tamurmusa ah takuce "" tanisa tana kallon khadija tace wannan itace kyautar taya murnar auren Ku nabarku kumore amarcinku har Kanwata tasamu rabo""" dasauri khadija tasun kuyarda kanta kasa saboda kunya

Usman yarasama dawadanne irin haruffa zaiyi amfani domin yagodemata dakyar ya iyah hadiye yawun bakinsa dasuka kafe yatttaro sauran maganarda ke bakinsa yace

Maman Abdul wai dagaske kike kuwa??? Tagyada kanta sosaima aikasan inason farincikinka fiye da nawa inaso kasamu cikar burinkane bazanso kacigaba tatauyewa kanka hakkiba

Nalurah kanwar tawa bazata saki jiki dakaiba saboda tanada kunya shiyasa nashirya maku tafiyar kozatadan sake dakai

Yasaki lallausan    murmushi Alhamdulillah amman naji dadi sosai bansan dawadanne irin kalamai zanyi amfanie wajen godemakina tnx matata

Murmushi tasaki najindadi tace basaika godemunba wannan aikinane nashirya  maka kayanka""" sauran nata tashirya dan jirgin shadaya zakubi

Yayi murmushi yana kallon khadija takasan ido wacce haryanzu idanuwanta suna kasa kosaudaya bata dagoba"" labila kam tashiga tashin hankali dankuwa tana tunanin wannan abun kamar wata munakisar lubabatu tashirya Amman babu yanda zatayi tawargaza tafiyar tunda batada bakin fadin komai akan mahaifiyarta Amman alal hakika ranta baikwanta da wannan tafiyarba

Dolene tasamu malaminsu saboda ayiwa khadija saukar qur Anie murmushi tayi afili sanin tasamo mafita lubabatu tana jefar labila da murmushi itama haka kowannensu shikadai yasan ma anar murmushin nasa

Labila tace sahiba tashi muje intayaki hada kayanki dankinsan dasafe bazaki samu damar hadawaba tayi maganar tanajan hannunta

Tamike jiki bakwari tabi labila kamar rakumie da akala sukuma suka rakasu da idanuwa lubabatu tanayiwa  Khadija kallon kingama yawo yarinya tunda kika auri mijina

Usman kuwa  yanayimata kallon  soda kauna yanarayawa aransa zaihuta sosai da Deejarh nsa" saida suka bacewa ganinsu sannan Usman yamike yaja hannun lubabatu suka dawo falon saman kujera suka zube

Yakuramata ido yana murmushi itama shitakeyi tace yadai mijina""" yamuskuta lubcy wlh mamaki kikebani sosai"" tarausayarda kai tace mamakin menene???

Yace yanda kike kyautatamun wai anyama zamanin nan za asamu mata masu irin halayyarki??? Gaskiya baza asamuba""" tace nidai kadaina fasamun kai da dadin bakin nan naka

Yajawota jikinsa yace badadin bakibane wlh dagaske nake nikam nayi sa ar mata tagari wacce kowanne namiji zaiyi mafarkin mallakar irinta"""

Hawayene suka sauko akan kumatun lubcy sanyinsu yaji ajikinsa yajuwoda itah dasauri yace lafiya lubcy menene kuma nakuka??? Please banason kukan nan nakie Dan Allah kidaina

Tashare hawayenta tace inajin takaiicin kaina daya kasance bana baka hakkinka dayake kaina yanda yakamata inayin hakanne kodan Allah yayafemun hakkinka danaketauyewa ninasan ina cutarda rayuwarka

Banason inzama daya dagacikin matanda Allah zaiyi fushidasu Usman yadorah yatsanshi akan labbanta yace bakyacikinsu matata nibaki tauyemun hakkinaba aihakan Allah ya halicceki kuma kinayin iya kokarinki wajen ganin nasamu kwanciyar hankali nagode maki Allah yabarmu tare yasake janta jikinsa yana aikamata wani sako mai rikitarwa

Al amarinsu labila kuwa suna hawa bangaren khadija tasheka dagudu saman gado taboye fuskarta""" labila mezatayi inba dariyaba saida tayi mai isarta tace wlh nifa mamaki kikeban kowaya fadamaki yanzun anajin kunyar soyewa danamiji

Kinganni nan wlh idan nai aure saina baki mamaki Dan wlh agaban kowayema zannunawa mijina soyayya gashidai kin girmeni Amman ninafiki sanin yanda ake tarairayar miji

Tazauna kusa da itah sahiba wannan tafiyarda zakuyi wata damace agareki daxaki saye zuciyar mijinki ki ajiye kunyar nan taki kinunawa mijinki tamkar dagake saishi kuke acikin duniyarku

Idan kinataredashi kimanta dakowa kigamsarda mijinki Dari bisa Dari kedin tashice kuma mallakarsa tarage murya kuma wlh karyanemi kibashi hakkinsa kiyita gudunsa

Khadija tamike takaimata duka tace waike yaushe kikazama marar kunya bansaniba??? Labila tace ke yarinya zauna nan ainadade inacemaki kifara chating kozaki koyi yanda ake ririta miji kinki hmmm wlh jinake damanice ke danatsula tsiya sai nasakawa wata hawanjinie😕😂

Khadija tatureta tace Allah yashiryaki mom din??? Tace au sorry namanta ashefa mom ce baridai inhadamaki kayan dannasan halinki innabiye maki manyan kaya zakidauka duka tayi maganar tana mikewa tabude drawer tajawo akwatin kayan khadija

Tahau duba kayan ciki kananun kaya tayita shiryawa khadija saboda Usman yasiyamata kananun kaya masu masifar kyau

Mini sket da kananun kaya gasunan kamar kazanta""" manyan kaya kala uku kawai tasakamata"" takoma hadamata kayan kwalliya komai saida tasaka tace sauran kuma idan kinje karkiyi kwalliyar""" nasan halinki"" danzankirah inji waima ina wayarki???

Khadija tace nafadawa dad fa yakarbomun gida namanta ta wlh kuma inason yin magana da Yayana Amman nakasa tambayarsa koya karbo kumashi baicemun komaiba""   labila tace kinsone wlh dakinason wayadashi aidasaikice inbaki Aron wayata saiki kirashi""

Tamere baki inna hardace nomber din kokuma inbar hardaceba"" labila tace kumafa hakane Amman aidason ranki lanbarda batawuce ashirinba keda kikeda kwakwalwa maikyau kikasa hardacewa

Tace kwakwalwata ta karatuce bawai danna hardace tarkacen numbers ba""" labila tace hakanefa ustaziyya  Amman  kinsan hardace number yanada amfani kodan watarana

Bawai ina fataba kisamu kanki inda kike neman agaji abaki Aron waya baki hardace number kowaba yakenan gashima dai yanzu karamin misali kinason waya da ya muktar Amman bakisan number saba

Khadija tace kinada gaskiya zanyi kokarin hardace tamutum biyu"" labila tace Yayana dakuma daddy ko ???

Murmushi khadija tayi labila tace bakomai mukoda ba a hardace tamuba badamuwa Amman inafatardai abunda nafadamaki dazun kinkwasheshi afaifan kanki wlh sahiba inajimaki tsoron wata baturiya takwace makishi

Aikuwa khadija tahade rai labila tahauyi mata dariya tatashi tabita sukahau zagayen dakin karshedai labila tafada saman gado tana hakiii tace tubanake small momy🤗

Khadija tace aisaikinsha rankashi aka"" labila tarumtse ido takankance kai tanadafe dakai tanajiran saukar rankwashi khadija tahauyi mata dariya tazube saman gadon tace waike atunaninki rankwashinki zanyi aka???


Ainibazan rankwashi kainaba idan dady yasamu baturiya aibanice zanyi kishiba kece dannasan kinfison farincikine fiyedani Kaina yanda kika damu dani nibandamu dakaina hakanba """

Labila tace aisaboda kinsan hakan shiyasa kikemun abunda kikaga dama takwanto saman kafafuwan khadija tace wlh sahiba jinakeyi kamar aduniya bazanso kowa sama dakeba

Idan akacire Allah da manzonsa   da sahabai dakuma ahalal baitiii   idan za akuma tambayana wanakeso bayansu kinsan wazanfada???

Khadija tagirgiza kai labila tace wlh sahiba sunanki zankirah !! Jinake tamkar sabodake akayini kullum soyayayrki sake shiga rainatake bansan daliliba kodan kinason babanane

Khadija tayi murmushi tace dama haka Allah yake ikonsa soyayya gamon jinice""labilata tashi  zaune takurawa. Khadija ido kamar mainazarin wani abun saikuma  tafashe dakuka data tunoda kudirin lubabatu akan Khadija

Itama batasan sanda tafara kukanba suka hade kai sunata kuka akarasa Wanda zai rarrashi wanie







Aisha✍🏼
[3/12, 9:25 AM] 1man: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 85
       By
Gentle Lady💃🏽



Saida sukai mai isarsu sukadawo rarrashin juna""" labila tace zanyi kewarki sosai sahiba idan kikatafi khadija  tace nima haka wlh sahiba Amman karkidamu ga wayanan ai zamudinga waya kodata daddy ce

Nibandama wani Abu mezaihana kicewa daddy kema zaki wlh zanfi sakewa idan inaganinki"" labila tace naki wayon aiko nan gani nane yasaka kika sakankance gobe aurenki sati dayafa Amman bakitaba zuwa wajen mijinkiba saikace haka akacemaki anayin auren"" wlh kebandah wani Abu dasaina hadaki da inna airanarda za akawoki bahaka akace kiyiba

Khadija ta marairaice fuska kamar zatayi kuka tace daddy nefa yace inbari yafadamaki kizo kirika tayani kwana kokuma haka kurum baikiraniba nidadi miji sai inkai kaina""

Labila tace ayya sahiba kinada gaskiya aibandauka hakan akayiba koni banbaki goyon baya kiyimasa rawar kafaba dole mudanja ajinmu irin namata aikingane dannafiso yagane akwai banbanci atsakaninku """ mudin bamasu arha bane

Khadija tace kedai akeji wai mahaukaci yafada rijiya kinga kitashi muje muyi alwala dare yayifa sosai musamu ko hizifi uku mukaranta"" labila takalli agogon dakin yabuga shabiyu da kwata tace hakafa aiyau babu maganar barci hirar bankwana zamuyi

Khadija tace nanfadai wlh saina kwanta kinsan bantabaa shiga jirgiba karnaje nayita kwasar barci ayimun dariya tayi maganar tana mikewa labila tace dariyadai waye zaimaki dariya Wanda ya aikeki bayankuma kowa  da abunda yashamasa kai babu ruwan kowa dawanie

Khadija tace to suda muje muyi alwalar tana dariya tatashi khadija  tafarayin alwala sannan labila sukasoma karatu sai uku saurah suka kwanta

Washe gari tunda sukai sallar asuba basu komaba sukahau shirya kayansu harda labila dantacemata itama kano zatawuce dazaran tarakasu


Bayan sungama suka gyare dakin "" dasauran inda suka bata"" sukai wanka suka shirya sannan suka fita falon kasa Usman yanakusa da lubcy sai shagwaba takemasa  kamar wata karamar yarinya shikuwa saibiyemata yake

Haka kurum khadija taji wani iri aranta tayi saurin soke kanta ahankali labila tace kinga yanda akeyi itama data tsufa ballantana keda kike sabon jinie yanzu kike lokacin ganiyarki ta rayuwa

Sam Usman baisan dazuwansuba lubcy ce kawai talurah kuma batadaina abunda takeba saima tayi tamkar bata gansuba""

Usman ne yaji kanshin khadija ya yawaita afalon yadago yakallesu dasauri yayi saurin saita kanshi yajanye lubcy daga jikinsa sosai yake jin kunyar labila

Khadija tagaidashi bayan sunkaraso ya amsa cikin dakewar murya "" tagaida lubcy itama ta amsa labila tagaidasu sannan suka karasa saman dinner haryanzu Khadija batadago kanta sunyi ido hudu dashiba

Tunda suka fara cin abincin yakeson tadago kanta danyakafeta damayun idanuwansa Amman taki dagowa dukda tanaji ajikinta yana kallonta

Bayan sun kammala yakirah habu driver labila tafitomata da kayanta sannan takulle bangaren  tarike key din"" lubcy ce tafitoda kayan usman driver yakwashe duka yasa mota suka rankaya dukansu

Yace banga kindauko mayafinkiba kokina nufin iyah nan zakiyimana rakiya??? tana dariya tace inalaifi aiga yarkunan zata rakaku basainajeba Allah yakai lafiya yace Ameen

Takalli khadija tace Amarya asha amarci lafiya khadija tasanne kanta dakansa yabudemata baya"" harzata shiga tadafe kanta""  innalillahi"" wlh nayi mantuwa

Usman yace mantuwar me kumata dama haka shirinku yake kosati zakuyi kuna shiryawa karshe saikunje kunmanta wani abun

Labila tace kabarta mana tadauko mekika manta??? Tace wlh littafaina da Qur ani kumafa dankar namanta  Na ajesu kusa kusa

Lubcy tayi karaf tace kekuma banda abunki Kanwata kudazakuje yawon amarci mezakiyi da littafai aikyabaridai harkudawo shima maigidan abashi lokacinsa

Labila tace sabodame zatabàrsu dankawai zatayi tafiya sai akace kabar addininka agida kejeki dauko sahiba tamika mata key wlh kar shaidan yarinjayeki ko inakikaje rike ibada saikace dai su oi daba ta dauki addinin dakimaba"" khadija tawuce cikin gidan

Lubcy tace aike komai saikin nunawa mutane kinfi kowa """ saikifadàman dawakike??? Labila ta marairaice fuska tace waini meyasa mom batasona daddy yanzufa dawata Yar makarantarmu nake tafashe dakuka

Usman yace haba lubabatu yarkiicefa baidace kinamata hakanba"" tace alhaji kanajinfa abunda takefada itah yadace tayihàkà?? Nifa mahaifiyartaçe

Yace aibadake takeyiba tafadamaki dawatà Yar skull dinsu take

Bandama abinki aikinaji batakirah sunaba koda ma takirah suna tundakedai kinsan bahaka kikeba aishikenan saikibarta"""

Tanisa shikenan alhaji yace yauwa kokefa yarnan dai takice komai lalacewarta nibansan dalilinda yasaka bakwason yayan fariba

Ainikam hajiya batayimun irin yanda kikemata karfanaje nadawo nasamu kinhanamun ya rawar gaban hantsi"" labila tace aini dad wajen hajiya zankoma saikundawo zandawo

Yace shikenan ma dama abdul sai Rigima yakewa hajiya waisaita kawoshi inda kike yauma naso turawa shima adaukoshi yadawo nan

Tace idan yadawo dad karatun shifa ??? Daidai kawowar khadija yace kece kikasan hakan Amman wlh danaje kuka Yakama saiya biyoni nakawoshi wajenki"" shibaima tunanin kowa saike

Khadija taimasu sallama suka amsa tamikawa labila key din bayan mota sukashiga shikuma dashi da driver suka shiga gaba tana tsaye tana daga masu hannu harsuka wuce sannan tajuya cikin gidan tana sake sake aranta sama tahau taduba inda ake ajemata sako tasamu layar wani murmushi tasaki tana juya layar labila kenan aiduk kame kamenki saina raba Usman da khadija saidai kuma kiyi hakuri

Tasheke da wata mahaukaciyar dariya irin wacce *hatsabibin boka* yakeyi saida naja baya dannatsorata nadaukama shine yabayyana agabana""

Tunda suka shiga mota labila saizuba takeyi harsukakai airport sunsamu jirginsu Saura minti talatin yatashi

Anan suka zauna zaman jirah duk abunda za ayi akagama lokaci yanayi suka soma shiga jirgi sai lokacin labila tasoma sharar hawaye tana kallonsu harsuka shige tana tsaye saida jirginsu yadaga tanasharar hawaye tana daga masu hannu""

Saida tadaina ganin jirginsu sannan tacewa habu suwuce ganin wani guy yanata kallonta"" tunda sukashiga motar tayi shiru sai sake sake takeyi aranta""

Sunakaiwa gida tace yajirata tashiga gidan lubabatu tana falo tayi sallama tahau sama tadauko jakar kayanta tasauko sannan tace ni mom zantafi

Tanisa kigaishesu"" labila tace zasuji hartajuya saita tsaya tace nasan kinturah dad da sahiba Dubai ne akan wani mugun nufin naki kisani Allah yafiku kibarganin bokanki yanacin nasara kidauka komai kika nema aduniya zakisamu awajensa shikanshi damace Allah yabashi domin yayimasa takunkumi kiji tsoron Allah Mom kidaina biyewa wanann bokan tafashe dakuka maitsuma zuciya lubabatu tamere baki

Idankundago kai tagado takalli indama labilar take saida tasakecewa please mom badanniba kidaina abunda kikeyi kinemi gafarar Allah

Tadago takalleta ahankade tace kingama??? Labila tayi shiru tace totunda kingama nagode da nasiharki muna gaidasu tamike tahaye sama tabar labila tsaye

Tabita dakallo saida tabace mata sannan tashare hawayenta tajuya taja akwatin kayanta
Tafita"" habu yabude mata tashiga yaja motar akabude masu get sukafita"

Fitarsu babu jimawa lubcy taciwo kwalliya tafita itama"" tashiga tanta tsetsiyar  motarta akabude mata get tafita tasoma yawo cikin unguwanni kozata samu inda akeyin dahuwar abinci tunsafe har dare abunfa dawahala kuma ance karwani yaganie danhaka badamar tabawa wani kwangila dole dakanta zata binne""

Haka tayita yawo""" duk inda tatambaya daga masuyi dasafe saimasuyin da rana"" kuma tafison ahanya Dan agida tayiyu ba a cika wutar yanda zatayi zafie

Su khadija kuwa tunda jirgi yatashi takankame idanunta kamar zatayi kuka sai addua takeyi hakan yasa usman yajawota jikinsa yakwantar harsuka lulaya cikin gajimare"" ahankali tasoma saukarda ajiyar zuciya ba awani dadeba tasoma barci maidadi asaman jikin Usman

Dayalurah tayi barci yagyara mata kwanciyarta ajikinsa yarufemata fuskarta danbayaso ana kallonmasa puska tuni shima yasoma saukarda ajiyar zuciya yajingina kansa jikin kujerar jirgin yana tunani

Lubabatu tana tsaka dayawo tabaro unguwarsu Danisa indama taje batasan sunan unguwarba bama tataba zuwaba wata yarkasuwace Dan kusa da bakin titi take komai anasiyarwa awajen wata maisuyar doya taganie da dankali da awara

Tatsaida motarta tafito zuwa wajenta matar tanaganinta tawashe baki tanamata sannu dazuwa lubcy ta amsa suka gaisa tace nawa doya matar tace hamsin ashirin dankali kuwa goma biyar "" haka awara

Lubabatu tace kullum kina fitowa??? Tace tomezaihana hajiya aizama gida banamu bane munada marayu agabanmu

Lubcy tace Allah sarki aiyanada kyau kanemi halak dinka kamar dayaushe akesamunki anan??? Matar tace ai hajiya kaman karfe bakwai nake fitowa indorah koko idan yakare zuwa yanzu shabiyu nasoma suyar doya da dankali saidare nake tashi inbarwa yata inkoma gida inyi tuwon dare infito dashi

Takwas muke tashi watarana harmunakai Tara"" lubabatu tace kainaji dadi bani doyar ta dubu uku kisa dankali Na dubu daya zandinga aiko driver na yana karbar Mani

matar tawashe baki tace kaiii Amman naji dadi hajiya tanata wasar baki tazubawa lubabatu doyar tabata tafiddo kudi sabbi hull Tamika mata sukai sallama takoma motarta hartabar wajen matar tanadaga mata hannu saikallon kudi takeyi

 tana juyasu bayan lubabatu tayi nisa tatsayarda motar tafito da ledar doya dantasan koda tajeda itah gida bazata iyah cintaba danmaituyar doyarma kyankyaminta takeji tasoma rabon ido kozataga wasu almajirai tanakiran wani

Yarugo kamar daga sama tajiii ance banda sadakaaaa aikinki zai lalace dasauri tajuya bayanta bataga kowaba tamiyarda doyar yaron yanazuwa tacemasa wanigida take nema kuma tagane tashiga motarta tawuce daniyar dadare zatadawo ta saka layar






Aisha✍🏼
[3/12, 11:31 AM] 1man: *RAMUWAR GAYYA........ 💘*


_Love story 50,50_



*Fertymerh Xarah*

          &

*Ummy Aysher*



     31


Shiru yayi yana saurarenta amma har lokacin bai ďaga kanshi ya kalleta ba,

Jikinta yayi sanyi, she is not happy a yanda yake yi mata kamar xatayi kuka, ta qara marairaice murya,

'kayi haquri idan na bata ma, wallahi faruq is nothing to me Kuma ni bansan da xuwanka ba da baxan tsaya gurinsa ba,

Ya tabe bakinsa haďe da ďaga kafadunsa ko ajikinsa, ya maida glass ďin sa ya rufe idonsa, ta ciki yake kallonta yaga duk ta damu, yaji daďin ganin yanda take bashi haquri tayi masa laifi, ya haqura amma yaqi ya nuna mata,

Alawiya ce ta qaraso da textbook a hannunta ta miqawa khairi,

'ga book ďin ki gida xn tafi duk na tafi, khairi ta karba tana faďin,

'anjima xaki shigo, kitso nake son kimin,

'ban maki alqawari ba dan xn raka qawata biki amma idan mun dawo da wuri xn shigo,

'shikenan sai Kindawo, Alawiyya ta dubi sawwam,

'mutumin mu yau ba mgn ni naga yau sai wani daurewa kakeyi, yayi mata banxa, ta dubi khairi,

'meke damunsa,
'fushi yake dani,
'shine ni Kuma abin ya shafeni, to kayi haquri ko menene ka sassautawa qawata haka,

Ya juya ga motarsa alamar xai shiga khairi taqi ta matsa, Alawiya ta fice tana dariya,

'haquri nake ta Baka kake min shariya haka,

'matsa xn shiga mota, ba musu ta matsa ta bashi guri ya shiga motar yaja ta a fusace tana tsaye tana kallonsa har ya fice daga Skul ďin,

Jiki a sanyaye ta nufi hostel,  baxata qara xubar da ajinta gurin bashi haquri ba har ya gaji da fushin ya sauko,

Sosai ta damu, ranar duk a kwance ta jini jikinta sukuku hankalinta da tunaninta duk yana kansa, ko ringing wayarta tayi da sauri take dubawa ko shine idan ba shi bane sai ta cillar da wayar tana tsaki, wayar kowa bata amsa ba ranar kamar yanda itama bataji muryar sahibinta ba,


Sawwam Kuwa har Ga Allah ya haqura, yayi mata Hakan ne dan ta gane laifinta sosai ta daina tsayuwa da wani, yana tsananin sonta da kishinsa baxai jure ganinta da wani ba, so a gobe xasu shirya ya nemi sulhu tunda yaga ta damu duk da itama yasan tayi fushi da shi tunda gashi bata nemesa ba, ba text ba Kira.

Washe gari da sauri tayi shirinta ta fita lectures kasancewar 8:00am suke da lectures,

Tana fita ta haďu da Alawiya xata shigo hostel sai suka wuce tare,

'shine kika qi xuwa jiya ko, kinbar ni dakai duk ya cunkushe,

'bamu dawo da wuri bane amma yau baxan je gida ba sai nayi maki,

'kinxo min da assignment ďina kuwa?
'yes yana jaka sai muyi submitting idan mun fito lectures,
'shikenan,  suka shiga hall ďin,

10:00am suka fito lectures, bayan sun fito Alawiyya tayi gurin saurayinta, sai ta sami guri ta xauna cos xasu shiga wata lecture basu gama ba, kamar wacce aka ce ta ďago, tana ďagowa idanunta suka sauka akansa, yana tsaye jingine da motarsa hannuwansa sarqe a qirjinsa, wata budurwa ce a gabansa batasan ta ba yau ta soma ganinta,

Jikinta ya ďauki rawa sosai hankalinta ya tashi, kada sawwam ya barta ne ya sami wata da Kuwa ta shiga uku yanda take mutuwar sonsa a ynxu takejin ba abinda xai iya rabasu,

Suna haďa ido da sawwam tayi Saurin ďauke kanta, ta tattara kayanta ta tashi daga wurin ta shige hall inda sauran friends ďin ta,


Sawwam yayi murmushi yana kallonta,
'kingane farida, Suhaib wani irin mutum ne mai wuyar al'amari, dole sai kina haquri dashi amma duk da haka bai kyauta ba xn mishi magana,

Tace Nagode sawwam, ina mutuniyarka yau duk ban ganku ba,

'ita nake jira ma anan inaji bata fito lectures ba, tayi murmushi,

'kuna birgeni dama haka Suhaib yake dana dace,

'kinma dace abokina fa First Class ne matsalar shi ďaya Kuma xn mashi mgn xai gyara,

'Nagode sosai ta juya ta fice, ya jingina yana jiran khairi yasan tayi fushi a ynda yaga fuskarta,


Wannan Karon lecture ďin da akayi komai bata fahimta ba duk hankalinta da tunaninta yana gurinsa gani take har ynxu yana tare da wannan budurwar,

Sun fito lectures Alawiya tace kije gani xuwa, man bai gaji da gani na ba,

Murmushi tayi kana tayi hostel fuskarta a ďaure ganinsa tsaye, inda yake ma bata kalla ba, ganin da gaske take yasha gabanta,

'kin ganni fa shine kika wani fuske, tun ďaxu Ina jiranki ingayamiki na haqura shi kenan komai ya wuce, tabi ta gefensa xata wuce ya qara tare ta,

'Ni ynxu Kuma menayi kike fushi dani,

Takaici na qara rufeta tambayarta yake meyayi bayan yasan abinda yayi, ta qara bata fuskarta taqi ma ta kallesa,

'Ni ynxu koma menene kiyi haquri sulhu naxo muyi Kinsan banda wacce tafiki fa ya faďa cikin xolaya, harara tabisa da Ita kamar kwayar idonta xata faďi qasa,

'ita wacce nagan ku tare fa?
'au na manta... taja tsaki ta fice yayi saurin riqo hannunta,

*'Ramuwar gayya* ce da gangan nayi dan kiji yanda naji jiya dana ganki da wani, tunda kinji ynda naji shikenan, _50,50_ kiyi haquri,

Tayi shiru tana kallonsa, batare da ta tankaba,

'budurwar Suhaib ce fa, mun fito lecture take gayamin abinda ya hadasu shine na jawota nan Muna mgn dan kigani, ni ynxu bama Wannan ba, abar mgnr, fushin ma kidaina nima na daina, Alawiya tayi maki kitson?

Kamar baxata tanka ba sai Kuma ta girgixa kanta,

'muje saloon ayi maki acan bnga alamar ta iya kitso ba fa,

'ta iya ita kemin ai, ynxu ma xataxo tana hanya, ya sauke ajiyar xuciya,

'idan tayi ki dauki pic ďin ki turomin ta whatsapp ingani inyayi kyau, dama ga gashin ba fasali,

Ta saki murmushi tana kallonsa,
'Kuma a hakan wani ya gani yace yana so,
'to ya xanyi tunda Ina son kayana, da haka suka bige da hira har Alawiya taxo itama tasa bakinta kana suka nufi hostel yayi gida.



*pherty xarah💞*

        &

*ummi shatu👌🏼*
[3/12, 11:43 AM] 1man: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮















                🔮🔮🔮🔮
*```Page 69```*
Hawayenta ne yaji suna sauka a hnkli kan qirjinsa ya kira sunanta a hnkli bata tanka shi ba ta qyale shi sbd wahalar da take ciki ko magana ma bata son yi don sae taji kmr yaune ta soma sanin d'a namiji a rayuwarta don wani  irin mugun zafi take ji a qasanta  har bata son tayi wani  motsin kirki.
  Mohd kuwa sae kallon ta yake cike da tausayi don shi kan shi yasan ya bata wahala ba kad'an ba.
   Ya sake kiran sunanta a karo na biyu bata tanka shi ba sae kuka da ta soma yi cikin dasassiyar muryar ta da tasha kuka.
    Wacce duk ta tattara zanin gadon ta rufe jikinta dashi sbd wutar da aka jima da maidawa bcs dama ba wutar gari ce aka d'auke ba daga laifin mitar gidan ce.
Man yakai hannu ya rage hasken d'akin snn ya nemi cire mata zanin gadon amma ta kama ta rirriqe ta hana shi cire zanin bai takurata ba sae d'aukar ta da yayi ya nufi bathroom da ita wacce tasha kuka ba kad'an ba don wanka ya mata kan dole ya kuma gasa mata jikinta sosai snn ya fito da ita ya kwantar kan bed sae kuka take marar sauti har tayi bacci.
  Mohd dake zaune can gefe guri d'aya ya sauke numfashi had'e da matsowa gab da ita ya kwanta tare da jawo ta zuwa qirjinsa ya rungume yana ta kallon fuskarta dake masa mugun kyau idan tana bacci,
 a hnkli ya d'aura lips d'insa kan goshinta ya mata kiss yana mae ci gaba da kallonta cike da so  daga haka ne shima bacci ya kwashe sa sae safe.


Washe gari mohd ya riga Ryynt tashi yaje bathroom ya d'auro arwala yazo ya sameta ta farka amma bata tashi daga kwancen da take ba sae hannun ta da take d'an moving dashi kan bed ,
ya durqusa gab da ita had'e da riqo hannunta yana mai kallonta cike da tausayi bata kalle sa ba sae hannun ta da ta  janye taje zuwa share qwallar da suka zubo mata ya riqe hannun ya kai nasa hannu ya share mata qwallar had'e da fad'in "yi hqr tashi kije kiyi arwala kizo muyi sallah kinji"
   Shaye da toka ta kalle sa kawae ba tare da ta iya ce masa komai ba don  kanta ke mata masifar ciwo a gurin ga zuciyar ta dake ta faman tashi,ba'a fi minti d'aya ba ta miqe lokaci d'aya ta tafi da gudu zuwa bathroom tana kwara amai ta samu da qyar aman ya tsaya mata mohd dake riqe da ita shi ya taimaka mata ta wanke bakinta ta d'auro arwala snn suka je sukayi sallah ko shi a daddafe tayi sllr wacce tana idarwa sae kwanciya tayi kan darduma mohd dake addu'a kallonta kawae yayi yaci gaba da addu'ar sa da ya gama ya tashi yaje ya bud'e fridge ya d'auko gasasshiyar kaza yaje ya mata warming sae gashi ya dawo d'auke da fresh milk a cup da kuma naman kazar da ya saka a cikin plate.
  Yazo ya durqusa gab da ita yana kiran sunanta a hnkli bata tanka shi ba don har bacci ya kwashe ta a lokacin shi kuwa bae kula da hakan ba sae zama da yayi tare da janyo ta zuwa jikin sa ya cire mata hijab nn ta soma kuka dan sae a lokacin ta farka ya kira sunanta a natse yana ta6a jikinta da yaji ya soma yin zafi bai ji dad'in zafin jikin ba dan sae yaji damuwa a ransa.
   Ryynt dake kan jikin sa sae qoqarin zamewa take ta kwanta kan darduma bai barta ba sae qara kwantar da ita yayi kan qirjinsa ya d'ebo naman kaza zae bata tayi saurin girgixa kanta alamar bata so ya ajiye naman ya shiga rarrashinta kan tasha ko fresh milk ce nn ma taqi kan dole ya barta ta koma kan darduma tayi kwanciyar ta bata jima ba bacci ya koma d'aukar ta.
Baccin qwarai tayi dan ba ita ta farka ba har sae da akayi sllr zuhur ta tashi a daddafe dan har lokacin bata jin dad'in jikinta taje tayi wanka ta fito ta nemi er doguwar riga ta saka snn ta sanya hijab tayi sallah a nn gurin tayi kwanciyar tana d'an jin tashin zuciya nn ta lumshe idanunta a hnkli
sae ga man ya shigo d'akin tana jinsa tayi kmr bata san da shigowar sa ba shi kuma yayi tsaye yana kallon ta d'auke da kular abincin da ya kar6o a gurin su Amir dan duk cikin gida d'aya suke kowa dae da nasa 6angare.
 Kan dining yaje ya ajiye abincin snn ya d'auki breakfast d'inta dake ajiye tun d'azun ya fita dashi dan yasan yanzu kam lokacin cinsa ya wuce sae dae kuma lunch.
   Bai wani  jima ba ya dawo ya same ta kmr yanda ya barta wanda duk a tunanin sa bacci take.
Ita kuwa tana nn kwance cikin jin jiki har akayi sllr la'asar,yayinda man ke zaune sae kula yake da duk wani  motsi nata.
Ganin anyi sllr la'asar ne yasa yaje yayo sllr ya dawo ya sameta itama tayi sllr tana zaune  kan darduma ta had'e kai da guiwa tana fama da kanta dake mata masifar ciwo.
   Yazo gab da ita ya durqusa ya shiga kiran sunanta a natse tayi kmr bata ji sa ba don ko magana bata son a mata.
   Nan ya tashi ya d'ebo mata abinci ya kawo gabanta ya ajiye yace cikin muryar rarrashi "yi haquri kici abinci dan Allah kinga tun safe komai baki ci ba kinji"
  Rynt kam qamshin abincin soma damunta ma yayi nn take taji cikinta ya hautsine ta soma yunqurin amae bai bar ta tashi ba ya riqe ta dan yasan ko taje wahala kawae zata yi dan ba wani  abu taci ba,nn ya kwantar da ita kan qirjinsa yakai hannu yana shafa bayanta yayinda ta cusa fuskarta gabad'ya cikin qirjinsa tana shaqar qamshin turarensa da ya soma kwantar mata da zuciya daga haka ne bacci ya kwashe ta sae kallon ta yake cike da tausayi dan yasan dole tana jin yunwa gashi jikinta har yanxu yana d'auke da zafi.

  Yana nn zaune abinshi rungume da ita sae bacci take ya soma jin zafin jikin nata sae qaruwa yake musamman kan goshinta nn ya d'auke ta yaje ya kwantar kan bed ya jawo wayar sa ya kira Amir ya gaya masa irin magungunan da yake buqata.
  Ba jimawa yaji knocking yaje ya bud'e qofa,
Amir dake tsaye a bakin qofar yace"inace  dae jikin da sauqi koh?
  Mohd yace"to jikin nata sae zafi yake tayi tun safe har yanzun wlh gashi tana fama da yunwa don tun safe komai bata ci ba yanzu da na kawo mata abinci ko qamshin sa ma bata son ji bare ta iya cin sa.

  Amir ya nisa tare da fad'in"bari naje to nasa my wife ta mata farfesun kifi ko zata iya cin sa"

 Mohd yace"olryt tnks"
snn ya kar6i ledar magungunan da Amir ya miqa masa ya maida qofa ya rufe yaje ya ajiye ledar magungunan kan bedside drawer  ya zauna jiki sanyaye kusa da Ryynt yana kallonta cikin tsabar tausayinta da yake ji don kallo d'aya zakayi mata kasan cewa tana jin jiki.
  Bata wani jima da baccin ba ta farka sae juyi take tana neman fad'owa kan gadon mohd da ya fito daga bathroom yaxo da gudu ya tarbota,
 ta dafe  kanta dake mata masifar ciwo har bata son bud'e idonta sae hawaye kawae dake fitowa a idanun nata.
     Fuskar sa d'auke da tausayi yakai  hannu yana share mata hawaye snn ya jawo farfesun kifin da mtr Amir ta kawo mata tana bacci.
 yana bud'e kular farfesun kifin knn,
 taji tashin zuciya sosai bakinta ya cika tap da yawu ta tashi aguje ta nufi bathroom tana kwara amae mai wahalar gske dmn amman kumallo ne kawae,
 tana gama amman ta samu da qyar ta wanke bakinta sbd wani irin jiri da ke d'ibar ta ga ciwon kai kuma.
  Mohd ya riqo ta zae taimaka mata su fito bathroom d'in ta zame jikinta a hnkli ta zauna qasan tiles d'in bathroom d'in ta had'e kai da guiwa sae numfashi take fitarwa a wahale.
  Mohd dake durqushe gabanta yana kallonta kmr ya cire ciwon yake ji ya maida jikin sa.
  Cikin damuwa kmr zae yi kuka yace"Ryynt yi hqr tashi muje ki d'an ci wani abu sae kisha magani kinji"
  Da qyar murya can ciki tace"um um bazan iya cin wnn farfesun kifin ba ka fita dashi dan Allah"
   Mohd yace"shike nn idan na fitar me kike son a kawo maki kici to"
   Cikin muryar kuka tace"nima ban sani ba kawai kaje ka fita da farfesun kifin tukun"
 Nan ya kalleta snn ya tashi yaje ya d'auki farfesun kifin ya fita dashi wanda ya d'an jima kafin yake dawowa d'auke da ledar snacks a hannun sa yaga still bata fito daga bathroom ba yaje ya sameta kwance  qasan tiles har ta koma yin wani bacci kuma,
ya d'auko ta ya fito da ita ya kwantar kan bed.
  Yayi zaune gefen gadon had'e da dafe kansa don ko kad'an bae so ta koma yin baccin ba har sae ta d'an samu abinda taci ta kuma sha magani tukun.

 Ba ita ta tashi daga baccin ba sae bayan isha'i ta tashi cikin kukan wahala  dan wata irin yunwar masifa take ji ga jikinta da mugun zafi har ita kanta bata son ta6a jikin nata.
 Mohd dake zaune tun d'azu zaman jiran farkawarta ya janyo ta a hnkli zuwa jikin sa yana share mata qwallah had'e da rarrashinta,
 ta qara narkewa sosai a qirjinsa murya can ciki tace"zanci abinci"
 Jikin sa na rawa ya jawo kular abincin su da aka kawo musu na dare ya d'ibar mata abincin a plate ya d'ebo a spoon zae kai bakinta ta kalli abincin kawae ta kauda kai,snn ta kalle sa qwalla tap a idonta kmr zasu zubo tace"kayi hqr dan Allah ni bazan iya cin wnn abincin ba idan da abun sha ka bani"
   Jiki sanyaye ya maida abinci ya ajiye snn ya jawo pillow ya kwantar da ita don ya fhmci ko zama bata iya yi.
  Ya tashi yaje ya bud'e fridge ya tsiyayo mata fresh milk ya kawo mata had'e da snacks d'in da ya siyo mata a d'azun ya shiga bata da kanshi ta d'anci ba sosai ba sae fresh milk da ta d'an sha rabin d'an qaramin cup tace zatayi sallah ya bata magunguna tasha snn ya ja hannunta zuwa bathroom ya taimaka mata har wanka tayi snn tayi arwala suka fito .
Tayi sallolin da ke kanta wacce da qyar taga ta kammala sallolin sbd har lokacin kanta kamar zae tsage take ji  amma ta fara jin qarfin jiki dae dae gwargwado sae dae a kwance tayi addu'a dmn in ta kwanta ciwon kan na d'an
mata sauqi.
   Mohd yazo ya sameta gurin ta kammala addu'a ya riqo hannunta tare da fad'in"zo muje to na kaiki kan bed ki kwanta koh"
   Komai bata iya ce masa ba har ya tallabeta cak sae kallon sa take tayi har yaje da ita kan bed ya kwantar.


Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 82
       By
Gentle Lady💃🏽



Ahankali tatako inda yake Amman bata zaunaba hannunta yajawo yayi mata mazauni akan cinyarsa kanta yanakasa tana wasa dayatsunta

Yadago fuskarta ahankali yace Deejarh na meyasa bakason kallona ne kodai fuskata tsoro take baki??? Kara sanne kanta tayi tana girgiza kai yace nibanji mekika ceba magana zakiyi"" ahankali tace ah ah"" yace inhakane saiki dago ki kalleni

Ahankali tadago takalleshi idanuwansu suka sarke Dana juna kowanne zuciyarsa bugawa takeyi kamar ganga""" dasauri khadija tasanne kanta bata iyah jimirin kallon cikin idonsa yanayimata kwarjini sosai sake dago fuskarta yayi wannan karon idanuwanta alumshe suke  hakan yabawa Usman damar sunbatar labbanta

Yadaukesu tsayin mintuna ashirin yana wasa da itah ko bihim bataceba kuma batayi yunkurin hanashiba dankansa  yagaji yasaketa yajingina kansa saman kujerar yana maida numfashi"""

Haryanzu tana nan indatake sai saukarda ajiyar zuciya take ahankali"" yadade kwance saidayaji yasamu natsuwa sannan yadago akasakalance yace kinci abinci kuwa??? Kaitagirgiza alamar ah ah

Yace to tashi kihadamun ruwan nayi wanka kobashi kikazo tayaniba"" batace komaiba tamike zuwa toilet din tayi addua sannan tashiga tahadamashi""  ruwan tanacikin toilet din bata fitoba harya gama cire kayansa"" yasameta toilet din

Yace waiharkin hada shine bakizo kinfadamunba kika tsaya anan kodai wankan zaki tayanie??? Cikin zolaya yayi maganar

Aikuwa zumut tafito tace ah ah ba amfanie a aje ruwane abayan gida afita saboda shaidanun aljanu sunayin wanka aciki kaikuma idan kashigo bakaganin sauyin komai saikayi wanka dasu hakan yanajawo safuwar jinnu dakuma cututtuka da shaidanun aljanu kan iyah jefar mutum dasu

Kaiyagyada alamar yagamsu """ yashiga ciki tareda addua yarufe ko far wajenda yake ajiye kaya tabude tarasa kalar kayanda zata daukar masa shiru tayi tana nazari

Wadansu kananun kaya taciromasa jar rigace da bakin wando ""  rigar tanada dogon hannu tayita juya kayan waikomadai bayason kananun kaya??? Farar singlet tadora masa

Saikuma ta aje tafesamasu tirare wayarsa tadauko tashiga massage tayi rubutu ta aje saman kayan tafita falon tazauna jiransa

Bayan yafito wanka baisameta dakinba yaga kayanda taciromasa wayarsa dayagani da haske yadauka

Bansan irin kayanda kakesoba nafitomaka dawan nan idan basuyiba saika sauya"" murmushi yayi ya aje wayar yashirya yasaka kayan rabonsa dayasaka kananun kaya haryamanta"" yataje sumarsa yagyara dankaramin sajensa saiyafito a Usman dinsa

Murmushi yayi lokacinda yakalli madubi yagirgiza kai wayarsa yadauka yasaka agefen aljihunsa nawando yasa daya abaya sannan yafito

Tunda taji kamshin turarensa tadago kanta tadauka baisaka kayanba saitaganshi sanye cikin kayan yayi masifar kyau tayanda khadija takasa boye kunyarta takuramasa ido cen kasan makoshi tace masha Allah tsarki yatabbata ga ubangijinda yahalitta wannan surar"" tsaye Usman yayi agabanta yasaka hannunsa daya acikin aljihunsa yana sakarmata murmushi

Jinkamshinsa"" gab da itah yasaka tadawo daga duniyar tunaninda taje""yace Deejarh na nayimaki kyaune??? tagyada kai saiyanzu tadanji kunya murmushi yayi yashafi gefen fuskarta yace muje muci abinci yunwa nakeji batace komaiba suka jerah zuwa kasa

Lubabatu da labila suna zaune saman dinner sukawai sukejirah kusan tare suka kallesu yanda sukajero sunyi kyau Sundace dajuna Usman yadawo kamar danshekara ashirin dabiyar

Wani mugun kishi lubabatu taji waidama haka Usman yakeda kyau??bata taba ganin shigarda taburgetaba  irin wannan
Harsuka karaso batasan sun kawoba saida khadija tace mata inayini"" tace uyum lafiya  qalau Amarya anyinie lafiya qalau tace sannan suka zauna lubabatu tazuba wakowa saita hadewa labila da khadija sukasoma cin abincin labila kam dadi kamar yakasheta kobakomai tasan yanzu dadyn ta yasamu matarda yadade yana nema kuma insha Allah babu abunda zaisamu sahiba"" wajen yayi shiru bakajin motsin komai sai karar cokullah kowa da abunda yake sakawa aransa"" bayan sun kammala"" Usman yamike yana kallon agogon hannunsa yakalli lubabatu yace yau Abdul zaikoma tundazu inataredashi yanzun ma nadawone inyi wanka saboda zafie

Tace habadai harzasu koma bazasu jirah suyimana ko sati dayaba??? Yace kinsan akwai aiki sosai idan zaiwuce zaikawo madam kugaisa nizanje kano yanzu"" tace to Allah yakiyaye yakalli khadija yace kina bukatar wani abun??? Kaita girgiza alamar ah ah yace shikenan sainadawo tace adawo lafiya Allah yakiyaye yace Ameen sannan yawuce

Labila tahau zungurarta tana nokewa saboda lubabatu tana wajen abun yabawa labila haushi ta mike taja hannunta saida takai bakin kofar tace saiki wuce khadija takalleta saitaga tana harararta tasakai tafita itakuma tajuya takoma cikin falon tazauna tana kallon wayarta kamar batayi komaiba

Lubabatu kuwa binta kawai takeyi dakallon mamaki watoma itah yarinyar tanada kunya dakuma kawaici yartane batasanshiba lallai dole taraba tsakaninsu wanann shegiyar abotar dole abarta"" 🙄

Usman yana bude mota zaishiga yahangota tajikin glass murmushi yasaki danyasan aikin labilane Dan indai Dan khadija yanda takeda kunya bazata iyah tasowa agaban lubabatu ba

Tanakawo wa wajen yasoma dariyarta ganin ta shake kamar zatayi kuka yanzu idan takoma dawanne ido zata kalli mom itah gata marar kunya hardawani zuwa rakiyar mijie

Yace menene Deejarh na??? Tace bakomai motar yabude yace tashigo ciki babu musu tashiga yace naga kamar ranki abace kokinazuwa inje dake???

Murmushi tayi tace sokakeyi Yayana yadakeni??? Yace akan mezaidakeki bayankuma kinataredani

Tace tabdi wlh bakasan halinshiba aizaice yaushe aka kawonie harnafara yawo idan kaje kakarbomun wayana wajen inna namanta bandaukotaba"" yace shikenan yasunbaceta akumatu yace sainadawo tace adawo lafiya tafita tarufemasa motar tana tsaye saida taga wucewarsa tajuya tàkoma  fàlon kanta yanakasa tashiga da sallama

Labila ce ta amsa cikin jindadi kusa da itah tazauna idonta haryanzu yana kasa abunyabawa labila dariya tahau yimata dariya saida taga alamar zatayi kuka sannan tadaina tace sorry small mom bazansakeba ayimun murmushi mana

Khadija takaimata duka tagoce sukahau dariya lubabatu tanagefe tana kallonsu mikewa tayi tace labila kizo inason ganinki tawuce zuwa sama

Labila takalleta takalli Khadija  batace komaiba harkusan tsayin min tuna goma da tafiyarta sannan khadija tace waiba kiranki mom tayiba naga bakida niyar tashi

Tanisa sannan ta mike tace tashi muje"" harararta tayi tace bangane intaso mujeba kikasan kiranda mahaifiyarki takemaki kijemana kinsan akwai sirri tsakanin uwa daya""

Labila tace tonidai idan bazakiba nima zamana zanyi"" khadija tace au ashefa badadi tokizauna Amman wlh nima duk kikasake cewa inje wajen daddy idanhar batare zamujeba nima bazaniba tamurguda mata bakie

Labila tawaro ido tasan khadija zata aikata hakan tace rufamun asiri nidanakeso asamamun Kanwa barito naje nidai tawuce  tana dariya""" khadija tace Allah yashiryaki sahiba

Da sallama tashiga ban garen lubabatu tana saman kujerah ta amsa sallamar kasa tazauna tacemata ganie lubabatu tayi murmushi  tace saiyanzu saiyanzu uwartaki tabaki izinin zuwa tundazufa nakiraki

Kanta yanakasa tace karki daukarwa kanki wani hakkin wandama yake kanki ya isheki ni sahiba batahanani zuwaba hasalima banyi niyar zuwaba itah tasakani dole

Danbakyau kisamu mutum biyu sunafirah batareda kinnemi izinin ganin dayanba kijadaya agefe wani abuñ zaitaba zuciyarsa
Haryayi tunanin kodai maganarsa za ayi lubabatu tamere baki tace wannan kuma kutashafa  tayi shiru nayan dakiku sannan tace labila inaso kifadamun mewannan yarinyar tafini dashi dakike sonta nibakya sona karfa kimanta Nice nahaifeki duk wani Wanda zakiso yasoki bayana yake

Labila tayi murmushi tace kwarai mom nasanda haka nima inasonki irin sonda ya takeyiwa nahaifiyarta halayenkine banaso saboda sun kasance ababen kyama

Kinsan makomar Wanda yakashe musulmi kuwa??? Bayankuma alhakin daddy dakike dauka idan harxaki watsarda miyagun halayyarki wlh zanbaki mamaki  danzandawo tamkar kare agaban sugabanta

Lubabatu tamurmusa tace ke yarinya ce labila haryanzu kuruciya tana cinki nifa gatane nakeyimaku amatsayina Na mahaifiyarku banaso kobayan ran mahaifinku Ku tagayyara

Labila takalleta da mamaki tace kekintaba tunanin mutuwarki???  Gaban lubabatu yabada rasss hartaruntse idonta

Kokintaba tunanin wannan dukiyarda dady yatara bazata kareba??? Ai ahaifi da da arzikinsa yafi amutu abarmasa gado duniyar nan dakike ganie bafa matabbata bace koshi bokan naki yafadamaki shibazai mutuba wlh boka makaryacine mom yanaso yabatardakene dake dashi idan har kuka mutu Baku tubaba wutace makomarku kiwatsarda duka abunda yabaki kidogara ga Allah shine zaibaki duk abunda kikeso

Afusace lubabatu tamike tayanka mata mari tace rufemun baki shashasha wacce batasan maisontaba tunkafin. Ahaifeki nakejin irin wannan wa azin ga malamanda suka keceki awajen karatu Amman kokadan baiyi aiki akainaba sai wanann maganar taki kedabanda bokana harma za ahaifeki kekanki darajarsa kikeci wlh

Labila tadago cikin kuka tace wlh karyane nibabu wani kazami mushiriki daya isah inci darajarsa shaidan kawai inna kintata daidai dadyna bama cikin hayyacinsa ya aurekiba kaico ni labila meyasa mahaifiyata tazama haka daga ina matsalar take???


