👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 1*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukra aunty ummi```
BISSIMILLAHIRRAHAMANIR RAHIM
DASUNAN ALLAH MAIJIN KAI ZAN FARA WANNAN NOVEK DIN ALLAH YA YAFEMUN KURAKUREN DA ZANYI ALLAH YA BAN IKON KAMMALAWA AMEEN
sultana MASARAUTAR MUCE tana cikin tashin hankali matanenmu na cikin mayuwacin hali me yasa kina zaune a Ana bazaki Kai agajinki ba,hawaye sultana take wai ke wace me yasa kikesan Sani cikin tashin hankali so kike in tafi in bar kawona taya kike tunanin Zan iya shiga wannan masarautar nida ba juruma ba?keba jaruma bace amma Ai ke jinin sarautace, sarautar muce sultana you to do some thing,Kallan ta sultana tai taya Zan yadda dake Sannan taya kikee ganin zanyi nasara ,murmushi matar tai zancen nasara karki damu kisa Allah a ranki zanca yadda kuma kika ki duba hannunki zaki ga wani zanen sarautar muce ki duba DA kyau ,
Kallan hannunta sultana tai zaro ido tai ganin Zane sosai a hannun ta DA Jan lalle ,Kallan mtar tai ya akai wannan zanen yazo hannuna wannan kuma Ai zanen MASARAUTAR gombe ce ,murmushi matar ke yi nasan ke yar baiwace sultana nasan zakiyi iya DA ga haka ta bace ,.
A razane sultana ta tashi daga bacci ta duk ta hada zufa kamar wacce take filing danbe Tana wani zaro ido ga uban gashinta daya rufe Mata fuska shima yana daya daga cikin Wanda suka hada Mata zafi,ajiyar zuciya ta sauke tare DA nade gashin Nata tayi dunot sannan ta mike kallan hannunta tai wannan zanen ta ga ni amma bai Kai na mafarkin turuwa ba, MASARAUTAR MUCE ta fada a hankali Kai wlh ba ruwana ba wani masarauta DA zani kawai in jawa kaina ni ba Yar sarki ba sannan a turani masifa Ina mafarki ba gaskiya bane ,haka ta fice tana ta surutai abinta,.
Kallanta kawu yayi Wanda ke tatsar nonan shanu lafiya sultana kina ta zance ke daya?aa kawo bakiji dai dai ba gaskiya ni bana wani surutu,wanke wanke ta Fara sannan tai share sharen ta,lokacin kawu ya gama tatsar, ta hada murhu sannan ta dauki tulunta Dan zawa debo ruwa ,kallan kawu tai kawu na tafi karfa ka ce zaka tafi siyo koko DA kosai ka Bari Inna dawo Zan siyo ,.
Tabe baki yai saiki ki rikeni Ai, au hakan yana nufin sai kaje kenan ?aa to mai zai Hana ficewa tayi batace komai ba tana fita ta Sani tsummata rufe gidan naga ta inda zaka fita aiki tai tafiyar ta,.
Tana fita ya mike amma yaji kofan a rufe ba yadda ya iya daya wuce ya hakura ya koma ya zauna amma sai masifa yake wai ta raina shi,.
Sultana na fita DA tulu a hannunta sai hijab dinta tafiya take a hankali kamar ba zata taka kasa ba,wasu maza dake bayanta suke fadin sai iyayi amma ba auruwa ,dayan ya karba wazai aura Ai duk Wanda yai boko tofa ya gama Dan Dan iskane sosai bafa kadanba,duk suka sa dariya ,sultana dake gaba ta tabe baki ,tin rashin auren na dumunta yanzu ya daina damunta ta barwa Allah komai tasan bazai manta DA ittaba ,.
DA haka taje rafi ta debo ruwa ta wuce gidan tana murmushi Dan tasan yau kawu namantane kawai bazaicoba
By hajara mami Natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 2*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
DA sallama ta shiga gidan bai bai amsa mataba ,ittama bata tamkaba illah murmushi datai ta ajjiye ruwan ,karasawa gunshi tai kawu kawu in siyo mana konun DA kosai baice Mata kamoiba juyar DA Kai yayi ,hakan yasa ta zauna kusa dashi tana dariya kawu maganafa nake, to kayi hakuri kaji,kallanta yayi wato tsabar kin rainani zaki wani rufeni ki tafi kamar danki ko? To yi hakuri kawu inkai fushi dani bansan inda zansa kainaba ta fada alamar zatai kuka naji ya fada tare da dakko kudin ya mika mata, ta karba tana murmushi, sultana Ya fada hakan yasa ta juyo karki kula abun da Yan garin nan suke miki ni AI ina tare da ke koma Maye ni kaina nasa baki dace da samarin garinnan ba shiyasa ban wani damuba nasan lokacine naki mijin nanan zuwa, murmushin jin dadi tai kawu yana ganewa indai Tana cikin wani hali shiyasa take alfahar dashi, kiss Ta bashi a kumatu hade rai yayi nace miki bana San wannan iskanci ha, a dariya tai wannan ne iskan ci nidai Na tafi,.
Layi ta gani agun kusan Amman ansa mata kunu, Tana ganin masu samari suna mikawa ana mazan shi ga wannan taron su karba musu Amman banda itta,.
Kallan wasu mata sukai suna dariya Yan mata saidai hakuri ba saurayi to wlh indai kema ba zama Na miji kikai ba ba zaki taba samuba, kallan su tai kunga dai danazo nan gun ba Wanda naiwa Magana a cikin ku to Dan Allah bana san neman masifa, matsowa kusa da itta sukai KO zaki dake mune? Eyye saka fada suna dungure mata kai, da sauri wata dake can wani gefe tazo ta shiga tsakiya ta hade girar sama da ta kasa ganin hakan yasa suka ja baya tare da fadin bafa dake akeba zaki zo ki wani shiga, Na shiga a dakeni mana yan rainin hankali waiku ME yasa indai mutun na muku shiru shiru kunfi rainashine, inafa kallanku komai da komai a idona aka yi ta juya Tana kallan sultana ke kuma kina tsayawa wadanda Ma kiika girma suna rainanki, mtswwwww taja tsaki tare da karban kwanon hannun sultana tana ture mutane ta shiga ba ruwanta da an rigata ta mikaa aka zubawa sultana sannan ta fito ta mika Nata, karba sultana tai tare da fadin na gode Nafi, hararar ta nafin tai tare da yin gaba abunta.
Tafiya suke Nafisa na gaba sultana na baya, ittama kanta sultanan tsoran Nafi take dan karyarw mutun yace yana wannan kauyen baya tsoranta itta kan sultana tun ba yauba take San Nafi kasancewar ba ta da wata kawa, juyowa nafin tai ta jirata suka tafi, kallanta Nafi tai sanyinki yayi yawa shiyasa aka raina ki wlh ki koyi masifa, murmushi sultana tai tare da fadin to, hakan yasa Nafi murmushi tasan ba wani iyawa zataiba ta amsane kawai, kallan ta sultana tai ni ba masifa nake San ki koyamun ba harbi da baka nake San koya tunda babanki maharbine nasan kin iya, dariya Nafisa tasa hakan yasa sultana sakin baki Tana kallanta bata taba ganin Tana dariyaba, saitaga ta kara kyau da tana dariya, ganin kallan Da sultana take mata yasa ta tsagaita ki daina kallona haka kamar baki taba ganin ana dariya ba,murmushi sultana tai wlh kinfi kyau IN kina dariya ME yasa baki fiya yin dariya bane? Kallan Nafi tai zan koya miki Amman saikin cire wannan sanyin naki Dan zaki dan ban wuya wajen koyar dake, kallanta sultana tai da murmushi a face dinta da gaske zaki kiya mun daga mata kai tayi alamar eh, hakan yasa sultana rungumeta nima zan koya miki murmushi kawai Nafi tai mata sannan sukaiwa juna sallama,.
Da farin ciki ta koma gida Ta zuba musu abinci suka ci kallanta kawu yayi sultana Ya naga kina cikin farin ciki? Kawu ina nafi Yar gidan maharbi zata koya mun harbi ne,zaro ido yayi ME zakiyi da harbi kuma? Shiru tai Tana kame kame itta a zahiri kawai zata koyane saboda masaurautar da zata gara ta fara practicing tun yanzu, kawune ya katse ta KO duk Na shirin tafiya masarautar taku ne? A razane taste kalleshi, murmushi yayi yana kallanta karki wani damu nasan komai game da mafarkin ki, dama ban fada miki bane so nake inga KO zaki fada mun amma kikai shiru,sultana ni na Sani ke Yar sarautace kawai boye miki nai saboda nafisan ki gane da kanki
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 3*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Sultana bani Na haifekiba, kallan shi tai duk ya sata cikin wani hali, karki damu bari IN baki wani labari,.
Can baya wasu shekaru ina cikin noma a gona naji wani hatsari alamar motace ta shigo wannan gonar ta buge da bushiya ,hakan yasa na ajjiye abun da nake Na nufi gun ina zuwa naga wata ta fito daga motan duk jikinta jini ga wuka a bayanta hakan yasa hankalina yai Bala, in tashi da sauri Na karasa gareta ina zuwa ta miko min ke, tare da fadin bawan Allah alfarma nake neke nema Dan Allah ga yataa ka rike Ta da amana, ta bude Bayan mota ta dakko min wani akwati,.
GA wannan kadarar dana taho da ittane ke saka wannan yarinyar a makaranta tayi karatun arabi da boko badan halina sannan abu daya zan fada ma itta jinin sarauta ce Yar sarki ce babanta yana can, kallanshi tai yanzu ina ne nan,? Masaaya kauyen birnin kudu jahar jigawa, jijjaga Kai tayi, Amman baiwar Allah wacce masauta? Gombe, dai dai lokacin mukagi ana ga motar ta can, Da sauri ta kalleni ka tafi plz, Amman baiwar Allah ki bari IN taimaka miki mana, Dan Allah ka tafi, Da sauri nabar gun na Bayan wani dutse, Tana tsayea agun sai hakin mutuwa take Dan kuwa tasha wuya ba kadanba har sukazo, suka sameta dariya suka dinga yi, an fada miki duk wani gudun ki zaki guje mana ne? Batace musu komai ba, kallanta yayi ina yarinyar, wani kallo tamai hakan yasa ya dauketa da Mari, ta dafe gun tanaa kallanshi yanzu Hafiz ka rasa damai zaka saka mana sai da haka, eyye ya fada yana kallanta ku suwaye zamu tsayan muna kallanku kuna mulki mu kun barmu a can aikin banza kallan suran yayi ku duba min inda takai yarinyar haka sukai ta dube dube basu ganmu ba, sannan suka dawo suka sanar Mai basu ganiba,a ido a kan idona ya dakko bindiga ya harbeta sannan sukai gaba,.
Nayi kuka Dan ban taba ganin abu irin wannan ba, cikin gari naje na sanar da mai gari Amman ban fadi kudinki da taban ba, haka akai mata sutura aka kaita makwancinta,.
Haka nakaiwa Matata ke ta kula dake har kika girma shine Na Saki wata makarant anan birnin kudu GREAT ALBARKA INTERNASIONAL SCHOOL, anan kikai primary zuwa jenior zaki tafi secondary Allah yaiwa Matata rasuwa Bayan kwana bakwai kika tafi makarantar Dutse wato Dutse model, to kinji yadda abun yake,.
Sultana da duk tayi wanka da hawaye batace komai ba kawai ta wuce daki a Daki ta kwana tana kuka bata gani bataji wannan kenan
By Hajara mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 4*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Words begin with ….A….B….C….
Number begin with….1….2….3….
Music begin with….SA….RE….GA….
BUT….?
FRIENDSHIP begins with….’
‘You&Me”
Washe gari kamar yadda sukai DA nafisa haka kuwa akai bayan ta gama aikace aikacenta ta wuce gidan su nafi ,nan suka Fara abun DA ya kaisu (nidai nace wannan Abu kamar a littafin yaki),.
Tafiya yake cikin kasaita DA gani ranshi a bace yake,yana zuwa ya kalli dogarin dake gun nan take ya zuba yana kwasar gaisuwa daya daga cikin yarima sultan ya Fara magana ka fadawa mai martaba yaranshi mai jiran kujera yana sallama ,DA Sauri dogaran yai ciki ,ba,a Dade ba ya fito ,sarki yana mai barka DA zuwa,ba tare DA yarima sultan hace komaiba ya shige ,dogaran suka kwashi gaisuwa kafin suka fice suka basu GU,.
Yarima sultan ya mai DA kallanshi ga sarki kafin ya Fara magana a hankalin yanzu abbah kana gani komai yake faruwa a wannan MASARAUTAR karfa ka manta wannan, MASARAUTAR MUCE hade rai sarkin yayi me kake bukatane ?yanzu abbah ace a wannan !MASARAUTAR kullun sai anwa Mata fade sannan a dinga kisa alhalin nasan dasa hannunka taya kake ganin zata gana DA Allah a ranar gobe kiyama ,sake hade rai sarkin yayi yanzu zuwa kayi kaimun rashin kunya kome? Kayi hakuri abbah indai abun DA na fada ya kona ma rai amma Ina bazai yuyuba ace Ina gani Ana abun DA bai daceba sannan into shiru yanzu inkaine akewa yayanka haka zaka ji dadi ?yanzu fisabilillahi ace kana ganin talakawa a wani halin ba zakai ba DA agajinkaba for how long zasudinga suffering kodan ba Kaine make suffering akaiba ,amma shikenan indai kaki barina in dau mataki Allah zai kawo mai yaye musu Masan kuma in Allah ya aiko kaima zakantafine nasan kaima mugune abbh na Sani tunda kaimkasa aka kashen yayanka akan wani Abu waishi mulki ,yana kaiwa nan ya fice rai bace ,DA kallo sarkin ya bishi zuciyanshi na tafasa lalai sai ya dauki babban mataki harshi danshi sultan ke fadawa haka ,.
DA sallama sultan ya shiga ban garen maman shi ,hakan yasa masu Mata hidima ficewa ,zama yayi baice komaiba ,murmushi tayi nima mulkin za,amun har sai na Fara yin magana kafin aimun ?Ina wuni ya hutawa ?lafiya qlau sadauki kina lafiya naga fuskarka haka ?amma wlh matanen MASARAUTAR nan suna cikin wani hali ya Kama akai musu agaji ace a kullun duk dare sai anyi wa Mata fade haaba ya kamata as an abunyi watarana zamu budi I do muga ba mutane a wannan MASARAUTAR, kallanshi tai itta tasan danta mai adalcine amma ya ta iya mujinta halinshi saishi amma ya ta iya dole saidai suyi adduar Allah ya kawo. Mai taimako,.
Hira sukai irin na uwa DA danta sannan yai Mata sallama ya wuce ,.
DA sallama sultana ta shiga gidan ,zama yayi kusa DA kawu,ya akayi DA fatan an iya Harbin tunda mai harbi like San komawa ?dariya tai kawu Ai ba wuyama har. Na iya ,murmushi kawu yayi to Allah ya taimaka ,Kallan kawu tai ,kawu Ina San zuwa gombe taya Zan iya shiga wannan masarautar ,zaro I do yayi a kice abun yazo inji mai tsoran wqnka ?hmmm kawu kenan bana San tafiya in barka amma ya na iya door inje zanje in dauki fansa ne ya zama dole DA banyi niyar zuwaba amma yanzu inasan zuwa Inaji a jikina zuwana can alkhairine ,jijjaga Kai yayi wannan haka yake karki damu DA kaina Zan kaiki can gombe zamuje can amma taya kike ganin zaki iya shiga wannan masarautar ?a matsayin baiwa mana ,matsayin baiwa hakan kina ganin ya miki ?to kawu inba tanan ba Ai banda hanya ,tonshikenan yaushe kikesan zuwa ?gobe ta fada mai ,DA wuri haka kice yau zama shirya amma bakiwa kawayenki sallama ba ,kawu Ina naga kawaye nafisa kuma nace mata zanyi tafiya ,mikewa yayi Allah ya kaimu goben ameen
By Hajara mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 5*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Sarkine ke tsaye a fadarshi ya rasa meke mai dadi yanzu ya zaiyi da sultan danma bashi zaiba sarautar nan ba da saidai ya jazawa kanshi masifa Dan yasan sultan bazaibi bayanshi, banko kofan akai bako sallama, kallan Wanda ya shigo yayi daga sama zuwa kasa Hafiz ne da gani yasha giya ya bugune, juyar da kai sarkin yayi ganin hakan yasa hafiz karasawa gunshi, wai abbah meke damunka kake cikin wannan halinne duk kabi ka wani canza? Ta tambaya a kalar maye, dauke kai sarkin yayi kafin ya kalli hafiz,hafiz ya kamata kafa canza bakaga Na fara tsofa bane kana tunanin a haka zaa baka sarauta alhalin kasan cewa sarki sai Ya zama mai addini ba shaye shaye ba bin mata amma kaf wannan duk kana yi karshema inka ma Mace fade kashe ta kake Ya kake San inyi wlh ka canza inba hakaba kanaji kana gani Za,a dage dole sai sultan kasan ba zamu Sami abun daa muke soba, zaro ido Hafiz yayi yanzu duk Quran din dana sauke ace banyi karatuba sannan naga matan bani kadai nake nemaba agunka na koya ai kuma su matan su suke jawowa mai maikon su amince Amman sai sudinga mun hauka shiyasa nake musu dole sannan kuma in kashe su daga karshe, kuma mulki dole IN hau yana kaiwa nan ya fice, da kallo sarkin ya bishi sai kuma ya tabe fuska ba matsala dole inbar yarona yayi abun da yake so ai ba yadda Na iya a guna ya gada kuma nasan wataran zai daina,.
Jin dogari na sallama yasa saurin yin shiru Ya koma ainihin sarkin shi, nan dogarai suka shigo suka zauna, aka ci gaba da gudanar da komai,.
Washe gari kamar yadda akai haka kuwa ya faru dan kuwa sultana da wuri suka Tashi itta da kawu, kallan kawu tai kawu Bari inje in sakewa Nafisa sallama! Tom kiyi sauri kije ki dawo, Tam tace tare da ficewa da sauri,.
Da sallama ta shiga gidan Nafisa Ta tashi daga wanke wanken da take Tana kallan sultana aina dauka zaki tafi bakizo munyi sallamaba, karasawa gunta sultana tayi ina Na isa na tafi ba tare da na miki sallama ba, murmushi Nafisa tai inaji a jikina wannan tafiyar da zakiyi ta alkairice Allah ya sa, murmushi sultana tai tare da cire zubon hannunta ta sawa Nafisa tare da fadin
*of all the friends I've ever met
You the one I won't ever forget
And if I die before you do I'll go to heaven and wait for you*
Dariya Nafisa tai Na gode da kyauta Amman bansan ME kika ceba, ittama ta cire wani stone mai kyau a hannunta ta sawa sultana nima GA nawa kyauta karki manta Dani a ko wanne hali, rungume juna sukai suna murmushi kafin Sultana tai dago Na tafi Nafisa wataran zan dawo kodan ke, Tana kaiwa nan Ta fice tana dagawa Nafisa hannu haka ittama ,.
Tana zuwa suka nufi titi dan hawa mota basu wani dadeba kuwa suka sami mota suka kama hanya,.
Masarauta
Wazirine zaune kusa da sarki su biyu, a hankali sarki ya Fara magana waziri ina San zanje dakin ajiya kuma kasan IN zanje bana shigata irin na sarki saboda haka kace wa dogarai Yau nace bana bukatar ganinsu hutawa zanyi ina tunanin ka fahimta dan banasan kowa yaga naje gun ,an gama ranka ya dade ya fada tare da ficewa, yana fita sarki ya canza shiga Ya fice ta kofar baya sannan ya rufe fuska da kafarshi Ya taka yana tafiya, ya danyi nisa Ya nufi wani gun da kwata kwata mutane basa yin gun Ma, wani bawane yazo wucewa yaga wani nayi gidan ajiya alhalin yasan an hana hakan yasa yabi bayan sarki yana dabe dan yaga inda zaije, dai dai da sarkin zai bude kofa yana inuwa alamar ana binshi ,murmushi yayi aidama yasan duk sanda zaizo wannan gun dolene yayi kisa hakan yasa yai fuska kamar baiga kowa ba ya shiga, shima bawan kuwa bai fasa biba, labewa Sarkin yayi abayan kofan saida bawan ya shiga ciki sannan ya rufe kofan yasa kwado ya rufe, bawan Ya juya baya yana dube dube sarkin yai gaba hakan yasa bawan bin bayanshi Sun danyi tafiya kafin bawa ya Fara fadin wai waye wannan? Da gudu sarki Ya kwasa hakan yasa bawan kwasar gudu shima,.
A razane bawan Ya taka burki ganin wani mutun da yayi a cikin cell, ya dago yana kallanshi a razane Ya furta SARKI ABDULSALAM?
BY HAJARA MAMI NATTY GIRL
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 6*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Da sauri ya karasa gunshi yana fadin sarki abdulsalam dama baka mutuba me kake anan? A hankali sarkin Ya fara magana ME yasa ka biyoshi bakasan bana San ana kashe mutanena saboda niba bakasan shi mugu bane, kallanshi mutumin yayi waye mugu yau zan fitar da kai anan zan fadawa sarki Abdullahi na ganka nasan zaiyi murna da hakan, hawaye sarki abdulsalam ya Fara yana jijjaga kai,.
Jin ANA tafi yasa bawan juyawa mikewa bawan yayi ganin sarkin su yasa ya karasa gunshi yana fadin sarki abdulsalam bai mutuba Ashe yana nan....... Saikuma yai shiru tanu abun da tsohun sarkin nashi yace mai mugune me yasa ka biyo shi Da sauri ya kalli sarkin nasu yana jijjaga kai, Amman ba wannan bane mugun badai sarkin muba, matsawa kusa dashi sarkin yayi nina kawo shi nan ai nana sashi anan ina jiran wani lokacine da zan kashe shi, Da sauri bawan ya kalleshi saboda me? Saboda kunfi sanshi kun sanshi akan ni alhalin nima inasan mulkin kuma nine babba saboda da ME bazan yanke wannan hkuncinba? Da sauri bawan ya kalleshi aikuwa kaiba sarki mai adalci bane kuma yau zan tuna ma asiri wlh, gadan gadan Ya nufi sarki, yana zuwa saijin saukan wuka yayi a cikinshi, kallan Cikin yayi ya kalli sarkin kafin yai kasa yana shahada nan take ya mutu,.
Kuka sosai sarki abdulsalam yake zama sarki Abdullahi yayi kusa dashi karka wani damu ni bani nace Ya biyoniba shishigine irin nashi kuma kasan duk zuwa ina samun irin su, cikin kuka sarki abdulsalam ya Fara magana wai ME kake jirane ka kasheni kawai mana, no no bazan kashe kaba ai nasan Yarka zata zo agabanta zan kashe ka ai karka wani damu, kallanshi sarkin yayi aikuwa babban kuskure zaka tabka dan ittace ajalinka itta zata tuna ma asiri inba kasaniba ,wata dariya yasa aikuwa zanso ganin wannan ranar tab kace akwai shagali, Hmmmm kawai sarkin yace bai kara cemai komaiba, haka yaitaiwa kanin nashi surutai yana bashi labarin yadda zai kashe shi, daga baya Ya mai sallama sannan Ya fita da gawar wannan bawan,.
Tunda suka shigo gombe take ta kalle kalle garin yai mata kyau tana feeling wani happy ta rasa dalili, haka suka sauka a tasha da kyar suka Sami wajen kwana dan gobe zaai sabin diba a masarauta gobe zataje dan shiga,.
Tans bacci ta Fara mafarki
Dan faraaa matar take kallan sultana barka da zuwa garinku masarautar mu Amman sultana sai kina hadawa da addua fa, kallan ta sultana tai na gode Amman Dan Allah ke wace, murmushj matar tai babanki xai fada miki, kallanta ta sake yi kawu ne zai fada mun? Aa bashiba mahaifi Wanda ya haufe ki, zaro ido tai yana rayene? Kwarai kuwa, to yana ina? Yana masarautar mu, ina zuwa zan ganshi taya zan gane shi? Aa ba zaki ganeshi ba shi zai ganeki, sannan IN kikaje karki bari ina ganin fuskarki sosai dan yan garrin manya yan iskane suna bata matane, zaro ido tai bama zan Bari aga fuskata ba, dariya matar tai bance kina kin bude fuska bafa, murmushi sultana tai,.
Washe gari Ta gama shirinta har wajen masarautar kawu Ya kaita sannan ya Mata sallama mtanene a jere kuwa yana jiran kira
by Hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 7*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Kallan masarautar tai daga wajentama abun kallone balle cikinta,.
Baccinshi yake mai dadi karar da aka sakine ya tasheshi da adduar bacci ya tashi, tare da mikewa Ya bude window, tsaki yaja yau za debi sabin bayi kenan ni na rasa me yasa ake samun bayi alhalin kullun kisa ake a masarautar mtswww yaja saki, gabanshine Ya fadi da sauri Ya dafe girjinshi tare da karanto addua, sannan ya Sami saukin dukan girjin nashi ya shiga wanka,.
Budewa musu gate din akwai ana sanarwa mata subi layi mazama haka haka kuwa sukai sannan wani yazo Ya fara musu jawahi zamu Zaga da ku KO ina Dan daukarku a kowanne sashe da ake da bukata ,basuce komaiba sudai sunyi tsaye kamar sojoji, gaba Wanda ya gama musu magana yayi suka bishi a baya,.
Wata matacw ke zaune a parlour Ta caka uban dan kwali Ta daura daya kan daya ga bayi a kusa da itta suna mata hidima, Da sallama wata baiwa Ta shigo ta zube kasa tana kwasar gaisuwa, sannan ta kalli matar gimbiya sabin bayine inkina da bukata, kallan jakadiyar tayi ina bukatar masu tsafta da kyarki gudu biyar, angama ranki shi dade Ta fada tare da mikewa,.
Tana zuwa Ta zabi gudu biyar din kamar yadda ta fada sannan Sukai gaba, haka akai Ta zagawa dasu ana diba Amman har wannan lokacin ba a dauki sultana ba duk tabi Ta damu kardai aki daukanta ace ta hakura,.
Part din Maman sultan suka nufa itta Ma baiwa Ta isar mata da sako sultan dake kusa da itta ya kalleta momy me zakiyi da bayi kuma banda wadannan da kike dasu? Murmushi tai ta kalli jakadiyar autana yace basai Na dauka ba amma ki dakko min daya mai hankali saboda wata rana, mikewa tayi Ta fice dan cika aiki kallanta sultan yayi wato dole saikin dauka KO momy? Shafa kanshi tayi kawai zan daukane saboda wata rana jijjaga kai kawai yayi baice komaiba,.
Baiwar Na fita ta Fara kallan Yan matan gun idonta ya sauka kan sultana da idonta ya cika da kwalla amma fuskarta a rufe, kallan bawan kusa da itta tayi a dakko waccan ta fada tare da nuna sultana, ajiyar zuciya Ta sauke najin dadin An zabeta da sauri Ta mike Har hakan yasa baiwar murmusawa,kallan sauran bawan yayi To ku zamu wuce daku dakin girki zamu raba muku sauran aikin, Da haka sukai gaba,.
Kusa da jakadiya sultana ta karasa har kasa tana fadin ina wuni? Murmushi matar tayi lafiya qlau ya sunanki? Sultana, zaro ido tai sultana dakyau shigo muje, tai gaba sannan ittama tabi Bayan jakadiyar,.
Da sallama suka shiga parlour nan take sultana taji gabanta ya fadi idonta ya sauka kan momy dake kallanta kafin Ta kalli sultan da hankalinshi ke kan Waya, ganin jakadiya tayi kasa hakan ittama yasa tai kasa Ta fadin abin da jakadiyar Ta ke fada, kallanta momy tai ya sunan ki? Sultana ta fada kamar mai shirin kuka, dago kai sultan yayi jin mai irin sunan shi idonta kawai ya gani dan Ta rufe fuska idon ya tara hawaye, tabe baki yayi kawai yaci gaba da abun da yake, kallanta momy tai tana murmushi mai sunan danace ma ashe Ta fada Tana kallan sultan,uhmmm kawai yace.
To sultana ina miki barka da zuwa wannan masarautar da fatan zaki rike amana indai kika kasance Mai hakan zanji dadi Amman fa indai kika ki rike amana anan zamu bata gaskiya, kasa sultana tai da kai tare da fadin insha Allahu zan kiyaye, murmushin jin dadi momy tai sannan tsafta ki kasance Mai tsafta hakan zaisa IN kara sanki sannan ki ksance mai addini, duk zan kiyaye insha Allahu, kallan jakadiya momy tai kije ki kaita part din bayi na wannan bangaren nawa gobe ki taho da itta zan baata aikin da Ya face Ta dinga mun, angama ranki ya dde jakadiyar ta fada, sultan ne ya katse su tare da fadin ke baki bude fuska NE?kallanshi sultana tai Dan itta kadaice mai rufe da fuska agun nan take mafarki ya dawo mata inda waccan take ce mata kartana barin ana ganin fuskarta yan iska nada yawa a wannan masarautar hakan yasa Ta dubul bulce tana fara kinkina, tsaki yaja tare da fadin you can go, Da sauri ta mike jakadiya kuwa bata mikeba tunda bata San me yace ba, shikewa mamaki yake Ta gane mai yace batai kama da wadda tai karatu ba, tabe baki yayi sannan suka wuce da jakadiya
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 8*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Suna tafiya sultana Na kallan masarautar, a hankali Ta furta MASARAUTAR MUCE kallanta jakadiya tayi me kika ce? Da sauri Ta kalleta ba komai bance komaiba kawai dai masarautar ce tamun kyau, murnushi jakadiyar tayi ai wannan ma kadan kikaga wannan ba komai bane a cikin wannan masarautar, murmushi sultana tai ,daga wanne gari kikazo nan? Daga jigawa nake masaya kauyen birnin kudu jijjaga kai jakadiyar tai kice daga nesa kike ,batace komaiba sukai gaba wani babban gune dakuna kamar Na yan bourding skull kowanne daki mutun uku da sallama jakadiyar Ta shiga dakin wasu mata dake sanye da wani kayan da gani uniform ne suka amsa suna kallan sultana da jakadiya, karasawa dakin sukai, kallansu jakadiya tai gata ukun ku da fatan zaku hade kai saboda baa mana fada a wannan masarautar da fatan kun gane? Murmushi duka sukai tare da mikawa sultana hannu a tare daya tace sunana Zuwaira daya tace Zulai murmushi sultana Tai tare da rike hannun nasa gaba daya sunana sultana naji dadin haduwa daku ina fatan zamu rike amana insha Allah suka fada, kallan gadonta sultana tai ga uniform dinta, jakadiya Ta fice kan cewa gobe zatazo Ta mayar da itta Dan taji maye aikinta,.
Kallan ta sukai bazaki bude fuskarki ba, murmushi tai tare dafara cire mayafin dake kanta gashinta ya fara zubowa sai kyakkyawar fuskarta sakin baki sukai suna kallanta, ganin suna kallanta yasa Ta saki baki tare da fadin lafiya? Masha Allah suka fada a tare, murmushi tai tare da zama akan gadon nan sukaji ana sanarwa ba, afita da daddare a wannan masarautar inba cewa kai kaje ba, kallansu sultana tai saboda me ba,a fita da daddre tabe baki sukai mu zaki tambaya muma yaufa muka zo, haka sukai Ta hira kafin suka kwanta bacci ,.
12:00 sai juyi sultana take a kan gado, ganin su Zuwaira suna bacci yasa Ta Mike tasa takalminta Ta bude kofa a hankali Ta fito, inuwa Ta gani tabi inuwar da kallo mutun biyu ne har ta daina ganin inuwar, mikewa tayi tana tafiya abunta hankali kwance,.
Tsaywa tai a bakin kofa tana tunanin Ta fita ko karta fice NE, jin ana cewa ina zamuje Bayan ance baa fita da daddare hakan yasa ta murda kofa zata bude aka finciko Ta, Da sauri Ta juya,zuwaira ce Ta hade rai ina zaki Bayan kinaji ance baa fita da daddare ai ina ganinki kifa fice tai tsaki tare da jan hannunta suka koma, sukai nafila sannan sukaa kwanta bacci ya dauketa,.
Washe gari kiran farko ana buga Musa karfe suka tashi suka fara aikinsu na dakuna da toilet kamar dai makarantar kwana sannan sukai sallah kowa yasa uniform dinsu sannan su Zuwaira sukace Sun tafi gun aikinsu,.
Tun tana jiran jakadiya harta gaji Ta koma bacci wajen 8:0 jakadiya tazo Ta tasheta suka kama hanya yaudinma Ta rufe fuska da dankwalin kanta,.
Bangaren Maman sultan sukai ki shiga bari inje can tana kaiwanan tai gaba, kirjinta na duka Ta nufi ciki kanta a kasa, kawai saiji tayi taci karo har yasa tai kasa timmmm Ta fadi
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 9*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Washhhh Ta fada Dan taji faduwar sosai, dagowa tayi dan ganin waye wannan da bai iya taimako ba,ke baki iya tafiya bane KO baki gani, a dole mutun ya wani rufe fuska ba dole ba, mtswwww ya wuce Ta gefenta, momy dake sama taiwa sultana sannu tare da cewa Ta karaso, murmushin yake tai ta Mike tai ciki har kasa Ta zube tana kwasar gaisuwa, kallan ka Momy tai to y'all kadaici kin kwana a masarautar mu ko? Eh kawai tace, biyoni momy ta fada tare dayin gaba ittama tabi bayan Ta, wata kofa suka shiga wani hadden parlour yai musu welcome, da kallo sultana tabi parlour dan kuwa ya hadu wanncan Na kasan banzane ai kallan parlour tai ba kowa a ciki GA TV Da aka kunna ansa sunnah TV sai karatu ke tashi, zama momy tai a daya daga cikin kujerun parlour, sultana ta zukunna a kusa da itta,.
Sultana kinga nan shine inda nake kwana wannan parlour nane saican tai mata nuni da wata kofa dakinane ni tunda nake da bayi bana Bari suna shigomun wannan gun KO abinci IN angama jakadiya kawai naba dama take shigowa Ta kawo min abinci sai indai Tana da sako shine abun da kawai yake kawota,kinsan dalilin da yasa nake miki wannan bayanin? Aa ranki ya dade, murmushi tai saboda ke zaki dinga aiki a nan ke zaki dinga gyaramun KO ina na wannan bangaren harda Ma dakine kinsan me yasa na zabeki ba tare da Na zauna na fahimceba tukun? Aa sultana ta fada, ajiyar zuciya momy ta sauke saboda zuciya tace tashi daya Ta amince dake kawai naji ba zaki cuceniba shiyasa na zabeki, sannan ina San sanar dake karki GA Na sake miki ki dauka zakiyi yadda kikaga dama no hakan bazai yuyuba ina fatan kin gane Dan wlh innna gane baki da shirri ke mai cin amanace wlh korar Ki zansa ayi, insha Allah zan kiyaye, Allah yasa momy ta fada, yanzu saiki buden fuskarki Inga, waida me yasa baki San bude fuskar ki ne? Inda inda Ta Fara, a zuciya momy taba kanta amsa saboda ana yiwa mata fadene oho Mata, cire Dan kwalin sultana tai tare dayin kasa da kai, kallanta momy like tasan wannan face din a inama ajikinta na bata a wannan masrautar Ta Santa wannan face din ganin zata wahalar da kanta yasa Ta hakura tare da mikewa in angama abinci zaki je kitchen ki dakko min sannan yanzu zaki fara aikin ki ,tam sultana tace tare da dukar dakai momy kuma Ta tashi tayi ciki abunta,.
Da kallu sultana tabi parlour ba wani daddi Amman dole tai abun da aka sata, nan kuwa Ta Fara aikinta baji ba gani sai share share Da goge goge take kamar gidan yayi daddi dama can,.
Matar dake sakkowa daga stairs Tana taku Cikin kasauta da murmushia fuskarta saka makon wayan da take, Allah ya kaimu Ta fada sannan tai sallama da Mai wayan Ta kashe nan take ta hade fuska kamar bata taba murmushj ba dan itta kwata kwata basan raini, itta a dole matar sarki, nan bayi Ta suka zube suna kwasar gaisuwa, a hankali Ta Fara magana jibi hindu wato yata zata dawo saboda aikin yau dana gobe zasufi yawa sannan duk waccce tai dare wlh haka zata tafi dan bamai kwanan mun a nan, nan take cikin Zuwaira yaba da kulllll, kallanta matar tai tare da fadin ke kizo ki sameni a parlour na aikinki da ban ne,.
Jki ba kwari Zuwaira tabi bayanta, kamar yadda Momy ta amince da sultana haka ittama Ta amince da Zuwaira,.
Aikinta sultana take yanzu kitchen take gogewa Ta gama parlour har 10:30 tayi gashi kamar ba aikin take ba, jin An turo kofa yasa ta leka, sultan Ta gani tsaye yana kallan a Gogo ,ina kwana? Dan ban kwanaba zaki ganni NE, tabe baki tayi zata juya yace ji mana,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 10*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Juyowa tayi Tana kallanshi ganin yana mata kallan sama da kasa yasa ittama Ta kalli jikin Nata kafin Ta sake kallanshi, tabe baki yayi nifa wlh ke bana San ganinki Ma Amman bansan me yasa momy ta kawo ki nan bama itta da bata Bari ana shigo mata, murmushin yake tai batace komaiba, kallanta ya sake yi haka baw kewa Uban gidan Sa ya wani tsaya ya tsare shi da ido?aa Ta fada da sauri tare dayin kasa, kallanta yake yasan ganin fuskanta Amman itta kullun fuskanta a kulle KO me yasa oho mata,.
Me yasa kika Bari aka Sa miki sultana alhalin kinsan sunana NE? Kasa tai da kai sosai tana murmushi dan dariya kesan kwace mata wannan waishi waye yana da abun da dariya wlh, kakace me, da sauri Ta dago ba komai ganin tana murmushi yasa ya kare hade rai karfa Ta rainashi, ina abinci jakadiya bata kawo bane? Aa momy tace IN an gaama inje IN dakko, to ME kike jira har yanzu baki dakkoba wannan ai shashancine. Mtswww yai gaba,.
Mikewa tai ta fice Ta kuwa samu angama abincin haka tai ta dakkowa saida taje tana dawowa sau wajen biyar sannan ta samu Ta gama,.
Aikinta taci gaba dashi Ta gama gobe kitchen Tana fitowa taga momy da sultan na sakkowa sai murmushi yake abunshi, gaida momy ta, ta amsa da Fara, a tana kallan parlour Ya gugu sosai ba kadanba,.
Zama sukai a dining din momy tace tazo Ta zuba musu, kallan sultan momy tai son waikai me yasa baka cin abinci naka part din alhalin kana danaka masu girkin? Momy duk basu iya girkiba wlh nina nan yafi mum dadi inci da momy Na murmushi tai zan samoma Mai maka girkin karka damu banasan kana shan wuya, to kawai yace,.