Lubabatu tace tashi kibacemun  daganie kuma nasan duk take takenki wato ke gamai Kawa?? Nibabu ruwana da kawancenku idankuma baki fita sabgataba harke zansa agama dake dannalurah kinashigarmun hanci nagaji da abunda kikeyi kinsoma shiga huruminda banakiba

Labila tasaki murmushin takaici tace kisa yakasheni mom saimuga idan agurinshi rayuwata take nikoda mutuwa nayi wlh banda takaici me akeyi dawannan kazamar duniyar maitattareda da dauda da kazantar masu halayya irin taku dake da bokan naku sainaganie idan kudin zaku gujewa mutuwa "" ta mike hartakai bakin kofa tace kiyi hakuri mom banason muryana tana zarta taki awajen magana kigafarceni Allah yaganardake gaskiya tabude ko far tafita anan tabar lubcy tsaye rayuwarta intayi dubu tabaciii kirjinta kamar zai balle kofar dakin takulle tawuce kuryar dasauri danfa dole *hatsabibin boka* yasan matakinda zaidauka akanta






Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




chapter 83
       By
Gentle Lady💃🏽




Dasauri takarasa wajenda ta ajiye akwatin madubinta tadauko tafito dashi tashafa tareda kiran sunan *hatsabibin boka* saigashi haske yayi tartsi saigashi ya bayyana saman kujerarsa idanuwa jajir lubabatu tasoma magana

Haba boka waimeyasa hakan Ashe akwai lokacinda zanga irin wannan ranar yata tacikina tana nema tafi karfina??? *hatsabibin boka* yakece dawata mahaukaciyar dariya yace babu abunda banganiba acikin madubin tsafie na kisani wannan aikin bakaramin aikibane dole kirabasu indai kinaso kiga karshen wannan yarinyar

Cikin damuwa tace yazanyi inrabasu boka??? Kaima kasan labila idan tanason mutum bazata taba barinsaba dama batasan shirina akantaba dasauki Amman yanzun bazata taba yarda inrabasuba

Yasake kecewa da dariya yace cikin sauki zakirabasu tace taya kenan boka??? Yamurmusa kicewa mijinki yakamata suje yawon shakatawa kodan sumore amarcinsu tunda kinlurah Amarya kunya takeji bazata sake jikinta ananba

Lubabatu taware ido tace habadai idan nayihaka anya banyi wautaba??? Wata razanannar tsawa yadakamata yace nifa ba amusu danie dazaran nace ayi kaza kar atsaya yimun musu idankuma bahakaba narantse dagirman tsafina bazanji tausayinkiba wajen nunamaki kuskurenki

Tuni jikin lubabatu yahau kyarma kamar mazariii tadukadda kanta tubanake yakai wannan gawurtaccen boka man tawa nayi Amman zankiyaye gaba

Batareda ya sauraretaba yace idan kin aikata bayan suntafi saiki nemenie yabace battt yaufa lubabatu tabatawa boka raiii jitake gabadaya duniyar tayi mata zafie kamar wutaa jin Kamar ana kwada sallama yasaka tamiyarda komai tashiga toilet tawanko fuskarta tadan goga powder tafesa turare sannan tabude kofa tafita matar Abdul ce tana ganinta tasaki fara a tace karaso mana

Hauwa u"" koda yake nayi fushi tunsanda kikazo sunan Abdul bakisake zuwaba karasawa tayi cikin falon tazauna tana dariya tace haba Anty luba kinsan balaifina bane wlh tunsanda mukaje minna bansake dawowa nan ba dadyn ameer ne kawai yake zuwa koshi bayawuce kwana daya kema kinsan danazo aidole inzo nandin saboda ke

Lubcy tace hakane ina yaranki ainasan yanzu kinyi haihuwa biyar ko??? Hauwau tarike baki tace lala Anty luba kebakiyi biyarba saini kanwarki"" lubabatu tayi dariya tace aimu munbarmaku bakiga Dan autana yagirmaba


Hauwa u tace inazanganshi labila kawai naganie ai"" nima haihuwana uku biyu mata daya namiji Asiya kausar sai Muhammad inakiranshi ameer dansunan babane"" lubabatu tace masha Allah Allah yarayamana su tace Ameen bari nasa akawomaki ruwa"""

Ah ah dakinbarsu labila tabani ruwa wlh tundazufa mukazo su asiyama sunakasa nabarsu"" tace shikenan ya minnar???
Tanacire mayafinta tace Alhamdulillah ai inasaran kwanan nan zandawo garin nan nagaji dazaman cen bansan kowaba saidai makota ko anawani Abu saidai kaji labari nacemasa yayi aure kawai saiyaje da amaryarsa  nikuma inzauna dani da Yayana

Kallon wata marar wayo lubcy taimata tace lallai Hauwa wasu suna gudun kishiya kekuma harnemanta kikeyi??? Tace to menene Anty luba arzikinefa ai abun farincikin kine mijinki yakara aure alamun kunada wadatar zuci kenan ni wlh koda hudu zaiyi inaso kowafa da halinta zata zauna nasandai duk inda zaije yazagayo  kaina zaidawo dannice uwargida kingakuwa girmana bazai taba faduwaba kobayan raina za adinga yabamun insamu kyakkyawan shaidu aduniya yafi inmutu inbarwa Yayana abun fada

Tuni lubcy tadauke wuta kardai hauwau tasan abunda nake aikatawa??? Takatse mata tunani dacewa amaryarki taburgeni wlh gata karamar yarinya zakuji dadin zama dajunanku dannalurah saitayi hakuri

Lubabatu tace hakane kam wlh ai inata addua dadyn labila yayi dace kinsan matan yanzu sai ahankali watama kina zamanki lafiya damijinki dazaran tashigo saitatashi rabaki dashi

Matanda yake aurah duka banakwarai bane Amman wannan kam ina tunanin andace!" Hauwau tace hakane dadyn ameer yasanardani ai Allah yasake shiga tsakaninmu da mugayen mutane lubcy tace Ameen

Mikewa Hauwa tayi lubcy tace waiharzakiyi me??? Tana yafa mayafinta tace tafita mana kinsanfa jirgi bazai jiramuba dole mujirashi dalokacin tashinsa yayi zaitashi tace hakane tamike turarukka dakayan shafawa tahado mata suka sauko kasan sun samesu sunata firah kamar dama sunsaba dajunansu duk Asiya tace kunga har mom tafito tonidai Anty kibamu number muyi chat

Labila tace wlh bata chat saidai kuyi waya kuma banama tunanin tazoda wayar inaji tamantata agida saidai inbaki tawa

Tace shikenan suka karbi number labila lokacin har su lubcy sun kawo wajensu tare sukai masu rakiya harkofa saida sukaga tashin motarsu sannan sukadawo

Daki suka wuce kaitsaye danyin sallar la asar bayan sungama sukai zamansu adakin"" lubabatu Sam takasa jinta daidai tun abunda tayi yazama dole tasake kiran boka tabashi hakuri hakan kuwa akayi tasake kiransa tabashi hakuri yace ya yafemata Amman kartasake aikata irin wannan kuskuren tace tagode zatakiyaye

Yace nasan abunda kike tsoro kisani babu abunda zaishiga tsakaninsu duk abunda yakefaruwa dasauran matansa itama aikin yashafeta muddin yayi niyar hada shinfida da itah zaisamukansa yana kyamarta saboda warinda zatarikayi kamar mushe

Dazaran sunbar kasarnan zakiga laya a inda nasaba aikowa a ajiye maki kije kisamu wajenda kikasan kullum sai anyi dahuwar abinci tundaga safe hardare"" saiki tona murhun kisaka layar karkibari kowa yaganki dazaran kinyi haka kingama komai

Yanda kikasan zafin wuta idan kikaje kusa da itah haka jikinsu zaiyi zafiii dazaran sun kusanci junansu zasuji kamar zasukama dawutaa dole su nisanci juna tahakan hankalinta zaitashi tadaina samun lokacinda zatazauna tayi addua saboda tunani alokacinne zamucika aikinmu akanta. Wayyo dadi tuni dadi yalullube lubcy tahauyimasa godiya yace maganar labila tabarkomai ahannunsa shiyasan yanda zaiyiii

Tayi masa godiya tace zaiga sako aranar ta siye dabbobin ta aikamasa"" cikin kwana biyu tasamarmasu biza dakomai dantasan inhar cewa tai sutafi labila tana iyah cewa saitabisu wannan dalilin yasaka taiwa tufkar hanciii







Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠



Chapter 84
       By
Gentle Lady💃🏽




Zaune suke dadare suna cin abinci lubabatu tace nikuwa yau akwai maganarda nakeso muyi dakai""" yakalleta yace Allah yasadai lafiya ??? Tarausayarda kai tana kallon khadija cikin fara a tace insha Allah baridai mukarasa cin abincin"" yace nidai kifadamun yanzu kinsanni da zumudi kamar sabon angwo gabadaya suka kwashe da dariya harsu labila""


Yace tokokunga laifina ninafison idan za afadamun Abu kawai afada yanzu kafin mugama bakisan iyah jaye jayenda zuciyata zatayiba""" adaure afadamun

Cikin siririyar muryanta tace daddy kasanfa ba amfanie ana cin abinci ana magana kamar bakabawa abincin mahimmanciba""" yakalleta gaskiyarkifa Deejarh tobari mugama yayi maganar yana kallon lubabatu murmushi kawai tayi tacigaba dacin  abincinta

Aranta tace wannan hartasoma tafi labila iyah yi shi abincin harsai anyiwani girmamasa 🙄"" tsaki tayi aranta tacigaba dacin abincinta""  bayan sungama  sannan yakalleta yace karfa kice naciga zanzari nasan duk abunda zaifito bakin nan naki alkhairine murmushi tasaki har hakoranta suka fito tace ko???

Yace koma zakice ainidanake dake nasan haliinki fiye dake kanki""" labila kam murmushi tayi aranta tace kadaisan Wanda kasani  amman babu Wanda yasan halin mom sai Allah nda yahalicceta"""

Tace hakane abunda yake gefenta tadauko Tamika masa tana murmushi shima murmushin yakeyi taredakuma mamakin  menene aciki???

Tagane abunda yakenufi tace kabuda kaganie mana""" bamusu yabude biza ce tazuwa Dubai

Baki sake yake kallonta yace biza naganie??? Tamurmusa ah takuce "" tanisa tana kallon khadija tace wannan itace kyautar taya murnar auren Ku nabarku kumore amarcinku har Kanwata tasamu rabo""" dasauri khadija tasun kuyarda kanta kasa saboda kunya

Usman yarasama dawadanne irin haruffa zaiyi amfani domin yagodemata dakyar ya iyah hadiye yawun bakinsa dasuka kafe yatttaro sauran maganarda ke bakinsa yace

Maman Abdul wai dagaske kike kuwa??? Tagyada kanta sosaima aikasan inason farincikinka fiye da nawa inaso kasamu cikar burinkane bazanso kacigaba tatauyewa kanka hakkiba

Nalurah kanwar tawa bazata saki jiki dakaiba saboda tanada kunya shiyasa nashirya maku tafiyar kozatadan sake dakai

Yasaki lallausan    murmushi Alhamdulillah amman naji dadi sosai bansan dawadanne irin kalamai zanyi amfanie wajen godemakina tnx matata

Murmushi tasaki najindadi tace basaika godemunba wannan aikinane nashirya  maka kayanka""" sauran nata tashirya dan jirgin shadaya zakubi

Yayi murmushi yana kallon khadija takasan ido wacce haryanzu idanuwanta suna kasa kosaudaya bata dagoba"" labila kam tashiga tashin hankali dankuwa tana tunanin wannan abun kamar wata munakisar lubabatu tashirya Amman babu yanda zatayi tawargaza tafiyar tunda batada bakin fadin komai akan mahaifiyarta Amman alal hakika ranta baikwanta da wannan tafiyarba

Dolene tasamu malaminsu saboda ayiwa khadija saukar qur Anie murmushi tayi afili sanin tasamo mafita lubabatu tana jefar labila da murmushi itama haka kowannensu shikadai yasan ma anar murmushin nasa

Labila tace sahiba tashi muje intayaki hada kayanki dankinsan dasafe bazaki samu damar hadawaba tayi maganar tanajan hannunta

Tamike jiki bakwari tabi labila kamar rakumie da akala sukuma suka rakasu da idanuwa lubabatu tanayiwa  Khadija kallon kingama yawo yarinya tunda kika auri mijina

Usman kuwa  yanayimata kallon  soda kauna yanarayawa aransa zaihuta sosai da Deejarh nsa" saida suka bacewa ganinsu sannan Usman yamike yaja hannun lubabatu suka dawo falon saman kujera suka zube

Yakuramata ido yana murmushi itama shitakeyi tace yadai mijina""" yamuskuta lubcy wlh mamaki kikebani sosai"" tarausayarda kai tace mamakin menene???

Yace yanda kike kyautatamun wai anyama zamanin nan za asamu mata masu irin halayyarki??? Gaskiya baza asamuba""" tace nidai kadaina fasamun kai da dadin bakin nan naka

Yajawota jikinsa yace badadin bakibane wlh dagaske nake nikam nayi sa ar mata tagari wacce kowanne namiji zaiyi mafarkin mallakar irinta"""

Hawayene suka sauko akan kumatun lubcy sanyinsu yaji ajikinsa yajuwoda itah dasauri yace lafiya lubcy menene kuma nakuka??? Please banason kukan nan nakie Dan Allah kidaina

Tashare hawayenta tace inajin takaiicin kaina daya kasance bana baka hakkinka dayake kaina yanda yakamata inayin hakanne kodan Allah yayafemun hakkinka danaketauyewa ninasan ina cutarda rayuwarka

Banason inzama daya dagacikin matanda Allah zaiyi fushidasu Usman yadorah yatsanshi akan labbanta yace bakyacikinsu matata nibaki tauyemun hakkinaba aihakan Allah ya halicceki kuma kinayin iya kokarinki wajen ganin nasamu kwanciyar hankali nagode maki Allah yabarmu tare yasake janta jikinsa yana aikamata wani sako mai rikitarwa

Al amarinsu labila kuwa suna hawa bangaren khadija tasheka dagudu saman gado taboye fuskarta""" labila mezatayi inba dariyaba saida tayi mai isarta tace wlh nifa mamaki kikeban kowaya fadamaki yanzun anajin kunyar soyewa danamiji

Kinganni nan wlh idan nai aure saina baki mamaki Dan wlh agaban kowayema zannunawa mijina soyayya gashidai kin girmeni Amman ninafiki sanin yanda ake tarairayar miji

Tazauna kusa da itah sahiba wannan tafiyarda zakuyi wata damace agareki daxaki saye zuciyar mijinki ki ajiye kunyar nan taki kinunawa mijinki tamkar dagake saishi kuke acikin duniyarku

Idan kinataredashi kimanta dakowa kigamsarda mijinki Dari bisa Dari kedin tashice kuma mallakarsa tarage murya kuma wlh karyanemi kibashi hakkinsa kiyita gudunsa

Khadija tamike takaimata duka tace waike yaushe kikazama marar kunya bansaniba??? Labila tace ke yarinya zauna nan ainadade inacemaki kifara chating kozaki koyi yanda ake ririta miji kinki hmmm wlh jinake damanice ke danatsula tsiya sai nasakawa wata hawanjinie😕😂

Khadija tatureta tace Allah yashiryaki mom din??? Tace au sorry namanta ashefa mom ce baridai inhadamaki kayan dannasan halinki innabiye maki manyan kaya zakidauka duka tayi maganar tana mikewa tabude drawer tajawo akwatin kayan khadija

Tahau duba kayan ciki kananun kaya tayita shiryawa khadija saboda Usman yasiyamata kananun kaya masu masifar kyau

Mini sket da kananun kaya gasunan kamar kazanta""" manyan kaya kala uku kawai tasakamata"" takoma hadamata kayan kwalliya komai saida tasaka tace sauran kuma idan kinje karkiyi kwalliyar""" nasan halinki"" danzankirah inji waima ina wayarki???

Khadija tace nafadawa dad fa yakarbomun gida namanta ta wlh kuma inason yin magana da Yayana Amman nakasa tambayarsa koya karbo kumashi baicemun komaiba""   labila tace kinsone wlh dakinason wayadashi aidasaikice inbaki Aron wayata saiki kirashi""

Tamere baki inna hardace nomber din kokuma inbar hardaceba"" labila tace kumafa hakane Amman aidason ranki lanbarda batawuce ashirinba keda kikeda kwakwalwa maikyau kikasa hardacewa

Tace kwakwalwata ta karatuce bawai danna hardace tarkacen numbers ba""" labila tace hakanefa ustaziyya  Amman  kinsan hardace number yanada amfani kodan watarana

Bawai ina fataba kisamu kanki inda kike neman agaji abaki Aron waya baki hardace number kowaba yakenan gashima dai yanzu karamin misali kinason waya da ya muktar Amman bakisan number saba

Khadija tace kinada gaskiya zanyi kokarin hardace tamutum biyu"" labila tace Yayana dakuma daddy ko ???

Murmushi khadija tayi labila tace bakomai mukoda ba a hardace tamuba badamuwa Amman inafatardai abunda nafadamaki dazun kinkwasheshi afaifan kanki wlh sahiba inajimaki tsoron wata baturiya takwace makishi

Aikuwa khadija tahade rai labila tahauyi mata dariya tatashi tabita sukahau zagayen dakin karshedai labila tafada saman gado tana hakiii tace tubanake small momy🤗

Khadija tace aisaikinsha rankashi aka"" labila tarumtse ido takankance kai tanadafe dakai tanajiran saukar rankwashi khadija tahauyi mata dariya tazube saman gadon tace waike atunaninki rankwashinki zanyi aka???


Ainibazan rankwashi kainaba idan dady yasamu baturiya aibanice zanyi kishiba kece dannasan kinfison farincikine fiyedani Kaina yanda kika damu dani nibandamu dakaina hakanba """

Labila tace aisaboda kinsan hakan shiyasa kikemun abunda kikaga dama takwanto saman kafafuwan khadija tace wlh sahiba jinakeyi kamar aduniya bazanso kowa sama dakeba

Idan akacire Allah da manzonsa   da sahabai dakuma ahalal baitiii   idan za akuma tambayana wanakeso bayansu kinsan wazanfada???

Khadija tagirgiza kai labila tace wlh sahiba sunanki zankirah !! Jinake tamkar sabodake akayini kullum soyayayrki sake shiga rainatake bansan daliliba kodan kinason babanane

Khadija tayi murmushi tace dama haka Allah yake ikonsa soyayya gamon jinice""labilata tashi  zaune takurawa. Khadija ido kamar mainazarin wani abun saikuma  tafashe dakuka data tunoda kudirin lubabatu akan Khadija

Itama batasan sanda tafara kukanba suka hade kai sunata kuka akarasa Wanda zai rarrashi wanie







Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 85
       By
Gentle Lady💃🏽



Saida sukai mai isarsu sukadawo rarrashin juna""" labila tace zanyi kewarki sosai sahiba idan kikatafi khadija  tace nima haka wlh sahiba Amman karkidamu ga wayanan ai zamudinga waya kodata daddy ce

Nibandama wani Abu mezaihana kicewa daddy kema zaki wlh zanfi sakewa idan inaganinki"" labila tace naki wayon aiko nan gani nane yasaka kika sakankance gobe aurenki sati dayafa Amman bakitaba zuwa wajen mijinkiba saikace haka akacemaki anayin auren"" wlh kebandah wani Abu dasaina hadaki da inna airanarda za akawoki bahaka akace kiyiba

Khadija ta marairaice fuska kamar zatayi kuka tace daddy nefa yace inbari yafadamaki kizo kirika tayani kwana kokuma haka kurum baikiraniba nidadi miji sai inkai kaina""

Labila tace ayya sahiba kinada gaskiya aibandauka hakan akayiba koni banbaki goyon baya kiyimasa rawar kafaba dole mudanja ajinmu irin namata aikingane dannafiso yagane akwai banbanci atsakaninku """ mudin bamasu arha bane

Khadija tace kedai akeji wai mahaukaci yafada rijiya kinga kitashi muje muyi alwala dare yayifa sosai musamu ko hizifi uku mukaranta"" labila takalli agogon dakin yabuga shabiyu da kwata tace hakafa aiyau babu maganar barci hirar bankwana zamuyi

Khadija tace nanfadai wlh saina kwanta kinsan bantabaa shiga jirgiba karnaje nayita kwasar barci ayimun dariya tayi maganar tana mikewa labila tace dariyadai waye zaimaki dariya Wanda ya aikeki bayankuma kowa  da abunda yashamasa kai babu ruwan kowa dawanie

Khadija tace to suda muje muyi alwalar tana dariya tatashi khadija  tafarayin alwala sannan labila sukasoma karatu sai uku saurah suka kwanta

Washe gari tunda sukai sallar asuba basu komaba sukahau shirya kayansu harda labila dantacemata itama kano zatawuce dazaran tarakasu


Bayan sungama suka gyare dakin "" dasauran inda suka bata"" sukai wanka suka shirya sannan suka fita falon kasa Usman yanakusa da lubcy sai shagwaba takemasa  kamar wata karamar yarinya shikuwa saibiyemata yake

Haka kurum khadija taji wani iri aranta tayi saurin soke kanta ahankali labila tace kinga yanda akeyi itama data tsufa ballantana keda kike sabon jinie yanzu kike lokacin ganiyarki ta rayuwa

Sam Usman baisan dazuwansuba lubcy ce kawai talurah kuma batadaina abunda takeba saima tayi tamkar bata gansuba""

Usman ne yaji kanshin khadija ya yawaita afalon yadago yakallesu dasauri yayi saurin saita kanshi yajanye lubcy daga jikinsa sosai yake jin kunyar labila

Khadija tagaidashi bayan sunkaraso ya amsa cikin dakewar murya "" tagaida lubcy itama ta amsa labila tagaidasu sannan suka karasa saman dinner haryanzu Khadija batadago kanta sunyi ido hudu dashiba

Tunda suka fara cin abincin yakeson tadago kanta danyakafeta damayun idanuwansa Amman taki dagowa dukda tanaji ajikinta yana kallonta

Bayan sun kammala yakirah habu driver labila tafitomata da kayanta sannan takulle bangaren  tarike key din"" lubcy ce tafitoda kayan usman driver yakwashe duka yasa mota suka rankaya dukansu

Yace banga kindauko mayafinkiba kokina nufin iyah nan zakiyimana rakiya??? tana dariya tace inalaifi aiga yarkunan zata rakaku basainajeba Allah yakai lafiya yace Ameen

Takalli khadija tace Amarya asha amarci lafiya khadija tasanne kanta dakansa yabudemata baya"" harzata shiga tadafe kanta""  innalillahi"" wlh nayi mantuwa

Usman yace mantuwar me kumata dama haka shirinku yake kosati zakuyi kuna shiryawa karshe saikunje kunmanta wani abun

Labila tace kabarta mana tadauko mekika manta??? Tace wlh littafaina da Qur ani kumafa dankar namanta  Na ajesu kusa kusa

Lubcy tayi karaf tace kekuma banda abunki Kanwata kudazakuje yawon amarci mezakiyi da littafai aikyabaridai harkudawo shima maigidan abashi lokacinsa

Labila tace sabodame zatabàrsu dankawai zatayi tafiya sai akace kabar addininka agida kejeki dauko sahiba tamika mata key wlh kar shaidan yarinjayeki ko inakikaje rike ibada saikace dai su oi daba ta dauki addinin dakimaba"" khadija tawuce cikin gidan

Lubcy tace aike komai saikin nunawa mutane kinfi kowa """ saikifadàman dawakike??? Labila ta marairaice fuska tace waini meyasa mom batasona daddy yanzufa dawata Yar makarantarmu nake tafashe dakuka

Usman yace haba lubabatu yarkiicefa baidace kinamata hakanba"" tace alhaji kanajinfa abunda takefada itah yadace tayihàkà?? Nifa mahaifiyartaçe

Yace aibadake takeyiba tafadamaki dawatà Yar skull dinsu take

Bandama abinki aikinaji batakirah sunaba koda ma takirah suna tundakedai kinsan bahaka kikeba aishikenan saikibarta"""

Tanisa shikenan alhaji yace yauwa kokefa yarnan dai takice komai lalacewarta nibansan dalilinda yasaka bakwason yayan fariba

Ainikam hajiya batayimun irin yanda kikemata karfanaje nadawo nasamu kinhanamun ya rawar gaban hantsi"" labila tace aini dad wajen hajiya zankoma saikundawo zandawo

Yace shikenan ma dama abdul sai Rigima yakewa hajiya waisaita kawoshi inda kike yauma naso turawa shima adaukoshi yadawo nan

Tace idan yadawo dad karatun shifa ??? Daidai kawowar khadija yace kece kikasan hakan Amman wlh danaje kuka Yakama saiya biyoni nakawoshi wajenki"" shibaima tunanin kowa saike

Khadija taimasu sallama suka amsa tamikawa labila key din bayan mota sukashiga shikuma dashi da driver suka shiga gaba tana tsaye tana daga masu hannu harsuka wuce sannan tajuya cikin gidan tana sake sake aranta sama tahau taduba inda ake ajemata sako tasamu layar wani murmushi tasaki tana juya layar labila kenan aiduk kame kamenki saina raba Usman da khadija saidai kuma kiyi hakuri

Tasheke da wata mahaukaciyar dariya irin wacce *hatsabibin boka* yakeyi saida naja baya dannatsorata nadaukama shine yabayyana agabana""

Tunda suka shiga mota labila saizuba takeyi harsukakai airport sunsamu jirginsu Saura minti talatin yatashi

Anan suka zauna zaman jirah duk abunda za ayi akagama lokaci yanayi suka soma shiga jirgi sai lokacin labila tasoma sharar hawaye tana kallonsu harsuka shige tana tsaye saida jirginsu yadaga tanasharar hawaye tana daga masu hannu""

Saida tadaina ganin jirginsu sannan tacewa habu suwuce ganin wani guy yanata kallonta"" tunda sukashiga motar tayi shiru sai sake sake takeyi aranta""

Sunakaiwa gida tace yajirata tashiga gidan lubabatu tana falo tayi sallama tahau sama tadauko jakar kayanta tasauko sannan tace ni mom zantafi

Tanisa kigaishesu"" labila tace zasuji hartajuya saita tsaya tace nasan kinturah dad da sahiba Dubai ne akan wani mugun nufin naki kisani Allah yafiku kibarganin bokanki yanacin nasara kidauka komai kika nema aduniya zakisamu awajensa shikanshi damace Allah yabashi domin yayimasa takunkumi kiji tsoron Allah Mom kidaina biyewa wanann bokan tafashe dakuka maitsuma zuciya lubabatu tamere baki

Idankundago kai tagado takalli indama labilar take saida tasakecewa please mom badanniba kidaina abunda kikeyi kinemi gafarar Allah

Tadago takalleta ahankade tace kingama??? Labila tayi shiru tace totunda kingama nagode da nasiharki muna gaidasu tamike tahaye sama tabar labila tsaye

Tabita dakallo saida tabace mata sannan tashare hawayenta tajuya taja akwatin kayanta
Tafita"" habu yabude mata tashiga yaja motar akabude masu get sukafita"

Fitarsu babu jimawa lubcy taciwo kwalliya tafita itama"" tashiga tanta tsetsiyar  motarta akabude mata get tafita tasoma yawo cikin unguwanni kozata samu inda akeyin dahuwar abinci tunsafe har dare abunfa dawahala kuma ance karwani yaganie danhaka badamar tabawa wani kwangila dole dakanta zata binne""

Haka tayita yawo""" duk inda tatambaya daga masuyi dasafe saimasuyin da rana"" kuma tafison ahanya Dan agida tayiyu ba a cika wutar yanda zatayi zafie

Su khadija kuwa tunda jirgi yatashi takankame idanunta kamar zatayi kuka sai addua takeyi hakan yasa usman yajawota jikinsa yakwantar harsuka lulaya cikin gajimare"" ahankali tasoma saukarda ajiyar zuciya ba awani dadeba tasoma barci maidadi asaman jikin Usman

Dayalurah tayi barci yagyara mata kwanciyarta ajikinsa yarufemata fuskarta danbayaso ana kallonmasa puska tuni shima yasoma saukarda ajiyar zuciya yajingina kansa jikin kujerar jirgin yana tunani

Lubabatu tana tsaka dayawo tabaro unguwarsu Danisa indama taje batasan sunan unguwarba bama tataba zuwaba wata yarkasuwace Dan kusa da bakin titi take komai anasiyarwa awajen wata maisuyar doya taganie da dankali da awara

Tatsaida motarta tafito zuwa wajenta matar tanaganinta tawashe baki tanamata sannu dazuwa lubcy ta amsa suka gaisa tace nawa doya matar tace hamsin ashirin dankali kuwa goma biyar "" haka awara

Lubabatu tace kullum kina fitowa??? Tace tomezaihana hajiya aizama gida banamu bane munada marayu agabanmu

Lubcy tace Allah sarki aiyanada kyau kanemi halak dinka kamar dayaushe akesamunki anan??? Matar tace ai hajiya kaman karfe bakwai nake fitowa indorah koko idan yakare zuwa yanzu shabiyu nasoma suyar doya da dankali saidare nake tashi inbarwa yata inkoma gida inyi tuwon dare infito dashi

Takwas muke tashi watarana harmunakai Tara"" lubabatu tace kainaji dadi bani doyar ta dubu uku kisa dankali Na dubu daya zandinga aiko driver na yana karbar Mani

matar tawashe baki tace kaiii Amman naji dadi hajiya tanata wasar baki tazubawa lubabatu doyar tabata tafiddo kudi sabbi hull Tamika mata sukai sallama takoma motarta hartabar wajen matar tanadaga mata hannu saikallon kudi takeyi

 tana juyasu bayan lubabatu tayi nisa tatsayarda motar tafito da ledar doya dantasan koda tajeda itah gida bazata iyah cintaba danmaituyar doyarma kyankyaminta takeji tasoma rabon ido kozataga wasu almajirai tanakiran wani

Yarugo kamar daga sama tajiii ance banda sadakaaaa aikinki zai lalace dasauri tajuya bayanta bataga kowaba tamiyarda doyar yaron yanazuwa tacemasa wanigida take nema kuma tagane tashiga motarta tawuce daniyar dadare zatadawo ta saka layar






Aisha✍🏼

☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠



chapter 86
      By
Gentle Lady💃🏽




Doyar datasiya da dankali saidai tazubar shara"" tana zauna sai sake sake takeyi aranta"" tamatsu dare yayi"""

Su khadija basu suka saukaba sai dayamma"" dama usman yana yawan zuwa Dubai bayazama a hotel gida yake kamawa haryagama zamanda zaiyi Amman gidan kusa dawani babban hotel yake"" mamallakin hotel din shiyakeda gidan yayishine  dama saboda saukar baki""

Gidan tsab tsab dashi Dan akwai ma aikatanda suke shareshi su goge kullum saboda irin haka karbako yafado kokuma Wanda zaidauki hayarsa yazamana yanada datti""
           Bayan sun aje kayansu saman kujerar falon khadija tazube saboda zaman jirgi Usman haryanzu yakasa gane kanta kumashi yakasa yimata magana

Idan tunaninsa gaskiyane Deejarh tana kishinsane"" murmushi yasaki ahankali ganin ko kallon inda yake batayi

Rigarsa yacire yabar wando sai farar singlet dinsa"" kusa da itah yazauna yajawo hannunta yace zo injimana Deejarh na wannan cin maganin duk na menene???

Kanta yanakasa haryanzu takasa dagodakai takalleshi"" yanisa please Deejarh na kisaki ranki dan Allah kodai garin nan ne bakyaso??? Kaita girgiza masa alamar ah ah

Yace towani abun akaimaki??? Nanma tace ah ah yace shikenan kitashi kiwatsa ruwa nibari insiyo mana abunda zamuci yayi maganar yana mikewa yadauki rigarsa yasaka yafita

Tabishi da kallo aranta tace meyasa hakan mezaisa inyi kishi matar sacefa??? Nibataji haushinaba danarikemata miji saini

Haba zuciyarta baikamataba mahaifiyar sahibar tawa saurin mikewa tayi  tayishirin wanka "" tashiga toilet da addua  aljanie haruzzal yana biye da itah saboda cika umurnin shugabansa""

Allahumma inni a uzu bika minal hubusi wal haba isi sannan tashiga take haruzzal yamakance baya koganin gabansa haka yayita bin hanya baiganin komai

Khadija kam batasan wainarda ake toyawaba bayan tagama wanka tadauro alwala tanafito wa Usman yana shigowa da sallama ta amsa masa sallamarsa ledarda take hannunsa takarba shima yayi shirin wanka maikawai tashafa sai powder tasaka wasu Riga da siket sundan matseta bakamar siket dinma""tafesa turare tasa hijab

Koda yafito hartasoma rankon sallarda take kanta shima yashirya cikin jallabiya yatada sallah bayan sungma sukai addua"" tajuyo da fara a tacemasa inawuni

Yasaki murmushi koba komai yaga fara arta yace qalau sarkin zuciya dariya tayi tace nifa dad bafushi nakeyiba kawai yanayin zaman jirginne yasaukarmun da gajiya

Yace kedai fadi gaskiya ainalurah dake tungida kiketa shan wannan kamshin harcikin jirgi kinkasa bari muhada ido

Ledarda take gefensu yajawo yajata jikinsa yace nasan yunwa kikeji bari kici abinci kozakifi sakewa danni banason ganinki cikin damuwa

Sinasir ne damiya dakuma jelof din shinkafa yace wanne kikeso dagaciki??? Dahannu tanuna masa jelof din

Yace to inazuwa yatada itah daga jikinsa yaje kitchen din gidan yadauko plate da cup da chokali yazuba jelof din sannan yazuba ruwa  dakansa yarika bata abaki tanaci hartakoshi""

Yace ga ferfesun tace nidaikam Alhamdulillah yace tonidai bari naloda yadauki chokalin zaici tarike yakalleta yadaga girah alamar mene???

Tace nima dad zanbaka"" yasaki murmushi  tonaji Amman banda katuwar loma kinga bakin yanda yake very small

Dariya tayi tanarike baki"" yace yidariyarki an jima nima zanrama"" tadibo abincin tasoma bashi yace wannan saiyawuna suntsinke kafinma tabanie kiyi dasauri kinsanfa cinedani kamar gara

Tayi dariya kai dad tobari nadinga baka dasauri tayi maganar tanaciko chokalin harbaka"" yace bafa cewa nayi kidibo Wanda yafi karfin bakin nawaba tace to sannan tarage tabashi baiwani cidayawaba yace yakoshi tace kaifa kace cinedakai

Yace aiwanda naci bakici korabinsaba""" murmushi kawai tayi tace shikenan jin ansoma kiraye kirayen magrib yamike bari naje sallah"" bayan yafita itama tayi alwala tayi sallah Usman baidawoba sai bayan isah koda yashigo yasamu hartayi barci saman abar sallah tada itah yayi yace takoma akan gado

Takoma takwanta sai lokacin yabude wayarsa yashiga wanka yanafitowa kiran labila yana shigowa  yadauka da fara a tayi sallama ya amsa yace nasan tundazu kinyita kirah kikajita kashe

Tace wlh kuwa kunkai lafiya??? Yashafo Kansa Wanda yake jike daruwa yace qalau muka sauka aitundazu """ muka sauka mantawa nayi ban bude wayarba"""

Tace ayya ina sahiba""" yakai kallonsa wajen khadija wacce tasake juya kwanciya saboda jindadin   iskanda yake kadata""" yasaki murmushi yace tayi barci ko atada itah..

Tace no barta tahuta nasan gajiyace kawai gobe kaafada mata nakirah yace shikenan harkinje kano??? Tace ah ganima kusa da hajiya tace tana gaidakai yace kibata mugaisa mana tace to""".

Sannan tamika mata"" takarba tareda sallama ya amsa hajiya inawuni tace lafiya qalau babangida"" ya khadijar yace qalau take harma tayi barciii

Tace ayya aidole Tasha hanya idan kuntashi kagaisheta "" yace zataji hajiya ina Abdul"" tace Abdul Dan Rigima aidarensa yayi yanacin abinci yayi barci""

Usman yace ainahuta kullum nazo saiyadameni anty labila hajiya tace aibakasaniba dayaganta shareta yayi waiyayi fushi saida tanuna masa sweet sannan yaje wajenta usman yayj dariya yace sarkin rigima ai hajiya kina fama" " tace toyazanyi tunda yanace saini aidole inyita hakuri kafin yasamu sabon jini kuma ni awatsani kwandon shara

Labila tasomayimata dariya sundade suna fira sannan yayi masu saida safe yashirya cikin kayan barcinsa masu taushi yahau gadon addua yayi masu sannan yakwanta yajawota jikinsa yakura mata ido kamar maitunanin wani abun daga bisani yasaki murmushi yasunbaceta  saman kananun labbanta sannan yajata jikinsa barci maidadi yadaukeshi

Lubabatu tanaganin karfe Tara nadare yayi tayi shigar ta kamardai almajirah tahau motarta zuwa kasuwar nesa da kasuwar ta aje motarta tataka dakafa zuwa wajen tayi sa akuwa maidoyar tatashi dadan karenta taje Wanda zata tona koda akwai zafi wajen

Babu mutane wajen duk anwatse tawuce kamar tana Neman wani Abu daidai wajen mai doyar ta duke taduba babu mai kallontaa wajen kuma akwai ragowar wuta

Tajaye garwasun tayi gina tajefa layar tamiyarda toka tarufe tajawo gawayi maiwuta tazuba tamike"" takarkabe jikinta tawuce saida tayi nisa tatsaya taga kodawani bakowa awajen tasakai takoma wajenda ta aje motarta tashiga tatada mota tawuce gida ranta fariii tasss hankalinta kwance bayan tagama abunda zatayi takwanta""

Makale yake da itah kamar Wanda yaji ance za arabasu cen cikin barcinsa yaji kaamar dakinne yakecida wuta

Al amarinda yafaru da khadija. Kenan kusan tare suka farka kowanne yaja gefe sukahau kallon kallo"" Usman yamurza idonsa ahankali yasake kallonta yace waibakida lafiyane???

Tayimasa duban rashin fahimta  tace mekaganie dad??? Yace jikinkine yayi zafi rau kamar wutaa hannu tasa tashafo jikinta bataji komaiba tace nima naji zafin Amman banyi tunanin jikina bane"" yace shikenan  tashi yayi yasake kara gudun ac sannan yacemata sukwanta

Sake kwantawa tayi yasa hannu yajawota daniyar tamatso jikinsa zafin dayaji yanzu tamkar anwatsamasa ruwan tafasasshiyar dalmace hakan khadija ma tajiii Amman dukkaninsu gefe sukah koma suna jefar juna da kallo"""

Usman yadade zaune sannan yajuya nesa da itah yakwanta yana mamakin wannan suracin dayakeji yana fesowa jikin khadija haryanzu baidaina jin zafinba dolensa yamike babu shiri yakoma falo

Yanafita yajishi wasai yasaukarda ajiyar zuciya yana kwantawa saman kujera barci yayi awongaba dashi

Bayan fitarsa khadija tadago tabishi da kallo aranta tana mamakin wannan lamarin barcin ma saiya kauracewa idonta ganin kamar tunani zaidameta tamike tadauro alwala tatada sallah

Saida asuba tafita falon daga nesa tatsaya tatadashi sannan tajuya dakin bayan tagama sallah saman abar sallar barci yakwasheta bayan tagama azkar

Sauri takeyi danyau tadan makara bata tashi dawuriba"""bayan tagama hada kayan kokon tabawa yarta tace taje tadorah kafin tazo tace to sannan tadau itacen dakomai tawuce

Dayake banisa daga gidan zuwa kasuwar tanazuwa tazube kayan tashirya itacen  tahurah wutaa"" tadorah dahuwar ruwanda za adama koko""

Usman yana kusa da khadija tanabarciii yakuramata ido yana nazarinta firgigit tatashi daga itah harshi kusan taresuka mike

Usman yarasa inda zaisa kansa dasauri yajuyaa yabar dakin Amman baiji sassauciba dole yafita gidan yanatafiya dasauriii

Saida yayi tafiya mainisa yadainajin komai ajikinsa bakin wata bishiya yazauna yadafe Kansa yanamaida numfashi

Bangaren khadija ma saida Usman yabargidan tadainajin zafiii ajikinta""" natsuwa tana dawomata tasoma furta innalillahi wa inna ilaihir rajiun

Harkusan azahar batasake ganin Usman ba"" shikuma yanacen dazaran yatunkaro gidan saiyajie kamar anasake huromasa zafii atakaicedai wani hotel Yakama nesa dagidanda khadija take
Harzuwa yanzu bakin Khadija baidaina addua ba"""

Al amarin mai doya kuwa tunda yarta tadorah koko hartasiyar Amman badukaba tadorah doya harkusan marece hajiyar jiya batazoba gashiyau tayi dayawa kumayau bakasuwa"" kawai saita saukartà tallen suya tajaye wutaa tadauko wuka tahau Gina kasa

Saida tayi Gina maidàñ zurfiii saiga layu sunyi jajirr sunata fesarda wutaa"" aikuwa tacirosu tawatsar tadibo ruwa jikinta yanarawà zaninta kamar zaifadiii tawatsawa layarnan sannan tacewa karamin danta yayiwa layar fitsarii







Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 87
       By
Gentle Lady💃🏽



Mutane sunfara taruwa sunaganin ikon Allah matar tafashe dakuka tace haba nikam nace tunda naga yauba wani ciniki Nasan nasamu wani dan bakinciki wanda yake hassadata yakaini wajen boka😩

Kaibawa ana bakincikin  agakana samu saiwani yayimaka munakisarda karasa komai adawo daya to aniyarku tabiku insha Allah babu abunda zaisameni

Wani dayake gefenta yace asabe lafiya??? Tace inafa lafiya malam mudi jiyajiya daga ganin masu mota sunfara hwakawa   wajena anamun gosulo shine wani Dan banza irin tsiya yakaini wajen wani matsafiii tanuna masa layar tace tunda nadorah kokon safe naga yaunayi kwantai jikina yayi sanyi dama nasaba tona murhuna kafin nahasa wuta yauma tsautsayine ganin mun makara saina turo "" batula ashedai darabon inga wannan Bakar ranar to Allah yafiku inazaune lafiya daku Ashe akwai wadanda sukejin haushina nibanajin haushin kudinda kowa yakesamu Amman yan wadanda nakesamu inciyarda Yayana sune suka tsolemaku ido""

Mutumen yace kiyi hakuri bani ruwa ruwa tadibomasa yayi addua yawatsawa Layun saiga wani hayaki baki kirin yatashii sama"" nan take sailayun suka kama dawuta  asabe tabuga salati tace kaganiko malam mudi wato so akayi talauciii yakashemu dani da yayana saitasake fashewa dakuka""

Saida layun suka kone kurmus tokar tabi iska "" malam mudi yace tayi hakuri komai ya war ware tayita masa godiya tace ainasan kaf kasuwarnan babu Maisona da arziki Saikai"" Allah yabar Kauna nagode yankasuwar sukaita mata jaje tace wlh inakallon kowa duk Wanda baizo yayimun jajeba shine tsohon munafukin"" ina kallace dakowa kai yinin ranardai akarasa gane kan"" asabe kowayayi mata yarmagana waccema batakai takawoba saitahayeshi da masifa

Hmmm bakutam bayeni meyasa har asabe tasan dakwai laya akasan madafin doyartaba"" asabe babbar macece kuma yarkasuwa maineman nakanta ammanfa akwai masifa batashiri dakowa idanhar ba sana arta akazo siyaba"" tanada wata Kawa jummala dukkansu mazansu sunmutu sunbarsu da marayun yayansu asabe yayanta shida biyar duk matane dayane kawai namiji karamie

Jummala Kuwa yayanta bakwai biyar mata biyu maza dayane mailafiyar dayakuwa bashida lafiya komai sai anyimasa ankwantar atayar sunkullah"" abota da asabe tunsuna yammata harsukai aure dasukafara sana a bayan rasuwar mazajensu shine sukezuwa saran doya wajen wata bayeraba

Idan sunsiyar sumiyarmata dakudi Sukarbi wata"" anahaka watarana dataje siyen doya maman cinedu take tambayarta wai ina jummala sati biyu batazo karban doyaba kuma bata kawomata kudintaba

Asabe tace jummalar??? Maman chinedu tace itafa tazo saubiyu takarbii doya bakudi gashi Nima inadau kotane Dan Allah kishemata takawomun kudina asabe tace Amman da mamaki nimadayake nadan kwana biyu bamuhadu da itah ba Amman bazatarike maki kudiba haka kurum baridai nabiya gidanta injiko lafiya sukai sallama damai doyar tadauki doya tatari Dan adaidaita tafadamasa unguwarda zaikaitaa

Bakin kofar gidan yasauketa tabashi kudinsa sannan tashiga gidan tanakwada sallama yayan jummala sunaganinta sukahau gaisheta dayake gidan ba bakonta bane"" tawuce uwardaka jummala tanaganinta tasaki fara a tace  maman batulace yau agidanmu shigomana

Ta aje doyarta tashiga dakin suka gaisa takirah yarta zulai tace takawowa mamanta ruwa tace to bayan tadibo ruwan tabata tashaa"" tayi Hamdala tanakallonta tace dagawajen maidoya nake tace satinki biyu bakije daukan doyaba kuma baki kaimata kudintaba meyafaru jummala kinsanfa matarnan abunda takemana babuwanda zaimanashi kiituna bashifa takebamu kuma idanbamuda kudi tasake karamana

Nifa aganina kodan uwanka bazaiyimaka hakaba wannan zamanin da akeciki"" jummala tace hakane wlh asabe harkunyar zuwanake wajenta bansan yazance mataba kaddarorine idan sun tunkareka bakada maganie sai abunda Allah yayi

Asabe kinsaidai akofar gidana nake tuyar doyar nan wlh kullum saina siyar har ana nema watarana kuwa baifi natashi daguda biyuba saina bawa wani kare dayake zama kusa danie kusan kullum saiyazo idan yakwatanci nakusa tashi

Kinsan komai marayunda suke gabana dan Adam sai addua keni asabe naga takaina wai Ashe wannan cinikinda nakeyi wata tahademun yawu

Tana bakincikina Allah yarufamun asiri dani dayarana babu Wanda yajini akofar wani gidan ina yarmurya ataimakamun natashi nanemi nakaina Amman kuma anajin haushina

Kedai bar mahassada watarana nadorah tallen suyana harnagama wlh asabe ko kuda babu Wanda yazoma kusadani gashi nasoye doya Amman babuwanda yasiya ke ingajarce maki labari karenda nakebaiwa doya koshi bairabo inda nakeba inazaune natasa doya gaba inkalli gabas inkalli yamma inazaune hardare sauro yayita cizona harkarfe goma shadaya dole nakwashe kaya nakoma gida ganin kafa tadauke.

Tace kinga wajen nan tanunawa asabe dayatsa tace umm nagani inajinki jummala wlh harkinsa jikina yasaki tace hmm kedai bari wlh nan nadorah bokitin doya nayi zaune inata rusar kuka"" 

Yayana dasukaga haka suma sukaita kuka akarasa Wanda zai rarrashi wanie asabe doyarma kasa cinta mukai kafin safe ta Lalace dole nawanketa tacire kwan nashanya

Nasake komawa wajen maman chinedu nakarbo wata nabata hakuri"nace kudinne basu haduba dazaran nasiyar zanhadomata kudin nakawo mata tadauko doya tabanie

Nazo nasake daura talle wlh asabe abunda yafaru jiyan shiyakuma faruwa wannan karonkam banyi kukaba nabawa yarana doyar mukaci muka kwanta washe gari muka karya da itah sauran nashanya

Najikunyar komawa wajenta sainayi tunanin kodai sungaji da doyarne nazo nakwashi yan kayana dawadanda nafarayiwa zulai cikon aure najinginar dasu Na auno wake nayi awara ke dai bantsiraba danjarin yabalgace

Tsawon satii danaga yunwa tanashirin halakamu dani da yarana shine naje kauyenmu kozansamo hatsi wajen Yayana shine yake tambayata nafadamasa yanda sana ar takini

Saiyace yanaganin jiface akaimun Amman inbari yafadawa wani abokinsa malamine illaikuwa anafadamasa yace asirine yana nan tsakiyar inda naketoya doya

Jikina yanarawa nace Allah gafarta malam kataimakeni yanda Allah yataimakeka wlh marayune dani yace inkwantarda hankalina

Inkoma inyi Gina wajenda nake tuyar doyar komai nasamu indauko inkawomasa yabani wani kyalle yace insako ciiki

Ai inadawowa nadau abun Gina nazowajen nagina saikuwa gatarin layu nakwashesu akyallen aibankwanaba asabe nakoma

Nakaimasa gabana yakarye asirin yace dagayanzu inzan hurah wuta indinga tonawa kafin nadorah ranar nadawo gida damarece inada sauran doya biyu nadafa nafita garka ai infadamaki har layi akamun

Jiya jiya naje nakaimasa sadaka nayi godiya Yayana yabanie kudi dayardar Allah an jima zankaimata kudinta nakarbo doya

Nasamu jarima dagayanzu babashi zankarbaba
Asabe tace kaicho Allah yashiga tsakaninmu da mahassa jummala tace ameeen

Asabe tace Amman yafadamaki wacce taimaki wannan danyen aikin??? Tagirgiza kai baifadaba yacedai inbarta  da Allah aishi baya fallasawa  domin wacce tamun shakikiyatace dab muke da itah Kuma munakusa dakusa nikuma atunanina nakasa gane kowacece

Saidai najabaya keduniya ke duniya duk abunda kakeyi saikasamu Wanda yake hassadarka yanzu kiduba kiganie dabara nakezuwa da anfara zundena anacewa dakarfina nakoma maula Amman kuma banje kofar gidan kowaba natsaya narufawa kaina asiri Allah yarufamun Amman nasamu wata tanason tonamun asiri

Aini yanzu mutane tsoro sukebanie"" asabe tace ainima kinsa jikina yayi sanyi kicenima indinga tona murhuna kafin nadorah suyar doya Allah dai yashiga tsakaninmu da mahassada jummala tace Ameen sundade sunafirah sannan asabe tatafi tokunji dalilinta wannan yasa kullum sai tatone murhunta kafin tadorah koko wannan layarda taganie bakin gaskiyarta asirine akaimata"" wannan kenan

Bangaren khadija kuwa tunda taga Dare yayi Usman baidawoba tadawo harabar gidan tayi zaune tanata rusar kuka"" Usman yanacen harabar hotel din yakasa zaune yakasa tsaye yinicur amasallaci yayishi gashi dare yayi Dan anyi magrib Amman hankalinsa yanawajen Deejarh

Yasan dakyar idanma taci abinci kamardai yanda shidinma baiciba kawai yayanke shawarar komawa yafita yabi hanyar gidan saidai baiji komaiba haryakai kofar gidan yahangota duke dasaurinsa yakasara haryana hadawa dagudu Sam yamanta dazafin da yakeji idan ya tunkareta""

Tanajin motsin mutum tadago dasauri tana ganinsa tafada jikinsa tafashe dakuka maikarfii"" gabadaya usman ya susuce yana tambayarta lafiya Amman khadija kamar cewa yakeyi tasake kukan

Daukarta yayi kamar yarbebi yashiga falon gidan da itah"" saman kujerah ya ajeta yadago fuskarta ganin yanda idanuwanta sukayi sutu sutu yanuna alamun tadade tana kukan

Usman jiyayi duk yatsani kansa saiyadorah laifin akansa meyasa yatafi yabarta"" murya araunane yace please Deejarh Na kukan nan ya isa haka yayi maganar yanajanta jikinsa yasoma shafar bayanta ahankali alamar rarrashi
Shiru tayi tanajinsa Amman bata daina kukaba ahankali yace Dan Allah khadija kiyi shiru wlh harcikinraina nakejin kukan nan nakie







Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠



Chapter 88
        By
Gentle Lady💃🏽



Shiru tayi saidai tarika jan ajiyar zuciya akai akai""" cikinta yashafo yace Deejarh na kinci abinci??? Cikin dasasshiyar murya tace bazan iyah cin wani Abuba dad bayan katafii kabarni saitasake fashewa dakuka

Yace ya salam ya isha Deejarh wlh kukan nan nakie yanakashemun jiki kirjina sai harbawa yakeyi"" tace to inakaje dad kabarni nidaya anan bayankuma kasan bansan kowaba

Yasake kankameta tamatukar bashi tausayi yace banje ko inaba Deejarh Na ina masallaci inaimana addua"" kiyi hakuri kinji banason kinamun hasarar  hawayen nan nakie masu matukar tsada!