A hankali sultana ta Fara magana ranki ya dade yanzu na gama saura aikin dakin, murnushi momy tai to jeki gyara kinga inkin gama ma saikeje part din son kimai abincin rana aikin iya KO? Gabanta ne ya fadi ittafa bata San abun da zai hadata dashi kwata kwata wlh Amman banda yadda Ta iya eh a fada tare dayin ciki,.
Dakin yai mata kyau sosai ba kadanba, hutan sultan Ta gani da momy shi haka Ta gama aikin sai wajen 12:00 Ta gama sannan taci abincin da suka rage ta wanke kwanikan,.
Sannan ta zauna Dan hutawa, 3:00 momy tasa jakadiya Ta rakata part din shi Dan tamai abincin ranar saboda 4:0 suke tashi a aiki, har kofan park din jakadiya the kaita sannan ta koma,.
Ya sanarwa da masu girkinshj kan zataxo su koya agunta abincin, zama tayi a kasan parlour duk Ta gaji tayama zata Fara abun da Ya kawota kullun tana cikin aiki daga nan ta koma nan, saida Ta huta sannan suka fara abun da ya kawota,
By Hajara mami nagty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 11*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Da sallama Hafiz Ya shiga part din mahaifiyar tashi bata parlour farko hakan yasa yayi Ciki a bakin kofa sukaci karo da Zuwaira da sauri Ta koma baya tai saurin zubewa kasa tana bashi hakuri kare mata kallo yayi kafin ya tabe baki yai wucewar shi da kallo Ta bishi kafin Ta sauke ajiyar zuciya Ta mike tare da ficewa, Dan zuwa aikin da aka sata .
Kusa maman shi ya zauna Ta kalleshi kasan cewa jibi hindu zata dawo KO? Eh Na sani duk tazo Ta dagawa mutane hankali akan wannan sultan din, ajiyar zuciya Maman tashi Ta sauke akiwa dolenka ka karbo mata soyayya agun sultan a matsayin ka na yayanta, turo baki yayi amma mama kinfi kowa sanin bana San rainin hankali irin na wannan yaron KO wlh ya fada mun magana nakan iya fasa Mai baki, oho koma Maye dole hindu Ta auri sultan kuma kaine zakayi wannan hanyar ki daina cewa dole fa nifa nakan iya illatashi babu ruwana wlh, mikewa yayi yanzu, Zanje IN sameshi inya amince to IN kuwa bai aminceba yayiwa kanshi ya Mike sai kuma ya kalli Maman tashi wannan yarinyar Data fita yanzu wace? Kallanshi tai sosai sabuwar baiwa tace, murmushi yayi nafasan halinka wlh karka kuskura kace zaka bata yarinyar mutane ina tsoran Randa wannan masarautar zasu ganeka kaida mahaifinka bansan wannan irin hukunci zasu daukaba, sudin banza sun isa suce zasu dauki wani fansane mulkin Na hannunmu wlh karyane itta kuma ai tsakani da Allah nake Santa badan komaiba yana kaiwa nan ya fice,.
A gajiye sultan ya shiga part din nashi duk ya gaji da wani dake dauke da kayan shi a hannun direct dakin ya wucw Bayan bawan ya ajjiye mai kayan ya fice zama yayi a bakin gado yana hutawa mtawww mutun Ma yayi aure two huta da wasu aikin da saidai kawai a hada mun ruwan wanka inyi IN fito wlh sannan a dakko min kayan da zan Sa Dan gaskiya ni bazan Bari wani bawa yadinga mun wannan abun ba indai ba wai Matata bace, mtswww ya kara jan tsaki ya mike tare da shigewa toilet yana Ta mita shi daya,.
Bayan Ya fito yasa kayanshi sannan ya fito har ya kama hanya dan zuwa part din mamanshi dan cin abinci idonshi ya sauka kan sultana Data tsaya tana kallanshi zai fice ohhhh fada danshi har ya manta da ittama, komawa yayi ya zauna ya wani hakimce a kan kujera yana kallanta, murmushi kawai tai duk baya ganin Ta yasan hakan tayi, karasawa dining tayi Ta zuba mai shinkafa da miyar dayasa kaji sai cabbage a wani ruba, ajjiyemai tai a gabanshi shibai dauka shibai daina kallantaba, dan tsaki taja tanasan yau tadan zaga masarautar Amman yana bata mata lokaci, juyawa tayi zatabar gun, taji yace where do you think you are going? Juyowa tayi tana kallanshi naga baka ci abuncin bane kuma ina da abun yi zaro ido yayi shi take fadawa Tana da abunyi shi wannan yarinyar nasan rainashi Amman zaiyi maganinta,.
Hade rai yayi ban Yadda dake ba fara cin abincinnan inga,ban ganeba Ta fada na sani KO kin samun maganin bita zai zai, zaro ido tai banganeba, ban damu da ki ganeba, ajiyar zuciya Ta sauke Ta dauki abincin tashi komai nagun saida Ta Taba yana kallanta sannan ya dauka ya fara ci yana wani yamutsa fuska, juyawa tayi Zata bar gun yayi saurin riko hannunta ,shock din dayajine yasa yai saurin saketa ittama da sauri Ta janye hannun, waya baki damar tafiya ya fada tare da cigaba da cin abincinshi? Babu tafada Amman plz karka sake rike mun hannun saboda back kyau kuma annabi yace yana wa matar Data gama budurcinta hartai aure ba tare da ta bari wani da na mijin daba muharraminta ba ya tabata ba indai wannan maganar Ta bata ma rai kayi hakuri duk yanzu Bada amincewa Ta ka tabaniba Amman kayi hakuri indai maganar tabata mai dole ne yasa na fada Ma saboda da gaba, tinda Ta Fara maganar ya tsaida cin abincin, me take nufi shi Dan iskane kome wannan yarinyar Ta rainashi wai yaushe ya farawa bayi hakane, juyowa yayi Dan mata magana yaji an shigo bako sallama KO baa fada mai ba yasan Hafiz ne shine maimai haka tsaki yaja tare da mai da kanshi gun Hafiz din ,karasowa Hafiz din yayi tare da fadin Allah yasa bani akewa wannan tsakinba? Ba dole aiwa mutun tsakiba ba yana shigowa mutane Daki ba KO sallama, murmushi Hafiz yayi kadai kasan dai bana San raini KO yanzu wlh sauna futar Ma Dad jini ya dakko abincin gaban sultan ya Fara ci,.
Wowww abincin yayi dadi a dinga hadawa da kwanona a wannan bangaren, malam fitar mun a bangare, mikewa Hafiz yayi sorry karka wani damu zan fice maka dama abu ne ya kawo ni inasan fada makane hindu jibi zata dawo saboda haka ka shirya zan hada auren kune, murmushi sultan yayi a matsayin ka nawa kenan nace banayi KO ana dole ne? Ba a dole amma ni zan maka, dariya sultan yayi yo aiko Dady wato sarki bai isah ba bare kai
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 12*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Zaro ido Hafiz yayi sarkin Allah sarki Amman ai zan iya saka halima wato uwarka Ta maka dole ko, Ya fada yana daga mai gira, a hargitse sultan yayi kanshi sultana tai saurin riko hannunshi, kallanta Hafiz yayi baiga wace ba amma yaga idonta aida kin bari yazo dana koyamai hankali wlh, yana kaiwa nan ya fice, sakin sultan tai ta tsaya tama rasa me zatai yanzu Ta gama wa,azi ,juyowa yayi yana kallanta rai bace kar ki sake mun shishshigi inba hakaba ranki zai baci, kayi hakuri gani nai abun naku zai koma fada ne..... Shut up Ya fada tare da yin wulli da kwanon hannunshi, Dasauri taja baya tana zaro ido ,hararar Ta yayi ya haura sama dakin shi ya kwanta, A rayuwa yaso yarinyar da bai san sunanta ko Tana raye KO bata nan oho, Cikin kojin tunani ya fada,.
A can baya
Sarki abdulsalam shine sarki wannan masarautar Wanda shine Na auta agun mahaifinsu Ahamad, Ahmad nada yaya maza uku mata uku KO wacce mata da nada dan, hajara ittace matar shi Ta farko Wanda take danta Mubarak(baban sultan )sai matar shi Ta biyu harira Tana da danta Abdullahi (baban Hafiz kenan )sai amarya wato Zainab Tana da danta abdulsalam (Baban sultana kenan ) haka yaran suka taso Cikin san junan su karatu duk a waje sukai duk Abdullahi shine halinshi daban shaye shaye bin mata duk shine sarki yasa anmai dukan Amman duk a banza sai dai addua kawai da yasa ake mashi haka har suka gama karatun su kaf cikinsu abdulsalam ya fisu komai farin jini ilimin boko da arabi baisa komai agabanshi yanasan talakawa hakana Mubarak halin Abdullahi duk yafi fita daban, bayan sun gama karatu Mahaifin nasu Ahmad yace KO wanne ya fito da mata saboda ya kusa murabus acikinsu wani zai hau, mahaifiyar Mubarak duk itta ke daure mai yin komai duk Ta ce yasa a ranshi shi zaa ba ma wannan sarautar tunda daga Mubarak bai wani damu da itta ba kuma ba yadda zaai ace abdulsalam Za,a alhalin shine karshe hakan yasa yabi ya daura WA kanshi San wannan sarauta duk sukai aure Amman banda abdulsalam Wanda yace shi baida wadda yake so,.
Haka har matan yayunshi suka haihu duk suka haifi maza, daya yaci sunan Hafiz dayan sultan Dan duk Rana daya aka haife su,.
Haka suka taso Maman sultan Nada saukin kai Amman banda Hajara Maman Hafiz saita dinga jan danta baya baya hakan yasa momy ittama Ta daina shiga har karta,.
Lokacin da abdulsalam ya gama karatu, lokacin yaran yayun nashi sun girma har sun Fara zuwa makaranta Ma, haka rayuwa taci gaba da tafiya har su sultan sun kama hanyar shekara wajen 9 hakan yasa Ahamad ya tsofa sosai yace yawa abdulsalam mata yar gun abokinshi dan lokacin Ma yana fama da rashin lafiya, shidai Abdullahi jira yake baban Ya mutu ya hau mulki abdulsalam bai yi musu ba hakama halima suka amince ranar daurin aure ciwon Ahamad yayi tsauri Dan baya iya zuwa KO ina hakan yasa baije daurin aurenba,.
Suna can daurin ya rubuta wasiya kan cewa abdulslam yake Sana daura a kan kujera saboda mutane da talakawa sunfi sanshi kuma abin da talakawa ke so hakan zaai,maman abdsalam jin mutuwar mijin Nata Ya jijjagata hakan yasa tabi banshi,.
Koda ka dawo daga gun aure hankalin yaran ya tashi dajin labari mahaifinsu ya rasu, shidai Mubarak bakin cikinshi ance kaninshi zaa daura, Maman Mubarak Ma bayan rasuwar su sarki da kwnaa uku tabi bayansu, duk masarautar Ta koma wni iri Maman Abdullahi kuwa tace saitaga danta akan mulki zata mutu, tace karya nuna baya so,.
Haka akai wta daya da mutuwar sannan aka cikawa sarki wasiyar shi nadaura abdulsalam a mulki, ranar kuwa Abdullahi a sha giya ba dadi
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 13*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Kuna fa sorry dani saboda da typing error,.
Haka aka nada abdulsalam a amatsayin wannan sarki a wannan zamani,.
Haka rayuwa ke Ta yafiya a wannan masarauta kowa hankainshi kwance hakama talakawa nasan sarkinsu ba kadanba, kuda wata rana Abdullahi ya taba gwada yayan shi Mubarak yaga yadda zaiyi acting bai nuna mai komaiba a kan wannan sarautar da baa bashiba dan shi nunawa yayi ba komai bane,.
Haka rayuwa ke tafiya har halima matar abdulsalam Ta Sami ciki kullun sultan yana can yakan cewa Maman sultana zatamai kani KO kanwa tunda Maman shi itta tadaina haihuwa lokacin yana primary 3 lokacin kuma Maman Hafiz itta Ta sake samun ciki cikin nasuna kusan tare yake tafiya dana Maman sultana a wannan lokacin ,.
Jinin Maman sultana da Na Maman sultan yafi haduwa Dan sultan yafi sabawa da maman sultan Ma, tai kuwa mishi alkawarin indai Mace ta haifa Ta bashi itta indai Na mijine shi kuma shi zai reneta,.
Wata na tafi lokaci na cigaba hakama second day minute gashi yanzu Allan Ya kawo mu ranar nakuda ga halima wato Maman sultan,.
Hakan yasa abdulsalam duk hankalinshi ya Tashi sai jeka ka dawo yake a daki, Mubarak part din Maman Abdullahi ya nufa dann sanar mata da haihuwar halima yana zuwa kofa yaji suna magana,.
Mama ni wlh na rasa Ya zanyi sarautar nan nake so KO Ta yayane, hmmm karka wani dumu ka dauki duk matakin da kaga yama indai zaka samu sarautar murmushi yayi naji wai matar shi nacan zata haihu mai zai hana kije ki kasheta itta da abun da zata haifa ni kuma zanji da sauran, hakan yama Ta fada Tana kallanshi eh yace, kaje kaji dashi nasan yanzu yana can wajen haihuwar kasan yadda zakayi ka jashi can inda ba mutane mikewa yayi Ya fice hakan yasa Mubarak buya bazai bari a aiwatar da wannan abun a gabanshiba, ya rasa ina zaisa kanshi Ya rasa meke mai dadi kawai Ya fice,.
Hakan kuwa akai Maman Mubarak Ta tafi dakin da maman sultana zata haihu sanda taje ta haihu ma taji dadi jin mace ta haifa tana zuwa Ta kuri duk Wanda suke gun sannan tasa nata yan gadin,kusa da gadon Maman sultana taje Ta tsaya, tasa hannunta zata shaketa dai dai lokacin Ta bude ido hakan yasa tai wulli da itta Ta Mike Da sauri Tana kallanta, kaduwa Maman Abdullahi tai a kasa Ta mike tare da dauka wukan dake kusa da itta a jikin fruit, Maman sultana ta juya Ta dauki yarinyar kenan taji saukan wuka a bayanta a dan razane Ta juya hakan yasa Ta bige Maman Abdullahi din sannan ta dauki yarinyar Ta rufe fuskan Ta yanke shawaran kawai Ta tafi da yarinyar inba hakaba itta kasheta zasuyi, haka dauki abun da zata dauka Ta dauki car key ya fice tare da rufe fuska Ta shiga Wanda aka tsaro sukabi bayanta Wanda harda bawan abdulsalm daya amince da shi Ashe shima mugune mai suna Hafiz, gudu kawai take a mota bata Ta damu da yadda bayanta ke mata zafiba haka har ta isa masaya anan ne Ta hadu dakawu Ta bashi sultana ta fadamai sunan da zai Sa mata (kuma kar kuce na danyi abun fa ),.
By hajara Mami natty
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 14*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
A bagaren Abdullahi kuwa sawa yayi aka kira Mai abdulsalam masarauta yana zuwa Ta baya Ya kwala mai karfe sannan ya sashi a bayan doki yayi dakin ajiya dashi Mubarak yabi bayansu Dan yana ganin sanda Abdullahi yayi can din,.
Yana zuwa Ya kwarawa abdulsalam ruwa nan kuwa ya mildew, kallan yayan nashi yayi, yaya ME muke nan? Murnushi yayi aiba kai daya bane kake Cikin hadariba harda matar ka,kallanshi yayi ban gane ba, ina nufin ittama tana can zaa kasheta indai bakai wani abu ba, me kake so yaya? Dariya yayi so nake in hau karagar mulki, yanzu yaya Akan hakan ka yanke wannan shawarar Na yadda zan sauka ka barmin Matata Ta, mikamai Ta karda yayi rubuta ka sauka Kana San a nadani sannan inasan kabar wannan masarautar, shiru yaya yana tunanin talakawan dake sanshi Amman baida zabi haka Ya rubuta, jin muryar Mubarak sukai yana fadin me kake wai Abdullahi? Shine abun da mahaifun mu Ya koyar damu kenan?.
Shiru Abdullahi yayi wannan zai tunamai asiri inbai dauki mataki ba ,juyawa yayi Ya dauki karfen dake kusa dashi ba tsammani Abdullahi yaji saukan farfe hakan yasa Ya fadi agun a Mace, Da sauri abdulsalan yayi kanshi shima Ya bashi daya akafa, hakan yasa Ya zube yana cije lebe, wayanshice Ta fara ringing yana dubawa yaga mamanshi ta gudu kawai tace sannan ittama the mutu agun Dan ta bugu,.
Wata kara Ya saki Ya kalli abdulsalam matar ka Ta gudu Da yarka da nayi niyar kasheka Amman zan barka sboda nasan zasu dawo wataran a gabansu zan kashe ka cikin takaici abdulsalam Ya kalleshi nasan zaka iya Amman da ka kasheni yanzu gara kawai in huta, naushi Ya bashi a baki bana bukatar jin komai daga bakinka, ya daurshi Ya dauki gawar Mubarak ya fice back Wanda ya ganshi haka Ya kaishi dakinshi ya rufe da bargo abun kamar asiri ba Wanda ya ganshi haka yaje masarautar Ya ajjiye takardar sannan ya fice,.
Yana zuwa yaga gawar mamanshi Ya sanar aka nemi sarki aka rasa dashi da matar shi sai wasika da aka gani, anje kiran Mubarak aka gawa, hankalin masarauta duk Ya tashi haka aka yiwa gawar sutura,.
Bayan andawo aka karanta wasika inda yake fadin zaiyi Dan tafiya bai sanarwa kowaba yanasan a daura wani yayan nashi Dan zai dade,.
Anan nan Abdullahi yasan yadda ya hada akace motan da suka fita tayi accident duk Sun mutu haka akai zaman makoki sannan aka Nada Abdullah akan mulki, haka masarautar taci gaba Da tafiya komai sai a hankali Dan halin Hafiz Na ubanshine kawai dai kisane da baya yi koda yawa mace fade sarkin shi yake sawa akashe su kawai kar a tunamai asiri Dan baa San Hafiz yana wannan halinba sai mamanshi ansandai yana shaye shaye, shima sarkin yace bashi daya bane ataya danshi da addua wannan kenan,.
Back to business
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 15*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Cigaban labari,.
Kallan glass din daya fasa tayi kafin Ta sauke ajiyar zuciya Ta zukunna Ta fara debewa Ta Fara tsaki nifa abun daya kawo ni daban bazanzo IN dinga abun dabai shafeniba mtswwww, sultan dake tsaye yayi holding arm, ya tabe baki dama bayi akwai abun da suke zaba zasuyi dawanda ba za suyiba ba, Da sauri Ta Mike tana kallanshi, mtswwww yarinyar nan bansan yadda akai kika rainaniba Amman zan koya miki hankali yana kaiwa nan yai gaba, tsaki ittama ta share gun tana fadin danma dai masarautar muce, sa kuma abun Ya bata dariya wai masarautar muce, Tana gamawa Ta fice tana Dan zaga masarautar karfa inje IN bata abun da tace kenan, kallan wani gabare tai bataga mutane nayin gunba KO me yasa oho kallan gun tai sosai dakin ajiya ne KO inje ingani ne?tA tambayi kanta,.
Hafiz na fitowa duk ranshi a bace shiyasa yacewa mama bazai jeba fa dai dai lokacin Zuwaira Ta dawo daga aikenta ganinshi yasa Ta zube tana kwasar gaisuwa, kallan ta yayi ke daga ina kika fito yaushe kikazo masarautar nan kinsan masarautar muce, kanta na kasa tace jiya itta tunda ta ganshi taji bata sanshi bai mataba ,OK ina fatan kin san koni waye bana daukan raini, a zuciya tace To me Ya kawo haka kuma a fili kuwa cewa tayi Na sani ai,.
Sultan yana fita gun Dady yayi saida akai mai iso sannan aka basu waje Bayan Ya gaida Dady ya amsa da fara, sannan yace lafiya na ganka nan? Eh Dady kawai ina zaune naji inasan bincike game da mutuwar mahaifina da kuma kaninshi abdulsalam Dan gani nake kamar dasa hannun,
Please remind me 2 remind U about reminding me to send U this reminder that reminds me of reminding U that U never have to remind me 2 remember U, I ALWAYS DO!
Only the open heart receives
LOVE
Only the open mind receives
WISDOM
Only the open hand receives
GIFTS
and...
Only the CUTE 1"s receive
MESSAGES From ME!
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 16*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Kallanshi sarkin yayi Ya hade rai, me kake nufi kana nufin ni banyi binciken daya kamataba kenan?aa niba haka nace ba kawai inasan kare lafiyarka ne saboda kaima zaa iya kawoma far maki, hmmm naji kuma Na gode Amman kabarshi kawai ina da masu kareni, Kallanshi kawai sultan yayi sannan ya tabe baki ya fice kawai,.
Sultana har tayi wajen bangaren ajiya kome Ta tuna kuma kawai Ta fasa Ta juya Ta koma baya kawai ,.
Haka yau din taci gaba, kafin magari duk suka koma dakinsu a gajiye Zuwaira Ta shigo lokacin sultana ta dade da dawowa, kallanata sultana tai sannu kin gaji ne? Sosai kuwa Dan yau aiki mukasha wai yarta zata dawo daga India Ta gama karatunta, tabe baki sultana tai tace Allah ya dawo da itta muga nata zaman,.
Direct part din mamanshi yaje, ana mata hira tana murmusawa zama yayi kusa da itta, Ya akai son meke damunka? Momy kinsan wannan hindu damuna take wai yanzu Ta kusa dawowa wlh ki ja mata kunne inba hakaba rai zaizo yana baci, ajiyar zuciya Ta sauke karka damu koni bana sanka da wannan hindu kwata kwata bada da kamun kai gata da rashin mutunci taya kuwa zanso dana Ya aureta, daura kanshi yayi a cinyarta zan koya mata hankali kuwa, aa ni bance ba karka Jawa mutane abun fada, baice komaiba sai tabe baki kawai da yayi,.
Son Ya girkin yarinyar Ya Ma ka ne? Tabe baki yayi eh yayi, OK KO zan ce Ta dinga zuwa tana maka aiki a part din naka NE? Shiru yayi Amman momy ke fa ba aiki take miki ba? Karka damu tunda na samu ka amince da itta ai shikenan kawai dai Kana addua kasan sharrin shaidan, kaiii momy ki daina wannan zancen ma nikam, murmushi kawai tai tasan halin danta bazai biyewa shidan ba da haka sukai Ta hira kafin Ya tafi masallaci sai bayan isha Ya koma part dinshi lokacin kowa ke kokarin komawa gidanshi Dan kare lafiyar shi,.
Sultana wai jiya me yasa kika wani dauki kafa zaki fice alhalin kinji jan kunnen da aka mana?uhmmm kawai dai ina san fitane Inga yadda masarautar takene, Hmmmm da rana bai isheki yawoba sai da daddare? Jan bargo sultana tai tare da fadin ba zaki ganeba bane yarinyara ,tasowa Zuwaira tai ta karasa gunta Allah ki fada mun Zulai ce Ta karba kuzo muci abinci kunsan mune masu girki a wannan masarautar saboda haka abinci sai kun kaji dashi, mikewa sultana tai kamar kuwa kinsan yanzu nake ji Ta fada tare da sakkowa sukaci abincin sannan suka kwanta,.
Yauma tayi niyar fita da daddaren Amman ganin Zuwaira taki bacci yasa Ta hakura saida Zuwaira Ta tabbatar tayi bacci sannan ta Rabu da itta Ta kwanta bacci ittama,.
Washe gari da safe ta tafi kasancewar yau Ta San inda zataw, part din momy taje ta Fara aikinta Ta dan lokacin bata atashiba Ta gama aikin kitchen kenan Ta fito parlour zata fara sultan ya shigo da sallama,.
Ta amsa Tana kallanshi sannan tai kasa tana gaidashi, hade rai yayi baice komaiba yayi sama danshi haka yake dole da safe sai yaje gaidata in ya taso daga masallaci,. Da sallama Ya shiga ittama Ta gama karatun Quran kenan Ta kalleshi tana murmushi antashi lafiya son?har kasa Ya gaidata sannan ya Mike zai fice, sultana tazo? Ta tambaye shi kallanta yayi wace sultana kuma? Daure rai tayi ban saniba, murmsuhi yayi momy ban santaba Amman naga wata Tana aiki a parlour, OK ka aiko min itta, Da sauri Ya kalleta momy bafa nasan Ma wannan yarinyar magana, to sai gashi nace yanzu ka mata Ya kenan?
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 17*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Turo baki yayi tare da ficewa, ganinta yayi a wajen Centre table tana gogewa aikinta take bama tasan yana kallanta ba har ya karasa Ta bayanta yakai hannu zai taba ba Ya tuna da maganar da tamai jiya hakan yasa Ya janye hannu yayi holding arm yana kallanta tana aikin shifa baya San mata magana yaga yanzu Ta Fara rainashi kuma baya San raini dole Ya Fara hade mata rai Ta daina ganin murmushin Ma duk tabi Ta wani rufe fuska kome take rufewa oho mata, tsaki Ya kara ja, Da zuciya daya sultana ta juyo zata dakko abu Amman saijin taci karo tai hakan yasa tai baya zata fada kan Centre table din yai saurin riko hannunta, sannan ya dago da itta Ya sake hade rai, duk Ta tsorata barinma da taga yadda ya hade rai tashi daya taci wani tsoranshi Ya saukar mata, kasa tai da sauri ME kake bukata ranka Ya Dade? Tsaki yaja banda ma abu irin na momy maye zata wani Sa yakira Ta, kije momy Na kiranki Ya fada tare da rabawa Ta gefenta Ya wuce, ajiyar heart ta sauke sannan tai dakin momy din,.
Da sallama Ta shiga, tai kasa tare da gaida momy,da murmushi momy Ta amsa, sultana so nake zaki Na zuwa can bangaren sultan kina mai aiki zai fada miki abun da yake bukata inkinje can din sosai gabanta Ya fadi ittafa tsoranshi take,.
Sannan Abu na gaba basan kuna zama tare duk da nasan dana Amman shaidan baibar kowaba, kallanta sultana tai, eh nasan kinsan me nake nufi ai, eh na gane kuma insha allahu zan kiyaye, Allah yasa mom Ta fada,.
Haka sultana ta fito jki ba dadi Ta gama abun da take sannan ta nufi bangaren sultan,.
Dake masu gadin gun jiya sunsan da zuwanta Tana shiga suka bata gu Ta wuce,..
Saida Ta Dade a bakin kofan kafin Ta yi shahada Ta shiga Dan kawai bata tana San dawowa part dinshi da aiki ba, a hankali Ta shiga tana rabe rabe tare da adduar Allah yasa baya parlour a hankali take tafiya kamar barauniya har ta kusa shiga kitchen taji yace Maye hakan sata zaki mun? A dan razane Ta juya tana kallanshi sai kuma tai kasa tuba nake ranka Ya dade,juyar dakai yayi kamar Ta Allah, zonan two fada yana kallanta, ittma kallanshi tai ni? Aa ni Ya fada tare da kara hade rai mikewa tai taje gun nashi kamar yadda ya bukata,.
A kasa Ta zauna tai kasa dakai, ina fatan kinsan aikace aikacen Da zaki dunga yiko gyaran daki wankin toilet gyaran parlour ,griki kindai sauran Ya fada yana kallanta, eh nasani Amman AI momy batace mun zan dinga shiga dakinka ba, zaro ido yayi me kike nufi zan miki wani abun kumama in rasa WA zanwa sai baiwata? Amman kin gama dani, tuba nake ranka Ya...... Bata karasa ba Ya daka mata tsawa shut up dallacan, inkin GA dama karkiyi nida ke naga Wanda saiyi winning,.
Yi hakuri, ke Ya dama wannan kuma dole ki buden fuskar ki in gani, kallanshi tai duk idonta Ya kawo hawaye Dan duk Ya gama bata tsoro, dauke kai yayi ganin hawaye a idonta tana karyamai zuciya shi so yake kawai Ta dinga jin tsoranshi, katseshi tai Dan Allah kayi hakuri bana San bude idoo fuska tane, har ya juyo zai yi masifar tashi ganin hawaye take yace tashi kije plz, Da sauri Ta mike har tana tuntube, abunma dariya yaso bashi Amman Ya dake
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 18*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
The page is for you Page Salsabila
F-E-A-R has two meanings : F- Forget
E- Everything
A- And
R- Run
OR ...
F - Face
E - Everything
A - And
R - Rise
The Choice is YOURS ...!!!
Koda da taje kitchen din Ma shiru tayi itta gaskiya zata nemi alfarma bata San wannan bangaren, haka Ta fara aikinta Tana ta jiran abokan aikinta na jiya su zo Amman bata gansuba kuma ba zata iya tambayar shiba,.
Duk aikin yau ya mata yawa kasancewar itta daya keyi haka har ta gama,.
A bagaren su Zuwaira kuwa soye soye suke sosai Dan walima Maman hindu zata hada saboda dawowarta,.
Da sallama Hafiz Ya shiga bangaren Maman nashi, ganin hakan yasa bayin ficewa suka basu gu, mama nifa wlh ki cewa Hindu ta hakura da wannan yaron baida mutunci, Hmmmm naji zan gwada Amman kana ganin zata hakura kuwa yadda take sanshi ya zanyi da alkawarin dana daukar mata kafa San autace, I can do anything for her, tabe baki yayi To ni kuwa ba zata jamun rainiba taje itta tasan yadda zatai Ta shawo kanshi ni bai damen ba, ya mike ni zan wuce, Da sallama Zuwaira Ta shigo hakan yasa ya bita da idol har Cikin ranshi yake Santa indai kuwa taki yakan iya mata dole ba ruwanshi,.
Sultana na gama abincin Ta jere a dinnig har lokacin yana parlour kallo yake abunshi taya zata fara zuwa tace Mai ta gama yau so take taje inda taje jiya.
Har kasa Ta duka ranka ya dade na gama, shiru yai mata baice komaiba, kallanshi tai hankalinshi na kan TV, Na gama Ta sake fada,nan Ma baice mata komai ba, ajiyar zuciya Ta sauke tare da sake fadin Na...... Bata gama ya juyo kinga aiba aikin gaba daya kika gama kin mun gyaran gidan ne? Da sauri Ta mike ai bansan kuma ina ne ya rage bafa, OK to zaki mun murdeni sai in fada miki tunda baki da ido, hawaye Ta Fara wannan nasan tada mata hankali, Da sauri Ta Mike tayi Sama inda taga yana sakkowa wani lokacin, binta yayi da ido tare da murmushi kawai yana San yaga Ta hargitse tana shirin Mai kuka ba abun da yake so ma irin yaga fuskanta Amman ba hali duk tabi Ta wani rufe fuska,.
Tura kofan dakin tai dakin a gyare yake kamar bana mazaba Amman Ya dage sai Ta gyara mai anya ba wayo yake San mataba yaje yai mata wani abunba? Da sauri Ta kawar da wannan tunanin Allah zai kare Ta fada,.
Rike kugu tai ta ina zan fara nema? Toilet ta fada hakan yasa Ta fada toilet, dukda a wanke yake Amman ta fara wankewa gashi babba, tunkan tai rabima Ta gaji,. Haka dai Ta daure Ta ci gaba da aikin Nata,.
Dakin nashi Ta dawo Ta fara gyarawa, tai goge gogenta sannan tai abun daya dace washhhh Ta fada tare da zama akan gadon, kallan drower dake kusa da itta tai ba tare da wani tunaniba Ta jawo drower din hutan wannan matar ta gani wacce take mafarki da itta itta da wani da gani mijinta ne yadda suke wa junan su kallan soyayya, wani hutan Ta dakko hutan families ne lokacin wannan matar nada ciki sultan take kusa da itta ya dafa Cikin yana murmushi, kallan hutan take sosai to me yasa matar take San tazo wannan masarautar, jin an turo kofa yasa tai sauri buye hutanan a bayanta amma ina kafin tayi hakan har ya gani kallanta yayi Sama da kasa yana hararar Ta, dan baya tayi taji ba har gudu duk tabi Ta dubul bulce sata kike mum? Ya tambayeta yana zaro ido tare da nufar inda take din, wlh ba sata nake ma ba a kasa naga su shine nake kwashema, ganin yaki tsayawa yasa tai saurin miko mai hutannan hannun nata gashi wlh a kasa Na gansu ,bai karba ba kuma bai fasa nufu tanba, rufe ido tai sai hawaye wannan shine tsautsayi ME Ya kaita taba mashi kayanshi, har ya matso kusa da itta sosai bata saniba idonta a rufe yake kawai dai tana jin saukan nunfashin shine, kallanta yayi ya kura mata ido a duk inda yaga idonta zai ganetq dukda bai gaba fuskarta Amman zai gane idonta namai kama dana aunty shi (wato maman sultana )karbar hutan yayi juya kawai lokacin idonta Na rufe
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 19*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
A hankali Ta bude ido jin ya karbi hutan Ta sauke ajiyar heart. Ganin ya zauna akan table din computer shi Na dakin yana kallan hutan yasa Ta juya zata fice, kallanta yayi kin gama aikinne, eh tace tana shirin fita, zonan yafada ganin tana san fucewa ne, a hankali Ta dawo duk jikinta yayi sanyi wai yau itta ake cewa barauniya akan huto, zama tai a kasa kanta yana kasa, so nake in fada miki bana san tabe tabe bawai kawai danna baki damar shigo min dakiba kina mun bincikeba zamu iya batawa akan hakan,.
Hawaye Ta Fara Dan Allah kayi hakuri bazan sakeba wlh wannan dinma tsautsayine kuma bazan kara ba, murmushi yayi baice komaiba wayanshi ta Fara ringing kallan wayan yayi dake kan gado ya kalleta dakko min wacccan wayan,mikewa tayi taje Ta dakko Ta kurawa screen din ido ansa hindatu,ganin Tana kallan wayan bata kawoba yasa yace mata waye? Kallanshi tai hindatu ce, tsaki yayi ki dauka kice mata bana nan, kallanshi tai itta batasan irin haka may be Ma bdurwarshi ce suka bata ya jawo mata bakin jini,.
Kallanta yayi ba dake nake ba indai Ta katse baki daga ranki yakan iya baci, dauka tayi Ta kara a kunne, can bangaren taji ance yaya sultan, bashi bane baya kus.......tun kafin Ta karasa Hindu ta katseta To ke uban waye me Ya hadaki dashi? Dauke wayan daga kunnenta sultana tai Dan ta cika mata kunne, tsaki sultanan taja Wanda yasa har hindun taji, maida wayan sultana tai kunnenta karki wani damu niba komai nashi bace kinzo kina Ta wani ihu sai anjima tana kaiwa nan Ta kashe, kallanta sultan yake da murmushi a face dinshi tsaki taja tare da ajjiye mai wayan Ta fice abunta kawai batace mai komaiba, murmushi yayi tare da juyawa yaci gaba da abun da yake,.
Sultana kuwa na fita taji tana San zuwa wannan dakin ajiyar, hakan yasa Ta nufi gun kawai ganin wani tayi yana Ta sauri da gani fuskanshi a rufe yake da sauri tabi bayanshi, Baba baba, jin ana kiranshi yasa ya tsaya Amman bai juyo ba Baba can zaka banga mutane a gunba kuma nim ina San shiga inzo muje Tare? Tsaki sarkin yaja yaci gaba da tafiya aikuwa Ta bishi a baya tana fadin ka jirani mana, murmushi yake may be wannan ranar mutuwar yarinyar ne ya fada a ranshi ganin yaki jiranta sai sauri yake yasa Ta tsaya tana tsaki ni a hankali zanje kawai kayi Ta sauri kamar ba tsohu ba, wani ne yazo wucewa ya ganta da sauri ya karasa gunta, yarnan me kike anan? Uhmm can nake San zuwa Ta nuna mai da yatsa, kallan gun yayi kafin ya kalleta baki San an hana zuwa can ba, can din Amman yanzu fa naga wani Baba yayi gun jijjaga kai yayi karki bishi aljanu sunyi yawa a gun nan yanzu haka aljanu ne kika gani duk Wanda ya shiga gunnan yawanshi saidai aga gawar mutun kinga kar kije, tabe baki tai Dan itta bata wani yadda ba kawai ace wai aljanu su ba Allah ne yayi suba,ganin tana wani dan zance zance yasa ya ce wuce mu tafi Da gani zakiyi taurin kai haka ya tusata a gaba suka tafi,.
Wannan ranar da sarki yaje kawai ya tusa abdulsalam a gaba wai saiya fada Mai yaushe yarinyar shi zata dawo, ka fada mun nace, kallanshi abdulsalam yayi maye naka na damuwa da sai na fada maka? Mafarki nayi wai tazo ta runs mun asiri shine naga kafin Ta tuna mun ni gara IN kasheta, murmushi abdulsalam yayi Ashe ai bai kamata ka tsorata haka ba maye naka na tsorata ai jarumi irinka baya tsorata KO ban fada makaba wannan abun dakai nakin kashene shine babban kuskuren dakai, sosai sarki ya zuciya ,ya Mike ni zan nemota da kaina saidai indai bata shigo wannan masarautar ba nasan indai batai kama dakaiba to zatayi kama da uwarta ai yana kaiwa nan ya fice ranshi a bace da murmushin takaici abdulsalam ya bishi wai ace dan uwanka ke maka wannan abun Allah ya kare Ameena
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 20*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Su Zuwaira ke zaune adaki suna cin abinci, Zuwaira ke fadin ni wlh bana San wannan Hafiz din Dan gidan sarkin nan cewar Zuwaira kenan da gani dan iska ne, kallan ta sultana tai to daman a bangaren shi kike aiki ne? Aa a bangaren mamanshine nake aiki ammq kallan Da yake mun ne bana so, murmushi sultan tai kika sani KO yana cikine, harararta Zuwaira tai ina cewa bana sanshi kina mum wani zance, Zulai ce Ta karba sanda zaku june sani mukai, tsaki taja tare da mikewa tabar musu abinci, murmushi sultana tai,.
Kinsan ranar yazo gun sultan yake nemanshi da fada, Da sauri Zuwaira Ta zauna kusa da itta ni inA ji ana fadan sultan dinnan Amman ban taba ganinshi ba inasan ganinshi haka Zulai Ta matso ta dameta akan Ta fada musu ya yake ,kallansu tai tai tsaki tare da mikewa nima Na fishi kyau fa ba wani mai kyau bane, ta fada Tana tsaki, kallanta sukai sai kuma suka yi tsaki suma kice kawai ba zaki fada mana ba eh bazan fada dinba ta kwanta tare dajan barko tayi kwanciyar Ta ,.
1:00am sultana ta tashi daga baccin da take kallan su Zuwaira tai baccin su suke abun su, hmmm Ta sauke ajiyar zuciya Ta Mike ta dauke hijab dinta tare da dankwali Ta rufe fuskanta yau ba abin da zai hanata zuwa wannan dakin ajiyar, saida Ta tabbatar duk baccin su suke baccin na masu dadi, fice tayi abunta Ta bude kofan Ta fice masarautar tayi tsif kamar ba mutane a ciki kamar ba halitta a ciki sai kuma taji gabanta na faduwa dum dum ganin masarautar ba kowa ,tafiya take a hankali gabanta Na dukan hamshin hamshin, haka Ta ci gaba da tafiya ,.
A dan razane taja baya ganin mutune da jajayen kaya a tsaye da sauri taja baya gabanta na dukan Tara Tara,Wasu dagarai ne ke dukan wani bawa ta ko ina tun yana ihu har ya kasa, kasa kunne tayi Dan taji me suke fada wato kune Wanda baku jin magana ance kar aje gu Amman sai kunje ance adaina zuwa dakin ajiya Amman sai kunje to yau zaka mutu inyaso sai muga Ta zuwa dakin ajiyar, dakanshi suka ci gaba dayi Wanda ke tsaya acan baya baice kalaba kuma bataga fuskarshiba,.
Tana gani suka caka mai wuka abisa umarnin Wanda ke tsaye acan baya, toshe bakinta tayi ganin tanasan yin ihu garin Ta juya Ta buge flower dake kusa da itta ya kuwa fadi gaba dakansu suka kalli gun harda sarki dake tsaye kallansu yayi kuje ku duba koma waye ku tabbaatar kun nemo shi ya zauna akan kujerar dake kusa dashi kuma waye a nemoshi dan zai iya tuna musu asiri,.
Sauri kawai sultana take kirjinta na dukan tara Tara wannan ai bala,i ne dama haka ake a wannan masarautar wannan wacce irin masarautace, jin motsin mutane yasa Ta kara sauri aikuwa sai ji tayi ance gata can, Da gudu Ta kuwa kwasa haka suma, haki Ta tsaya Tana yi Dan ta balain gajiya, ji tayi kawai an jata bataga fuskar kowa ba kawai taga ana janta bata San inda ake jantaba dan kwata kwata hankalinta baya jikinta, har part dinshi sultan ya kaita, sannan ya saketa, tana ganin mutanen Na wucewa sai kuma suka dawo suka tsaya a kusa da kofan part din sultan din suna ganin inuwar su, dayane ya fara magana ai kawai muna ganinta kasheta za muyi inba hakaba zamusha wuya dan da gani mace ce, kallan sultan tai suna kallo Na Ta Fara mai kuka har yana shirin fita hakan yasa yai saurin rufe mata baki tare da jinjinar da itta a jikin bango
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 21*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
This page is for you shamsiyya Umar Dan zomo
Kallan shi take duk idonta ya ciko da kwallah, matse Ta yayi sosai bayasan tayi wani motsi zata iya sawa a kamata kuma bashi da yadda zaiyi shidai kawai yasan bazasu ce zasu kamashi bane, matsawa yayi dai dai kunnenta, karkiyi wani motsi kuma kidaina mun kuka ba ina tare dake ba zakisa su kamaki kuma badake zanyi indai suka gano kika nan, rike shi tai sosai bata San ya saketa a yanzu,bai saketa ba har saida suka tafi suka daina ganin su, dagowa sultan yayi yana kallanta to ki sakeni baki San Allah ya hanaba, Da sauri Ta sake shi taja baya tana dan zaro ido murmushi yayi,kallanshi tai kayi hakuri rashin sanine kuma Allah Ma yasan da haka,.
Kallan yayi ya hade rai me Ya fito dake da wannan daran? Kame kame ta Fara, baa fada muku ba,a fitowa da daddare a wannan masarautar ba? Kinsan da ban fito shan ruwaba na ganki Ta sama ba da kina cikin matsala da saidai a sami gawar ki badai ke ba, Dan hawaye Ta Fara abu nake nema NE shiyasa Na fito fa, wannan abu kike nema da ba zaki iya hakura ba sai gobe iyeh ba tambayar ki nake ba kinmun shiru? Hawaye Ta Fara Dan Allah kadaina mun tambaya mana ni nasan yadda nakeji fa, kallan ta yayi sosai OK da kyau fitar mun a part, zaro ido tai tare da kallanshi inje akasheni, OK yanzu ya ME kike San in miki shiru tayi tana tunani, sai kuma Ta kalleshi ban San inda zani bafa, OK baki da zabin daya wuce ki fice kawai, ganin da gaske yake yasa Ta juya Tana hawaye Ta juya zata fice Ta kama handle din tana kallan shi KO zaice Ta zauna Amman Ya juya ma yaki ya juyo addua kawai Ta Fara zata fita yai saurin jawota har saida Ta dan buge dashi sannan taja baya,.
Kallanta yayi Tana hawaye, sai kuma Ta bashi tausayi, OK ke bakisan ki bada hakuri bako shine zaki fuce kenan da kiba daba hakuri gara ki futa KO? Kallan shi tai Dan itta bataga laifin da tamai ba,ranka ya Dade banfa San me nama bafa, sakinta yayi ya haura sama abunshi ta bishi da ido itta yanzu tsoro take ji gara ace Tana dakinsu wlh tsoro take ji, kan kujeran daya tahau Ta kwanta duk Ta kasa sakewa ,kitchen taje tai alwala tazo tada sallama Ta zauna tana Ta addua, sultan ya fito yasan ba zata iya kwanciya a parlour ba yai mata girma, key ya mika mata, karba tayi Tana kallan shi irin Na karin bayanin nan harararta yayi ki biyoni nace haka tabi bayanshi wani dake dake can gefe yasa Ta bude kallanta yayi kije ki kwanta anan zuwa gobe dakin Matata nane saura kuma ki bata mum yana kaiwa nan yai gaba da ido Ta bishi dama yana da mata ne? Shiga tayi Ta zauna akan gadon itta har yanzu tsoro take ji Amman she feels better anan, kallan dakin tai daga madubi sai gado da wardrobe dakin yayi mata kyau sosai,.
Kwanciya tayi tare da jan bargo gara Ta rufe kanta kawai inba hakaba gani take kamar za,a zo a kamata ne ,.
Washe gari kiran sallah ya tada sultana ta mike Da adduar Tashi daga bacci, toilet din Ta shiga Ta yi alwala Ta Da sallah kafin a shiga, haka tai sallah sannan tai karatun Quran da ka tunda ba taga Al Quran ba,.
Tana idarwa Ta fito tayi aikace aikacen Amman banda girki tunda lokaci baiyiba, haka Ta fito Ta nufi gangaren mamanshi da sallama Ta shiga part din ba kowa zama tayi tana dan hutawa jin ana sakkowa yasa Ta mike Tana kallan stairs din sultan ne sakkowa, kasa tai tana gaidashi kallanta yayi who permitted you to come out? Sir lokacin aikina ne yayifa, and so ya fada yana daga kafada, tabe baki tayi Tare dayin kasa da kai,. Thanks for the help ta fada mai
Taski yayi tare da ficewa, ta bishi da ido tare da sakin murmushi sannan taci gaba da aikinta ,,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 22*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Su mama anci kwalliya Za,a je dakko hindu a airport, Da sallama Hafiz Ya shigo,mama kin gama kinfa San 12:00 zasu sakko yanzu lokalaci ya kusa kuma Daddy ya gama yace tare Za,a tafi saboda tsaro kaiiii sarkin zuba Na gama fa muje, kallan ta yayi mama ina wannan yarinyar da itta zaa je,?saboda wanne dalili? Ah to mama IN anje wazai dauki kayan Hindu din? Murmushj tai duk bayin gun a rasa Mai dauka sai Zuwaira KO? Sosa keya yayi plz mama, tsaki tayi tare da ficewa yabi bayanta, a parlour tace Zuwaira tazo da itta zasu tafi, itta kuwa tayi murna koba komai xataga filin jirgi,suna fitowa kuwa ya hadu harda Maman sultan Amman banda shi, sultana Ma nagun Amman bada itta za,a jeba, kallan momy sarkin yayi ina yarona bazaije bane? Kallan agogan hannunta tayi banjin zaije Dan nace ya shirya yace sai yayi tunani, tsaki sarkin yaja kisa a kiramun shi, kallan sultana tai je kice sultan yazo, Da kallo sarkin yabi sultan baiga fuskarta ba KO wace itta oho baima taba ganinta a wannan masarautar ba,.
Da sallama sultana ta shiga parlour yana zaune yana dannan system nashi, kasa tai ranka ya dade kai kadai ake jira fa mai martaba yace a kiraka, zuwa ina kenan? Ya tambaya ba tare daya kalleta ba, kallan shi lallai wannan uban gidan Nata sai a hankali, zuwa dakko Yar sarkin da zata dawo mana ,kallan ta yayi it's important to go with me or what? Wlh ban saniba ranka ya Dade nidai yar aikece IN kuma nayi laifi tuba nake, tsaki yaja je kici bana jin dadi bazan samu zuwaba, mikewa tayi and yes kinsan baki gama mun aiki bako? Eh ranka ya dade Na sani, that good na baki 5m kije ki dawo kimun aiki OK, OK sir Ta fada tare da fucewa,.
Tana zuwa Ta isar musu da sako momy dai murmushi tai tunda tasan halin Dan nata baiyi niyar zuwaba,sarki kuwa yaji haushi dan yaji haushi yasan niyar zuwane baiyiba zaiyi maganinshi dole Ya auri yarshi tunda Tana sanshi no matter what,.
Da sallama Ta shiga part din nashi sannan ta Fara aikin da bata karasaba,.
Saida suka dan jira sannan jirjin yayi landing, tun daga nesa Ta hango su Tana takunta Na yayan saraura, tuni bayi suka zagayeta sai fasa kai take farace kyakkyawa ba laifi, Da murmushi a kan face Nata ga uban glass Data kafa Ta nufi mamanta Ta rungumeta, murmshi manana tai welcome home my daughter, gun Dady taje shima Ta rumgumeshi, yayi dariya saida kika gama da Maman ki, gun yayanta taje Ta rumgumeshi duk sukai murmushi, dagowa tayi Ta nufi gun momy ina sultan abun Data tambayeta kenan batasan tace Bari ta rumgumeta ba itta tabe baki momy tai yana gida, meyasa bai zoba? Inkinje saiki tambayeshi Ta fada tare da shigewa motan da aka kawota taya zata yarda danta ya auri wacee bata damu da mamanshiba, Da kallo hindu tabi momy, Mamace Ta riko Ta karki bata ranki daga dawowa yau kinji Mai daughter dan bakin ciki saidai ya mutu ttunda kin dawo aure kuma bashi haka suka shiga motan duk Hindu ta matsu suje taga sultan dinta,.
Ana parking Ta fito tai gaba suka bita da ido sunsan bazata kwabe musu da kyau ba, bata damu da gaidata da bayi keyiba kawai burinta Ta ganta a gun sultan.
Bako sallama tashiga parlour lokacin sultana Na aiki share wa, ganin kafa yasa tago dan ganin waye, kallanta Hindu take da mamaki da a iya saninta da sultan bai yadda da wata baiwa Ta shigo Mai bangareba har yakai tayi mai aiki Amman wai yau take ganin wata anya idonta ba gizo yake mataba?
Kallan ta sultana tai tunda dai taga bata taba ganintaba tasan ittace wacce ake fadin zata dawo Amman tunda bata mata sallama ba zata bata respect ba, durkusawa tai taci gaba da aikinta, kallan ta kawai Hindu take ai da gani tasan baiwace Amman tsabar rashin mutunci bata San ta gaidata ba, amma zatai dealing Da itta ba yanzuba jin ana sakko daga stairs yasa Ta kalli gun sultan ne da sauri tayi gunshi tana murmushi, niyar rumgumeshi tai yai saurin ja da baya yana kallanta
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 23*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
A friend is someone who listens when you speak, understands when you cry and guides you on your way!!
Kallan shi tayi Yaya are you not happy to see me,murmushin dole yayi kin dawo lafiya?ba tace komaiba sai kallanshi DA take ranta Na Mata soya shida ya kamata yayi murnar ganinta amma bai nuna ba,kusa DA itta yaje kin dawo lafiya?qlau ta fada tare DA ficewa Wanda said a ta ture sultana. DA kallo sultana ta bita kafin ta tabe baki no nakar zomunne aikin banza kawai ta fada tana mikewa hada I do sukai DA sultan ya gallah Mata harara ,kasa tai dakai tare DA wucewa ta gefenshi ,.
Ficewa yayi ya nifu dakin momy shi DA sallama ya shiga ,bata parlor farko hakan yasa yai sama ,a man kujera ya ganta tana duba jarida,sannu DA aiki momy Na ,murmushi tai tare DA ajjiye jaridan kana lafiya yarona ?murmushi kawai yayi ,son me ya hanaka xuwa tarbo Hindu? DA Sauri ya mike kardai kicemun zuwa kika ?nasan rankine zaizo yana baci ,murmushi tai ba dole injeba kafi abun yazo yana zama Na magana ,table baki yayi DA kuma a batan mun ranki ia gara aje ayi ta maganarba ,ya fada tare DA turo baki,hmmmm kawai tace dashi ,.
Rai bace Hindu ta fito daga bangarenshi kadan take jira ta fashe,a hargice ta shiga part din nasu ,wani design DA akai akasa welcome back hindatu shi ya kawatata ,wowwwww ta fadi tare DA karawaa ciki Idanta ya sauka a kan wani kayataccen cake yayi bala,in Mata kyau, kallan Maman ta tai DA murmushi ta rungumeta I know you are that did all this am so proud of you my sweet mama ,dariya Maman tai me to my sweet auta daughter,su Zuwaira dake kallan idon god abun ya basu sha,away sai sukaji inama sune ,.
Yau a gajiye sultana ta koma dakinsu,Dan duk sun rigata dawowa washhhh ta fada tare DA zama duk suka kalleta,ganin suna Mata kallan tambaya yasa ta tuna jiya ba anan ta kwanaba,zulaice ta Fara magana jiya ya akai kika rigamun tashi wai ?kawai muka tashi mukaga baki man ,Kallan Zuwaira sultana tai ganin ta kafeta da I do yasa tai murmushin yake tana adduar Allah yasa bawai Zuwaira ta ganta bane ,murmushi ta sake Ai jiya tun kafin Ku tashi na tafiyata ,tabbbbb Zuwaira ta fada wannan wanne irin sammakone DA had zaki fice da safe bamu saniba saikace wash kasaye ,mikewa tai takwanta said kuyi tayi tunda karya nayi kunsan Ai Na Saba ,tabe baki sukai ki sakko muci abinvi
Plz koyi sorry DA wanna banda charge me
By Hajara Mami Natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 23*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
A friend is someone who listens when you speak, understands when you cry and guides you on your way!!
Kallan shi tayi Yaya are you not happy to see me,murmushin dole yayi kin dawo lafiya?ba tace komaiba sai kallanshi DA take ranta Na Mata soya shida ya kamata yayi murnar ganinta amma bai nuna ba,kusa DA itta yaje kin dawo lafiya?qlau ta fada tare DA ficewa Wanda said a ta ture sultana. DA kallo sultana ta bita kafin ta tabe baki no nakar zomunne aikin banza kawai ta fada tana mikewa hada I do sukai DA sultan ya gallah Mata harara ,kasa tai dakai tare DA wucewa ta gefenshi ,.
Ficewa yayi ya nifu dakin momy shi DA sallama ya shiga ,bata parlor farko hakan yasa yai sama ,a man kujera ya ganta tana duba jarida,sannu DA aiki momy Na ,murmushi tai tare DA ajjiye jaridan kana lafiya yarona ?murmushi kawai yayi ,son me ya hanaka xuwa tarbo Hindu? DA Sauri ya mike kardai kicemun zuwa kika ?nasan rankine zaizo yana baci ,murmushi tai ba dole injeba kafi abun yazo yana zama Na magana ,table baki yayi DA kuma a batan mun ranki ia gara aje ayi ta maganarba ,ya fada tare DA turo baki,hmmmm kawai tace dashi ,.
Rai bace Hindu ta fito daga bangarenshi kadan take jira ta fashe,a hargice ta shiga part din nasu ,wani design DA akai akasa welcome back hindatu shi ya kawatata ,wowwwww ta fadi tare DA karawaa ciki Idanta ya sauka a kan wani kayataccen cake yayi bala,in Mata kyau, kallan Maman ta tai DA murmushi ta rungumeta I know you are that did all this am so proud of you my sweet mama ,dariya Maman tai me to my sweet auta daughter,su Zuwaira dake kallan idon god abun ya basu sha,away sai sukaji inama sune ,.
Yau a gajiye sultana ta koma dakinsu,Dan duk sun rigata dawowa washhhh ta fada tare DA zama duk suka kalleta,ganin suna Mata kallan tambaya yasa ta tuna jiya ba anan ta kwanaba,zulaice ta Fara magana jiya ya akai kika rigamun tashi wai ?kawai muka tashi mukaga baki man ,Kallan Zuwaira sultana tai ganin ta kafeta da I do yasa tai murmushin yake tana adduar Allah yasa bawai Zuwaira ta ganta bane ,murmushi ta sake Ai jiya tun kafin Ku tashi na tafiyata ,tabbbbb Zuwaira ta fada wannan wanne irin sammakone DA had zaki fice da safe bamu saniba saikace wash kasaye ,mikewa tai takwanta said kuyi tayi tunda karya nayi kunsan Ai Na Saba ,tabe baki sukai ki sakko muci abinvi
Plz koyi sorry DA wanna banda charge me
By Hajara Mami Natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 24*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
This page Is for you Sadiya alhasan auyo
Washe gari da safe Bayan sunyi sallah,zuwaira dake kan sallaya Ta kalli sultana, hmmmmm Allah Mai iko wai mutun yayi Ta rufe fuska kamar Mara gaskiya Ta fada tare da tabe fuska, murmushi sultana tai shi kuma mutun sai Sa ido kamar Wanda akanshi mutun yake, Zulai ce Ta karba wai Dan Allah sultana maye dalilinki Na rufe fuskarnan, hmmmm bazaku ganeba ku tashi mu tafi kawai, mikawa Zuwaira tai ta shirya sannan suka Kama hanya suna tafiya suna hira, sun danyi tafiya sannan Zulai Ta Kama hanyar Ta Zuwaira da sultana ne hanyar su wajen daya, suna tafiya iska na kadawa,.
Tun daga nesa suka hango Hafiz na tahowa, kallan sultana Zuwaira tai wlh bana San haduwa da wannan mutumin Ta fada tare da sake hade raiii, uhmmm kawai sultana tace, yana zuwa dai dai dasu ya tsaya sukai saurin yin kasa tare da fadin ina kwana ranka ya dade? Kallan Zuwaira yayi kafin ya kalli sultana Ya Kara kallan Zuwaira wannan kawarki ce? Ya fada tare da nuna sultana, eh ranka ya dde tabe baki yayi ya kalli sultana kece wadda kika ceci uban gidanki ranar KO? Eh kawai tace dashi, to dakyau,.
Kallan Zuwaira ya sake yi mu bamu harda da wanda yake harka da sultan saboda haka kisan abun yi, kallan Zuwaira tai ranka Yaya dade kayi hakuri ban gane me kake nufiba?murmushii yayi Dan kece da wata tace zansa ai mata bulala ne sakamakon tambayar da kika mun,tabe baki Zuwaira tai tare da yin kasa da kai KO maye abun laifi anan oho Mai, katseta yayi ina nufin karna sake ganin ku tare KO kin taba ganina da sultan ne? Batace Mai komai yai gaba tare da fadin a kiyaye.
Mikewa sukai suka kalli juna kafin suka saki murmushi, Zuwaira ce Ta Fara magana KO maye nashi a ciki oho Dan suna yar tsama sai akace muma sai muyi mtswwww taja Saki, murmushi sultana tai wlh wannan Hafiz din tausayi yake bani, Amman sai naga kamar kallan so yake miki, duka Zuwaira Ta ba sultana ke Allah ya sauwake sau nawa ina ganinshi da matan banza ME zanyi dashi Allah ya sawake kuma in kika kara mun wannan zancen gaskiya zamu bata, Hmmmm zawai sultana tace tana zancen zuci haka kowa ya kama gun nashi aikin sultana bangaren Maman sultan tai, Dan yanzu aiki biyu take yi danma aikin mama back wani wuya ne dashiba ,.
Da sallama Ta shiga musu aikin parlour farko suka amsa Ta gaidasu tare da yin cikin parlour da take aiki,.
Kallan parlour tayi itta kawai Tana san parlour nan Tana san Maman sultan, Bayan baki zuwa gaidata Ta fada a zuciyar Ta sannan taba Kanta ansan to ai duk sanda nazo bata tashiba shi yasa, yooo inka zo basai kijaikibe ki gaidata kafin ki Fara aikiba duk da zuciyar Ta take wannan maganar, sauke ajiyar zuciya tai sannan ta nufi dakin momy,.
Da sallama Ta tura kofan, momy nakan sallaya Tana karatun Al Quran, murmushi sultana tai shiyasa take burgeni matar nan akwai addini,.
Har ta juya zata fita taji momy tace shigo mana, juyawa tayi Tana kallan momy Tana rufe Al Quran nin, karasawa tayi har kasa, ta durkusa ina kwana ranki ya dade?? Murnushi momy tai kina lafiya, qlau wlh momy, to mun gode Allah kin gujeni KO kin koma can, murmushi kawai sultana tai, kallan ta kawai momy take jin shirun yasa Ta dago momy tai saurin dauke kai, uhmmm duba wancan drower ki dakko min wani album , mikewa sultana tai ta dakko Ta mika mata, karba momy tai ta bude sannan ta Kalli, sultana Dan bude fuskarki muga, gaban sultana Ya fadi tana kallan Momy, murmushi momy tai tare da fadin plz, zaro ido sultana tai itta wace harda momy zata Na ce mata plz,nan take ta bude, kallan ta momy tai kafin Ta cire wani hoto Ta kafa a fuskar sultana, murmushi momy tai tare da fadin masha Allah
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 25*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Jin batun da momy tai yasa kirjin sultana bugawa, dauke hutan momy tai tare da riko hannun sultana, sultana wlh kina mun Kama da Wata faccalata wlh jinin mu ya hadu da itta ranar haihuwar Ta data haihu da itta da yar da mijin lokacin sarkine sukai tafiya ranar Data haihu a lokacin sukai accident suka mutu IN na ganki duk sai inji kamar itta shiyasa ranar dana Fara ganin naji kin shiga raina abun da baki Sani bama kullun IN kuka zo aiki sai Na fito na ganki Amman baki Sani, kawai naji ina sanki sultana, shine nake neman alfarma kinga bani da ya mace mujina ya mutu shine nake San ki dauke ni kamar uwa kanwar sultan Amman bance dole bafa,.
Hawaye sultana ta Fara itta kuwa har ta isa Ta musa uwar gidanta wacce Ta dauketa matsayin baiwa sannan yanzu tazo tace Tana san Ta zama yarta har itta wace da zatai wasa da wannan damar wannan Ma wata damace ai ,ganin Tana hawaye hakan yasa momy jin ba dadi dama taya zata ce wai Ta zama uwa gareta bata saniba KO Tana da take ta mahaifiyar, kiyi hakuri sultana bansan abun zai bata miki raii....... Tun kan ta karasa sultana ta riko hannunta na amince momy har na isa naki yadda da wannan tayin naki, murmushi momy tai mamanki fa, banda itta ranki ya Dade tunkan IN taso Ta mutu, sosai momy ta tausaya mata,.
Amman momy plz wannan kawai tsakanin mune xaki barni ina abuna kamar yadda bayi suke zan ci gaba Da aikina wata rana sai labari ni nasan da haka ai, murmushi momy tai shikenan tunda hakan kike so Amman IN kin gama aikin bangaren sultan sai kina zuwa muna hira KO? Daga mata kai sultana tai tana murmushi, Jinn an turo kofa da sallama yasa sultana saurin maida mayafinta tana rufe fuska baiga komai ba sai habarta da ya gani da pink din lips dinta, zama yayi kusa momy, Ya kalle Ta laifi tai miki KO Na ganta a durkushe a gabanki, murmushi momy tai ta kalli sultana AI yanzu Ta zama yata Kanwar kace, kallan sultana yai ittama Ta kalleshi ya gallah mata harara itta kuma tai murmushi kawai ,sannan ta Mike Ta Fara gyarawa momy Daki,.
Kallan shi momy tai Ya naga yau ka taso daga masallaci da wuri? Wlh momy sauro yayi yawa shine nazo inyi karatun anan dakin, mikewa momy tai To kayi Amman a masallaci yafi ni yanzu bacci zan koma Ta fada tare da hawa gado Ta kwanta, murmushi yayi Tare da mikewa ya rufeta da barko, sannan ya zauna akan sallayar data tashi ya bude Al Quran din, Sultana dai aikinta take Ya bude ya Fara karantawa, sosai kira,arshi taiwa sultana dadi zataso ace ya zauna yai tayi tana sauraro, shi kuwa karantunshi yake abunshi haka har ta gama Ta kama hanya tayi parlour tayi komai sannan ta sauke ajiyar heart ta fice Ta dakko abincin momy, Tana shigowa shi kuma zai fice, ina kwana ranka ya Dade? Baice komaiba ya raba Ta gefenta ya wuce Ta bishi da ido sannan ta ajjiye abincin,.
Bayan Ta gama Ta kama hanyar zuwa bangaren shi, tana tafiya kawai idonta ya sauka kan wani dake dauke da kwari da baka,hindu na hakince a kan kujera wai koya mata ake, dan taji yana IN kika rike nan saiki riki nan, murmushi tai a hakan zaa koya, zata juya kenan Hindu ta gano Ta tabbas Ta ganeta dukda bata fuskarta ba, murmushi tai bari taba wannan yarinya kunya anan, kallan wani bawa tai kira mun waccan yarinyar Ta fada tana nuna sultana da sauri yayi gunta,
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 26*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
This page Is for you rabia,atu adamu Dan haya
Da sauri bawan yaje gurinta, wai kizo, ni Ta fada tana nuna kanta,eh ke mana inji gimbiya Hindu, kallan gun tayi kafin Ta sauke ajiyar heart tabi bayanshi, Tana zuwa Ta duka Ta gaidata, bata amsa illah kallan Wanda yake dauke da bakan tayi ka bata tayi in gani, kallan sultana tai aiban iya meye hadina da itta,kallanta Hindu tai hake kikewa sultan magana kina Mai magana akai baki da respect ne? Sosai ran sultana Ya baci bataa San raini da gani kuma yarinyar ba zata fitaba, mikewa tayi Ta nufi gun, karba,.
Sau uku tana yi Amman bata samu inda ake San ta samuba, tsaki Hindu taje ke wacce irice kamar ba daga kauye kike ba, kallan ta sultana tai ranta yana kara baci, sai kuma tai kasa da kai ranki ya dade AI a kauyen namu ba mawunwata bane kinsan mayunwatane kesan koyan harbi Dan su dinga farautar abun da zasu ci, kinyi hakuri da abun da zan fada ranki ya dade muba mayun wata bane, huci kawai Hindu take wai itta baiwa ke cewa mayunwaciya to haka take nufi mana tunda yanzu dai itta ake koyawa harbi, mikewa tayi Ta nufi kusa da sultana,tai facing nata har tana jin nunfashinta, kallan Hindu kawai take kafin Ta dauki hannunta Ta bata wani kyakykyawan Mari Wanda har saida yasa daurinta kusan cirewa Amman tai saurin taro shi, rike kuncinta sultana tai kafin Ta kalli Hindu idonta yayi jaaa ranta ya baci Amman ba damar daukan fansa,.
Ba tare da tace da Hindu ba ta raba ta gefenta zata wuce hindun Ta Sa mata kafa saiii ji kake timmmmm Ta fadi a kasa ai kuwa yan garin suka fara dariya, murmushin mugunta Hindu tai kafin Ta karbi bakan Ta Fara harbawa cike da kwarewa Dan mina Ta Bala,in ban mamaki dama haka Ta iya harbi,.
Mikewa sultana tai ta tafi inda Ta nufa tana shiga parlour bako sallama ta jin gina Da jikin kofan sai a lokacin wani zaffafen hawaye ya Fara zubo mata, Kasa tai kawai tana kuka itta aka mara yau abun da ba,a taba mataba saidai bata saniba KO tana yarinya hakan ya faru da itta Amman itta back Wanda ya taba marinta,sultan dake zaune a parlour yana danna system dinshi yayi shiri da gani gun aiki zaije, ganin Ta shigo Tana kuka yasa ya tsaya yana kallanta, gyaran murya yayi da sauri Ta daga kai Ta kalleshi sai kuma tai saurin mikewa kwata kwata bata San yana ciki ba, hanyar kitchen tayi, kafin Ta karasa ya kirata, juyowa tayi ganin itta yake kallah yasa ta juya Ta karasa gunshi tai kasa tare da fadin ina kwana? Me ya sameki kike kuka? Ba komai, har zaiyi magana sai kuma ya fasa kar Ta dauka ya damu da itta sosai ne, OK Allah yaa kare kiyi sauri ki mun breakfast patien na jirana, to ranka ya dade,.
Hindu ce Ta shigo tare da fadin karata kika kawo ai wannan ma kadan miki badai a kasana kike ba wannan masarautar muce ba yadda kika iya dani kuma Wanda kika fadawa shima ba abun da zaimun tunda dai masarautar muce shima bai kaini power ba ta fada tana kallan Sultan Tare fadin KO Yaya?get out Ya fada ranshi a bace, what yaya ME kuma nayi, Cikin tsawa yace how dere you zaki shigo min ba sallama sannan kizo kina gaya mun magana can you please get out? Turo baki tayi sorry bari inje inyi sallamar bata jira Mai zaice ba ta fice tare da fadin salamu alaikun, mikewa sultana tai tai kitchen jiki ba kwari zata koyawa wannan yarinyar hankali abun Data fada kenan,.
Amsa sallamar yayi Ta shigo Ta zauna kusa dashi mikewa yayi ya zauna a wata kujeran, kallan shi wai Dan Allah yaya Maye Haka nan gaba fa aure zamuyi, wani kallo yai mata ni zaki aura? Yai wani murmushi ni kuma bazan aurekiba, dan marairaicewa tayi saboda dame yaya? Saboda bana sanki nasan inna aurekima ba zan iya miki adalciba saboda haka kiyi hakuri kawai, ni naji karka soni aini ina Sanka tsaki yayi baice komaiba yaci gaba Da abun Da yake itta kuwa sai zuba take mai itta a dole zata shawo kanshi ne
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 27*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Bayan Ta gama Ta jere a dining sannan tace Ta gama, tun kanya tashi Hindu har ta karasa gun, ta zauna tsaki yayi tare da zuwa ya zauna, daukan flask sultana tai zata Fara zubamai Hindu tai saurin rikewa tare da harara sultana Na baki permission ki zubawa mijina abinci ne? Kallan sultan Hindu tai itta shima yake kallo dauke yayi ganin hakan yasa Ta sakewa Hindu flask din, Tana tsaye har Hindu ta gama zubamai sannan ta dawo Ta zauna kallan sultana tai saiki zuba mun aiko, murmushi tai tare da Fara zuba mata Hindu sai hararar Ta take, kallan sultana tai kewai ya sunanki?sultana Ta fada a kaice, kuttt wlh baki isa ba dole ki canza suna aba yanzu hakama asiri kikai Mai wlh abun yana ban mamaki kuma zan karya asirin shine harda Sa irin sunan shi, murmushin takaici sultana tai hakama shima sultan din murmushi kawai yayi Hindu masifa, garin Ta mika mata glass cup din Ya subuce ya fadi akasa ya fashe, a hargitse Hindu ta Mike Da niyar kai mata mari sultana tai saurin ja baya sultan kuma yai saurin rike hannun Hindu, garin matsawa sultana ta taka kwalba hakan yasa Ta Saki kara tare da runtse ido Da sauri sultan Ya karasa gunta Ya rikota ya kalli kafar jini Na fita.
Kallan shi Hindu tai yaya baiwace fa ka riketa ta, harararta yayi Ya kalli kafar sultana dake jini, sannu ya fada ma a hankali, batace komaiba sai hawayen Da take, rike hannunta yayi ya kaita parlour Ya zauna Da itta ki jirani ya fada tare da yin sama, kallansu kawai Hindu take kafin Ta fice Da gudu, murmushi kawai sultana tai,.
Da first aid box ya fito, Ya zauna a kasa Tare da riko kafar tata, daurewa kawai take itta tasan ME take ji inya tabata,runtse ido tai, har ya gama aikin Ya dako yana kallanta, murmushi yayi Ta wani runtse, raguwa ya fada a hankali ya kurawa idonta kallo yana San ganin face dinnan Amman baisan taya zaiyi hakan ba, jin ya daina mata yasa Ta bude ido idonta ya sauka kan nashi murmushi yai mata tare da fadin sannu, dauke kai tayi tare da fadin Na gode ,mikewa yayi ki shigar mun dashi daki nina tafi yana kaiwan nan ya dauki nashi ya nashi ya fita, Da kallo Ta bishi shi duk yau sai taga ya canza mata kamar ba shiba, murmushi kawai tai Tare da mikewa tana dingishi,haka yau tayi aikin nata,.
Hindu kuwa part din Maman taje tasa mata kuka, mama yaya sultan baya sona Allah kinga yadda yamun rashin kutunci yau akan wata baiwa, kallan Mama tai wacce baiwace itta Yar wacece har da za, ai miki rashin mutunci akanta, daura kanta tai a cinya mama, mama ki bari zan dauki mataki, yauwa gara ki dauka in ba zaki iyaba kimun magana ni zan daukar miki farin cikinki shine nawa ai, murmushi Hindu tai kawai,.
Dady ki yace ki shirya ya hada miki party dawowa,gobe zaai saboda haka saiki shirya, yace duk wata baiwa zata iya saka kayan da ba uniform ba Dan kawai tazo tayaki murnan dawowa, dariya tayi tare da rumgume mamanta shiyasq nake kara sanku wlh kuna faranta mun rai ,zan shirya Da wannan party zan fadawa yaya sultan ya shirya
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 28*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Yau a gajiye duk suka koma dakinsu, kallan Zuwaira sultana tai kinga har yanzu Zulai bata zoba,tabe baki Zuwaira tai yo ni AI naci abinci a namu bangaren ke wai baki cine? Aa ni bana ci gani nai baa ce in dinga ciba to me zai kaini, gaskiyane cewar Zuwaira da sallama Zulai Ta shigo, zama tayi Tare da fadin washhhh, sannu suka ce Mata,kallan su tai kunsan kuwa gobe ance kowa yaci kwalliya Za,ai abu a wannan masarautar, kallan ta sukai me kuma Za,ai? Wai bikin dawowar hindu mana, kallan ta Zuwaira tai banda wanda muka hada mata a bangaren mamanta kai wannan suna asarar kudi, uhmmmm kawai sultana tace,Ta zuba musu abincin suka zauna suna ci,.
Washe gari Cikin farin ciki Hindu ta tashi yau za,ai mata perty zata gasa kuwa,.
Direct bangaren momy taje Da sallama ta shiga dakin ganin momy na addua yasa Ta wuce toilet tare da fara wanke mata toilet sai da ta gama sannan ta fito kallan momy tai dake addua Ta daga hannu sama, hakan yasa Ta zauna kusa Da momy sukai adduar tare sannan suka shafa, kallan momy tai da murmushi ina kwana momy? Shafa kanta momy tai kin tashi lafiya? Murmushi kawai tai, ta mike taci gaba Da aikinta, saida Ta gama, kallan momy tai,momy zanje parlour inyi aiki, OK zo ki zauna za muyi magana, tam tace tare da zama,.
Nadai San kina Da labarin yau zaai party Hindu kuma ance zaku iya saka KO wanne kaya? A wannan masarautar indai irin haka Ta faru To har bayi ma kwalliya suke sha, balle ke kuma Da kin kusa zama Ya Dan nan ba dadewaba zan kaiki gun sarki in fada Mai ina sanki kuma nasan bazai mun musu ba saboda haka ki shirya,shiru sultana tai itta gaskiya bata San su gane ko itta wace Amman ba yadda Ta iya tunda momy ta bukaci haka, mika mata wata leda momy tai ga wannan kayan shi zakisa, karba sultana tai ta bude wata milk doguwar rigace Da ratsin brown sai stone a KO ina kallan kayan tai kafin ta Kalli Momy ranki ya dade, da sauri momy ta rufe mata baki bana San magana kawai ki karba sannan ki taba ganin inda Ya take cewa Maman ranta ya Dade? Murmushi sultana tai momy ma tayi Na gode momy ta fada Tana murmushi, ba komai kawai abu daya zaki mun kisha kwalliya kema an mark you banda rufe fuska dariya sultana tai tare da ajjiye kayan momy zan dawo in dauka anjima Ta fada tare da ficewa,.
Da kallo momy Ta bita zataso ace matar sultan sultana ce Amman tasan wannan abu Mai wuyane kuwa ,.
Da murmushi Yau take aiki kawai Ta tsinci kanta Da murnusa War, morphing take abunta duk hankalinta baya jikinta kawai Tana tuna kawu Da Nafisa ne har sultan yai sallama ya shigo bata saniba, tsayawa yayi abayanta Ya kallan yadda take aikin komai a nutse shidai zaiso ganin wannan fuskar kuma Yau dinnan KO taki KO taso yanzu Ma kuwa, zuciya daya sultana ta dago, kawai taga mutun a gabanta hakan yasa Ta tsorata garin yin baya santsi Ya kusa dibarta Amman yai saurin rikota tare da jin ginar Da itta a chest nashi, sosai gabanta ke faduwa Dan ta kawo kawai tasha kasa tasan ba karamin ciwo zata jiba ,saida tadan dauki second sannan hankalinta ya dawo ta daga kai tana kallanshi Da sauri taja baya Amman Ya kara rikota, a dan tsorace Ta kalleshi Tana san kwace kanta ranka ya Dade Maye haka, tabe baki yayi ba komai kawai danna taimaka miki shiyasa kika samu baki shi kenan Na taimaka miki Amman nima ki taimakan sannan karfa ki kawo komai a ranki, a Dan tsorace take kallan shi, OK naji to sakeni nacema ba kyau wannan abun kadaina tabani, murmushi yai mata, sorry 5m zaki ban, plz ta fada Tana kokarin kwacewa Amman yaki sakinta, a hankali ya Fara magana kawai fuskarki zan gani shikenan saina sake ki,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 29*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
A Dan tsorace Ta kalleshi Ta Fara zancen zuci dama Da gani sultan baiyi halin mamanshi ba Da gani Dan iskane yanzu ya zatai, jin ya riko dankwalinta daga kasa yana shirin dagawa yasa tai saurin rikewa, kanawa Allah ka bari nace banaso KO ana dole ne, aa ba,a dole Amman Yau zaa Fara kuma a kanki dan bazai yuyuba ace ina zaune Da wadda ban taba ganin idonta ba, ganin bata Da yadda zatai yasa tai shiru kawai tare da sakin hannun nashi, murmushin nasara yayi ya kalleta yadda Ta wani rufe ido, tashi daya kuma yaji ya tsani kanshi wai baiwarshi yakewa haka Da sauri ya saketa yaja baya tare da juya mata baya ,ajiyar zuciya Ta sauke Ta gode Allah Amman da gani yau ba sultan bane wannan, kallanshi tai Ya wani juya baya tabe baki tai tare da hararar shi Ta taho zata wuce shima ya juyo zaiyi sama sukai gware, kallan ta yayi sannan ya koma dayan bangaren suka sake gwaren kafin suka kalli juna, jin wani iri yasa sultana tai saurin dauke kai Ta raba Ta wuce abunta ,ajiyar zuciya ya sauke tare da baza kanshi what wrong with me ne?yai sama abunshi da sallama ya shiga dakin momy ya gaidata Ta amsa cikin kulawa,.