Tace nidai kayi mun alkawarin bazaka sake tafiya kabarniba"" yasake kankameta ajikinsa yace nayimaki alkawari Deejarh na bazansake tafiya nabarkiba""

Tace kayi alkawari??? Kaiyagyada ah nayi alkawari sake shigewa jikinsa tayi tace nagode dad"" ahankali yasoma Shafa kanta yace gashi anfara kirah barinaje sallah dagacen zansamo maki abunda zakici

Tagado dagajikinsa tace kaikumafa??? Idanunsa yalumshe yace nima zanci idan mai sanyi ta taci!" Murmushi khadija tayi tana lankwasa yatsunta nahannu tace shikenan

Yamike yadauro alwala haryanzu tana nan inda yabarta yace kitashi kiyi sallar tace to haryakai bakin kofa tace dad tsayawa yayi yajuyo yace yadai mai sanyita"" tace Dan Allah karkadade kadawo gareni🙊

Hannu tasaka tatoshe bakinta Dan itah kanta batasan sanda maganar tafito bakintaba"" murmushi yasakar mata lallausa yace angama deejarh na"" sainadawo yasakai yawuce

Khadija daki takoma dafada saman gado tana dariyar kanta gaskiya yakamata tacire kunya tanunawa mijinta tana sonshi kamar yanda yakesonta

Tunranarda tadorah ido akanshi taji kirjinta yanabugawa kullum cikin mafarkinsa take tomeyasa itakuma yanzun takasa nunamasa. Itadin tasace

Tashi tayi tarungume filo tana juyashi ahankali idanuwanta alumshe tace anya zan iyah zaicefa nayimasa rashin Kunya cikintane ya bada kuuuuuuuu alamar yunwa yakeji saiyanzu tashafo cikinta Wanda yasake lafewa damaya lafiyar kurah ballana antabota

Damacikin kamar marar tuwo yake saigashi Kuma yanajin yunwa saiyasake matsewa
Murmushi tasaki sannan tamike tayo alwala tatada sallah " bayan ta gama tasoma addu o inta kamardai yanda ta saba"tanaxaune saman abar sallar Usman yadawo da sallama fuskar nan tashi wasai sai murmushi yakeyi"" ta amsa masa sallamar kanta yana kasa kayan hannunsa ya aje yafita zuwa kitchen yadauko plate da cup dawani katon tire

Yadawo kusa da itah yazaune yatankashe kafafunsa yajawo daya ledar ya xube kajinda suke ciki manyan kajine anyimasu gashin injin sunsha albasa dakayan yajie saikamshi yake tashi

Ya yimasu pillah pillah sannan yacemata bisimillah""" ganin tanadan noke noke kumashi yasan yunwa takeji yace inazuwa

Wasu kopunan yadauko yazubamata tea zace tafara dashi danhanjinta su saki babu musu takarba tasha kuma taji dadin tea din bayan tashanye yasoma bata naman tanaci ahankali saida yatabbatar takoshi yabata lemu tasha sannan shima yasomacin ragowar

Kuru tayi tana kallonsa daya dagokai saisuhada ido susakarwa juna murmushi"" haryagama""" takwashe kayan"" yace tasamu tayi wanka tadauro alwala shima zaishiga dayan dakin "" kayansa yadauka yakoma dakinda yake kusada nata shimadai ciki da falone da toilet kayan ciki kawaine suka banbanta"" kayansa yacire danshikanshi kyankyamin jikinsa yake tunsafe hardare jikinsa baigaruwaba saina alwala

Yadade yana wanke jikinsa kamar Wanda yakeson sauya fata"" sannan yadauro alwala yafito yasharce sumar kansa" yagoge ruwan jikinsa"" maiyashafa wani maisanyin dadi yasaka kayan barcinsa masu kauri da taushi kaman auduga"""yafeshe jikinsa  da turare sannan yafita yasameta zaune tana jiranshi"" abar sallar yagyara yashiga gaba yace tataso suyi sallah

Bayansa tatsaya yatada sallah raka o"i biyu sukai kamardai yanda akeyi bayan sungama yadafa kanta yayi addu a sannan yasoma tambayarta akan wankan tsarki duk dayasan tasanie haka tayimasa bayanie dalla dallah duk tambayarda yayimata tabashi amsarta daganan yamike yaja hannunta suka koma saman gadon suka zauna hijab din jikinta yacire yace Deejarh abarsaka wannan abun idan inakusa please

Batacemasa komaiba yana kallonta. Yace wai bakizoda kayan barcibane?? Muryanta tanadan rawa tace banice nahada kayanba sahibace" baice komaiba yamike yajawo akwatin Wanda haryanzu ba ashirya kayanda suke cikinsaba jerin kayan barci daban yakasosu duka yanadubawa khadija tana kallo duk wacce yadaga saita waro idonta saboda kaf rigunan barcinda labila tasako babu ta mutunci injifa khadija saida yagama ganin kayan duka sannan yadauko mata wata Riga "" rigar milk ce maiturii hade take da bes saidan karamin pant dinta

Aituni khadija tahade wasu yawu saida yamiyarda kayan duka sannan yabata yace tasaka tsuru tayi kanta yanakasa"" shidimma itah yake kallo""

Zaiyi magana tace kunya nakeji dad toka rufe idonka" murmushi yasaki aransa  yace inada aiki kuwa yajuya yafita falo Yakoma yazauna akan kujerah

Kayanjikinta tacire tasakasu"" wata kunya takamata tamatse jikinta dahannunta tace wannan kayan kunyar ina zankaishi tararumo hijab tasaka

Tana nan tsaye bakin madubin Usman yashigo yarufe kofa tsayinsa yayi yajingina kansa jikin kofar yarungume hannuwa yana kallonta

Ahankali tadago danganin shirun yayi yawa""" sukai ido hudu yace wannan hijabin kumafa banacemaki kidaina sakashi idan muna tareba

Gabadaya jikin khadija yamutu bayanda ta iyah idonta yanarufe tajaye hijab din daga jikinta""" masha Allah kalmarda Tafara fitowa bakin Usman kenan

Ido yakuramata kamar maisabuwar makanta"" saiyaji bakon al amari atattare dashi Wanda baitabajin irinshiba ahankali yatako zuwa inda take kirjinta yanasake harbawa saboda tsoro

Fuskarta yatallafo da hannunsa yana kallonta da idanuwansa dasuka soma rikida daga farare zuwa ja yasoma shakar kamshin jikinta jikinsa harrawa yakeyi dagashi har khadija kafafuwansu kasa daukarsu sukayi

Sukazube kasa wannan cedamarda Usman yasamu yasoma sunbatartà"kirjinsa yana harbawa dasauri khadija kuka tasomayi ahankalie

Yatsaya da abunda yakeyi yana kallonta murya dausashe yace Deejarh kitaimakeni wlh zan iyah mutuwa idanhar bankusa"" bakinsa tarufe dahannunta tabude idanunta  dasuke tsiyayarda hawaye daga gefe tace dad karka roki abunda yake mallakinka

Nibazan hanakaba kadakuma kukana yahanaka abunda kayiniya""" gashin kanta yashafa yace zan iyah hakurah inkauda kai dasauraren komai Amman banda kukanki

Tadanyi murmushi Duk da a tsorace take Amman babu yanda zatayi halak dinsane""" ahankali tajuya kanta gefe tanamai lumshe idonta daukarta yayi yadorah akan gadon sannan yakashe masu hasken dakin

Wannan Daren shine nafarkon darenda Usman zairubutashi acikin tarihin rayuwarsa "" Daren yakumshi abubuwa da dama Wanda babu Wanda zaisan sirrin dake cikin Daren face Usman dakuma khadija

Tunda Usman yake baitaba tsintar kansa cikin farincikiba sama da na darenyau jimayake tamkar bashidin bane waidama akwai ranarda hawayenda suke sauka akan fuskarsa zasudaina kwaranya

Ada mata bugu daya yayi masu Amman yanzu Deejarh nsa takaryata maganar zuciyarsa lallai ko acikin matan kowa dahalinsa Abu maikyau shine idan zakayi aure ka auri yargidan mutunci mai ilimin Islam

Usman harda kukan farinciki yayi awan nan Daren"" dare sukutun bairuntsaba"" hakazalika Deejarh nsa bata nuna masa gajiyawar taba

Karshe dankansa yabarta saboda tausayinda tabashi toilet yashiga wajen wanka yazauna yadarji kukansa kamar mace nidariyama yabanie😂😂😂

Bayan yafito yahadama khadija ruwa shiyataimaka mata tagasa jikinta yanadota a towel yagyara masu gadon sannan yashimfideta"

Janta yayi cikin jikinsa yanashafa kanta ahankali saida barci yadauketa sannan  yamike yasake dauro alwala yatada sallah domin nuna godiyarsa ga Allah dayabashi wannan tukuicin nahadashi da wacce zata soshi fiye dayanda yakesonta
Wacce zata dauki damuwarsa kamar tata ya Allah kabarni tareda Deejarh na ka mallakamun zuciyarta






Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 89
     By
Gentle Lady💃🏽




Bayan yagama yadaga hannu sama yadinga gwararo godiyarsa ga Allah madaukakin sarki yakirasa da sunayensa tsarkaka zazzabine maikarfi yasaukar masa

Saman abar sallar yadankwanta nantake yasoma rawar sanyi bashi kadaiba har khadija tashi yayi dakyar yakashe ac dayake cikin dakin yahau gado yaja bargo yarufesu babu jimawa wani nan nauyan barci yadaukeshi

Sai shida saurah yabude idonsa sunyimasa nauyi sosai tamkar banashiba""" dakyar ya iyah tashi zaune yakai dubansa wajenda khadija take yadaga hannunsa ahankali yashafo fuskarta tayi zafi rau dasauri yajaye hannunsa"" ahankali yasoma tashinta ganin harsun makara gashi har angama sallah

Itakanta jikinta yayimata nauyi"" yasauko dakyar yaje yadauro alwala haryafito yana dafe da kaiii yana saramasa kamar zaidare gida biyu khadija tana Zaune bakin gadon kafafuwanta akasa Amman takasa takasu "" yalura dahakan shikanshi gayanda yakejin jikinsa haka yatallafota haryakaita toilet din yasaukar da itah yadawo waje yatsaya saida tagama abunda zatayi tabude kofar tanajan kafarta ahankalie

Sake daukarta yayi yakaita saman gado yashimfida abar sallah sannan yadauko hijab dinta yasakamata"" yatada sallah bayan sungama sukai addua dayake khadija tahardace azkar datakeyi safe da yamma duk daciyonda takeji baihanata yinsuba

Bayan tagama tasake kwanciya saman dardumar barcii mainauyi yasake dauketa" koda Usman yajuyo hartayi barcii yasafo fuskarta cikin tausayawa aidole zazzabi yakamata irin juriyarda tayi jiya duk da karancin shekarunta"" dakyar yamike yasake daukarta yadorata akan dago wayarsa yadauko yakamo lambar wanda yakeda mallakin gidan yafadamashi yanason aturo mashi doctor mace bashida lafiya dashi da iyalinshi yayi masa sannu""

Bayan yakashe wayar yaga miscall din lubabatu kusan ashirin dabiyar yadanja tsakii yacillarda wayar yakoma yakwanta idanuwansa arufe Amman babarci yakeyiba shine kawai yasan abunda yakeji""

Yana nan kwance yasoma jin anayin knock din kofa yatashi dakyar damadai baicire jallabiyarsaba haka yaje yabude kofar gidan"" masu aikin hotel dinne tareda wata doctor baturiya suka gaisa yawuce gaba tana bayansa harsuka kai dakin

Taduba khadija tace bawani Matsala zazzabine kawai Kuma akwai bukatar ayimata Karin ruwa kodan taji karfin jikinta"" yace badamuwa shimadai bayajin dadi ahada dashi

Kudi yabata tasiyo allurai da maganie dakuma ruwanda za akara masu"" anan dakin akajona masu Karin ruwan acikin ruwan tasaka masu allurar barci kodan susake samun natsuwa babu jimawa sukai barci bataje ko inaba tana nan taredasu har ruwan datasaka suka kare khadija aka sake sakawa wasu shidai basai ansake sakamasa wasuba

Daya saura yafarfado Alhamdulillah yadanji karfin jikinsa yasamu yawatsa ruwa ma Sudan zafi yasha tea yayi sallah sannan yadawo dakinta doctor dintake tareda khadija

Tayimasa yajikin yace Alhamdulillah kudi yadibo masu yawa yabata yace tatafi idan ruwan sunkare shizaicire mata"" tace to tayita godiya sannan tatafi

Kusa da itah yazauna yazubamata ido bayako kiftawa sai murmushi yakeyi Wanda shikadai yasan ma anar murmushin""

Bayan ruwan sunkare yaciremata alokacin tafarka"" yataimaka mata tawatsa ruwa tayi sallah"" ma aikatan gidan yakirah suka karbomata abinci yabata saida tace takoshi sannan yamiyarda itah kan gadon shimà yakwanta

Yadora kanta akan kirjinsa yana Shafa lallausan gashin kantaa ahankali yasoma magana"" Deejarh ahankali ta amsa yace yajikin nakie" ahankali tace naji sauki yanisa Allah yakara saukii tace Ameen

Shirune yabiyo baya nayan dakiku sannan yamuskuta yace Deejarh na bansan wadanne irin kalmomi zanyi amfanie dasuba wajen godemaki akan ni imarda kika jiyardanie Daren jiya

Sauran kalamanda suka rage abakina bazasu isah ingodemakiba koda zantattaro dukkan dukiyarda namallaka aduniya nabakie nasan basukai Rabin darajar abunda kika mallaka munba "" banida abunda zanbaki Wanda zaizama tukuici aganina komai zanbaki kamar narage darajar abunda kikabanine

Babu abunda zaizama tukuicinki anan duniya danbanidashi saidai inroki Allah yayimaki sakayya dagidan aljanna nagode khadija nadade inajiran wannan ranar harnafitarda raii dasamunta


Saigashi Allah majirokon bawansa yasadanie dake alokacinda banyi tunaniba"" wasu hawayene sukasoma sauka akan kumatuñsà"""


Sunsoma sauka akan goshin khadija wacce itama kukan farinciki take Wanda Batasan lokacin fitarsuba

Jin hawayensa yasaka tadago dasauri tanamai goge nata hawayen takalleshi ahankali tafurta meyasa hakan dad??

Tayi maganar tana shafo ragowar hawayen fuskarsa wadanda basu karasa gangarowaba hannunta yarike yana kallon cikin idonta yasakar mata murmushi yace sanyi kikaji da hawayena kozafi??? Ahankali tace sanyi

Yasake murmusawa yasaki hannunta yasake kwantarda itah ajikinsa yace wannan kenuna hawayen farincikine danasameki

Yasake kiran sunanta akaro nabiyu ta amsa cen kasan makoshi"" yace kifadamun mekikeso arayuwarki inyimaki amatsayin tukuicin soyayyarki agareni"""

Hannuwansa tarungume tace kasonie"" !! Shine kawai abunda nake nema agareka"" yace indai wannan ne Deejarh na kinsamu hakan fiye dazatonki wlh Deejarh inaji ajikina tamkar banida wata wacce nataba so faceke "" zancigaba dasonki harkarshen rayuwata

Tashi yayi dasauri yana tada itah zaune yahada hannuwansa danata waje daya yace akwai abunda bakisani dangane damijinkiba bazan boyemaki komaiba na kasance namiji mai tsananin yawan bukata wannan dalilinne  yasaka nakeson kara aure saidai duk matarda na aurah karshe saita ha inceni

Nafiddarai dasamun matarda zata sharemun hawaye saikwatsam Allah yaturomun dake amatsayin hasken rayuwata yasake kankame hannuwanta hawayen idanunsa suka soma sauka dasauri dasauri yace  Dan Allah Deejarh karkema kigujeni saboda lalurarda nakeda itah

Nasan dole komai Daren dadewa zakigaji da yawan bukatata  bazan ga laifinkiba Amman karkiyi nesa danie"" Khadija duk da kunyarda takeji na maganganunsa baihanata dago fuska takalleshiba tace Allah karyataba nunamun ranarda zangaji dabukatarka

Aikin ladar zanyiwa gudu??? Danaga ranarda zakaso biyan bukatarka agareni inki wlh nafison inga ranar mutuwata"" bakinta yarufe yace meyasa zakifadi hakan??? Hannunsa tajaye daga bakinta tace saboda inciremaka shakku da kokonto ko  zan iyah bijirewa anan gaba

Duk lokacinda kake da bukatar nishadantuwa tokazo gareni nikuma zanzama rijiya maibaka ruwa akoda yaushe zanzame tamkar lambu maikumshe da daddadan kamshi dakuma furanni bazan taba gajiya wajen ganin nafaranta rankaba saboda inasonka

Tayi maganar tana mai turah fuskarta saman kirjinsa saboda kunya dayan hannunsa yasaka yasoma dagota Amman taki dagowa  dariya yasoma yimata"" yace kidago mana inga idonki dahar kika iyah boye kunyarki saibayanda kikagama magana zatadawo

Ninafison kunyar nan tatafi har abada dariya takama yimasa yahauyi mata chakulkuli itama tarama garin dariya tazame kasa saisuka fara mulmula akan gadon idan tayi kasa yadawo sama saitayi sama yadawo kasa kowannensu murmushine kwance akan fuskarsa

Dakagansu kasan sunacikin farinciki daga wasa akazarce gamai gabadaya""" sundade suna faranta ranjunansu"""


Hajiya lubabatu😂 Zaune dawaya ahannunta tunjiya take kiran wayar Usman yaki dagawa tasaka ranta watakil sunbabe yama yarda wayar Amman duk" dahaka batadaina kirah ba

Yini sukutum ajima a jima saitasake Kira Amman babu amsa"" wannan karonma wayar tasake kirah alokacin sungama jindadinsu barci maikumshe  da dadi ni ima yadaukesu wayar tasoma kara wayar ya lalabo yadanna yakara akunnensa maisanma wayeba kafin tayimagana yace roll number kawai yakashe  saita tasake Kira maimakoñ yadàuka saikawai yaja tsaki yakashe wayar gabadaya

Yasake rungume khadijarsa"" cen bangaren lubabatu hankalinta yatashi danba muryar Usman tajiba kardai abunda boka yabata yataba lafiyar Usman yayarda wayarsa wanie yatsinta Dan tabbas wannan bamuryar Usman dinta bace! Towaye🤔



Nikam nace komawaye oho😕

Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠




chapter 90
      By
Gentle Lady💃🏽





Ana kiran la asar yafarka""" yamike yareda addua""ya Murza idonsa sannan yatashi zaune "  ahankali yasoma tashin khadija itama tabude idonta tareda addua zaune tatashi jikinta yasakeyi mata tsamie usman yasauka yayi wanka sannan yadauro alwala yashirya cikin wata shadda ruwan antaa mai duhu masallaci yawuce lokacin khadija  itama tashiga bandakin tayi wanka tadauro alwala Sam tayi mamakin yanda barcin yadauketa

Bayan tafito tasharce ruwan sumarta tagoge jikinta simple makeup tayi tabude kayanta dazatasa tasaki tsaki lallaima labila yanzu kala uku kawai tasakomun manyan kaya suma acikinsu babu maizanie duk siket ne kuma kayan duk sun matseta gashi dad yahanata saka hijab

Haka tadauki kala daya tasaka"" tasa hijab tatada sallah"" bayan tagama tatsaya lazumie tana saman abar sallar Usman yadawo""" da sallama yashigo ta amsa sallamarsa "" kusa da itah yazauna yatankwashe kafarsa"" yana fuskantarta murmushine kwance akan fuskarsa Sam baya gajiya da kallon Deejarh""itama martanin murmushin tamiyar masa""" yana kallonta kasa kasa yace wannan kwalliyarfa ni akaiwa itah???

Tarausayarda kai sannan tadaga masa kaicikin jin kunya"" yace to inhakane yakamata acire wannan hijabin babu musu kuwa tacire""" yasoma kallonta  yana mai tasbihi dagodiya ga Allah daya zaba mashi Deejarh amatsayin matarsa

Hannunsa yasa yajawota jikinsa tayi matashi da kirjinsa shikuma yana wasa da yatsun hannunta ahankali tace dad wai sahiba bata kiraba??? Sai alokacinne ma yatuna kamarfa yakashe wayarsa"" dantsaki yaja yace inatunaninfa haka kuma nakashe wayata

Mikewa tayi tadauko wayar tadawo Tamika masa yabude wayar lambar lubabatu yakamo yasoma kiranta kamar akunnenta dasauri tadauka saitaji muryar Usman yana sallama

Tasaukarda ajiyar zuciya tace dafatar kana lafiya?? Yakalli khadija wacce itama shiitake kallo yace qalau nake yagidan


Tanisa lafiya tunjiyafa naketa Neman wayarka tanashiga Amman akaki dagawa duk hankalina yatashi nadauka kowani abunne yasameka

Yalumshe idonsa sannan yabude yace wlh wayar alokacin batakusa Dani hasalima  bansan inda nabartaba dazukuma banajin dadi harda Karin ruwa nasha

Lubabatu tahau sallal lamie tace kanwatafa?? Yasake kallon khadija yana murmushi yace ai adalilintane komai yafaru""

Wani farincikine ya lullube lubabatu batasan sanda tatashi saman kujerarba tasoma tikar rawa""" tace toyanzu yajikin naka ?? Yace naji sauki sosai

Tarausayarda kai Amman dadyn Abdul mezaihana kadawo gida nifa banaso kayi jinya garinda bakada kowa idan kana kusa dani hankalina yafi kwanciya

Yajawo khadija jikinsa yace karkidamu kanwarki zata iyah kuladanie sosai "" sauran kadan lubcy tafado akan kujerah adimauce  tace wacce kanwar tawa bayankuma"" saurin dafe bakinta tayi jinta na shirin yin katobara

Yace Deejarh mana"" kokinada wata bayan itah??? Tuni zufa yasoma yayyafowa ajikin lubabatu jinyace mata" yadai tayi saurin tattaro ragowar natsuwarta tace

Bakomai ina kanwar tawa kabata mugaisa haryanzu lubabatu bata gasgata zancenba saida taji muryan khadija tana ratsa dodon kunnenta"" tace mom inawuni lubabatu tasharce zufa tace lafiya qalau yagarin khadija tace alhamdulillah tayi saurin mikamasa wayar

Lubabatu tace kakularmun dakanwata barinadan duba Abu awuta kafin Usman yace to tuni lubcy tayanke kiran "" zufanda yake zuba ajikinta har tarara yakeyi tashiga rudanie sosai wannan wacce irin matace da maganie bayakamata???

Dasauri tamike tayi sama saiga ruwa sunazuba takasan zanenta ashewai fitsarine tasaki lokacinda taji muryan khadija""🙄

Dasauri tahau saman ta lalubo madubinta tashafa tareda kiran *hatsabibin boka* babu wani bata lokacii boka yabayyana

Jikin lubabatu yanarawa tace nashiga uku boka asirina yakusan tonuwa cikinta harwani kuka yake saboda firgichi tsawa yadakamata yace kinatsu kiyimun bayanie nibanason Dan Adam maisaurin karaya akan abunda yasa agabansa

Saurin karayarki tunfarko shiyasa aikinki baiyi tasiribà kisani nibanyarda darashin nasaraba banyarda da faduwaba kullum cingalaba akan aikina shine farko

Lubabatu tafashe dakuka tace Dan darajar tsafinka dakagada ga iyayenkà kataimakeni

Wlh komenene zankawo kaikoda jinin mutum ne muddin zansamu inkauda wannan annamimiyar yarinyàr wlh zanyii

*Hatsabibin boka* yatuntsure da dariya yanamai kyakyatawa daga bisanie yatsuke fuskarsa tamkar gwaggon biri yace kwantarda hankalinki bukatarki zatabiyaa

Amman akwai hadari sosai idan harzaki iyah"" tace mezaihana boka ai komai hatsariñshi zanyi inhar" zansamu biyan bukata yasake kecewa dawata hatsabibiyar dàriyà yace kayanki yatsinke abakin kaba

Hayyanul zarri yadawo duka bakaken aljanuna sunkasa rabarta ammanshi yanazuwa yace zai iyah

Sharadin da zakibi maiwahalar shi wannan aljanin bayashan jinin dabbobi saina bil adama lokacinda yamaki aiki akan samira dabokanta jiñinsu shiyazama làdar aikinsa

Koyanzun yayarda yashanye jinin kishiyarki Amman yace kafin nan dole abashi jinin jinjirin jariri Wanda akagama haihuwarsa ko dimin cikin uwarsa baigama fita daga jikinsaba""

Lubabatu tawaro ido tace nashiga uku"" inazan samu wannan jinjirin??? Aranta tayi maganar boka yasake tintsirewa da dariya yace zanbaki wadansu mangwaro guda uku dazaran kinga maiciki wacce kikasan takusa haihuwa saikibata shi kitabbatar taci ko kadanne""

Dazaran taci aikinki yagama bazatafi mintuna gomaba yaron cikinta zaisoma motsi zaice shifa waje yayi saboda mangwaronda yafada cikinta bazaikara mintuna talatin acikinba zaifito

Dazaran kan yaron yafito waje hayyanul zairi yana kusa da itah zaizuke jinin jikinsa koda yaron zaifado aduniya bashida rai"" kekuma dazaran kinbata mangwaron saikisan nayie karkuma kisake taganeki danzatayi tunanin mangwaronki shine yayi silar nakudarta""

Yawunei suka tsinke mata"" tace nagode da wannan taimakon yace saikuma sharadi nabiyu aljani hayyanul zairi bazaitaba iyah tunkarar taba muddin tayi azkar datakeyi dasafe nasha fadamaki  masu yawan addu a da sallah sunada matukar wahala aiki yakamasu..

Sannan yarki tanacen tana tayata da addua abunda zakiyi kigggauta samun dabararda zakiyi mijinki yadawo Kasar nan idankuma kinajin tsoron karya zargeki dawani Abu kijira nanda wadansu kwanaki dakammu zamu karkatoda rayuwarsa zuwa gida

Dazaran yadawo dole dakinki zai sauka"" saboda kwanakinda yayi batareda keba kinunamasa kema kinada bukatarsa

Yarki zamu turamata aljani saagakimu Wanda yake hurawa mutane iskan bakinsa take sihirtaccen barci yadaukesu wannan aljanin shine mukai amfani dashi wajen kishiyarki suwaiba yanata sakarmata barcii

Zaije kusa da itah dazaran yaji zatayi addua saiya hurah mata sihirtaccen iskan bakinsa take barci zai dauketa yana iyah sakata barci nawata biyar koma abunda yafi hakan

Dazaran mijinki yakwana dakinki lokacinda yakezuwa sallar asuba tareda ma aikatan gidan duka karkiyi barci dazaran sunfita kije kofar dakinta kisandai yanda zakiyi kafin tafara adduar kikirata cikin firgita  dazaran tafito aljanie hayyanul zairi zaidauketa dakinga hakan kiyi sauri kikoma benen kasa zakiji anbugeki saikifadi bazaki sake sanin komaiba  dawannan zaki Kore zargin kowa akanki

Shikuwa saiyafita da itah daga kasar gabadaya sannan yatsotse jininta yayarda gawarta"" zamu rubuta takarda mubarta akofar gidan mijinki yana dawowa""bakin gidan zaiga tashin mota saidai tabadeshi dakurah """   dakinta zamusa shaida atakarda zamuce mumuka saceta kuma bazamu dawo da itah ba duk rintsi karkima nuna waikinga mutanen kisandai karyarda zakiyi.

Yana kallonta yace Amman bansan mezai iyah faruwa da mijinkiba  saidai kekam aikinki yagama

Lubabatu  tayi shiru Abu biyune yatashi hankalinta jin za asakarwa labila barci saikuma abunda yashafi Usman kuma gashi idan boka yayimagana bazai sauyaba

Tacekai mezaisa indami kaina koma nezaifaru yafaru indai burina zaicika anan tayi sallama dabokan dacewar zatajirah harya karkatoda rayuwar Usman zuwagida

Sannan Adan sausautawa labila dazaran andauke khadija atasheta daga barcin"" maganar jinin jinjirin Kuwa abarkomai zatayiii yakasance ashirye ranarkuwa *hatsabibin boka* ya aikomata da mangwaron


Tundaga ranar lubabatu take ta yawon neman masuciki Amman duk wadanda tasani dagamai wata uku saibiyu harsu khadija sukai watadaya adubai batasamu mafitaba

Khadija da Usman kamar zasu hadiye Kansu saboda soyayya yazata itah tazama shi jiyakeyi tamkar yafasa kirjinsa yasakata aciki saboda soyàyya







Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 91
      By
Gentle Lady💃🏽



Zaune suke cikin falo tayi matashi dacinyarsa yana wasa dagashin kanta waizaiyi mata kitso itakuma sai wash takecewa

Harcikin jininsa yakejin yanayinta yakirah sunanta my heart tace na am hubbyna shiru yayi baice komaiba hakan yasa tamirgina tana kallonsa murmushi yakeyi tace au waidama dankawai kasani amsawane kakira sunana

Tamurguda baki takoma takwanta dariya yayi yace bakin nan nakie ya iyah tsokana sosai shiyasa idan nasameshi bana ragarmasa

Tadafe bakinta tace au ashefa harda mugunta kake hadamun lallai zansan yanda zanyi nasamu Abu maidaci nasaka abakina aidazaran kaji daci zaka cire bakinka

Takai karshen maganar tana tashi daga kan kafarsa tana dariya ido yakuramata aransa yace wai itah komai tayi sainaga takara kyau komai kyau yakemata

Ganin yakafeta da ido yana murmushi taturo baki kamar zatayi kuka subhanallah wani masifaffen kyau takara datayi hakan""" hannunta yajawo tamatso  kusa dashi hancinsu yana gugar juna suna kallon junansu yace koda kinsaka Abu abakinki

Inhar zanhada bakina dawadan nan kyawawan labban nakii danyatsansa yasaka yana zagayen karamin bakinta itakuma tanabinsa da kallo yacigaba babu abunda zanji bayan zakie Wanda yafi Zuma dakomai dakika sanie

Ya sassauto da muryarsa yace wlh Deejarh dazanwuni inkwana ina tsotsar wannan bazandamu da abinciba saboda dadinsa muah yasunbaci yan yatsunsa  kinga Kuwa komai yarabeshi zaizama sweet ne yakanne mata ido daya

Kanta takada tace bawanin nan sai idanhar ba dacin kalasaba aikomai da mazauninsa zaki danashi haka daci inamai tabbatar maka idan nashafa shuwaka a bakina hmmm kai ko abincima bana tunanin zakaci aranar tadaga masa girah tana dariya

Kuru yayi yana kallonta aransa yace wai idan narasaki yazanyi??? Yayi maganar yana buga uban tagumie Deejarh tatsaya da dariyarta ganin yanayinda yashiga tace meyafaru dad???

Tayi maganar tana jaye hannunsa daga taguminda yayi cikin yanayin damuwa yace wlh inaji ajikina kamar wani bakon al amari zaisameni

Yayi shiru daga bisanie yace inarokon Allah yasa komene zaifaru karyabiyo tawajenki banason narasaki idan narasaki wlh zan iya rasa rayuwata gabadaya

Jikin khadija yayi sanyi takwantarda muryarta tace haba masoyina annurin zuciyata kasani komai ruwa komai iska komai rintsi inataredakai bazantaba gudunkaba

Muddin ina nunfashi adoron kasa bana tunanin akwai wani Abu dazai nisantanie dakai kadaina saka damuwa Aranka Dan Allah

Wlh damuwarka daidai take darashin kafiyata nakwana arba in dazaran naganka adamuwa duka natsuwata nakan rasata kaima kasan inasonka indai tawajenane bazaka samu matsalaba tayi maganar tana riko hannunsa

Yace nasanda haka Deejarh Na nasan bazaki taba gudunaba Amman tabbass akwai abunda zaifaru Dan gabana yana tsananta bugawa akullum kamar lokacinda zanfara haduwa dake

Tuni idanuwanta suka kawo ruwa"" ido yaware yace kesarkin kuka wasafa nake waimakinsan me??? Batace komaiba kuma batadaina kukanba yace tunani kawai nake dazaran munkoma gida duk wannan soyayyarda kike nunamun zakibartaa

Harnadawo kalar tausayi yayi maganar yana turo baki kamar yanda takeyi aikuwa tasoma dariya gakuma hawaye sunazuba a isonta

Yace umm ansamu mugunta dole ayidariya waishinkam agarinku akeyin wannan??? Tace mefa??? Yace kuka da dariya alokaci daya mana abun mamaki🤔

Tace habadai yace mubar zancen wasa Dan Allah koda munkoma karkirika jaye jikinki danie kinjii"" yamarairaiçe fuska kamar zaiyi kuka

Tace toyazanyi kaima kasan inakunyàr mom sannan kuma sahiba haba nidamunkoma zanjaye jikina"" Usman yatsuke fuska yace wannan akekirah taleko takoma"🙁" to idan kikaihaka nikuma menene ribata wlh daredaya zakiji likita yace ciwo yakamani

1 Ciwon rashin jin dimin jikin Deejarh na

2 ciwon rashin tsotsar my sweet

3 ciwon rashin kwanciya taredake

4 ciwon soyayyarta da shakuwarta

Ke atakaicedai zaice maki jinina yahau Amman Na soyayya"" namakance Amman narashin ganinki kusadani nazama kurma rashinjin tsiwar nan takie
Ke intakaicemaki labari zaice zuciyata tabugaa adalilinki wayyo Usman yazama abun tausayi shiru yayi yana kallonta yanda take murmushi yace haryanzu baki sauya ra ayibane ???
.
Tarausayarda kai tace sauyi Sam"🙅🏻" inazankai kayan kunyar??? Yace kizubasu bayan dakinmu mana"" tosaidaifa  ayi yanda za ayi ko wlh agabansu inrungumeki insakiji kunta kinga daganan kunyar tafita
.
Tace uhum tanan zaka bullo tosaina daina fitowa sahiba tarika kaimun abincina dakie"" yace karkimun haka kinji wlh badawasa nake maganarba

Tace ainima badawasa nakeba mezaisa naguji mijina bayankuma yazama rayuwata yazama farincikina inhar zan iyah kauracewa numfashinda nake shaka akoda yaushe tozan kauracemaka

Kasa aranka duk sanda kakirah Deejarka acikin zuciyarka zatazo dagudu tarungumeka Tabaka kulawa "" shinko kataba sanin akwai wadansu zuciyoyi masu amsa amo taredajuna sukanyi shawara dajunansu hakazalika sukan amsa kiran junansu wadan nan zuciyoyin bawasu bane face zuciyata da taka

Dani dakai abudayane tanisa waikana tunanin zan iyah yinnesa dakaine""  kasabamun dajikinka nasaba dakwanciya asaman faffadan kirjinka bansan soyayyaba sai akanka kashayardani giyar sonka

Nashata sosai hartana Neman illatani muddin ka kauracemun  zan iyah rasa raina saikawai tafasheda kuka tofa wai anadara gadare yayi tuni Usman ya susuce sai sambatu yake saki menene yasaki kuka my heart wlh bazan taba iyah yinnesa dakeba bazantaba kaura cemakiba Dan Allah kidaina yimun hasarar hawayen nan nakie
Tashare hawayenta tace nasanda haka kawai ina tausayin kainane danasabarwa zuciya da soyayyarka wacce zata saka nashiga damuwa aduk sanda nawara ido bangankaba!!


Shiru tayi usman yagano maganarta toyazaiyi??? Inama khadija ce yafara aurah ba lubabatu ba dahar abada bazaitaba iyah yimata kishiyaba" ahankali yasoma rarrashinta yace koda yaushe kikaso ganina zankasance taredake har acikin barcin kima yayi maganar yana dago fuskarta yasoma kissing din bakinta rayuwa kenan soyayya tanada dadi aure maikumshe da rahama da nishadantuwa""" Allah yasada kowa da masoyinsa na gaskiya dankuwa duk matarda Takai mijinta wajen boka danyasota kodan karyamata kishiya kodan tajuyashi yanda takeso inaso tasani wlh karya take bata sonshi

Bawannan ake kirah soyayya ba" abunda ake kirah so kiso duk wani abunda mijinki yakeso farine ko bakine matukar dai abun baisabawa addiniba kuma baisabawa koyarwar *Annabi Muhammad  (S A W)* to tazama mai murna dahakan kaitamafi mijin jindadi wannan shine cikakkiyar soyayya



Tuni Usman yamantarda khadija bacinran datake ciki idan sunatare kowannensu mantawa yakeyi dakowa sunaji tamkar babu wadansu mutane aduniyarsu

Tamkar sune kawai suketa shawagi awata duniyar daban usman yana rikita khadija da zazzafar soyayyar shi " shikanshi baisan ya iyah soyayya irin hakaba saiyanzu

Ashedai komai lokacine dashi duk Wanda yake faranta maka bakasanin sanda sonsa da kaunarsa zaiyita linkawa azuciyarka""

Tuni khadija da Usman suka tsallake siradin masoya sunacen sunajin dadin rayuwarsu irinta ma aurata sosai yanzu khadija tasaba dayawan butakar Usman"" dama" cen batadamuwa kuma bata taba nunamasa batasoba kullum tayi sallah tana rokon Allah yasake bata juriya dakuma kokarin biyawa mijinta buktarsa  akullum bata mantawa dawannan acikin sujadarta takanyi tsayuwar dare tana rokon Allah karya nuna mata ranarda zata gajie

Cikin ikon Allah dakuma hikimarsa khadija Sam batajin gajiya kamarma karamata karfi akeyi Hakika duk abunda kasa Allah aciki baxaka tabeba hakazalika idan kasa abu aranka Inhar na alkhariine sai Allah yataimakeka wajen cika burinka








Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 92
       By
Gentle Lady💃🏽




Akwana atashi babu wuya khadija da Usman harsunyi wata biyu da sati uku bayan sunyi wata da sati biyu adubai daganan sukaje India sati daya sukawuce America sati biyu dagacen sukawuce kasa maitsarki satinsu daya sukadawo madina sukai sati khadija tayi ziyara tasha kukan farinciki bata taba tunanin zataganta kusa da kabarin fiyayyen halittaba Allah kenan maiyin yanda yaso dagacen suka dawo Dubai suka fara shirin dawowa gida


Al amarin sarauniya lubabatu kuwa tunda taga har anyi wata uku harda kwana biyu Usman baidawoba haka zalika duk tayi wayadashi bata taba nunamasa waiyadawo saitace yazauna abunsa yaci amarcinsa

Saibayan sungama wayar takama kuka haryanzu  ta gagara samun abunda akace takawo ganin wankin hula yanashirin kaita dare kawai tayanke shawarar ziyartar asibiti taje kasuwa tasiyo likaf da safar kafa"" dama tanada manyan riguna ma aikatan gidansu ta aika suka samo mata mangwaro gashi baijima da farawaba "" yana wuya shima dakyar yasamoshi

Washe gari tashirya tasaka kayanta Amman batasa nikaf dinba tafita cikin motarta saida takai asibitin tasaka nikaf din taxuba mangwaron da boka yabata ajaka Wanda aka. Dibomata ahannu tatusa raggaduda ajikinta tadawo tamkar maiciki dama tanada sarbano saicikin yataso"" sosai
Tafito tana turah ciki tatafi wajen da masu ciki suke zama idan sunzo awo matarda take wajen tafi mace Dari towazataba wakuma zata hanamawa

Mata dashegen kwadayi musamman masu ciki dazaran taga Abu saitace yawunta sunkawo tabbas inhar zata fitardashi awajen bashakka duk matanda suke wajen saisunci aikuwa za ayita haihuwa jikinta baiyarda tayi hakanba dankuwa asirinta zaitonu idan hakan tafaru ga mace sama da Dari alokaci daya

Tatari layi itace ta Dari da talatin"" zaune tayi waje daya"" tayi shiru matarda take kusa da itah sai zubarda yawu takeyi duk saitaji zuciyarta tana tashi mikewa tayi tabar wajen

Takoma cen bayan wani dakin Amman tahanyar masu zuwa awo cen bakin kofar shigowa tahango wata maiciki tafe tanadaga kafarta dakyar"" lubabatu tayi saurin Ciro mangwaronta tanasha Sam batakallon wajenda matar take kamarma batagantaba

Hartakawo inda take zatawuce saita dawo tace asslamu alaikum"" lubabatu wacce taturo ciki tace wa alaikumus  salam""

Matar tace Dan Allah baiwar Allah inbadamuwa mangwaron kinnan zakidan sammanie yawunane sukadan tsinke""  lubabatu tasaki fara a tace Allah sarki bakomai barinabaki dama biyune aka samomun tasa hannu ajaka tadauko mangwaron tabata""

Matar takarba"" tasoma sha"" tace Amman ba awo kikazoba naga kinzauna anan??? Lubabatu tace shinazo wlh mutane sunyi yawa sainadawo nan din Amman ke aikin makara bakizo dawuriba

Tace hmm wlh dakafa nakezuwa kuma akwai nisa daganan zuwa gidanda nake"" lubabatu tace ayya to ina maigidanki matar tace kedai bari tasamu kusa da lubabatu tazauna dakyar tace mijina bayason haihuwa

Tunsanda mukai aure Anty saiyana bani wani maganie inasha bansan nahana daukan cikibane sai ranar najishi dadare yanafadawa abokinsa dan nataba samun ciki saida yayi wata uku yazube  Ashe lokacinda banda lafiya allurarda akamun tazubarda cikine

Nikuma tundaga lokacin sainadaina shan maganin idan yabani saina kaikaici idonsa inwatsar dayalurah nasamu ciki duk da boyemasa danakeyi duk wahalarda cikin yakebanie aikuwa tunda yagano yace waibanida lafiya bariyakirah amun allurah nikam nace fafur lafiyata qalau dayanace saina nunamasa baxan yardaba kuma naji firarsa da abokinsa

Tundayago naji yace koda tsiya sai anzubar danshi baiyi shirin tara yaraba nayi kukan takaici da aurensa dama shine illar ka auri Wanda bakasan asalinshiba
..
Sanda yazo aurena iyayena basuyi wani bincike akansaba ganin yanada kudi kawai aka auramunshi "" gashi iyayena yan Cameroon ne acen ya auroni"" yakawoni nan banida kowa bansan kowaba"" tundaga lokacin yakwashe kayan abincinsa duka baya bani abinci duk da katon gidan da nakeciki saidai inje inyo bara asace inci abinci idankuma yakamani yace wai Zanzubar masa da mutunci yalakadamun shegen duka Amman banfasa zuwaba saboda bazan zauna yunwa takasheniba tuni yahana kowa shiga gidansama

Ganin bazan daina fitaba shine yasiyo garin kwaki kullum idan zaifita saiyabani gwangwani daya darabi hakanan bakomai haka zanjikashi inci"" saiya fara shigowa dayan matansa suna holewa matansa suna sakani dahuwar abinci tanan ne nakesamu inci maikyau watarana wasuma harkudi sukebani danyacemasu nidin Yar aikin gidansace

Dana lurah cikina ya isah zuwa awo shine nasoma aiki wani gida aboye inamasu wankakau anabiyana harnatara kudi yanzu inajiran kawai nahaihu natara kudin mota zankoma garinmu

Dama date din haihuwata Yakama likita yace dazaran nawuce sati banhaihuba indawo togashi harnakara sati biyu""

Lubabatu taji tausayinta sosai tace natausaya maki gaskiya hannu tasaka cikin jakarta tadibo kudi masu yawa tabata tace idan tasauka lafiya tayi hidimar biki dasu tanata godiya harda kukanta

Tatambayi sunanta tace Mariya"lubabatu tace kefa??? Maicikin tace saudatu""cikinta taji yafara motsawa tace Anty Mariya barinaga likitan zansameki Annanko "" lubabatu tace ah tatashi tanaturah ciki tawuce

Tana barin wajen lubabatu tamike tafita tashiga motarta tacire likaf tana saukarda ajiyar zuciya tatada motar ta cikin farinciki tawuce gida

Al amarin maiciki kuwa tana kaiwa cikin mutane ciwon Mara yataso mata taduke dasuka lurah haihuwace suka dauketa aka Kaita wani dakin akakirah wadansu likitoci kunsan likitoci akwai dagawa kowacce akakirah saita ce akwai abunda zatayi

Matarda taje Kiran likitocin harda kukanta"" dakyar tasamu wata kiristan tace sutafi koda sukazo saudatu harta gama fita hayyacinta gakan danda yafito Amman barai dantuni aljanin yazuke jininsa

Tanazuwa tajawoshi saigawani yakunno kai koda tasoma jawoshi daransa kafin yafito babu rai ko kuka baiyiba itakuma tuni tasuma aljanin yanaganin haka yabace yana mai murna dawan nan jininda yasamu

Matarda takirah likitar tayita kuka tana tsinewa likitocin ba ita kadaiba duk matanda sukewajen laifin likitocin sukaganie aidasunzo dawuri dayaran basu hawalaba harsuka kaida mutuwa

Abunda basu saniba kowa bayawuce kwanansa Hakika hakane Amman dangane da wulakancinda likitoci sukeyiwa marasa lafiya bakarya bane barinma likitoci mata wlh masu imani acikinsu kalilanne

Kumawai musulmai dankuwa MASudan tausayin zakasamu kiristanne Yar uwa Norse shinbakisan ladarda zaki samuba idan kika taimakawa Yar uwarki tasauka lafiya

Karki manta"" biyanki akeyi ga albashi ga ladakuma Abu biyu zakisamu Amman saikuga mace tazo haihuwa wlh wasu har Marin mata sukeyi waisuncika raki tasan bazata iya haihuwaba meyasa tayi aure sanda takejin dadinta damijinta meyasa bata tuna wannan ranarba

Kosuhau yimata  fada waitadamesu da kuka ninan shaidace akan wulakancin likitoci mata waikina tunanin Allah bazai kamakibane??? Koke aganinki bakomai bane wannan mezaihana idan akakawo marar lafiya kirika kwantarmasa da hankali

Dagashi harmai jinyarsa kirika fadamasu magana maidadi saikiga kowa yanasonki kobayan ranki wlh zakisamu kyakkyawan yabo zakuji anacewa Allah sarki ai wlh doctor wance mutuniyar arzikice tayikaza tayi kaza Allah daiyajikantà Amman idankedin mugunyacefa kina tunanin Wanda kikayiwa rashin kyautawa danbaida lafiya idan yaji labarin mutuwarki zainema maki gafarar Allah

Bazainemà makiba wlh"" sannan kisani wannan abunda kikai sai anyiwa zuri arki kodakuwa kin mutune acikin yayanda kikabari ko jikoki keharkema bakiwuce hakan tasamekiba tundakema kina rashin lafiya kuma kina haihuwa

Rokona agareku likitoci kusan irin yanda zaku kyautata alakardu da majinyatanku"" kodakedin ba likita bace Amman kinasaran zamowa anan gaba saiki sanyanda zaki kyautata alakarki

Allah yasa masuhakan zasu gyara wadanda basayi kuma Allah yasake sakamasu imani da tausayin marasa lafiya dankuwa duk Wanda kaga bashida lafiya shikawai yasan abunda yakeji aransa idankayiwa Wanda yake gangar ajali rashin mutunci yazakaji idan akacemaka ai majin yacin nan yamutu Allah yakyauta

Saudatu bayan tafarfado akanuna mata gawar yayanta tayi kuka hartagodewa Allah tadangana tasan damacen sudin bamasu tsawon raibane tadauki yaranta koda tafito duk masu ciki sungama awo suntafi tace Allah sarki Anty Mariya watakil tayi nemana bata ganniba kuma gashi bansan unguwarda takeba

Datakoma gida mijinta yaga gawar yayan yayita kuka Allah yadauki son yayan yasakamasa azuciyarsa sanadin hakan yakamu daciwon zuciya

Itakuma tace yasaketa garinsu zatakoma yayita bata hakuri yace wlh yanzun yanason Yaya Allah yadoramasa son Yayansa dukda basa raye  harkasa yaduka yana Neman yafiyarta tokunsan tsakanin mata damiji sai Allah tayafemasa Amman tace saiyaje an aunashi Idan bayada cutar HIV batareda musuba yaje tareda itah ma sukaje aka tabbatar bayada cutar komai sannan sukacigaba dazamansu cikin soda kauna kamar yahadiyeta yakeji""" sai rokon Allah yake Allah yasake bashi kyautar yan biyu


Al amarin lubabatu Kuwa tatafi datunanin wannan saudatu din ganin tunanin baida amfani kawai tawatsardashi takama harkokin gabanta

Ranar Usman yakirata yace gasunan zasu taso"" tasa akashirya masu abinci na musamman koda suka sauka bayan isha"i taturah habu driver yaje daukarsu

Sunyi kyau sunyi kiba Usman harwani sheki yakeyi alamun yaji dadin amarci rayuwarsa tayi kyau tunda lubabatu taganshi wani bakin kishi yataso mata baki sake takebinsu dakallo saiga kuka yakwace mata

Shikuma Usman daukarsa kukan murnane dasauri yasake hannun khadija yatafi yarungume matarsa yana saukarda ajiyar xuciya ahankali yasoma shafan bayanta murya cikin kuka tace nayi missing dinka sosai mijina"" cikin zakuwa shima yace nima wlh nayi missing dinki matata kullum cikin tunaninki nake

Khadija tuni tasadda kanta kasa wasu hawaye masu zafi suka sauko mata ganin idan tatsaya tacigaba da sauraren ma auratan kukanta zai iyah fitowa hakan yasa taja kafarta dakyar tahau na urarda zata sadata bangarenta tadauko mabudin bangaren tabude tashiga bangaren duk yayi kurah Amman batadamuba tashige dakin saman gadonta tafada tasoma darzar kuka marar dalili😭😭😭😭






Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 93
        By
Gentle Lady💃🏽




Ah kuka marar dalili mana tunda batada ikon hanashi kusantar matarsa kamar dai yanda itama matar bazata hanashi zuwa gunda takeba

Aranta tace waidama haka akejin kishi??? Lallai najinjinawa mom danamijin kokarinda tayi harta iyah barwa dad ni tabarmana kwanakinta bayankuma tasan abunda zamu aikata abunda tayin nan koni bazan iyah ba gaskiya.

Gashi daga zuwanmu harnaji daban"" Allah kasamani hakuri acikin zuciyata indinga kauda kaina akansu"" Usman kuwa Sam baisan khadija tabar gurinba sai liliyar matarsa yakeyi"" sundade tsaye sannan taja hannunsa sai alokacin yaduba baiga khadijaba

Aransa Sam baiji dadiba kaitsaye bangarensa suka nufa tahadamasa ruwan wanka koda yafito harta fitomasa dakayan dazaisaka bayan yasaka kayan ya simpida abar sallah yarama sallarda take kansa

Bayan yagama lubabatu tace suje yaci abinci tasan yakwaso yunwa tana makale da hannunsa suka sauko kasa haryazauna yamike

Takalleshi inakuma zakaje"" murmushi yasakarmata yace badadewa zanyiba zanduba Deejarh nane baijirah jin mezata ceba. Yasakai yawuce
Tabishi dakallon takaici kamar tature duka abincin takeji kodayake bakomai aidaga yaune yarinya ""

Koda yakarasa dakinta harkurya yashiga yana karkabe kurah tana kwance saman gado tanajin sallamarsa tayi saurin goge hawayenta tatashi zaune ta amsa sallamar tana kirkiro murmushi tace waiharkayi wanka

Murmushin shima yake yana jefenta dawani kallo kusa da itah yazauna yajuyo fuskarta tanoke kanta yace hmmn kuka kikayiko???