Son nasan kasan Da party hundu yau kuma inasan kaje Dan nasan halinka, kallanta yayi kafin ya tabe baki momy ina Da aikine yau dinnan Da yawa wlh, eh dama party ai sai Bayan la, asar saboda haka baka Da mafita, shiru yayi kawai KO shiyasa Hindu take ta jiranshi so take ta sanar mai kenan, uhmmm kawai yace suna hira Da momy Hindu ta kira bai dagaba har ta katse, har uku tana kiranshi baya dagawa,kallanshi momy tai tare da harara babu kyau dai mutun yana Sanka kana mai wulakanci, aa momy ba haka bane wlh yarinyar akwai takura Amman wlh bana santa itta kuma duk tabi Ta damen, kallan shi momy tai to aiba haka ake rabuwa Da mutunba saika bita a hankali babu kyaufa wulakanci, dai dai lokacin Hindu ta kara kallanshi tai oya daga,.
Mekewa yayi bari inje parlour in amsa Ya fada tare da fucewa, yana fita yaga sultana da sauri ya karasa Ya mika mata wayan kallanshi tai ta kalli wayan, karbi ya fada karbata tayi taga hindu Ta kalleshi kice bana kusa koma meye Ta fada miki zaki fada mun, kallanshi tai Ya harareta ,taro baki tai tare da dagawa tun kafin tai magana Hindu ta Fara, haba yaya tun yaushe nake kiranka kodan kaga nafi damuwa dakai shiyasa kake mun rashin mutunci haba yaya abun Da kake baka kyautawa, shiru sultana Tai duk sai taji tausayin hindu, a hankali Ta Fara magana bata kusa, runtse ido Hindu tai batasan tana kiranshi sultana Na dagawa, wayace to ki daukarmai wayan ba gani a part dinshiba baya nan wato sacewa kikai KO? Aa a bangaren momy yake to ya fitane shiyasa, kashewa Hindu tai tare da yin wulli Da wayar sannan kuma Ta dauka Ta tura mai message na party,.
Mikamai wayan sultana tai Tana kallan shi,thanks yace tare da karba ya wuce,.
Haka sultana tai gama komai. Lokacin Da taje sultan ya tafi aiki hakan yasa batai breakfast ba,.
Da LA, asar taje dakin momy ta karbe kayan sannan ta nufi dakin su,su Zuwaira sunsha mamaki sannan suka dakko kayansu Wanda sukasan yana Da kyau sannan suka sa sultana Na kwancewa wai itta bacci zatai anjima zataje hakan yasa sukai gaba kawai, saida tai baccinta sannan ta Mike ta Fara shiri,.
Sultan dake gaban madubi yana shiri sai tsaki yake ja duk An cika mai kunne wlh da momy zaije ya kara jan tsaki sannan ya fesa turare ya fito,.
Kallan dankwalin hannunta sultana tai ta kasa daurawa Dan head ne, ga gashinta Ta rasa ribom dinta, tsaki taja tare da fitowa Ta karbo wani agun zuwaira yau bata rufe fuskarba bama
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 30*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Da sauri take tafiya burinta kawai Ta hadu Da Zuwaira, sultan dake tafiya yana danna wayarshi, sai tsaki yake a akai akai, idonshine ya sauka a kanta Da take ta sauri shidai baiga fuskarba gashin kawai ya gani, zaro ido yayi tare da murza ido wannan gashin a irin na Yan India yake gani Amman yau gashi yaga wata Da irinshi hanya ba aljanu bane ya fada yana Dan kara sauri Ya matsu yaga wace,. Sultana kuwa sauri take kamar zata tashi sama ganin kamar saurin yaki mata yasa Ta kara Da gudu, ohhh god ya fada ganin tayi gudu shi kuwa Da girmanshi bazaiyi guduba ina,tsaki kawai yayi yana tafiya abunshi,.
Tana zuwa Ta riko hannun Zuwaira sukaja baya kallanta Zuwaira tai kaii Amman wlh kin yi kyau sosai, murmushi tai tare da fadin nagode ,ribom daya zakiban tabe fuska Zuwaira tai kawai dai kice so kike in bata daurina, sorry mana Ta fada tare da hade hnnun gu daya, to yana iya Da samarin kakana tunda sunce ni suke so, wani gu suka rabe Ta ciro ribom din guda daya Ta Sa mata sannan tamai Da daurin Ta, kawo In daura miki Ta fada tare da karba Ta daure mata gashin Nata sannan ta daura mata Dan kwali,kallanta sultana tai ni bazan iya zuwaba kawai ki tafi sakin baki Zuwaira tai Tana kallanta akan wanne dalili ba zaki iya zuwaba? Ban sababa Ta fada tare kallan jikinta tsaki Zuwaira taja tare da tafiyarta Tana ta masifa mutun sai ustazancin banza Na karya,.
Party na tafiya dai dai, musamman doctor ibrahim ya kawowa Hindu babban gift abokin sultan ne dake balain santa Amman itta ina baya gabanta ne itta kawai sultan,.
Mika mata gift din yayi sannan ya nufi gun sultan, Da murmushi sultan ke kallanshi har ya karaso ya mika Mai hannu suka gaisa sannan ya zauna abokin kana sha,aninka kafa cewar sultan, murmushi yayi na kaika kaida ake so nida baa so, tsaki sultan yaja kai karka wani damu Hindu taka ce,wani murmushin jin dadi yayi tare da fadin Allah yasa Ameena duk suka amsa ,haka sukai Ta hira abun su wayan sultan ne yai ringing hakan yasa Ya mike tare da kallan Ibrahim ina zuwa yawuce zuwa wani bangarem dan amsa call, tun daga nesa ya hangota, yana ganin bayanta ya gane ta ,karasawa gunta yayi ya tsaya a bayanta he feels some how, jin kamar ana bayanta hakan yasa ta juyo, a dan razane taja baya gabanta na dukan hamshin hamshin, kallan ta yayi har bai San sanda ya furta masha Allah ba,kallanshi tai Allah yasa bai ganeta ba sai kuma Ta sauke ajiyar zuciya ai bai taba ganin fuskarta ba dagowa tayi sukai ido hudu Da sauri tayi niyar dauke idon yai saurin riko habarta is like yasan wannan idon ya fada tare da tsareta Da ido, cire hannunshi tai yi hakuri malam Na sanka ne? Runtse ido yayi tabbas yasan wannan muryar Amman a ina agun sultana ya fada a hankali jin yace agun sultana yasa hankalinta dan tashi, bude idon yayi yana kalleta, tsaki taja Ta raba Ta gefe zata wuce yai saurin rikota,.
Kallan hannunshi tai yadda ya wani rikota, janye hannunshi take San yi Amman ta kasa kallan ta ya sakeyi sultana ya fada tare da tsareta Da ido, saita kanta tai sosai kafin Ta Fara magana wace sultana kuma ni banma Santa ba, ta fada zata wuce yai saurin kara rikota ban gama miki magana ba banasan karya ki fada mun wace ke? Hade rai tayi niba itta bace plz ka Rabu dani nifa kawar Hindu ce daga zuwa part saika tsaya kana batan lokaci, murmushi yayi Dan iya saninshi kawayen Hindu duk ya sansu ba wacce batamai kwar kwasa, kallan ta yayi sosai anya Da gaske kike ke kawar Hindu ce ya akai ban sankiba?hade rai Ta sakeyi Ta kalleshi ta bashi harara zata wuce yakara rikota Tare da matsata a jikinshi kinga inna barki gaskiya kika fada mun,sakeni Ta fada tare da hade girar sama Data kasa, saikin fada mun gaskiya, OK kai dole saika San duk kawayenta ganin yaki Sakin Nata yasa Ta gantsara mai cizo aikuwa ba shiri ya saketa tai saurin barin gun da Dan gudunta, binta yayi Da ido tare da murmushi, yarinyar Ta burgeshi Amman mai yasa zuciyar shi take kawo mai sultana tace ina sultana yasan bata Da kyau har haka, Amman zanyi comfier KO sultana taki KO taso sai yaga face dinta ya fada tare da kallo inda Ta cije shi,.
Itta kuwa tana guduwa direct bangaren momy Tayi, har ta kusa sai kuma idonta ya sauka kan bangaren dakin a jiya wani murmushi tai tare da nufar gun kai tsaye abun mamaki Tana turawa taga kofan a bude kuwa
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 31*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
A hankali Ta saka kafa tana karanto addua sannan ta shiga idonta ya sauka kan keys din dake jikin kofan duk iri dayane Da gani kuma duk na kofa ne wani murnushi tai tare da cirewa Ta dauki daya a ciki, kallan gun tayi abubuwane a ajjiye kuma Na amfanine kallan gun take Tana tafiya abunta Tana kalle Kalle wata hanya tazo guda biyune bata San wacce zatabi ,kawai tabi damanta wai yafi alkhairi tafiya take tayi Dan dube dube Ta sannan ta juyo Ta dawo har yanzu yadda tabar kofan haka take, tabe baki tai tare da ficewa abunta, Tana fita tai dakinsu,.
Sarki dake zauna kusa Da abdulsalam sai dariya yake kafin ya kalleshi wlh brother abu mai sauki kaci abincinnan nasan ka dade baka ciba kuma nasan kana so nifa ganinai Yau babbar ranar yatace shiyasa na kawoma to me yasa kake wani jan aji, kallan shi abdulsalam yayi Allah sarki tausayin ka nake Dan uwa ni nasan ka kasu zuwa karshe dan nayi wannan mafarkin kasan wazai kawo karshenka? Tabe baki Abdullahi yayi ya wuce kace yarka, murmushi abdulsalam yayi ba itta bace aikasan wannan back aikin na Mace bane Amman na baka assignment kaje kana gano waye GA wani point dinma a halin yanzu yata tana Cikin wannann masarautar Amman itta zata taimakawa wannan bawan Allah wajen tunama asiri, sauran ya rage gareka nidai kawai satar amsa na baka Dan nasan zaka shiga wahalane indai banma hakan ba ,kallan shi Abdullahi yayi ya kaimai naushi a baki wlh karyane ba wani wanda yake Da karfin cireni a kan mulkina KO shi waye kuwa, dariya abdulsalam yayi hakan yasa Abdullahi ficewa rai bace taya zai dauki zancen wannan banzan may be Ma ya fara samun matsalane ya kara jan tsaki,.
Hafiz ansha kyau sai kallan mata ake yanasan hango wacce zai ce a dakko Mai yau idonshi ya sauka kan Zuwaira, kallan yake saikuma ya saki murmushi hakan zaifi Ma ya fada tare da kira wani bawanshi sukai magana, rasunawa yayi tare da fadin angama ranka ya Dade,.
Sultana kuwa dakinsu Ta wuce Ta ajjiye wannan makullin sannan ta dauki wasu kayan Ta nufi bangaren momy Dan tace saita Fara nuna mata kwalliyar Ta kafin zata cire wannan kayan,.
Da sallama Ta shiga dakin momy, momy ta amsa tare da ajjiye jaridar hannunta, kallan sultana tai ta gane Ta amma tsokana take San yi, aa yau wacce bakuwa nayi daga India haka? Dariya sultana tai tare da fadin kai momy abun harda tsokana, zaro ido momy tai yo ai kin sannima ni kuma ban sankiba ya akai haka, dariya sosai sultana tai, kafin Ta Kalli momy momy nayi kyau? Sosai yata kinga yadda kikai karfa ki sacemun zuciyar dana, murmushi sultana tai tare da tuno dazu haduwar su, dauka Waya momy tai Bari IN daukeki a huta,haka Ta tsaya momy tai ta mata hutuna kafin, suka zauna suna hira nan momy ke cewa Dan wake take so hakan yasa sultana ta cire kayan Ta sa wasu kayan Ta ce zatai mata sannan ta fice,momy Ta bita Da murmushi kafin Ta dauki wayan Tana ganin hutunan datai mata, mikewa tayi Ta dakko Wata Waya sabowa a cikin kwali tare da fadin yata zanba,.
Aiki take a kitchen tana tuno dazo Da suka hadu Da sultan KO nashi na damuwa Da sai yasan wace oho taja tsaki ganin tana zufa yasa Ta cire dankwalin Ta bude fuska tare da fadin nasan ba zasu dawo yanzuba,.
Debo flower tai Tana jika kanwa sannan ta zuba kuka a cikin flower, tana juyawa Ta bayanta taji muryar sultan yana fadin sannu Da aiki sosai gabanta ya fadi tama rasa ya zatai tama manta da Dan kwalinta dake gefe jin yana takowa kawai Ta yanke hukunci Ta dauki wannan flower ta zuye a fuskarta gaba daya
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 32*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
*Sorry about those texts I sent you last night, my phone was drunk.*
Da sauri yaja baya yana kallanta, anya bata sami matsalaba? Ya tambayi kanshi,kasa tai tare da fadin ina wuni ranka ya Dade? Hade rai yayi mekenan?maye hakan kin sami matsalane? Kuma wannan flour da kika zubar a bakacin kudin aikin ki na wannan watan, ajiyar zuciya Ta sauke gara haka dadai ya ga fuskarta,tsaki yayi Tara da juyawa tabar gun, kallan shi tai tare da dafe kirji thanks god ta fada tare da mikewa Ta nufi tap karkuma ya dawo ta fada sannan ta koma ta sawa kofar kitchen din key Ta kuma ta wanke fuskar sannan ta dauki dan kwadinta ta goge fuskarta, sannan ta bude taci gaba Da aikinta,.
Da sallama ya shiga dakin momy shi ya zauna a kan kujeran dakin tare da kwantar Da kanshi, kallanshi momy tai lafiya son naga kamar kana cikin damuwa? Ba komai mom kawai ina San hutawa anan ne, to kawai tace taci gaba Da abun Da take,.
Jinginar dakai yayi waccan yarinyar yake tunawa yama cuci kanshi dahar zai ce wai wannan yarinyar sultana ce yarinyar Da iya kayan jikinta abun kallo nema, ka sani KO Yar watace abune ya kawota wannan masarautar tunda bata San a ga fuskarta, tsaki yaja tare da fadin kai ina ba itta bace, kallan shi mom ta sake yi son waime ke damunka ne? Gyara zama yayi mom wai Dan Allah kin taba ganin wannan sultanan ya take fuskarta nake nufi? Kallan shi tai sosai eh na taba gani, yauwa mom ya take plz ya kamarta yake kawai inasan ganin fuskanta ne, saboda wannan dalili, dafe kai yayi kafin ya kalli mom wlh mom wata na gani yau shine nake tunanin KO ittace tunda ban taba ganinta a wannan masarautar ba Amman Na tambaye ta tace wai itta kawar Hindu ce kuma duk nasan kawayen Hindu, murmushi momy ta, to ka sani KO kawar tatace, aa mom Na kasa yadda da hakan ne shiyasa wlh, kallan shi sosai momy tai kodai ka kamu Da santa ne? Baice komaiba ya jinginar Da kai,.
OK naji indai sultana ce zaka sotane? Da sauri ya Mike ya kalli mom haba mom indai ittace gara Na mutu Da Santa bazan auri baiwata ba haba ai koke saikimun fada, hade rai momy tai dajin zancenshi tai mai banza batace komaiba ,kallan ta yayi ganin ta hade rai, murmushi yayi tare da karasawa kusa Da itta, mom sorry indai Na bata miki raine, kallan shi tai sultan sau nawa zan fadama sultana Ya na dauketa Amman har ka dinga fadan haka a gabana, rike hannunta yayi sorry bazan karaba, juyar dakai tayi naji Amman zaka aureta yarinyar ce take ban tausayi wlh, mikewa yayi tare da hade rai momy kiyi hakuri Amman bazan iya auren wannan yarinyar ba zanje IN nemo wannan yarinyar ta yau ya fada tare da komawa ya zauna, kallan shi tai nikuwa bazan Bada gudun mawaba ina gani so zai kasheka, murmushi kawai yayi,.
Da sallama sultana ta shigo daki Da cooler a hannunta ta ajjiye sannan ta fita ta dakko sauran abun Da zata dakko, zukunnawa tayi ta zubawa momy sultan baice komaiba kawai dai yasan yana San ci Allah yasa momy ta tambayashi KO zaici, shareshi momy Tai Dan tasan dan nata akwai San dan wake Amman yanzu tana fushi dashi bazata mai maganaba ba, sultana nan Ma batai mai maganaba illlah zama datai a kusa Da momy tana Dan sanna mata kafa, wayan kusa Da itta momy ta dauka ta mikawa sultana, dubamin wannan wayan lafiyar nake San ka duba, karbar wayan yayi wannan wayan daya taba shiyowa momy ce sanda yaje India bata taba amfani Da itta ba, karba yayi yana murmushi yau kuma San wannan wayance ta tashi yau aka Tuna da itta? Kallan shi tai ba surutu nace kaimun ba, murmushi yayi tare da kanna wayan yai dube duben shi sannan, kashe Kallan wayan yayi komai normal amma sim NE kawai babu, OK tace tare da kallan sultana, jeki karban waccan wayan!mikewa sultana tai ta karasa gunshi tare da zukunnawa ta mika hannu, baice komaiba yazo mika mata idonshi ya sauka kan zanen dake hannunta,kalln zanen yake sosai duk Da yayi dishi dishi
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 33*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Kallan shi tai kafin ta kalli hannun Nata da sauri tai niyar daukewa yayi saurin riko hannun tare da daura mata wayan a tafin hannunta Amman bai sake hannunba, kallan shi momy tai tare da fadin maye haka? Kallan sultana yai suka hada ido tai saurin dauke ido gabanta na dukan Tara Tara sakin hannun yayi Ya jin gina jikin kujeran tare da lunshe ido wace sultana me tazo yi wannan masarautar wannan zanen hannun Nata ai MASARATAR MUCE ya fada a hankali,.
Mikawa sultana tai ta kaiwa momy wayan bata karba sai Kallan sultan datai son ka shirya gobe kafin ka kita aiki ka sauketa tasai sim kama siya mata sai kasa ta a texi ta dawo gida, Da sauri sultan ya kalleta Da mamaki bai gama mamakinba taji tace sultana wayarkice Na baki kyauta, sakin baki sultana tai tana kallan momy sai hawaye duk na farin ciki wannan wayan duk itta momy zataba, daura kanta a cinyar momy tai tare da fadin na gode momy Allah ya saka a rayuwa bansan Dame zan saka mikiba, murnushi momy tai batace komaiba, mikewa sultan yayi ya fice ba tare da yace komaiba, momy ta bishi Da tabe baki,.
Part dinshi ya nufa kawai yai kwanciyar shi,.
Sultana kuwa tsabar murna KO bangaren shi ba ta kallah ba Tana gun momy suna hira tana ta murnar Waya bata San indai su Zuwaira suka gani me zasu ce mata ba,.
Sai wajen magariba ta nufi dakinsu Da sallama ta shiga lokacin kuwa duk Sun dawo, zama tayi tare da fadin washhhh ta dakko wayan tare da mika musu, karba Zulai tai tana juyawa Zuwaira kuwa ta wani kafeta Da ido alamar karin bayani take so, murnushi sultana tai, uwar gidana ce taban kyauta, duk suka zaro ido suna kallanta murmushi baku yadda ba? Mum isah ai nasan zata iya baki cewar Zuwaira inama nace nake aiki agunta Amman fa karkice wai ina miki bakin cikine, batace komaiba sai murmushi take,.
1:00am wato cikin dare a hankali aka tura kofar dakin su sultana ta, sultana da tun dazu ta kasa bacci tana daukin Waya jin zaa turo yasa tai saurin tura wayan a karkashin pillow,.
Marka ce baiwar dake kula dasu kallan su tai duk ta haska su Da touch tana kallan su kafin ta sauke ajiyar zuciya tare da fadin duk bacci suke, bude kofan tai wasu mata suka shigo duk ta kasan ido sultana ke wannan kallan idon Allah, ...Tana gani suka saka mata wani abu a handkerchief sannan suka dauketa suka fice marka ta rufe kofa, Da sauri sultana Ta Mike tasa ta kallimi tare da daukan Dan kwali ta rufe fuska, ta dauki wayan ta, tabi bayansu,.
Suna yi suna juyowa Da taga alamar zasu ganta saita buye ,haka taita binsu har suka shiga wani bangare daban itta batasan bagaren wayeba tunda bata taba zuwaba,.
Da sauri ta shiga ta buye abayan wani daki, ajjiye Zuwaira sukai a kujeran parlor kafin suka fita,.
A hankali ta Sami gun buya Tana leke, Hafiz taga ya sakko tabbas ta ganeshi, sakkowa yayi ya tsaya ta Bayan kujeran Da Zuwaira take kafin ya saki murmushi, Ya dawo ya zauna kusa Da itta, kawai kallanta yake wai Da gaske itta yakeso wannan San kuwa bawai yaji yana San bata ta bane as santa yake Da aure,.
Da sauri sultana taja baya ta dakko wayanta ya zama dole ta fara aikinta yanzu video record zatai Da kyar ta binciko video sannan ta Fara,
Fridge yake ya dakko ruwa a garka ya na zuwa ya bude tare da yayyafawa Zuwaira, a hankali ta fara motsi kafin ta bude ido tun Tana kallo dishi dishi har idonta ya bude Da sauri ta mike tare da tsala ihu Hafiz yai saurin rufe mata baki,.
Sultana garin ta gyara, wayanta ta buge glass din dake bayanta
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 34*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Dasauri tadanja baya tare da toshe baki tana zaro ido, kallan gun Hafiz yayi duk yadda akai akwai Wanda yake gun Dan haka kawai abun bazai fadi ba, kallan Zuwaira yayi ya bata wata uwar harara, duk ta tsure sai zaro ido take Dan a iya saninta itta ba anan take ba to me ya kawo ta nan, sakinta yayi kafin ya nufi gun da yaji karan, Da kyar sultana ta samu ta Sani kofa idonta ya sauka kan sarkan dake gefe Na stone kuma manya a hankali tasa hannu ta dakko sannan ta fara kokarin tsinkawa Da kar ta samu ta tsina ta rike a hannu tana adduar Allah yasa wannan abun Da take shirin yi yayi aiki saida ta tabbatar Da Ya kusa zuwa gunta kafin ta juya ba shiri ta zubar Da stones din, zuciya daya yake tafiya kawai sai jinshi yayi yasha kasa hakan Yasa yayi lass tare da fadin washhhhh yana runtse ido Da gudu sultana ta kwasa ta fice Hafiz yabi bayanta Da kallo koma waye yasan masu gadinshi zasu kamo Mai shi ya fada yaci gaba Da abun Da yake ji a jikinshi,.
Kallan shi Zuwaira tai a ranta Tana fadin Allah ya kara, ganin Ya kasa mikewa Yasa ta Tashi tazo ta kalleshi ta duka tsaki har zata wuce sai kuma ta dawo Tare da fadin ka fadawa dogaranka su barni na wuce, hararar ta yayi bama tayi tunanin taimaka maiba Tana Mai wani zance, Da kyar ya samu ya dago, kallan ta yayi magana nake San muyi dake ya fada tare da mikewa Da kyar, wacce irin maganace wannan Da zaka wani dakko ni daga makwancina ka kawoni nan AI wannan iskancine,.
Kalkanta yayi kafin ya saki wani murmushi ya karasa kan kujera ya xauna, zo ki zauna za muyi magana, banza ta Mai batace komai ba ,ta tsaya tana kallan idon Allah ,kallan ta yayi ganin taki zuwa yasa Ya dauki remote tare da kunna Tv ,ganin Ya kunna TV MA Yasa ta karasa ta zauna acan gefe dashi,. Kallan ta yayi bansan ya akai kawai naji daban akanki ba na kasance a wannan masarautar muddin naga Ya Mace tamun babu ruwana Da wata matsala sawa nake a kamomin itta kawai inyi yadda naga dama Da itta, sosai jikin Zuwaira Ya dau rawa, yaci gaba amm bansan dalilin Da Yasa ke naji bazan iya miki hakan ba kawai naji ina sanki Da aurene, a dan razane ta kalleshi ya daga mata gira Amman ba dole indai baki sona sai IN miki yadda nakewa sauran ba wata matsala bane,.
Dan Allah kayi hakuri ni wlh...... Sai kuma tayi shiru tabe baki yayi bawai sanki nake ba aa kawai inaa sanki Da aure ne karki wani damu Na baki time kije kiyi tunani ni kuma ina nan ina jiranki, mikewa yayi tai saurin mikewa ittama to Kasa a maidani gun kwanan plz, murmushi yayi aike Da fita anan sai gobe saboda ana mutuwa duk wanda Ya fita awannna lokacin kinga kuma ina sanki a raye feel free ki kwana anan ba abun Da zan miki Ya fada yana daga hannu amma fa wannan maganar ta zama sirrin tsakanin mu,.
Da sauri ta gada kai, murmushi yayi good, wani Daki Ya nuna mata zaki iya kwana anan, Da sauri ta daga kai tare da yin gaba ta bude dakin tasa lock Ta ciki, haka kai Da gwiwa tayi Tana kuka,.
Sultana kuwa Da gudu Ta fice, ganin ana gadin gun Yasa ta tsaya tana mai Da nunfashi kafin ta karasa a hankali Tana tafiya basuce mata komaiba Dan duk a xacensu wadda Hafiz Yasa aka dakko Mai ce, Tana fita daga bagaren ta sauke ajiyar zuciya,.
Tana fita wasu suka Fara binta a baya, juyowa tayi kartine har uku banda idonsu Wanda ba dugon imani ba abun Da take gani Da sauri ta Fara tafiya, tanaji dayan Na fadin ai kasheki zamuyi wannan umarnine daga sarki duk wadda hafiz Ya kuka kisa ne, zaro ido tai tare da kara sauri,. Tafiya take suma basu fasa binta ba saiji tayi An riko ta, kafin Wanda ya rikota Ya juya Ya Kalli sauran tare da fadin zanji Da itta , jin hakan Yasarm suka juya dan sun ganshi Da irin kayansu .
Tunda ya rikota tasan shine dan taji kanshin turaren shi handala tayi,. Rike hannutq yayi har part dinshi Da gani ranshi a bace yake hakan Yasa sultana ta fara tsorata,yana zuwa Ya hada ta da bango tare da kallon idonta, kafin yace dole yau ki fadan dalilinki Na fitowa Da daddare a wannan masarautar
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 35*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Tsuru tsuru tai da ido, saboda yadda ya tasa ta a gaba har tanajin nunfashin shi, dan juyar da kai tayi yai saurin riko habarta, bani amsa inba hakaba wlh saidai mu ta tsayowa a haka muma kwana a haka ba damuna zai yiba, to sakeni sai in fada ma Ta fada Tana kallan shi, harara Ya bata kafin Ya saketa, ajiyar zuciya ta sauke ta na tunanin wacce karya zata shirga mishi kuma, kallan ta yayi ganin Tana tunani Yasa yai murmushi tare da fadin wlh kika sake kika mum karya nida kene, rau rau tai da ido kafin ta sami gu kusa dashi Ta zauna, uhmmmm dama dai wlh kasa bacci nai shine Na fito waje to dana fito shine nake yawo, shine wadancan suka ganni suka biyoni ni ba abun Da nai musu, ganin yadda ya hade rai Yasa tai kara tsorata baice komaiba kawai kallan ta yake ranshi a bace,.
Dan kara dubul bulcewa tayi wlh kadai bari in fada maka gaskiya wlh, dama muna bacci ne naga anzo an dauke Zuwaira shine Na biyo bayansu dan inga inda zasu kaita,hmmm yace tare da dauke kai, ya dauka ba zata fada Mai gaskiya ba,.
Kallan ta yayi, wato so kike a bataki kema KO?dan zaro ido tai Tana kallan shi, eh mana hakane inba haka maye naki Da zaki biyo bayansu inyaso koma Maye a hada dake KO? Ranka Ya Dade Zuwaira fa yar uwatace, tare muke a daki daya taya ina gani zaa dauketa ban biyo baya ba, haba ai ban cika kawaba, murmushi yayi ganin yadda take fada mai kenan zata iya yin komai game da kawarta wowww wannan abun Ya burgeshi friendshi kenan,. Dauke kai yayi Ya dauki system dinshi Da dama can a kunne take Ya ci gaba Da aikin shi,.
Kallan shi tai, kafin ta Fara magana a hankali ranka Ya dade na gode Da taimakon da kake ban na gode dafa tuni Na Dade da, mutuwa baice mata komaiba yaci gaba Da abun Da yake, Amman ranka Ya Dade wai taya kake fitowa a irin wannan lokacin ni abun naban mamaki fa, kallan ta yayi, kafin Ya dauke kai baki San komai game da wannan masarautar ba, MASARAUTAR MUCE baki San komai game da itta ba, tabe baki tai, wai masarautar suce,.
A kullun irin wannan lokacin ina fita ina zaga wannan masarautar saboda Inga ta,asar Da ake aikatawa tun ina yi a boye har yazo nake baiya na kaina har ya kasance nasan Wanda suke Da sa hannu a wannan abun, uhmmm to zaka fada mun dawa dawa ne suke Da hannu a hakan? Kallan ta yayi saboda ke wace? Dauke kai tayi Tare da fadin hmmmm, sai kuma Ya kalleta tare da fadin zonan sultana, kallan shi tai bata gane zonan ba, ganin Ya kafeta Da ido Yasa ta Mike ta Dan matsa kusa da shi, mikon hannunki wancan Ya fada yana nuna mata hannun hagunta, kirjinta ne Ya fadi, ran ka Ya Dade ban ganeba, eh cinye hannun Xanyi Ya fada yana kallan ta, kayi hakuri ranka Ya Dade Amman bazan iya baka hannunaba ai babu kyau Na miji Ya taba hannun Mace kuma ba badan dole ba aibanga abun Da zaisa IN zauna Da kai anan ba niba Matar ka ba, zaro ido yayi ni kike fadawa magana? Aa ranka Ya Dade ba magana nake fada maka ba yi hakuri indai Na bata maka rai, ajiyar zuciya Ya sauke kafin yace to muga hannun naki niba tabawa zanyi ba, kallan shi Tai kafin ta mika mai hannun, kallan hanun yayi sultana wannan zanen nake San karin bayani da gani bada lalle aka Yishiba so nake nasan Dame aka yi kuma kamar zanen masarautar mu,.
Dauke hannu tai ni haka Na taso naga hannun nawa, bansan daga inda yake ba, kallan ta yayi kafin yace zan iya ganin fuskarki sultana yana magana a hankali kamar ba shiba, gabanta ne Ya fadi ina ba zata yadda ba wlh, Dan Allah ranka Ya Dade kayi hakuri ni bazan iya budema fuskata ba tsorata zakai dan fuskata nada matsala, mikewa yayi Ya zauna kasan kusa Da itta, ni a hakan nake San ganin naki, gabanta banda dukan tara tare ba abun Da yake, Dan Allah ranka ya Dade kayi hakuri bana San abunda zaisa hankalinka Ya tashi Amman maye naka Na San dole sai kaga fuskata? Nima kawai Na tsinci kaina Da hakan ne Amman karki fassara dan ba sanki nakeba kkawa jikina yana ban ke kamar kina Da hadi danine saida naga wannan zanen ma, danja baya tai niba wani hadi Da nake dakai ni a jigawa nake Dan Allah kayi hakuri ,kallanta yake kafin ya fara tunani saima ta rainaka Ta dauka santa kake Amman ka tsaya kana wani damun dole sai kaga fuskarta alhalin ka wuce wannan gun, tashi daya yaji haushin kanshi ya mike ya koma kan kujera Ya hade rai karta raina shi
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 36*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Binshi tai da kallo yadda ya wani hade rai kamar ba shine Wanda ya gama make mata murya ba,.
Shiru tayi tana tunanin koya Zuwaira zata kasance may be Ma yanzu Ya gama bata ta Yasa ta fito an kashe ta KO ma meyasa yake sawa ake kashe bayin Allah oho Mai Amman zataso jin dalili kuma Zuwaira ce kawai zata mata wannan taimakon,.bacci take ji Amman shi KO a jikinshi Ya wani bude system kamar ba dareba,hamma tayi Dan ya gani Ya nuna mata inda zata kwanta KO kallan inda take baiyiba, ta sake yin hamma Da karfi har saida yadan tsaya Da abun Da yake kafin yaja tsaki yaci gaba Da abun Da yake tabe baki tai kafin tai murmushi bari tadan tabo masifar shi, karayi tayi Tana salati, a hargitse Ya kalleta waike meke damunki kinzo sai damuna kike, ha,a kallan shi take yana mata masifa, ranka Ya Dade bacci nake ji shi yasa, to rike ki nayi kije kiyi kwanciyar ki mana, kallan shi tai sai kuma ta mike ta nufi kofa taga Ko zaice Ya dawo, ganin har taje kofa baice komaiba yasa ta dan Saki tsaki ta bude kofan, idonta na sauka kan duhun tai maza ta dawo,.
Shi kuwa Kallan ta yake yana Allah dai Yasa yarinyar nan ba ficewa zataiba dan yaga tana fama Da danye kai, kallan shi tai kafin tai sama inda ya nuna mata ranar,.
Washe gari Zuwaira Da wuri ta tashi Dan batai wani bacci bama, tana jin Hafiz Ya fice masallaci, ta Mike Amman sai Da take bari gari Ya danyi haske kafin ta fito ta kama gabanta har gudu take hdawa dashi,..
Sultana bata tashi Da wuriba saboda ba sallah take ba gashi jiya bata Sami wani bacci ba, baccinta take bilhakki abunta gata tajita akan lallausan gado haka abun baa magana,.
Hindu Yau 9:00 nayi ta shirya ta nufi part din sultan Dan itta ta gaji wlh auren shi take San yi, zataje suyi magana tunda 10:00 yake fita aiki,.
Da sallama ta shiga part dinshi ganin baya parlour Yasa tai sama xuwa dakin shi knocking Ta Fara yi tana fadin Yaya sultan,.
Sultana dake bacci taji ana knocking da sauri ta mike ta saka dankwalinta ta fito, dai dai Hindu zata sake knocking kenan sultana ta fito, kallan Hindu tai ta kara murza ido Dan tabbatar wa Da idonta abun Da take gani indai ba karya bane sultana anan ta kwana.
Hade rai Hindu tai Me kike yi anan kardai kice anan kika kwana dan zan iya yin kisa indai naji hakane,? Ta fada tare da nufar sultana, kallan ta sultana tai batace komaiba Tana shirin rabawa ta wuce Hindu tai saurin rikota tare da hada ta jikin bango, wlh ki fada mun KO kuma yanzu inyi kisa ba abune mai wuya a guna ba, ta bayanta taji sultan yana fadin eh anan ta kwana KO kina Da ja ne? Bata kalleshi ba sai kallan sultana Da tai kika kwana a bangaren mijina daga zuwanki zaki bata mun miji, ta fada tare da sake sultana gara wlh in kashe ki IN huta, kokarin kwace kanta sultana take, har kin isa ke Yar uban wace kina baiwa,.
Cikin zafin nama sultan ya jawota tare da dauke Ta da mari , Da sauri ta dafe gun Tana kallanshi, gara suit dinshi yayi yana hararar ta, wlh duk sanda na kara ganinki a kan wannan yarinyar ni da kene bazan iya auren kiba, na fada miki baki cika abun Da nake so ya mace ta cika KO a harkar addini sai na Yar dake balleh aje ga tarbiya, Da gudu Ta fice tana kuka, direct bangaren babanta sarki tayi.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 37*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Direct fada ta nufa, da zuwanta taji cewa baban Nata bai shigo ba tukun hakan yasa ta juya ta nufi part dinshi bayi na gaidata amma ko a jikinta burinta bai wuce ta ganta a gun baban taba, Da sallama ta shiga parlour, ganin ba kowa Yasa ta nufi stairs dai dai lokacin suka fito itta Da mamanta suna tafiya suna hira ,a stair Da take ta duka tana kuka ranta kamar ya fice, Da sauri ya karasa gunta yana fadin subhanallah me Ya faru?kara fashewa tai da kuka sosai, hakan Yasa sarkin riko kafadarta suka nufi parlour mama na binsu a baya ittama hankalinta ya tashi,.
Kallan ta yayi fada mun Waya miki wannan abun har ya saki kuka koshi dan gidan uban waye dole IN daukar miki fansa, kallan shi tai sai kuma ta karaa fashe WA da kuka, Dady An ci mutunci na An wulakanta ni duk akan baiwa,da sauri Mama ta tashi tana zaro ido uban waye yai miki wannan abun? Kallan ta Dady yayi fada mun aka miki, Dady me aka mun ba wannan bane kawai dai inasan ka nunawa sultan iyakarshi ka Aura mun shi ta hakane zan dauki fansa, kallan ta yayi shima kanshi yasan bai isa Da sultan ba Amman ina dole yaiwa yarshi abun Da take so, kallan ta yayi shikenan abun Da kike so baiwar haka xa,a barta? Murmushi tai kabarta Dady zanji Da itta wannan Bayan aure, murmushi yayi tare da shafo kanta yayi anythin for you my daughter kije zanyi magana Da momy shi nasan itta zata sashi ,murmushin jin dadi tai sannan ta share hawanyenta ta Mike fice, Da kallo mama ta bita tanajin tausayin yar tata Amman Ya zama dole su dauki fansar wannan abun, zuciya wasai Hindu ta nufi part dinta taji dadin abun Da Ya fada mata,.
Kallan shi sultana tai ganin yadda ranshi ya baci, kallan ta yayi kije ki hada mun breakfast Wanda baida wuya saboda Na kusa makara sannan kije ki shirya kizo tare zamu fita, kallan shi tai wannan Tashi daya yake canzawa kamar bashiba, wucewa tayi ya bita Da ido kafin yabi bayanta,. Kwai kawai ta soya Da dankali sannan ta hada tea ta kai mashi ta wuce bangaren su,.
Da sallama tashiga part dinsu Zulai Ta gani zauna kusa Da Zuwaira tana mata sannu, Da sauri ta karasa gun me Ya sameta? Sultana ta fada Tana taba jikin Zulai Da damuwa ta Kalli sultana bataji dadi ne wlh nig ke Da itta yau kwata kwata banganku ba da na tashi daga bacci, karki wani damu muna lafiya, abu muka fita yi kafin ki tashi karki wani damu, fita tayi kafin wani lokaci sai gata ta dawo Da magani a hannunta dauko ruwa tai ta mika mata Ta Tashi ta sha kallan su Zulai tai Bari zan tafi gun aiki kar suga bana nan, to kawai sultana tace taci gaba Da abun Da take ,saida ta gama abun Da take sannan ta Mike taje tai wanka ta shirya kallan Zuwaira tai wacce take bacci sannan ta ja kofan ta fice,.