Tace ah ah banyi kukabafa??? Saiga hawaye sunzubo sharrrrr yalakuto hawayen dadan yatsansa yace wannan shine shaidar bakiyi kukanba"" shiru tayi yace saunawa nake fadamaki hawayen nan naki tsadane dasu meyasa kikeyimun asararsu

Cikin dasasshiyar murya tace kayi hakuri bazan sakeba yanzumna nakasa tsaida kukanne"" yace tomezaisa  dole saikinyi kuka

Ahankali tadago takalleshi da idanuwanta wadanda sukacika da hawaye tace nikaina narasa dalilinda yakesani kuka

Abudaya kawai nasani nakanji kukan yazo batareda natarbeshiba takai karshen maganar hawayen suna zubowa. Yajata jikinsa ya isah haka Deejarh Na nafuskanceki insha Allah zankiyaye

Tasake lafewa jikinsa tana saukarda ajiyar zuciya bayan wasu lokutta yace tashi inhadamaki ruwa kiyi wanka kingafa ko sallah bakiyiba muje muci abincin nasan cikin nan naki yanajin yunwa

Noke kanta tayi tace kaje kawai innagama zansauko kar mom taga kadade"" yace kinga kitashi konadaukeki dakaina naimaki wankan dasauri tamike tace yihakuri towel tadauka tashiga bandaki shikuma saman gadon yadan kwanta yana kallon silin tunaninsa daya yazaiyi da kishin da yalura khadijansa tanadashi akansa

Sam bayaso yaganta cikin damuwa  kuma hakan bashizaisa yadaina kula matarsaba danma yasamu lubabatun maihakurice"" yana kwance hartafito tashirya doguwar Riga tazura bawata doguwar kwalliya tayiba"" tatada sallah saida tagama sannan yariko hannunta suka sauko
.
Lubabatu tunda suka Dade ranta yasake bacii" tadawo cikin falon tazauna takunna kallo"" kamshin turaren khadijane yadawo da hankalinta inda suke saurin kawarda kanta tayi"" kusa da itah yazauna yace rankiyadade inafatardai banyi laifiba "" murmushi tasaki tace wanne laifi kuma kaida matarka kamardai amarcin haryanzu bai ishekaba

Kunya ce takama Usman yadan Sosa kai yana kallon khadija kasa kasa"" itakuwa idonta yana kasa tunda sukazo wajen"" yace bahaka bane maman Abdul"" tace tomene idan amarcin bai ishekaba ashirye nake danasake sadaukar maku da kwanakina harsaikun gajie

Aran Usman yace indai zakibiyemu bazamu taba gajiyaba Amman azahiri murmushi yayi yace ah ah aiwan nan makadai mungode kohakan kikatsaya dolene najinjina maki yariko hannunta muje kibamu abinci nitundaxu hadiyar yawu kawai nake

Yaja hannunta suka wuce khadija tabisu abaya kamar kazarda kwai yafashewa aciki"saman dinner suka zauna sune gefe dagefe sunsaka Usman atsakiya"" lubabatu tazuba masu abincin sukasoma ci tanagefe tana kallonsu

Khadija kam saiyawo take da tsokali acikin plate takasa cin komai"" Usman ya dibo nasa yanufaci bakinta dashi tadago fuska takalleshi murmushi yasakar mata "" yalumshe idanuwansa yabude  alamar taci itama tamiyar masa damartanin murmushinsa takarba Sam tamanta da lubabatu tana wajen

Rayuwarsu ta Dubai kawai take tunowa ganin hakan yasa lubabatu mikewa takoma falo tacigaba dakallonta dankarta kalli kayan takaici

Amman acendinma takasan ido take satar kallonsu"" yayita bata tanaci itama tadauko tasoma bashi idan tayi masa babbar loma yakasa hadiyewa takamayi masa dariya

Sosai sun shagaltu sun mantama dawata lubabatu saida suka koshi yagogemata bakinta sannan yaja hannunta suka koma cikin falon suna zaunawa wayarsa tahau ringing yadauko yaduba yana murmushi yamikawa khadija

Ganin ansa Yayana takalleshi saikuma tadauka tareda murmushi"" daya bangaren akace amincin Allah yatabbata agareki Kanwata"" tadaga ido takalli Usman shima itah yake kallo tace taredakai Yayana""

Yace yakike ya gidan Yakuma gajiyar tafiya nasan bakujima dasaukaba da mamaki tace waidama kasan bama NaN??? Yace sosaima aimuna waya da dady tabata fuska kai ya muktar Amman shine kokace abanie mugaisa

Yace kwantarda hankalinki ainakusa dawowa abunda yasaka bance abakiba banason shegen surutun nan naki zaki iyah share mijinki kiyitamun zuba damadai konakirah Dan inji lafiyarkine Kuma dad yafadamun  qalau kike saime kuma

Tarausayarda kai tace Amman duk dahaka banji dadiba saina fadawa sahibata"" yace rufanie kisayani bazan iyah da itah ba "" tahauyimasa dariya sundade sunafirah sannan tabawa Usman suka gaisa bayan sungama wayar tace dad kakiramun sahiba inata zuba ido munyi da itah zamu sameta anan Amman bangantaba

Yace gawayar nan ahannunki nantake gaban lubabatu yabada rasss khadija takamo lanbar tayita kirah akace ba network karshe tahakurah dole tabashi wayarsa

Yace yadai batashiga tace ah taredajan  karamin tsaki"" mikewa tayi tace mom saida safe"" lubabatu tace harzaki kwanta??? Tayi hamma wlh nagajie mom zaman jirgi badadi"" tace shikenan Allah yatashemu lafiya tace Ameen batareda takalli inda Usman yakeba tawuce abunta

Yakalli lubabatu yace bari narakata indawo kai kawai tagyada masa yamike yabita abaya"" taresuka shiga Na urarda zata sadasu hawa nahudu

Suna kaiwa yasunkuceta zuwa dakin "" saisaman gadon yadireta saman jikinta yakwanta rabinsa yanasaman gadon kallon juna sukeyi ido cikin ido "" daga bisani yahade bakinsu waje daya yana tsotsa ahankali cikin kwarewa

Sundade ahakan ganin yanashirin wuce gona da iri tamirgina gefe"" tanamiyarda   nunfashi kamar yanda shima yayi idanuwansa harsun soma rikida ahankali yasake mirginowa zaisake hada bakinshi danata tasa gefen hannunta takare

Cikin kasalallar murya yace menene haka my heart??? Takwantarda idanunta tace basaina fada makaba kasan yau dole zaka kwana wajen mom ne baidace ka aikata abunda kakeson aikatawaba

Katuna yanzun bani kadai bace kaje wajen mom nasan zakasamu abunda kakeso acen itama tanada bukatarka"" tunda tafara maganar yake kallon Dan karamin bakinta hartagama"" yace bazanyi maki komaiba Deejarh kibarni nayi wasa dake"" kafin tabude baki tayi magana haryasake hade bakinsu waje daya"" babu yanda zatayi itama tacigaba damiyar masa da martanie dakyar ya iyah raba jikinsa danata yamike yacemata saida safe batace masa komaiba haryafita tabishi da kallo tareda zartowar hawayenta saman kumatu tashi tayi tarufe kofa"" takoma tazauna tayita darzar kuka harbarci yadauketa


Usman yana fita baisamu lubcy falon kasaba kaitsaye dakinsa yawuce yasameta kwance saman makeken gadonsa tayi daidai idanuwanta alumshe tamkar maibarci

To dama khadija ta takulomasa sha awa  ganin lubabatu kawai saiya kashe wutar dakin"" toilet yashiga yasake watsa ruwa yayi shirin kwanciya yakwanta ranarma sosai lubcy tanuna mashi tayi missing dinsa bayan sungama raya dare barci yadaukesu

Da asuba bayan Usman yayi wanka yayi shirin zuwa masallaci lubcy batayarda takoma barciba yanafita dakin khadija yanufa yasamu kofarta akulle yayita bugamata cen cikin barci taji tace natashi"" yasakai yafita yatada sauran ma aikatan gidan suka wuce masallaci

Saida lubabatu taji Tsit alamar kowa yawuce sannan tasadado bangaren khadija takwala mata Kira khadija innalilahi wa inna ilaihir rajiun shikenan labila tatafi tabarni khadija tun lokacinda Usman yake tashinta bata tashiba

Jin ance labila tatafi tabarmu ahirgice tasauko daga kandagon tabude kofa tace mom meyasamu Sahib""batagama rufe bakintaba kawai taji kamar anshafeta nantake tasulale kasa saikuma yasunkuceta batttt yabace

Lubabatu tana ganin hakan tasauka kasa dasauri tanasauka saitaji anbuga kanta dagini nantake tafadi kanta yasoma fitarda jinie

Koda akagama sallah Usman yaji gabansa yana faduwa yaubaima tsaya haske yafitowa kawai yataso yana kawowa yahangi mota tabar kofar gidansa atsiyace dasauri yakarasa kofar gidan tareda daidaikun ma aikatan gidan dasuke taredashi dankwalin khadija yafara ganie dasauri yadauka cikin mamaki yana kallon gidan dagudunsa yayi hanyar gidan

 Habune yaga""Farar takardar kofar gidan yayi saurin dauka 
 yabudeta rubutunda sukejikinta layi dayane darabi mune muka sace matarka kuma kasheta zamuyi karka wahalda kanka wajen nemanta!

Usman yanashiga gidan ahirgice yaga lubabatu kwance cikin jinie kawai rayuwarsa tayardar masa Deejarh sa aka dauke take yayanke jiki yafadi daidai shigowarsu habu da sauran ma aikatan gidan bayan habu yasanardasu abunda takardar takumsa







Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 94
        By
Gentle Lady💃🏽




Dasauri suka karasa inda yake habu ne yacewa muhd taimakamun da ruwa Dan Allah dasaurinsa yadibo  ruwan yamika masa ya yayyafawa Usman Amman komotsi baiyiba"" aka yayyafawa lubabatu tana farka takwamtsa ihu nashiga uku zaku kasheni"" habu yace kwantarda hankalin hajiya aimune sai lokacin tabude idonta

Idanuwanta tasaukar akan Usman Wanda ko motsi bayaya dashi dagawa duk daya dasauri  tamike tayi wajensa tace mesuka masa?? Kufadamun mesuka masa""

Habu yace bakomai muje asiviti muhd ne yadauko mota suka taimaka akasa Usman cikin Mota sai asiviti"" likito wajen biyar suka rufa kansa Amman ko motsi baiyiba""

Take hankalin lubabatu yasake tashi tarasa inama zata sanya ranta taji sanyi karfa aljanun *hatsabibin boka* sun tsotse masa jinie Amman aiba hakan mukai dashiba

Ganin harrana tayi daya saura bawani haske kawai habu yakirah hajiya yasanarda itah tace itama tana asiviti labila ce batada lafiya Amman  tafarfado yanzun hankalinta atashe tace ayimaza azodashi kano khalifa teaching hospital tanajiransu Zata sanarda doctor dinsa

Amman basu fadamata musabbabin abunda yasameshiba""" sunsanarda doctor zasu daukeshi zuwa kano akabasu sallama suka kama hanya har kano

Koda suka shiga sunsamu hajiya bakin kofa takasa zama anaganin su akazoda gadon Daukar mara lafiya akaturashi zuwa dakin taimakon gaggawa

 Duk iya kokarinda zasuyi wajen ganin yafargado abun yafaskara abunda yayi matukar basu mamaki gashidai baya nunfashi Amman zuciyarshi harbawa take dasauri  dasauri


Al amarin aljanie hayyanul zairi kuwa kwananshi daya dayini daya yana gudu asararin samaniya harzuwa lokacin khadija bata farfado daga doguwar sumarda tayiba sakamakon bangazarta dayayi

Baisake sa a guda yana guduba khadija tafarfado ahankali tabude idonta Kalmar dabakinta yasoma ambata kalu innalillahi wa Inna ilaihirrajiun

Saiyanzu take tuno abunda yafaru ahankali tasoma kallon wani bakon al amari kamar anagudu da itah acikin iska bakinta ne yasoma Karanto a uzubikalimatil lahi tammat min sharrima halaka""

Aljanie hayyanul zairi baisan Khadija tafarka daga doguwar sumaba radadin da yasomaji akirginsa tamkar ya chachumo wuta ahannunsa sune suka ankarardashi

Kafin yayi aune tuni sun lankawo daga sararin samaniya zuwa kasa kafin sukawo tunie khadija iskan dake tashi sama yasake sumarda itah

Saurah baifi sa o i susauka kasaba akayi wuffff akatare khadija tafada hannun wata farar mata maicike da kwarjini sannu ahankali tasaukarda itah kasa yayi daidai da farkawar khadija

Ganinta awata duniyar daban yasaka tafara jadabaya daga zaune wata iskace mai karfiii sukaga tatunkarosu bayan tagama saukowa saiga aljanie hayyanul zairi yabayyana cikin siffar jemage

Wani irin wargajine girmansa zaikai tsayin daki fadinsa ma haka""" faratansa manyane masu dauke damanyan kumbuna

Bakinsa dauke yake da zakwazakwan hakorah masu matukar  tsinie ko wanne daya tsininshi yakai tsinin mashii  kaurinshi kuma kamar kaurin takobie

Idanuwansa kadai abun tsorone "" idan yayi huciii wutace take tartso abakinsaa

Daganin wannan halittar wani mugun tsoro  yakama khadija hantar cikinta takada tunda take ko acikin fina finai bata tabayin arba dawata halitta maigirma dakuma firgitarwa irin wannan ba """ Amman wannan karamar aljannar

Datake gabansa kamar bera yatsaya agaban kurah Sam bata tsorata daganinsaba""" wata kururuwa yayi wacce tasaka khadija shedewar kunnnuwanta na dakiku arba in

Tsawarsa daidai take da tartsatsin wuta gaba daya dajin kansa saida yasauya launi sakamakon wannan karar yayi girgiza saigashi yasake zama wanie katon basamude"""

Kallon kallon sukafarayi da aljannar daga bisanie yabude bakinsa Cikin nuna isah dakuma takama yace yake wannan aljannar kisanie wannan kalacina ne kigaggauta barin wajen nan tunkafin fushina yasauka akanki

Cikin murmushi tace kai awa kuma kaiwanene dazanbaka itah"" inabaka shawarar Kayi saurin barin wajen nan tunkafin raina yakaiga bacii

Dariya yafashe da itah yace ke kinsan kodawa kike magana??? Tace bandamu dasanin kokai waye bane Amman nasan zaluncine zaka aikata kuma ni naharamta hakan acikin yankina

Wata kuru ruwa"" yayi yace yanadakyau yarinya kisan kodawa zakija kafin kifara fada! Nasan kaf duniyar nan babu wani aljaninda baisanda zaman"" jajirtaccen matsafi kuma gawurtacce Wanda yafi kowa sanin sirrukan sihiri wato *hatsabibin boka* wannan dakike ganie aikinsace kuma nine akabaiwa itah jininta amatsayin ladar aikina""

Aljannar tasakeyin murmushi akaro nabiyu tace bandamu dakaiba hakazalika fadar sunan bakin azzalumin shugabanka bazai tayarmun da hankaliba inamai baka shawara ka gaggauta barin wajen nan

Aljani hayyanul zairii yayi wani huciii saiga wutaa tayi tartsatsi dasauri wannan aljannar tasa hannu takare dazaran wutar tataba hannunta saikaga tamutu tamkar acikin ruwa take
Wannan yasake fusatashi yataso mata kamar zaicinye namanta danye take itama tayi girgiza saigashi tarikida takoma katuwar kada mai tsananin girma dakuma bantsoro

Hakoranta manya manya faratanta kamar fartanya kaifinsu da tsininsu yakai kaifin takobiii take itah ma tasoma kururuwa tayi girgiza     saisuka fara kallon kallo dagabisani suka rugo dagudu nantake kura tatashi sama bakako ganin gabanka jikake kafff sukahade waje daya  karar hadewarsu kaisaikace dutse da dutsene sukahadu


Hmmm wai ance fada inba ruwanka dadin kallo zamuga yanda fadan aljanu zaikaya shin ko aljani hayyanul zairi zaiyi nasarar kashe wannan aljanar yatafi da itah??? Kokuwa wannan aljanarce zataci galaba akansa??? Waishinma itah wannan aljannar wacece??? Ya al amarin Usman Wanda yasuma haryanzu bai farfadoba??? Shin labila tafarka daga barcin da aljani saaagakimu yasakata??? Duka amsoshin wadan nan tambayoyin suna cikin cigaban labarin saiku kasance taredanie


Kuyi hakuri banda chaji wannan kawai kukasamu







Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 95
      By
Gentle Lady💃🏽





Tunie Khadija taja baya tana kallon ikon Allah"" sun dade suna murkususu sannan sukasake jabaya kowannensu yana hucii

Abun yabawa hayyanul zairi haushi  taya wannan tatsitsiyar zata hanashi abunda yayi niya bakaken aljanu ma shakkarsa sukeyi ballantana wannan dabaiwuce  yayimata lakuma dayaba""

Bari kawai kafin wankin hula yakaishi dare yanuna mata ruwa ba sa an kwandobane" " aikogaba da gabanta"" take yayi kukan kurah yadauke kadan sama"  yasoma wujijjigata"" karshe yawurgar da itah tafada saman wata bushiya take bushiyar takarye saiga aljanar tadawo cikin suffarta tafarko bakinta da hancinta duk yana yoyarda Jini kamar mayanka"" tayi matukar galabaitaa


Aljani. Hayyanul zairi ya kyalkyace dawata mugunyar dariya yace bake bace banda abinki mezaikaiki fada dawanda kikasan yafi karfinki??? Tunfarko dakinbani itah cikin lalama dahakan baisamekiba"" bari kiganie agaban idonki zanshanye mata jinie idan ma bakiyi wasaba kema zanhada dake inkashe tunda kikayi kokarin jadanie

Yana kai karshen maganar yasake kecewa dawata hatsabibiyar dariya yatasamma gurinda khadija tace tuni khadija tasoma jada baya gabadaya tsoro yahanata yin addua Batasan wanne irin tashin hankali take cikiba

Aljanar nan tanadago kai taga bakin aljanin baifi Saurah kamu hudu ya isah wajen khadija ba "" dakyar tabude baki tace ya Allah"" tareda mikewa dakyar tarikede izuwa wani katon basamuden namiji tanarike dawani babban takobi mai matukar tsini dakaifiii cikin guguwa tawuce fuuuuu saigashi ta isah gaban khadija

Hayyanul zairi yakalleta da mamaki danbaiyi  zaton rauninda yayimataba zatasake tashi kafin yagama mamakinsa muryanta takatsemasa tunani tace kaibakin azzalumi mushuriki kasani Allah bazaitaba baka sa a akainaba bazaka taba shanjinin wannan bil adamarba saboda yafi karfinka

Akaro nabiyu inabaka shawarar kagaggauta barin wajen nan idankuma kaki lahira tayi babban bako"" hayyanul zairi ya kyalkyace da dariya jin abunda tafada yana nunata da yatsa yace "" kenan Yar fitsitsiya harkin isah kitsoratani da alamu kingajie da duniyar toyanzu kuwa zanturaki inda ba zaki dawoba take shima yayi girgiza Yakoma wani katon sadauki jikinsa daddaure da kayan yaki kowanne damtsensa daya yakai kaurin cinyar babban mutum

Gurayen jikinsama kadai kaganie saika firgita dogone sosai"" tsayinsa zaiyi kamu ashirin tuni wannan aljanar takoma tamkar kiyashe agabansa kwatakwata tsayinta iyah kaurinsa tatsaya

Khadija tamatukar firgita daganin yanda yakoma lallai dakyarne idan wannan aljanar zatayi galaba akansa""  wannan aljanar bakinta tabude tasoma hura masa iskaa mai matukar karfiii amman ko gyangyadawa baiyiba""

Takobin dayake hannunta tadaga iyah karfinta tabuga masa akaurinsa"" abun mamaki jitayi yayi kara kamar ajikin dutse tabugashi take takobin yakarye yazube akasaa""

Hayyanul zairi yana tsaye kikam yarike kunkuminsa yana kallonta""" saibayan data gama abunda takeyi""" yadaga kafarsa daya yataketa gabadaya fadin kafarsa bakako ganinta saimotsi take shikuma yacigaba da busar dariyarsa

Dakyar tadaga jikinta taciro wata karamar wuka tasoka masa atafin kafarsa taredakiran sunan Allah tuni wukar tahudashi zafinda yajine akasan kafarsa yasa yadaina dariyar dayake yakwalla kara yadage kafarsa wacce takemasa zugi dakyar ya iyah fincike wukar yayar jinin jikinsa yadinga zuba akasa take kasa tasoma zurmawa

Duk inda jininsa yadiga yashige cikin kasa saikawai kaga bakin maciji yakunno kai yafito yatasamma wannan aljanar tuni itama tajawo takobinta

Tasoma fillemasu kai Amman Abun mamaki duk Wanda tafilleewa kai maimakon yamutu saikuga wasu kawunan sunsake tartsowa ajikinsa

Tuni macizan suka kewayeta""" ganin hakan yasa itama tayi kururuwa tatofarda yawunta akasa  yinhakan keda wuya saiga wata katuwar mesa tatsago  kasa tafito wata irin shirgegiyace """ girmanta zaiyi girman kada babba bakinta yana feshin wutaa

Dagama fitowarta kawai tatasamma wadan nan macizan haka tayita lakumarsu tamkar tanacin cinnaku"" ganin haka yasa dai dagacikin macizan tasoma hadiyar yan uwanta tana kara girma saida tahadiyesu duka saigashi tadawo wata katuwar macijiya wacce taruba wannan  mesar sau biyu tsayi dakuma fadii takekuma suka soma fada tsakaninsu hayyanul zairi shima saiya tasoma wannan aljanar suka soma fada dazaran yadaga kafa zaitaketa saita goce itakuma takaimasa Sara duk da ko alama bayajin saran""

Sun sake shafe sa o"I biyar suna wannan fadan haryanzu aljani hayyanul zairi baici nasaran sake takar taba"" bakinciki yasake turnukeshi  yayi matukar fusata take yakwantsa ihuuu yasoma huro iska tabakinsa tuni iskannan yadauke wannan aljanar dakuma macijiya tareda wannan katuwar mesar yasomayin hajujuwa dasu sama khadija kanta inda Allah yataimaketa tanakusa dawani katon icce

Shitakama tarike kam tanata rusar kuka tunda take banda cikin film bata taba ganin bala i irin wannan ba"" kananun bishiyoyi tuni suka soma fincikowa daga kasa sunayin sama komai nadajin yahargitse wannan aljanar tuntanayin kokari dantasauko harta kasa anyi wajen mintuna goma suna shawagi Asama sannan yazubodasu kasa ragafff take wannan mesar dakuma maciji suka mutu ko shurawa basuyiba"""

Itakanta wannan aljannar dakyar take iyah daga yatsanta batako ganie daidai "" bayan sa"a guda komai Yakoma daidai sannan aljani hayyanul zairi yatako zuwa gaban aljanar da babban Dan yatsansa yasaka yaturata tamirgina tadawo daidai fuskarta tana kallon sama

Yakyalkyace da dariya yasoma yiwa kansa kirari kamar haka"" saini Aljanie hayyanul zairi dangidan kabusa"" fada"dani bala ine mai shirin gaba dagaba Dani saiyashirya "" yaro aikona goye yasan kura saini na *hatsabibin boka* uban hatsabibai duk Wanda yajadakai sunansa matacce asoka kaki mutum mutum yakiga yakwana kiyama"" saini angon mirqiyanatu"" uban sakafilu"" maidakawa maza gunba" faduwar gaba kotsoro badai gareniba da inja baya gayaki kara namutu danni bazan barwa Yayana abun fadaba!"   karyarki yarinya bakaken aljanuma sunbuga sunbarni ballantaana ke"" yanagama wannan surutun yajuya wajenda khadija take

Tanaganin haka tasake kankame wannan bishiyar tana kuka" girgiza yasakeyi saigashi Yakoma katon jemage mai fukafuki yasaki fiffikensa yasoma tashi daniyar yasunkuce khadija yayi sama da itah

Amman kafin yakai gareta saiyaga tabacewa ganinsa wata iskace maikarfii yaji tasha gabansa lokacin yajuya da mamakin inda gawar wannan aljanar take baiga komaiba""

Ashe lokacinda yakoma jemagen nan wannan aljanar ta farfado ganin yakusa dauke khadija saitazama iska tabi ta karkashinsa tasunkuci khadija tabace acikin iskar

Saigasu wani katon gidaa maicike dakayan more rayuwa tsakiyar  falon aljanar tasauka ahankali ta aje khadija itakuma tafadi gefe tana nisawa dakyar bakinta da hancinta suna zubarda jinie"""

khadija kam tun lokacinda wañnan aljanin yasoma tunkarota takankame bishiya tana kuka tasadakar mutuwa zatayi saikawai taji ansureta anyisama saiyanzu tadaji an ajeta kamar asaman kafet sannan tabude idonta

Tasoma kallon falon har tasaukarda idonta akan wannan aljanar dasauri takarasa wajenta tadago kanta tadora akan cinyarta tana kuka ganin abunda yasami wacce ta taimaketa

Aljanar tasakar mata lallausan murmushi Wanda dadukkan alamu nakarfin haline tabude baki ahankali tace karkiyi kuka Allah yanatare dake babu Wanda zaicutardake Amman rayuwarki tanacikin hatsari


Tasoma tari Cikin kuka khadija tace kaina yakulle wlh inane nan??? Meyakawoni nan?? Ina mijina??? Kuma ke wacece??? Waye wannan aljanin dakukai fada dashi??? Kumani menaimasa dayakeson kasheni??? Kifadamun yazanyi nakoma gida??


Wannan aljanar tamurmusa tace babu lokacinda zansamu damar amsamaki tambayoyinki kirike tambayoyinki harnadawo tasakeyin  tari yajimin ciwo ajikina dole naje nayijinya kafin raunin yacigaba datafiya ajikina
Kizauna nan harnadawo karkisake kifita kofàr gidan nan









Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 96
        By
Gentle Lady💃🏽




khadija tace ina nibazan zauna ananba"" wajen mijina zantafi " aljanar tasake murmusawa tace  kiyi hakuri Amman fita dajin nan agareki babban hatsarine

Wannan gidan dakike ganie gidanane kuma shine kawai adokar dajin nan babu wani matsafi ko aljani dazaiganshi ko abunda yake cikinsa

Wannan aljanin bazaitaba tafiyaba inhar baisha jininkiba kuma yasan bakibar dajin nanba danyanajin kamshin jininkin Amman bayaganinki"""


Muddin kikafita gidan nan kasheki zaiyi danbazai bar dajin nan ba"""  duk abunda kikaji karkisake kifita kiduba ko ina agidan nan duk abunda kike nema zakisamu  inafatar zaki ji shawarata nabarki cikin amincin Allah tanakaiwa nan tazama hayaki tatashi sama khadija tadaga kai tana kallonta haryanzu data daina kukaba"" harsaida tadaina ganin hayakin taja jikinta kusa dakujerar datake falon tasake barkewa dasabon kuka


Al amarin aljani hayyanul zairi kuwa    lokacinda yanemi khadija tareda wannan aljanar yarasa sai hankalinsa yatashi   yasoma dube dube gashidai yanajin kanshin jininta Amman baya ganinta hakan yasa yasoma sunsunar kasa yanabin saitinda yakejiyo kamshinta yayita tafiya  yana sunsune haryadaina jin kamshinta dole yadawo baya indayakejin kamshin nata yaja yatsaya saikuma yafashe dakuka tareda kururuwa aikuwa khadija tamike afirgice Dan kamar agabanta yake haka takeji

Tuni tasheka tabude wani dakin tafada ciki kai dakin yahadu iyah haduwa Amman tashin hankalinda khadija take ciki baisa talura da haduwarsaba ""

 Saman makeken gadonda taganie cikin dakin tafada cikin tsoro"""  Dan itah gidan kansa tsoron sa takeyi gatagama yarda dazamansaba ""


Aljani hayyanul zairi kuwa yadauke wajen sa o"i goma yana kuka """kukanda yakeyi bawai na wahala bane kukan bakincikine ai abun kunyane agareshi ace wannan karamar aljanar tahanashi Khadija hakan na nuna kenan taci galaba akansa?// dakarfi yace ina wlh karyane ba ataba bashi aiki yakasaba saboda banda yake aljani kuma shima matsafine bayan haka kuma majiyi karfine sadauki yanzu kwatakwata shekaransa Dari biyar aduniya"" kaf aljanunda *hatsabibin boka* yakedasu shine babba bawai agirman shekaruba saboda hazakarsa dakuma kwazonsa babu wani aikinda yake gagararsa duk inda akaturashi babu makawa saiyayi nasaraa dajin  Iraqi da *hatsabibin boka* yaturashin yaje yayi fada damugayen namun jeji masucin naman aljanu dakuma bil Adama yakarkashe su yadawo cikin nasara shiyasa *hatsabibin boka* yake jidashi duk cikin dakarun aljanunsa""


Tayama zaikoma wajen shugabansa "" toyace me idan haryafadi ainahin abunda yafaru bashakka girmansa zaifadi kuma zaijawa Yayansa dakuma matarsa abunfada Wanda zaiyita yawo aduniyar aljanu harnabaya susamu abunfadi ga zuri arsa

Damadai aikinda akabashi yadauketa kuma yacika aiki jininta ladarr aikinsace yasan duk inda taboye acikin jejin dole tafito kokuma yunwa takasheta gabanza""

Kawai zai zagaye dajin da mugayen tsafaffin namun jeji dazaran tafito sugama da itah shikuma yatsotse jininta yabasu gangar jikinta zaicewa boka yagama aiki yasandai bazaiyi bincike akan hakaba tunda yayarda dashi dawan nan shawarar yayarda"" yayi busaa saiga manyan namun jeji sunata yawo awajen kuraye zakuna damisa bauna giwa "" dadai sauran namun jeji masu firgitarwa

Dakuma cutarwa"" sannan yazama iska yatashi sama yabace cikin gajimare"" lokacinda yayi wannan tsapin khadija tasomajin kukan kuraye dana namun jeje hankalinta yasake tashi tasoma kiran sunan Usman tana kuka maimatukar ban tausayi


*Kano*
Hospital dinda aka kwantarda Usman tareda labila wacce tasoma farfadowa tasake komawa barci likitoci atunaninsu barcin arzikine takeyi Amman basu saniba barcin ciwone domin zaizama cutarwa arayuwarta

Yau kwanan Usman biyu kenan dasuma Amman ko alamar farfadowa baiyiba duk wani taimakonda yakamata suyimasa sunyi amman sunkasa nasarar farfado dashi
Sun yanke shawarar dayakai gobe baifarfadoba saidai afitardashi waje


Lubabatu tunda taga halinda usman yashiga dakuma yarta labila sai hankalinta yakara tashi lallai yazama dole ta nemi boka aibahakan tace ayiba"""

Suna zagayeda Usman har hajiya damasu aiki sunyi. zugum zugum lokacinda khadija tasoma kiran sunansa saiga Usman yasoma motsa Dan yatsansa"" kamar anturoshi  yatashi dakarfi yace khadeeja!!!!

Badai khadeeja na akadaukaba bazai yiyuba hajiyace tafashe dakuka tace badai hauka takamakaba babangida meyasamu khadijar??? Saiyanzu hajiya talurah da waima bada khadija akazoba

Habu ne yasheka dagudu yakirah likitoci dakyar aka rirrike Usman ganin yana nema yafi karfinsu yasa akaimasa allurar barcii

ahankali yake kiran sunan khadija harbarci yadaukeshi"" hajiya tana share hawaye takalli lubabatu wacce take sharar kwalla tace wai meyasamu khadijar???  lubabatu kam batace komaiba saidai tabita dakallo saida tasake tambaya habu yace suma wlh basu saniba sundawo masallaci kenan sukasamu"" wata bakar jeep tawuce kofar gidan atsiyace koda suka kawo saisukaga alhaji yadauki dankwali saikuma yaruga cikin gidan

Nikuma sainaga  takarda kasa"" nadauka nakaranta mukayi cikin gidan dasauri saimuka sami alhaji dahajia duk asome bamusan menene musabbabin sumarsaba
Hajiya tarabka salati tace tomeyasamuu Khadija???




Hakuri hakuri hakuri wlh banda chajiii fatan alkhairi agareku





Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 97
      By
Gentle Lady💃🏽




Hajiya tace aibaikamata kutaho dukaba sai asanarwa yan sanda habu yace nayi tunanin hakan kuma ai munbaro maigadi tareda maibawa fulayoyi ruwa da idi maiwankin mota"" duk da bagidan yake kwanaba nasan yanzu yasamu labari

Hajiya tace duk dahakan kukoma kusanarwa yan sanda dama anzo dawayar babangidan saina kira abokinsa dpo lubabatu tace suje kawai idan anfadawa yan sandan saita dauko wayarsu dakuma kaya Dan itah ko mayafi batatsaya daukaba

Hajiya tace shikenan Amman kidaina kukan nan haka insha Allah zasu samu sauki lubabatu tagyada kai"" da itah da muhd da habu driver suka dawo kaduna

Koda sukaje suka sanarwa yan sanda ashema har maidagi yatafi tun ranar yakai report  anyi nema har angaji Amman ba agansuba"" anyita sanarwa kafafen yada labarai dagacen gida suka wuce bayan lubabatu tasake jaddada masu asake tsaurara nemanta

Bayan sunkai gidan akabude masu get suka shiga"" habu yatsaya magana da ma aikatan gidan "" Tace su habu sujirata tafito kaitsaye tashiga gidan


Dasauri tahaye bangarenta  tajawo akwatin tadauko madubin tashafa tareda kiran *hatsabibin boka* shafawarta keda wuya saigashi yabayya asaman buzunsa

Lubabatu tayi shiru kanta yanakasa takasa cewa komai dominkuwa bataga idon wasaba Dan fuskarnan tashi murtuke take sanadin kuwa wannan karon saboda rudanie ko kayan aikinma bata turoba

Jin surun yayi  yawà yace idan bakida abuncewa meyasa kika kiramu alhalin muna cikin wani aikin??? Tace tuba nake uban hatsabibai inacikin tashin hankali dakuma rudanie

Mijina dakuma yata yaukwanansu biyu basa motsi kuma bahakan mukai dakaiba nidaikawai nace adauke khadija tomezaisa ataba Usman da yata???

Yace maganar yarki yanzun zata farka sauran sihirin barcinne baisaketaba mijinki kuwa dama saida nafadamaki bansan abunda zai iyah faruwaba bayan dauke matarsa

Tunfarko kinason mijinki bakyaso kirasashi meyasa kikace akashe kishiyarki??? Tace boka menene alakar kishiyata dakuma mijina

Yace soyayya"! Soyayyarda yakemata talinka wacce yayiwa matarsa tafarko danhaka kikaga yashiga wannan halin"""

           tace to boka mezaihana itah ma acireta dagacikin zuciyarsa"" yace abune maiwahala tamarairaice fuska ataimakamun boka banaso yarika tunawa da ita idankuwa harzaituna da itah kagakuwa babu amfanin kashetan da akayi

Kayan aiki daban turoba wlh  afirgice nake hankalina yarigada yatashi"" yace karkidamu zanbaki wata laya kisamu kabari sabo wanda akarufe yaudin nan saiki Gina kabarin kisaka layar dazaran kinsaka shikenan koda mijinki yafarka kikaji yana ambatar sunanta karkidamu

Danbazai manta da itah lokaci dayaba saidai adadin kwanakinda gawar zatayi cikin kabarin kullum anacire masa itah aransa akwana atashi haryamanta da itah duka wannan  itace kawai hanyarda za abi bayanta kuma babuwata hanya yakikaganie

Wannan layar dakike gani dazaran kin binneta duk acikinsu har yan uwanta daduk Wanda tasani sannu kan hankali zatafita aransu kamar yanda kikasan idan mutum yamutu lokacinda yamutu anajinsa arai anakwana anarage jin zuzin harma kiga magadan sunsoma mantawa dashi suncigaba da sha aninsu tokamar hakane awajensu tamkar matatta zatazamo tunda damacen bata duniyar saidai wani lokacin zasurika tunawa da itah dankuwa  abune maiwahala acireta aransu farat daya


Tace abunda kace aihakan za ayi godiya nakeyi boka Kajima kayi karko"" yajinjina kai yace kiduba zakiga layar agaggauta birneta yaudin nan

Tace angama boka takeyabace tamiyarda madubin to dama magriba takawojiki har an soma kirah tacewa habu baritaje gidan malam tanemu tasa ayi saukar Qur ani duk indasuke saisundawo da itah yace aihakan yanadakyau

Tanafita gida kaitsaye makabarta tanufa tasamu maigadin wajen
Suka gaisa tace Dan Allah wani taimako zakamun"" shikam yaga hajiya damota dama yasaba da irinsu Amman saiya tsuke fuska yace wani irin taimako a makabarta??? Dajin hakan sai lubabatu tazuge jaka tadauko daurin kudi yan dubu dubu dubu hamsin tace wannan ne ladar aikinka"" aikuwa yawashe baki yace tome kikeso acikin sassan jikin bil adama"" murmushi tayi tace duk ba wannan ba ankawo sabuwar gawa yau??? Yace dazun nan kuwa aka birne uwani yargidan malam habu "" kai yarinyar akwai"" lubabatu ce tadakatar dashi tace bawai sonake kafadamun halintaba ko dangantakarta da mutane

Yace tuba nake tadauko laya tace tsakiyar kabarin nakeson katona kasakamun layar

Yace Abu maisauki aikoda nera darima  zan iyah yimaki wannan yakarbi layar yashiga tana biye dashi harsuka kai kabarin yatona yasaka layar yamiyar yarufe sannan suka fito tayimasa godiya tashiga motarta tawuce""

Bayan takoma tacewa su habu kawai suwuce bawani bata lokaci suka kama hanyar kano koda suka isa hospital sunsamu inna da malam garba dukkansu sunsamu wannan mummunan labarin

Dasukazo ganin labila hajiya take sanardasu ansamu nasara labila tafarfado Amman batacewa uffan tunda su lubabatu suka shiga takurawa lubabatu ido kamar maitunanin wani Abu tuni jikin lubabatu yayi sanyi karfa labila tatona mata asiri kodayake ai anrufemata baki dawan nan tasaki ranta"" andade ana jajantawa juna"" wannan al amarin hajiya tatambayi su habu kosun sanarwa yan sanda sukace ah aikoda sukaje harmaigadi yasanar masu

Tace toshikenan "" Allah yasa aganta"" suka amsa da Ameen"" lubabatu tamatsa kusa da labila tace mata yajikin illah kawai tabita da kallo batace komaiba""

Hajiya tace aitunda tafarfado batace kalaba saidai binmu dakallo takeyi oh ni binta wannan Abu duk alokaci daya Allah yabaku ikon cinye wannan jarabawar"" suka amsa da Ameen

Saikarfe goma allurarda akaiwa usman tasakeshi tunda yafarka baice uffan ba shima sai tsirarun hawaye dasuke zubomasa akai akai yana sharewa hajiya sai sannu takemasa yanabinsu da kallo

Bayan kwana biyu jikinsu yayi dansauki suna amsawa idan anyimasu sannu ganin haryanzu  ba labarin khadija su malam garba suka Kira muktar akasanar dashi ranar yataso koda jirginsu yasauka kano Tara nadare kaitsaye yatari dan adaidaita zuwa gida

Da sallama yashiga gidan kamar wani mahaukaci yasamu su innah dasu gwaggo hassana sunyi zugun zugun dukawa yayi yagaidasu suka amsa sunyimasa ya hanya yace alhamdulillah

Shirune yabiyo baya sannan yace yanzu ina dadyn yake??? Inna tace aitunda yaga dankwalin khadijar baimatsaya jin itah suka daukaba yayanke jiki yafadi yanzu suna asiviti itama labila sai shekaranjiya ta far fado muktar yace nifa abun nan yadauremun kai satar mutum kuma harcikin gidansa ni wlh bana zargin kowa sai Abba danhaka  nigobe yola zanje koyabani Kanwata ko wlh inmakashi kotu  malam garba yace Dakata dakata bahaka za ayiba taya zakace shikake zargi gadukkan alamu mahaifinku baisanma akwai cikin khadija ba""  kamardai yanda mahaifiyar Ku tace sannan kuma baisan tayi aureba baisan inda takeba haba muktar aiko anan yaci kagane

Yayi shiru tokuwa inhakane saidai shi Usman din inyanada abokan gaba lallai dole yaganshi yanadakyau yaje asivitin

Yanisa inna to ansanarda yansanda??? Tace ansanardasu"" Amman sunce basukama suba sunanan dai suna bincike yanzu matsalar Usman yasamu lafiya

Inna tayi tagumie tace ni wlh tsorona kawai karsu cutarda itah"" wadan nan masu satar mutanen dabasuda imanie tayiyuma kidnapping ne

Muktar yace bahaka bane inna Aida kidnapping ne kudi zasu tambaya yanzu wanne hospital din aka kwantarda dadyn""

Malam garba yace ah to yanadakyau kaje danyanajin jiki saidai kabari saida safe mukammu munason sake ganinshi

Yace shikenan yamike zuwa bangarenda dakinsu yake zuciyarsa tanayimasa kuna""

Al amarin khadija kuwa tun lokacinda taji kukan namun jije ya yawaita saitaji hankalinta yatashi kwance datake tana kallon agogo tuntana kuka tanakiran sunan Usman hartagaji dankanta tayi shiru

Tashi tayi tashiga toilet tasamu akwai ruwa tadibo tayi alwala tazo tayi azahar la asar tadauko Qur'anin dataganie tabude tasoma karatu ahankali taji zuciyarta tanayimata sanyi tana nan zaune hardare gashi babu fitila duhu yafara take tasakejin tsoro

Kamar walkiya taga kwayayin lantarki nagidan duk sunkama haske ya mamaye ko ina tamkar rana


Saikunyi hakuri yaugashi daya kuka samu wlh yau fitanayi kuma gobe biki zanje zanyidan kokari inyi biyu goben in Allah yayarda I love u all






Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 98
        By
Gentle Lady💃🏽



Ganin hasken yasaka taji hankalinta yadan kwanta da agogo take amfanie idan lokacin sallah yayi  sai wajen karfe dayan dare sannan barci barawo yadauketa

Washe gari bayan tayi sallar asuba taji cikinta yana murdawa saboda yunwa tarasa yazatayi inama zatasamu abinci tashi tayi tasoma zagayen gidan dakunanda suke gidan sunkai goma kowanne dakin Kalar kayanda suke cikinsa daban ne danadayan"" karshe tasamu kitchen dakayan ci gasunan kayanmiya gasunan jawur dasu saikuma kayan lambu kawai sutadibo tawanke tadawo falon tazauna tasoma sha takwantarda hankalinta dankuwa tasan baranar zuwanta gida abudaya take tunani Usman tambayoyinda suke cikin ranta sunada yawa kuma tarasa wazai amsamata amsar tambayoyinta


Bangaren Usman washe gari muktar yatafi hospital din tareda su malam yagaisa da Usman Wanda kansa yake done baicewa ko wa uffan" su hajiya suka jajantawa juna"" muryan Usman sukaji yace hajiya muje gida haka Dan Allah"

Kusan tare suka kalleshi hajiya tace gidakuma babangida aikanabari kasakejin karfin jikinka ko??? Yagirgiza kai hajiya bazan taba warkewaba muddin dagaskene andaukemun Deejarh na inaji ajikina tana gidan nan bakudai duba dakyauba

Hajiya tace haba babangida kazama mai tawakkali mana insha Allah khadijarka zatadawo gareka kadaina kukan nan kamar mace tunshekaranjiya haryanzu koruwa baka hadaba aikoyunwa kawai ta isah tasamaka ciwo

Murmushi yayi mai ciwo yace abinci hajiya aini nayi bankwana da abinci kamaryanda nayi bankwana da farincikina hajiya nifa bazan ma kwana ananba sainaga khadija


Muktar yanisa yace dad kayi hakuri kajirah kasake samun sauki saimuje kaduna gabadaya"" nikaina hankalina bakwance yakeba""

Usman yace wlh tana nan kusadani muktar gashi  inaji tanakiran sunana Dan Allah kutashi mutafiii idan bantafiba hankalina sake tashi zaiyi ganindai Usman yakafe lallai sai sunje kaduna babu yanda zasuyi haka suka karbi sallama akarubuta masu magunguna suka kama hanyar kaduna hardasu  inna

Suna Isowa kofar gidan habu yayi hon maigadi yabudemasu yakunna kan motar motarsu muhd suna baya Dan aciki su muktar sukashigo

Anatsayarda motar Usman yafito yayi cikin gidan dasauri kaitsaye hawa nahudu yahaye yabude dakinta anan yacikaroda bargonda ta lullube ahankali yakarashi ahancinsa yashaki kamshinta yalumshe ido jiyake tamkar yanzun khadija tayafashi saboda kamshinda yakeyi"" dakin yasoma dubawa yana kwalamata kirah harcikin toilet yagama bade bagarenta danema Amman baigantaba cikin falon Yakoma yarumgume bargon yafashe dakuka

Damadai  Usman kuka bayayimasa  wuya kamar mace su hajiya suna shigowa basu ganshiba hajiya tace to inakuma yayi lubabatu ce tace yana saman duk tare suka rankaya saman sukasameshi yana kuka

Labila takurah masa ido sannan takalli hajiya tace waimeyake faruwane haryanzu banga sahiba ba??? Meyasa dady yake kuka??? dukkansu takebi dakallo tanayimasu tambayar akarasa Wanda zaibata amsa Usman ne yamike kamar Wanda akatsakurah yayi waje hajiya tanakiransa yace policetetion  zaitafi muktar ne yabi bayanshi waje sukasamu su habu suka dunguma zuwa opishin yansanda wajen abokinsa idris yatafi dayake DPO ne bayan sungaisa Usman yasanardashi

Yace wlh yasamu labari Amman sunanan sunayin iyah bakin kokarinsu kuma insha Allah duk inda take za aganta sundade cen anayiwa Usman tambaya tareda ma aikatan gidan Amman usman yace baya zarginsu dantare sukaje sallah

Towama  za adorawa laifi haka sukadawo gida jiki sanyaye hajiya tace asanar masallaci domin atashi da addua Allah yabayyanàta duk inda take

Lubcy kam dagekawai take kallonsu saiyanzu labila tasan mekefaruwa taci kuka harma yasake jawomata wani zazzabin  kullum cikin addua take Allah yabayyana sahibarta yanzukam Sam batadorawa lubcy wannan aikinba

Kawai tahakikance akan waninedai maijin haushin babanta"" rayuwa kenan Usman cikin sati biyu karkuso kuga yanda yazama kullum yazauna baidawata magana saita khadija saikuma yawan tunaninta
I

Kullum zakasameshi bangarenta yatasa kayanta agaba yana kallo watarana yayita surutu saikuma kasameshi yana kuka"" labila makusan hakan saida lubabatu tayita basu baki tuni muktar Yakoma sannu kan hankali labila taware  Usman mahakan yasama mata admission tawuce London dantacigaba da karatunta Usman mayakoma bakin aikinsa!"

Khadija sannu sannu hartasoma sabawa dagidan abunda yake yawan bata mamaki kullum saitaji kamar anayimata motsi acikinta tun lokacinda tacika wata daya agidan takejin hakan

Saikuma yanzun taji motsin ya yawaita gashikuma mararta tasoma tasowa kamardai maiciki yanzun balaifi tanayin hargirki taci kuma dazaran kayan miya sunkare saikawai tasake ganin wasu

Bayan watanni uku alokacin kam khadija tasan cikine da itah tashiga tashin hankali ita dabakowa agidan towaye zai taimaka yakaita asiviti gashi bakowa agidan"" koma adadin watannin cikin batasaniba nidai inakan kirgamata watansu uku wajen yawon shakatawa yanzun tayi hudu anan cikinta Yakama kwata bakwai kenan

Karkuso  kuga kirmansa kamar gobema zata haihu danyagirma sosai duk dayake cikin budurwane!"


Usman zaune cikin falonsa suna firah da lubabatu tanacewa yakamata yadauko Abdul majeed yadawo hannunta"! Yakalleta da mamaki yace yanzun kuma kefa kikace bakyason hayaniyar yara

Tarausayar dakai tace toyanzun gidan nan yamun fadi nidaya!! Shiru yayi daga bisanie yace shikenan zanyiwa hajiya magana kometace shikenan"" tace harsaika tambayeta haba usman to indai bazaka daukoshiba kasamamun Yar aiki wacce zanrika ganie kuma tana tayanie aiki


Yace shikenan kamar dayaushe kikeson ta??? Tace umm
Nifa tafiyama zamuyi namanta bansanar dakai ba Usman yakalleta kamar zaiyi magana saikuma yafasa kansa yajingina jikin kujerah yadafe saitin zuciyarsa dayakeyi masa ciwo lubabatu takalleshi tace yadai kociwonne??? Kaiyagyada mata tace sannu yadaga mata hannu alamar yauwa"" tace kai ni wlh ciwon nan naka yasoma isata ayi Abu bayajin maganie

Ya murmusa yana lumshe ido yace baisamu ingantaccen maganinda yadace daciwonba"" tace kamar wanne maganie kenan  ai atunanina babu maganinda zai gagaremu siyensa komai tsadarsa

Yayi saurin tarar nunfashinta yace akwai mana ai maganin ciwona khadija ne muddin baxan gantaba ninasan nayi bankwana da lafiya harkarshen rayuwata Nina San sonta shine zaizama ajalina

Ahankali lubabatu taja siririn tsaki wannan abun na Usman yasoma Kaita makurah ko kwanciya sukayi duk ranarda yasamu tabashi hakkinsa babu sunan wacce yake ambata sai khadija

Idan yakwanta kwana saidaifa kowa nagidan yadade kunnuwansa dan sunanta yaketa kiran hargarin Allah yawaye abunda yakekuma bata mamaki Sam Usman yanzu baidamu dayakwanta da itah ba

Dantun bayan batan khadija yanzu tsayin wata hudu Usman saudaya yakwanta da itah koshi ita tajashi dankuwa haka kurum taji tana ra ayinsa ranar taci kuka Sam kashe khadija baiyimata ranaba tunda gashi haryanzu Usman baidaina sontaba

Kuma baimanta da itah ba dukda abunda boka yace Amman kamardai shidin abun baiyimasa aikiba"" Amman su labila kam aiyayi masu""

Mikewa tayi tahaura sama ranta abace Usman kam baidamuba saima yasake mirginawa yasoma tunanin ruhinsa duk da haryanzu yana tunaninta Amman baisan yazaiyiba Sam yakasa tuhumar kowa yabarwa   Allah komai"""


Akwana atashi hasarar mai rai cikin khadija yashiga wata Tara komai dakyar takeyiwa kanta"" zaune"" take cikin falo" kamar""daga sama taji muryar Usman yana kwalamata kirah zunbur tamike tasoma waige " jin kiran yayi yawa kawai tafita harabar gidan tunda take bata taba kaiwa harabar gidan ba

Hartasa kafa zata fita tatunoda maganar wannan aljanar jiki bakwari tajuya zatakoma taji yasake kwallah mata kirah batareda shawarar komaiba tasakai tafitaa








Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠




Chapter 99
        By
Gentle Lady💃🏽




Tana fitowa sukayi ido hudu da Usman bakinta tadafe tana kuka tana dariya alokaci daya shikuma murmushi yakeyi tace dad Kaine yaushe kazo nan wayafadama ina nan??? Yace haba Deejarh duk inda kike aidole zuciyata tasanardanie

Kizo maza mubar dajin nan mugun dajinie"" batareda shakkar komaiba tatunkaroshi gabanta taji yayanke yafadi saikuma tatsaya chak

Zuciyarta tanacewa wannan ba Usman bane kaitasoma girgizawa tana jadabaya """ cikin sansanyar murya yace menene kuma khadija kizo gareni mana kinkuwasan halinda nakeciki sanadin kewarki

Cikin daga murya tace karyane kaiba dady bane kaiwayee? Meyakawoka wajena "" meyasa kakeson cutardanie""

Jinhakan keda wuya kawai sai aljanie hayyanul zairi yarikida yakoma katon jemage"" mai fika fiki sosai yayi mamakin da khadija ta iyah ganeshi dariya yasoma kyakyatawa wacce tasaka khadija Dade kunnuwanta saboda karar muryarsa dakuma rukukinta yatsaya da dariyarsa yace ke yarinya baki isah kisan koni wayeba abudaya nakeso kisani kafin nashanye maki jini shine nine nan zanzamo ajalinki

Yau ina wacce zata taimakeki kikirata kokuma kikirah Wanda zai ceceki daga hannuna yauba makawa zakikwana lahirah

Aini taimakoma akamun yauzanyi murna bayan kema Ashe harda kari nasamu yau zanmore dajikinku

Khadija tace karyane jinina bazaitaba zama abincinkaba in Allah yayarda yaunice zanga karshenka Allah bazaitaba baka sa a akainaba

Tanagama fadin haka tajuya daniyar komawa cikin gidan kamar walkiya yasha gabanta babban kuskurenda yayi kenan shaf yamanta khadija tanayin azkar dasafe babu wani mahalukin aljaninda ya isah yarabi jikinta batareda yakoneba

Iska yazama tayanda bakaganin komai face iskan yakai hannunsa yadankota alokacin khadija tasomayin addua dakarfi

Hayyanul zairi yarigada yariketa wata wahalalliyar kara yasaki yafada gefe daya hannunsa yasoma dayewa kamar yasaka hannunsa jikin dalma tuni Dan fiffiken dayake gadara dashi yafincike

Hakan baisa ya daddaraba kawai yataso gabadaya yayi mata baran makauniya yasake kwamtsa wata uwar kururuwa cen nesa da ita akayi wurgidashi take dukkan ilahirin jikinsa yasoma cidawuta

Khadija haryanxu batadaina addua ba cen taji iska yana kadawa maidadi ahankali tabude idonta tayi Arba dashi cen yashe bayako motsi wasu hawaye masu zafii suka saukomata mararta taji tafara ciwo

Dakyar ta iyah daga kafa zuwa cikin gidan tanajan kafa tanashiga falo taduke tasoma kuka danciwonda bata tabajin irinshiba""" nantakama murkususu

Haryanzu bakinta baidaina ambaton sunan Allah ba""Allah yabata ikon yin numfashi maikarfi saiga kan danda yafito sallama tajiyo cikin gida duk da bushi bushi takeganie

Wata dattijuwa ce tashigo dasauri takaraso wajen tataimaka  mata tajaye yaron saigakuma wata dabuwar nakuda bajimawa  tasake suntulo wani Dan wannan tsohuwar tayanke cibi tawanke yaron tahadamata ruwa tayi wanka

Duk wani taimakonda za ayiwa maijego itah tayimata tea tahadamata maikauri tasha takwanta babu jimawa barci yadauketa

Saidai tafarka tana tunanin mafarkinda tayi wai wani aljani yaso kasheta Amman sunyi fada baici nasaraba kuma tahaihu harwata mata tataimaka mata tatuno damaganar aljanin dayake cewa yasamu Karin Jinie

Hannu tasaka tashafo cikinta kwalelen batagama rufe bakiba taji cikinta wayam dasauri tamike daga kangadon tace innalillahi badai shiru tayi saikuma tasoma dariya ganin jarirai guda biyu cikin shigarsu ta alfarma kowannensu hannunsa yana bakinsa yanata tsotsa

Dukawa tayi takuramasu ido kamarsu daya da sahiba kenan Usman sukabiyo murmushi tayi najin dadi kenan ba mafarki tayiba Alhamdulillah

Dayan tafara dauka takurama ido tsirarun hawaye suka sauko sai akan kumatunsa saiyabude idonsa yana kallonta yana lumshe ido kamar yasan dalilin kukanta

Saman gadon takoma takwanta tarungumesu tafashe dakuka kowanne uba zaiyi gurin a Haifa. Masà yaransa gabansa yakallesu yaga kyautarda Allah yayimasa

Tashare  hawaye kutaku kaddarar haka tazodashi babanku baisan mada cikin kuba  saiyanzu take tuna in tsohuwarda ta tai maketa kowacece

Tana kwance harkusan magrib saiga dattijuwar tadawo tasake hadamata ruwa tayiwa yaran wanka tashiryasu takawomata lafiyayyen abinci yaji kayan yajie saida tagama komai tatafi

Khadija dakanta tayiwa yaran huduba" takirasu da sunayensu hassan da husainie yaran akwai hakurin yunwa danko alama basuyi kukaba  saiwashe gari da tsohuwar tadawo ta umurceta data basu nono

Kullum haka takezuwa harsukai sati ranarkuwa tana zaune dasafe tsohuwar tazo bayan tagama shiryasu khadija tace innah matar takalleta da murmushi tace na am"" tace inaso ingodemaki akan taimakonda kikamun

Tayi murmushi tace bakomai yata aiyiwa Kaine"" khadija tace innah wanne gida kike?? Tasake murmusawa tace Niger nake kokintaba zuwa cen ne???


Khadija tace ah ah kafin tasake jehomata tambaya hartafita hakadai sukacigàba dazama damatar hartayi arba in

Tasoma hadamata maganie akwai nasha nawanka dakuma nahayaki cikin sati biyu khadija tagoge tayi haske fatarta sai sheki takeyi

Su hassan sunada wata bakwai sannan dattijuwar nan tayiwa khadija sallama tace itah zatakoma khadija tatambayeta sunanta murmushi tayi tace Hauwa u kafin khadija tayi magana dattijuwar tafita khadija tanata nanata sunanta acikin ranta itakuma wannan aljanace ko mutum???

Amman naga aikinta kamardai irin na mutane sosai khadija tasaba da itah duk da bawai fira takeyi da itah ba Amman tanajin dadin zaman gidan tunda akwai mai tayata zama kuma koda yaran tana rikemata itakuma tayiwa daya wanka sa arta daya basuda kuiya basa kuka yanzun harsun soma tashi tsaye batareda sunrika wani abuba"" khadija idan tana karatun Qur anI   saitaji sun natsu kamardai sunsan abunda take karantawa "" bayan watanni biyu datafiyar dattijuwar alokacin su hassan sun iyah tafiya idan kagansu zaka rantse da Allah sun shekara biyu domin jikin girmane dasu gakuma wayo dansun fara magana


Khadija Sam tasaba dazaman kadaicin itah Kadai acikin gidan zaune take cikin falon tazaunarda su hassan tanayimasu karatun qur ani

Sukaji anyi sallama Kusan tare suka kalli kofar danganin maiyin sallamar wannan aljanarce  tashigo cikin murmushi dakuma fara a tanasanye cikin lifaya fara tayafa farar alkibba""" khadija bazata taba mantawa da fuskar taba ta amsa sallamarta tatashi dasauri ta isah inda take tarungumeta saikuma tafashe dakuka


Hannu tasaka tana bubbuga bayanta alamar rarrashi cikin kuka tace dan Allah kimiyardani gidan mijina  nagaji dazama wajen nan "" tajayeta daga jikinta tariko hannunta suka dawo wajenda su hassan suke tazauna tana kallonsu sannan tayi murmushi tamiyarda  kallonta kan khadija tace yagidan ya yaran""" ahanzarce tace qalau muke Dan Allah kifadamun yaushe zaki kaini gida bansan halinda yan uwana sukeba da mijina atakaice inason Yayana suga mahaifinsu

Tanisa tace hakane zaki iyah tambayata nikuma ashirye nake inbaki dukkanin amsoshin tambayarki"" Amman kidaure kiyimun tambaya daya daya domin insamu damar baki amsa gamsasshiya""

Khadija tace meyasa aka kawoni nan??? Aljanar tace ai ina tunanin kinsan wannan amsar Amman zansake tunamaki ankawoki nan ne domin akasheki hasalima banan yaso yakashekiba zaikaiki duniyar aljanune datake kasar Iraqi wajenda babu wani mahalukinda zaije cen yadawo daransa saiwanda Allah yanufa kuma yakeda Karin kwana anan gaba

Lokacinda yaratso tawannan jejin sakamakon Neman tsarinda kikayi ga Allah lokacinda kika farka shiyasa yafado daga sama kuka fado wannan jejin

Khadija tace nandin wacce kasace??? Tace kasar sin"" inajin kintabajin labarinta ko acikin tarihi"" khadija tagyada kai tace tome naimasu sukeson kasheni???

Aljanar tasake gyara zama tace yanadakyau kisan asalin tarihin shugaban wanan aljanin wato *hatsabibin boka*

Khadija tace menene alakar tambayata dakuma wannan bokan ina Neman tsarin Allah daga sharrinsa dashi da shaidanun aljanunsa

Aljanar tasake murmusawa tace tambayarki tanada alaka da labarinsa zaifi kyau kisaurareni kiji ainahin koshi waye daga cikin labarinsa zakisamu amsar tambayarki shiru khadija tayi batace komaiba

Aljanar tasoma kamar haka

Tarihin *hatsabibin boka* mukoma bayà wadansu shekaru Dari biyu baya anyi wani kasurgumin matsafi Wanda aduniyar lokacin babu wani boka mai tsananin tsafi dakuma siddabaru kamar shi sunan wanann bokan haiiiiranu wàsu suñamasa lakabida uban shaidanu👹👹👹






Aisha
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 100
       By
Gentle Lady💃🏽



Bashida imani kokadan sannan kuma yashahara" harwadansu matsafan sukanje wajensa yakowaya masu siddabaru da bokanci azamaninsa babu wani wanda zaijadashi yanada aljanu dayawa wadanda sukaimasa hidima yanada yaro daya  sunansa kanzaru"" yanakoya masa yanda akeyin tsafi

Lokacinda ciwon ajali Yakamashi"" yatattara dukkanin kayan tsafinsa yabashi amatsayin gado yakara dacemasa karike wannan aikin domin shine kawai abunda zanbarmaka gado

Kowanne da yakanyi tutiya dacewa ubansa yamutu yabarmasa gado kudine gidajene filayene dakuma kaddarori tonikuwa wannan din shine abunda nabarmaka kamardai yanda nima nagaji wannan awajen babana shima yagada awajen babansa danhaka karka kuskura kawatsarda wannan Sana a Dan acikinta aka haifeka

Lokacinda  haiiiiiranu yamutu wadansu bokaye da matsafa sunyita murna saboda Ya addabesu gabadaya aljanunsu suna shakkar sa danhaka ba kasafai suke samun aikiba kowa yafiso  yaje wajensa sunyi murna sosai da mutuwarsa aganinsu sunhuta zasu sake suci karensu babu babbaka saigashi kanzaru yazo yakere ubansa da mugunta iyah tsafi siddabaru zalunci harsuke ganin karama ubansa dashi

Lokacinda kanzaru yayi nisa yana damawa  acikin tsafinsa saiyayi bincike yagano maciji shine zaiyi ajalinsa kuma bazai Dade aduniyaba

Yashiga Neman inda zaisamu matarda zatahaifamasa dan da danbayaso yamutu baibar wanda zaiyi gadonsaba""

Acikin bincikensa yagano wata diyar  sarkin yan bori akasar Igbo kiristance sosai tayimasa aljannunsa kawai ya umurta suka daukomasa itah yacigaba da amfani da itah batareda andaura masu aureba

Saida tashekara biyu sannan tasamu ciki tun cikin yana karami yakeyin tsafi wacikin kuma baiyarda matarsa taci nama dafaffeba saidai danyen nama cikinta yana shiga wata tara"" tasoma nakuda"" yana ganin hakan yatsafeta tasandare dakansa yadayeta yafitarda jinjirin dake cikinta yakwashe jinin jikinta  sannan yabawa aljanunsa masu cin nama suka cinye gangar jikin

Hikimaryin haka awajensa yanaso Dannasa karyayi tausayi danmuddin yasha nonon uwarsa zaizama maitausayi gawasu

Jininta shiyatsafe yadinga baiwa yaron yanasha amatsayin nono lokacinda yaron yasoma girma yalaka masa suna *hatsabibin boka* aikuwa yaci sunansa dankuwa tunyana danshekara biyar yakanyi wani kalar tsafinda ko ubansa bai iyah shiba alokacin yacika damurna danyasan koda yamutu yabar wanda zaicigaba da daukaka gadon gidansu

Ko ina na kogonsa akwai hadiman aljanu masu kulamasa dankar maciji yashigo tunda yaga maciji shizaisama ajalinsa yasa akashirya masa wani gado maikyau

Kullum zakasameshi akan gadon baya yarda yaje ko ina dangudun haduwa da ajalinsa abunda baisaniba dukkan abunda aka kaddara shine  zaiyi ajalinka baka isa ka kaucemasaba

Shiwannan boka abincinsa nonon shanu Wanda aka tatsashi yanxu yanzu kuma baya yarda yasha nonon awani guri kohannun wani aljanie sai hayyanul zairi danshi kawai ya amin dashi watarana ya aiki hayyanul zairi diban madara bayan yadibo yanakan hanyar dajin zaikaimasa toshikuma yanajin yunwa saiyayi katari dawadansu fatake sunsamu hatsari akan hanya saiya  yanke shawarar zuwa yasamu jininda zaisha

Yasamu guri yagirke kwaryar nonon yatafi bayan tafiyarsa da sa o i biyar saiga wani maciji yafito raminsa yanajin kishirwa yanaganin kwaryar nono kawai yakafa bakinsa yasha asheyazuba kuma dafinsa aciki

Yayi tafiyarsa hayyanul zairi yana dawowa yadauki nono yakaiwa shugabansa bawani tunani yakafa kai yasha

Bayan shudewar rabin awa saidafin maciji yasimayimasa aiki yanajin yanayinsa yasauya kawai yadauko madubin tsafinsa yasoma bincike yagakomai saninkuma ajalinsa Yakama yakirah *hatsabibin boka* yadamkamasa gadon

Kujerar mulkin bokanci yasake jaddada masa karyayi wasa dashi danshine zaiyi tinkaho kobayan ransa take  yasoma shure shure bakinsa yana fitarda kumfa harrai yayi halinsa

Tanisa tana kallon khadija tace daga lokacin *hatsabibin boka* yafara shuka mulkin bokancinsa  cikin zalunci dakuma cin amana

Bayajin tausayin kowaye akabashi yayiwa aiki saikuma akasamu mutanen yanzu sunada rauni sosai akan addu a karancin  ilimi dakuma rashin tarbiya

Kezan iyah cemaki babu wani aiki daza abawa *hatsabibin boka* ya gagareshi babu wani aikinda yabashi Matsala samadanaki

Tanisa tanamai kallon hassan tace Ku mutane kunada sakaci yawanci sakacinku shine yake jawomaku matsala

Ansanardaku tayanda zakunemi kariyar Allah daga dukkan wani abun cutarda hakan yashafi aljanu da mutane irinsu *hatsabibin boka* dankuwa sharrinsa yakere duk wani sharrin aljani

Yayi nazari dakuma tunani Dan Adam baida tsawon rai kamarmu aljanu Dan adam duk dadewarda zaiyi yayi tsawon rai   bazai haura shekara Dari da ashirin ba

Wannan dalilinne yasaka abincikensa yagano wata Yar sarkin aljanu tanahiyar kudancin Nigeria yaturah bakaken aljanunsa suka daukomasa itan

Yanaso yayi amfani da itah yahaifi danda zaigajeshi yazamana jinsin aljani yafi yawa atare dashi danhaka zai Dade aduniya yanashuka tsiyarsa

Itakuma taki aminta dahakan dankuwa musulmace duk da dagabaya takarbi musulunci tayiriko dashi sosai wannan dalilin yasaka yakaita kurkukunsa dayake karkashin kasa yana ganamata azaba harzuwa yanzu baisamu yardartaba

Kuma atsafinsa yagani aladole saida yardarta idanba hakaba bazaisamu danda yakesoba zaisamu yaron jinin bil adama yayi yawa ajikinsa

Yanzun haka tana tsare acikin kurkukunsa karkidauka itah kadaice akwai mutane da aljanu dayawa awajen wadanda yakeganawa  azaba idan suka bijiremasa acikinsu harda bokaye  babu Wanda yasan mabudan kurkukun saifa shi danbaiyarda  dakowaba yakance shiko kansa baiyarda dashiba ballantana yayarda dawanie khadija tanisa tace ni wannan gimsasshen labarin ya isheni babu wani abun dadi acikinsa menene ribata tasauraren labarinsa tundashidin ba wani malamibane baikafa tarihin komaiba saina zalunci tanisa haryanzu banji amsar tambayataba saidai kawai cikamun kunne  dakikai dawannan  tatsuniyar banzar


Aljanar ta murmusa tace munkusa ai kisake hakurii

Dajinda yake acikin taraba yake Amman yatsafe dajin tayanda kodamutum yatafi bazaiganshiba
Saifa idan wajensa kikaje sannan zakisamu damar shiga
Shikuma dalilinda  yasa yatsafe dajinda yake saboda yagano wadansu yara biyu shune zasu zama ajalinsa
Wadan nan yarankuwa sunzo duniya






Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 001
        By
Gentle Lady💃🏽




Tamurmusa wadan nan yaran bawasu bane face yayanki"" jin hakan yasa khadija tawatsa mata wani mugun kallo tana jansu hassan ajikinta tace wannan aizancen banzane akan wanne dalili zanbar yarana suje wajen wannan azzalumin

Wanda bai maida rayuwar mutane abakin komaiba"" Yarana basa bukatar hada idoma dashi

Aljanar tace khadija kenan kisani tunkafin kizonan nasanda zuwanki wacce *hatsabibin boka* yadauka kanwatace

Khadija tayi saurin Tarar numfashinta tace aiho kicedama dabiyu kika taimakeni ni atunani kinyine saboda Allah Ashe akwai wata mummunar manufa axuciyarki game damu

Tace kisaurareni  khadija dazan iyah aikin nan wlh datuni nagama da matsalar khadija tasake wurgamata wani kallon tace saikuma akace dole Yayana suzasuyi??? Dayake sune kawai ubansu baisan dasuba??? Toni inason yayana bazantaba turasu wajen wannan mugunba kudakuke aljanu ma yagagareku saiwadan nan yaran dako abinci basu iyah baiwa kansuba

Aljanar tace khadija kifuskanci maganata wannan abun banikawai yashafaba hardake
Khadija tace nibanda Matsala  dashi bansanshiba bansan inda yakeba danhaka kinunamun hanya inkoma gida"" tayi maganar tana mikewa tadauki su hassan

Aljanar tace nibazan hanaki tafiyaba Amman kishirya domin yatura bakaken aljanunsa duk inda wadan nan yaran suke adaukomasa su aka she inadai kinason yaranki nandin shine maboyarsu

Khadija nasan zakice akan Karen bukatata nataimakeki shinkokinsan wannan bokan shine yayi sanadin mutuwar mahaifiyarki Fateema??? !!

Kirjin khadija ne yaharba dasauri tajuyo dahanzari tace waike waye yafadamaki hakan?? inakuma kikasan mahaifiyata???

Tamurmusa gazahiri kuwa  dattiijuwar nan wacce takarbar maki haihuwa maisuna Hauwa u to kakarkice"" !!! Dam gaban khadija yasake faduwa haba tadade tana tunanin kamar tasan mai fuskarta ashefa da mamantane suke kama

Dasauri takarasa tazauna kusa da itah murya narawa tace toyanxun ina take Dan Allah "" tadafata karkidamu zakije inda take khadija komai dakike gani kaddararrene kakarki tabison zuciyarta

Ga abunda iyayenta suka zabamata Amman takafe sai kakanki takeso dasukace tazaba kosu koshi saitace tazabeshi tayi wauta mezaihana talallabasu harsu amince

Wannan abun datayi mahaifinta yayita fushi da itah sanadin hakanne kishiyarta taimata magani tabargidan takoma Niger duk da batakoma wajen mahaifintaba saboda furucinda yayimata

Akan komai yabiyo baya kartanemeshi gata yargidan sarauta dankoda takoma babantane akan karagar mulki lokacinda tatafi tatafi daciki wata uku haka tayita rainon cikin hartasauka tahaifi yara biyu Mace danamiji

Tasake maida sunan mahaifiyarki fateema idan kikaganta bazakice kedin nan bace dankuwa babu abunda yarabaku

Namijin kuma Muhammad sunansa duka sunyi aure sun hayyafa Amman basacikin jindadi duk tasanadin abunda mahaiifiyarsu tayi abunkuma saiya shafeki keda kike jikanya"" sumacen din kusan hakane

Ranarda nabar nan naturah hadimina yasamoman cikakken tarihinki shine nasamu kakarki nafadamata hadarin rayuwarda kike ciki dukta dalilin kin biyayyarda tayiwa mahaifinta tayita kuka aranar kuma nasanarda itah mutuwar kakanki dakuma kishiyarta

Aranar namatsa mata saida takoma gidan mahaifinta tasamu yayanta shine sarki bayan tatafi wajen mahaifiyarta tanemi tayafe mata tasanarda itah duk abunda yasamu yayanta gashi haryanason taba jikarta batajiba bata ganiba mamarta takaita wajen mai martaba bashikoda lafiya

Yanaganin Hauwa yasoma hawaye shikanshi yayi wauta baidace danyarsa tayi badaidaiba yayimata wannan horon dama saida yayansa yace baidace aimata hakanba"" yadade abun yana damunsa saidai baisan yazaiyi yanemotaba tunda baisan inda take aureba

Dakyar yatashi zaune yayimata alama tazo cikin Dari Dari takara inda yake taduka saikuma tafashe dakuka tana neman yafiyarsa yace shikam aituni yadade dayafemata

Yace ina maigidanta?? Anan tadanardashi labarinta tunbayan barinta garin dakuma halinda kike ciki yajinjina Kai lallai wannan abun saiyazama izna ga iyaye dasuke nuna isa akan yayansu  yanzu kuduba ba itah datai abunba yashafi yayanta harda jikokinta kuskure gudadaya data aikata

Inagamu masuyiwa iyayenmu kallon hadarin kaji kallon gidadawa aimu munwaye"' kallon basu isah ba aini bayaro bane dazasu nunamun Abu maikyau nasan abunda yadace ga rayuwata

Waisu dansunyi lokacinsu ana takuramasu muma saisun takuramana subarmu muci zamaninmu mana"" hmmm yammata samari yawancinku duk haka kuke

Kusani duk abunda kukaiwa iyayenku lallai kukwana dashirin karbar sakamako kukalli abunda Hauwa tayi kuma da abunda yasameta agurinka zakaga kamar abun bakomai bane nankuwa babban laifune.

Tacigaba karkiso kiga yanda ake murna sainunata  akeyi gadangi "" satin tadaya agidan mahaifinta yarasu bayan kwana uku mamanta tabi Allah mai iko ashedai darabon zasugana ne

khadija tace Allah yajikansu tace Ameen "" khadija tanisa tana kallonta tace haryanzu magana kike  akan dangina haryanzu bakibani amsataba menene dalilinda yasaka wannan bokan yakeson kasheni
..
Tace bashine yakeson kashekiba shima aikine akabashi tatari nunfashinta tace wayabada aikin akasheni??? Bana fada dakoma bantabacin zalin waniba bantaba hayaniya dawaniba to akan wanne daliline za ace akasheni??? Tayi maganar tana kallon aljanar

Murmushi tayi tace bakodaya Amman itah wacce tasadin akasheki tanaganin kintaremata wani jindadin duniya

Khadija tatareda dacewa wacece wannan??? Batareda shakkar komaiba tace kishiyarki lubabatu""

Khadija tace ban...ban.banfahinci mekike fadaba"" aljanar tamurmusa tace nace kishiyarki lubabatu khadija tace never wlh nifa kinsani aduhu wacce lubabatun???

Tace ina tunanin bakisan wata lubabatu bayan Itaba kuma Usman bashida wata Mata ayanzu sai itah akan me kike tantamar anya itane kuwa???

Khadija tace saboda itah ce mahaiifiyar labila kinga kuwa nasan bazata cutardaniba"" aljanar tamurmusa tace ke yarinyace khadija ai lubabatu ba itah tai nakudarkiba dahar zataji tsausayinki barimadai infadamaki  bayan batanki tasa akaturawa yarta kuma kawarki aljani yahurah mata iskar barci Na sihiri kwananta biyar tana barci yanzun haka bata kasar anturata karatu kuma duk bacikin hayyacintaba

Gabadaya yan uwanki sunmanta dake kamardai yanda lubabatu tace bokan yayimasu "" nasan bazaki yardaba saboda kinyarda da itah idan zaki iyah tuna kalaman yarta datake maki zakigane hakan domin itah tasan abunda uwarta take aikatawa

Khadija kam bakibude take kallonta"" tace waima kinsan usman yanada da saurayi babba yayan labila ne Amman ba lubabatu tahaifeshiba sunansa kaleed

Bayan lubabatu tasa ankashe mamarsa ameenatu tasa kuma boka yakashe kaleed saidaikuma abunda basu saniba acikin aljanunsa akwai wani maisauran imanie saboda lokacinda ana tsoratarda maman kaleed hardaashi cikin masuyimata gizo suna zama kadangaru


Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 002
       By
Gentle Lady💃🏽


khadija ce tayi saurin Tatar nunfashinta  tace waiikina nufin dadyn labila?? Tace sosai kuwa lokacinda lubabatu takeson miji taje wajensa kuma itah tasakashi akashe matar Usman"" shine yatura aljannu sukarika tsoratata karshe aka sakomata ciwon zuciya tarasu bayan nan kuma tasakecewa akashe kaleed saidai aljaninda yaturah yakasheshi kafin yaje wani dagacikin aljanunsa yayi saurin zuwa yadauke kaleed din tareda kayanshi

Aka idar *hatsabibin boka* kuma duk yabawa aljaninsa aiki kuskure banaka bane kuma rashin aikata aikin zaijamaka mummunan hukunci

Lokacinda yaje gidan baitararda kaleed dinba saikawai yakama bakinshi a zuwan shine yadaukeshi domin bayan yadawo yana taraddadin sanarda *hatsabibin boka* saikawai akabashi kayan aiki saikawai  yakarbe kayansa yayi shiru

Takai kwarshen maganar tana kallon khadija"" khadija wacce hawaye sukebin fuskarta"tanisa toke taya kikasan dukkan labarinsa??? Aljanar tamurmusa tace kakana shiyayiwa kakan *hatsabibin boka* aiki lokacinda  yamutu sai kakana yatuba dalilin wani malami anturashi jikin wata mata domin yahanata zaman aure

Awajen rakiyyya da malamin yayimasa wa azi saiya tuba Amman bayada hujjar sanarda kakan *hatsabibin boka* haka"" shine yagudu zuwa makka yayita tura mayakan aljanunsa  Amman sunkasa samun nasarar shiga inda yake saboda duk wani mugun aljani bazai iyah shiga wurinba

Yanacen har yamutu dansa yasoma mulkin  bokanci shima yamutu wannan yazauna lokacinda yadauke Kanwata alokacin labarinsa yadawo farko danmukammu bamusan kakanmu yayizama dashiba kuma akwai wani aljanin abokin kakana dayake wajensa shine yakesanar dashi sirrinsa"" kinji tayanda nasamu labari

  Saboda yanagudun  ranar mutuwarsa yasa matakan tsaro sosai adajin tayanda babuwani mahalukin daya isah yaje dajin inhar bawai dan ayiwa wani maganiba dazaran katunkari dajin komai zaijuye maka zakayita haduwa damiyagun namun jeji karshe sukasheka

Khadeeja tace to ahakan taya su hassan zasuje dajin??? Tamurmusa wannan aikinane bukatar bokan banaso tacika khadija kitaimaka kicire sauran  mata daga sharrin wannan azzalumin bawan"" khadija tace totaya kenan"" aljanar""  tace bayanxu zasujeba inhar kinyardaa zandaukesu inkaisu wajen kakana har lokacin""  da yakamata suyi gaba dagaba tunda kinason komawa wajen mijinki damadai baisan kinada cikiba saiki koma duk ranarda akagama komai  zakiganni gidanki tareda yaranki

Tanisa ammanfa zuwanki gida akwai rudani"khadija takwalalo ido tace rudanin menene??? Kardai bazasu ganeniba??? Tace kodaya dazaran sunganki duk Wanda yayi ido hudu dake komai zaidawomasa take asirin zaikarye

Saidaikuma  abunda sukahada da itah dabokanta sun aje sako azuwan wasune suka saceki kuma sunce kar anemeki""

Dankuwa kasheki zasuyi "" danhaka idan kika koma saikisan yanda zakiyi kisan yanda zaki bullomasu domin kishiyarki *hatsabibiyar matace* tabugawa ajarida tunda nake bantaba ganin bil adama Marar imani kamartaba Sam kamar ba musulmaba"" batada imani kokadan ke intakaice maki labari akan acire sonki acikin zuciyar Usman tabada jinin wadansu jinjirai biyu

Khadija tace innalillahi wa inna ilaihirrajiun yanzun mom din tabada jinin jarirai akan wani banzar burinta na duniya??? Tanako tunanin mutuwa???

Aljanar tace bana tunanin haka khadija saboda abunda tayi yawuce saninki ina tunanin bakida labarin aurenda Usman yayi kafin ya aureki??

Khadija tace inazan sani tundashi baisanar daniba aljanar tagyara zama tabata labarin duk matanda tasa aka kashe dakuma wacce takora dakuma wadanda akayita turawa aljanu takareda cewa kece kawai kika Gagari dukkan aljanunsa sunkasa rabarma jikinki

Khadija wacce take rusar kuka haikan tace yanzun dady yasan abunda takeyi??? Aljanar tace baisaniba kuma koda fadamasa kikai akwai wahala yayarda domin macijiyace itah maidafi biyu ketafi kunama hadari

Duk wanda zakibaiwa wannan labarin azuwan makaryaciya  zaidaukeki danbazai yardaba cikikuwa harda iyayen duka kishiyoyinta saboda rabuwar arziki sukai baza ataba zargintaba saboda batabar wata shaidar dayakamata azargeta

Takauda hankalin duk wani maitunani mugunyar matace dakike ganinta Nina San koke yanzun kina shakkar labarin nan

Khadija tanisa tace haryanzu bangama yarda ba inaganin kamar bazata iya aikata wannan mummunan laifinba

Aljanar tace karkidamu bazan tilas taki yarda da abunda nafadaba Amman duk ranarda kika koma zakigane hakan dakanki Dan dazaran taganki zatashiga rudanie kuma tamakara Dan lokacinta yazo da itah dabokanta alkadarinsu zaikarye

Khadija tace Toni taya zanfita dajin nan injegida tunda bansan hanyaba kuma wannan mugun aljanin nasan yana nan yanajirana duk sanda nafito

Aljanar tayi murmushi tace wanne aljanin?? hayyanul zairi??? Khadija tace nikam inazansan sunansa"" aljanar tace ai khadija kinyimasa illah "" illarda kodama yarayu bazaisake moruwaba inajiwa lubabatu tausayi danhar naga yanda zaidau fansa

Khadija Tatari nunfashinta tace mezaimata bakuma kince ita tasaka aturoshiba??? Tace hakane Amman abunda bakisaniba su wadancen aljanun duk akaturasu suyimaki aiki inhar basuci nasaraba akaimasu illah bamakawa jikinka zasudawo saisun fanshe ajikinka

Khadija tace yanxun kina nufin zaikoma jikinta??? Tace babu makawa domin gabadaya jikinsa yakone fikafikansa dayake tashi dasu gabaya sun raunata wainikuwa wacce irin addua ce kikai haka???
Khadija tamurmusa tace bankaranta komaiba bayan surori guda uku Na karshen  Qur'an masu fara wa da qul

Kisani babu wadansu surori acikin qur ani Wanda zakinemi tsarin Allah dasu wadanda sukafi wadan nan surorin aljanar tagyada kai tace kwarai dankuwa sunhada daneman tsari daga sharrin mutum aljan da maihassada  khadija tace kinsan wani Abu wlh saiyanzu nake tuna abunda sahiba takemata ina hanata ashedai itah tasan abunda tasani

Aljanar tace sosai abunda yasaka takasa sanarmaki anrufemata bakine"" tanisa yanzun kisake zama nan nawadansu watanni kafin su hassan susake kwari tayanda koda kinyayesu baxasu cutuba""khadija tabuga tagumie tace ni wlh kinsa jikina duk yayi sanyi"" anya zansake komawa gidan kuwa??? Aljanar tayi dariya danjin furucin khadija tace kintsoratane??? Khadija taja majina tace bawai naji tsorobane dannasan babu abunda zaisameni face abunda Allah yarigada yatsaramun rayuwata "" kingakuwa ban isah in karkare kaddarata ba Amman gaskiya inajin tsoron wannan matar da sharrinta indai abun nan dakika fada duka ta aikatasu gaskiya tayi nisa saidai inyimata fatan Allah yashiryeta  da itah daduk wata maihali irin nata"" Amman gaskiya baxansake komawa gidanba nahakurah dawan nan auren

Aljanar tasake darawa khadija takalleta da mamaki tace dariya nabaki??? Tace um um maganarkice tabani dariya shindakike cewa  bazaki koma gidan Usman ba yazakiyi  da soyayarsa??

Zugum khadija tayi gabanta yafadi tayi shiru" aljanar tacigaba Ninasan kinason Usman sobana wasaba danhaka karkitaba karyarda zuciyarki khadija ninasan wacce zansa tasake maki shiri takuma koyamaki dabarun zaman aure dankedin karamar yarinyace bakisan kirsar mataba""

Zatakoya maki yanda zaki tarairayi mijinki duk da nasan kakarki tagamayi maki komai Amman zansake hadaki dawannan matar dan nayarda da itah sosai zaku zauna da itah nawani lokacin kafin kitafi gida


Gaisuwa da fatan alkhairi agareku baki daya banhakuri "" inamai Baku hakuri kunjini sai ahankali kwana biyu biki mukayi shiyasa yanzun dayama kukasamu saikuyi hakuri dashi zuwa gobe nagaida kowa kyauta🙋🏽





Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 003
         By
Gentle Lady💃🏽




Khadija tace nifa mamaki nakeji haryanzu jifa yanda take nuna halin ko inkula akan mijinta tamkar batada kishi"" aljanar tace ai mugunyar kenan munafukar boye aikara Wanda zaifito fili yanunamaki Abu dawanda zairika yimaki zagon kasa idan harmutum zainuna maki aike zakisan yanayin takunki dashi

Khadija tace hakane kam wlh datacemana tabarmana kwanakinta tausayi tabani nace tanason mijinta sosai harnafara zargin kaina anya banyi shishshigiba nashiga tsakanin masoyan asali

Aljanar tace abunda bakisaniba aidabiyu taturaku Dubai saboda *hatsabibin boka* yace muddin kina gidan baza asamu damar yimaki komaiba saboda kullum kinayin azkar Amman idan kikabar gidan kukaje yawon shakatawa hankalinki zaidauku kimanta dayin azkar

Tayarda kuje dantasan babu abunda zaishiga tsakaninki da usman kamar yanda akeyiwa sauran matansa """ kuma dazaran kuntafi za aimaku asirinda zaishafeku khadija tayi shiru daga bisani tace wainikuwa bakifadamun sunankiba?? Tayi murmushi tace sunana maimunatu khadija tace masha Allah suna maidadi

Tace ko nagode khadija tace mubar maganar "lubabatu "" au momy maimunatu takamayimata dariya tace kibarshidai nafarkon khadija tayi dariya tace ah ah mom din sahibace kinga komai tamun matsayinta yana nan""
Tanisa yanzu maimunatu ya maganar kaleed kuwa???  Inayake ??? Ina zamuganshi tunda kinga shidin baisan danginsaba kuma yazaiyi yasan inda suke""

Maimunatu tace sai angama war ware komai zakidawo dashi gida"" khadija tace toni ina nasan inda yake??? Maimunatu tace yana  gidan hassan"" kanin mamanki yanzun haka baya ma kasar yana London wajen karatu

Khadija tace ikon Allah shikuma cen aka kaishi?? Maimunatu tace hakane aljanin yakaishi cen"" kuma dakinganshi basaikin tambayaba dankamarsu daya da Usman saidai kawai kice shidin yafishi kuruciya Amman babu abunda yarabasu kamar hassan dahusaini

Khadija tace nikam danakoma zanje wajen kakata inason ganin kaleed din nan koba kamai inason yadawo hannun mahaifinsa

Maimuna tace akwai sauran lokaci karkiyi saurin sanardashi gaskiyar lamarin kibari saisu Husain sunkara girma kamar nan da shekara hudu saidai zaki iyah zuwa kiganshi koda zakifadamasa gaskiya Amman kifadamasa yasake hakuri kifadamasa shirinmu zai fahimceki yanzun saura shekara daya yagama karatunsa
Khadija tace shikenan

Allah yakaimu .maimunatu tace Ameen"" duk labarin nan da akeyi su husaini suna zaune bakajin ko motsinsu tamkar sunsan abunda ake fada"" tare sukacigaba dazama gidan yanzun hartakan fita dajin da itah da maimunatu Amman banda su hassan

Akwana atashi babu wuya wajen Allah su Husaini sungirma shekararsu daya dawata takwass Amman magana chauchau gasu dajikin girma hargudu sunayi idan kaji yanda suke karatu saika rantse da Allah sunyi shekara biyu aduniya tunsunada shekara dawata biyar suka yaye Kansu danbasa Neman mama saidai abinci hakan yasa maimunatu tace tayayesu

Saitakara watanni su Husaini sunada shekara biyu sauran wata daya suyi shekara biyu maimunatu  tacewa khadija tashirya zatakaita gun matar

Yanxun Sam khadija batayin murna dakomawa gidan Usman dantun ranarda taji komai gameda lubabatu taji gidan yafice aranta tamadaina sakawa ranta tunani

Sam batasake nunawa maimunatu tana kewar mijintaba sosaikuma taji dadin zama da itah danzamanda sukai da itah tagano yawan ibadar da takeyi dadere bata barci itama take koyawa su Husaini karatu dan itama tahardace Qur ani

Ranardazasu tafi khadija harda kuka tayi narabuwa dasu hassan kunsan tsakanin uwa Dada sai Allah Amman abun mamaki su Husaini basuwani damuba saida tayimasu addua sannan suka fita gidan"" sunafita tacewa Khadija tarufe idonta

Batareda musun komaiba tarufe idonta tarike hannunta take suka bace tamkar guguwa tsayin  awanni biyar saigasu kofar wani gida Dan madaidaici tsarin gidan yanada kyau batareda bata lokaciba tace munkawo kibude idonki

Khadija tabude idonta tasoma kalle kalle tasoma ganin mutane saitayi hamdala dantasan tashigo cikin jinsinta maimunatu wacce haryanzu murmushine kwance akan fuskarta tace Yar uwa nanne gidan matar Kuma nayimata bayaninki duka danhaka komai tace kiyi kiyi karkiyimata musu

Khadija tagyada kai"" maimunatu tacigaba yaunakeson mukama hanya dani dasu Husaini saikiyitamana addua Allah yakaimu lafiya dannasan *hatsabibin boka* yana nan yana Neman inda zaigansu  danabarki nan zanwuce danhaka karkimanta da abunda nafadamaki karkiyi sanya dazaran kinsauka gidan kisamu kidauko madubin nan kikona aljaninda yake gadin madubin dannasan muddin taganki zata sanardashi daganan zasu sake yimaki wani shirin kamardai yanda suka yaudareki tunfarko khadija tace karkidamu Yar uwa ban manta dakomaiba
Tasaki murmushi tace hakan nakeso Yar uwa tomuje taresuka turah kofar gidan tareda sallama"" saida sukai sallama kamar sau uku sannan aka amsa akace kushigo mana

Maimunace agaba khadija tana baya aranta tace tofa ashedai harda aljanu sunazama cikin mutane lallai saimuyi taka tsantsan daidai sunshiga falon tana zaune tanacin abinci tanaganin maimunatu tasaki fara a tace kece tafe maraba kushigo mana,  suka wuce tanuna masu kujeru tace suzauna taresuka zauna sannan sukasoma gaisawa

Tace yahanya Yar uwa maimunatu tace alhamdulillah  tace hajiya gatafa nakawo tayi maganar tana kallon khadija matar tayi murmushi tace ainagane Amman maimunatu ai Yar uwartaki ma da damarta baza asha wata wahala akantaba"" tace hakane gatanan dai nakawo maki kiyimata gyara na musamnan sannan kikoyamata yanda ake tarairayar Miji inason idan takoma yadauka wata sabuwar khadija ce aka kawomasa

Kusan Tare suka sa dariya tace karkidamu kinyi dashe gida mai albarka inamai tabbatar maki dasaitafima yanda kikeso"" kedai kawai kibar komai ahannuna"" maimunatu taciro jakarta tadauko kudi tace gacikon kudinki"" nizantafi  tace to maimunatu Allah ya kiyaye hanya khadija tataso sukafito

Bakin kofa suka tsaya suna fuskantar juna maimunatu tace to khadija nizan tafi "saina dawo maki dayaranki insha Allah zancika alkawari zanyi iyakar kokarina inkaremaki yayanki saiki tayamu da addua Allah yakaremu"" khadija tace Ameen nagode sirarun hawayenda suke cikin gurbin idonta suka karasa gangarowa  tace zanyi kewarki sosai ashedama anasamun aljanu masu son mutane nibanyarda dahakanba saiyanzu

Maimunatu tayi dariya har hakoranta suka bayyana tace ai khadija kamar yanda kikasan acikin mutane akwai mugaye salihai nakwarai yan iska dasauransu komai kikasan za asamu acikin jinsinku muma akwaisu anamu

Khadija tace Yar uwa yanzun wannan ma aljanace??? Amman naga tanacin abinci irin namu Amman kenaga bakyaci

Maimunatu tasake darawa tace mutumce kamarki bakiga tayi kama da jinsinkuba"" khadija tace aibanganewa aikema babuwanda zaice kedin ba bil Adama bace Amman Ina mamakin ya akaitasanki

Tace nima nasantane wajen wata Yar uwata takebamu labarinta duk sanda zanzo wajenta nakanyi shigar bil Adama kamardai yanda kikeganina itama haka danba ainahin siffata kenanba khadija tajinjina kai tace tonikam nandin wanne garine???

Maimunatu tace Maiduguri ainasan dai kinsan garin kobaki taba zuwaba kinada labarin garin yanzun gakudi tayi maganar tanazuge jaka tabata kiyi amfanie dasu kikoma gida idan hajiya tarana tagama sallamarki   Dan Allah kuma idan kinkoma kiyi amfani daduk abunda tasanar dake karyazama anfadamaki Abu kirikajin kunya danbabu kunya kikyautatawa mijinki inhar karace kikewa labila yanzun kinsan matsayin lubabatu danhaka bata chanchanci kara awajenkiba

Khadija tayi murmushi tace bakida matsala dawan nan zanyikomai kodan natusa mata takaici nimadinfa bata wasabace wlh irin rayuwarda nashiryawa kaina bagaskiya bane Amman danatuno mahaifin kawatane sainaji kunya banaso yadauka nidin banda kunyane

Maimunatu tace babu wannan khadija kinga barinayi sauri yana jirana" khadija taleka waje tace wayene yakejiranki?? Ina mukawaine mukazo nan??

Maimunatu tace ah ah aini banda isasshen karfinda zandaukeki inyi tafiya dake saboda karancin karfina danice zankawoki nan saimunyi kwana uku ahanya

Saurayin Kanwata wacce take hannun *hatsabibin boka* shine yakawomu yanada masifar sauri yanzunma. Abunda yasaka mukadan jima ahanya nace yayi ahankali sabodake khadija kam tasake tsurewa da al amarin aljanu






Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠



Chapter 004
         By
Gentle Lady💃🏽



Khadija tace shikenan Allah yakaiku lafiya yatsareku" maimunatu tace Ameen Sannan tasakai tafita khadija tana tsaye saida taga tabace sannan tajuya cikin gidan jikinta sanyaye""

Tashiga da sallama hajiya tarana ta amsa mata sallamar tashiga tazauna hajiyar tace yata bari nazubomaki abinci kici saikije kiwatsa ruwa kisamu kihuta gobe saimu fara dankar akure lokaci

Khadija tace inaso nayi sallah ne tace badamuwa muje innunamaki dakinda zaki zauna bamusu tamike tanagaba khadija nabinta wasu dakunane kusan guda biyar Jere dajuna tabude mata daya tashiga tana biyeda itah dakine maikyau kayan dakin madaidaita naxaman Mace daya tace gabandaki cen gakuma abar sallah nanne gabas saikiyi hanzari gashi ankusa magrib

Khadija tace to tacire mayafinta tashiga toilet din sannan hajiyar tafita bayan tafito tashinfida abar sallah tarama sallarda akebinta tatsaya lazumi tanamai rokon Allah yakaremata yayanta kuma yabasu sa ar abunda zasuyi
Tana zaune saman abar sallar har akayi magrib hajiyar tanakan lekowa saitasamu tana laxumi  saita koma bayan tayi magrib bata bargurinba saida tayi isha i sannan tawatsa ruwa koda hajiyar tashigo tasamu khadija tana miyarda kayanta tace tafito taci abinci tace to bayan tashirya tafita tasameta falon zaune tagaida itah ta amsa cikin sakin fuska tanuna mata abincin tadauka tasomaci tuwon shinkafane damiyar kubewa tasha kayan yajie saikuma maganie da akasaka aciki da bisimillah tasomacin abincinta hartakoshi tabata ruwa tasha ruwankam badadi ace war Khadija dafarkoma  tadauka lemune saida takai bakinta kamshin kayan yaji yadaki hancinta aranta tace kilanta wani hadin lemune maidadi saida harshenta yadandana tagane komeye tasha iyakar shanta

Hajiyar takarba tamiyar a fridge  tace kingansu nan koda zakiji kishi dagayau sune ruwanki batareda musum komaiba tace to fruit tadaukomata anyankasu kana na kana na sunsha madara gashi dasanyi daidai gwargwado

Tabata tace tasha shima duka tashanye  sundan taba fira yawancin maganar duk hajiya keyi khadija iyakarta eh ko ah ah saikusan goma tayimata sallama  tace taje takwanta tayimata saida safe tashiga dakinta alwala tadauro tasomayin sallah

Al amarin *hatsabibin boka*kuwa tunranarda aka haifi su hassan dajinda yake ciki yasoma girgiza al amarinda yatashi hankalinsa sosai dasauri yajawo madubin tsafinsa yasoma bincike aikuwa dama yasan alamun dayaganie na haihuwarsu shine yabayyana kenan sunshigo duniya

Lallai dolene yagansu tunkafin sugirma yakashesu yadukufa nemansu acikin madubin tsafinsa Amman abun mamaki andai nunamasa dajinda suke Amman bayaganin komai yayita turah aljanunsa dajin Amman basaganin yaran hakan yasaka ya ce tokodai sudin ba mutane bane kokuwa dabbobine

Madubin tsafinsa yatabbatar masa mutanene kuma suna nan cikin koshin lafiya hankalin boka inyayi dubu yabachi yayimatukar tsorata da al amarin wadan nan yaran tundaga lokacin yasoma bincike hanyarda zaibi danyagansu

Yagano dajinda suke tsafaffen dajine babu Wanda zai iyah ganin abunda yakecikin yayi bakinciki matuka yasoma kururuwa wacce taisanadin firgitar duk namun jejinda suke zaune dajin sukasoma yankan nakare

Saigashi yaukuma dajin yasoma girgiza tamkar ana girgizar kasa "" *hatsabibin boka* tuni yatsure yasake shafo madubin tsafinsa yanawadansu surutai saiga wani wargajin aljanie asararin samaniya yanagudu tareda wata aljana Amman Sam baiga wasu yara ataredasuba"" Amman nadubin tsafinsa yatabbatar masa lallai sunatare dasu kuma sunkusa shiga saudiya muddin yabari sukashiga tosuntsira

Lokacinda zasufito kuma shine zaizama ranar ajalinsa yayiwani gunji yace karyane saidai ninaga karshensu

Take ya umurci wani aljani kankabusa yayi sauri irin Wanda baitaba yin irinshiba yacinmasu yanzun yadawomashi dasu bayanshi Kuma yaturah tawagar aljanu

Batareda bata lokaciba suka zama iska sukatashi sama sukabaza hanyarda *hatsabibin boka*  yanuna masu aljaninda yake dauke da aljana muimunatu yakalleta yace rankiyadade inajifa aljanun *hatsabibin boka* sunabiye damu dannasoma jin kamshin iskarsu kinkuwasan wannan aljanin yafini gudu sosai niko rabin rabin saurinsa banyiba inajin tsoro karya kamamu nibakaina nakejiba yaran nan damuke dauke dasu

Maimunatu tace kacigaba da tafiyarka ninasan Allah yana taredamu domin yanxun haka nasan mahaifiyar yaran nan batayi barciba tanakan rokon Allah yakaremu daga sharrin wannan azzalumin

Dayardar Allah lafiya qalau zamu isah aiyanzu baiwuce tafiyar yini daya mukaiba yace hakane rankiyadade saiyasake dage fukafukansa ya auna cikin gajimare saigashi yanagudu tamkar jirgi yamaso yafi jirgin gudu shikanshi yayi mamakin saurin nashi

Al amarin *hatsabibin boka* kuwa sanda yaturah aljanie kankabusa yabi bayansu aljana maimunatu yanazaune gaban madubinsa yana kallonsu"" duk abunda suke fadakuwa yanajinsu kamar walkiya yaga sunkara gudu dasauri ya umurci aljani kankabusa yasake karfin gudunsa iyakar gudunsa yacinmasu dankar suwuceshi

Aikuwa shima yakara gudu tareda tawagar dasuke bayansa kafin sushafe  sa aguda harsun cinmasu koda aljana maimunatu tawaiga tayi arba dasu tacemasa yakara sauri gasu abayansu
Yace iyakar karfina kenan rankiyadade saidai suzubawa sarautar Allah ido"

Khadija tana gama sallah tadaga hannunwanta sama tasoma jero addua tanakiran sunayen Allah taname kaskantarda kanta tanamai yakinin cewa Allah zaikarbi adduar ta take hawaye sukasomaa  zuba akan fuskarta

Allahu Akbar Allah majirokon bawansa saura kiris tawagar aljanun *hatsabibin boka* sutari gabansu saigawani iska maikarfi yataso Wanda sukansu basusan daga inda iskan yatasoba gashi balokacin damuna bane take iskan yasoma jansu baya baya fukafukansu  sukakasa yimasu rana tunisu aljana maimunatu sukabace cikin iskan kafin sa o i ashirin suka kai sunashiga  garin makka sukayi hamdala

Al amarin *hatsabibin boka* kuwa lokacinda abun yafaru madubin tsafinsa duhu yayi Na wadansu sa o"I sannan yadawo daidai saidai baiga aljana maimunatuba saitawagar aljanunsa

Tashin hankali kam Wanda yashiga basai anfadaba lallai dolene yasake wata hanyar danganin yakashe wadan nan yaran saikuma yashiga binciken hanyarda xaibi

Hanya dayace akanuna masa itace kawai xaibi danyatsira hanyar itace yasamu yakusanci wannan aljanar datake boye akarkashin kasa wato kanwar maimunatu

Dazaran tasamu ciki danda zatahaifa zaikasance musulmi shine xaishiga har kasa maitsarki yakashe yaran komai kankantàrsa

Al amarinda yatsoratarda *hatsabibin boka* danyasan  dakyarne aljana murjanatu tayarda da bukatarsa kuma gashi ance karyayimatà dakarfi saidason rantaa
Yanzukuma saiyasamu hanyarda zaibi danyashawo kanta cikin saukiii

Washe gari bayan khadija takarya hajiyar takiratà sukazauña cikin falon tasoma magana kamar haka khadija nàsandai kinsan dalilin kawokinan dayar uwarki tayi

Kafin mujekan gyara yanadakyau kisan wani Abu "" duk abunda zanfadamaki karkibar kodaya nafarko kikasance mace maiyawàñ ibada yinhakan Allah zaisake cusa soyayyarki axuciyar m[truncated by WhatsApp]
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠



Chapter 005
         By
Gentle Lady



Abu na biyu kuma tsafta ki kisance maiyawan tsafta kekanki zakifijin dadin jikinki idan kikajiki kina zuba kamshi dakinki yana kamshi

Turakar mijinki yakasance duk ranar girkinki kigyarashi kigoge abunda yakamata agoge kiwanke nawankewa kishare kisauya abunda kikasan yadace asauyashi

Kigyara ko ina kikunna turaren wuta toilet dinsama haka kiwanke kigyarashi"" sai Abu na uku kwalliya"" kikasance kinamai yin kwalliya dakuma kyalkyali duk abunda kikasan mijinki yanaso idan harkinyi abun zaiyi farinciki tokinuna kinfishi son abun duk shigarda kikasan mijinki yanaso tanadaukar hankalinsa tokirika yinta karkice waike kinajin kunya garin jin kunyarki zaki cutarda kanki

Kodakuwa kinaganin yagirme maki sosai aidakunya kiyi Abu gabansa inaso akoda yaushe kirika sakawa aranki da mijinki kike kuma tamkar danshekara ashirin kamar yadda budurwa zatayi da saurayinta kema kidauka kamar hakanne

Kar kunya tasaka ki cuci kanki kicuci mijinki" "" Abu na hudu girki karki kuskurah kibari wata katuwar mata tadafawa mijinki abinci inharma baki iyaba nizan koyamaki yata Amman karkibari mai aiki tadafa abincinda kikasan mijinki zaici

Koda kunada yawane mai aikin tadafa nagida namaigida kuma kitashi dakanki kidafa masa hakan zaikaramaki kima a idonsa

Menene amfanin mujinki yaji dandanon girkin wata banakiba bakida kishi kenan harmayarika santi idan mai aikinku ta iyah girki sosai"" nasandai bazaki rasa iyawaba Amman daya yau zamufara shiga kitchen dake in soma koyamaki

Abu nahudu iyah magana kikasance maitaushin lafazi idan kinatare damijinki yazamana yawan shurutuma baidamekiba duk maganarda zatafito bakinki yazama mai amfanice agunki dakuma shi"

Maganar kishiyarki kuwa babu ruwanki ke bawai dadyn kawarki bane koda ace matar tatabayin kishi da mamarki karkiji kunyarta kizage damtse kirungumi mijinki kinunamasa soyayya wacce baibata shan irintaba ki aje kunya agefe bayan yafita kidauko aburki dankunya adon yamace ne inafatar kingane bayanina

Khadija tagyada kai alamar tagane"" hajiya tarana tace yanzun bari mubarshi haka tashi muje daki zan nunamaki yanda akeyin kwalliya

Bamusu tamike suka shiga wani dakin kayane gasunan nakwalliya kamar hauka dakuma kayan sakawa tayi zaune tayimata kwalliya Yar ubansu sannan tawanke mata tace tasakeyi taganie

Dayake khadija tanada kai sosai saigashi tasake maimaita kwalliyar harma tafi wacce hajiya tarana tayimata

Aka koma bangaren dressing kuma kananun kaya suna karbar jikin khadija duk kalarda tasaka saikaga tasake kyau kamar daman dansaboda itah akayosu talkama masu tsinie damadai khadija bata iya sakasuba Dan takalmanta duka yan kasane flat"" ansha wuya kafin tama iya tsayuwa akansu

Kwana uku tanakoyon tafiya dasu saigashi ta iyah harma tanayin gudu "" dasu aka koma bangaren girki

Kullum sunacikin kitchen anakoyamata kalolin abinci saida suka kwashe sati biyu suna wannan aikin karkuso kuga khadija tayi jawur kamar kakwanta jini yafito saisheki take gabadaya gidan kamshintane dazaran tawurga zatabar tsarabar kamshi" cikin yan sati uku khadija tadawo ainahin khadija itakanta tasan yanzu tasauya ana saura kwana biyu takoma kaduna hajiya tarana tadauko maiyin Zanen lalli tayimata Zane Dan ubansu""  yayimata daskuwa ajikinta gashi janda akazana shima yafito das

Masu gyaran kaikuma suma sukayi nasu saikuma hajiya tarana tacigaba danata nagyaran jiki habawa khadija tasha dilka tasakeyin kyau ranarda zata tafi hajiya tarana tasa akayimata biza taxuwa kaduna dankarta shigo motar haya
.tasake jaddada mata komai tahadamata turaren wuta dakuma najiki dakayan mata data hadamata masu inganci tacekuma kartayi wasa dashan fruit ranarda zata tafi har airport hajiya tarana tarakata tareda kayanta duka dama acikin kudin aikintane akasiyo kayan da takalma

Khadija tarungumeta tanakukan rabuwa hajiya tarana tace haba yata yaufa ranar murnace kidaina kuka aibamu rabuba ga katina duk sanda kikaso ganina saikizo koki kiranie tawaya mugaisa""

Khadija takarba tana godiya sukarabu suna dagawa juna hannu hajiya tarana batabar wajenbà saida taga tashin jirginsu

Khadija kam tuni jikinta yayi sanyi tundasuka shiga jirgin tamakure waje daya harjirginsu yasauka Kaduna tashar adaidaita tadauka zuwa unguwarsu

Tundasuka shiga unguwar tasoma kalle kalle damadai bawani dadewa tayi cikintaba tunda bata taba fitaba tunda aka kawota saifa ranarda sukaje Dubai kuma amota suke Amman duk dahakan taga unguwar tayimata haske takara kyau kamarba unguwarba

Kofar gidan tacemasa yatsaya tasomabin gidan dakallo yana nan tamkar sabo daganie sabon fenti aka sake yimasa

Tadauko kudinsà tabashi tadauki kayanta ta tunkari kofar gidan taturah maigadine yayo zumut yatare kofa yace yammata lafiya ??? Kewaceçe kuma da izinin waye kikazonan

Khadija tayi murmushi tace baba wajen mom nazo yargidan nan labila Usman itace tabani sakodaga makaranta inkawowa mom

Yayi shiru sannan yace kintabbatar??? tasakeyin murmushi tace inhar bakayardaba zaka iyah sanarda mom din

Yace ah ah tundadai kince yarlele ta aikoki ainabari ki shiga inbasonake akoreniba yayi maganar yana budemata kofa yace afito lafiya tace tagode tasakai tabi hañyarda zata sadata da falon shiga gidan

Yan aikin gidan saibintà sukeyi dakallo sunga bakuwar fuska

Kaitsaye takutsa kanta cikin gidan tareda sallama lubabatu tana zaune cikin falon tahakimce tana kallo sallamarda akayine yasaka tadago fuskarta takalli maisallamar tareda amsa mata bawai dantagane wacce tayi sallamarba

Khadija tabita da murmushi tace mom sannu dahutawa"" bakisake luababatu tace yauwa Amman yata banganekiba"" khadija datake tsaye rike da akwatin kayanta takaraso gaban lubabatu tace mom nicefa khadija bakigane niba ina sahibata

Kafin khadija tarufe baki lubabatu tazama tatsaye taja baya dasauri tace karyane wakika taba ganin yamutu yadawo "" kinzama fatalwane

Khadija ta aje jakar hannunta tace kitabani kitabbatar nidin ba fatalwa bace tayi maganar  tana tunkararta aikuwa lubabatu takwamtsa ihu saigashi tasulale kasa asume

Dasauri khadija takarasa wajenta tana jijjigata saikuma tatuna damagar maimunatu lallai wannan itace kawai damarda zatasamu tashiga dakin lubabatu kafin ta farfado

Dasauri tajuya zuwa kitchen tadauro alwala tasamu wani cup tadibo ruwa tazauna tasoma yin addua acikin ruwan tsayin mintuna goma sannan tafito tasake kallon lubabatu tana nan yanda take batako motsi dasauri khadija tahau na urarda Zata sadata dakin lubcy tanazuwa taturah kofar tareda bisimillah tana .mai sallama kuryan dakin tawuce kaitsaye tana dube dube

Inama zataga madubin abunda Baka ajeba aibazaka daukaba Amman hakan tayita nema budacen leka cen hartakai kan drawer din karshe taturah hannu tabude kawai taga wani bakin hayaki yanafitowa tajikin kusuwar drawer din tuni khadija tamatsa baya gabanta yana faduwa duk da taji tsoro kawai dakewa tayi hayakin yatattara waje daya kafin yarikida zuwa siffarsa khadija tayi bisimillah tareda kabbara tawatsa masa ruwan adduar aikuwa watsawarta keda wuya take aljanin  yakwallà ihu Wanda yayi sanadin saka khadija toshe kunnuwanta take hayakin yasoma kamawa dawuta haryanzu baidaina kururuwaba zuwa cen hayakin yabace bat

Cikin tsoro tsoro khadija tabude drawer din saitayi Arba dakaramin akwati tadauko akwatin tayi bisimillah tana murda kwadon yabude

Saiga madubin cikin akwatin yana kyalli tamkar zinari hannu tasaka da addua tadaukoshi kasa ta ajeshi ragowar ruwan adduar tazuba masa

Saigawani bakin hayaki yana fita tajikinsa  take dakin yasoma girgiza yana juyawa ""Khadija tacigaba da addua saida hayakin yabace komai yakoma daidai sannan khadija tamiyardashi inda yake tamaida kwadon tarufe tasaka a drawer din tarufe sannan tafito dakin..

Hartayi gumie saboda tsoro haryanzu kirjinta baidaina dukan uku ukuba" tasauko kasan tasake shiga kitchen din tawanke fuskarta tadibo ruwa tadawo falon sannan tawatsa mata ruwan

Saiga lubabatu tatashi firgigit"" ganin khadija kusa da itah yasa tadaddage zatasake kwamtsa ihu khadija tarufemata baki tace haba mom menene na ihu nafadamaki Ban mutuba daraina mutanenda suka saceni sundauka namutu dasuka ganamun azaba saisuka yardani cikin wani dajie

Wadansu fulanine suke tsinceni sukakaini gidansu acen sukaimun maganie harnawarke kiyarda Dani danidin fatalwace aibazaki iyah tabaniba

Lubabatu dai saibin khadija taceyi dakallo kamar zararra khadija tasakarmata murmushi tace bari nadangyara bangarena nasan yayi kurah tayi maganar tanajan Jakarta tahau na urarda zatasadata bangarenta hawana hudu lubabatu tabita dakallo tahadiye wadansu miyagun yawu masu dacin gaske.. Batasan sanda tabarke d[truncated by WhatsApp]
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 006
        By
Gentle Lady💃🏽



Takunda khadija takeyi da takalmanta masu tsini suna amsa kuuwa kwas kwas kwas harcikin zuciyar lubabatu takejin takun

Zaune take dirshan tana darzar kuka hardasu majina wannan wacce irin hatsabibiyar yarinyace Usman yahadu da itah???ayimutum magani baikamashi tsafinta yazarta nata duk hanyarda akabi danganin bayan khadijar ace kuma tana raye ??

Indai hakane lallai *hatsabibin boka* yayimata karya dayace ankasheta dankuwa ta tabbata Wanda yamutu baya dawowa tomeyasa kuma khadija tadawo

Tadafe kanta lallai dolene tasan abunyi gashi yanxun rana tayi tsaka *hatsabibin boka* yahanata ziyararshi irin wannan lokacin dole tayi hakuri zuwa dare tacigaba da kukanta

Bangaren khadija kuwa tanahawa saman tasoma dariya dansosai lubabatu tabata dariya yanda tatsure kamarma harda fitsari tayi awando yanda khadija tayi Tsammani zatasamu dakin tada kurah saitaganshi fes alamu sun nuna akwaimaiyin  rayuwa acikin dakin

Aranta tace Kodai Usman aure yayi???🤔 Tayi saurin girgiza kai baxaizama hakanba danaji azuciyata tasoma bin dakunan dakallo kayanta suna  nan saikuma kayan Usman hakan yanunamata kenan dakinta yadawo tausayinshi yakamata

Afili tace Allah sarki hubbyna gani nadawo gareka kayanta tayimasu mazauni tahau gyaran dakin batawani jimaba tagama tunda bashida wani datti tafesa wanka riga da siket tasaka nakanti sun kama mata jikinta hula maitaushi da adon gashi kamar jikin mage tadorah akanta tayi mata kyau sosai tagabatarda sallar azahar bayan tagama. Laximie taninke abar sallar tasako takalmanta tasauko kasa

Falon tasamu lubabatu zaune amman yanzun tadaina kuka batadamu dakallon inda takeba tayi hanyar kitchen din tadauki duk abunda take bukata takunna gas tadorah dahuwar indomie cikin mintuna ashirin takammala tadawo falon tazauna tace mom bisimillah

Lubabatu wacce takebinta dakallo tace ah ah nagode kici abunki khadija batasake cewa komaiba tacigaba dacin abarta hartakoshi tamiyarda kayan kitchen jin ansoma kiran la asar tahaura sama

Bayan tayi sallah tazauna falonta batasake saukowaba hardaare bayan tayi isha"I tashiga toilet tasake Daukar wanka tadade tana tsara kwalliya sannan tajawo akwatin kayan lefenta kananun kayanda usman yasiyamata acikinsu tadauko tayita dubasu daibayan daya

Kowacce tadauko saitaga kamar batayiba saitadauko wata karshe wasu yan kantin tadauko Riga dawando wandon baikai kasaba dakadan yawuce guiwarta gefensa yanada wata yarsarka maikyau tana kyalli kamar zinari rigar farace mai Karamin hannu kamarna bes '' gashin kanta tataje dama yasha gyara bakin ribbon tadaureshi dashi saitakawo hula baka tadorah saman kanta daga sama tadan karkace hular gefedaya

Takalma farare tadauko masu matsakaicin tsinie tadauko turarukka tasoma feshewa ajikinta daidai lokacinda taji dirar motar Usman takalli agogo taga karfe Tara daidai sweet dinda hajiya tarana tabata tabude jaka tadauko daya taballe tasaka bakinta sannan tasauko tahau na urarda zata sadata kasan ******************
Tana saukowa Usman yana bude kofa lubabatu wacce takezaune tamike tana kallon khadijar cikin mamaki sam khadija batama lura da itaba
.
Ido hudu sukai da Usman yakuramata ido tundaga sama harkasa yake kallonta kirjinsa ya tsananta bugawa jakar hannunsa ta subuce tafadi hannunsa yana rawa yanunata dadan yatsa yace de de Deejarh na kece?? Kodai gizonda kikasaba yimunne.

Hawaye takeyi tanakuma murmushi tace hubbyna Deejarh nkace inanan daraina banmutuba nadawo gareka "" Usman yace dagaske ba mafarki nakeyiba farincikina ne yadawo tashare hawaye tanamai gyadamasa kai

Hannuwansa yabude yace taho gareni inji dimin jikinki deejah na danna tabbatarda hakan"" khadija taruga tafada jikinsa yagame hannuwansa yakankameta ajikinsa..

Saikuma tafashe dakuka maitsuma zuciyar mai saurare   "dasauri Usman yadagota daga jikinsa yana tambayar lafiya kumatunta sunarike cikin tafukan hannunsa idanuwansa shima sunyi jawur yace me.. Me...akaimaki Deejarh na Dan Allah kidaina kukan nan"" tadago idanuwanta masu zubarda kwalla tace hubbyna dole nayi kuka nayi kewarka sosai tasake rungumeshi tanacigaba da kukanta

Yasake kankameta kamar Wanda zaimiyarda itah ciki yace nima haka Deejarh na wlh nayi kewarki fiyeda tunaninki banada wani tunani bayannaki narigada nayi bankwana da farinciki ashedai zakidawo gareni nagodewa Allah yadago fuskarta dasauri yace inafatar basu cutarmun dakeba

Hawayen fuskarta sunazuba tace ai Allah baxaibariba soyayyarka itace tasaka haryanzu nakasance ina raye Allah bazaibari ba bazaitaba basu damar cutardaniba

Inasonka  sosai mijina"" I love u so much  hubbyna you are my persistence u are my life "" i really miss u dear tasake shigewa jikinsa murya narawa yace nima inasonki sosai Deejarh na please stop cry""

Shafar kanta yakeyi tamkar yar bebe Amman kukan khadija kamar cewa yakeyi takara"" dago fuskarta yayi dasauri kafin tayi aune tuni yahade bakinsu waje daya yasoma tsotsa kamar yasamu sweet """  idanuwansu arufe suke kowanne kirjinsa harbawa yake tuni khadija tadaina kuka sai ajiyar xuciya datakeyi tama manta wacce duniyar take

Hajiya lubabatu maikan doya 🙈tsaye take kamar mutum mutumie tuni tasandare jinin jikinta yadaina gudana kwakwalwarta tadaina aiki nawucin gadi gabadaya masarrafan jikinta suka tsaya chak

Usman da khadija tuni tsayuwa ta gagaresu Usman jikinsa saibari yakeyi kawai yasunkuce khadija yadorata akan kafadarsa yawuce sama"" itakuma tayi lamo akafadarsa baisauketa ko inaba sai akan gado yarufamata baya sukadorah daga inda sukatsaya to masu karatu aganinku *nizan iyah fassara adadin zumudin wadan nan ma auratan??? Musamman usman nasankoda nafada tokuwa zanfadi badaidaiba dankuwa zumudinda yake kodarenda yasoma sanin khadijar baiyi hakanba nikam hardariya yabani
Baiwani tsaya tambayarta ina suka kaitaba kawaishidai ayiharka

Kodayake yabanie tausayi tunda nasan halin lubabatu maikan doya""tunkafin aje ko ina Usman yasoma surutai da alamu bayama cikin hayyacinsa dasauri nafito najamasu kofa

Hajiya lubabatu kuwa tana nan kamar andasata saicen tazaburah kamar wacce tasuma tadawo taduba batagansuba aranta tasoma tunanin to yaushema sukabar wajen??

Take tasoma tariyo abunda yafaru akanta dalla dallah tagama tariyar har lokacinda Usman yahade bakinsa Dana khadija lokacinne wutar jikinta tadauke komai najikinta yadaina aiki"" sharaf tazube akan kujera kamar kayan wankiiii



*Gaisuwa dafatan al khairi agareku yan group din 🅿harty novels  (SUZ) sakonku  ya iso gareni nakuma gode da soyayyarku nima inasonku sosai " soyayya marar adadi Allah yabar kauna*


*Sauran masoyan wannan littafin inagaidaku musamman rabie da bilkisu "  fateema "miss zuhura"Aisha   shafa atu zurmie"  maryam" yar lele  dakuma anty ameena soyayyarda kukeyiwa wannan novel din bazai faduba damadai sauranku  fatana daya Allah yasadai basaboda nishadi kukesonsaba Allah yasahaka[truncated by WhatsApp]
[3/26, 8:34 PM] Nabila Elharun Q: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠



Chapter 007
       By
Gentle Lady💃🏽


*sakon gaisuwa zuwaga friends an novels group (S U Z) ina gaidaku baki daya nagode da soyayyarku*


Hannu tadora aka kamar wacce takeshirin kwallah ihu kilantama shidin taso kwallawa saikuma tafasa dankar tatonawa kanta asiri da alamu khadija batasan komaiba tunda bataga wani alamun dasuka nuna khadijar tagane itah ce tasaka akashetaba""

Yanzun kenan yazama dole tazuba masu ido ?? Ina bama zaitaba yiyuwaba babu wata yamace dazanbari tarabi mijina tayi maganar tanamikewa dasauri tahau na urarda zatakaita bangarenta hartanacin tuntube garin sauri

Tanashiga tanufachi inda madubin tsafinta yake tabude tadaukoshi tanamaiyin murmushin mugunta dantasan *hatsabibin boka* bazairasa mafitaba""

Shafashi tayi tare dakiran sunan hatsabibin boka "" tayi shiru tanajiran yabayyana har akashude awanni biyu babu alamar sa tace yahaka kodai wani abun yadaukemasa hankali barinabari sai anjima tasake miyarda madubin takoma gefe tabuga uban tagumie

Kamar wacce akece babanta da mamarta ne suka mutu"" hawayen bakincikene suka soma zarya akan kuncinta zuciyarta tanamai kuna da tususi kamar zatakama dawuta musamman idan tatuno yanzun Usman yanatare da khadija komesukeyima oho indai cin amanata yake wlh banyafeba😩

Al amarin usman kuwa yau harda kuka yayiwa khadija domin abunda baitaba jiba shiya tsinci kansa acikin yanayin sambatu kuwa saida khadija tarufemasa baki"" yaukam yadarji deejarn sa sonransa abunda lubabatu take hanamasa kamar wacce zatayi kwalliya dashi gashi yasamu saida yagaji dankansa yasaurara mata sannan yajata ajikinsa yana shafar sumar kanta saiga hawaye suna zuba sharr akan kumatunsa

Saida sukazubo ajikin khadija tadago dasauri takuramasa ido shima itah yake kallo yatsanta tasaka tana gogemasa hawayen tace
.
My hubby wannan kukan dakakeyi wlh sainaji kamar bakayi murna daganinaba" "" takai karshen maganar tana sanne  kanta kasa

Hannunsa yasaka yadago habarta yace kokadan bahaka bane karkibawa wannan maganar muhallin zama azuciyarki kisani Usman dinki yayi murna daganinki yakumayi farinciki

Farincikinda bazai faduba kukanda nakeyi najin dadije Deejarh na kinshayardani Zuma maimatukar dimautarda hankalin mai hankali narasama mezanyi nikaina dadin dayayimun yawa shine yasakanie kuka yasassauto da murya saitin kunnenta yaradamata kinada matukar ni ima Deejarh na hakika nayi babban dace danasameki""
.wata kunyace takama khadija tashige jikinsa tana nuku nuku

Dariya yayi marar sauti yace yanamai sake sakata jikinsa sannan yakirah sunanta Deejarh na "" tace na am batareda tadago fuskarta daga jikinsaba

Shimadin baidamuba Yace   suwaye waisuka saceki??? Dam gabanta yafadi anya karyarta zatashiga kuwa?? Gashi batasaba dayin karyaba saida tayi danjim tace wlh nimadai bansansuba

Inadaki bayan kafita sallah sainaji kamar kururuwar mom awaje shine nasauko akangado dasauri nafita waje naga menene yafaru

Dafitana sainaji kamar anbugamun Abu akaina" sainafadi nasume bansake sanin meke  faruwaba Ashe bayan suntafi danie saisukaga kamar namutu danban farfadoba saisuka yardani cikin jeji wadansu Fulani masu yawo sukaganni dasukaga inada rai suka daukeni zuwa Dan sansaninsu

Acen sukacigaba dayimun maganie harna warke saidai namanta komai sun tambayeni garinmu da sunana nacemasu banda suna  dasukaga kamar namanta tunanina sukacigaba

Dazama danie sunakuma banie maganie nawarke komai inayi kamar lafiyata qalau amman inada damuwa dasu da yayansu adda sukecemun taredasu nazauna hartsayin shekara biyu sai alokacin tunanina yadawo jikina

Tunda nabude baki sunanka kawai naketa ambata anan ne inna wacce itace  matar hardo "" tatambayeni wayekaidin nacemata mujinane """ tace ayya toyasunanki????? Nacemasu sunana khadija

Todayake sudin fulanin tashine kuma damadai jinyana kawai yatsaidasu dasukaga nawarke saisuka kaini gidan wata hajiya sukace inzauna nan kafin nasakejin sauki sainakoma gida

Sukatafi sukabarni dayake matar tanada kirki wajenta nazauna harna sake wartsakewa shine tabanie kudinda fulanin sukabata tabanie nadawo gida takai karshen maganar tana kallonsa

Kallonta yakeyi. Cikin tausayi yace sannu Deejarh na Ashe bakyada lafiyane kullum  cikin kiran sunanki nake azuciyata koda zuciyarki zataji kixo gareni Amman sainaji shiru

Ninasan basu kashekiba Dan inajin haka azuciyata shiyasa nakasa fitarda raina dasake ganinki Allah shine abun godiya wlh khadija nikadai nasan halinda nashiga narashinki akusa danie kowaye yadaukeki yacutarda rayuwata hisabi tsakaninmu saigaban Allah danbazan taba yafemasaba !

Khadija tsuru 😳tayi tana kallonsa aranta tace bakasaniba ai matarkace wacce kakeso kakeganin kamar babuwata maisonka sama da itah

Usman ganin takafa masa ido kuma tayi shiru sai yahurah mata iska cikin idonta take tarufe idon tana murmushi"" shima murmushin yakeyi Dan farincikin dayake cikinsa bazai faduba

Ahankali taradamasa katashi muyi wanka hubbyna" kanta yadago yace dani zakiyi wankan yau tarausayarda kai tace sosaima idanma kanaso inyimaka nizan iyah

Dariya yayi maidan sauti yace ainasan bazaki iyaba kodama kinyi kunya bazata barkiba tace hmm hubbyna kenan tobari kaganie mikewa tayi tasoma Jan hannunsa waizata tasheshi Amman ko motsi baiyiba sai dariya takemata wai tazama raguwa

Kukan shagwaba ta azamasa nidai katashi"" yana dariya yamike yace tokar amun kuka natashi kawai yasunkuceta sukayi hanyar toilet itakuma takwantarda kanta akan faffadan kirjinsa tare sukai wanka yasake daukota suka dawo dakin"" tashirya sukayi ra ka a biyu tanuna godiyarsu ga Allah sannan suka kwanta tana makale ajikinsa" wani sanyin dadine sukeji yana ratsasu hardai Usman ganinyau komai khadija tanayimasa  babatun kunya yace aransa dama idan kayi nesa damutum kukahadu jiyake kamar yacinyeka Allah yasadai Deejarh na tadaure dayin hakan yayimata addua sannan yasake janta jikinsa

Babuwani jimawa barci maidadi yadaukeshi Wanda rabon dayayi irin wannan barcin tunsuna Dubai da khadija mafarkai masu dadi masu kumshe da ni ima farinciki dakuma soyayya yaukam sunkusan makara saida habu yakirashi awaya yaji kolafiya yaubaitashi dawuriba

Dasalati yafarka yadauki wayar ganin habu Kuma gashi yaga lokaci yayi cemasa kawai yayi kuje ganinan zuwa yakashe wayar yasake watsa ruwa yadauro alwala yatashi khadija sannan yawuce

Bayan tayi alwala tayi sallah"tana lazimie Usman yadawo saman gadon yaje yazauna tashafa addua tamike tanade abar sallar sannan takarasa akan gadon

Saman jikinsa tazube tasunbaceshi akan labbansa tace morning dear"" hannunta yajawo tasake hayewa jikinsa yasagalo hannuwansa ta kugunta yarike yana kallonta yace antashi lafiya tarausayarda kai tace rasss makuwa indai annurin zuciyata yatashi lafiya""

Usman murmushin dadi yayi yace nikam ai kalaunake tunda inatare dake"" murya kasa kasa tace dagaske?? Yanda taimaganar saida tasaukarwa Usman da kasala yalumshe idonsa wadanda suka kankance yabude yanayin yanda yake kallonta kadai ya isah yagamsarda khadija yanayinda Usman yakeciki

Murmushi tayi tasake matsowa tahade bakinta danashi tana tsotsa ahankali kamardai yanda taga yanayimata"" Usman saiyakara susucewa yasoma aikamata da wadansu sakonni masu rikitarwa dakuma wuyar fassarawa khadija kanta tasan Usman yahadu bashida wata makusa gashikuma ya iyah soyayya duk lokacinda suka kasance atare yakan mantarda itah komai dakowa bataganin kowa agabanta saishi





Aisha✍🏼
[3/26, 8:34 PM] Nabila Elharun Q: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠



Chapter 008
         By
Gentle Lady💃🏽




Tanaji aranta inama Usman natane itakadai"" sundade suna faranta ran junansu sannan suka sake komawa barci

Wainikuwa nace Usman yamanta da lubabatu ne??? Hakanne kuwa wlh Sam yamanta da itah yadauka wata duniyar suke daban""

Zuwa kamar karfe takwas darabi  khadija tafarka ahankali tajaye jikinta dagajikin Usman taturah masa filo ganin zaisake rungumeta

Tasauko ahankali takoma daya dakin tayi wanka kaya maras nauyi tasaka tasa karamin hijab tasauko kasan bakowa hanyar kitchen tanufa tasamu kukunda yake dafa abinci yazo yana jiran lubabatu  tasanar dashi abunda za agirka

Saiyaga bakuwar fuska"" tashigo takalleshi tace morning"" yace morning Anty"" batareda tasake kallonsaba tasoma hada kayan da zatagirka abinci

Ganin hakan yamata magana anty me za ayi yau" tadan yatsina fuska tace katafi kawai idan mom tanada bukatarka Zata nemeka yace okay yasakai yafita abunshi

Khadija tasoma fire doya tadora awuta sannan tahau gyaran kayan ciki"" tacire anta daban tayankata kana na2" tadora tafasarta daban " tasamata magi da gishiri bamasu yawaba

Lubabatu tanacen dakinta tunjiya dadare taketa Shafa madubin tsafinta Amman shiru babu bayanie karshe madubin yana hannunta  tana kuka barci yadauketa"" garin barci tasaki Dan madubin yafado kasa yawatse""

Batasan yafadiba sai kwasar barcinta takeyi abunta"" khadija kuwa doyar tanayin taushi tasaukar da itah"" tareda antar tayi lubus"" kwai tafasa tanika tattasai da tarugu kadan ta zuba ciki sannan taxuba antar aciki""takara murzashi yadargaje tasaka kayan dandano"" sannan tadorah ferfesun kayan cikin tadan matsamasu lemun tsami kadan tazuba ruwa dakayan miya batasa kayan kamshiba tamiyar tarufe

Tadorah  tasar tuya tazuba mai"" dayayi zafi tarika tsoma doyar acikin ruwan kwan masu anta saita jujuyashi sannan tadibo daruwan kwan da hantar tazuba acikin tallen haka tayi hattallen yacika dayasoyu tajuya

Tuni kamshi yasoma gauraye gidan"" kayan cikin bayan sun taso sau biyu sannan tazuba kayan dandano Dana kamshi""

Usman yasake juyi yasake makale filo saiyaji yalotsa ahankali yasoma lalubar filon yatabbatar shidinne yadaukeshi yawurgar yasoma lalubar khadija baijitaba zunbur yatashi zaune yasoma saurare kotana toilet ne kuma baiji saukar ruwaba mikewa yayi yawatsa ruwa

3quarter baki yasaka dakaramar Riga ja mai karamin hannu"" yataje sumar kansa yafesa turare sannan yafito sauran dakunan yasoma lekawa ganin haryanzu bata dawoba Amman bataciki""

Sauka yayi kasa tunkafin yakai yasoma shakar kwamshin girki yalumshe idonsa"" Sam baiyima tunanin agidansa kamshin yake tashiba" yasauko falon baigantaba"" sai ya tunkari kitchen din"" bakin kofar yatsaya yajingina jikin kofar yarungume hannuwa yana kallonta Batasan da zuwansaba saida kamshin turarensaa yadaki hancinta

Tajuyo ido tadan turo tace badai harka tashiba"" ??? Harararta yayi cikin wasa yace aidole kice hakan""kintaso bada izininaba shine harda turamun filo ko anfadamaki jikinki daidai yake dafilo"" tace todakumafa??? Yace aijikinki yafishi taushi

Dariya tayi  tajuya tana motsa ferfesun tace sorry hubbyna banaso katashine bangamaba"" takowa yayi zuwa indatake yadorah kansa akan wuyanta yashaki kamshin jikinta yalumshe ido yace kimmanta yau weakened ne bazanje ko inaba"" kodama ba weakened bane banajin zan iyah fita nabarki hutuma zanyi konasati biyune inmaida jikina

Dariya khadija tasamasa tace waikana nufin karame?? Ganin nawa zaisaka kamaida jikinka" murmushi yayi maidan sautiii yace sosaima kuwa aikinsan mutum yanacin abubuwan Gina jiki masudauke da  vitamins calcium tyrosine dasauran abubuwanda suke gina jiki Toni kodanacisu abanzane danbasuda sinadarin

Kece kawai kikeda sinadarinda duka kayan marmari basudashi danni banga amfaninsu ajikinaba

Khadija tace kadai fada"" yace kuma dole ayardaba kusan taresuka sa dariya" tace kaganie kanaxuwa nasoma shiriricewa

Yace bakuma zantafiba saidai mukwana anan munayi nimafa na iyah girkin nan bari kiganie "" tace kabarshi karka bata jikinka yace aiga kayan aikinan baki sakaba kema yajawo wata drawer saiga rigunan dayawa wasuma cikin ledarsu ba ataba sakawaba"" yadauko biyu yacirosu aledar yasaka daya

Itama yadauramata tanacewa dama kabarshi nida nakusan gamawa"" yaharareta yace munkusan gamawa dai ina taremukai girkin nan

Tace hakane kam munkusa gamawa da surutunka ba yayi dariya yace aiyau zakuci abinci maidadi tunda nasaka hannuna"" baridai inhadamana tea dannaga bakiyiba"" yayi maganar yana kunna wani gas yawanko tukunya yadorah yazuba kayan yaji daruwa da Lipton yarufe tana gefe tana kallonsa

Yajuyo yakalleta yadaga mata girah yadai kallo haka waikindauka nidin ban iyah komaiba babu abunda mace zata nunamun sai Abu daya"" yayi maganar yana dariya kasa kasa tasan abunda yake nufi dariyar itama tayi tace aiho ashedai akwai abunda zamu nuna  maka dasauki to

Yace hakane kam bazanyi jayayya ananba" yace wainikuwa ina kukun gidan nan dakika shigo kitchen bakiga yanda momyn Abdul takeyiba""

Tace naganie tomenene ranar hannuwana  idan nakasa dafawa mijina abunda zaici banason kanacin abincin kukun nan dakaina zandinga yimaka """

Kallonta yake yanasakin murmushi karasawa yayi wajenta dasauri yarike kugunta yadagata yana juyi da itah yasakar mata kiss yace ashedai nidin dan lelene bansaniba Amman naji dadi sosai shiyasa nake kara sonki

Dariya tasomayimasa shima dariya yake lubabatu wacce tunda tafarka tsarabar kamshi yadaki hancinta tataso afusace dantadauka kukune yadorah abincin kuma tafadamasa karya sake yadorah girki inba ita tace ga abunda takesoba

Tana kawowa kafarta taji talake ganin Usman dinta yana juyi da khadija acikin kitchen suna dariya wasu hawayene masu zafi suka saukomata gashi jiya tasha kuka fuskarta duk ta kunburah nikam nace yi aniyar hawayenki sukare

Ganin kamar zasu juyo taja kafarta dakyar takoma falon tazauna tadafe kantaa"" tanajiyo dariyarsu harcikin ranta""ga takaichin madubin ta yafashe gakuma takaichin Usman da Khadija dayarufeta harsuka gama girkin suka zuba komai acikin kula sukadauko sunafirah ta soyayya suka jerah saman dinner Sam basu gama lubabatu ba khadija tagyara kitchen din Usman yana gogewa

Kitchen din yayi tsaf kamar ba ayi aiki acikinsaba"" sukacire rigunan suka fito yana rike dahannunta harzasu wuce yaga lubabatu zaune tadafe kai hannun khadija yasaki yace yasalam meyake damunki yayi maganar yana zama kusa da itah yadago fuskarta ganin yanda takumbure

Yace meyasamu idonki haka lubcy"??? Murmushin yake tayi tace bakomai kainane yakeyimun ciwo tunjiya" Usman yace haba lubcy shine bakisanar daniba

Tasake murmusawa tace bakomai naga kanatareda Amarya kuma kundade Baku haduba banaso nakatsemaku jindadinku""

Yayi murmushi Allah sarki matata shiyasa nake kara sonki yayi maganar yana janta jikinsa "" khadija juyarda kanta tayi gefe saboda takaici Usman yalurah dahakan yamike yace bari muyi wanka kema kishirya sainakaiki asiviti

Tace ah ah dama kabarshi yace kinsanfa banason musu kitashi tace to yajuya wajen khadija yanayin yanda tajuya kanta yabashi dariya saidai bayaso yadara yasakata kuka

Hannunta yariko yace mujeko harararsa tayi tawuce yabita dasauri taruga tana dariya yana cinmata yadauketa yahau mataka zuwa bangarenshi

Lubabatu tabisu dakallo jitakeyi kamar taje tarufesu da duka"" saida suka dade dawucewa sannan tamike tahau saman tayi wanka tashiryo hartadawo dasu fitoba tazauna jiransu gashi tanajin yunwa

Ajima a jima saitakalli hanyarda zasufito tajatsakie tanajiyo dariyarsu asaman"" takai akalla mintuna goma zaune sannan suka sauko shigar shadda sukayi iri daya tunna aurensu

Itama lubabatu shaddace Amman ba irinsu dayaba khadija rigarta doguwace anfitarmata da shefdin jikinta tamkar ajikinta aka kero rigar""

Suna zuba kamshi khadija tace mom sorry mundan Dade gashi bakida lafiya"" tayi yake bakomai khadija tayi maganar tana mikewa suka karasa saman dinner khadija tazuba kowa nashi itakam da Usman tahade nasu

Sukasoma ci babu Wanda yasake magana harsuka gama khadija takwashe kayan "" yace tadauko mayafinta tarakasu

Tace ah ah katafi nizanyi aikine"" yace tarezamu dake kibari idan mukadawo natayaki aikin"" batasom sutsaya musu tajuya tahau saman

Lubabatu tace meyasa kakesoñ tilas tamata abunda batayi niyaba"" yamatso kusa da itàa yace lubabatu bakisan yanda nakejinta ajikinaba banajin dadi idan banajinta kusadanie

Lubabatu tarufe idonta tabude saboda radadin maganarsa tayi danasanin tambayarsa"" shikuwa Usman baidauka wai zataji  haushiba

Shikam iyakar gaskiyarsa yadauka bataji komaiba har khadija tafito lubabatu tayi gaba shikuma yatsaya  kallon khadija tare suka jerah koda suka kai yabude kofar gaba lubabatu tace khadija tazauna itah tazauna baya

Khadija tace ah ah mom bayan nakeso kafin lubabatu tasake yin magana har khadija tabude baya tashigà








Aisha✍🏼
[3/26, 8:34 PM] Nabila Elharun Q: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠



Chapter 009
        By
Gentle Lady💃🏽



Usman yace kishiga to muje tarufe kofar tashiga gaba"" shikuma yazauna mazaunin drever yatada motar maigadi yabude masu kofa yana gaida Usman yace adawo lafiya

Hannu yadaga masa sannan suka fita "" madubin motar yasaitashi tayanda zaidinga ganin khadija itama shitake kallo suna hada ido yasakar mata làllausan murmushi""

Kiss tayi tahura masa "" shima yamiyar mata yanamai lumshe ido cikin murmushi "" itama tamiyar masa""da  martanin murmushinsa  duk tsiyarda sukeyi lubabatu tana kallonsu lallai wannan yarinyar bariki kawai takoyo waima  wannan khadija ce???

Yarinyarda tasanie tanada kunya sosai Amman yanzun tafitsare idanuwanta agabantama komai yitakeyi tayi kwaba ai wlh bazan zuba miki ido kinayin abunda kikaga damaba abundama mijina baiyimunba"" keyana maki yarinya kamar aljana""

Tanata sake sakenta sukuwa daga nesa suke aikawa junansu sakon soyayya harsuka kai hospital din yace khadija tajirasu amota bayaso ana kallonta"" yakunna mata Ac  wayarsa takarba"" takwanta jikin kujerah tana latse latse sukuma suka wuce

Kowannan maganar takona ran lubcy waibayaso ana kallonta watoga zinariya"" tanagaba yana bayanta suka karasa dakin doctor

Khadija lambar wayar labila takamo tanasoma ringing akadauka da alamu barci ma take tace hello""

Khadija tasaki murmushi tace Assalamu Alaikum zunbur labila tamike tana mutsuts tsuka. Ido "" saida khadija tasake maimaita sallamar sannan labila tace muryar wanakeji kamar sahiba???

Khadija tace nice mana labila"" sai labila tafashe dakuka tace kina ina sahibata Dan Allah kifadamun

Khadija tace da wayar wakikaga nakira??? Labila taciro wayar akunnenta takalla tamiyar tace wannan number dadyce ai

Khadija tace to ina tare dashi"" labila tace dagaske ganinan zuwa" khadija tace dakata karatun fa??? Tace wlh bazansake kwana daya agarin nan ba kedai kawai sainazo batajirah jin mezataceba  takashe wayar tahau shirin kaya""

Khadija taciro wayar ajikin kunnenta tana murmushi sannan takamo lanbar ya muktar farinciki fal ranta tasoma kiran layin harta tsinke baidagaba saida tasake kirah sannan yadauka

Yakara akunnenshi tamkar Wanda bayason magana shikanshi duk yarame dankullum cikin tunanin yar kanwarsa yakeyi sallamarta dayaji tasashi mekewa cikin farinciki yace sapna kece kuwa??

Dariya takeyi tace nice Yayana kana ina??? Yace shekaranjiya nabar kano  Amman ke kina ina"" tace inatare da dady cikin kaguwa yace sapna kina duniyar nan Amman kika kasa nemanmuko?? Tace Yayana kaima kasan inhar inacikin jindadi dole na nemeku saitabashi labarin yanda tasamu kanta kamar yanda tafadawa Usman yatausayawa kanwarsa sosai

Yace yana nan"" tafe shima Dan yanason ganinta yagasgata lamarin tacemasa saiyazo sundanjima suna magana ganin su Usman sunfito yasa taimasa sallama

Taresuka kawo bakin motar yabudemata tashiga shima yazagaya mazauninsa yana kallon khadija yace dawa dawa kika Kira??

Tace kai hubbyna bafa waya nayiba"" yanda tayi maganar kamar wata Yar yaye yabawa Usman dariya lubabatu kuwa guntun tsaki taja Wanda babu Wanda yaji sai itah datayi abunta

Yace ainasan wayakikai tunda naga fara a tayawaita afuskarki "" tarausayarda kai tace ya muktar kawaifa nakirah sai sahiba

Yace dama ainasani" tace kumafa tace tana nan zuwa yau zatashigo jirgi"" yace haba aidole ainasan itama tayi kewarki Nisam namanta ko hajiya bansanarwa dawowarkiba inacikin zumudi

Yayi maganar yana kanne mata ido daya motar yakunna suka hau hanya wajenda ake siyarda maganie

Yasiya mata maganie suka wuce gida"" yanayin pkng khadija tafito tayi cikin gida saida yafito yabudewa lubabatu suka wuce tare yana mata magana Dan Allah maman Abdul kicire damuwar aranki tunda gashi tadawo aikomai yawuce ko""

Tace hakane aibakaji dadin danajiba wlh murmushi yayi  yace bakikainiba ai daidai sunashiga gidan harsama yarakata yadibomata ruwa tasha maganie sannan yakwantarda itah yanabata labari harbarci yadauketa sannan yajaye jikinsa daga nata yajamata kofar yafita

Bangaren khadija yanufa yashiga yanakarewa dakin kallo waidaga zuwansu hartashiga tayi gyaran daki ko ina yayi fes yana zuba kamshi

Tana bandaki tanawanka saboda yanayin zafine tafito daure da towel"' tana goge jikinta tacee harkafito?? Yace ah sarkin aiki harkinyi garanki bayankuma nace kijirah natayaki"

Tace nahutardakai kwanta kahuta"" rigar jikinsa yacire yace saimunyi wanka" tace saidai kayi wanka aini nayinawa towel yadaura kawai yasunkuceta yayi toilet yana cewa ban yarda dawan nan wankanba aiwayo kikamun

Bayan kibari sainazo muyi tare tana dariya tahau zillewa tacee kasaukardani to"yace abahon wankaba zatasake magana yahade bakinsu waje daya

Tanata hum hum hum bahalin magana tafito sai cikin bahon wanka yasakata har towel din"

Yatara ruwa shima yashiga tasha mur wai itah tayi zuciya yakura mata ido ruwan yadibo yawatsamata afuska ta kyalkyace da dariya tadibo itama tawatsa masa  saisuka koma wasar ruwa sundade kafin suyi wanka sannan suka fito basu Shafa komaiba suka kwanta suna  makale dajuna barci yadaukesu

Sai kusan karfe biyu suka farka khadijace tafara tashi saida taje tadora abinci sannan tatasheshi yayi sallah ita ma tayi suka je kitchen din tare dama jelof din shinkafa tadora danganin sun makara

Tace wainikuwa meyake damun mom??? Cikin alamun tausayawa yace mata jinintane yahau saboda tunani

Tace tunanin lafiya hubbyna metanema tarasa?? Yace kemana tunanin batankine yasakata adamuwa"" khadija tace ko??🤔
Yakalleta bangane koba bakiyarda bane??
Tace nayarda mana aibansan harhaka takesonaba yace toyanzu kinsani ai tace Allah sarki itakuma tata kalar soyayyarce tazodahaka"" 🤔

Usman dabaisan dawon garinba yace aikuwa nitausayima takebani wlh kinga yanda tadamu lokacinda kika bata kullum cikin kuka take Khadija tamere baki kawai saida abincin yanuna takwashe tahadamasu lemun kwakwa"" sannan suka jera kayan yatafi tashin lubabatu danyasan batafarkaba.

Khadija kam wani wankan tasake fesawa tasaka kananun kaya tana fesa turare Usman yashigo yace tundazufa muke zaune kekadai muke baikarasaba sauran maganar ta makale abakinsa yace wow

Masha Allah kinganki kuwa"" yakaraso inda take dasauri"" "" tagama nade gashinta tace tomuje"" jawota yayi yana shinshina yace muje ina kibari nabiya kudin kwalliyar nan mana""

Tace ah ah nayafe yanzunfa kace kunajirana da mom zataga mun Dade ai"" tayi maganar tana jaye jikinta daga nashi

Yace haba Deejarh. Yanzun rowa zakimun inaji inaganie??? Tarausayarda kai tace kasan bansababa Amman ai yakamata kaji uxurina akwai anjima aiko

Yatsuke fuska ainasan da anjimar nifa baburuwana datana jiranmu barito nacemata taci nata "" ta gwalo ido tace kukuma kuyi mene??? Yace karatu kawai zankaramaki saimuje muci ko""

Tace nagode dawan nan bitar dannituni nahardace komai kazo mutafi Dan Allah kamin ranta yasosu"" hannunta yariko yace haryanzu baki fuskancetaba nasan bazataji komaiba Deejarh

Takalleshi da mamaki tace hakane dayake itadin batada kishi toni yunwa nakeji Tanakai karshen maganar tajaye hannunta daga jikinsa tafita aranta tanacewa bakasan damuwar matarkaba dai

Usman bakisake yake kallonta yagirgiza kai sannan yafita koda yaje harsun soma cin abinci dagayya yasaka chokalinsa cikin abincin lubabatu yanaci waishima saiya sosawa khadija zuciya kamar yanda tasosa masa

Illai kuwa khadija taji haushi Amman tagano yayihakanne dagayya saikawai tashareshi" tacigaba dacin abincinta tamadaina kallonsu

Lubabatu kam ganin hakan saitasoma Jan Usman dafirah shima yabiyemata" khadija kam tamiyarda hankalinta wajen cin abincinta

Saida takoshi tamike tadauke plate dinda tabata takai kitchen tafito tayi hanyar dakinta"" Usman tagefen ido yake kallonta sai hadiyar yawu yakeyi

Lubabatu talurah dahakan aranta tace nimafa Na iyah barikancin nan yarinya idan kinsan wata bakisan wataba indai dawadan nan kayan kike rudar Usman nima zandinga sakasu inga karyar bariki

 Tsaki taja Wanda yasaka Usman juyowa dangabadaya yakarkata kansa wajenta. Damamaki yace lafiya menene yasakaki yin tsaki???
.
Waiyau wace rana lubabatu takasa boye kishinta" kamar jirah take ya tambayeta saikawai  tafashe dakuka yace yasalam menenekuma Dan Allah karki tayarmun dahankali yajata jikinsa yana rarrashinta

Yace me akaimaki matata Dan Allah kidaina kukan nan yana konamun zuciya"" cikin kuka tace yanzun kadaina so nane ko??? cikin sauri yace wayafadamaki akwai ranarda usman zaidaina sonki???

Aiduk wacce zanso bayanki take"" lubabatu dankenafara sokamin wata"" Amman meyasa kikace haka??? Nayimaki wani abunne dabakiso??? Kifadamun banason nacutardake koda cikin rashin sanine







Aisha✍🏼
[3/26, 8:34 PM] Nabila Elharun Q: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 010
       By
Gentle Lady💃🏽


Taja nunfashi tace neyasa kakeyimun haka nalurah tunsanda yarinyar nan tadawo gabadaya hankalinka yakarkata zuwa gareta menene kakeso ajikinta Wanda nibanidashi
.
Dankawai kanaganin ina kauda kaina bashizaisa komai kanayi agabanaba nimafa inasonka kuma dole inyi kishinka tunda nima macece"" takai karshen maganar tanasake fashewa dakuka nikam nace takarewa lubcy🙅🏻 tundahar tafurtawa Usman tana kishinsa

Sosai yaji tausayinta lallai kuwa tayi hakuri sosai yace kiyi hakuri bansan abun nan zaibata maki raiba aidabazan yiba Amman zankiyaye bazan boyemakiba lubcy

Wlh duk sanda khadija tabar inda nake jinakeyi kamar tareda zuciyata tatafi gabadaya zanrasa natsuwata sainajita akusa danie Amman nibabu abunda takedashi Wanda bakidashi"" aransa kuwa yace akwai abubuwa dayawa Amman bazaiso ranta yasosuba yanda itama tanuna masa halacci aiyadace yayi mata" sosai yaso yaje wajen Deejarh danfa soyake yabiya kudin kwalliyar nan Amman yanajin nauyin tashi badan ransa yasoba" yazauna suna taba fira saida akai la asar yatashi yayi alwala"" dakin khadija yawuce yaturah kofar yajita arufe yagirgiza kai kawai yafita zuwa masallaci

Khadija kuwa tun lokacinda tabarsu takoma dakinta tarufe kofa takwanta tunanine falranta sosai tanason boye kishinta badan komaiba tasan muddin lubabatu talurah tanada kishi zatayi amfanie tawannan hanyar danta muzguna mata Amman duk yanda taso taboye kishinta akan Usman takasa tana kwance wani barcin yadauketa

Sai lokacinda Usman yaturah kofa sannan tafarka tayi sallah tasauka kasa tadorah girkin dare"" lokacinda Usman yadawo sallah yanajin motsi kitchen yasan khadijace kaitsaye yanufaci kitchen din dama kofar bude take

Tabakuma kofar baya tana yankan alayyahu"" saman drawer din yahau yaxauna yana kallonta"" uffan batace masaba tacigaba da abunda takeyi"" shima baicekomaiba saidai binta dayake dakallo yana murmushi" bayan tagama dorah ruwan tuwon tazuba shinkafa tahada komai namiya tawanke hannunta tafita abunta nan tabarshi zaune

Mikewa yayi yabi bayanta"" tanaganin hakan tasoma sauri taresuka kai kofar dakin taturo kofar zata rufe yatura da daya hannunsa saiga khadija tayi baya zatafadi yatarota dahannu daya" tajuyo daniyar magana suka kurawa juna ido

Hancinta yaja yace bakida karfi meyakaiki rufe kofa"" murguda masa baki tayi tace narufe din nika kyaleni"" tayi maganar tana tashi daga jikinsa shikuma yaki sakinta yaja ta sai kuryan dakin damadai yace saiya biya kudin kwalliyar tuni khadija tamanta dakomai sukacigaba da soyewarsu

********************
Karfe goma jirgin su labila yasauka Dan adaidaita tahau zuwa gidan yana sauketa tabashi kudi dasauri taja kayanta tashige gidan tana kwalawa khadija Kira

Khadija tamike tsaye cikin fara a dagudu suka rungume juna saisuka fashe dakuka Usman da lubabatu suna kallonsu Usman tausayi sukabashi itakuma lubabatu haushi sukabata saima tadauke kanta daga garesu""

Sundade suna kuka akarasa Wanda zai lallashi wani khadija ce tasoma rarrashin labila ganin takidaina kukan tamike taja hannunta sukahau sama"" saman kujerah tajata suka zauna

Khadija tace kidaina kukan nan Kawata komaifa yawuce tunda gani nadawo ban mutuba"" labila tashare hawaye tace Amman suwaye suka daukemunke?? Khadija tace Allah masanie kinjidai yanda nasamu kaina tabata labari kamardai yanda tafadawa Usman

Labila tace shegu sosukai rubani dake Allah yafisu wlh banyafemasuba dansun cutarda zuciyata"" khadija ta ce hardake hakan zakice to hubbyna yarigaki..