Da sallama ta shiga part din nashi, mikewa yayi tare da fadin muje, ba musu tabi bayanshi, kallan shi tai dan bata San inda zata shiga ba gaba KO bayaba, ranka Ya Dade ina zan shiga? Duk inda yai miki ya fada tare da shigewa baya tashi GA ta zauna baice komaiba yaja motan sukai gaba,.
Tuki yake abun shi yana bin karatun dake Tashi a cikin motan, itta dai batasan inda suka nufa sai get da taga abun bude ana fadin barka Da zuwa doctor yau kaso makara inji masu gadin, wlh yau ban tashi Da wuri kallan motan mai gadin yau aa yau Da iyalin ake tafe, kallan shi sultana tai sai kuma ta Kalli sultan Wanda yake abun dake gabashi kallan mai gadin yayi aa kanwa tace, ayyo Mai gadin ya fada shi kuma yaja motan yai gaba, parking yayi Ya juya yana kallanta, fito mu tafi,ranka ya dade anan ake siyar da sim din, bansani ba yace tare da ficewa hakan Yasa itta ta fito tabi bayanshi duk inda sukaje sannu ake mai ana gaidashi yana amsawa, office dinshi suka je, ya bude Da sallama sannan ya ajjiye abun hannunshi, Ya dauki abun Da yake bukata, ki zauna ki jirani ya fada tare da ficewa
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 38*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Kallan office din take sosai yai mata kyau, idonta sauka kan hotan dake office din na momy ne itta Da wannan wacce take mafarkinta,.
Da sallama sarki two shiga bangaren momy yace Da bayinshi su tsaya a bakin kofa su jirashi, haka kuwa akai, yana zuwa duk bayin suka zube suna kwasar gaisuwa, sannan jakadiya tai ciki dan kiran momy, momy tayi mamaki sosai kuma ta tabbatar koma maye abune babba, hijab tasa ta fito parlour kuwa ya basu gu zama tayi suka gaisa,..
Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya Fara nasan dai kin hadina Da marigayi Yaya Mubarak kuma nasan inda yana raye ba abun Da zan nema a gunshi IN rasa,kallan shi tai Abdullahi baka Da wata matsala ka fada mun maye indai zan iya yi ba komai ni Mai makace,hmmm yai ajiyar zuciya, yauwa Na gode Da wannan magana Da naji, ina fatan kina sane da cewa sultan bai daukeni tamkar Mubarak ba ni nasan kinsan Da haka shiyasa dana tashi neman alfarma banje gunshi ba nasan abun Da babba zan gano yaro bazai iya ganowa ba, haka yake Abdullahi ka fadi koma Maye ina jinka,yauwa dama zumunci ne nake San mu hada mai zai hana tunda wadannan yara nasan junansu mu hada su aure ina nufin sultan da Hindu, kallan shi tai nadan second tabbas kafin Mubarak ya mutu yana fada kamata yayi adinga auren dangi a wannan masarautar mai zai hana indai Maman sultana ta haihu a hada su aure indai macece (lokacin Maman sultana nada ciki kenan, )Amman GA abun Da Allah yayi ME Yasa back zatabi wannan hanyar ba ta cikawa mijinta burinshi tasan wataran sultan zaiso hindu kuma Hindu zata shiryo, Amman matsalan ba anan take ba sultan dinne taya zata Mai wannan maganar,?
Ajiyar zuciya ta sauke ta kalli sarki ba matsala Allah Yasa Hakan shi yafi alkairi indai sultan yazo za muyi magana IN sayo sai kaji yadda akai, wani murmushin jin dadi yayi kafin Ya mike tare da cewa Allah ya taimake Ameena ta fada sannan Ya fice,.
Da sallama sultan ya shiga office din nashi, banda tsaki ba abunda sultana take dan duk ta gaji, kallan ta yayi tashi mu tafi, ranka ya Dade harka gama aikim ne? Baice komaiba ya fice hakan Yasa tabi bayanshi, mota suka shiga Ya mika mata sim a gidan shi sannan yaja motan, sosai taji dadi ashe Yasa a siyo basai tasha wuya ba,.
Na gode ta fada sannan ta kara kallan shi Zuwaira bata jin dadi ranka ya Dade inasan IN naje zan wuce part dinmu, OK kawai yace,...
Tana parking Ta kama hanya,.
Bagaren shi yaje ya ajjiye abun dake hannunshi KO hutawa baiyiba ya nufi part din Hafiz,
Da sallama ya shiga, Hafiz Ya juyo yana kallan shi Da kwalban wine a hannun shi, murmushi yayi Ashe babban bako nayi ya fada tare da zama akan kujeran daya dake parlour, kallan bayin parlour sultan yayi yace su basu guri, zaro ido Hafiz yayi yace kace abun babbane,.
Ya dauki wine zai kai bakinshi kenan sultan ya dauke yana bashi harara, zaro ido Hafiz yayi tare da fadin easy men Me ke damunka part dinafa kazo, zama sultan Ta yayi wai me Yasa baka Da tunanine mai Yasa kake San batawa yaran mutane rayuwar su,? Yanzu fisa billahi ka batawa yarinya rayuwa sannan bakaje kaga Lafiyarta ba? Gyara zama Hafiz yayi men ban ganeba go on straight to the point mana, Zuwaira Da kaiwa fade jiya bata jin dadi, a dan razane Hafiz Ya tashi baice komaiba Ya raba Ta gefen sultan ya fice hakan yasa sultan mikewa yabi bayanshi,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 39*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Bin bayanshi yayi yaga inda zai nufa yana fita ya kira bayinshi kan cewa Sumai jagora zuwa dakin bayi na mata tunda bai saniba, angama ranka ya Dade sukayi gaba sannan aka Fara binshi a baya,
Tsaki sultan yayi KO Mai zaije yace oho Mai Amman gara ya bishi kar yaje ya cutar Da Yar matane tunda shine sanadi shiya fada mai,.
Cire Dan kwalin kanta sultana tai ta zauna kusa Da Zuwaira Da yanzu taji karfin jikin nata sai zufa take alamar zazzabin sauka zaiyi,. Sannu, murmushi tai nama samu sauki ina San zuwa in sanarwa Da Mama kartaga banjeba, da wanne karfin zakije daga tashi sai ki Fara yawo ai itta yakamata ta aiko taji KO lafiya bakeba kiyi zamanki zanje IN mata bayani,. To kawai Zuwaira tace, kallan ta sultana tai Zuwaira jiya Da daddere ina kikaje? Gabanta ya fadi ya zatai gaskiya zata fadawa sultana koya,tsareta Da ido sultana tai tana San taji me zatace,ta bude baki kenan zata fara magana sukaji ana fadin ga yayan sarki nan zasu shigo, hakan yasa KO wacce baiwa ficewa suka zube suna kwasar gaisuwa banda sultana dake kokarin daura Dan kwalinta Zuwaira kuwa jan bargo tai ace bata Da lafiya,.
Ta bakin kofansu sukaji marka Na fadin ga dakin nan, sosai gabansu gaba daya ya Yanke tsabar tsoro ai tuni Zuwaira tai kara shigewa bargo, Da sallama marka Ta tura kofan dakin ,sultana dake tsaye Ta amsa, idonta kan sultan ya sauka Da yake yiwa dakin kallan kurillah, dauke kai tayi ganin hankalin nasan dawowa dakin, kallan ta yayi ya dauke kai, karawa Hafiz yayi ya kalli sultana, ke Amman duk yadda akai baki da gaskiya ace mutun kullun fuska a rufe yau shine hadauwar mu Ta wajen uku kenan Amman ban taba ganin fuskarkiba ya zama dole Inga fuskar wacce take zama daki daya Da wacce nake so, zaro ido sultan yayi yaune yataba jin Hafiz yace GA wadda yake so allahalin ya batata Allah yasa ta wannan haryar ne zai shiryu,.
Gabanshi sultan Ya shiga malam kayi abun Da ya kawo ka ba kasawa wata idoba ina ruwanka Da itta, yana kaiwa nan ya riko hannun sultana, saida yaji shock Amman Ya daure ta fice Da itta,.
Zuwaira kuwa maloo tai bargo ya zatai Da wannan mutunmin kawai guduwa zatai, kallan dakin Hafiz yayi ya Saki tsaki baiga gun zamaaba, ke meke damunki ya fada a dan tsawace, ba komai dama zazzabine kuma ya sauka, tabe baki yayi, gobe ki sameni yana kaiwa nan ya fice ta sauke ajiyar zuciya itta ya zatai dashi ne Ma kawai so yake ya jaza mata masifa Dan tasan mama ba yadda zataiba,.
Suna fita waje sultan ya Saki hannun sultana ya gallah mata harara kinga ki kiyayi kanki Da wannan banzan ba hankaline dashiba banda bata mata ba abun Da ya iya,batace komaiba kawai binshi take, ganin Ya nufi bangaren momy Yasar tabi bayanshi dama nasan fadawa momy Sun dawo ,.
Da sallama ya shiga Tana biye dashi bayin gun suka kwashi gaisuwa Amman momy bata nan itta kwata kwata bata fiya zama a cikin bayiba,haka take, kallan jakadiya yayi jakadiya yaufa kindirmo nake San sha, a aikuwa kazo a saa dan kuwa akwai yau aka siyo yana fridge, kallan sultana yayi jeki debo ki kawomin ki sameni agun momy, an gama ranka ya Dade Ta fada tare da wucewa shi kuma yai sama,.
Da sallama ya shiga taba parlour tana rubuce rubuce, kallan shi tai Tana murmushi welcome son yau ka tashi Da wuri agun aiki, murmushi yayi tare da fadin wlh mom,
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 40*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
```indicated to maman shukrah aunty ummi```
Zama yayi a kujera, sannu son kunje ka siyawa sultana sim card din dan yau kwata kwata ban gantaba, Da sallama sultana ta shigo, zama tai kusa Da momy ina wuni Momy, shafa kanta tayi tare da fadin kina lafiya? Qlau wlh Mom yama siyamun sim din, OK mom tace sannan ta karbi phone din, matsawa kusa dashi tai ranka ya Dade gashi Ta ajjiye, sannan ta koma kusa Da momy,.
Mika mata wayan momy tai ta karba zata Tashi mom tace ta koma ta zauna tanasan yin magana Da sultan, daukan kindirmom yayi yana sha, son magana zamuyi Mai mahinman ci, OK inaji, son kana Da wacce kake sone?kallan momy yayi sai kuma ya kalli sultana ya bata wata harara a hankali yace aa mom, ajiyar zuciya ta suke, OK naji kana San Hindu ne, Da sauri ya furzar Da Da furar Da yakai bakinshi har saida ya kware, sannu mom tace kallan ta yayi,.
Haba mom meyasa kika mun wannan tambayar wlh badan Allah take sona ba ittama nina Na sani sannan kinfi kowa sanin bana Santa, hmmm aiko hakuri zakayi Dan na yanke shawarar hadaku aure nida mahaifinta nasan wata rana zaka sota ai, Amman kana Da chance a duk sanda kaka wacce kake so zaka iya Aura koda kuwa ranar auren sai mu hada duka Amman wannan auren zumunci zamuyi Wanda babanka yake mafarkin yi ina fatan ba zaka ban kunya ba plz son ,.
Shiru yayi ranshi na soya Amman duk soyan rannan nashi hakan bazaisa yayi mata musuba ittace maman shi kuma bananshi zai iya yin komai wa itta,.
Sultana shiru tai batace komaiba Amman tana hango masifar Da zaai tsakanin hindu Da sultan tunda itta shaidace baya santa,.
Kallan mom yayi bakomai mom Allah Yasa hakan shi yafi alkhairi yana kaiwa nan ya fice abunshi, Mon ta sauke ajiyar zuciya tasan kawai ya fada ne dan ba yadda ya iya, kallan sultana tai wadda ittama jikinta yayi sanyi, jeki kira mun jakadiya,to tace tare da mikewa ta fice, sai gata ta dawo, .
Dakko takarda da biro hakan akai, sultana karbi ki rubuta abun Da zan fada, karba sultana Tai,.
Bayan sallama ta daura Da sako zuwa fada a sanarwa Da sarki cewa sultan ya amince Da auran hindu zasu iya saka rana a ko wanne lokaci sannan akai sallama, taba jakadiya tace takai sakon, Ta karta tare da ficewa dan cika umarni,.
Kallan sultana momy taii dauki furar nan ki kaiwa sultan, sannan a matsayinki ka kanwarshi kisan yadda zaki kwantar Mai Da hankali, daukan furar sultana tai ta fice ta nufi bangarshi,.
Da sallama ta shiga yana parlor ya jingina Da kujera
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 41*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Da sallama ta shiga Part din nashi, yana xaune a kan kujera ran a bace yake, wai taya zaai ace ya auri Hindu yarinyar Da bata Da tarbiya bata san abun dake mata ciwo ba dadin dawa bama ya Santa,.
Karasawa parlour tayi tana kallan shi taya zata fara tunkarar shi gaskiya momy Ta hada ta da aiki ,Jiyar zuciya ta sauke ta karasa gunshi ta ajjiye Mai, kallan ta yayi Maye wannan kije dashi bana so, murmushi tayi kayi hakuri ranka ya Dade bai kamata wai dan akan hakan kana fushiba ai abun alkhairine Ma ace kana Da aure kamarka ranka ya Dade ace baka Da mata, juyawa yayi yana kallan ta it like yasan wannan muryar, tsaki yaja ya koma ya zauna ki dauke abunki ki wuce dashi banaso nace, OK Ta fada tare da ajjiyewa amma ranka ya Dade aduk halin daka tsinci kanka kana salati hakan zai sanyaya maka zuciya, baice komaiba kawai yayi shiru Amman zuciyarshi tafar fasa take, daga waje yaji ana shelar cewa gobe ana taron kowa Da kowa zuwa gun Sa ranar yarima sultan da yar sarki Hindu, Wanda zaa yi gasar harbin kwari Da baka a bisa Al, adar wannan Masarauta indai abun farin ciki ya samu suna wannan gasar sannan ansa babbar kyauta GA Wanda yaci wannan gasa , kallan sultan sultana tayi ya wani Kara hade rai kamar hadari,.
Juyawa sultana tayi zata fice dai dai lokacin Hindu ta shigo Da sallama, kallan sultana tayi, ittama kallan ta sultana tayi kafin tai kasa Tana kwasar gaisuwa, murmushi Hindu tai kiyi mikewar ki yau ai ranar farin cikine saboda haka karki wani damu so nake muyi magana dake, kallan ta sultana tai sai kuma Ta Saki murmushi Ta Mike tabi bayanta, zama Hindu tai a kusa Da sultan, Ta tabe baki dole dai a so ni wlh, yana jinta baice komaibq kuma bai dagoba,
Kallan sultana tai plz zuba min wannan furar yau kinsan yadda nakejina kuwa a sama nake jina, murmushi sultana tai ta mike taje kusa Da furar Ta zuba mata Ta mika mata, thanks ta fada Tana murmushi,plz zauna akan kujera yanZune lokacin ki Da ya wuce bazaki sami wannan damar ba kinsan yaushe zai wuce? Aa sultana ta fada tare da zama daura kafa kan daya tana jijjagawa tare da fadin Bari inyi anfani Da damata,, murmushi kawai Hindu tai, daga ranar dana shigo wannan bangaren a matsayin matar uban gidanki kashinkine zai bushe,, zaro ido sultana tai kice inyi anfani Da wannan damar karta wuce, amma dole insa wannan ranar a tarihi, murmushi Hindu tai hakama sultana,.
Hindu taci gaba kinsan me yasa gasar harbi? Gyara zama sultana tai fada mun insha plz, saboda ke nasan ba abun Da kika iya nasan ba zaki iya ciba shiyasama nace harda mata, wani kayataccen murmushi sultana tai inkuma naci fa mai zai kasance? Motace haddadiya nasa kinaci shikenan ittace kyautar ki, gyara zama sultana tai ai kuma baki tsanmanim zan ci ai kamata yayi kiban dama IN dama KO?ok fadi ina jinki koma Maye zan iya miki ,koma maye kin dauki alkawari? Daga kai Hindu tai batare Da wani tunani ba, koma Maye Dan nasan ba iya ci zakiyo ba, mikewa sultana tai Tana murmushi zan wuce sai mun hadu gobe, ta juya tana kallan sultan dake dauke Da murmushi KO Na maye oho Mai, ta kalli Hindu tai tare da daga mata hannu, da harara Hindu ta rakata ai nasan ba zaki iya ciba koma Ma ye ina dauke dake banza kawai, haka taitaiwa sultan surutu shidai baice komaiba dan kanta Ta gaji Ta fice,.
Suna zaune a daki duk su ukun, Zulai take fada musu zancen kasar, tsaki Zuwaira taja wannan ai shashanci ne sai kace a littafin yaki wannan ai aikin banzane, mtswwww taja tsaki, murmushi sultana tai kinga kuwa nima zan shiga wannan gasar kawai saboda sultan da momy duk basa San auren saboda zan shiga, duk kallan ta sukai To dan basa so taya kika ganin zaki cecesu a matsayin ki Na baiwa? Murmushi tai sannan ta fada musu abun Da take shirin yi, zaro ido Zuwaira tai kafin Ta taba wuyan sultana anya kuwa ba zazzabi kike ba, dariya Zulai tasa kaji bama wannan ba a ina Ta isa harbi sai kace yar gidan maharba, murmushi kawai sultana take,.
Riko kafadar Ta Zuwaira tai Dan Allah ki tashi daga wannan baccin kinsan Hindu ba zata taba amincewa Da wannan kudurin nakiba,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 42*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Ture hannunta sultana tai banisan Iskanci Na fada miki saboda abun Da zanyi babu ruwanki, tabe baki Zuwaira tai kawai,.
Kallan Zuwaira sultana tai Ya kukayi Da Hafiz wai?tsaki Zuwaira taja sannan ta fada mata abun Da yake so, kallan ta sultana tai, Zuwaira taimako zakiyi kodan baki San Hafiz mai zai hana ki amince may be take sai kiga ya shiryu taimako ne zakiyi,kallan banza Zuwaira tai mata lallai baki da hankali Da bakinshi yasha fada mun ya bata Yan mata ba dadi ni kuwa mai zanyi dashi, plz Zuwaira, ganin sultana nasan damunta yasa ta amince Amman karya take,.
Hafiz ne zaune kusa Da Mama, Hafiz naji ance kaje wai gun Zuwaira meya kaika can? Mama bata Da lafiya naje dubata, kallan shi tai ka tabbatar daga haka ba komai? Aa mama Santa nake, hade rai tayi taya zanso ka auri baiwa haba Hafiz, mikewa yayi nidai itta nake so wlh indai ba hakaba saidai ya fasa auren yana kaiwa nan ya fice, tabi bayanshi Da kallo dole Ta yadda Ta bashi wadda yake so amma ina bazata so ace yaronta zai auri baiwaba amma zata fi kowa murna indai danta ya shiryu maybe sanadiyar auren ma Ya shiryuu,.
Da sallama ya shiga fadar, zama yayi kusa Da Dady nashi aka basu gu, kallan shi sarkin yayi ya akai Na ganka haka? Dady inada wacce nake San a samana rana Da ittane gobe indai zaa Sa naa Hindu saboda haka ai yi double din komai ,.
Gyara zama sarkin yayi wace itta yar gidan wace? Ba kowa bace kawai baiwace kuma itta nake so, to kai kuma tanan ka bullo haba Hafiz baka San Dan sarki sai yar sarki ba? Turo baki yayi nibansan wannan ba kawai itta nake so, hmmm kawai sarkin yce to naji itta ta amince ne? Niban fada mata zancen saka ranar ba Amman Na fada mata ina Santa kuma goben zanje IN sanarwa iyayenta,to kace abun babbene, Amman ka yi hakuri sai bayan an gama na sultan sai muyi naka kaga lokacin Ya kure, Da kyar sarkin Ya sha kanshi ya amince ya tafi, .
Lallai Hafiz yana san jaza mai wani abun ai abun kunyane wannan wai Dan sarki Da auren baiwa,.
Washe gari
Da safe kuwa ya kama gun aikinshi, bayan sultana ta gama taje suka gaisa Da momy sannan ta nufi bangaren sultan ,.
Sallama tayi Ta shiga yana zaune kamar jiya, dukawa tayi Ta gaidashi Ya amsa har zata tashi yace Ta zauna za suyi magana Ta zauna tana sauraren shi ,so nake naji me zaki nema agun Hindu indai kince wannan gasar, kallan shi tai sai kuma tai kasa da kai, kawai innnaci kaji, tabe baki yayi ya Mike biyoni, yai gaba Ta bishi wata hanya Ta gani itta bama Ta taba ganin wannan hanyar ba, wani gune babban fili sai baka dake gefe Da kuma wani abu acan nesa Da digo a tsakiyar shi, kallan ta yayi dauki gwada in gani, kallan shi tai sai kuma Ta dauka Ta saita Tana harbawa bai taba point dinba, tsaki yaja a haka zaki cinye Bari IN koya miki, ya matsa bayanta, juyawa tai suna facing juna ranka ya Dade me zakayi nima fa Na iya, baice komaiba ya juyar Da itta tare da riko hannuntq Ya nuna mata yace taita yi yana gani
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 43*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
*this page is for you Hajara alhasan namesy hajara friend*
Kallan shi sultana tai ranka ya Dade nifa na iya wannan abun no need ka sani a gaba kace zaka koya mun wlh Na iya, OK kinfi San ta baki kunya a cikin jama,a kenan KO? Juyar Da kai tayi ranka ya Dade yau ba zuwa aikine? Babu ruwanka ki kedai ki Yi abun Da Na Saki, kunkuni Ta Fara wai anzo ansa mutun a gaba nace na iya nace na iya Amman anki abar mutun, murmushi yayi saiki tayi,.
Itta kuma kawai ba zata iya sakewa tayi abun Da zata tayi bane yana gun,.
Hindu data shigo tun dazu Tana neman sultan ganin kofan a bude Yasa ta shiga ciki, idonta ya sauka kan sultana dake harbi bata sami ko daya ba, wata uwar dariya Hindu ta fashe dashi, wai ke a dole so kike kiyi ki cinye komai ko, wowww Ta fada tare da jan kujerar daya daga gun ta zauna, Bari inyi guiding naki, Hmmmm kawai sultana tace Ta dauki bakan, saida Ta tabbatar Ta saita kamar yadda bahubali yake yi a film dinnan sannan ta Saki, aikuwa bai tashi sauka ba sai a point dinnan harda ya bula ya fice Ta ciki, zaro ido sultan yayi ya akai haka yarinyar Da bata wani iya ba Amman yanzu tayi Sa, a data sami point din,.
Hindu kuwa mutuwar zaune tai tama rasa Ta hinda zata Fara, kallan ta sultana tai ta daga mata gira, wani murmushi Hindu tai kafin Ta mike Tana tafi ai dan ci anan ba shine yake nufin zakici a can ba, Amman fa abun naki yaban mamaki, karkiyi wani mamaki sai kinga Ma naje wajen gasa na cinye anan ne zakisha mamaki, kallan Hindu tai tabbas Ta Fara shan jinin joints what if in sultana ta cinye ya zatai Da itta me zata nema a gunta kaii ina, kallan sultana tai kafin aje can so nake inji me zaki tambayeni in kinci,dariya sultana tai sosai har Yasa ta Hindu ta Fara kulewa, dagowa sultana tai kardai kice mun har kin Fara karaya haba matar sultan Ta fada Tana kallan sultan Wanda ya bata harara tai murmushi tare da kallan Hindu.
Hade rai Hindu tai wayace miki na karaya kawai dai ina San jin abun Da zaki bukatane, zaro ido sultana tai naga kina Da tabbacin ba zan ciba to Maye naki najin sai na fada miki me nake so, Hmmmm kawai Hindu tace Ta koma Ta zauna Tana rayawa a ranta tasan ai sultana ba zata iya ciba haba bazai yuyu ba AI wannan Ma Allah NE kawai yayi zataci ,.
Kallan sultan Hindu tai Yaya sultan, anjima ne fa za,aje ayi a filin Da ake hawa nacan unguwar jeka Da fari, bazan Sami damar zuwaba ya fada yana danna wayarshi, Haba yaya yaunefa Sa rana taya zakace ba zakaje ba haba Dan Allah,ina Da aikin yine shiyasa babu ruwanki, hawaye idonta ya kawo yanzu yaya saika nunawa kowa cewa kai baka sona ni kadaice ke haukana gun Sa ranar Ma kace ba zakaje ba haba Yaya sultan, kallan ta yayi duk sai yaji tausayin Ta, ya zaiyi koba komai nan bada dadewaba matar shi zata zama kawai ya rungumi kaddara ya lallashi kanshi Ta hakan NE zai Sami saukin abun, kallan ta yayi Yai murmushi to naji share hawayenki zanzo, zaro ido tai Tana kallan shi Da gaske kunne yaji kuwa batai tsammanin zaice zaijeba, dariya tayi hade Da hawaye Ta mike ta fice kawai abun tana murna ya bita Da murmushi, duk sai jikin sultana yayi sanyi indai har da gaske sultan ya Fara San Hindu tofa ba zata rabasuba, dama kawai Dan shi zatai Amman in ya nuna ya Fara Santa zata hakura farin Cikin uban gidanta shine Nata, ajjiye bakan tayi sannan ta fice,.
Parlour taje tayi aikace aikacenta sannan ta hada breakfast taje ajjiye sannan ta nufi part din momy, Da sallama Ta shiga ,Da murmushi momy Ta tarbeta, zama tai a kasa ya zama momy? Har kin gama aikin? Eh momy to ya akai, momy wai kina San auren sultan da Hindu kuwa, gyara zama momy tai, me kika gani sultana aa momy ba komai kawai dai tambayarki nayi, gyara zama momy tai inaso mana sultana kodan hadin kansu kina gani sultan bai dauki mahaifin Hindu a bakin komaiba Amman kinga IN akai auren nan komai zaiyi dai dai nasan zai daukeshi matsayin uban, kasa sultana tai da kai ina amfanin abun Da take San aikatawa kawai gara Ta hakura kodan momy ma, kallan ta momy tai kema zakije ganin gasar ne? Eh mana momy, OK kice zakisha kallo inajinma ba zaa sami macen Da zatayi wannan abunba, Hmmmm kawai sultana tace yaka sukai Ta hira,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 44*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Bayan la,sar masarauta Ta Fara shirin zuwa gun Sa rana, .
Da sallama sultana ta shiga bangaren su na bayi, kallan su Zuwaira tai dake Ta fama Da shirin tafiya gun sa rana, Zulai na ganinta Ta saka dariya kaga Mai harbi kaga Mai harbi yar gidan maharba hararar Ta sultana tai bana San iskanci fa Zulai zamu iya batawa dake wlh, murmushi Zuwaira tai to ya ake ciki ina fatan kin fasa wannan banzar kudurin naki, tsaki sultana taja ni nama fasa zuwa, Da sauri Zuwaira ta karasa gunta Dan Allah kiyi hakuro nifa ba cewa nayi kar kijeba kawai cewa nayi ki fasa wannan kudurin naki Dan nasan Hindu ba zata amince ba Amman indai abun ya bata miki rai kiyi hakuri,riko hannunta sultana tai bawai haka bane kawai dai na fasa zuwane, dagyar suka shawo kanta Ta amince,.
Shiri suke sosai, kowa a masarautar shiri yake suna gamawa aka kwashe su zuwa filin gasa, sosai indo sultana ya rena fata ina zata iya fita Wannam dan dazon tayi wata aba wai itta gasa, Allah Ma dai yayi Ta fasa shi, Dan harda yan gari can gefe kuma manyan mutane ne harda governor na garin ba sarki Da Da dogaranshi a gefe ga kuma wasu mayan mutane masu ji Da kudi a gefe suma,.
Gu suka samu suka zauna suna kallo, haka akai Ta zuwa sannan Bayan gu ya cikane ana jiran shigowar Hindu da sultan,motoci sukai tayin parking,ta Su a tsakiya sannan aka bude musu a Tare suka fito sunsha ankon shadda kalar ruwan toka Wanda dinkin yayi musu kyau ga doguwar rigar Hindu da tasha dinkin shurfani Ta daura alkabba a kai tayi kyau ba kadan ba sosai kuwa sannan suka fito aka dauki yi musu tafi suka nufi gurin zaman su,kusa Da Hindu mama taje Ta bata kiss a kumatu tare da fadim kinyi kyau sosai yata, murmushi Hindu tai kafin aka Fara gudanar Da harka inda mai shela ya dauke Lauderspiker ya Fara bayani kamar haka ,.
Kamar yadda muka taru anan gun zamuyi kallon waye jaruminmu KO kuma jarumarmua a wannan gasa sannan zata sami kyautar hadaddiyar mota Wanda gimbiya kuma sarauniya hakima ranta ya Dade gimbiyaa hindatu yar gidan sarki tasa, nan aka dauki tafi rapp rappp rappp,.
Haka aka fara gudanar Da gasa gun harbin gudu ukune indai ka Samu duka kaci indaj KO ka sami biyu baka sami dayanba shima ka fadi,.
Wani ya fito sai kuri yake ana Mai kirari kaga dan maharba jikan maharba munsan wannan gasar takace dole motar nan Ta zama taka, shi kuwa sai wani fasa kai yake baya shi ana mai kirari, bakarma dakkko mai akai yana wani cin magani ya nufi gun Yan dakko bakan, ya saita yana harbawa ya caki tsakiyan,nan aka hau tafi rafff rafff rafffff, aikuwa ya kara fasa kai bayashi yana zuwa na biyu with full confidence yaje zai harba Amman ina tuni mashin yayi nashi gun, aikuwa kahau fadin ohhhhhhhhh ya fadi jiki ba gwari Ya koma ya zauna,.
Wanine ya mike yaje sai kirari yakewa kanshi saishi Dan gidan maharba karyar maharbi yace zai kasa dashi koshi waye, Da kafama ya dauki bakan yai wulli Da itta ya cafe a hannu sai ihu ake mai yana fasa kaiii, haka yai abunshi tun a farko Ma ya fadi,. Haka akai tayi mutane na faduwa daga Mai cin biyu saura daya sai Mai cin babu, haka har akazo kan wani Da gani bashi Da kudi badan gidan kowa bane, Da addua ya shiga gun ya dauki bakan kuwa yana harbawa ya Sami first point din hakama na biyu, ana ukun duk ya saddakar yana zuwa Da adduar yana harbawa ya samu, nan take yai sujjada Ya godewa Allah yana murna. Nan aka hau Mai tafi, anje zaa mika Mai kyautar shi hindu ta mike tare da fadinn ina Da magana .
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 45*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Saida cikin sultana ya bada wani kugi kallan Zuwaira tayi kashi kikejine? Hararata sultana tai taamai Da kallan ta ga Hindu Dan Tana da tabbacin akanta zatai magana ,.
Karbar speaker Hindu tai, ta hau kana tage. Kafin ta Fara magana ina mika godiya GA duk Wanda ya taru anan saboda mu mun gode sosai, kallan Wanda yaci gasar tayi sannan ina Mai jinina naka yakai wannan jarumi dan tabbas ka zama jarumi jaruminma babba, saidai bafa anan aka kawo karshen gasar ba wannam shine karo na farko a cikin gasar, kallan ta yayi yana San karin bayani, murmushi tai,.
A bangare na mata basu fito gasa saboda sun riga Sun gama zabar zakagurar su wacce tayi daya yi fuce wajen harbin baka kuma fa harda ni a wannan zabe Da mukai, saboda haka zata fito nan Ta gwara Da jarumin mu na bangaren maza, sannaan ni Hindu na mata alkawarin indai har taci wannan gasa koma Maye take so zan mata koma Maye nadauki alkawari,.
Juyawa tayi Tana kallan sultana, wadda duk ta gama tsorata, ba tare Data karasa gun sultana ba ta fara magana haba zakarar mu ki fito mana naga kina TQM zaro ido kamar wacce ta kama barayo aikuwa duk gun aka Sa dariya harda Zuwaira Da Zulai Da basu San inda zancen ya dusa ba, tabo sultana zuwaira tayi wannan wacce macece Data zabi yin haka wlh na tausaya mata Allah sarki,sultana batace komaiba Amman ranta ya baci wai itta Hindu xata ciwa mutunci,.
Kallan gun dai sultana take haba Dan Allah kar ki bada damu, ganin sultana taki mikewa tasa ta Fara tafi Dan Allah a tafawa zararmu ta mata Ashe mulkinne Ya tashi ta fiso a Sami Wanda zai take mata baya Amman karki Damu Da kaina zan take miki, da sauri sultan ya karasa gunta, Ya matsar Da speaker din, wai me kike Hindu wannanfa cin kutuncine, daga zasa sukaji wani na fadin mun matsu muga jarumar taku, karku wani damu ga yarima da kanshi Ma yazo zai taka nashi rawar ganin, yace shima zai take mata baya saboda haka maza ya kamata KO karaya tun yanzu fa, ta riko hannun sultan sunaka nufi gun sultana,.
Kirjin sultana sai dukan hamshin hamshin yake duk ta gama tsorata, saida Hindu ta biya ta dauki bakan kafin ta nufi gun sultana, kallan sultana Zuwaira tai kai kefa wannan nan take yowa gunwa zatazo,?guna zatazo sultana ta fada da sauri su Zulai suka kalleta gunki kuma Mai Ya hadaku? Kafin ta basu amsa tuni su sultan Sun karaso, kallan Hindu sultana tai ittama haka, Hindu ta sakar mata wani uban murmushi, idon sultana duk ya kada dan Hindu taga bata shiga shine take San ta yalbatsa ta a gaban mutane ranta inyayu dubu ya baci, kuka ne kasan kwace mata, zaro ido Hindu tai jama,a jarumar mu kuka take san yi dukda banga fuskarta ba Amman idonta ya kawo hawaye ta safo hawayen idon sultana dake San zubowa ta Kalli, haba jarumar mu kardai kice har kin karaya? Ganin sultana na hawaye yasa Hindu fadin aa basai kinyi kukaba zamu hakura muba jarumin maza kyauta ta fada Tana shirin juyawa dan barin gun, sultana ta mike tare da mika mata, hannu tafi Hindu tai ta zucuyo wlh Ta zuciyo, ta fada tare da mika mata, gaba daya yan gun sunyi shiru Dan sun gane cin mutuncine Hindu kewa sultana, karba sultana tai, Tana kallan Hindu, tazo wucewa Hindu tasa mata kafa, Tai gaba zata fadi, sultan yai saurin rikota, Ya dagota thanks ta fada tare da wucewa gun, sukabi bayanta,.
Gun mashin sultana tai nufa ta dauki guda shida, nan aka hau mata tafi, daga baya ta tsaya tasaka mashin duka shidan a jikin bakan, kamar yadda akai bahubali,.
Ta daga Tana shirin danawa ta juya Tana kallan Hindu dake mata murmushin mugunta, Tana kallan Hindu ta saki duka mashin guda shidan, masu karatu kunsan abun mamaki suna tafiya mashin duka kowa ya kama Dan uwanshi suka raba kansu biyu biyu, suka raba kansu gida uku, basu tashi sauka ba sai a point din Da ake so kuma KO wanne abu yana dauke Da mashi biyu dake tsakiya Sun shiga har sun ratsa biyu, da sauri Hindu ta Mike daga zaunem Da take hakama sarki wato Abdullahi yana fadin Irin harbin abdulsalam NE wannan
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 47*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Ganin sarki ya Mike Yasa na kusa dashi suka Tashi suna tafi tabbas Ta burge haka gun ya dauki tafi rafffff raffff, Hafiz da saida ya cire glass dinshi sannan ya Mike yake kusa Da gun datai harbi tabbas taci Amman duk yadda akai ba itta daya bace kodai tayi amfani Da tsafi KO kuma aljanu sun taya ta, kallan ta yayi ganin yadda suka kallan kallo Da Hindu, saida ya wani Saki murmushi lalli akwai abu anan gun .
Ganin Ana tafi Yasa sarki shima ya Fara Amman na dole, wannan KO ittace kai ina ba itta bace ina shidai abdulsam saidai yayi amfani Da gudu uku Dan bai iya guda hudu bama wannan baiwace kawai Allah ya bata bai zama lallai itta bace to taya zai Fara binciken shi may be ma Ta dade Fara tin bincikenta ,.
Sultan kuwa mutuwar zaune yayi danshi kwata kwata nuna Mai ta iya ba, Hindu kuwa duk tabi ta tsure mai xata tambaya a gareta tasan yanzu indai ba cewa sultana zatai ta fasa auren sultan ba shine kadai zata ta shiga wani hali baya dashi bataga abun Da zai sata a wani hali, sosai gaban Hindu ya fadi ina intace hakan kuma ya zatayi tasan dole sultana taa dauki fansar abun Da tama Amman ina zata Yi amfani mulki indai akan hakane wlh bazata iya cika wannan burinba Allah Ma Yasa bashi bane,.
Saida Mai shela yai magana sannan gun yayi shiru kowa ya zauna sannan ya Fara magana, gaskiya munyi mamaki sosai da wannan zakarar matan jurumar Matam mungode sosai kuma taci zabe, yanzu zamu bata kyautar ta Dan kuwa koshi zakaramu na maza ya sara mata yace no need Ya bugu yasan itta zata cinye yace yaji ya sare, duk aka hau tafi, sannna zamu so ganin fuskar wannan jaruma tamu sannan zamuba jarumarmu gu Dan ta tafo albarkacin bakinta,.
Hawa gun sultana tai bayan tayi sallama sannan ta daura ina Mai godewa Allah daya ban damar cin wannan gasa, sannan na godewa Yan uwa Da abokan arziki game da tayi murna Da suke na gode Allah ya saka sannan game da kyautar gasa ittama na gode sannan kamar yadda aka ban kyautar wannam Mota haka nima zanba Da itta kyauta ga zakaran maza nan aka Hau tafi sannan taci gaba ni kyautar Da gimbiya hakima sarauniya Hindu zata mum ma Ta isheni ta juya Tana kallan Hindu, wacce ta hadiye wani yawu ta Saki murmushi sannan ta ci gaba maganar ganin fuska ta kuma bai taso ba dan inah Da matsala a fuskata ina bude zuciya mutane da yawa anan takan iya tashi, saiji nayi ana eyyyah Allah ya bada sauki, aka amsa da Ameen,.
To yanzu dai zan gudanar Da kyautar Da nake so gimbiya Hindu tai mum kuma ba akan komaiba bane illah, kawai kawai abune kadan shiyasa nace kawai INASAN GIMBIYA HAKIMA SARAUNIYA HINDU TA HAKURA DA AUREN YARIMA SULTAN, a razane Hindu Ta mike hakama mama da sarki, da sauri mama ta karasa gun sultana tai karbi speaker wannan wanne irin kudurine Amman kinsan hakan bazata iya yuyuwaba kuwa ke a wa ke a yar bayi harma kin isa ke din wace ke yar gidan uban wace, ki fadi koma nawa kike so zaa iya baki Amman banda wannan, wani murmushin takaici sultana tai batace komaiba kuma bata Da niyar yin maganar, .