Labila takwashe da dariya tace habadai yaushe kikahau hanya"" 🤔khadija tace zauna nan ainiyanzu saidai inkoyardake"" 😉

 saiyanzu labila taga kayanjikin khadija tamikarda itah tasoma  kallonta sama dakasa takwashe da dariya tace kinyimun daidai banmusha 💁🏻suka taba..

Usman sunajiyo dariyarsu kamar al mara"" labila tace Amman waye yaciremaki wannan kunyar??? Khadija tayi fari da ido tace hubbyna mana keya karatun???
..
Labila taja hannunta suka zauna tace bawani dadi wlh sahiba inacikin matsala" khadija tace matsalar mene sahiba??? Tace hmm tunani mana bakiga yanda na lalaceba shekarata biyufa acen Amman duk akai jarabawa sainafadi danbana iyah rubuta komai..
.
Damuwa tayimun yawa kema kinsan bamatare hankalina bazai kwantaba tundanaje bandawoba saibikiñ uncle hafis

Khadija tace waikina nufin yayi aure???

Labila tace sosai kokina nufin bai isah ba aini naga yadadema baiyi aureba"" Khadija tace nibance yayi sauriba nasodai ina nan akai bikin inason zuwa kano wlh

Labila tace tosaibiki kishirya gobe mutafi saidagacen ma kiga matar"" kusa da layin mu gidansa yake babuwani nisa

Khadija tace kinaganin hubbyna zaibarni natafi nimafa banason inyi nesa dashi"" labila tayi dariya tace keyar nan yaushe kikazare har haka???

Tayi farr da ido tace ran talata sukasake darawa tace bari nadebomaki abinci yaufa akwai labari labila tace mujeto tare suka sake fitowa labila taradamata akunne tace kinja kayafa wlh bakiga yanda kike tafiyaba har magana suke aidole kiruda babana daidai suna saukowa ""

Khadija tace Abu dole yakika ganie tayi maganar tanawata tafiya maidaukar hankali labila tasaki baki tana kallonta Usman shima baki bude yake kallonta labila tace wow wlh kina burgeni sahiba suka tafa atare suna dariya khadija taja hannun labila dasauri suka shiga kitchen tarufe bakinta tace ke wlh Sam namanta hubby yana falon nan nayi wannan tafiyar
Labila tace toshine me ni wlh bakiji yanda kika burgeniba gabadaya kintafi da imaninsa kinayifa aini hakan nakeso tawan

Khadija tace nifa mom nakeji aisaita daukeni marar kunya labila tace saime ina agidanki kikeyi bawajeba kinga wlh danice nasamu wadan nan mazaunan sake turosu zanyi"" haka zanrika tafiya labila tasoma tafiya tana murguda duwawu khadija mezatayi inba dariyaba "" sosai tabata dariya itah batada duwawun Amman tadaddage taturosu

Khadija tace baridai mukoma daki kinji tazuba abincin tadauka suka fita labila tace dansakeyin tafiyar mana"" harara tamaka mata tace bazanyiba

Sukawucesu tamkar basu gansuba" dakima sai surutu suke har labila tagama cin abinci tawatsa ruwa tace sahiba rakanie inje inkwanta nasan kinmatsu kije wajensa""

Tace waima nifa yau tarezamu kwanta shiyaje wajen mom"" labila tace wlh baki isah ba baban nawa zakijawa ajie dolefa kitashi yarinya kitafii

Taja hannunta jeki kiyi wanka inrakaki dakinsa"" ganin khadija tatoge labila tatasa keyarta saida tashiga wanka tadawo tafitomata dakayan barci masu sharara taciromata after dress
Tafeshesu da turare

Khadija tana fitowa labila tace kiyi saurifa kishirya gashi har shabiyu dakwata"" tayi maganar tanafita

Khadija tabita dakallo kawai tashirya bawata kwalliya tayi maiyawaba yar simple ce tasaka kayan barcin"" tadauko sweet dinta tasaka abaki sannan tadorah after dress din Asama takalma masu tsini tasaka tasake feshe jikinta  da tirare tafito labila tace haba kokefa kinga yanda kike daukar ido kuwa "" muje wlh nikaina barci nakeji tayi maganar tanajan hannun khadija suka sauka zuwa hawa na biyu

Bakin kofar tabarta tace asha soyayya lafiya sahiba saida safe tawuce tana dariya bangaren lubabatu tanufa" Khadija taturah kofar da sallama Usman yana zaune saman kujera yana danne danne dantun kokacinda su labila sukahau saman yaji duk bayawani sakewa yanagudun kar khadija tace tareda labila zata kwana basuwani jimaba yayiwa lubabatu saida safe danyanada aikinda zaiyi

Saida yayi wanka yayi shirin kwanciya yadawo falo yazauna yana danne danne ga laptop"" Amman gabadaya hankalinsa yana wajen khadija jiyakeyi kamar yatashi yaje dakin Amman bazai iyah ba labila yakejima kunya

Yana cikin sake saken yaji takun takalmanta saida yasaukarda  ajiyar zuciya"" yacigaba da abunda yakeyi saida tayi sallama saubiyu sannan ya amsa batareda yadagoba"" tsayinta tayi bayan tarufe kofar""

Bayan kamar mintuna biyar baiji takarasoba saiyadago yakalleta itakuma saita dauke  kanta takama hanyar dakinsa tacire after dress din tafiya take maidaukar hankali dajan ra ayin maikallo tuni Usman yakulle laptop yabi bayanta""

Bayani yasha banban korafinda Usman yaso yayi natabarshi shidaya tuni yamanta dashi"" bayan sunyi wanka suka kwanta asuba tagariiii

***********************

Washe gari da labila suka hada  abun break bayan sungama sukai wanka sunacin abincin labila tacewa Usman dady kano zamuje da sahiba taga matar uncle tunda batanan akai bikin""

Yakurba tea yana kallonta yace zaki koyamata yawoba shekaranjiya daga dawowarta" " tace kai dady itafa tacemun  tanason ganinsu malam kumafa ya muktar shima yazo shine nacemata tabari saimuje tare"

Yallalli agogon hannunsa yace shikenan kushirya saimuje tare nima inason ganin hajiya akwai maganarda zamuyi Amman dakuzandawo bazaku kwana acenba"

Tace haba dad"😩 khadijace ta zungureta ta waigo takyapta mata ido alamar tayi shiru tace shikenan dad zamudawo taren"






Aisha✍🏼
[3/26, 8:34 PM] Nabila Elharun Q: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠



Chapter 011
        By
Gentle Lady💃🏽


Lubabatu dai batace masu cikankuba "" harsuka gama cin abinci suka shirya Usman yace idan tanazuwa tataso suje tace ah ah sutafi kawai tana gaidasu haka sukafita labila tazauna baya sukuma suna gaba sunafara tafiya tadauki wayarsa takirah ya muktar tace gasu ahanyar kano dankar susha banban"" yace yanzun kuwa yake shirin fitowa barito yajirasu taka she wayar ta ajemasa

Basujima dafara tafiyaba khadija tasoma hamma alamun barci takeji hartasoma gyangwadi "" jawota yayi takwanta akan cinyarsa"" tacigaba da barcinta

Harsuka kai kano batasaniba kofar gidansu khadija dad ya tsaida motarsa sai lokacin  tafarkà muktar kuwa yana bakin kofar suna tsayawa khadija tafito dagudu tafada jikinsa suna dariya yace sapna waisai yaushe zakisan kingirma

Daidai Usman yana kawowa yace bana tsammanin yanzun saidai inta haihu"" muktar yace hakane dad  khadija kam dariyama suka bata basusan tadade dahaihuwaba "" yaduka yagaidashi Usman yamika masa hannu suka gaisa

Yayimasa yahanya"" yace alhamdulillah nan sukaiwa juna barka da dawowar khadija usman yace shizaiwuce wajen hajiya  susameshi cen

Yashiga motarsa yaja labila tana tsaye saida khadija tawaigo tace mekikeyi anan kuma sahiba tace bakomai takaraso tace ina kwana ya muktar yace kalau yagidan

Tace lafiya atakaice "" takalli khadija tace barinawuce gida kigaida inna"" khadija tace yahaka bazakishiga bane nifa banason fi ili""

Labila tace nidai sako nabaki malama saikinzo"" tayimata gwalo tawuce abunta muktar yabita dakallo kasa kasa shima yadauke kansa wani gefen Na zuciyarshi yanamasa radadi

Saiyaushe zai sanarda labila sirrin zuciyarshi .. ??? Sam batadamu dashiba tana nuna halin ko inkula duk lokacinda zasuhadu shikuma  maganar nauyitakemasa bayaso yafurta sirrin zuciyarshi dagakarshe tace batasonshi""

Gauran nunfashi yaja yace Allah kasa labila tasoni koyayane taji abunda nakeji"" Khadija tace yadai Yayana??? Baki yadan tabe yace bakomai mushiga  dagaciki kafin tasakeyin magana haryawuce tabi bayanshi

Gidan cike yake tamkar anabiki gwaggo hassana da Husaina dayaransu sulaiman dahiru duk sunagidan yauko malam. Baifita kasuwaba"" jin khadija zatazo dama tunda muktar yadawo yasanardasu sapna tadawo

Zokuga murna kamar zasu hadiyeta sai nan nan akeyi da ita muktar gefedaya yakoma yana sauraren firarsu Amman zahirin gaskiya tunaninsa baya wajen

Tunaninsa yanawajen miskilarsa sunanda yasaka mata kenan awayarsa saikayan number dinta yakeyi yakan kirah idan tadauka  sallama kawai yakeyi yayi shiru tayita magana yana sauraren muryanta saitagaji taja tsaki takashe wayar

Kuma itama takasa goge number awayarta duk da Batasan Wanda yake kiranba" amman muryansa tanayimata dadi sosai "" miskili itama hakan tasaka awayarta sosai tasaba duk ranarda baikiraba saitajita wani iri

Tana kokarin cireshi aranta danbataso tasaba alqawarinda tadaukarwa sahiba cewa kowannensu shizai zabawa Dan uwansa miji Sam hankalin muktar yabar jikinsa tunowa yayi datsiwarta yayi murmushi

Su khadija sundauka yana biye dasune basusan yatafi wata duniyarba sundade suna firah muktar yadauko mata wayarta dazata tafi gidan hajiya taresuka fita suna tafiya tacemasa ya nikam intambayeka

Kallonta yayi yace inajinki"" tace kataba zuwa Niger wajen dangin mama??? Yace ah ah meyafu ??? Tace kawai inason  zuwane" murmushi yayi yace aganinki zasu kalleki kitunafa mahaifiyarmu ma batasamu kallon arzikiba"

Khadija tace nasani Amman insha Allah inada burin zuwa" yace shikenan nidai bazan hanakiba idan mijinki yayarda kije daidai sunkai kofar gidan tace yaushe zaka komane???

Yashafo sajensa yace gobe zankoma aiki yanajirana wlh haka nadauki Hutu dannazo naganki dayake banine kawai mai duty ba

Tace shikenan aitunda gawaya zamurika waya akai akai"" yace shikenan sundan jima suna  firah tace bari tashiga yace to yajuya itah kuma tashiga gidan

Cikin falon tasamu hafis da Usman da hajiya suna firah tagaidasu sannan tamike tashige dakin labila

Kwance tasameta tana kallon silin da alamu tunani takeyi duka khadija ta danamata acinya saida tasa kara tamike"" zatayi magana kenan wayarta tasoma ringing takalli khadija takalli wayar

Khadija tace me nakallona kidauka mana""  labila tadauka takara akunnenta"

Muryansa maikashe mata zuciya taji taratsa dodon kunnenta "" amincin Allah yatabbata agareki annurin zuciyata"" wani dadine yaratsa zuciyarta talumshe ido tabude tace taredame magana""

Ajiyar zuciya yasaukar mainauyi"" daganan shiru yabiyo baya"" takatsemasa tunani dacewa dan Allah wayekai??? Kuma meyasa kake damuna dakirah duk sanda kakirah bakayin magana komadai kai mugune aniyarka tabika tana kaiwa karshen maganar taja tsaki takatse kiran ""


Khadija tayimata kuru dayan idanuwa tana kallonta"" tace sahiba"" waima waye yake kiranki inadai ba saurayi kikai a skull dinkuba dankinsan wlh nayimaki miji tuntunie

Tayi chilli dawayar tace kishare banmantaba sahiba aike shaidace banakula kowa wannan dinma wlh bansan  kowayeba yakedamuna dakirah

Kuma kodanadauka iyakarsa  sallama bayaga hakan bazaisake cewa komaiba"" Khadija tace dama yadaina wahalda kansa danni nagama zabamaki miji"" tayi maganar tana kwanciya

Batajima dakwanciyaba barci yadauketa labila tanata zubamata surutu Batasan tayi barciba"" saikusan la asar labila tatasheta sukaci abinci 

Sanñan sukaje gidàn uncle hafis matarsà Hafsat tanada fara a gasoñ mutañe sundade sunafirà sannan sukàmatà sallama sukafito

Khadija takoma tayiwa su innah sallama harbakin mota muktar yarakata badan komaiba dankawai yasake ganin labila Amman tunda tagansu tare tayi saurin shigewa motar yayiwa Usman sallama sukawuce yana kallon su harsaida yadaina ganin motarsu labila tana kallonsa tajikin madubinda yake gaba nakusa da khadija

Ranar kam Usman tareda lubabatu yakwana"" washe gari tasaka kuku yashiryamasu girki Sam Usman baiwanici dayawaba dankwana biyun nan khadija tabatashi dagirkinta hakadai yake daurewa yanaci

************
Bayan watanni hudu abubuwa sunfaru dayawa lubabatu duk ta lalace khadija kuwa tatika kiba Sam batahankalto cikine da itah ba batawani laulayi kamar dai cikinsu hassan
.Usman ne dayaga yawan barcinta yayi yawa gaci kamar gara yamatsamata saida sukaje asiviti ana aunata akace tanada juna biyu nawata hudu zokuga murna kamar Usman yalasheta ranar kowa saida yasamu labarin khadija tanada ciki""

Kulawa babu irin wacce batasamu daga bangaren Usman labila batabarin tayi komai yanada wata bakwai   cikinta yayigirma sosai   kamar gobene  zatahaihu " tafiyama dakyar takeyinta

cikin khadija yana wata Tara tatashi da nakuda Usman yadauketa hankali atashe suka garzaya hospital batawani dadeba tahaifo yaranta uku daya namiji biyu mata"" wayyo dadi

Usman dadi duk yakumeshi lubabatu tunda tasamu labari tace shikenan khadija takwace gidan saiyanzu takedana sanin mahaifarta da akacire

Daga asiviti gida akawuce da itah tundasukam amatsayin haihuwar fari suka dauka"' labila ta tattara kayanta takoma gidan hajiya Usman makusan kullum yana hanyar kano'' "" alokacin lubabatu tayanke shawarar zuwa taraba

Amman bata sanarda Usman ba dantasan cewa zaiyi watasani acen"" cemasa tayi zataje gidansu sajida" tunsafe  yana fita dama tayi biza jirgin karfen bakwai tabi danbataso takwana acen

Amman takasa gane ainahin dajinda yake dankomai yasauya agarin rabonta da dajin anfi shekara ashirin"" haka takarace yawonta tashigo jirgi tadawo gida raibace dankuwa tayi bakinciki kuma batason tatambayi su sajida bataso suyimata dariya Dan basusan tanazuwa wajensaba haryanzu
Cika bakinta duk yazama nabanza kenan

Aganinsu tahanya suka haduda Usman bawai wajen boka tatafiba sukam basuje wajen bokaba dansamun mijin aure saidai dasuka yi auren sun karbo Na mallaka dakuma wanda baida ikon yimasu kishiya iyah nan suka tsaya

Amman kullum idan suna tareda lubcy cemasu takeyi itah Usman natane mezaisama  tawahalda kanta zuwa wajen boka domin tasa amallakeshi sukan jinjina mata toyanzu idan har tatambayesu

Sunsamu abun dariya ranar Usman kano yakwana bagidaba"" Dan saurah  kwana biyu suna""washe gari lubabatu itama tashirya tatafi tunda tunranarda akatafi da khadijar bata komaba

Tahada kayan jarirai kala arbain duka amatsayin tata gudunmuwa"" saiyabonta akeyi gawanda baisan halintaba Amman labila da khadija ahankade suke kallonta""

Sai dare tabaro kano takoma kaduna"" ana gobe suna muktar yazo kayanshi kawai ya aje yayi dakin inna inda khadija tace bakinsa har kunne waiyanzu kanwarsa tahaihu kuma har Yaya uku""

Labila tana rike da macen khadija tana zaune biyun suna akan gado muktar yayi sallama idonsa sai akan labila wani sanyin dadine yaratsashi yakasa dauke idonsa akanta!"

Tare suka amsa masa sallamar wa alaikumus salam""" gefen gadon yazauna saiyanzu labila tadago suna hada ido tadauke kanta tace sannu dazuwa ya mukty""

Yace yauwa "" yagidan tace qalau tamike ta aje jaririyar tace sahiba bari naje gida anjima zandawo"" khadija tabata fuska tace haba kinsanfa magana mukeyi gashi gobe suna bamu tanadi komaiba

Tace sahiba komai dazaki bukata bazaiyi wuyaba idan naje gidan yanzun zankirah dad infadamasa sai asiyo bajima zanyiba ai zandawo

Khadija tace dan Allah kizauna sahiba nifa banason kitafi "" harararta tayi cikin wasa tace inakekike  da kafafuwana toyunwa nakeji aikyabari incika cikina

Khadija tace yanzunfa inna takawo abinci kikace kinkoshi kedai kinsan abunda kikewa gudu labila tace toyanzu naji yunwar barimadai naje na karbomana dinki

Tanakaiwa karshen maganar tajuya tafita muktar yabita dakallo"" ransa yana sosuwa shibaisan meyasa duk lokacinda yashigo yasamesu tare saitatashi

Wata zuciya tace kaine batason ganie" yayi saurin kawarda zancen dankarma yasamu muhalli azuciyarsa









Aisha✍🏼
[3/26, 8:35 PM] Nabila Elharun Q: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 012
       By
Gentle Lady💃🏽




Khadija takalleshi tace yadai ya muktar"? Yanisa bakomai Kanwata yayi maganar yana Daukar hassan yace sannu sapna kinyi kokarifa haryara uku

Murmushi kawai tayi sannan tace kaga kyautar da Allah yabamu mamana zata samu takwara saimukirah ta sapna tunda naga  kanason sunan nan

Kamar kinsanie dannima idan nayi aure yata tafari sunanki zansaka mata sainakirata sapna
Khadija tace sunan baiyi yawaba murmushi yayi yace kokadan ""ya aje hassan yace to acikin wadan nan wacece babba???

Dariya yabawa khadija tace nima bansaniba katambayi dady"" kada kansa kawai yayi yace zangane dakaina""  tatambayeshi ya aiki yace Alhamdulillah " sukaci gaba da firarsu


Labila batasake dawowa gidan ba saidare tashigo dakayan dinkin su gwaggwo hasana sunata hadin miyar buki tayi masu sannu da aiki sukace yauwa  tashiga dakin khadija tasameta tanacin tuwo kusa da itah tazauna tazube kayan hannunta

Khadija tace saiyanzu kikadawo"" hannuwa  tayarfar tace wlh bakisan yanda mukai da telan nan ba saida nayimasa rashin mutunci kinga rigunanda yamana?? Aisaida nasaka yabudesu natsani insa Riga inji tamatsemun jiki waishi zamanie saiyabari sainayi aure yayimun irinsu idan mijina yanaso koni banason  Dan kwalliyar gida zansaka masa

Khadija tace gwadamun naganie nidai banason katuwar Riga inyita rawa acikinta Yar daidai nakeso" labila tabude tasoma nuna mata""

Ba laifi sunyi kyau"" labila tace gasunan dai kigwada idan basuyiba tunda safe inmiyar nikwanciya zanyi barci nakeji wlh "" tadauke su husaini tamiyardasu akan gadonsu takwanta babu jimawa barci yadauketa""

Innace tashigo da sallama khadija ta amsà tace tataso kawunta yana kiranta"" tatashi tabi bayan innah batajima da fitaba muktar yashigo dakin baigantaba harzai fita yahango tauraruwarsa tana barci ido yakuramata bayako kyaftawa"" tana barci tamkar tana murmushi takowa yayi kusa da itah yazauna"" wani dadi yakeji aransa motsinda yajine alamar za ashigo yasaka yatashi dasauri Yakoma wajen gadon su hassan khadija ce tashigo tace ah Yaya yaushe kashigo??

Yace yanzun nashigo bangankiba"" tace dama kayan barkane inna takiranie inganie"" yace ainagansu dazu Amman khadija kiyimasa magana yadaina kashe kudi haka ai abun yayi yawa

Tace toyazanyi najima kawu yayimasa magana aini naga kokayanda mom takawoma sun isah" yace Hakane samun wuri yayi yazauna sunafirah yana satar kallon labila sai shabiyu saurah yayimata saida safe yayi dakinsa

Yaukam yayi barcinsa cike da soyayyar labila dazaran yarufe idonsa itah kawai yake ganie
****************
Washe gari suna hassan yaci sunan mahaifin Usman Adam anakiransa anwar sai Husaina fateema anakiranta sapna" saita ukun binta sunan hajiyar Usman anakiranta husna""

Biki kam yayi biki maijego saishiga dafita takeyi su labila kam ba a magana duk da batawani sakewa Dan duk inda tawurga saitaga ya mukty""

Bangaren lubabatu kam batayi taron komaiba"" kamarma ba abiki danbata gayyaci kowaba kawayenta mabasusan da haihuwarba

Kwance take tunsafe "" taji kamar ana sallama tamike daga kwancen tana Jan tsaki tasauko kasa wacce taganie ce yasaka tasaki fara a tace wanake ganie kamar khairat??? Itama dariya take tace nice mana"" kinga nasakene

Lubabatu tace karaso saman mana"" wacce akakirah da khairat tahau na urar zuwa sama sukashiga falon lubabatu""

Khairat Kawar lubabatuce  unguwarsu daya a Lagos tariga lubabatu aure haihuwarta daya tunda tayi aure suka tare india batasake zuwaba saibayan lubabatu tayi aure

Kuma tadaxo gidan taretake da mijinta basuwani jimaba suka tafi yanzun tsayin shekara biyu kenan da dawowarsu katsina dazama Dan mijinta Dan katsina ne"" lubabatu takawomata ruwa tazuba mata tace ya hanya"" khairat tace alhamdulillah nazo wajen wani bukine nace bari nabiyo mundade bamu haduba kinsan bancika zama kasarba

Lubabatu tace hakane ina kikabar anisa?? Tace tana America wajen karatu kwanan nan takeshirin dawowa "" " lubabatu tace su aneesa anzama yanmata ni aikonaganta baxan ganetaba

Tace gaskiya kam rabonki da itah tuntana Yar shekara daya yanzun aitasake kamannin mahaifinta  "" duk sunfito ina labila da Abdul"?

Lubabatu tamere baki tace Suna kano kinsan yaune sunan matar babansu"" khairat tace banganeba waikina nufin maigidanki yayi aure harkuma matar tahaihu???

Lubabatu tace ah yara uku tahaifa mace biyu namiji daya"" khairat takalleta sororo tace kuma kike kwance kinashan iskan fanka???

Anya lubabatu kedince danasani?? Kinfini tsiya dakomai Amman harkika bari mijinki yayi aure hartasamu gindin zama tahaihu?? Kinbata wayonki wlh

Nantake idanuwan lubabatu suka kawo.ruwa maison kukane akajefeshi dakashin awaki antonowa lubabatu inda yakeyi mata kaikayi"" khairat tace waikina nufin kuka zakiyiwa kishiya??? Aibakiga komaiba wlh gashi yanzun kintsufa mijinki yasamu yarinya danya sakaf kekuma zaizubaki kwandon shara mekika tsayayi Kawata baki kada yarbanzaba?? Kodayake nasan kedin bakyazuwa wajen boka

Lubabatu tace haba kawata  kalleni kiga yanda na lalace kema kinsan duk abunda kikaga yasakani nayi sanyi yafi Karfina

Tatari numfashinta tace banganeba akwai abunda zaigagari boka Kuwa saidai idan bakizube kudiba"" tashare hawaye tace Kawata kudin ayanzu sunkasa yimun rana yarinyar batajin maganie kuma wlh takaimun intaha harsawa nayi akasheta Amman daga karshe saikuma tadawo yanda kikasan aljannune sukayi rainonta

Khaitar tace bagaskiya bane gunwanne bokan kikaje??? Lubabatu Tanisa tace sunansa *hatsabibin boka* taraba yake kuma shi ka idarsa inhar kafara aiki dashi bazaka sake zuwa wajen wani bokan ba naje dajinda yake nakasa gane wurin

Khairat tace aiwannan zancen banzane"" dakudinka harsai anyimaka yanga saikace shine Kadai boka tobari kiji inada wani boka danake zuwa wajensa aikinsa kuwa shayanzu maganie yanzu take yanke bukatarki zatabiya ammanfa saikinzube masa shegun
Akan kudikuwa wlh bashida mutunci danmuddin yayimaki aiki baki bashi cikon kudinsaba zaijuye aikin zuwa gareki Amman nasan kedin baza asamu matsala taban garenkiba dankinadasu

Lubabatu tayi shiru daga bisanie tace nifa tsoron sharrin *hatsabibin boka* nakeyi wlh bashida imani zai iyah kasheni muddin na je wajen wani bokan"" tace kimanta dawani *hatsabibin boka* tunda yakasa kisake wani indai zakiji shawarata nidanake hulda da bokaye Kusan biyar duk Wanda yamun aiki baiyiba wani zansake Abu dakudinka harsaikayi yanga

Kamar kinshiga kasuwane kowa yabaje hajarsa aiwacce kikeso zakisiya ko anamaki Dole" kinga kawai kisaka rana kisameni katsina nakaiki wajensa nibanason naga Wanda nakeso yashiga damuwa

Lubabatu kam tanajin tsoron *hatsabibin boka* kuma tanason akawarda khadija khairat tace mekikace??? Lubabatu tace to to shikenan saikibanie address din gidanki dazaran angama komai zansameki saiki kainie tunda kinga yanzun bakowa gidan idan nafita za a iyah zargina

Khairat tasaki fara a tace yauwa yargari kokefa saina ganki takai karshen maganar tanadauko ruwa 
Tasha"" tace ammanfa koda munje karki nunamasa kintaba zuwa wani gurin kedai kawai aiki kikeso ayimaki kuma zai iyah







Aisha✍🏼
[3/29, 10:13 AM] YAYA HAYAT: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 013
        By
Gentle Lady💃🏽


Lubabatu tace Indai dan wannan aibanda matsala indai kinsan aikinai zaiyi shikenan nayarda komai zakice"" khairat tace yauwa tawan kokefa Amman kinazama ace kishiyarki Yaya uku wannan zurare kamar akuya""!

Lubabatu tace kemadai kyafada wannan kafin aje ko ina zatacika gidan tana haifo uku uku kumafa karkiso kiganta kamar lagwanie wlh suka kwashe da dariya tace shikuma mijinki kome yaganie atattare da itah inba jaraba tada namijiba""

Lubabatu tace aidama itane"" bari nakawo maki abinci" khairat tace ah ah kibarshi yanzun zandaga sauri nakeyi tayi maganar tana mikewa kedai sainaganki ina zuba ido

Lubabatu tace insha Allah zakiganni aini dama zanice ta tararda mujemu wlh yandakikasan akan kaya nake nakijinin nabuda idona naga wannan yarinyar sainaji kamarma inshakureta kowa yahuta"" 😕

Khairat tace basaikin wahalda kankiba Abu da komai yacigaba kedai saikinzo harbakin kofa tarakata sukai bankwana azuwan saitazo sannan tadawo dakinta farinciki fal ranta saiga lubcy harda barcin rana Wanda rabonda tayi irinshi tunranarda khadija tadawo gidan""
Khadija sunacen sunacin buki Batasan anacen ana shirya yanda za a gama da itaba"" gaskiya taron sunan yakayatar da mutane anyi abubuwan rabo tundaga bokiti kwanduna darduma turame agogo shaddodi  jikkuna "" dadai sauran kayan rabo"" anci ansha kowa yazo bikin yakwashi gara bakamar yan group din Haneefa dannaga dayawa cikinsu amarorine"" an iyah zuwa biki kodakuwa ba a gayyacesuba😝😝

Labila kam karshe gidan hajiya takoma wajen mama kubrah dantagaji dayawan kallonta da muktar yakeyi itah tanaganin kamar kallon rainin wayo yakemata shikuma yanaganin kamar tsabar wulakancine yasaka takewani dauke kai duk sa inda taganshi

Tarodai yayi alhamdulillah kowa yawatsa anbar maijego da ya"" ranta saimuyi mata addua Allah yaraya matasu"
Muktar kwanabiyu dasuna yakoma""  khadija sosai tana tausayin mijinta dantasan yanayinsa kwanansu ashirin tacewa innah zatakoma  duk da nauyinda takeji Amman inna batakawo komai arantaba

La akarida yawan zuwanda Usman yakeyi saitaga kamar danshine khadija ta tausaya mashi"" innah tace tadankara hakuri agama shiryamata kaya nanda kwana biyar

Tundaga ranar akasoma shiryata anasaurah kwana bakwai suyi arba in su gwaggo hassana suka miyarda itah" ranar Usman kamar yahadeta Dan murna

Khadija tamatsawa labila takoma makaranta hakanan zaman bazaiyimata ba tashafe shekara gida tace itah karatu indai batareda khadijaba tayafe

Khadija tace tosaidai idan aure zakiyi"" kuma tace bayanzuba saida sukayi fada khadija tayi fushi sannan labila tayarda Amman akaduna zatacigaba da karatun tarika kwana agida

Khadija tace batayardaba "" labila tace to Zaria fa??? Ko kano"" khadija tace zabidaya saitayanke shawarar zuwa A b u Zaria

Cikin sati daya akagama komai tasoma zuwa lubabatu kamar hakan takejirah tatambayi Usman zataje gidan sajida kawai tawuce katsina batawani sha wahalaba ta gane gidan khairat din dayake ba boyayye bane mijinta kumagidan akan hanya yake

Da sallama tashiga gidan babban gidane tangarere kamar wani Karamin kauye

Khairat tana falonta ta amsa sallamar mai aikinta tanayimata tausa tace tatashi tacewa mai sallamar tashigo

Tace to tareda mikewa tafita tagaida lubabatu sannan tanunamata inda uwardakin nata take

Takaràsa tanamai sakeyin sallamar"" khairat ta amsa fuskarta tanakallon maishigowa


Tana ganinta tawashe  baki yarhalak kenan yanzun nagama zancenki axuci nace shirudai kodai kinsauya shawara""

Lubabatu tanazama akan kujerah tacire mayafinta tace shawaradai aisaidai idan harmutuwa nayi Amman daraina dalafiyata aibanida wata Mafita wacce tawuce wannan""
Khairat tace babu kam bari nasa akawo maki ruwa kisha idan kinhuta saimuje lubabatu tagwalo ido tace wanne irin Hutu aisauri zamuyi inkoma nafadamaki banaso idon kowa yasauka akaina afara zargina

Khairat tace totashi muje damadai nidin ashirye nake muje yanzun ma baza asamu jirah sosai wajensaba dakinta tashiga tadauko mayafi sukafito

Takwalawa mai aikinta kirah talatu""" dasauri tarugo tafadi gabanta tanahaki tace ganie rankiyadade"" tayatsina fuska zandanfita bajimawa zanyiba kafin nadawo kitabbatar kingama hada abincin idan alhaji yadawo kikaimasa Nashi kuma kicemasa banisa nayiba dankaryafita harsaina dawo

Sauran kuma naje nadawo natarar kinbarshi da yunwa taran kwasheta  aka tashi kibanie wuri tadafe kanta tamike dasauri tabar wajen khairat  tatofarda yawu tareda Jan tsaki tace mujeko hajiya

Lubabatu tabita suka wuce tunkafin tashiga mota maigadi ya hangame masu kofa danyasan halinta idan ranta yabaci ba Karamin aikinta bane ta gaggaurah masa mari babu ruwanta da tsufansa""

Motarta suka shiga taja atsiyace tawuce yagada mata hannu Allah yakiyayeki hajiya guntun tsaki taja tabadeshi da kurah su lubabatu kam tazama Yar kallo gaskiya wannan yaburgeta sosai itama yakamata tasoma shinfida milkinta agidanta kowa yadinga jin tsoronta

Duk da mijinta yafi mijin khairat kudi nesa bakusaba Amman ita ko maigadon gidan baya tsoronta tunda tunfarko batanuna masu hakanba Amman zatasauya taku kodan surikajin tsoronta har uban gayyar

Ahakan zatasamu ta tatattare kadarorin Usman tasoma kasuwanci harsuka kai dajin bokan lubabatu batasaniba saida khairat tace kifito munkawo sannan tahankalto tafito sukasake nausawa cikin jeji

Dayake lubabatu tasaba ganin makamancin irin wannan dajin koma Wanda yafishi abun tsoro da abun al ajabi Sam bataji tsoron dajinba

Sai hawan duwatsu sukeyi wani gurin dajan duwawu suke wuceshi danbahali kataka dakafa"" bakin wata katukar kuka suka nufa khairat tacewa lubabatu sucire takalmansu

Taresuka cire sukasoma tafiya da baya baya harsukai kai wajen bokan ya umurcesu dasu zaune sukazauna shikam wannan yasha banban da *hatsabibin boka*

Bayada wani jiki sosai saitarin suma akansa kamar rumbum kara"" hakoranshi jawur duk sundafe saboda cingoro dakuma kazanta kayan jikinsa duk sunyage saikace matsiyaci duk ina kudinda yakesamu

Ace war lubabatu Dan *hatsabibin boka* baida wannan kazantar"" fadarsa kawai abun kalloce Amman wannan cikin kogon kuka saidan wani daki dayayi agefe nakasa" karami kamar bandakie

Lubabatu tayinisa wajen karewa wajen kallo muryansa maikamada kukan jaki taji yace meke tafedaku??? Khairat  tace tsafi yakara maka lafiya kajima kayi karko Kawata nakawo akan batun kishiyarta kamar yanda nafadamaka
.
Yagyada kai sannan yadauko wata katuwar kwarya akwai ruwa acikinta kamar ruwan jinie yakalli lubabatu yace saka hannunki nahagu

Jiki narawa tatsoma hannunta yayi wadansu surutai da tsifface tsiffacensa daga bisanie yace tacire hannunta"

Tacire yace yasunan kishiyar takie??? Tace khadija mijinkufa??? Tace Usman""

Yayi Zane saman ruwan sannan yakalleta  yace yakikeso ayimata, ?? Lubabatu tagyara zama tace ran boka yadade nidai inson samunane akasheta daga itah har yaranta""

Yajinjina Kai sannan yasakeyin rubutu yashafe yasake yinwani zuwa mintuna kadan yarufe idonsa yasomayin wadansu surutai yana girgiza kai tsayin mintuna biyar sannan yadago duk yayi jibi kamar Wanda yayi wasan tsere yakalli lubabatu  wacce tamatsu taji mezaice idanuwanta zuru zuru kamar wadda taiwa sarki karya



Kuyi hakuri dawannan wlh banda chaji yau. idankuma NEPA tadawo kafin dare zakujinie








Aisha✍🏼
[3/29, 8:28 PM] YAYA HAYAT: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 014
       By
Gentle Lady💃🏽



Yace gaskiya aikinki yanada wahala" kuma akwai hadari sosai acikinsa" lubabatu takallikhairat race  bana fadamakiba "" ai wannan yarinyar tunda ta Gagari hats""

Khairat tayi maza ta zungureta tace ranboka yadade asake dubawadai ataimaka mata kawatace"" yajinjina kansa sannan yasake yan tsiffacensa yace wanan yarinyar dakuke ganie gabadaya jikinta haskene aiki da irinsu yanada hawalar gaske Dan aljanu ma Kansu tsoron rabarsu sukeyi intakaima aljanie yamatsa bashakka zairasa rayuwarsa

Wannan yanuna koda tanajinin al ada bataxama sakaka kullum cikin Neman tsari take danhaka kasheta gabagade bazai taba yiyuwaba saidai akwai wata mafita daya idan kinji zakibita meyiyuwa zata bulledake

Tunkafin lubabatu taji menene mafitar tace nidai komenene ayi indai zatamutu banda Matsala"" bokan yajinjina kai yace hanyar itace zanbaki wani garin maganie nagubar aljanu"" kibarbada mata kofar dakinta

Saiki koma gefe kikirata kilabe dazaran tafito tataka maganin koda kadanne tozata fadi awajen tayita mulmula"" shikenan zata tashi kamar bakomai saidaga baya zatarika jin kaikayi ajikinta

Duk inda tasosa kurji zaifito dazaran kurjin yafashe ruwan suka tabi jikinta wasu kurajen zasu sake fitowa kuma idan tabarsu zasurika girma harsu zamemata gyambo

Tarika wari yanda kowama baya iyah zuwa wajenta dagakarshe ciwon zai kasheta kinga kinhuta Amman ki kula karkibari wani yatsilga maganin indai  ba ita ba zaisake magana tace kwantarda hankalinka aibana kuskureba!

Yace kinason mai makari kokuma Wanda baida makari??? Tayi saurin Tatar nunfashinsa tace wanne irin makari ai makarinsa mutuwa boka aini banason tawarke yace shikenan an gama ammanfa aikin nan yanada wahala sosai"" danhaka zakibada kudi tace banda damuwa dasu nidai bukatata tabiya yace an gama yadaga hannunsa sama yaruntse idonsa yasoma wadansu surutai marasa dadinjin bamakagane meyake fada"" saiga wani kullin maganie yafado ahannunsa cikin wata Leda yake sannan angefashi cikin battar kwarfe yamika mata dahannun hagu yace kirikeshi karkisake yataba hanun dama harsaikin kai gida  kina iyah aikidashi yau kogobe Amman dazaran yawuce kwana biyu yatashi aiki kikula karkibari wani yaketara inba itaba danduk Wanda yatsilga shine zaiyi wannan jinyar kodakuwa kece

Lubabatu tace Allah mayakiyaye intsilga tsawa yadakamata yace ba a kiran sunan Allah anan " khairat tace tuba muke boka batasaniba bakuwar zuwace

Atsawace yace ta aje abunda tazodashi subacemasa daganie jiki narawa lubabatu tazuge Jakarta tazubemasa kudin duka suka mike yace kutafi dabaya kuna tsalle jiki narawa suka juya suna tsalle gashi lubabatu katuwa da itah nan take tasoma hakie saida suka daina ganin kogon kukar sannan sukajuya

Wannan karon wajen haye duwatsu lubabatu harda kuka danta wahala wajen tallen nan"" suna kaiwa gunda khairat ta aje motarta suka shiga suka kama hanya""

Sunata nosawa cikin jeje Ashe dajin yanada nisa bata lurah da hakanba saiyanzu kamar dagasama sukaga tarin ayarin yanfashi

Hantar cikin lubabatu takada tace yanfashi darana tsaka??? Kafin tayi aune taji sunharba bindiga take khairat tataka burki babbansune yadaka masu tsawa yace kufito jiki narawa suka fito

Akace sukwanta suka kwanta duwawun lubabatu sai mazari sukeyi tunda take bata taba ganin bala I irin wannan ba babbansu yabada umurni aduba motarsu komai akaganie adauko

Dayake basuzo dakudiba kudin khairat daine dasukasamu dubu hamsin"" dawayoyinsu daya dagacikin yanfashin naga yaje wajen ogan yayimasa rada akunne

Yayi dariya yace kahuta usher"" aisunacikin ganiyarmu" kahole kawai"" Wanda naji ankira da usher yakalli lubabatu yace tatashi Sam Batasan niyarsaba tamike yatasa keyarta cikin wata bishiya maiduhuwa yace tacire kayanta

Idanuwa kulu kulu😳 tace ban....ban.. gane incire kayanaba mezakamun"" cikin muryarsa tamashaya yace ke hajiya zakitubene kosainayi maki takarfi idan bakiganeba kibari nizan nunamaki yasoma zuge wandonsa

Saiyanzu lubabatu tagano abunda yakenufi tafashe dakuka😭 taduka harkasa tace karufamun asiri wlh bantabayin iskanciba banama ra ayin wannan arayuwata konawane nizan baka Amman kabarni natafi

Yace ke hajiya bamagiya nakirah kiyimunbà kiyimaza sauri nakeyi Dan amatse nake" lubabatu tasake rudewa taciro yan kunnenta nazinari dasarka duka tabashi akan yakyaleta ganin tana nema tabata masa lokaci yakirah wasu acikin tawagarsu suka riketa yabiya bukatarsa takarfi sumakuwa sukaçe saisun Dana

kato shida yataka lubabatu wanima sau biyu yayi dayake su goma sha biyune saisuma shidan sukahole da khairat
Anan suka barsu sunata kuka bakamar lubabatu tayi Allah wadarai dazuwanta wannan dajin abunda take hanawa mijinta yana roko yana karawa

Yaugashi wadansu kartin banza batasan kosuwayeba kazamai sunsameta sunyita jijjiga kamar injin Wankie kuma harda maroranda tasha duk na iska gashikuma suntafi da sarkarta

Duk wannan wuyarda lubabatu tasha batayarda tasaki kullin maganin nan dayake jikin battaba"" khairat tafita karfin hali tamike tamiyarda kayanta tarikata tatashi tamiyarda zaninta sukawuce wajen motarsu lubabatu babbare take tafiya saboda abun bana arziki bane hardajini fita yakeyi kamar anbare budurwa

Sukashiga mota khairat taja lubabatu kam sairusar kuka take harsuka kai gidan"" bayan anbudemasu kofa sukashiga tayi fkng tajuyo tana kallon lubabatu tace haba Kawata saikacee bamaceba baidace Dan wannan yadamekiba Kituna abunda kikaje karba kuma kinyi nasara nanda kwana uku zakidaina jin wannan radadin Amman kishiyafa harkimutu bazakidaina jin zugintaba

Lubabatu takalleta da idanuwanta dasuka rine kamar gauta tace khairat kinsanni batun yauba nibana harka damaza harnayi aure garake kinsaba dakwana danamiji biyar komafiye

Wlh ni dayanma bana iyawa Usman hakuri kawai yakeyi danie dalilinda yasaka yakara aure kenan"" yanzun takaicina daya Kawata wadannan kattin bansan cutarda suke dauke da itaba kar ace sunada kanjamau sulikamun mugun Abu ina zaman zamana

Khairat tace manta basatare dakomai nikaina nayi barikin harnayi aure bankwashi cutar komaiba saike da akayi saudaya dake kinga kishare hawayenki mushiga gida kiyi wanka kigasa jikinki tayanda zakiji dadinshi saikiwuce gida

Lubabatu tace to sukashiga gidan mijin khairat yana nan zaman jiranta tace yabasu wuri tana tareda bakuwa yace to sannan yagaida bakuwar yafita tasa mai aikin tahadama lubabatu ruwan zafi tagasa jikinta taci abinci tadan huta sannan sukai sallama da khairat tashiga motarta tayi kaduna

Ana kiran magrib takai gida tanata addua Allah yasabakowa falon cikin sa akuwa batasamu kowaba tahau Na uwarda zata sadata bangarenta tanashiga tasaukarda ajiyar xuciya kayanta ta aje tarage kayan jikinta takwanta saibarcin gajiya

Usman baidawo gidanba sai karfe Tara falo yasamu labila da khadija suna firah su anwar sundade dayin barci nan khadija tabar labila taje dakinsa tahadamasa ruwan wanka saida yakimtsa suka sauko dancin abinci yace ina maman Abdul bangantaba??

Khadija takalli labila suka kalli juna yace menene kuke kallon kallo?? Khadija tace tunda tatafi unguwa batadawoba ai"" yace injiwa bayan ga motarta nan naganie awaje yayi maganar yana wucewa zuwa bangarenta"

Dasallamar sa yashiga yasameta kwance saman gadon yazauna yasafo fuskarta ahankali tabude idonta murmushi yasakar mata

Yace kekadai mukejirah  muci abinci gashi harkin kwanta"

Ta muskuta tace bazan iyan cin komaiba agajiye nake wlh jikina duk ciwo yakeyi""

Yace subhanallah me take damunki?? Tayakuna fuska wlh aiki Nataya sajida tahadawa kanwarta cincin shinefa jikina yake ciwo yace ayya sannu bari nadanna maki

Yatankwashe hannun rigarsa yahaye kan gadon yasoma yimata tausa"" sosai takejin dadin tausar

su khadija sunacen sunazaman jiransu ba Usman ba lubabatu kowannensu yanayi yana kallon ago go kadan kadan labila ta[truncated by WhatsApp]
[3/29, 8:28 PM] YAYA HAYAT: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 015
        By
Gentle Lady💃🏽



Bayan kamar mintuna goma labila takalli khadija tace kinga sahiba babu amfanie wannan jiran muci namu muje mukwanta

Murmushi kawai khadija tayi dankuwa ranta yasosu dawan nan abun Amman kuma batason nunawa labila dankartaji wani iri" Usman yasan girkinta ne Amman yaje dakin lubabatu yayi zamansa saikace ranar girkinta

Saida labila tasakeyin magana tukun Khadija tazuba masu tasan bawani cizatayi dayawaba Amman hakan tayita wasa da chokali har labila talura takirah sunanta

Sahiba khadija takalleta daguntun murmushinta tace yadai sahiba?? Labila tanisa tana aje tsokali tace kiyi hakuri" khadija tasake murmusawa tace da...akayi mekuma??

Labila tace nasan kinsani Amman kiyi hakuri nikaina abun nan baiyimun dadiba Dan gaskiya dad bai kyautaba duk danasan balaifinsa bane akwai sahannun mom

Khadija tayi Sako tana saurarenta kenan tana nufin maganie mom tayiwa Usman??? Komadai menene zataganie daga baya idan taga yacigaba dahakan tozargin gaskiyane

Tanisa tana kallon labila tace bandamuba sahiba bakisan menene yatsaidashi ba kirika yiwa Mutane kyakkyawar fahimta mana

Tasoma cin abincinta ganin hakan yasaka labilama tasoma cin nata harsuka gama usman bai saukoba sukayiwa juna saida safe kowa yawuce inda zaikwanta

Dayake labila bangaren lubabatu take kwana saida Usman yaji motsinta"" sannan yataso Dan lubabatu tadade dayin barciii

Kallo daya yayiwa labila yasan akwai Matsala Dan dauke kanta tayi tashige daki" yayi shiru waima meyasa yadade harhaka ??? Sam yamanta suna jiransa jiki sanyaye yasauka kasan baisamu khadija ba saiyawuce bangarenta

Itakam harta kwanta rigar jikinsa yacire yahau saman  gadon yakwanta gabanta yanda zai iyah ganin fuskarta

Yajawota jikinsa Sam batacemasa komaiba kuma batayi kokarin jaye jikintaba"" andauki tsayin mintuna ashirin yakasa barci saijuyi yakeyi yasake kallonta idanuwanta arufe suke bazai iyah tantancewaba barci takeyi kokuwa idonta biyu

Sunanta yakirah Deejarh Na" bata amsaba saida yasake kiranta sannan ta amsa batareda  tabude idonba

Yanisa kikalleni Dan Allah Deejarh na"" yamarairaice murya Dan murmushi tayi sannan tabude idonta ahankali takafa masa ido

Tuni yasanne kansa kasa Dan abunda yaganie acikin idon khadija "" baice komaiba tagajie dajin shirun tace kaci abincinka kakwanta nima barci nakeji tanakaiwa nan tasake gyara kwancinta Usman yarasa yazaiyi yace khadija maganafa zamuyi

Tace dad abar maganar nan saigobe barci nakeji yanzun" kafadarta yadafa yace tokiyi hakuri Dan Allah

Tasaki lallausan murmushi tace laifin me kayimun?? Ina anabada hakurine gawanda akayiwa laifi  nibakamun komaiba karma kasadamuwa aranka

Yasake sukurkucewa yace Nina San nayi laifin ai tunda nanemi ayafemun wlh bazan iyah yin barciba inhar bakince kinyafemunba

Danaje kiranta nasamune batada lafiya aikisukai gidan kawarta jikinta yanamata ciwo shine nataimaka nadan daddannamata""

Khadija tace hakan yanada kyau Allah yahutarda gajiya ""😑 sosai Usman yasan khadija da ma ana biyu take yin magana yace bawan nan ba nidai kice kinyafemun""

Takalleshi tace tonayafe maka shikennan ko saida safe"" yasake bata fuska"" tace menene kuma?? Yace kincemun saida safe yanzun haka zakibarni

Tome zanyimaka nibarci nakeji" kenan baki hakuraba???