Sarki ya tako kusa Da itta yake wannabe baiwa kinsan dai wannan MASARAUTAR MUCE bai kamata ace ana abu maka mancin hakana ke kuwa me Yasa kike San raba wannan zumuncin Da muke San hadawa, a matsayine na wannan sarki naku nake rukanki Da ki hakura Da wannan burin naki kome kike so zan miki shi, murmushi sultana tai kafin ta karbi speaker,.
Ba komai tunda sarki ya nemi a alfarma zan iya mishi Amman a bisa sharadin saidai inhar shi uban gidan nawa shi ya amince Da zai auri Hindu din Dan ni nasan komai bawai Santa yake ba Amman indai har ya nuna IN janye kudurina zan iya saboda dashi sannan inasan itta gimbiya Hindu ta zauna tayi tunani akan hakan nasan itta zata fuskanci inda na dusa saboda Da itta mukai wqnnan maganar ni Dan Na fadi abun Da nake so banga abun daga hankaliba,yanzu sai a jira daga bakin uban gidana, mikewa sultan yayi dole zai ramawq sultana abun Da Hindu tai mata Dan shima baiji dadi bai kamata ace tai mata abun Da ta mata ba, Hindu kuwa duk ta gama sadakarwa KO Da fadin sultan ya Santa akai ai an gaa Da itta,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 47*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Bayan yayi salama ya Fara, eh kamar yadda Ta fada bana San Hindu hakane sannan na gode Da wannan dama Da baiwata ta bani, sosai ran sarki Da Mama ya baci waisu saaiwa rashin mutuncia tozar tasu a gaban matane wannan wanne irin abune dole su dauki fansa akan wannan baiwa koma itta wace, Hindu kuwa kadane ya rage bata saki futsariba ina Dole dauki fansa duk yadda akai sultan shi Yasa sultana ta mata haka sosai ranta ya baci,.
Sannan yaci baga itta Ma kuma Hindu bata kyauta ta itta wannam baiwa batai niyar tashiba Amman dole saida itta hindun ta zigo ta dan ta mata haka ba wani abu bane kamata yayima mu gode mata da har ta bani zabi inba hakaba kunsan dole ne a cika wa wannan baiwa alkwarin Da gimbiya Hindu ta dauka mata duk Da nasan saboda daukan fasa tayi hakan Amman ina Mai bawa baiwata hakuri Data yi hakuri komai Ya wuce inyaso su hadu itta Da gimbiya Hindu su yi magana daga baya amma zancen fasa aure bai tashiba, yayi sallama sannan ya koma gunshi ya zauna hindu ta cika tayi fam jira take kawai ta fashe,.
Sarki Ya bada umarnin mai shela ya fada kan cewa Yau laraba yana San san wannan jumaar axo daurin auren yayanshi Da zaai a babbana masallaci,.
Haka kuwa ya fada akai ta murna ana buduri Amman banda iyayane amarya Da Hindu da duk ransu yake abace,.
Ganin sarki ya mike Ya sultan mikewa yabi bayanshi aboye wani gu yaga yaje ya tsaya Da wasu kartin mutane, so nake duk inda wannan yarinyar take kafin abar wannan taron KO tabbatar kun kamamin ittaa kai mun itta dakin ajiya a masseurs zanzo Da kaina zan kasheta a gaban mahaifint dan ina Da tabbacin ittace yrinyar abdulslam, sosai gaban sultan ya fadi, buya yayi sarki ya wucw sannan ya fara dube dube kamar daga sama ya hango Ta fito daga wani gu tana gyara daurinta, da sauri ya karasa gunta ya riko hannunta Da sauri ta kalleshi ganin shine Yasa ta sauke ajiyar zuciya mota ya sakata sannan a dakko biro Da takarda ya mika mata, ki rubutawa Hindu cewa kinbar wannann masarautar kin koma garinka saboda ba a cika mika alkawarin kiba, saboda me Ta fada Tana kallanshi, zaki rubuta kowa kinje kinsa rayuwarki a hadari, karba tayi ta rubuta sannan ya karasa gun Zulai yace gashi tayi shigar sultana ta kaiwa Hindu karta bari a ganta ,haka kuwa akai Zulai bata tsaya tambayar daliliba ta kai mata sanda Hindu ta gani murnushi tai tare da fadin yafi miki ma,.
Direct masarautar suka nufa yana zuwa yai parking ba kowa hakan Yasa yace ta fito bangaren momy suka nufa yana zuwa you shigar Da itta bangaren, momy mikewa momy tai Tana tambayar lafiya, tsaki yaja kafin TQM sanarwa momy sannan yace ta ajjiyeta awannan bangaren kafin wani lokaci tama yi saa bata taba bude fuskanta ba Sai ta bari IN zaai daukan sabin bayi ta fito a ciki ,.
Kallan sultana yayi saura inga kafarki a waje, yana kaiwa nan ya fice,, kallanta momy tai me Yasa kikai haka sultana yanzu gashi kina Cikin matsala, momy kiyi hakuri wlh rainane ya baci kuma itta ta jawo, Allah ya kare kawai momy tace,.
Sultan kuwa can gun ya koma bayan gu ya lafa ne Hindu take sanarwa Da yan gun Yadda akai, ran sarki ya kara baci ya kirasu kan cewa duk inda take suje su nemota,.
Taku har kuulun HAJARA MUHAMMAD FALALU
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 48*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Sanda ya koma angama abun Da ake Hindu ya dauka suka Kama hanya,.
Kallan shi Hindu tai ni bansan rashin San da kake munba har zai kai ka iya fada a bainar jama,a ni bansan Da mai sauran Yan mata suka finiba xancen gaskiya wlh banji dadi abun Da kaimun sosai kuma raina ya baci, tabe baki yayi ohooo Ashe ba dadi kika wa wata haka kodan itta baiwace, kwarai kuwa yarinyar ce akwai rainin hankali wlh duk randa akace an daura mana aure wlh zata gane bata Da mutun ci, tabe baki yayi ta fiki wlh saidai kusa kafar wando daya ,tsaki taja ni Yaya kodai kai ka kasakata taimun wannan rashin mutuncin wlh indai har kai kasa wlh nakan iya hakura Da auren nan naka KO kaine autan maza, dariya yayi kinga kuwa Da kin cika alkawarin Da kika daukarwa kanki Da nima kuma naji dadi, hawaye TQM Fara Ya tabbata Yaya sultan baya Santa itta kuwa KO shine dan gidan kyau duniya ya kamata ta hakura dashi bata kara cewa komaiba har suka isa, ko gama parking baiyiba ta kama hanya ta fice Da gudu,.
Da kallo ya bita kafin ya saki tsaki wlh yarinyar nan Na shiga Mai hanci Da kudundune ,tsaki yayi tare da ficewa ya nufi bangaren momy shi,.
Da sallama ya shiga sultana na mata tausa kamar ba abun dake damunta ,zama yayi akan kujera, sannu momy Na dawone Akan maganar, inaji momy ki gaya mata karta sake ta fita Dan wlh tana fita sunanta macacciya wlh kinsan dai wannan masarautar,hmmmm kawai momy tace,.
Momy bikinnan fa Sun dawo dashi wannan satin wai Dan kar wani abu ya faru wlh wai wannan jumaar gashi KO shiryawa bakiyi ba, murmushi tayi karka wani damu dama ran alhamis aunty ka Khadija zatazo Da kayan lefe Da nace ta hado acan kasan taje ummara zata dawo gobe kaga sai in kirata tazo jibi, mikewa tayi Bari in sanar Da yan uwu gobe zaka gansu akwai mairo kanwar fatima (Maman sultana )tace duk sanda bikinka yazo a gaiyace kaga itta zan Fara kira ta fada tare da mikewa ta fice,.
Kallan sultana yayi, Anan zakici gaba Da zama, shikenan ta fada ran daurin aure na Dade Hindu zaa sake daukan bayi zaki fito a ciki kema a hada dake sannan wani abu banda wannan rufe fuskan Da kika, to kawai tace Mai, yauwa waike dazu Da kikace so kike ta hakura Da aurena Da wa zakiban kinsan dai bazan iya auren kiba ni har na tsorata Ma kar kice taasa in soki, hade rai tayi kafin ta kalleshi ai nima ba iya auren naka zanyiba nasan kamun nisa balle ma ni ban taba jin sanka to da wannan dalili ne zaisa in ce tasa ka sona sai kace wacce nake tallan kaina, zaro ido yayi ni kike fadawa magana? Aa inranka ya baci kayi hakuri yau raina a bace yake karkaga ina fadan magana yadda na ga dama kace zakaji kayi hakuri, ta fada tare da juyar Da kai, kallan ta yayi lallai yarinyar nan Ta fara rainashi dole Ya bi a hankali fa, jijjaga kai yayi kawai,.
Da sallam momy Ta shigo kaga nasan Yan uwana AI gobe zasuzo sukace, murmushi kawai yayi ,kasan wadanda zasu zosaga masarautar mu fatima kowa yanzu mukai Waya Da aunty mairo duk sunce zasu zo ai, Allah ya kawo su lafiya, Ya fada tare da mikewa ni zan koma bangarena ya Mike ya fice,.
Hindu na shiga taci karo Da Mama, Da sauri ta rungume Mama, mama kinga abun Da Yaya sultan yaimun agun wannan Sa ranar ko wlh da hadin bakinshi duk wannan yarinyar tai mun wannan cin mutuncim mama yanzu taya zanyi in rama abun Da yai mun, dagowa mama tai ta zaunarta akan kujera,indai kina San da gaske ki rama abun Da yai miki dole kiji abun Da zan fada miki ke koda baki amince wlh mu mun amince nida Dady ki, zama tayi inaji mama,.
Yauwa dole ki hakura Da auren sultan, tabe baki Hindu tai taya dan na fasa aurenshi zan rama abun Da yai mun? Murmushi mama tai ai kaiki nake ba kinaji ba inasan ki nunawa jama,a kema fa ba sanshi kike ba karki wani nunamai kin fasa auren shi sai ranar auren zaiji kawai an fasa dashi yaji an daur Da wani kinga abun zai kuna Mai rai nasan zai nuna bacin ranshi kinga anan mutane zasu dauka shine yake sanki tunda har ya kasa boye bacin ranshi, to mama naji wannan kinsan fa ni bani Da Wanda nake so da wa zanyi wannan abun kuma ,murmushin jin dadi mama tai karki wani damu aidama mu badashi mukasa rana dazun ba Da, yarima Hashim dan gidan sarkin kano mukasa, saboda ya taba cewa yana sanki Dady yace sai yayi magana dake To kuma Da yaji GA wanda kike so shi Yasa bai karaa yin maganar ba,to jiya sarkin ya kira Dady ki kan maganar bainuna Mai cewa kina Da Wanda kike so saboda akwai alkunya tsakanin su, to da yaga abun Da ya faru sai ranshi ya baci shiyasa ya yanke wannan shaawarar yace in sanar dake kinsan dai yarima Hashim indai kyaune Da kudi ya taka wannan sultan din kuma kinsan masarautar kano ba daga nan ba,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 49*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Dan Allah Mama abun Da ya faru kenan yo ni inda nasan Da wannan maganar ai Da bazan biyewa wannan sultan dinba, kaii Amman naji dadin wannan maganar ba kadanta wlh sai sultan yayi kuka shima ,rumgumeta momy tai dama tana tunanin ta inda zata Fara tunkarar Hindu da wannam maganar sai gashi Allah ya kawo saukin abun,.
Hindu kuwa taji dadin haka dama tun abun Da ya faru taji bata San wannan sultan din kuma sannan zata cika alkawarin Data dauka KO ba komai,.
Da sallama Hafiz Ya shigo ,hararar Hindu yayi aina dauka dukad cin mutuncin nan da aka miki ba zaki hakura dashiba Da kuwa na canza kanwa, dariya tayi tare da rungumoshi, shima yayi dariyar,.
Zama yayi kusa Da Mama, mama nafa tambayo iyayen Zuwaira wlh akwai su Da san kudi ai in fada miki Da kudi Na siye Yan banxa so nake a hada auren da namu, tabe baki mama tai tunda ka dage ai ban da yanda zanyi, murmushi kawai yayi,.
1:00pm
Tana baccinta ta fara mafarki, Da sallama fatima fito mata a cikin mafarkin Nata tana miko Mata hannun wata yarinya Da bata ganin fuskanta sai gashin kan yarinyar dake kadawa iska na dagashi, kallan Fatima tai Yar uwa ban gane me kike nufiba fa? Halima gata na kawo miki itta Da kaina Dan Allah ki hadata Da wanda zai mata jagora zuwa inda take so bazata iyaba itta kadaiba ,Dan Allah Yar uwa Tana kaiwan nan Ta bace tabar yarinyar tana kuka tana kiran mamana,.
Da salati momy ta tashi, sultana dake daka kusa da itta tai saurin mikewa tare da riko hannunta lafiya me Ya faru momy? Kallan sultana tai, sultana mafarki nayi babban mafarki ta tsurawa sultana ido, ganin hakan Yasa sultana fadin mafarki kikai Sun kamani Sun kasheni KO karki wani damu momy inmates sun kasheni haka Allah yaso, aa sultana ba haka bane, gobe inasan yin magana dake, jijjaga kai sultana tai to momy, kallan momy tai ME yasa ba kije kin kwantaba zakiyi ciwon wuya fa, aa momy banasan tafiya in barkine, murmushi momy tai, OK zo ki kwanta anan ta fada tana nuna mata kusa da itta, aa momy wlh takuraki zanyi ta koma kan sofan dakin ta kwanta ba yadda momy ta iya dole ta hakura,.
Washe gari,
Abun mamaki sarki da wuri ya je fada, wanda Yasa aikin neman sultana nane zube a kasa zube, ba kowa an basu gu, ranka ya Dade wlh munyi duba Amman bamu ganta ba, taya zaai kuce baku ganta ba?kunsan lokacin dana dauka ina jiranta, a wanne gari take? Jigawa wani kauyen birnin kudu masaya, inasan kuje wannan kauyen ku dakkota in bata nan KO taho min da danginta nasan sunsan inda take, mikewa sukai tare da fadin angama ranka ya Dade (ALLAH SARKI KAWU)
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 50*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Yana gama sallamar su ya nufi dakin ajiya,.
Rai bace ya zauna kusa da abdulsalam, kallan abdulsalam din yayi, uhmmm yau da gani wannan yayan nawa yau ranshi a bace yake, kallan Abdullahi yayi wlh Ta gudu yauwa in tambayeka lokacin da kake harbi ai naga baka iya harbi da mashi shida KO? Gyara zama abdulsalam yayi kodai kun hadu da ittane? Juyar dakai Abdullahi yayi, a duk yadda akai kun gamu yooo banda abunka ai indai itta jina nace zata iya yin da gomama ai gado ne saika ni ban iyaba itta ta iya, in fada ma wani abu? Bazaka taba iya ganeta ba saboda kana cikin duhu Amman Kasa a ranka sarautar ka tazo karshe, idon shi yayi ja ya kalleshi aikuwa saidai mu kasa nida itta, kuma wlh a gabanka zan kasheta yana kaiwa nan ya mike Ya fice, abdulsalam ya bishi da kallo tare da jijjaga kaii,.
Zama sultana tai a kusa da momy, ina kwana momy,? Murmushi tai tare da shafa kanta kina lafiya? Qlau momy, momy jiya kince zakiyi magana dani wacce magana ce? Murmushi momy tai yanzu dai kaina ya dauki zafi zanyi baki yau saboda haka ki bari sai Bayan biki zA muyi magana, shikenan momy Amman zan taya su aikin ai, aa bakiji abun da sultan yace ba karki sake ki fita indai kuwa zaki fice tofa saidai ba zaki rufe fuska ba, shiru tai gaskiya itta ba zata iya fita haka ba Amman shikena zatai zamanta kawai,.
Da sallama Zuwaira ta shiga bangaren mama, a bakin kofa taci karo da Hafiz, Kasa tai Tana kwasar gaisuwa, murmushi yayi kije gida ana San ganinki, kallan shi tai saboda me kenan? Tabe baki yayi auren ki zanyi wannan jumaar kije ki shirya yana kaiwa nan ya fice da kallo ta bishi Yau Tana ganin karfin hali ana so dole NE? Tabe baki tayi ta shiga ciki abunta,.
2:00pm
Yan uwan momy suka Fara zuwa su aunty Huraira, aunty Ummi, Da aunty Zainab,cike da murna suka shiga bangaren yar uwar tasu ana ta murna nan aka fara shigo da kayan lefe, parlour cika yayi da bayi suna hidima,.
Sama momy tai ta Sami sultan dakko wasu kayan atamfa tayi ta mika mata ungoo ai bakyata zama a ke daya anan ba kisa wannan kayan nasan bamai ganeki, karba tai Tara da fadin to,.
Bayan Ta saka taje ta gaida baki sannan ta koma Daki, kallan momy Yan uwan Nata sukai wannan wacece kuma? Murmushi tai maganar babbace, to kawai sukace, bayan sun gama ganin kaya sukasa bayi dauka zuwa bangaren su hindu,.
Kallan kayan kawai mama take da murmushi a fuskarta kayan lefen ainihi suma suna nan take, kayan mama ta karba hannu bibbiyu kamar gaske sai murna take nunawa hakama Hindu tazo ta gaidsu kamar ba abun da suke shirin hadawa,.
Da sallama hindu ta shiga bangaren sultan yana dana system dinshi,takardar daukan hutu yake aikawa zuwa asibi,zama tai uhmmm yaya aiki kake? Eh ya fada yana murmushi zanyi aure ba dole inbar aiki in dauki hutuba, murnushi kawai tayi, lallai kam, gyara zana yayi Bayam ya gama abun da yake wai ni kuwa in tambayeki banga kina tambaya ta irin kudin su patty dadai sauran su, murmuahi ta Saki taya zaai in tambaya halhalin nasan ni kadai nake San auren ai ina da kudin yin duk wannan abun, wayece miki ke daya kike San auren ki daina fadan hakam, ledan kusa dashi ya dauko ya mika mata,karba tayi ta bude kayane dana mace dana namjiji, wannabe kayan fa? Su zamusa har a gama biki kayan kala bakwai ne, wowww ta fada Amman ka ajjiye agunka sai gobe zan zo in karba, . Bai kawo komaiba ya karba ya ajjiye,
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 51*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
3:00 Yan uwan fatima (mana sultana )suka karaso, tare da bayin su suke tafe abun abun ban sha,awa ,momy dake jiran zuwansu ta rumgume aunty mairo Tana fadin sannu da zuwa yar uwa, murmushi aunty mairo tai mun sameku lafiya?wlh lafiya qlau har kasa momy ta durkusa ta gaida mutumin dake tsaye shidai ba Za, a cemai tsohuba ba kuma zaa cemai magidanciba, Amman Sawa yayi da Fara,a a fuskan shi,yaudai Allah ya kawo mu auren sultan kinga da kanwar mu Tana nan da tuni yarta zai Aura, murmushi momy tai wlh haka Allah yaso, wlh Amman ai duk dayane da wacce zai Aura din,.
Sarki Dake zuwa inda suke ya karaso tare da mikewa sarki ibrahim hannu suka gaisa, barkan ku Da zuwa daurin auren yata gaskiya naji dadi ai atunani tunda wacce ta hada ta tafi shikenan zumuncin zai gudu, haba ai wannan Yan uwanta takene tun daga kakani kaga ai ba damar ruguzashi, hakane sarki ya fada sannan suka kama hanyar fada shida Ibrahim,momy kuma suka shiga ciki irta Da aunty mairo ,.
Haka suka zauna ana ta hira sultana na daga dayan dakin Da momy ta bata bata fitoba dan ba zata iya zama a cikin manyaba, hakan Yasa basu gamu Da aunty mairo ba,.
Da kyar Wanda sarki Yasa nemo sultana suka samu isa wannan kauyen,.
Bayan sun shiga kamar na Allah suka Sa akai musu iso zuwa gun sarkin gari, suka fada Mai sunzo neman Baban sultana nane, haka Yasa aka rakasu,.
Da sllama suka shiga Bayan sun gaisa suke sanar Mai cewa daga masarauta akace su tafi tafi dashi ,shiru kawu yayi yana tunani danshi a iya saninshi jiyama sunyi saya Amn bata cemai zaa zo daukan shiba, ganin yana San bata musu lokaci suka shaka Mai powder suka tafi dashi,.
11:00pm suka koma suka kira sarkin suna sanar dashi yace su ajjiye shi a wani gun gobe zasu hadu,.
Washe gari masarautar ta Tashi Da shiri Dan yaune daurin aure,sosai momy tai shirim biki ba abun Da batai ba, haka koma mama Ma ta gama shrinta hakama sultan kawai ya cintsi kanshi Da murnar bikin,.
Masallacin cike yake sosai da mutane kowa ya taru kawai jiran ayi sallah a daur aure suke,.
So sarki Abdullahi Da kuma sarki Ibrahim Sun karasa zuwa sai daga baya tawagar su yarima Hashim ta karaso,sarayi iya saurayi Amman duk kyanshi baikai sultan ba,dai dai zuwansu sultan ya karaso sukai musabaha sannan suka karasa cikin masallaci akai sallah bayan an idarne kafin a Fara daurin aure sarki ke sanarwa cewa anfasa daura aure Da sultan an koma kan Hashim saboda itta yarinya tace bata sanshi ga Wanda take so, mutuwar zaune sultan yayi, ran sarki ibrahim kuwa ya baci.
Fita yayi ya kira momy Ya labarta mata komai ranta ya baci wato shiyasa su dawo Da kayan lefen sukace wai a ajjiye agun, a hankali ta fara magana yanzu kasan yadda zaaii tunda dai har na shirya auren shi bazan fasa ba Dan Allah kace dama shima ya fasa auren tun Da can saboda ka bashi yarka kuma ya nuna yana so inyaso ka daura Da sultana, sultana wace itta kuma, Dan kawu kayi yadda nace zamuyi magana daga baya, tana kaiwa nan ta kashe wayan, su aunty Huraira ke tambayarta lafiya, ina xuwa kawai tace tayi sama zuwa dakin Da sultana take,.
Bayan an gama daurin auren hindu sarki Ibrahim shima yace zaai na sultan saboda shima ya fasa auren Hindu, nan suka bada kudin Da sukaxo dashi a matsayin na Hindu aka maidashi na sultan nan aka daura auren SULTAN MUBARAK DA SULTANA IBRAHIM akan zinare goma, Ibrahim yayi amfani Da sunan shi a matsayin uba dan baisan na sultana ba,.
Sultan muwa mutuwar zaune yayi a ina kawu yasan sultana?
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 52*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Tsayawa momy tai a bakin kofan shiga dakin sultana Tana tunanin ta ina zata Fara sanar Da sultana abun Da tayi, hawayen fuskarta ta goge bata Da yadda zatai daya wuce hakan in batai hakan ba yaya zatayi Da yan uwa Da abokan arziki tada gaiyata, Amman tunaninta daya kardai sultana taki amince Da hakan, yanzu ya zatai,?
Jin An bude kofa Yasa ta kalli gun tare da saurin goge hawayen fuskarta, kallan ta sultana tai momy meke damunki kamar kina cikin damuwa, shiru momy tai Ya zama dole ta fada mata tunda ta riga tayi aikin gabanta, murmushin yake ta saki kafin ta riko haannun sultana sukai cikin dakin, zama sukai a bakin gado so take kawai taji me zai fito daga bakin momy,.
A hankali ta Fara magana, plz sultana nasan na miki shishiji a rayuwar ki Amman Dan Allah kiyi hakuri, taimako na zakiyi, Da sauri sultana tai riko hannunta, momy maye hakn har kike neman abu a guna kina roko na Da Allah haba momy AI kamar uwa kike a guna, murmushin jin dadi momy tai Amman duk Da haka zuciyar ta a karaye take,.
Sultana yaune Da akaje daurin auren sultan bayan an taru zaa daura sarki baban Hindu yace yarshi ta fasa auren wai zata auri yaron sarkin kano, sultana bansan abun Da Abdullahi zai munba kenan ya kunyata yarona a gaban jama,a sultana Abdullahi yaci mutuncina kiga abun Da ya aikata mun kamar na Allah haka ya fito min har Hindu da mahaifiyarta sun gama dani sultana,.
Gogewa momy hawaye tai momy kuma haka kika bari haba momy bai kamata ki bar yaronki ya kunyata ba, ni naji yanzu ki kira kice a daura dani nadaukar miki alkawarin share miki hawaye kamar yadda kike so, kawai a daura dani duk sanda sultan ya sami wacce yake so saiya sakeni ya aureta taimakone zan miki momy karki wani damu,.
Dariya hade Da hawaye momy ta saki sultana na gudu sosai nadauka bazaki fahince niba, wlh kafin inzo nan saida nasa aka daura miki auren Da sultan da na dauka ba zaki amince ba Ashe nai miki kallan wani gun ,rumgumeta sultana tai Tana hawaye tasan sultan ba Santa yake ba Amman kawai Dan momy zatai hakan,.
Momy ki daina kuka ai kin isa dani ne kamar uwafa kike a guna Dan kin yanke hukunci akan yarki aiba wani abu bane, murnushi momy ta saki insha Allah wannan auren naku har abadane, murmushi kawai sultana tai tasan abun da wuya ballema ba San sultan take ba hakama shi Ma ba santa yake ba,.
Dagowa momy tai akwai kayan Da sultan ya kawo min kan cewa in hindu tazo in bata Amman yanzu kinga ke zanba sannan kayan lefan Ma sun dawo dashi kinga shima naki, kallan mother take Tana magana Tana hawaye, share mata hawaye sultana tai ki daina kuka mana momy kina karyan zuciya fa, dariya momy tai don't mind me kawai kukan murna ne,.
Turo kofan dakin aunty mairo tai hakan yasa suka kalli kofan ,zaro ido sultana tai Dan tabbas suna kama Da matar sannan kuma suna kama Da waccw take mafarki Da itta, kallan sultana aunty mairo tai kafin ta kalli sultana, Tana kallan sultana take fadin aunty halima wannan wace Mai Kama Dani kodai Yar Fatima bata mutuba?
Riko hannun aunty mairo momy tai kafin ta zaunar Da itta, Sister kinganta so nake ki fadawa Yan uwana cewa kece mamanta dama ta dade Da zuwa nan, nan Ta sanarwa Da aunty mairo abin Da ya faru ittama ranta ya baci, Kallan sultana tai keko danginmuce naga kina kama Da danjin mu? Shiru sultana tai batace komaiba tama rasa ta ina zata fara,.
Kallan ta momy tai yauwa sultana zamuyi maganar Da nace muyi dake Yau, jiyane nayi mafarki Da Fatima Tana miko min hannu wata kinga yadda kike shiga wlh haka yarinyar take shine nake tunanin KO kece,uhmmm momy uhmm bafa ni bace ta fada Tana inda inda, riko hannunta momy tai yanzu fa kika gama fadin maman kice ai bai kamata Ya tana boyewaa uwa sirrin ta ba, kallan momy sultana tai Tana hawaye, momy nifa Da zanzo saida wacce nake gani a mafarki tace karna fadawa kowa, riko hannunta momy tai wace kike mafarkin Da itta ya take taimakon ki zanyi sultana itta wacce kike mafarkimce tace in taimakeki,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 53*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Da gaske ta fada Tana kallan momy, daga mata kai momy tai, kallan aunty mairo tai da wannam take kama Amman ta fita haske Da kyau, murmushi aunty Maori tai tabbas Da Fatima sultana take mafarki, riko hannunta momy tai, kin tabbatar Wanda kike gunshi shine baban ki? Daga kai tayi alamar aa ya fada mun cewa a hannun wata mata Ya ganni, kawai dai Ta fada Mai cewa ni Yar sarkice, rumgumeta momy tai tabbas wannan yarinyar Fatima ce ni tun ba yauba nake zargin haka, rikota aunty mairo tai to meya kawoki wannan masarautar,? Itta tace mum inzo in taimaki mahaifina yana nan,.
Murmushi aunty Mairo tai shikena Allah ya bada saa Amman babanki ya dade Da mutuwa karki wani daga hankalin ki kinga ni kanwar Maman kice saboda yanzu na zama mamanki, ta fada tare da rumgumeta sultana, mikewa momy tai ta fice ta Sanar Da yan uwanta komai Amman aunty mairo tasa an daura Da yarta sosai ransu ya baci kuma suma sai sun batawa su mama rai baa tabasu a zauna lafiya ,..
sultan kuwa ansan gaisuwa yake kawai kawai yanzu abun Da yake so bai wuce yaji Da wacce sultana aka daura Mai aure, kusa Da kawo yaje, dake ta amsa gaisuwa, hakama sarki Abdullahi bai kawo komai ba Dan bai kawo cewa wannan sultana bace,.
Kusa Da kawu ya matsa, kawu wai wacce sultana aka daura min auren Da itta? Oho nima ina na sani mamankace tasa gabanshi yaji ya fadi, message ne ya shigo Mai waya hakan Yasa Ya koma gefe .
Hindu ce
Slm ina fatan hakan bai baka haushiba kana tunanin zaka wulakantani ne sannan in hakura haba wlh kayi kadan kaima kanka kasan a masarautar mu kake, MASARAUTAR MUCE dole kabi umarni dukda naji an daura Ma da wata Amman ni ina Da tabbas Bakasan wace ba wai sultana waccan dai sultana da kake so ta tafi kuma ansa a nemota dole ta mutu sakamakon cin mutuncina datai,.daga haka nake maka bissalam,.
Kallan wayar yayi tabbas ranshi ya baci, Hindu ta gama dashi,.
Reply yai mata
Na gode miki sosai da kika fasa aurena kema kinsan bana sanki kuma bazan taba ta wlh wannan babban kyauta kika mun Da kika Sa Na auri Yar uwata wacce na Dade ina so na kasa fada mata, ina miki rokan Allah ya bada zaman lafiya saboda ke sister tace,.
Bissalm
Guga motanshi yayi ranshi yau ya baci Hindu ta bashi kunya, Hafiz ne daga baya ke fadin take it easy nina haka komai, juyawa sultan yayi ya bashi Waya harara kafin ya shiga mota yaja,
Aunty mairo tasa aka kira Mai kwalliya kan cewa zataiwa yarta mijinta yau zai fara ganinta yaci ace ya ganta kamar angle,.
*plz sister kuyi manage da wannan wlh am sick karma ku wayi gari kuji ance na mutu abun ya baku mamaki all I need is your prayers Dan wlh ina jin jiki sosai karfa kuce wasa*
Wishing you happy sallah fans ALLAH ya maimata mana ameen
Taku har kullun hajara Muhammad Falalu
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 54*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Parking sultan yayi a farfajiyar masarautar, kafin ya fito sai gaidashi ake ana tayashi murna yake kawai yake, bangaren momy shi ya nufa direct, parlour farko bayine ke aikin su hakan Yasa yai sama suna gaidashi baima amsaba, Da sallama ya shiga parlour indaa su aunty Huraira ke zauna, suna ganin shi suka kara sakin murmushi kaga ango, murnushin yake yayi kafin yace ina momy, aunty Ummi ce ta karba gani, murmushin shaguba ya saki plz little MOm ina mom take magana za muyi,tabe baki tayi inkai dani ai duk dayane bakaga muna kama ba ta fada Tana murmushi, shima murmushin yayi tare da yin sama zuwa dakin mom dinshi,.
Da sallama ya shiga Tana zaune a bakin gado Tana duba kayan Da Ya kawo mata zata zabarwa sultana Wanda zata Sa in zasuje walima,daga kai Tana kallanshi Da sauri ya karasa gunta yama rasa ta ina zai fara, ganin Ya kasa magana yasa ta Tashi zaunar dashi, menene fadi inji, riko hannunta yayi mom kinji abun Da hindu tai mun tsabar wulakanci tasan ta fasa auren bata fada munba, murmushi ta Saki tawa kanta dai tunda gashi kaima na baka mata, kara hade rai yayi mom wai sultana kika Aura min wlh bana santa itta ittace miki Tana sona? Aa ittama bata sanka ba itta ta fada sandama nasa aka daura muku aure batasan anyiba saidaga baya nai mata bayani dake itta Mai fahintace ba kamar kaiba Ta fahimta sannan tace duk sanda ka sami wacce ka ke sai ka bata takardarta, ta fada tare da uci gaba Da abun Da take .
Da sauri ya riko hannunta Mom kardai kice mun haushi kika ji? Kallan shi tai ba dole inji haushiba yarinyar ta taimakeka Amman ka nuna ko in kula ai kamata yayi kaima godiya Amman wai kawai daga zuwa ka fara sanarmun kaifa ba santa kake ba yanzu inda baa daurama zakaji dadi ka gaiyato abokanan ka aji ba dakai aka dauraba zakaji dadi ace Maman tayi shiri duk ya tashi a banza ittamafa ba sanka take ba, OK naji mom kiyi hakuri insha Allah zan mata godiya, murmushi yayi kafin ya Mike ni zan wuce zansa a kara gun walimar kinsan mun zama mu hudu kenan, murmushi kawai tayi ya mike Ya fice,hmmm banjin sultan ya taba ganin sultana that why Amman nasan wannan auren gaske ne ,yana fitowa dai dai lokacin aunty mairo ta fito kenan, kasa yayi yana gaidata dan saiyau yasan tazo,.
Amsawa tayi sai kuma kaji Allah yasa hakan shiyafi alkhari kuma Allah ya bada zaman lafiya sannan. A kular mum da yata, murmushi yayi wai su duk yarsuce sultana dinnan, ko zaka gantane? Aa mom zamu hadu agun walima, Ya fada tare da mata sallama ya wuce,.
Tana fita ya kira doctor habib kan zancen gun walima, aboki Amman wai me yasa kaki auren Hindu ne? Aboki maganar babbace sai mun hadu Da haka sukai sallama,.
Mama kinji wai shima sultan din anbashi wata wai sultana yar uwar wannan matar sarki Da kike ban labari, oho dai aike dai kin rama auren huce takaicine ki shirya kinsan yanzu zasuzo ku tafi walimar
Sultana da ake mata kwalliya ta kallli sister ANA Amman sister wannan kwalliyan batai yawaba? Dariya ANA tai ina abun yawa anan keda zakije gaban angonki ai inda wacce tafi wannama yaci in miki kuma light makeup nai miki kinsan wannan kwalliyar Mai yawa bata cika kyauba? Gaskiyane Amman wannan dinma ina laifin asa huda sai lipstick shikenan, look at you bakinki kamar na lipstick din ni kawo in miki dauri ta fada tana murmushi,ittama dai murmushi din,.
Da sallama su Zuwaira suka shigo, sakin baki sukai suna kallan sultana wacce tai murmushi tare da fadin ku zauna mana ,za sukai Bayan ANA ta gama ta fice ta basu gu ,.
Karasawa kusa dasu tai, kallan Zulai tai anya wannan sultana dana sani ce? Harararta tayi keni bana San iskanci magana zamuyi kunga dai ni bani Da kawaye sai ku kuma bansan abun ya zaiyi ace naje ba kawaye, amman nasan ya zanyi ta mike Ta dakko wasu kaya ta mika musu kuyi amfani Da wannan za kuga yadda zanyi in anje can kunji, karba sukai OK kice zamuga drama,murmushi kawai tayi,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 55*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Su sultan da habib ke tsaye a bakin mota, kallan shi habib yayi waikai aboki ba zakaje kace munzo bane? Kai inafa ina shiga waddan tsofin zasu Fara damuna kawai bari in kira momy, Ya dakko Waya ya kirata Bayan sunyi magana yace gasunan suna jiran fitowar su, to tace tare da kashe wayan,.
Suna tsaye motocin su Yarima Hashim sukai parking, Bayan an bude Mai Ya fito har wajen su sultan yaje suka gaisa ya tayashi murna shima haka sannan shima ya kira Hindu kan cewa Sun karaso,.
Da sallama MOm ta shiga dakin sultana da suke zauna itta Da aunty mairo murmushi Tai sai a tashi ai angwaye Sun zo, sosai gaban sultana ya fadi, mikewa aunty mairo tai ki Sa wannan alkabbar bari IN kira bayin Da zasu take miki baya kinsan Da tamu masarautar zakiyi aiki, ta fada tare da ficewa, duk sultana sai taji wani iri itta zaa take wa baya yau wai itta, mikewa tai taje gaban madubi, kallan kanta tai tabbas ittama tasan tayi kyau Amman abun mamaki wai yau ittace rana TQM farko Da sultan zai Fara ganin fuskarta banda waccan ranar koyama zai kalleta, yace bana sanki kinmun shishigi nace ki aminci Da aurena ne, tabe baki tai inya fadan haka nima sai ince aiba sanka nake ba tsaki taja ganin tana Ta surutai itta daya ,.
Alkarbar tasa Ta jawota har wajen idonta sannan ta zauna, aunty mairo Ta shigo tashi muje kinsan ni zan kaiki mota kafin muma mu karaso, mikewa sultana tai suna tafe itta Da aunty mairo Yan uwan momy tabarakallah suke, haka suka fito harabar masarautar, inda bayi hudu mata ke take masu baya, dai dai lokacin su Hindu Ma suka fito Da Yan uwan mama suna Ta guda abun suna fadin ya tayi farin kashi dama kyau Yar sarki sai Dan sarki,.
Sultan dake cikin mota yana kallan fitowar su shidai baiga face dinta ba Amman Allah yake roko Alla yasa tana Da kyau kar tasa abokan suna Mai dariya, dai dai motan suka tsaya Da sauri habib ya karaso, Ya gaida mom hakan Yasa sultan fitowa shima ya gaidata,.
Habib ne yaci gaba amarya ina kwayen? Kinfa San ni zan dauke su, murmushi tai nibanda kawaye anan Amman na maka alkarin muna zuwa zan maka kawaye, dariya habib yayi to ai shikenan Allah ya kaimu, ta amsa da ameen, murmushi sultan yayi kafin ya shiga mota hakama sultana ta shiga Ta zauna aunty mairo Ta rufe musu kofa,.
Su Hindu ma suka shiga kafin aka kama hanya
Tafiya suke ba Wanda yake magana sultana ma wasanta take da awarwaron hannunta, a hankali ya rage karatun dake Tashi a motan,sannan ya fara nagode Da taimako, basai ka godeba nima kamun abun da yafi haka so no need kawai nayi hakanne dan nafitar Da kai kunya, murmushi yayi, thanks amma kinsan dai yadda auren ya kasance gaba dayanmu ba...... Bai karasaba Ta karba basan junan mu mukeba ninasan Da hakan sannan duk sanda ka Sami wacce kake so kana iya ban takardata Amman fa wannabe drama karta wuce one year saboda nima ina bukatar change dina kuma Da aurena bazanje ina abun dabai daceba duk auren is like kamar ba aure bane, OK nagi dadi Da kika gane Annmarie fa kiyi hankali Da zuciyar ki karkije ki fada sona danni nasan baxan fada nakiba, murmushi auren Da ba so ME kuma zai kawo so karka wani damu Da wannan, kallan ta yayi zaiso ganin fuskar wannan mai surutun, hakan Yasa ba tsammani sai sultana ji tayi an bude glass din side dinta, iska Ta danno kai hakan Yasa alkarbar data saka akai Ta fadi bayanta Da sauri tasa hannu Tana kare iskar dan Ta mata yawa ,Da sauri ya rufe glass din kamar wannan fuskar ittace ya taba gani tace Mai wai kawar Hindu ce, a dan zuceye sultana ta juya Tana kallan shi haba ranka ya Dade aisaikace mun zaka bude IN shirya,. Kallan ta yake sosai a ranshi yana fadin ittave wlh, dama sultana ce
Thanks sisters for your prayers wlh naji sauki ban mutuba hhhhh thank
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 56*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Ganin yana kallanta yasa ta dauke kai Tana gyara mayafin tare da fadin kadai kalli gabanka karkasa mu yi accident,juyar dakai yayi yana kallan tukinshi, Amman tunani yake wai dama sultana ce wadda suka hadu dinnan to Amman ya akaima bai taba ganin fuskarta ba, ina kuwa zaka gani Bayan kullun fuska a rufe take, tsaki yaja Wanda ya fito,to maye nashi na damuwa tunda ba santa nakeba ya fada a zuciya tare da jan tsaki, kallan shi tai ranka ya Dade lafiya? Baice komaiba kuma bashi Da niyar cewa komai din, hakan yasa tai shiru,. Haka ba Wanda ya sake magana har suka isa,.
Parking yayi yana parking bayin dake binsu a baya sukai saurin bude musu kofa, hakan Yasa sultana gyara alkabbar Ta a tare suka fito, kusa Da itta Sultan ya dawo Dan ba zasu shiga hall dinba har sai anjira iyaye sun shigo, kallan sultan tayi dolefa zan Ma Yaya habib kawaye kuma acan zanyi mashi, Kalb gun yayi sai kuma ya saki murmushi dole kiyi mishi agun mana tunda kema baiwar ce, murmushi ittama tayi na Sani ai, dai dai lokacin su Hindu suka karaso, Da sauri bayi suka tsaya abakin kofar tasu, sannan aka shinfida wani carfet a both side a tare suka fito,, yadda Hindu keji dakai Yasa sultana sakin murmushi kafin kalli sultan mutuniyar taka fa sarautar ce yau Ta motsa, ohhh KO kema zaki gwadane? Innace zan gwada saina taka Ta ai wannan ba komai take ba, zaro ido yayi Da gaske, daga mai gira kawai tayi, ganin su Zuwaira Sun karaso yasa ta kalleshi ina zuwa yanzu zanje inwa yaya habib kawaye, tabe baki yayi kawai, ganin Tana shirin tafiya yasa bayin karasowa gunta, wacce ke kusa Da itta tai saurin yin kasa ranki ya Dade aikinmune kare ki baikama Ta ace kina tafiya wani gun bamu ba, murmushi sultana tai OK zanje canne Ta nuna gun su Hindu zaku iya biyuni, mikewa sukai tana tafiya suna bin bayansu Bari in nunawa wannam ba abun data iya, ganin Tana nufo inda suke yasa Hindu hade rai itta Da kawayenta dake taya Ta karbar gift, Da sallama sultana ta karasa gunta hade Da murmushi, amsawa himdu tai kamar bata so, sultana zata Fara magana kenan waccan tai saurin tarar nunfashinta ranki ya dade zan mata bayani kinsan bamusan kina bata bakinki Amman kiyi hakuri in ranki ya baci, murmushi sultana ta saki karki damu ai Yar uwatace wannan no need kice zakiyi magana Da itta,.
Sakin baki Hindu da kawayenta sukai Yau suna ganin abu, sultana ce Ta katse sunana sultana mata ga sultan kuma yar uwa nasan baki sanniba Amman yanzu ai mun xama daya, murmushin takaici Hindu tai tare da mika mata hannu Tana fadin you are welcome, ganin sultana bata mika hannunba yasa baiwar kusa Da itta Ta mika, dasauri Hindu ta janye hannuta, kafin Ta kalli sultana ranta ya fara baci kuma, wannan wacce irin baiwace dake Da har zata hada hannu dani itta wace? Ohhhhh Yi hakuri Na sabane bai kamata ace Na bari Ta miki haka duk inda zani tare muke zuwa Da itta so irin su wadannan gaishe gaishen duk itta take amsa mun plz kiyi mata afuwa laifi nane, kallan baiwar Hindu kisan a inda kike bamasan shashanci, cike Da girmamawa baiwar Ta bata hakuri,
Dama so nake zanyi kawaye a cikin wannan mutanen naki plz in bazaki damuba, kallan gun Hindu tai kafin Ta Saki dariya haka itta kawayenta saida sukai abunsu kafin Hindu ta kalleta kice mulkin naku ba komai bane tunda har kuna kawance Da bayi lallai baku Da aji indai wanne na baku dama, murmushi shirin bada magana sultana tai, ai wannan ba nuna mulki bane a KO wacce masarauta baka Da kawayen daya wuce bayi to maye danna inasan yin kawaye anan sannan kuma a masarutar akwai mutunta mutun masarautar mu Ta daban ce sannan na gode Da bani dama, ta fada tare da yin gaba Hindu ta bita Da ido,.
Gun su Zuwaira sultana taje sannan ta fada musu yadda sukai aikuwa sunsha dariya,.
Sultan dake kallan su shi mamakin sultana yake kamar Yar mulki in tana wani abun shidai kawai binta yake Da ido,.
Bayan iyaye Sun iso aka shiga hall dan gudanar Da walima
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 57*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Bayan an zauna aka Fara gudanar Da walimar inda aka nemi kawayen amarya suzo su bude taro da addua ganin ba Wanda ya Tashi Yasa Zuwaira taje Ta bude taro da addua sannan ta koma Ta zauna aka nemi cewa amare zasu Yi karatun Al Quran, Hindu CE Ta Fara zuwa tayi fatiha Da falaqi Da nasi, akai mata kabbara sannan sultana taje Ta Bayan Ta karatun fatiha sannan ta daura Da suratul baqra, ittama akai mata kabbara nan dai walima taci gaba akaiwa amare nasiha sosai game da rayuwar aure Da abun Da ya dace suyiwa mazajen su sannan aka rufe taro ko wanne ango ya dauki amaryar shi suka Kama hanya,tun a mota sultana ke kwada wayar kawu Amman bata shiga, kallan wayar tayi kafin taja tsaki wayan taki shiga, kallan ta sultan yayi wayar waye?kawu mana Ta fada Tana shirin yin kuka, murmushi yayi Maybe baida charge nasan wannan kauyen naku ai ba wuta kuke samuba,hmmmmm kawai tace taci gaba Da trying, yana parking Ta bude Ta five ,.
Da sallama Ta shiga, taro Ta mom tayi ya akayi ya walimar ina su aunty mairo? Suna anya mom walima tayi dai dai, OK kije ki yi wanka sannan kiyi shirin sallar magriba, to tace sannan tai sama saida Ta sake trying bai shiga sannan ta ajjiye Ta shiga toilet tayi wanka sannan ta fito lokacin sallah yayi tai sallah,da sallama aunty mairo Ta shigo, Da abunci a hannunta tashi sultana tai ta karba Ta ajjye sannan ta koma Ta zauna, kallan ta aunty mairo tai sultana meye naga duk kamar kina cikin damuwa,kalln aunty mairo tai aunty kawu nake Ta kiran number dinshi Amman yaki shiga kuma bai taba mun hakaba, ohhhh inajin baida charge ne, aa aunty ba zaace baida charge ba nasan yawancin lokacin Da baida charge, ta fada da Dan damuwa, riko kafadarta aunty mairo tai karki damu yana lafiya,..
Shiru tai Tana tunani sanda sultan yacewa mom gatana taje tasa rayuwarta a Cikin matsala, Mai yake nufi Da hakan kodai sarkine Yasa a kasheta shiyasa sultan ya yanke wannan hukuncin indai hakane kuwa sarki zaisa duk inda take aje anemota, Amman ina tana San tayi magana Da sultan yanzu kuwa, kallan aunty mairo tai aunty ankaiwa sultan abincin shi kuwa?kallan Ta aunty mairo Tai saikuma Ta Saki murmushi baa kaimaiba dama yace akai mishi Amman kuma Da bake zance ki kaimai ba, no aunty ki kawo in kaimai, taya zaai in Baki alhalin kinsan baa fiya fita da daddere a wannan masarautar ba, plz aunty zan dawo Da wuri in dare yayi sai in kwana acan..... Bata karasana tai saurin rufe baki tare dajin wata kunya, murmushi aunty mairo tai tun kafin a kaiki ai ba matsala tunda am daura zo muje ki karba, Da sauri Ta riko hannun aunty mairo wlh ba haka bane Allah abu zan tambayeshi nida ban sami kawoba duk hankalina ya tashi shiyasa Allah ba komai bane Allah ba abu Da zai faru, tabe baki aunty mairo tai kuka Sani ni ina ruwana zo muje taja hannunta sukai parlour,.
Kitchen sukaje Ta hada mata kayan abincin duk sai yanzu sultana taji kunyar kanta Ma, kallan aunty mairo tai aunty Na fasa gobe zakuyi magana Ma kawai, aikuwa baki isaba wlh sai kinje haka momy tazo Ta samesu take tambayar lafiya, aunty mairo tace abinci zata kaiwa mijinta, nan momy tace ina bata yadda ba Amman aunty nairo Ta dage, da kyar mom ta yadda duk Da tasan ba wani abun dazai faru kawai dai tasan sultana komai dare zatace zata dawone, badan tasoba haka sultana ta tafi ittadai burinta bai wuce taji lafiyar kawunta ba ,.
Da sallama sultana tai shiga bangaren nashi, ba kowa a parlour a hakan yasa ta ajjiye abuncin Ta shiga dakin ba kowa shima, nan Ta tabbatar yana masallaci, zama tai a bakin gadon sannan ta bude drower Ta dakko waddan hutanan ranar Tana kallo ,hutan mamanta take kallah sai hawaye, mikewa tai ta koma wajen window Tana kallan waje Da hutan a hannunta, ,.
Sultan Yana shigowa ganin abinci Yasar Yai sama sai yayi wanka Yana shiga ya hangota a wajen window Tana tsaye ,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 58*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Ganin Tana ciki yasa yai sallama Amman shiri bata amsaba,tunanin me take Ya fada tare da karasawa ciki, kusa Da itta ya tsaya kwata kwata batasan Da tsayuwarshi a gunba, uhmmm yai gyaran murna Da sauri Ta Kalli side din nashi sai kuma tadan ja baya tare da buye hutan a bayan Ta, kallan ta yayi shi baima lura Da hutanba Amman ganin Tana buye buye yasan bata Da gaskiya,me kike dauka mun Da gani baki Da gaskiya, uhmm uhm ba komai ni kawai abinci na kawo maka sannan za muyi magana ne, holding arms yayi kinsan me kwata kwata baki iya karya ba indai zakiyi kindinga kame kame kenan baki tsayawa gu daya, bafa karya nake Allah, eh nasan ba karya kike ba ki fada mun Me kika dauka kike buyewa, tabe baki tayi tare da mika Mai hutan, bai karba ya Kalli hotan, ashe kema kinsan kuna kama Da itta kenan? Karban hutan yayi ittace aunty inasan santa sosai mijinta shine sarkin mu a da Amman sai kuma lokacin Data haifar mun matar Da naso in Aura Ta rasu itta Da Yar Da sarkin sakamakon accident din mota, kallan shi wacce Ta haifa Da kaso ka Aura? Eh mana KO kina kishine, murmushi tai tare da shirin barin gun yai saurin riko hannunta, jin wani shock yasa yai saurin sakinta itta tai saurin janye hannun nata, ban gama magana dake ba ai tukun, eh a parlour zan jiraka sannan kayi saurin dan tafiya nake San inyi, Tana kaiwa nan tai gaba, murmushi yayi tare da shigewa toilet ,.
A Parlour ta jirashi har ya fito saida yaci abinci sannan ya zo yaji maganar Da take San ta tambaye shi, gani nazo fada mun abu Da ke tafe dake, gyra zama tai Yaya sultan sanda kazo kasa na rubuta wasika ga Hindu a wannan gun me dalilinka na Sani hakan? OK yanzu dai tuciyene zakiyi sai na fada miki kenan dan kin samu na ceceki KO? Plz wlh ba haka bane Allah hankalina bai kwanta Da kawu wlh jikina naban wani abun na faruwa dashi, kallan ta yayi OK sarkine yasa aje a nemomai ke, zaro ido tai a nemoni KO kuma basu ganni ba wlh nasan tunda basu ganniba cewa zaiyi aje garinmu a taho Mai Da wani nawa shine zasu dakko kawu,dan Allah yaya sultan ka bari inje in sami sarki ince mai Nice bana San wani abun ya sami kawu na wlh, ganin duk Ta rikemai yasa Ya riko kafadarta, ke ki tsaya baki Da hankaline kinsan waye sarkin nan kuwa? Eh na sani shi makashine mai kashewa yana sawa ana kashewa meye ban sani ba wlh Daya taba lafiyar kawu gara ya kasheni....... Squad sauri ya rufe mata baki,baki Da hankali ya kasheki inya kashe ki mutane nawane zasuyi asara, ina nufin kinsan momy ba zata ji dadi ba Aunty mairo yadda naga Tana wani janki a jiki ance miki Bari zatai kumama baki Da tabbas ya kamo kawun nakine KO aa Amman duk kinbi kin daddage, to wlh Bari in fada miki kikace zakisa ranki a cikin mutuwa niba ruwana, cire hannunshi tai daga bakin Ta, eh ni naji gara inje in fada Mai koma maye ya faru kuma yanzu zanje, ta fada tare da mikewa, kallan ta yayi wlh in kika fita a daga parlour nan zan saba miki sultana, ko kallan shi bataiba itta a dole fita zatai ganin Da gaske take yasa yai saurin mikewa tare da rikota Ta baya ke me yasa bakijin magana ne Bari in kira momy in fada mata, ganin Tana san kwacew yasa kawai ya rufe kofan Tare da cire key din, Ya koma ya zauna, ittama zatai a bakin kofan kuka kawai take wai zai kashe mata kawo kawai ya bari taje Ta fada Mai gaskiya,.
Momy Ya kira ya fada mata yadda sukai Da sultana, sosai hankalinta ya tashi tace karya Bari Ta fice Ma, gobe Za suyi magana, Da haka sukai sallama, .
TV ya kunna yabarta zaune abakin kofa Ta hada kai Da gwiwa Tana kuka, kallan sultan tayi yanzu hakama Da hadin bakinka a komai, murmushi yayi baice mata komai ba, mikewa tayi kazo ka bude mun kofa zan tafi bangaren mu, kallan ta yayi nanma bangaren mijinkine kiyi kwananki anan bamaiyin gulmar ki ai, Dan Allah kazo ka budemun ni IN tafi, kallan agogo yai kinsan karfe nawa yanzu, 11:00 ki tashi kije ki Kwanta dan nima tafiya zanyi ya fada tare da mikewa yana kashe TV din,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 59*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Har ya gama kashe TV bata motsa bama, kallan ta yayi KO so kike inzo in dauke ki kinsan ku amare haka kuke baki Da matsala sai in daukeki in kaiki din, tsaki taja bari Ma in fada maka wannan auren aiba aure bane saboda haka karka Ma bari jikinka ya taba nawa barinma yanzu dana gano cewa Da hadin bakinka a komai, dariya abun ya bashi aikuwa ya dara, zan kashe wuta kizo ki wuce, ba inda zanje a bangaren momy zan kwana ni, murnushi yayi tare da wucewa switch Ya kashe wuta,nan take parlour Ya koma duhu, kallan parlour sultana tai yayi duhu sai yanzu kuma Ta fara jin tsoro tsaki taja tare da Fara lalube Tana neman hanyar stair din, jin Ta taba abu yasa ta fara shafawa har fuskar sultan, jin shine yasa tai saurin dauke hannunta tare da fadin sorry Da ME ya kawoka kusa dani plz ka kunna mana wuta, rikota yayi tare da fadin daukarki zanyi bake kika fada kinfisan in daukekiba kuma Ma aike kika zo bangarennnan amarya Mara kunya wacce ba zata bari akaita dakin mijinta taba tazo Da kanta, tsaki taja Tare da fisge hannunta zata juya yai saurin rikota tare da daukarta, wannama ai iskancine nace bana so ana dole ne, baice mata komaiva har saida yakaita dakin Data saba zama indai ya cutota Da daddere sannan ya direta, tsaki taja Ta kalleshi ya wani hade rai,kallan dakin tayi an gyarashi sosai an sake kayan dakin komai da komai yayi kyau sosai, kujeran madubi yaja ya zauna tare da fadin zauna zamuyi magana ganin Ya hade rai Yasa taji wani iri, zama tai,.
Sarki dake fada a zaune yana shirin tafiya makwancin shi ya kira Wanda yasa aiki yace su hadu dashi a inda suka saba haduwa Da misalin karfe 1:00pm na dare su zomai Da kawu yana san za suyi magana,.
Kallan ta a sultan yayi sultana karki ga ina sake miki fuska kice hakn zai kawo mana raini dake bana San raini bana San inawa mutun magana yana nuna KO ajikinshi banasan raini ki kiyaye karki manta matsayinki na baiwa kinsan ke baiwa ce haryar har gobe sannan karki dauka wai dan kin aurenin kin Tashi daga baiwa a guna ba haka bane kinanan a matsayinki inasan kina tunawa Da hakan Da fatan kin gane, kallan shi tai da hawaye a fuskarta aranta fadi tade Data gama abun daya kawota shikenan kuma wlh yau zata Fara Ta tsani ya dinga kiranta Da sunan baiwa dinnan, ganin taki magana sai hawaye hakan yasa Ya mike Ya fice,.
Kallan dakin tai kawai tai kwanciyarta tana hawaye tare da tunanin kawunta ko a wanne hali yake yanzu Allah masani ,.
1:00pm
Sarkine azauna a farfa jiyar masarautar shida Yan aikinshi sai kawu dake kan kujera a daure, kallan shi sarki yayi Da gani baka gama tsufa ba zaka Dan jigata kafin ka mutu IN kuwa bakai taurin kaiba ka fada mun abun Da nake nema shikenan zan sallameka Da abun alkhari, kallan shi kawu yayi inaji meye abun Da kake nema? Murmushi sarkin yayi wannan Yar taka yama sunanta itta nake San Ka fada mun inda take, kallan shi kawu yayi tunda baisan sunanta Bari ya sa mata wani au wai ummina dama wai kaine sarkin bata gama dakaiba aina dauka har ta gama dakai Ta fadawa duniya kokai waye me ta tsaya yi, kallan shi sarki yayi fuskarshi a daure, ohhhh Da saninka tazo wannan masarautar daukan fansa kenan? Eh mana nidakaina na kawota kuma nasan tana kan hanyar yin hakan, sign Ta ido sarki yayi na kusa Da kawu bashi wani duka a kafa Da saida ya sashi sakin wata kara Ta wuya,.
A razane sultana dake bacci Ta tashi Tana salati ,ya kamata Tasaba Da wannan hali irin na wannan masarautar kaitaji ihu Da daddare sannan inkayi tambaya ace aljanun masarauta ke fada itta kan ihun yau ya fitar mata daban dole taje taga Maye, ta window ta leka, ganin haske a farfajiyar masarautar yasa ta Mike tare da daukan mayafimta Da dauki phone dinta, ta fito parlour,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 60*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
A hankalj take sakkowa parlour duhu ba kowa, kunna wutan tai Tana neman key a akan Centre table din daya zauna Ta gani, hakan yasa ta dauka Ta bude kofan Ta fice Da addua abunta,. Tafiya take haske masarautar dake akwai hasken farin wata, Da raba rabe Da komai har takai wajen gun da suke Ta buya ta can bayansu bataga fuskar kawuba Amman Tana ganin ta sarki, gabanta banda dukan hamshin hamshin ba abunda yake, wayarta Ta ciro dukda bazai fito sosaiba Amman a haka zatai video record din ya kaamata ace ta Fara abun daya kawota,a hankali Ta saita wayan itta abun Da take bukata bai wuce Ta dauki fuskar sarkinba Amman da yake duhune bai fito sosai ba, Amman a hakan Ta tsaya take abunta,.
Dukka batajin abun Da yake fada Amman Tana ganin abun Da suke,.
Kallan shi sarkin yayi badai zaka fadi gaskiya bako shikenan mu zuba nida kai zan baka nanda sati daya inkaga zaka iya fitowa kana fadi gaskiya shikenan in bazaka iya ba Elgar kasheka zan yi Da kaina kamar yadda dakaina zan kasheta ittama, sannan in kashe mahaifinta Da kaina, mikewa yayi ya kallesi kuje dakin ajiya Ku nuna mai mahaifinta sannan ku bashi a zaba sannan ku sanar Da abdulsalam gobe inna dawo daga wajen taron bikin Hindu zanzo in sameshi, kallan gun da sultana take yai kamar Da mutun agun matsawa yai gun, hantar sultana kuwa bugawa take kawai Amman bata fasa daukan record dintaba, yanzu fuskanshi ya fito sosai, zan kamata kuma zan kasheta su kadaine makiyana a duniyar nan, sannan ya juya yai musu alama su tafi dashi, sannan shima yai gaba ,ajiyar zuciya sultana ta sauke saida Ta Bari sunbar gun sannan ta kama hanyr komawa bangaren sultan din,.
Dakin ajiyar suka kaishi har gun sarki abdulsalam,kallan kawu sarki yayi bawan Allah me ya hadaka Da wadannan mugayen? Kallan sarki yayi babu shakka kaine mahaifin sultana, riko hannun sarkin yayi karka damu yarka nada dakarkiyar zuciya nasan zata fitar dakai anan KO ba dade KO ba jima kaidai adduar ka take bukata, bawan Allah ban ganeba? En nine Wanda na rike yarka har ta girma koma tazo nemanka, to bansan taya ya gano taba shine yake San in fada mai inda take Dan naki yace akawo ni nan, Amman karka damu nasan Tana zuwa, murmushin jin dadi sarkin yayi,.
A hankali sultana ta tura kofan parlour ta shiga sannan ta rufe kofan zuciya daya Ta juyo zata wuce idonta ya sauka kan sultan dake gaban fridge da ruwa a hannshi Yana kallan ta,.
Cikintane ya bada wani kuluuuuu luuuuu Ta hadiye wani uban yawu ,ajjiye ruwan yayi ya nufin inda take,da sauri Ta juya zata bude kofan Ta koma tai hada Da gudu tare da dawo Da itta ya rufe kofan ya hadata Da jikin kofan, kallan ta kawai yake, kamar yayi kuka, a hankali ya fara magana sannu Da zuwa aunty jaruma waike wacce irin Mace Mace Dan Allah ki fada mun abunda ya kawoki masarautar nan Dan da gani bawai aikine ya kawo kiba nifa kin fara ban tsoro banda aljanar Mace wacce macence zata iya ficewa a wannan uban daren fisabillahi kuma ko ajikinta Dan Allah ki fada mun, kallan shi tai uhmmmm uhmmm damafa bangaren momy zan tafi shine kuma dana fice naga naji tsoro shine Na dawo, ta fada tare dayin kasa dakai,dago habarta yayi ban fada miki baki iya karya ba Yau saikin fada mun abun Da Ya kawoki marautar nan,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 61*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Shiru tamai batace komaiba, shima kuma bai matsaba,kallan shi tai KO a jikinshi, ranka ya dade nifa baiwace ba uban gidan mutun baikama yana takurawa baiwarshi hakaba ni bacci nakeji plz zan wuce, baccin kike ji kika fice Da daddare? Yaufa sai kin fada mun ,OK naji Dan matsa to muje mu zauna sai in fada maka Amman saika ban amsa tukun Da alkawarin duk abin dana sakaka zaka mum, kallan ta yayi sosai yanasan karantar Ta Amman baiga komaiba illah zillar rashin tsoro, OK naji Ta fada tare da matsawa, zama yayi akan kujera yana kallan ta Ta Sami daya ittama Ta xauna, uhmmm so nake ka fada mun wai me yasa baaa fita a wannan masarautar Da daddare? Saboda yawanci duk Wanda ya fita da daddare a wannan masarautar mutuwa yake, OK kuma itta wannan masarautar me take tunanin Yana wannam kisan, gyara zama yayi aibansan sanda kika zama yar jarida ba, uhmmm kaifa kace saina fada maka me ya kawoni wannan masarautar to maye Dan ina Maka tambaya kuma saida na fada maka ka amince maye a ciki to, OK naji, a iya bincike na wannan masarautar mum gano cewa aljanun wannan masarautar ce wadda akai musu gini a tasu masarautar suke kashe Yan garin nan da daddare, wata dariya Ta sake wadda saida Ta dade Tana yi kafin Ta kara kallan shi tana murmushi kuma kai ka yadda da hakan? Eh mana me yasa bazan yadda ba ,tabe baki tai OK to meyasa ni basu taba kasheni ba duk fitar Da nake sannan kuma abun mamaki ban taba gamo Da aljanuba sai mutane dake yawo Da addare me hakan yake nufi kenan, murmushi yayi tare da gyara zama hakan yana nufin kema aljanace shiyasa mutanen basa iya kamaki, OK ni aljanace Amman harda Mai taimakata ko? Ta fada Tana daga mai gira, hade fuska yayi ke banasan shashanci kawai ki fada mun abun daya kawo ki wannan masarautar, OK bari in maka tambayar karshe,ai gwannati ya kamata ittama Ta bada gudin mawa me ta bayar, taba dpo dake bincike Amman iya binciken shi bai gano komaiba Yaya iya dawa wuce yai hakuri, Hmmmm Ta sauke ajiyar zuciya zaka iya hadani Da dpo din? Sakin baki yayi Yana kallan ta me zakice Mai, gudun mawa zan bashi tunda shi ya kasaa aikinshi, tsaki yaja bani amsata plz mikewa tayi sarkin ku nada nazu fitowa dashi sannan in tuna asirin mugawaye, kallan ta yayi gwannatice Ta aiko ki? Aa nina aiko kaina gobe zamu karasa magana saboda ina bukatar taimako, saida safe tai fada tare da yin sama, Ya bita Da kallo tunba yauba yake tunanin sultana Nada aljanu may be yanzuma aljanun nata ne suka tashi banda hakan mutumin daya dade Da mutuwa tace tazo dakkoshine aya, mttswwww yaja tsaki tare dayin sama ,.
Washe gari tunkan gari ya gama haske sultana ta wuce bangaren Momy lokacinma basu tashiba,.
Saida tai sallah sannan ta koma Ta kwanta,.
Da sallama momy Ta shiga dakin nata, ganin Tana bacci yasa ta tasheta, ina kwana mom? Lafiya qlau sultana, sultana me yasa bakijin magana ne so kike kamar yadda muka Rabu da mamanki kema mu rasa ki? Aa momy wlh hankalinan jiyan yaki kwanciya shi Yasa Amman bazan sakeba, murmushi mom tai tare da shafo kanta karki sake plz, daga kai tai alamar to, mom wlh yau bazan Sami damar zuwa wajen party dinnamba kaina ciwo yake mun, OK zan fadawa sultan din Amman kinsan ana dawowa zaa wuce dake bangaren kiko? Eh momy na sani Allah ya dawo dasu lafiya, ficewa mom tayi Ta barta, murmushi sultana tai aikina zan Fara yanzu kamata yayi ace Ma har na gama Tara shaiduna Amman ina abun yakici yaki cinyewa, Da sauri Ta Mike Ta dauki wani hijab sannan ta fice bangaren bayi Ta nufa, sai gaidata ake Tana amsawa Tana zuwa tacewa marka gun su Zuwaira tazu saboda dasu tai kawaye agun walima, har dakin marka Ta kaita sannan ta fice, Da sallama Ta shiga tare da fadin ina kewar dakin nan, kallan sukai me ya kawo ki taya akai kika fito Da wannan uwar safiyar?
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 62*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
To wacce zan Fara amasawa kawai Dan nafito ganin kawayene saia tsareni Da tambaya sai kace Yan jarida, abu nazu dauka Ta nufi gadonta Ta daga sannan ta dakko key, wannabe ta nuna musu, key din maye wannan din? Wlh na wani gune aiki zanyi yau dinnan, wanne aiki alhalin kinsan party zakuje, aibanda lafiya Allah bazanje ba ina Da abun yi, tabe baki sukai, kaga matar yarima sultan, murmushi tai tare suka fito, Zulai Ta kama hanyar gun aikinta itta kuma Zuwaira Da sultana suka tafi suna hira kamar ranar Hafiz suka hango Yana tahowa, kallan su yayi wannan ai Matar sultan ce nan take sanda yaga sultana da Zuwaira ya fado Mai, kallan su yayi yaushe suka zama kawaye haka,?
Sultana ta Kalli Zuwaira ga mutumunki nan bari kiga, suna zuwa sultana ta kalleshi, kamar Yayan Hindu habibu KO hafixu KO, eh Hafiz ba hafizu ba, me kike Da Matarr dazan Aura yaushe kika Santa, kallan Zuwaira tai ta kalleshi Da gaske itta zaka aura aikuwa kun dace kasan banda kawaye ran walima na hadu da itta naji ina San yin kawa Da itta, kallan Zuwaira take Sun dade basu haduba Amman kamar ya canxa ba kamar yadda ta sanshiba, murmushi yayi tare da kallan Zuwaira, kefa kar kiga nadaina miki magana ki dauka na canza shawarane inanan kuma ki jirani so nake a gama da nasu ya fada tare da yin gaba, murmushi kawai Zuwaira tai, kallan sultana tai kodai yar uwa ta kamu NE? Tsaki Zuwaira taja kawai, haka suka karasa kowa yakama hanyar shi,.
Sultana ganin lokacin party ya kusa hakan yasa ta shiga bargo itta a dole bata Da lafiya aunty mairo sai sannu aike mata, Tana amsawa Da kyar,.
Da sallama sultan ya shiga dakin jin sallamar shi Yasa sultana rufe ido alamar bacci take, ina wuni aunty? Qlau ango yaudai zamu kawo maka amarya, murmushi yayi wai bata Da lafiya ko? Eh wlh tama Yi bacci jirani ina zuwa Ta fada tare da ficewa, .
Zama sultan yayi kusa Da itta akan gadon yana tuna maganar su Ta jiya shi kwata kwata bai yadda bata Da lafiya ba, kallan ta yayi ya taba wuyanta, ba wani zafi gyara mata Gashin kanta dake shiga mata hanci yayi ganin fatar idonta yana motsi hakam yasa Ya tabbatar baccin karya take, murmurshi yayi anya wannan rashin lafiyat gaskece, Allah sarki gashi har bacci take nifa nasan halin Matata yanzu haka wani gun take zuwa a wannan masarautar, tsaki kawai sultana take ja yazo ya wani sakata a gaba, duk Ta takura, murmushin mugunta yayi,.
Kusa Da itta ya matsa sosai har tanajin nunfashin shi sosai gabanta yahau faduwa badai kissing Nata yake San yiba,,Allah ya kawo aunty mairo abun Da take aiyanawa kenan ,ganin taki bude ido yasa Ya kara matsawa har yana shirin bata kiss tai sauri bude ido tare dasa hannnu Tana kallan shi, murmushi yayi tare da ja baya, aida baki tashiba Da saina in tasheki Da kaina kuma ki shirya dan ban Yadda dake ba wlh
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 64*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Hajaramaminattygirl20.WordPress.com
Mikewa zaune tai Tana kallanshi kallan mamaki, daga gira yayi no karki daukeni daban dama ba kissing naki zanyiba kawai Dan ki tashi nai hakan, juyar dakai tayi ni banajin dadi bazan Sami damar zuwaba, uhm uhmm fa nasan halinki wlh kika sake kika fice naji labari nida kene ya fada tare da mikewa, tabe baki tai ta koma ta kwanta,.
La,asar kowa ya kama hanyar zuwa wajen party, masarautar tayi shiru dukda akwai sauran bayi Amman basu Da wani yawa,.
Mikewa sultana tai taje Ta leka dakin momy,tana karanta jarida a hannunta,kallan sultana tai Ya jikin yata, karasawa tai ta zauna sannu Da karatu momy, yauwa kinji dadin jikin ko? Eh momy xanje kitchen ne in dafa wani abun kiyi zamanki momy karfa ki fito, kallan ta momy tai saboda me karna fito kenan? Aa momy ina nufin kiyi zamanki ki huta a daki kinga baki San hayaniya, tabe baki momy ta itta kuma sultana ta Mike ta fice,.
Key Ta dauka Ta dauki mayafi babba Ta fice abun,kofan Ta bude Ta fito gaidata wani bawa yayi dake waje yayi Ta amsa sannan tai gaba abunta,dube dube take bata San kowa ya ganta, haka har ta karasa, dai dai kofan Ta tsaya Ta dakko key din Ta bude sannan ta cire key din Ta shiga Ta rufe kofan Ta ciki Ta kulle, kallan gun take babba ne sosai Amman waime yasa zuciyarta take raya mata akwai abu anan ne? Tsaki taja ki tsaya bata lokaci dai har su dawo, gaba tayi Tana dube dube saida Ta kalli hanyar Da tabi ranar bataga komaiba hakan yasa ta yanke hukuncin bin daya hanyar, tafiya take abunta, tun daga nesa Ta hango mutane biyu zaune, tsayawa tai ta tsorata sosai me ye wannan mutane dama akwai mutanen Da suke rayuwa anan, karasawa take a hankali, a hankali kawu ya dago Yana kAllan ta,zaro ido yai tare da fadin sultana, Da sauri Ta karasa gunshi kawu Ta fada idonta Da hawaye kawu sawa yayi aka kamoka KO? Kawu nina jawo maka ko Dan Allah kayi hakuri zanje in fada mashi nice inyaso sai kashemu tayi, riko Ta yayi bance kije ba sultana, sultana bakiga canba ya fada yana nuna mata gun sarki, kallan gun sultana tai ido sarki ya Zuba mata, tabbas wannan ittace yarshi gashi yaga Tana kama Da Fatima, karasawa gunshi tai Tana kallashi kafin Ta kalli kawu ,kawu ban ganeshiba, mahaifinkine sultana, kallan sarkin tai hawaye na zuba a idonta, riko hannunshi tai Tana kallan yadda hannun ya koma Irin Wanda yasha wuya, Kallan shi tai kaine abbana, me kake anan sarkine ya ajjiyeka anan? Ta fada tare da rumgumeshi Tana kuka sosai bubbaga bayan Ta yake alamar tayi shiru,amma kuka take sosai dama mamanta Ta fada mata a cikin mafarki cew zata hadu Da abbanta gashi yanzu T ganshi, dagowa tayi Tana sharemai hawayen fuskar shi, abbah Da kawu yanzu zan daukeku kubar wannan gun tafiya za muyi kawai ni bazan iya barkinku anan ba, rike hannunta abbah yayi aa yata baa abu kai tsaye haka ki Bari ba yanzuba in kika fita damu ina zaki kaimu? Shikenan abba Amman dole inkai sarkinnan kara jibi yadda ya mayarmun Da mahaifi, dole zan sanarwa Da sultan nasan zai taimaka mun dashi za muyi aikinnan, kallan kawu tai kawu yanzu yaushe yace zai dawo? Anjima yace kuma sati daya yaban in fada Mai inda kika inba hakaba zai kashe ni ,sati daya nima kuma a sati daya zan fitar daku a wannan gun I promise Amman dole sai na tambaya hadin kan sultan dole saida na dpo din dake handling din wannan case din kara zan shigar Da sarki akan wannan abun wlh bazan yafe mai ba imani tsakanina dashi,.
Mikewa tayi Tana kallan gun ta ina zata Fara ne?wayarta Ta dakko Ta cire sim din sannan ta kunna wayar can sama Ta samu Ta juna wayar yadda zatai mata record da kyau, kallan kawu ta kawu Da kaji alamar zai shigo Dan Allah ki danna nan Ta fada Tana muna Mai ban sa mata key ba record kawai zaka mun saina Tara shaidata sannan zan tunkareshi, komawa gun abbanta tai, abbah na kusa fitar daku anan insha allahu, karku nuna Mai wani yashigo nan, Bari inje yanzu in kawo muku abinci sannan ta mike yanzu zanje in dawo, Da haka Ta kama hanya saida Ta rufe kofan sannan ta koma bangaren momy din, Tana shiga taga momy a parlour, aa dama baki kitchen din? Eh momy abu Na duba abaya yanzu dai zan shiga Ta fada tare da fadawa kitchen din,.
Tana Cikin dafa abincinne daji ana dawowa abun ya bata mamaki Da aka dawo Da wuri ba zata Sami damar kai musu abincinba kenan
Jin sallamar aunty mairo yasa ta fito, kallan ta aunty mairo tai Ya jikin har naga kin shiga kitchen INa masu aikin?jiki Da sauki kuma nafisan inyi aikin Da kainane aunty Ya naga kun dawo Da wuri? Eh kinsan mu iyaye ba zamu dadeba shiyasa kumama nabar yata ba lafiya ai dole inyi maza inje in dawo, murmurshi sultana tai aunty kuma har sarkin shima ya dawo? Ahhh to shiba uba bane mai tsaidashi, ajiyar zuciya zuciya sultana ta sauke Tana tunanin abunyi, kallan ta aunty mairo tai lafiya naganko haka kamar bakiji dadiba? Aa aunty ba komai kawai dai na dauka kuma acan zaku zauna har zuwa anjima ne, aa gamu dai mum dawo, ta fada tare dayin sama tabarta anan,.
Ayi manage Da wannan xuwa anjima plz
By hajara Mami natty girl
👑👑👑🕍🕍🕍👑👑👑
🕍🕍🕍👑👑👑🕍🕍🕍
👑👑👑🕍🕍🕍👑👑
🕍🕍👑👑👑🕍🕍
*MARAUTAR MUCE 65*
🕍🕍🕍👑👑👑🕍🕍🕍
👑👑👑🕍🕍🕍👑👑👑
🕍🕍👑👑👑🕍🕍🕍
*INDICATED TO MAMAN SHUKRA AUNTY UMMI*
Azujiyar zuciya sultana ta sauke ya zama dole ta naimi taimakon sultan itta daya dai ba zata iya wannan abun ba, ajjiye abincin tai ta nufi kofa, Gani tai masarautar Ta kara cika abun zai mata wuya Ta fice Ta kai musu abinci, tsaki tai tare da komawa tayi sama,.
Bayan sallah i,sha suka gama party dinsu,. Da sallama aunty mairo Ta shiga dakin sultana,.