Wayafadamaka??? Aidakin hakurah dabazaki hanani abunda kikasan nafisonsa fiye dakomaiba

Hannu tasagalo masa awuya tace kafin nan yakamata taci abinci dannasan kanajin yunwa"" kaiyagirgiza yace bazan iyah cin komaiba yanzun kina wannan yanayin lumshe idonta tayi sannan tabude tana kallonsa sannan tamike tadaurah zanie tafita shima yamike yabiya abaya harkasa tazubamasa abincin tajuyo sukadawo tare

Dakanta tarika bashi abaki haryakoshi tamiyarda kayan yayi brush sannan suka kwanta
***********************
Washe gari tunsafe suka gama hada kayan break labila kam dataga khadija tasakewa Usman haushi tabata nikam nace baki iyah shiga tsakanin mata damiji

Taresuka zauna cin abincin Usman ne yafara tashi danyana sauri zaije company yau akwai bakinda suke saran zuwansu akan wani hadin guiwa""

khadija tarakashi harbakin mota tayimasa adawo lafiya tadawo sukacigaba dakarya warsu labila ma takoshi tadauki littafanta tawuce akabar khadija da lubabatu

Khadija takwashe kayanda suka bata tamiyar kitchen tadawo tahaye sama abunta lubabatu dadi yakumeta tatashi tahau saman tadauko battar takarasa bangaren khadija" da sanda tabude battar tabarbade maganin duka sannan takoma dabaya dakwallawa khadija Kira

Tana kwance kusa dasu anwar taji kamar mom takirata tamike zatafito kawai sapna tabare baki tasoma kuka"" nafitar hankali kamar wacce akaciza

Dasauri khadija tadawo tadauketa saitayi shiru "" lubabatu tasake kiranta dasauri tamike tareda sapna tawuce

Anwar da husna suka kata kusan atare harda sapna din dolenta khadija takoma tamarasa yazata daukesu duka

Lubabatu dataji shiru saita dauka khadija batajibane tadawo kofar dakin tasake kwalamata kirah kamar wani yaturata saikawai tazame tafadi dabas kafafuwanta suka tabi maganin saiga lubabatu tana mulmula akan maganie

Data hankalto damenene yasameta tafasa ihu nashiga uku na lalace🙆🏿 " wannan Kalmar da khadija taji yasaka tayi saurin ajesu anwar tafito dasauri  wannan karon su anwar  wasasuke dayatsun hannunsu basuyi kukaba

Ganin halinda mom takeciki yasa hankalin khadija yatashi tace hasbinallahu wa ni imal wakil mom meyasameki??? Sai lokacin  akadaina jujuya lubabatu

Tayi saurin mikewa idanuwañtà zuru zuru tace bakomai dama zance idan kinyi ajiyar maganin ciwon jiki kibanie sainazame anan

Khadija tace Allah sarki wlh fitsari anwar yasaki dazu awurin shine nagoge daruwa Ashe akwai sauransu sannu gashikuma banida maganin Amman barinakirah baban sapna saiyaturo yaronsa yakawomaki

Lubabatu tace ah ah kinjifa yace sunada baki baridai nahakurah zuwa anjima khadija tace shikennan lubabatu tawuce tana dingishi khadija tabita dakallo cikin tausayawa tajuya dakinta

Lubabatu dasauri ta isah bangarenta tayarda battar tacire kayanta takulle daleda tafada toilet takwarawa jikinta ruwa

Tasa so so tayita darzar jikinta saida tayi sabi goma shabiyàr sanan tafito daure da towel tana tsane jikinta

Aranta tace shegen yaro yatsula fitsari gashi yabatamun tsari dole sainakarbo wani kuma taja tsaki badaihakan nasoba

Tasoma duba jikinta ainasan babu abunda zaisameni tunda nawanke tàsau kàrdà ajiyar zuciya saiyanzu tajisanyi aranta ganin tawanke maganin kuma bataji wani sauyinba"""
Ajikinta kwanciya tayi tanata yan tunani harbarci yadauketa" bata farkaba saikarfe biyu qalau tatashi tayi" wanka tasauka taci abinci alokacin labila tadawo tazauna cikin falon suna kallo har Dare bataga komai ba saikawai tasaki ranta dama tasan dakyarne idan aikin bokan nan zaiyi kawaidai  yacimata kudine abanza

Taresukayi lunch dadare bayan suntaba yarfira kowa Yakoma dakinsa yakwanta""


Suna kwance Usman yana wasa da gashin kanta yakirah sunanta" ta amsa yace albishirinki"" tace goro fari Kal yace nashiryamaki tafiyarki Niger gobe kuma nasanarda"wani abokin kasuwancina dazaran jirginku yasauka zaizo yadaukeki duk inda zakuje taredashi zakuje banason kisha wahala kafin kugane inda take

Khadija tace kamanta gidan sarautane aibazai boyuba"" yace hakane Amman aikince batagidan tunda bayan barinta nandin bagida takomaba

Khadija tace hakane kam Amman najidadi sosai  mijina""zanyi kewarka yace bakiji mamaki danasauya ra ayiba nantake??? Tace najimana Amman bankawo komai araiba

Yamurmusa tafiya takamani gobe kuma sati daya zanyi america zanje akan harkar da zamuyi dama banafadamaki munyi bakiba??? Khadija tace ah yace akwai tattaunawarda zamuyi sunason kafa company a kano shine zamuyi hadin guiwa komadai yamukayi idan nadawo zakiji tace to Allah yabada sa a yace Ameen Tonaso najedake saidaikuma wajen maza zasuyi yawa danba hotel za azaunaba shiyasa kawai nacebari nashirya  maki kiwuce nima saina wuce""

Ammani saida yamma"" jirginmu zaitashi gobe warhaka kina niger ko???


Khadija tarungume usman cikin jindadi damurna tasomayimasa kiss tatonowa kanta dankuwa shimai gabadaya yayi"""

********************************lubabatu ta sakeyin wankatabi lafiyar gado

Misalin karfe dayan dare lubabatu tasomajin kaikayi Cikin barcinta tasoma sosawa cen kuma tasakejin wani gurin yasoma kaikayi cikin barcinta tahau soshe soshe cen taji kurji yafito"" aizunbur tamike zaune tasoma duban jikinta duk inda taji kaikayin tasosa ga kurjinan yafito hankalinta yayi mugun tashi  tanajin wanigun yana kaikayi Amman taki sosawa kaikayin yayi yawa batasan sanda tahau sosawaba

Kuma idan tana susarsu wani dadi takeji gabadaya jikinta Yakama yam yam yam idan tasosa nan sainan yakama tazama kamar mahaukaciya dagudu tafada toilet ""'tahada ruwan zafie tawatsawa jikinta saitaji sauki sauki tagoge jikin tadawo takwanta
Kwanciyarta keda wuya gabadaya jikinta Yakama kaikayi"" harcikin kai"""

Lubabatu barci ya gagareta takoma gefe tanata kartar jiki kamar maiciwon kazwa""






Aisha✍🏼
[3/29, 8:28 PM] YAYA HAYAT: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 016
      By
Gentle Lady💃🏽




Idanuwanta biyu har akayi kiran asuba tanaji Usman yana buga mata kofa tatashi tayi sallah "" tacemasa to mikewa tayi takunna wutar dakin ganin kurajen minini ajikinta tasoma binsu dakallo "" gabanta yana faduwa dole takoma wajen bokan nan tunkafin abun nan yayi nisa yakareshi ""

Nikam nace kinmanta kincemasa Wanda bayida makari sai mutuwa?? Dama ance idan zakagina ramin mugunta kaginashi gajere dankoda kai kafada zaiyimaka saukin fita

Wanka tasakeyi saboda kaikayin tasaka kaya masudan tsayi duka sunrufemata jiki tayanda babu Wanda zaiganie

Karamin hijab tasaka saboda wadanda suke awuyanta"" tana zaune sai sake sake takeyi har haske yafito Usman ne yashigo dakin da sallama ta amsa tana dago kanta

Kusa da itah yazauna race masà inakwana" yace lafiya qalau kintashi lafiya?? Aranta tace bakalauba shegiyar   matarka tanason ganin bayana"" 🙄

Afili kuma tace qalau saidai kewarka"" murmushi yasaki cikin jindadi yace kitaso mukarya Dan khadija Niger zataje wajen dangin mahaifiyarta"

Tace waidama ita Yar Niger ce??? Yace ah kishiryamun kayana kafin nakaita airport Dan nima tafiyace takamanie mutanenda nafadamaki sunzo company jiya tosune sukahada mana zama a America akalla zanyi sati acen

Lubabatu tace shikenan suka tashi suka sauka kasa sunsamu su khadija harsun soma karyawa tazuba masu sannan tacigaba daci

Duk da zumudi baibarta taci dayawaba"" tana gamawa labila tatayata suka dauko kayan labila taso tabita suje tare Amman gobe zasufara jarabawa shiyasa kawai bazata bitaba harbakin mota lubabatu tarakasu tanayiwa su anwar adawo lafiya

Abunda zaibaku mamaki su anwar basayarda lubabatu tadaukesu dazaran tadaukesu saisukama ihu dole sai an karbesu hakan yasakama  tadaina daukarsu

Khadija tace shegiyar kiuya kamar wadanda akexizo lubabatu saidai tace hmm kawai saida motarsu tabar gidan sannan takoma cikin gida
.

Sunje adaidai kuwa suna isah akagama komai khadija takude jirgi su labila sunatsaye hargirjinsu yadaga nikam nace khadija dakarfin hali yara uku kuma babu mairike mata kodaya

Amman tunda tasaka ranta datafiyar aisaitayi tanason ganin kaleed ne sosai ""
Karfe biyu jirginsu yasauka" Niger tana saukowa tasoma kalle kalle inama zataga mutumen jitayi anyimata sallama"" ta amsa dafara a yace madam nine Wanda akace zankaiki gidan

Tace okay anwar dayake hannunta nadama yakarba"" tanagoye da sapna husna kuma tana rike gahannunta nahagu motarsa yabude tashiga yasaka Kayanta bayan motar tareyake dawani da alamu driver sane sukashiga motar yatayar

Sukahau hanya"" sunatafiya khadija kam sai kalle kalle takeyi " harsuka kaigidan sarautar mutumen yace wajenwa kikazo???

Tace sunanta Hauwa u yace shikenan fita yayi yayiwa maidagin bayani akasheka akasanarda sarki yanada baki daga Nigeria sunzo wajen hajiya babbane""

Yace ayisauri ashigo dasu nantake fadawa sukayimasu iso sarkin Wanda yake kan kagarar dazaran kadubeshi kaga khadija saikace shine yahaifeta dankamar tasuma tabaci yana ganinta yamike yasaki fara a

Yanayimata lale marhabin"" anwar yakarba yana kallo yacewa fadawa yau manyan bakine dasu danhaka zaigana da bakinsa kaitsaye cikin gidan yawuce dasu wajen matansa sukuma wadanda suka rakota yace akaisu falon baki akarramasu

Sosai khadija tashiga mamaki ya akai yasanda zuwanta babban gidan sarautar cike yake damanyan ginuka ko ina Kaduba bayine gasunan sunata aiyuka

Kaitsaye turakar Fulani yanufa itace uwargida "" itama tanaganinsu tatashi daga kishin gidenda take tace wanakegani kamar khadija??

Maimartaba yakalleta da murmushi akan fuskarsa yace itace ina hajiya?? Tace yanzun nan takoma bangarenta saimuje cen kawai tamike ta umurci sauran bayin dasu sanarda Amarya gabadaya suka rankaya dakin hajiya

Duka yaran khadijar andaukesu anwar yana hannun mai martaba husna tana hannun Fulani sapna Amarya takarbeta

Ita haryanzu mamakine kwance akan fuskarta sunashiga tayi arba da dattijuwar data taimaka mata lokacinda take nakudarsu Husaini

Itama tana ganinta tasaki fara a"" dasauri khadija taruga tarungumeta saikuma tafashe dakuka"" tashafa bayanta tace menene nakuka aikindawo cikin yan uwanki

Cikin kuka tace dama Ashe kece kikahaifi mamana meyasa bakifadamun hakanba lokacinda muke cikin dajin zaune???

Tadago da itah tana murmushi tace khadija kenan ba maimunatu tasanardakeba abunda yasaka banfadamakiba nasan idan kikaji zakiji haushina saboda duk nice silar shigarku wannan damuwar

Saiga hawaye sunabin fuskarta Fulani da mai martaba suka zauna tareda Amarya""

Khadija tasharemata hawaye tana girgiza kai tace kokadan bakece silar damuwar muba kowa naduniya bayawuce kaddararsa

Kaddararmuce tazo dahakan"" Hauwa u tafashe dakuka tace inada laifi sosai gashi asanadin rashin bin iyayena nayisanadin da yata Tarasa ranta bazantaba gafartawa kainaba wannan bakincikin dashinake kwana naketashi

Najamaki gashike bakisan dadin uwaba kowayanaso  yatashi tareda mahaifiyarsa itah tarayu babuni kekuma kinrayu babu itah mezaisa bazanyi kukaba kaichoni hauwa

Nina San har abada bazandaina kukan nanba"" khadija tace dangirman Allah kidaina cewa hakan babufa Wanda ya isah yakaucewa kaddararsa


Kinmanta da Allah yadauke ummana yabarmun Yayana Wanda yakesona fiyedakomai yazamemun uwa uba

Bantaba kukan maraiciba harnakanji araina abunda yakemun komai uwama bazata samu hakanba

Yayimun abunda babu Wanda zaiyimun sannan Allah yahadanie da labila wacce takesona fiyeda kanta ""saikuma yasake hadani da Miji nagari"maisona duk wannan gatane da""Allah yayimun"aiwan nan kadai ya isah ingodemasa "" Hauwa ta share hawayenta tace hakane Amman nikam inaji ajikina bankyautaba gashi naja kinrabuda yayanki yan kananu lokacinda yadace kirungumesu sunyi nisa dake

Khadija tayi dariya tace kuma Allah saiyasake bani wasu tayi maganar tana kallonsu anwar sai lokacin Hauwa tagansu daibayan daya take kallonsu baki bude tace yara uku kikasake Haifa??

Kai masha Allah "" Allah abun godiya mikomunshi Muhammad inganie tayi maganar tana kallon mai martaba yatashi yakarasa gabanta yaduka sannan yamika mata

Tace barakallah kyakkyawa dashi shiru tayi tace kuganemun nikuwa kamar nasan maiwan nan fuskar??? Fulani tace nikaina hakan nakerayawa araina

Maimartaba yace narigaku azuciya tunsanda sukashigo naraya hakan" Amarya tace waiku bakugane dawa yake kamaba?? Ai ina ganinsa naga kamannin sultan""

Maimaitaba yace wanne sultan din??? Tace nagidan Yaya Husaini mana"" Hauwa tace hakane Kuwa wlh sunyi kama da kaleed ikon Allah kunga yanda akeyin kama

Khadija tana saurarensu saiyanzu tayi magana tace aidole suyi kama mana tunda  kaninsane"babansu  daya

Gabadaya suka kalleta da mamaki sukace taya zasuzama uba daya kuma bayan ba ubansu dayaba???

Khadija Tanisa tace abunda yakawoni kasar nan kenan akan maganar kaleed din tanisa mahaifin kaleed shine mijinda nake aure

Idanuwanta suka kawo kwalla tacigaba matar uba wacce takeneman ganin bayana itace tarabashi da mahaifiyarsa aka kasheta sannan shima tasaka akasheshi saita fashe dakuka

Tundanake arayuwata bantaba ganin mace marar imaniba irin lubabatu gabadaya jikinsu yayi sanyi tasoma basu labari duk yanda aljana maimunatu tasanarda itah





Aisha✍🏼
[3/30, 6:14 AM] YAYA HAYAT: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠



Chapter 017
        By
Gentle Lady💃🏽



Mai martaba yajinjina kansa yace Amman kewayafada maki wannan labarin??? Ko wajensa kikaji???

Tagirgiza kai tace shiyanzu baimasan yanada yaro kaleed ba haka baisan yataba aureba kamar yanda suka mantardashi matarsa mahaifiyar kaleed

Nikaina hakan taso ayimun saidai Allah baicika mata burintaba"" mainartaba yace lallai nayarda haryanzun akwai sauran jahilai aduniyar nan kodayake bazasu kareba ai yanisa Amman taya zakifahimtar da yaron nan dantunda yake baitaba sanin basune suka haifeshiba yanada shekara biyar aikomai yamanta Amman bari akirah yayan kiji yakalli fulanie yace saka akirashi yanzun harda  maidakinsa tace to sannan tamike tafita

Wata baiwa takirah tace tayimaza gidan sarkin fada tace anakiransa inji mai martaba"" tace angama rankiyadade dasaurinta tahanzarta domin cika umurnin uwar dakinta.


Ba adauki tsayin mintuna ashirinba sukashigo tareda sallama Sundaukama ciwon Hauwa ne yatashi da akace anakiransu yanzu yanzu

Ganinta zaune yasaka suka saukarda. Ajiyar zuciya"" mai martaba yanuna masu waje suka zauna " yakalleshi yace kokasan wannan??? Yayi nunida khadija

Da mamaki yace wannan kamar  na ima Amman tafi na ima fari kodai itace idanuwana ne suka soma ganin buji buji gabadaya sukasa dariya"" yakalli Hauwa yace inna koban fadi gaskiyaba???

Mai martaba yace kafada kam Amman kamace kawai wannan ba na ima bace sunanta Khadija Yar fateema yayarka wacce hajiya tabaro a najeria

Zunbur yamike yace Allahu Akbar Allah maiyin yanda yaso ashedai darabon zanga jinin Yar uwata "" yamatsa yana kallon khadijar maimartaba yace bawan nan ba tazone akan maganar yaronka sultan

Yace tofa Allah yasa lafiya "" yace qalauma kuwa kalli wannan yaron"" yayimasa nuni da anwar dayake hannun Hauwa" hassan yace tsarki yatabbata ga mahaliccin kowa dakomai ai wannan photocopy din sultan ne""

Yayi maganar yana Daukar anwar yana kallonsa"" mai martaba yace wadan nan yaran Na khadijane

Mahaifin wadan nan yarankuma shine mahaifin kaleed tazone sabodashi tanaso tasanardashi ainahin tarihinsa ..gadai yartaka nan kaji daga bakinta"

Hassan yakalli khadija yace ikon Allah sanardani yata menene gaskiyar lamarin"" ?? Khadija tasake sanardashi komai kamar yanda tafadamasu takai karshen maganarta dacewa  shikanshi Mahaifinsu baisan meyakawoni nandinba dankoda nafadamashi ma zaice baidawani yaro kaleed

Hassan yace babbar magana yata sultan baisan ainahin tarihinsaba nikaina naso sanardashi ganin yanda yakeson Zainab kamar me ammankuma yanaganin tunda iyayensu daya babu aure tsakaninsu

Amman dagashi har itah suna mutuwar son junansu duk dabasufito suka fadaba itah yanzunhaka takasa tsayawa dakowane saurayi shidinma yanzun yakeson yayi aure danyakaucewa soyayyarta

Naso infadamasa gaskiya mamanshi tahana waizantono masa miki tayiyuma idan yaji bamu muka haifeshiba yagudu yabarmu tunda bamusan inda zamuga iyayenshiba

Amman yanzun tunda kinsan asalinsa komai yazogidan sauki zuginda zaiji kadanne" Khadija tace hakane yanxun yana ina???


Hassan yace sarkin buga boll aiyana filin wasa bakyarabashi da kwallo yaro kamar Dan danbe sukasa dariya khadija tace shikenan idan yadawo zanso ganinsa

Wata baiwace tashigo taduka tace sarkin gida yace mutanenda suke tare da bakuwar hajiya sunce zasuwuce" khadija tamike Sam tamanta dasu

Mai martaba yace batare kuke dasubane zasuwuce tunyanzu???
Tace ah ah batare mukeba abokin babansune dayake kasuwanci anan shine yacemasa idan nazo yadaukeni yakawo nan bari nayimasa godiya.
Tayi maganar tanafira

Sam tama rasa hanyarda zatabi tamiyarda itah waje saida tatambayi wata acikin bayin gidan tanuna mata""" bakin kofar fadar tasamesu dafara a takarasa wajensu tace harzaka wuce ??? Yace ah maigidanki yakirah yace meyasa kika kashe wayarki yakirah yaji kinsauka

Nacemasa harkintsufa gidan sarauta murmushi tayi tace kaga kuwa wlh tunda nakasheta  dazamu
shiga jirgi namanta inkunna nafa gode yace bakomai Allah yahutarda gajiya tace ameen
Sukai sallama takoma cikin gidan falon Hauwa u tasamu anjeramata kayan abinci da abubuwan motsa baki kayan marmari dasauransu""

sallah tafara gabatarwa tadan watsa ruwa taji sanyi jikinta sannan taci abincin saida takoshi tayi hamdala kuyangin gidan suka kwashe kayan dataci abincin

Wayarta tadauko takunna takamo lambar Usman takirah tanasoma ringing yadaga cikin murmushi tace amincin Allah yatabbata agareka dan autan maxa

Sosai tabashi dariya dansaida yadara yace kema aminci yatabbata agareki sarauniyar mata"" tace tofa yaukuma sarauniya nasamu yace sosai aikin koma gidan sarauta danhaka kedin sarauniyace

Tace ah ah kam kamanta bakunta nazo haryanxu inanan matsayina"" yagidan??? Yanisa gida yayi fadi sosai kamar Rabin gari

Tarausayarda idanuwanta tace bayan mom tana nan taya zaiyimaka fadi"?? Maganar kikeso kenan

Aimuddin bakece awajeba komaima fadi yakemun Deejarh na nakanga duhu ya yawaita koda kuwa ranace


Komai hasken waje banaganin komai kece pitilarda ke haskakamun gabana"" khadija tasake gyara kwanciya  sosai kalaman mijinta suna isarda sakonda yakamata su Isar sunabin kowanne bango lungu dasako na zuciyarta

Tasaukarda ajiyar zuciya tace Nima hakanne hubbyna"" yagyara  kwancinsa yace dagaske bayan kuma kedin kinacikin danginki anyama zakituna dani???


Wainikam zan iyah sati dayan nan bangankiba?? Wlh yanxun ma dabanajin motsinki wani iri nakeji "

Takwantarda murya karka damu nawan kaima ba anjima zakatafiba aizamudinga yin waya akai akai

Yayi shiru tace banjikace komaiba"??? Tomezance Deejarh na gaskiya zanyi hakuri nasatin nan daya dole asaka sunana cikin jarumai

Khadija tasoma dariya yace mekikewa dariya kuma??? Tace ah ah bakomai Kaine za asaka Cikin jarumai tosaika fadamun jarumtarda kayi ???

Murmushi yayi yagyara kwanciya yace jarumtar hakurin rashinki akusa danie mana kinsan bakaramin kokari zanyiba harsati daya banjini alallausar fatarkiba Haba dolema ayimun jaje bayan anbanie kyautar karramawa dajinjina

Tace hakane zakasamu shakuruminka "" Amman saikaje filin daga tukun"" yayi saurin Tatar nunfashinta yace dama ainidin jarumine nasaba zuwa yakiiii kobaki saniba


Dariya tayi tace habadai"" bakiyardaba kenan bari nafadamaki tace ah ah basaika fadaba nagane "" shima kanshi dariyar yakeyi

Yace ina yarana banji motsinsuba???

Wlh nikaina bansan inasukeba tunsanda mukashigo aka karbesu bansake ganinsuba"" dasauri yatashi zaune yace yaran nawa toke kina ina zakibarmun yara kowa yana dauka

Tace kwantar bawan Allah iyayena suka daukesu kokuma zuwa zan nakarbosu daga kawai anhutardanie

Yace hakanma zakice kinsan bazaki iyah dawainiyar suba meyasa kika tsiri tafiyar"" dariya take ciki ciki tace waikai saikace gareka farau yaya bayan kanada wasu bayansu

Yace nasanda haka Amman wadan nan namusammanne "" tace saboda???

Sunfito ta karkashin macenda nakeso fiye dakomai "" kuma jinin jikinta yagauraya da nasu kingane ai""

Tace hmm barci nakeji gashi sai hamma nake" yace badai yanzuba kyabari saidare"" tace hakane nikaina banda niyar yinsa yanzu sundan jima suna fira sannan sukai sallama taka she lambar ya muktar takirah






Aisha✍🏼
[3/30, 6:14 AM] YAYA HAYAT: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 018
        By
Gentle Lady💃🏽



Tana soma ringing yadauka tayi sallama ya amsa ya aiki yace alhamdulillah ina yarana tace basa kusa danie

Ansama maki masu rainone??? Tace ah ah banagida yanzun haka ina dakin hajiya"! Yace kano kikaje kenan"


Ah ah ba hajiya ta kano ba ina nufin kakata"" wacce tahaifi maman mu

Muktar dasauri yamike yace waikina nufin kinganta???😀 Tagyada kai kamar yana ganinta yanzun hakama ina dakinta kwance gaskiya Yaya yakamata kaima kazo bagaka dangin muba kuma kowa naganie muna kama dashi

Duk da banga yaran gidan ba da alamu basa nan nijinakema kamar nazauna anan🙂

Muktar baki harkunne yace Alhamdulillah koba komai munsamu dangin mahaifiyarmu

Tace hakane yaushe zakazo?? Yadan shafo kansa yace inaso nadawo kano gabaya nacigaba da aiki hospital saboda wani dalili

Khadija tace kai Amman danaji dadi Amman meye dalilin?? Yadanyi Jim sannan yace aure nakeso zanyi"" ! Khadija tace badai kasamu matarba ???

Ah to nasamu Amman gaskiya haryanzun bansanarda itah ba saboda batasona naso sanardake Amman nakasa

Banaso nafada daga karshe tace batasona zanji natsanie kaina"" khadija tace karma kafara sanarda itah aini nayimaka mata Yayana"" tayi maganar tana murmushi""


Shiru yayi daga bisanie yace kowakika zabamun yazama dole agareni nasota"" khadija tace ainasani Yayana kasan Kuwa wacece?? Murmushi yayi yace basaikin fadaba nasan labila kike nufi

Danban manta alkawarinku da itah ba nikuma itace nakeso saidai inaganin bazata soniba kinaganin duk sanda tasamemu tare dake saitafasa zama idankuma nasameta agurin


Danashigo take tashi"hakan bayamun dadi" Khadija tayi murmushin jindadi tace"" karka damu indai sahibace zataso ka

Muktar yace anya kinmanta shiso ba ayinsa dole""

Hakane Amman batadawani zabi tunda nima ta tursasanie na auri babanta aikuwa dole ta auri Yayana"" muktar abun na khadija dariya yabashi
Yace batada laifi damacen kinasonsa"" kunya taji tace to aikaima tana sonka""

Itah tafadamaki hakan?? Aikobata fadaba indai tanasona zatasoka Dan kamanninmu iri dayane idan tana taredakai zataji kamar nice

Muktar dai dariya kawai yayi yacedai Allah yasatasoni shine kawai fatana"" kasa aranka kasameta ya muktar. Yace shikenan adaitayani addua idan kinje wajensu hajiyar kice inagaidasu duka

Tace zasuji sukai sallama takirah labila shukasha firah Amman batayimata maganar muktar ba hardare ba adawoda su anwar ba""" dayake yaran basuda fitina basa Neman mama ""

Dadare tana falon Hauwa sai shigowa akeyi ganinta"" yara da manya sosai khadija tasake cikin yan uwanta harwajen takwas sannan akadaina taruwa sosai harda na ima taganie diyar inna Husaina  ""  tagakuma zainab dakannensu da yayyunsu kaleed ne kawai bataganie ba""

Tanashan tupa yashigo gidan da sallama yana sanye da kananun kaya sunbala in karbarsa tunda yashigo yakafama khadija ido kamar yasanta kodan tana yanayi da zainab dinsa
Itama shitake kallo tana tasbihi ga Allah dayayi wannan halitta Kama iri daya kamar wada kani

Haka zalika bazakace Usman ya isah haihuwar saba"" kujerar kusa da hajiya yazauna haryanzu baidaina kallonta ba,"" idanunsa suna sauka akan anwar dayake kwance yana wasa da kafafunsa

Yazaro ido"" saikuma yasake murzasu hakan bai wadatarba yamike yadaukeshi yakuramasa ido daga Hauwa har khadija shisuke kallo""

Yajuya wajen Hauwa yace matar kinga abunda nakeganie kuwa???  Kodayake kinada matsalar ido balallai kiganiba "Ta harareshi tace ja irin yaro nadaifi matarka ganie idanuwa kamar gwazalma""

Dariya yayi yace haba kinsan kuwa wacce zan aurah aiduk kasarnan babu kamarta""

Tace wajen munintaba"" aikowa zaka aura bayana take dannice uwargida dariya yayi yace hajiya nashiga mamaki Ashe akwai Irina aduniya???

Yazauna kusa da itah yace daxun naga nshi ahannun baba Amman banlurah dashi sosaiba inasauri zanje siyowa zainab"" maganie ikon Allah yasake kallon shi yace wannan itace mamansa???

Hauwa tace itace sarkin surutu kanaganin baki kogaisheta bakayiba kakatse kaiko ina kaje saika saida halinka""

Baki yarike yace ikon Allah yaunaga inda akehana mutum yayi magana dashi dabakinshi wannan tsohuwar akwai takurah inbakiyi wasaba sainadauke kafata daga shashenki

Tace dagadai nahuta kullum saika shanyemun furah"" yace najidai yaukam bazanshaba anyimun gori Amman zuwa gobe zanhuce""yayi maganar yana shafo cikinsa"""
 gabadaya sukasa dariya khadija kam bakibude takebinsa dakallo

Idanma baiyi surutuba ai dasauransa Dan Usman ma surutune dashi harta muryansu iri dayane""

Kallon anwar kawai yakeyi shikuwa sai wangale bakiyake yana dariya kamar wasa yakemasa"" yace Kinganie ko hajiya shima yasan muna kama gashi yanamun dariya😁

Hajiya tace nidai kadameni da surutu katashi katafi gidanku"" ido yadanturo yace ko ina gidane awajena inama zantafi bakisanardani inda wannan lu"u"lu"un yafitoba

Tace saiyanzu kagadamar tambaya to jikatace diyar antyn babanka wacce tarasu a Nigeria !" Kaleed yace haba no wonder naga muna matukar kama dawan nan yaron Ashe danane

Khadija kam aranta tace kaninkadai""  yace  hajiya kinsan me??? Tace ah ah saikafada""

Yace duk su fauziya  da bilkisu da yaya ahmad  kaf jikokin gidan nan basu iyah haihuwaba"" tace sabodame zakace haka 

Yace wannan Mamar lu u"lu"u itace kawai ta iyah haihuwa aceduk fadin masarautar nan babuwanda yayimun kara yahaifi maikama danie aini karnake kallon kowa dannima idan nai aure Yayana kamannina kawai zasuyi

Hajiya tace to alhuda huda katashi dareyayi wannan firar ta asheni kullum sai anzohirah acikamaka kunne dasurutu babu Dan abun tabawa

Kaleed yamike ya aje anwar yace tosaida safe bakuwa tunda korata akeyi  yakalli anwar yace night    diamond   yawuce abunshi""  yana kwala kirah ina beranyar gidan nan take

Kaitsaye bangaren Fulani yatafi yatasota yabata kaza gasassa yace takaiwa hajiya"" tace ya sultan assignment dinfa""

Yadafa kanta yace kikaiwa Aisha tayimaki sauri nake wajen abokina zanje"" tabata fuska nidai ah ah idan nacesuyimun dariya sukemun"" yace tokawo littafin idan nadawo zanyimaki sainaba Yar dasafe akawomaki tace yee nagode yayana

Tasheka dakinsu tadauko littafin takawo masa sannan tasheka takaiwa hajiya

Hajiya tace tatsaya takarba tace takoshi tajuya takoma"" khadija tace badai wannan yakecewa beranyaba??? Hajiya tace itace bakisanshi da shegantakaba"" abokiyar wasar sace incemaki duk bayakiran sunansu kowa dakalar sunanda yake Kira kema idan bakiyi saurin sanardashi  ainahin matsayinkiba nanda kwana biyu zaiyimaki suna

Shi bakinsa bayako ciwo kullum hakamuke dashi dadina dashi abudayane baruwansa dashiga sabgarda bata shafeshiba nitunda nakema bantabajin yayi  koda musayar yawu dawaniba shiyasa yaran gidan nan suke sonsa

Danyanda yake sakemasu fuska duka sauran yaran basa sakemasu kinsan manya akwai  jangirma khadija tace aihakan yayi bari nakwanta barci nakeji gashi anwar yakibarci

Tace aidole dazun barcinsa yatirga koda kawunki yakawoshi yayi barci"" kidau kazar dandan naki kichi"" tace nikam koshe nake hajiya kedai kici tunda tatoshiyar bakice🙊

Tasa dariya tace karkisa na ajeta gobe idan yazo inyaba masa itah afuska Khadija tana dariya tadauki anwar tace dadai kinci kinrage zafi danko bakiciba. Sai anmaki kishiyar tawuce tana dariya

Saida tawatsa ruwa takwanta dayake takwashi gajiya babu jimawa barci yadauketa dawaya ahannunta tanason Kira taji ko Usman yakai


 Al amarin lubabatu kuwa daren sai ahankali domin kaikayin kamar jirayake takwanta  yanda taga safiya haka taga dare ""

 Washe gari tunda safe kurajen sunsake girma hardawasu kananun Abu suna yawo acikin kurajen kamar tsutsotsi sai tsikaranta sukeyi"" illai kuwa tana sosawa daya yafashe saiga kananun tsutsa ruwan suna taba jikinta wani kurjin yabullo

tashin hankali lubabatu Batasan sanda tafashe dakukaba kaya tasaka harda nikaf Dan kurajen sunfara fitowa agefen fuskarta tadauki key din motarta takama  hanyar katsina


*Ganie gawanie*ya ishi wane tsoron Allah




Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠





Chapter 019
       By
Gentle Lady💃🏽




Koda ta isah katsina khairat tana lankwashe saman gado tana barci mijinta yana kitchen yana hadamata abun karyawa"" kamar anjeho lubabatu tafado gidan

Ko sallama babu tasoma kwalawa khairat Kira mijin yace tana daki barci take kizauna kamin tafarka " lubabatu  ko arzikin kallonsa batayiba tafada dakin khairat

Tace tashi khairat kitashi"" tasoma bubbugarta mikatayi tana mutsutsuka ido ganin lubabatu yasaka tayi zunbur tace lafiya Kawata kikadako wannan sammakon😳

Lubabatu tace inafa lafiya khairat nashiga uku nikam wajen bokan nan zakirakani"" khairat tace kina nufin maganin baiyiba nikuwa nasan maganinsa yanaci Dan inada tabbacin haka

Lubabatu tace Nima ainatabbata tunda nakai kaina nabaro kitashi muje Dan Allah" khairat tace haba Kawata komadai menene kikwantarda hankalinki dazaran muntafi komai yawuce kijirah mukarya nasan kekanki bakici komaiba kikafito

Lubabatu tace wanne irin abinci zanci inacikin tashin hankali khairat dubafa kiga yanda nakoma"" tayi maganar tanacire likaf din tanuna mata hannunta dubi jikina kurajen harda tsutsotsi acikinsu

Saiga khairat tafado tui akan gado tace munshiga uku garin Yaya hakan yasameki??? Wayayimaki wannan danyen aikin???

Lubabatu tamatso kwalla tace kamardai yanda bokan yace nayi hakan nayi saidai ansamu matsala maimakon itah tataka maganin nicenan nataka

Khairat tahau sallallami tace haba Kawata meyakaiki yin wannan danyen aikin"??? Ta share hawaye tace tsautsayi mana kawaifa nakirah sunanta bata amsaba sainaje kofar dakin nasake kiranta dan ina tsammanin batajibane


Ashe yaronta yayi fitsari tazuba ruwa tashafe baishafuba kinsan santsin tayil kawai sainaji yajani inataba maganin akasoma mirgina dani kamar cincin

Nafasa kuwa khadijar tafito inajinta tafadi wata kalma sainaji andaina jujuyani ina zarginma anya bawajen boka takainiba??? Biri yayikam da mutum

Khairat tace aini banga zamaba tashi muje tamike kobakinta bata wankeba taja mayafi suka fito


Tacewa mijinta zataraka kawarta wani gurin idan yagama hadawa yaci yawuce wajen aiki yace to"" sukasa kai suka fita wannan karon motar lubabatu sukashiga''

Koda sukaje dajin sunsamu mace hudu"" gefe sukatsaya lubabatu kamar tatashi sama takeji bayan an gama dasu suka shiga tunkafin bokan yabasu damar magana lubabatu takwaye hannun rigarta tace boka kalli yanda nakoma kataimakeni kakare wannan asirin

Tsuru yayi yana kallon kurajen daga bisani yace garin Yaya kika kuskure bayan kuma saida nafadamaki karki kuskura wani yataka sai itah..

Tace tsautsayine karabani dawannan masifar wlh ko barci rabonda yadaukeni tunshekaran jiya

Kai yagirgiza yace yamukai dake??? Saida nacemaki ayimai makari kikace ah ah sai mutuwa
Tayi saurin tarar nunfashinsa tace yanzun ahakan kakenufin zan tabbata??? 🙆🏿

Yagyada kai hakkun Dan banida maganinsa saidai zan iyah maki taimako daya"" tace namenene nidai bukatata inrabu dashi

Yace bazaki rabudashiba sai dai kiji sauki wannan kece kikajawa kanki dakince ayimai makari dayanzu saina warware taimakonda zan iyah yimaki shine zanbaki maganie dai yanzun kijikashi saikiyi wanka dashi zakiji sauki Amman ciwon nan naki yadauremun kai ciwonda yakamata kiyi ba irin wannan bane

Shi kurajene kawai Kuma bazasu dameki da kaikayiba tonaga wadan nan harda mugunyar tsutsa maicin jikin Dan Adam wannan tsutsarda kike ganie tsapappace sannan kullum karagirma takeyi

Kuma duk bayan awadaya saita haihu ahankali zasuyita daduwa ajikinki gaskiya banine nayimaki hakanba kije kiyi bincike


Wanda yayimaki wannan aikin bakaramin matsafi bane lubabatu bakiyamutu haka yabasu sukashiga motar lubabatu

Sai  sharar kwallah takeyi khairat ma takasa magana suna kawowa gida bata tsaya shiga gidan khairat ba tashiga motarta sukai sallama tawuce gida


Tanazuwa tajika maganin tayi wanka dashi takoji sauki danharda barci yadan dauketa"" labila tana gidan Amman batasan meke faruwaba

Danbata ganinta kodakuma tashiga dakin kwance takesamun ta batalura Sam dakurajenba .

Kuma itama boyesu takeyi danbataso yarta taganie""

Khadija bayan takarya dasafe tayiwa yaran wanka "" tana zaune dahajiya kaleed yashigo centajiyo muryansa yana magana da yaran gidan""

Yadade sosai kafin yashigo bangaren hajiya yagaida itah tareda khadija suka amsa"" hajiya tace yau bazakaje kwallon bane naga kashigo tunda safe??

Yace ohh nikam ansamin ido kinmaidani mayen kwallo kinmanta yau ana aiki idan banje office dinba kece zakiyimun aikin

Baki tatabe tace zuwa aikin naka naganin dama "" tonidai bawajenki naxoba mai kamadani nazo dauka dashi zantafi""

Yakalli Khadija yace maman lu"u "lu"u baya kuka ko??? Hajiya tace kaci gidanku anwar sunansa bazaka kirashi da sunansaba saiwani lu'u'lu'u""

 ohhh!!! Aibansan sunansa hakaba suna maidadi yalakuci kumatun anwar shikuma saidariya yakeyi tun zuwansa""

Yaduka yadaukeshi su sapna suka kafamasa ido"" yace kudaina kallona bana daukar mata duk dadai kuma kuna kamadanie bansan yazanyi nadaukeku Ku ukuba

Yasaba anwar ga kafadarsa yace kayiwa mom bye mumuntafii yayi maganar yana daga mashi hannunshi suka fita"

Hajiya tace waike saiyaushe  zakisanardashi ?? Mumushi tayi tace yau zanje gidan uncle idan yadawomun  da anwar saikice inacen

Nafiso ayi komai agabansu danzai iyah cewa bagaskiya bane"" hajiya tace kema kinsan saihakan tafaru ni wlh tausayi yakebanie wannan mata wannan mata ta cuceshi" "

Basujima suna firaba hajiya takirah daya dagacikin masuyimata hidima tace tadauki sapna saita rakata gidan tace to

Khadija tana gaba tana biyeda ita batakoso sujera da khadija harsuka kaigidan shikanshi babban gidane kuma jere suke dajuna Amman saboda tsayin gidan sarautar saikayi tafiya mainisa kamin kakai dayan

Kamar iri dayane Amman wancen yafi girma dakyau"" suna shiga aka karbi husna daga hannunta kaitsaye wajen hutawar matar gidan aka kaita tanaganin khadija tasaki fara a saiyau tunjiya naketa buda idon ganinki

Da murmushi " tazauna tagaida itah""

Ta amsa cikin sakin fuska ""  kuyangin suka ajemata su sapna suka fita"" tace yau naganki dasu biyu ina anwar din?? Khadija tace yana hannun Yayansa tunda safe yadaukeshi

Tarike baki badai dashi yaje aikinba??? Tace aikuwa dashi yatafi"" tace hakafa jiya yazo da Dare yanatamun surutu niharnafara barci yadameni wai bakuwarda akayi yar Nigeria tazo damaikama dashi sama sama nakejin"" maganarsa

Khadija tayi dariya tace haka yayita zuba surutu wajen hajiya tayi shiru " dagabisani takalla tace naji gidan shiru bakowane???

Ayya basanan duka sunyi makaranta" zainab ce kawai agidan"" batajin dadi""
Khadija tace Allah sarki tana ina???  Tace Bari nasa akaiki bangarensu

Wata baiwar takirah tace takaita dakinsu zainab tace to sannan tamike tana gaba khadija nabayanta harsuka kai bangarensu

Dakinta tanuna mata sannan tajuya takoma khadija taturah kofar da sallama"" Zainab tana kwance idanuwanta suna akan waya takurawa pic din kaleed ido sai sharar kwalla takeyi"" Sam batajima sanda khadija tayi sallamaba

Tsaye tayi tana kallon ta tasaki murmushi sannan tasake yin sallama dadan karfi Zainab tazaburah tatashi zaune tana boye wayar bayanta

Ganin bakuwar gidansu yasaka tayisaurin share hawayenta tasaki fara a Anty kece Ashe ina kwana"" khadija tace lafiya qalau tana zaunawa kusa da itah tace yajikin naki???

Tace dasauki tana taba jikinta meke damunki zainab??? Shiru tayi batace komaiba "" khadija tasake tambayarta meke damunki??? Murya raba raba alamun maikuka tace zazzabi""

Khadija tace Amman kinsha maganie ko??? Tagyada kai ya sultan yasiyomun jiya nasha"" khadija tace yaukumafa??? Tayakuna fuska bankaryaba shiyasa banshaba

Shine kikazauna kina kuka kuma me akaimaki??? Zainab tace la Anty bafa kuka nakeyiba abune yafadamun a ido😀





Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠




Chapter 020
        By
Gentle Lady💃🏽



Khadija tasaki murmushi tace naji kitashi yanzun kikarya saikisha maganin kokinaso idan yadawo yasamu bakishaba yayi fushi dake


Tayi saurin girgiza kanta tace ah ah banaso wlh anty"" khadija tace yauwa kokefa tashi maza kikarya

Mikewa tayi Amman haryanzu batayarda ta aje wayartaba"" khadija kwanciya tayi  akan gadon daidai kiran Usman yana shigowa

Cikin fara a tadauka "" tareda sallama daya bangaren aka amsa"" khadija tace tunjiya naso kiranka  wlh wayar tana hannuna barci yadaukeni

Yayi dariya aishine dalilin dayasa bankiraba tunda naji kince barci kikeji"" tagyara kwanciyarta ya America din??

Yace ba dadi"" taturo ido saboda me kace babu dadi?? Danbakya kusa danie "" dariya khadija tayi Cikin jindadi tace  bakada magana kullum sai wannan kamar gobenefa  sati daya bagashi yanzun anyi kwana dayaba??

Yace saboda abun yadameni ai shiyasa banda magana sai itah" Amman naga alama kedin bakidamuba kinsan Allah sauri zanyi ingama komai nanda kwana uku zandawo kema kigaggauta kidawo

Tace un um""tana daga kafada yace please Deejarh na "" kinsan halin mijin naki tausayamun zakiyi "" tace mubar zancen nan

Tunda bakyaso anbarshi  ina manyan gobe??? Tanisa suna wajen hajiya suna wasa nikuma inadaki kwance" toyar laushi koyarana saisunyi kewarki suma dasuke taredake

Zainab tea ne ahannunta Amman khadija take kallo yanda take firarta da alamu tanacikin jindadi wani ciwo taji yanacin zuciyarta

Waimeyasa haka dama akansamu Kanwa taso yayanta??? Kuma soyayya ta aure??? Kullum saitayiwa kanta irin wannan tambayar saidai batada amsa zuciyarta batayimata adalciba

Batason kowane danamiji aduniya inba yayantaba Wanda suke uwa daya uba daya"" tasan haukace takeyi danhar abada bazata taba samunsaba

Wasu hawaye masu zafine suka saukomata"" tayi saurin gogewa dankar khadija taganie Batasan tana kallontaba saida sukagama wayar tace yadai Zainab ko jikinne??/

Kaitagirgiza mata tacigaba da kurban tea kamar maishan madaci bayan tagama tasha maganie takwanta suna firah jefi Jefi harbarci yashureta"" tana rungume dawayarta

Khadija tagyaramata kwanciya tamike takoma wajen hajiya su sapna ma sunyi barci batajima da zamaba kaleed yashigo anwar yana hannunsa yana barci

Yayi sallama suka amsamasa yaduka ya ajeshi kusa da su sapna yayi hanyar bangarensu zainab""

Yasameta tana barcinta fuskarta sake murmushi yasaki yakaramata iskan ac sannan yafito"" yace mom zanwuce idan zainab tatashi kice tasha maganinta dazun danashigo nasamu tana barci yanzun ma haka banaso natasheta

Tace sultan zokazauna magana zamuyi dakai"" yace to sannan yadawo yazauna "" tana kallonsa tace tambayarka zanyi

Yana murmushi yace to mom tambayar saidakikasa nazauna"" tace saboda maganar tanada mahimmanci"" yace hakane saiyasake tankwashe kafarsa yana fuskantarta"" Tanisa akan maganar kanwarkace zainab"" gabansa yaji yabada rasss yakalleta jiki sanyaye yace mekuma yasameta???

Tace bakomai matsalarku dakai da itah tazo karshe"" dariya yayi har hakoransa sukabayyana yace mom bamudawata matsala dake da dad kunkasa ganewa

Nidai abar maganar nan yayi maganar yana yunkurawa zaitashi khadija tace kaleed kasan wannan pic Usman takamo awayarta Tamika masa"" yakurawa pic din ido kamarshi ammankuma bashida wadan nan kayan hasalima shidin ba ma aboci saka manyan kayabane Yakoma yazauna yanakallonta yana kallon pic din yace mom kalli wannan kiga kamarni sak kodai mubiyu kika haifa???
Kai ta girgiza tace kaleed"" dasauri yadago yakalleta dantunda yake da itah bata taba kiran sunansaba"" talura da mamaki yakamashi

Tace kanatsu kasaurareni yauzan sanardakai abunda bakasaniba "" zanfadamaka abunda mukadade muna boyemaka tsayon shekara ashirin da uku"" dam gabansa yayanke yafadi karfa mafarkin da yadade yanayi shine zaifaru dagaske??

Ta katsemasa tunaninsa dacewa magana tagaskiya bamune muka haifekaba?? Zunbur yamike jikinsa yasoma rawa yace wannan mafarkine bagaskiya bane meyasa nakeyawan yin irin wannan mafarkin Dan Allah mom kidaina fadarhaka

Tadago takalleshi tasake kiran sunansa akaro nabiyu yanakallonta idanuwansa harsun kada sunyi jajir tace ba mafarki kakeyiba"" wannan maganar gaskiyace kazauna kaji mezanfada maka

Jiki bakwari Yakoma yazauna tayidan jim sannan tace sanda mukai aure tareda mahaifinku muna son junanmu sosai duk da auren hadine munkwashe shekara uku muna tare bantabayin ko batan wataba abun yadameni sosai kullum sai inyita kuka nikadai tun inayi abayansa harnakai nakanyi agabansa ya shiga damuwa sosai watarana dadare muna kwance saimukaji ana bugamana kofa

Mahaifinku yamike yafita yanacewa waye akai shiru kuma baiga kowaba ta gefen kofa yaleka"" saikawai yaga guguwa tatashi sama zuwa yan mintuna yaga tabace harzai koma wata zuciya tace yabude kofardai yaganie

Yana budewa saiyaga wani yaro kwance shekarunsa bazasu haurah shida ba"" dakayansa agefensa saikuma farar takarda asaman kayan

Hassan yaduba gabas dayamma baiga kowaba yakarasa yadauki takardar abunda akasa aciki wannan yaron sunansa kaleed gashinan nabaku kurikeshi yazama danku watarana gaskiya zata bayyana

Yaninke takarda yaduka yadaukeshi tareda kayanshi lokacinda yafito nikuma danaga yajima sainabiyo sahunsa"" sainaganshi dayaro

Cikin kaduwa nace wannan kumadaga ina? Ina kasameshi??? Baicemun komaiba yawuce daki nabishi guiwa sake"" yashinfideshi nikuma inabinsa dakallo da tambaya abakina yamikamun takardar nakaranta tazube zaune ina taslima nace koyaron wanene kuma

Amman daganinsa nasan danmai kudine la akaridanayi dakayanda ke jikinsa"" washegari damuka kaiwa hajiya kai saitace murikeshi Allah ne yasharemana hawayenmu yabanie kai

Tundaga lokacin mukarika kiranka sultan"" yasakaka makaranta Sam bakataba kukan gidaba tamkar kamanta kowanaka shekaranka biyu anan nasamu cikin Zainab

Kayi murna sosai Wanda komu iyakar Wanda zamuyi kenan"" tunkana karami kakecewa ita zaka aurah dukda asanin kanka ba aure tsakaninku

Idankuma wani yaro yace yanasonta saikamasa dukan tsiya harkagirma akan wannan soyayyar tanisa babanku yaso sanardakai gaskiya dankarya haramta maka zainab nicenace karyafada danzaitado maka damiki kaji ainahin yanda muka sameka!

Kaleed Wanda hankalinshi yagama tashi yace yanzun mom dama bakune kuka haifeniba?? Tagyada masa kai yace Toni suwaye iyayena???


Tace wannan najikin pic din wayar hannunka shine mahaifinka"" kaleed yasake duban pic din damamaki "" yace wannan ne yahaifeni??? Yanisa Tayiyuma batahanyar aure suka sameniba shiyasa suka yardani""

Khadija tace karka ce hakan kaleed kaidan sunnane"" mahaifinku daya da anwar kamannin mahaifinku kukayi"" yayi saurin tarar nunfashinta yace bakida tabbacin haka yama akai kikasan shine mahaifina dankawai munakamà bashizaisa inyarda dahakanba kodama shine mahaifinnawa nibaruwana dashi natsaneshi tunkafin nasanshi

Ashe harzai iyah yarda dansa bayankuma tahanyar aure suka haifeshi shinzaiyi alfahari harma ya iya kiran kansa uba Sam baidace dawan nan sunanba banasonsa natsaneshi

Khadija ce tadakamasa tsawa tace yimun shiru kaleed Sam mahaifinka baichanchànci wadannan  miyagun kalamanba ka adanasu saikafadawa lubabatu

Itace tadace dasu"" yace waye kuma hakan??? Mahaifiyatace??? Tagirgiza kai ba itah tahaifekaba matar babankace ita ya aurah bayan rasuwar mahaifiyarka

Amman duk abunda yasameka itace ummul haba isi tarabaka da mahaifiyarka Sannan taso akasheka daganan tasoma bashi labarinsa atakaice tunkafin tagama kaleed hawaye sukasoma sauka afuskarsa yasoma la antar lubabatu bayajin zaitaba yafemata idonsa idonta saiya nakkasata!!! Ashedai kaleed ma yanada zuciya""


Hmmmm anan nakawo karshen *hatsabibin boka* kashi nadaya* saikunjini akashi nabiyu

*shin lubabatu zatawarke daga wannan sihirin datasa akaiwa khadija saigashi itah tafada??*

*Shin kaleed zaiyarda yakoma wajen mahaifinsa???*

*Wai ina labarin hatsabibin boka???*

*ya makomar hatsabibin boka zata kasance???*

*Ko su hassan zasuci galaba akansa sufito da aljana murjanatu idan sukaje dajin???*

*ko aljana murjanatu zatayarda da hatsabibin boka???*

*Labila da muktar zasuyi aure kuwa???*

*Ya labarin kishiyar Fateema mahaifiyar khadija dakuma mahaifinta???*

*yalabarin soyayyar kaleed da Zainab???*

*ina Labarin garba dakuma matarsa huwaile wacce tayita ganawa maman kaleed azaba*

*faruq kanin muktar shinkoyana raye???*

*menene makomar lubabatu maikan doya???*


Duka amsoshin wadan nan tambayoyin sunacikin *hatsabinin boka* kashi nabiyu kubiyoni danjin cikakkun amsoshin tambayoyin taku mai kaunarku Aisha Ibraheem

Sakon gaisuwa zuwa gareku yan group din

*NISHADI GROUP*

*ZANGON LABARI*

*MUMBARIN HAUWA JABO*

*Clever's writer's*
*M khady novels*
*Littafan hausa*
*Feedy luv novels*
*Novels only*
*Zuhurah novels*
 *Herwwerh Jeedah fans*

Inakaunarku kamar yanda kuke kaunata





Aisha✍🏼

Download Complete Book Here