Yata ki tashi ki Fara shiri Dan yanzu zaku Kama hanya, marairaicewa sultana tai kuma aunty nan da can ai duk dayane abarni anan plz, harararta aunty mairo tai comon jare Tashi kiban gu ko inyi ciki dake mikewa sultana tai aunty to wanne kayan zansa? Mika mata na hannunta aunty mairo tai wannan zakisa wata atamface purple da baki Da yellow a jiki atamfar tayi kyau sai mayafi purple, karba sultana tai idanta ya kawo kwalla duk sai take jin wani iri,mika mata abu aunty mairo tai a cikin ruba ki zuba wannan a Cikin ruwan wanka sannan wannnan in ki fito kisha, juyar Da kai sultana tai itta duk wannan abun bataga amfaninsu ba tunda auren bawai suna San junane ba, murmushi yake tai ta karba, kallan aunty Mairo tai wlh saura ki zubar ba naga kina wani ya mutsa fuskar kiba, murmushi kawai tai tare da shigewa toilet din,.
Mama dake fama Da Hindu kan tai maza itta ake jira, Mama plz inasan zuwa Zanyiwa matar sultan magana, haba Hindu wanne magana kuma?bayan kun Rabu ina ruwanki Da itta plz mama, yanzu zan dawo, saiki sauri, murmushi tai tarw Da mikewa Ta fice,.
Da sallama Ta shiga bangaren su momy, kallan ta sukai murmushi tai tare da gaidasu Ta gaida mom abun ya bata mamaki abun Da Hindu bata taba yi mataba kenan Ta gaida Da respect, kallan mom tai Mom inasan zanyi magana Da sultana matar sultan, kallan ta momy tai sai kuma Ta tabe baki tana Sama, nurmushi tai tare dayin sama,.
Da sallama Ta shiga dakin yayi dai dai Da fitowar sultana daga toilet, kallan Hindu tai tana tunanin Me kuma ya kawota, karasawa Hindu tai tare da fadin sannu Sai kuma tai shiru me zata cewa sultana kuma? Ta tambayi kanta, zama tai a bakin gadon kafin Ta Fara magana yanzu zan wuce Amman inasan inyi magana NE dake game da wata Mai Irin sunanki,amma kuma jikina ya ki tabbatar mun cewa bake bace waccan sultana kawai inaji ajikina kece, Da sauri sultana ta kalleta baa suna iri dayane? Sultan yaban labarin waccan yanzu me kuma ya kawo maganar wacccan? Tabe baki Hindu tai sako zan baki ki bata koda zata dawo bana nan, bana daukan alkawari ban cika ba gashinan na cika mata alkawarinta alkawarinta na daya daga cikin abun Da Yasa na ki auren sultan sannan kuma naso rama rashin mutuncin Da sultan yai mun sai kuna hakan bai yuyuba Amman ai nasan hakanma bai Mai dadiba any way so nake in ta dawo ki bata wannan number tawace duk sanda take Da bukatar wani abun tai mun magana saboda kawai naji inasan tai maka mata ne ta mikawa sultana, kallan number sultana tai to me xatai Da wannan, uhmmm wannan sultana da kike fada ba zata dawoba nibanga amfanin bada wannan ba, murmushi Hindu tai imma kishi kike ni baida menba Ta ajjiye takardar tare da ficewa, Da kallan sultana ta bita wai kishi abunma dariya ya bata, tsaki tayi tare da zama agan madubi Ta Fara kwalliya abunta,.
Hindu na fita suka Kama hanya dama itta daya ake jira duk jikinta yayi sanyi gani take kamar zata rabu da waniqa cikinsu in ta tafi, Amman hakan Ta daure taso haduwa Da sultan Amman bata ganshiba,.
Da sauri aunty mairo Ta karasa dakin sultana me kike haka nace kiyi kwalliya Da kankine nasan ai baki iya ba, dariya sultana tai kaji aunty wai ban iyaba haba sai kace ba Yan mataba, murmushi aunty mairo tai sannan tasa ai mata kwalliyan, haka aka xauna aka Fara tsara mata kwalliiyan har aka gama sannan ta kalli kanta a madubi Ta Saki murmushi,haba gaki kin fito amaryar ki, uhmmm kawai tace,.
Sultana na gama shirinta suka dauketa zuwa bangaren Ta nan da nan dimma saida suka sha yawu a masarautar kafin aka kaita bangaren sultan din bnagren sultana kuma,. ,.
By hajara Mami natty girl
👑👑👑🕍🕍🕍👑👑👑
🕍🕍🕍👑👑👑🕍🕍🕍
👑👑👑🕍🕍🕍👑👑
🕍🕍👑👑👑🕍🕍
*MARAUTAR MUCE 66*
🕍🕍🕍👑👑👑🕍🕍🕍
👑👑👑🕍🕍🕍👑👑👑
🕍🕍👑👑👑🕍🕍🕍
*INDICATED TO MAMAN SHUKRA AUNTY UMMI*
Habib ne Da sultan a gidanshi, kallan shi habib yayi aboki yanzu fa ankai amarya kafa Sani, gyara zama sultan yayi amaryar Da ba soyayya akai auren, kallan shi habib yayi wai Kana nufin ka cemun har yanzu baka Santa? Maye abinta kuma haba aboki, Hmmmm aboki ba zaka ganeba kawai yarinyar na amatsayin baiwa Ta kuma kawai sai in hau santa haba girmana faduwa zaiyi wlh, zaro ido habib yayi su girma manya to wannan wanne irin zama zaai kenan? Wannan Irin zama kuma Da ya wuce Ta zauna a matsayin baiwar Ta ba abunda zai hadani Da itta, kallan shi kawai habib yake Amman dazun kace mun ittace Da ka fara tsaidawa a rayuwarka kuma kace ba Santa kake ba? Mtswww kai ai wannama a rashin sanine plz kadaina mun irin haka, shiru habib yamai, yauwa aboki a wadannan Da amaryaka tai Abokai dasu naga wata kuma ina Santa, kallan shi sultan yayi duk dinsufa bayine, eh na sani a hakan nake santa ance Ma kowa irinka ne, Tsaki sultan yayi tare da mikewa ni zan wuce, zaka wuce aini saina raka ka KO? No kasha zamanka ya fada tare da ficewa, jijjiga kai kawai habib yayi yai zamanshi,.
Sanda aka kai sultana aunty mairo ke sanar mata gobe zata wuce, Aunty ba zaki zauna anan ba? Dariya Aunty mairo tai kawai sai IN zauna ke kina dakin mijinki lallai Da anzo kallo, Ta fada tare da mikewa ni yanzu zamu wuce gobe Da safe zaki ganmu, daga kai kawai sultana tai duk idonta ya ciko, haka suka tafi suka barta itta daya ,.
9:00 Da yan mintina sultan ya shigo masarautar, parking yayi sannan ya fito, karasowa kusa dashi sarki yayi, Amman dai kasan bana San ana kashe mun Yan gari saboda hakan Yasa na hana fitowa Da daddare ko? Kallan bayin kusa Da sarki yayi hakan Yasa suka basu gu, kallan sarkin yayi Dady ai no need ka wani Sa a daina fitowa Da daddare bayan kasan inda matsalar take sannan kasan Wanda yake kisan, ya juya ai wlh abu dayane yasa bai kai karar kaba Dady saboda dady yana fadan kwana dubu Ta barawo kwana daya tamai kaya wlh dady Da baba kashe akai ba abunda zai hana in dauki babban mataki Amman saboda bashi ni banga anfanin wani yin kara akan abunda akeyi a wannan masarautar back saboda ba masarautar mu bace, wannan banzan Dan naka ne Hafiz shiya kamata ya dauki mataki to shima bai dauka ba saini, kallan shi dady yayi ka gama ka gama mun rashin kunyar dan bani na haifeka Na Da kake maganar baban ka me kake nufi nina kasheshi koma? Oho ni ina zan sani abu daya zanyi nibanma yarda Da mutuwar shiba dole IN dauki kataki wlh da kaina zan dauki mataki dole Ma in sake bincike game da wannan matuwar, murmushi Dady yayi duk Wanda zaka tambay basu duniyar Sun mutu mutun dayane shi kuma Ma baka San wayeba amma kaje ka nemo Da kanka mu zuba nida kai, yai murmushi tare da yin gaba, Da kallo sultan ya bishi kafin yai ciki shi duk jikinshi bai kwanta mai Da dady ba wlh ,.
Da sallama ya shiga pparlour,tsaki yayi saboda Da tuna yanzu fa bashi daya bane a bangarenba, sama yayi ya wuce dakinshi,.
Sultana dake zaune a dakinta taji dawowar shi tun dazu shi take jira Amman sai yanzu ya dawo, ajiyar zuciya Ta sauke bari Ta bashi minti talatin kafin nan ya gama abun Da zaiyi sai taje suyi magana, mikewa tai ta nufi window Tana kallon waje masarautar fayau sai hasken farin wata, ya zama dole in fits Yau zanje inga abbah na muyi magana amma wai mema zancewa sultan game da zuwa gun, yes idea ta fada Amman bayau ba sai naje naiwa kawu magana yanzu dai bari inje in Sami sultan, Ta dauki mayafinta tare da ficewa tai dakin shi, .
Da sallama Ta shiga bata jira amsawar saba Ta shiga, yana tsaye gaban madubi daga shi sai towel yana taje kai, Ta mudubi ya hango, itta kuwa Da sauri Ta juya zata fice dan bata taba ganin wani a haka ba ba riga Dan ta tsani taga maza ba riga, hakan Yasa ta juya zata fice ya kira sunan Ta sultana!!!
By Hajara Mami natty girl
👑👑👑🕍🕍🕍👑👑👑
🕍🕍🕍👑👑👑🕍🕍🕍
👑👑👑🕍🕍🕍👑👑
🕍🕍👑👑👑🕍🕍
*MARAUTAR MUCE 67*
🕍🕍🕍👑👑👑🕍🕍🕍
👑👑👑🕍🕍🕍👑👑👑
🕍🕍👑👑👑🕍🕍🕍
*INDICATED TO MAMAN SHUKRA AUNTY UMMI*
Saida Yasa singlet sannan ya karasa gunda take ta juya mai baya, riko kafadarta yayi Tare da juyo Da itta duk tabi Ta dubul bulce, uhmm uhmmm ranka ya Dade dama fa zuwa nai in tambayeka KO zakaci abinci, murmushi yayi me ya kawo Dakina yanzu kowa ba yana Da dakinshiba KO kin manta da hakan? Nifa dama abinci nazo tambayar ka daga gira yayi OK na gane so kike ki tambayeni kazar amarya KO? Kara dubul bulcewa tayi aa wlh ina ni ina wannan matsayin ai nasan bazaa siyo min ballema auren daba soyayya Maye na wani siyo kaza plz ka sakeni zan fita bacci nake ji, kallan ta yayi aa fadi abun Da Ya kawo ki Da gani akwai abin Da kike San fada fadi inaji,, duk Ta tsorata dashi hakan yasa ta dubul bulce,na fasa Ma plz ka sakeni wlh ba abun Da nake San fada ma, riko hannunta yayi Mai zanen, sultana wannan zanen nake San kimun bayani akai, yana kallan zanen yana mata magana, uhmmm sanda zanzo wannan marautarce nanne shine naje aka zana mun,murmushi yana Shafa zanen sosai zanen yamai kyau fisge hannun Ta tayi sannan ta fice Da sauri, tsaki sultan yaja meke damunshi ne me Yasa wataran baya iya control din kanshine a gaban wannan yarinyat, zuciyar shi Ta bashi amsa da santa kake hakn yasa yasa dariya harda kwanciya Akan gado,.
Sultana kuwa dakinta Ta koma itta duk sultan ya bata mata shiri shi wataran sai yana abu kamar mashayi, mtswwww dole IN kwanta Da wuri saboda in tashi Da daddare inje gun abbah na,.
Wanka tai kafin tazo Ta kwanta tai shirin bacci,.
Kamar kullun tsakan dare sarki ya fita ya nufi dakin ajiya, jin zai shigo yasa kawu yin yadda sultana ta tashi, ya koma ya zauna, tunda yashigo yake kallan gun jikinshi na bashi akwai Wanda ya shigo gun, kallan kawu yayi akwai Wanda ya shigo nan ne? Ehto indai ba aljanuba nidai banga Wanda ya shigoba, tsaki yaja tare da zama, kallan abdulsalam yayi kafin ya kalli kawu wancan shine Baban umminka, kasan ya akai na kawo shi nan kana San in baka labari? Daga kai kawu yayi alamar eh, aikuwa sarki ya karkace dowawu ya fara bashi labarin harda yadda akai ya kashe Mubarak (baban sultan kenan )kallan shi kawu yayi har ina abun so a bada irin wannan labarin haba kai kuwa kana tunanin ranar tuna asirinka kuwa? Dariya kawu yayi ai nasan asirin Nawa bazai tunu bane shi yasa, murmushin takaici kawu yayi haka ya zauna ya basu labarin yadda zai kashe su nanda sati daya KO biyu masu zuwa koda kuwa bai hadu Da sultana ba yaji Da itta daga baya,.
1:00 dai dai sultana ta Mike tai shirinta na fita ,Ta fito parlour sadaf sadaf, kofa direct Ta nufa sultan dake kwance kan kujera yaji fitowar yai shirune kawai Saida Ta nufi kofa Tana shirin budewa ya dalleta Da touch din hannunshi, Da sauri Ta juya Tana kallan gun tasan shine shikenan ba itta ba fita, switch Ya kunna ya dallah mata harara Ta dauke kai tana turo baki, hannunta kawai ya riko yai dakinshi Da itta, a dakinma Saida yasa key, ya juya yana kallanta anan zaki dinga kwana dama tsatsayine yasa na barki ke daya marajim magana kawai, ranka ya Dade anan fa kace, harararta yayi karki kara cemun ranka ya Dade ai yanzu na tashi daga nan in kuma so kike mutane so ganeki to shikenan, kashe switch Tare da kwanciya abunshi
By hajara Mami natty girl
👑👑👑🕍🕍🕍👑👑👑
🕍🕍🕍👑👑👑🕍🕍🕍
👑👑👑🕍🕍🕍👑👑
🕍🕍👑👑👑🕍🕍
*MARAUTAR MUCE 68*
🕍🕍🕍👑👑👑🕍🕍🕍
👑👑👑🕍🕍🕍👑👑👑
🕍🕍👑👑👑🕍🕍🕍
*INDICATED TO MAMAN SHUKRA AUNTY UMMI*
Da kallo Ta bishi bata San inda zata kwanta ba, doguwar kujeran dake dakin Ta kwanta sai tsaki take,.
Sarki kuwa Da yazu fita saida yabar gun su kawu sannan ya zuba wani farin abu inma Da Wanda yake shigowa zai gane,.
Washe gari Da sassefe bayan sultana ta tashi lokacin sultan baya nan yana masallaci Ta mike tai waje abunta Da yake gari bai gama haskeba yawanci mutane na masallaci kuma a wannan lokacin bayi suna nasu bangeren suna shirin fitowa aikin su, direct dakin ajiyar Ta nufa, saida tai ta dube dubenta kafin ta shiga, wannan karon Allah ya sota bata bi takan abun Da sarki yasa ba, ciki tai Tana sauri ganin bacci suke Yasa tai a hankali Ta dauki wayanta Ta fice, lokacin charge din wayan ya kare,.
Saida Ta isa part dinsu sannan hankalinta ya kwanta, dakinta Ta nufa Ta fara gyarawa sannan tai wanka Ta fice parlour ta fara aiki sannan tasa tai wayanta a charge,.
Gari na wayewa Ta gama aikin parlour tasa turaren wuta sannan ta nufi kitchen table hau gyare gyaren Ta, Bayan GA gama Ta koma parlour ta zauna tunda tasan ba yanzu zaici abinciba yayi wuri yau Ma ta tashi NE da wuri kodan Da saita biya bagaren momy tai mata aiki take zuwa nan,.
Da sallama ya shigo parlour, kallan ta yayi tayi kyau sosai dukda ba wani kwalliya tai ba Amman tayi kyau, karasawa yayi tai kasa tare da gaidashi sannan ta zauna a kasan, Ta gefen ido ya kalleta yau kuma ba zaai mun breakfast bane? Aa zaai gani nai kamar yayi wuri, ba wani wuri yanzu nake San zanje wani gune,.
Kallan shi tai takuwa kamata yana kallanta yai saurin dauke kai, anban wasika IN kawo maka wani bawane yanzu ya kawo yace wai ance ya baka, OK dakko inga mikewa tai tare da yin sama,ko minti uku baaiba Ta sakko Ta mika Mai wasikan, karanta inji, jijja kai tai tare da budewa,.
*Sako daga mai neman tai mako inasan kaje dakin ajiya akwai abun Da nake San ka gani*
Tsaki sultan yaja Ashe da gaske akwai aljanun a wannan dakin yanzu har ya kai suna zuwa kawo mana sako AI antaba aikawa sarki irin wannam wasikar sanda yaje saida yasha wuya kafim ya fito banga abun Da zai kainiba, shiru tai wai Da gaske wannan plan din nata bazaiyi aikiba kai ina, haba yaya sultan AI yakamata kaje kaidin tsoran aljanun kake? Hararar Ta yayi ke kije, OK ka yarda inje kenan Amman da daddarw zanje fa, daga kai yayi alamar taje,.... A ranta take fadin kaima kuwa dole sai kaje Da haka Ta Mike Tana shirin daura abinco taje an danna bell, mikewa sultan yayi yaje yabude abincine aka aiko, ya karba ya bata, sannan yai sama Dan zuwa yin wanka,. Yana fitowa tai saving nashi yaci sannan suka Kama hanya zuwa bangarem momy, lokacin Da sukaje har aunty mairo sun gama shiri, hakan yasa idon sultana cikowa Da kwall jira take kawai Ta fashe musu Da kuka,.
Aikuwa Da zasu tafi haka Ta sasu gaba tana mata kuka, dakyar suka Rabu duk idon sultana ya kunbura saboda kuka ,haka suka tafi sannan sultan ya kam hanya,.
Haka sultana ta zauna Da kewar aunty ta gashi Tana Allah Allah dare yayi yau zatasa sultan ko yaki ko yaso sai yaje
By hajara mami Natty girl
[9/11, 10:33 AM] Hajaramami: 👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 69*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Da rana Tana zaune a parlour jakadiya Ta shigo Da wasu bayi, gaida sultana tai cikin girmamawa abun sai yabama sultana kunya,haba jakadiya ku zauna mana Ta fada tare da nuna mata kan kujera, zama jakadiya tai inda take sanar Da itta momy ce tace akawo mata masu mata aiki, kallan bayin tai kwata kwata bata Da ra,ayin Yan aikin nan itta dayama zata iya, kallan jakadiya tai jakadiya dama kice mata Ta barsu zan iyayin komai fa, aa dama momy tace zaki iya fadan hakan Amman tace bata yadda ba Dan ba,a barin matar Dan sarauta itta Ta dinga aiki Ta fada Tana kallan sultana ,Hmmmm kawai sultana tace sannan ta kalli bayin ukune,shikenan xanzo muyi magana anjima ki fada mata kije zan nuna musu aikin Da zasuyi Amman banda girki gaskiya, shikenan kawai jakadiya tace sannan ta tashi Ta fice, kallan su tai sannan ta nuna musu inda zasu yi mata aikin goge gogeneDa share share sai wanke wanke ,.
Yau kam sultan bai dadeba ana sallah isha ya dawo part dinshi ya nufa direct,.
Sultana na kitchen Tana hada abinci saboda hakama bata San ya dawoba,.
Bayan Ya gama abun Da yake ya nufi dakinta, Da sallam ya shiga bata nan, ina kuma taje,kallan dakin yayi har zai fice idonshi ya sauka kan wayarta dake june nan ya tuna wayarda yake socefa ya siyawa momy Amman ta dauka Ta bata, karasawa gun wayar yayi dole Ya raba Ta da wayar Ma, dakan wayar yayi ya cire sim Da memory ya ajjiye mata sannan ya fice yaje dakinshi ya ajiiye sannan ya sakko parlour a stair suka hadu, kallanta yayi sama Da kasa kafin ya dauke ido tare da fadin an sake wanka kenan, gyara tsayuwa yayi wannan kwalliyar wani akaiwa duk Dan a burgeni, kallan kanta tai Wata Arabian gown ce a joints Da mayafinta sai Dan huda Da jan baki Data Sa Amman yake kiran hakan Da kwalliya, murmushi tai ai in ka yaba Ma ba matsala bane tunda yayana ne ya yaba, tabe baki yayi imma danni akai wannan abun to ni baa burgeniba, AI kwalliyar Da xanyi ta burgewa sai na auri mijina na asali,ka sakko in zuba maka abinci, Da kallo ya bita tare da tabe baki wai mijinta na asali basai na yi sakinba tukun, sarai ta jishi Amman ta share, zama yayi ta zuba mai abincin ittama ta Debi Nata Tana ci, ta kasan ido yake kallan yarinyar gaba daya canza Mai take kwana biyun nan,.
Bayan sun gama tayi dakinta Dan watsa ruwa, Bayan Ta fito tayi shafe shafenta Da feshe feshenta sannan ta dauki kayan baccin ta Tana sa riga yai sallama hakan yasa tai saurin karasa saka rigar, kallan ta yayi niba abun Da zan kallan, tsaki taja tare da fadin kasa kasa mutun ya dinga bari ana amsamai sallama kafin ya dinga shigowa plz, bazan bariba din inma na ganki a haka AI matata na gani, zaro ido tai yaushe na zama matar kuma? Plz bana San magana muje mu kwanta, zaro ido tai ban gane muje mu kwanta ba? Look malama karki daukeni wani abun daban kinsan bazan Bari kina fitar daren nan bako? Hade rai yayi banasan shashanci wuce, ganin yadda ya koma yasa ta dauki abun Da zata dauka kwata kwata ta manta da wayar Data Sa a charge, dakin nashi suka shiga kamar yadda yace jiya ta kwanta hakan yaje tai kwanciyar ta a gefe, shi kuwa saida yai wankan shi sannan yazo dan kwantawa sultana dake jiran taga ya kwanta a kan kujera sai gani tai Ya hau gadon ya kwanta ta daya barin, mikewa tai Tana kallan shi shima kallan Nata yayi alamar Maye dinnan? Yaya sultan naga a kan can zaka kwanta? Kallan gun yayi baxan kwanta acan dinba kema kuma ban yarda ki kwanta ba saboda zaki iya ficewa ban saniba,batace komaiba illah kallan shi Da take, Amman ai Kasan Da ficewa ta yau KO? Kallan baki squad hankali yai mata Ya kwanta abunshi tare da juya mata baya, pillow tasa guda biyu a tsakiya sannan ta kwanta yana jinta baice mata kalaba,.
Basu dadeba bacci ya daukesu dikansu,.
12:30 dai dai sultan ya tashi Dan yin sallah dare, juyawa yayi yana kallan sultana da kashin kanta ya Dan rufe mata fuska, kallan ta yake sosai ta KO ina yarinyar ta hadu matsala daya baiwat shice Amman daba Dan hakan ba ba abun Da zaisa ya Rabu da itta, gyara mata Gashin yayi sannan ya cire pillow din Data Sa ya Mike yai toilet yai alwala Danna ya dawo ya tada sallah .
1:00 dai dai sultana ta tashi Da adduar bacci a bakinta yanzuma dai ta saba Da tashin daren nan. Kallan gun da tasa pillow tai bayanan, kallan jikinta tai kafin ta Kalli sultan dake addua kawar Da tunaninta tai sannan ta mike taje toilet, ittama sallah tai lokacin sultan na shirin kwantawa, Da sauri ta karasa gunshi.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 70*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Yaya sultan ka manta da alkawarin Da kamun kace xaka Bari in fita shine nake San tafiya yanzu, fasa kwanciyar yayi ya zauna waike Da gaske zuwa xakiyi? Eh ta daga Mai kai, baki Da hankali ko? Plz mana Yaya sultan kaifa kamun alkawari, ganin Da gaske San tafiya take Ya ce Bari dai ya gwadata, OK jeki, Da murna ta Mike tai kofa taje dakinta ta dauki abun Da zata dauka, sai a lokacin ta tuna da wayarta, garin dubawa ta daga bedside drower Da xubar Da memory dinta Da sim dinta, ganin dai bata ganiba kuma zata bata lokaci yasa ta hakura ta fito, tana fita taci karo dashi saida ta tsorata hararta yayi a hakan zaki iya fita, Allah zan iya tsaki yaja tare da fadin muje, Da murna ta kalleshi ka daina tsoran aljanun kenan? Harararta yayi hakan yasa tasa dariya shi kuma yai murmushi,.
Fita sukai abun Da ya bata mamaki tafiya kawai yake ba tare da wani tsoroba,.
Saida suka zo bakin kofan kafin ya kalleta yanzu ya kike San ayi na key, key din ta dakko mutumin Da key yaban, kallan key din yayi lallaii wannan aljanin hatsabibine, karba yayi ya bude suka shiga Da addua,murna kawai sultana take,.
Ni Banga alamar Da wani anan ba ,wlh da mutuna tunda kaga an aiko AI akwai ne,itta take nuna hanya abun har yaso bashi mamaki Amman ya danne haka suka karasa, kallan gun sultana tai babu abbahta babu kawu sai takalmin kawu Da taga daya, ganin babu kowa yasa sultan kallan ta kinga ni banga kowa bafa, ganin kamar bata hankalinta yasa ya tabata Da sauri ta kalleshi idonta ya ciko Da kwallah, Yaya sultan wlh akwai mutane anan gun, haba sultana gashi dai ba kowa takalmin ta dauka ta mika Mai, kagafa yaya kace kuma ba kowa karbar takalmin yayi ganin kamar ta Fara fits haiyacinta ya ajjiye sannan ya rikota suka fice, kuka kawai take a ranta Tana aiyana ya kashe sune kawai shikenan ya gaama Da itta,.
A haka suka karasa part dinsu kuma abun Mamaki ba wanda ya tunkareshi Yau abun ya bashi mamaki, zaunar Da itta yayi a bakin gado ya dakko ruwa ya bata tasha kuwa Da yawa kuka kawai take. Kallan ta yayi sultana kin taba shiga wannan gun KO? Shiru tamai tambayarki nake,daga Mai kai tayi, dole dole AI aljanu su bude miki ido mana saida nace ki daina fitann daren nan kikaki, a fada yake maganar, saiki San yadda zakiyi ai ba zaki Sani aikiba wlh, a fusace ya mike yaje ya kwanta,.
A hankali take kuka yanzu ya xatai tasan shikena ya kashe su abbah ne danma ta taba ganin abbah Da shikenan indai kuwa hakane ba zata yafe ba zata dauki fansa,.
Kashe switch din yayi Amman yana jin kukan Nata baya San kuka har heart dinshi yake ji Amman ya rasa yadda zaiyi ganin taki yin shiru baima San sanda ya karasa kusa Da itta tare da jawota ya rumgumeta ba, Tashi daya sultana ta dauke kukan ta rasa inda ya tafi,.
Plz bana San kukan nan ya isa haka, duk ke kika jawo gashi yanzu aljanu sun bude miki ido, Yaya bafa........ Da sauri ya daura Dan ya tsanshi a kan lip Nata bana San jin komai kiyi baccinki kawai, shiru tai Tana san kwace kanta Amman ta kasa, plz ni ba abun Da zan miki kukan ne bana so, batace komaiba sannan tai shiru bacci ya dauketa,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 71*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Sultan Ne ya fara tashi, kallan gari yayi ya fara haske that mean ya makara kenan har itta sultana baccinta take hankali kwance, kallan yadda ya riko ta yayi, sai kuma ya tuna abun Da ya faru, bude ido sultana tai alamun ta tashi, Da sauri ya saketa itta tun kafim ta gama watstsakewa ta sauri ja Da baya, mikewa yayi ya shiga toilet, ittama ta mike ta fice a dakin Ma gaba daya, kan gado ta zauna, kafin ta saki tsaki ta mike ta shiga toilet, tai alwala sannan tai sallah,.
Bayan Ta idar ta koma ta kwanta, kwata kwata abun Da ya faru jiya take tunawa ba taga su abbah ba to ina sarkin ya kaisu komai kashe su yayi? Yanzu ya zanyi ta ina zan bulowa sultan kuma yanzu banma San inda ya maida suba, wai itta ce jiya suka kwana tare a manne Da juna Da sultan, inta tunama wani abun ke tukare mata wuya saidai kawai taja tsaki,. Duk waddan tunanin sunbi sun dameta,haka har bacci ya dauketa,.
.shima hakan take agun sultan inya tuna sai dai yayi murmushi kawai, azzakar dinshi daya saba yayi sannan ya kwanta shima din,.
9:00 dai dai sultana ta tashi daga bacci, ta Mike Tana salati kwata kwata Ma batai aikin gidan ba, wanka tayi tasa atamfarta sannan ta fito, ganin wadannan bayin tai suna aikin su, ajiyar zuciya ta sauke Dan kwata kwata ta manta dasu Ma, shiyasa hankalinta ya tashi Da taga ta makara, gaidata sukai sannan suka ci gaba Da abun Da suke kitchen ta shiga Dan yau Monday may be sultan zaije office,.
Doya ta fere ta dafa sannan ta soya Da kwai sai tea da ta hada sannan ta tai sauran aikin,jerewa tai a dining, ta nufi dakinta Tana san duba wayarta ko zataga abun Da zata nunawa sultan game da su abbah,.
Bincike take a dakin sosai Amman ba Waya babu dalilinta, innalillahi ina wayar nan taje kuma bamu dai Da barawo anan gidan balle ince kwata kwatama daga ni sai yaya sultan, kodai shine ya Dauka zai dubu Abu? Mikewa tai ta nufi dakin nashi, tai sallama tare da shiga, yana tsaye yana balle Ma ballin rigar suit,uhmmm yaya sultan banga wayata shine nace ko ka gani? Me kike nufi ni barawone KO me? Aa yaya sultan ba haka bane bafa kawai tambayar ka nayi fa, uhmmm nina dauke ai dama wayar ni naba momy tai wani dauka ta baki, hawaye ta Fara Dan Allah yaya sultan ka bani wlh Abu zan nuna maka Dan Allah tai kasa Irin rokan nan, ganin yadda tai duk sai yaji tausayinta ya bude drower ya dakko gashi nan, sim Da memory dinki yana kan bed side drower dinki, karbar wayar tai ta fice Da sauri Dan tasan a kan memory zai mata video,bincike take sosai iya bincike bata ganiba duk hankalinta ya tashi shikenan sultan ya jika mata aiki yanzu ya zata Yi kawai zama tai duk dube dubenta iya sim Din ta gani itta bata san sim din tafi San memory din, sultan ganin Ya gama cin abincin bata sakkoba hakan yasa yai sama zuwa dakinta,.
Kuka yaga tanayi, karasawa kusa Da itta yayi ya zauna me kuma ya faru? Maye kuma na kuka anan, yanzu Dan Allah Yaya abun dakai ka kyauta kenan Dan ka cire mun memory gashi yanzu banga shiba duk fitar darena ya tashi a banza kenan? Fisabillah gashi kaje a kurarren lokaci baka abun Da nake San ka ganiba yanzu me zan nuna a matsayin shaidata game da sarkin nan yanzu ya zanyi, jikin yayi sanyi yama rasa ta inda zai Fara zaiso bata hakuri Amman bazai iyaba baiga abun bada hakuri anan ba, mikewa yayi kawai ya fice, inda ta kwanta kawai kuka take abunta
By hajara Mami natty girl
[9/12, 9:09 AM] Hajaramami: 👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 72*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Saida tai kukan Mai isarta sannan ta mike taje ta shirya bangarem momy tai tafi, Da sallama ta shiga bangaren Nata, parlour sama tai tunda tasan mom bata wani saba zama anan ba, Da sallama ta shiga Tana zaune sultan na kusa Da itta dauke kai sultana tai Dan itta yanzu kawai fushi take dashi in tana ganinshi ranta baci yake koma me yake bai wuceba oho Mai,.
Aa amarya ce Da kanta kuma murmushin yake tai,sultan na kallamta sai kuma taji dadi koba komai yaga tayi murmushi dama kasa fita yai yana ganin Ya bata mata rai,.
Ina wuni mom? Lafiya qlau sultana ya fama Da amarci, murmushi kawai tayi nan Ma,mom naga Yan taya aiki na kuma gode Amman mom nace Da kin bari kawai ai zan iya aikin ni daya, aa haba taya zaai abar mutun Mai matsayi haka ba bayi abun sai ya zama na surutu aii, momy zan dinga zuwa ina miki aikin safen nan fa, Da sauri sultan ya karba wanne aiki kuma ke baki San kinn wace wannan gun ba, kallan shi tai rai bace Irin na ina ruwanka dinnan, shikenan mom Amman akwai wata kawata ki dauketa wlh kamar ni take ba babu ruwanta Allah ba abunda zai faru, shikenan ki kawota In gani, murmushin jin dadi tai, sannan ta dakko wayarta, mom ga wannan wayar kiba Mai shi kawai saboda yana bata mum rai akanta kawai ki bashi kayar shi ta fada idonta duk ya kawo hawaye, murmushi sultan yayi wato bata huce ba karar shi ta ma kawo, kallan ta momy tai sai a lokacin ta lura kamar Ma bata jin dadi, ajjiye wayan kawai sultana tai tai sama abunta Dan kuka taji ya taho mata, ta wuce dakinta kawai,.
Son ka batawa sultana rai KO? Mom wai wlh wayar na dauka na ajjiye mata sim dn shine memory ya bata shine take ta fushi kuma ni bansan hakan zai faruba Allah, tsaki mom taja kawai Dan wayar kace fisabillilahi saika cire mata, yi hakuri mom bari inje in bata hakuri ya fada tare da yin ssma, Da kallo mom ta bishi kafin ta saki murnushi duk yadda akai sultan ya fara San matarshi zata fi kowa jin dadi kuwa,.
Tura kofan yayi yaganta kwance a kan gado Tana hawaye kawai abunta, ta ina Ma zan Fara duk kawai Dan Tana fushi nabi na damu, mtswwww ba dole IN tamu ba mine da laifi,just be strong kaje ka lallabata, Hmmmm Ya sauke ajiyar zuciya kafin ya karasa bakin gadon ya zauna, wai sultana fushi kike dani naga na baki hakuri, kallan shi tai wai ya bata hakuri KO a ina Yaj hakan oho Mai, juya Mai baya tai taci gaba Da abun Da take, OK naji koma maye xan biyaki fada mun maye, wani haushin shi kawai take ji ta ina xai biyata Bayan lokaci ya kure,mikewa yayi ya koma ta dayan side din data juya ya kwanta a kan gadon suna facing juna, sosai gaban sultana ke faduwa bata San wannan moment din dake fara shiga tsakaninta Da sultan zuciyar bugawa take da sauri Da sauri, ganin Tana shirin juyawa yasa yai sauri Dan mike Ya tare Ta da duk hannun shi, inda ba zata iya juyawaba dinma, kallan shi tai maye hakan Yaya sultan plz ka matsa mana,yi hakuri kinji kiyi hakuri naji nayi laifi amun hakuri plz, kallan shi tai da ganima bai shirya fitowan hakurin ba, dama yana iya in banyi hakuri Da kaiba Yaya sultan AI ka riga ka gama dani kuma, OK naji fada mun Maye zan biya ki koma maye, no Yaya sultan ba zaka iya ba lokaci ya kure kawai ni ka matsa mum,ta fada Tana kallan hannnun nashi Da yasa ya tattare duk gefe biyun, OK indai baki fada munba hakan yana nufin kawai baki yafe ba, shiru tamai baki yafe ba ko? Ya fada tare da matsawa kusa Da itta sosai, Da sauri bugun zuciyarta ke karuwa gashi Ta kasa furta KO A ne Ma, ganin Ya matso sosai yasa Ta rufe idonta Da sauri, kallan fuskarta yayi, a zuci ya Fara magana wai sultan me xakayi zaka jawowa kanka raini ne, wata zuiyar kuma ke fada mishi shida yaxo Neman yafiya aiba zancen raini kuma, wayarshi dake aljihunshice tai ringing, Ya duba habib ne yake fada mishi client na jiranshi, OK yace tare da kashe wayan, daidai kunnen sultana ya rada mata zan wuce sai anjima sannan zan biyaki koma maye sannan ya bata kiss a kumatu kafin ya Mike ya fice
by Hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 73*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Mutuwar kwance sultana tai, itta tun jiya sultan yake sata cikin tunani me yake damunshi kuma oho, taba kumatunta tai kafin ta Saki mmurmushi kawai ta Mike zan Zuwaira zata dagaa nan Ta wuce gun Zulai suyi magana .
Tuki sultan yake Amman gaba daya zuciyar shi nagun sultana karo karo yakan sakin murmushi, tare da alkawarin dole xaiwa habib tambaya yau Dan yaji ta bakinshi, ha karma Ya isa asihitin Bayan Ya duba marasa lafiya ya karasa office dinshi ya dauki abun Da zai dauka sannan ya nufi office din habib,turawa yayi tare da sallama,habib ya amsa da murmushi saman fuskarshi, kodai amarya ce Yau ta rike ka ne? Murmushi sultan kaidai bari aboki, to ai shikenan, zama yayi ya bashi hannu suka gaisa,hmmmmm aboki tambayar ka zanyi, OK Allah yasa na sani, gyara zama yayi zama ka sani saboda kaidin gwanine wajen harkar, gyara zama habib yayi OK ina ji, sign din sosai zaka fada mun, dariya habib yasa sosai,gyara zama sultan yayi yana kallan yadda yake ta mai dariya,saida yai Mai isarsa sannan ya kalli sultan din,ka gama sultan din ya fada? Eh na gama ya fada da dariya har lokacin, OK ina jinka, aboki kodai baiwar tayi babban kamu ne? Haba mana habib dan zaka fada mun abun duniya sai Kana jamun rai, OK yanzu yadda zaai ka fada mun Mai kake ji game da itta?ni kawai ka fada mun ya ake ji, OK zakaji kana San ka Sa mutun agaba kana kallah kwata kwata baka San kaga abun yama nesa dakai sannan zakaji zuciyarka na bugawa a duk lokacin Da kuka hadu haka dai yaita bashi labari yadda zaiji, shiru sultan yayi komai Da habib ya fada yana ji game da sultana kenan na kamu Da santa kenan? Ya fada a fili kwarai kuwa,kallan shi sultan yayi yakenan zanyi aboki? Dan Allah banda dariya kaba ba abun wasa bane, OK kasan yadda zakai kawai ka koya ma sanka ta hakene abun zaizo Ma da sauki, jijjaga kai sultan yayi zan gwada Da haka sukai sallama,.
Komawa dakin ajiyar sarki yayi dan daukan cemara din Da Ya sa saboda tun lokacin daya shigo jikinshi ya bashi akwai Wanda ya shiga hakan Yasa ya dauke su abbah ya fita dasu daga masarautar gaba daya sannan Yasa cemara Dan yaga wanda yake shigowa,cemaran kawai ya dauka ya fita da yake yau yasan ba abun Da zaa gani hakan yasa yaje Da yan fada Amman yace su tsaya a waje, yana fitowa yace su tafi yanasan zuwa bangarenshi zai hutane, har bangaren nashi suka rakashi kafin suka tafi,.
Yana zuwa ya dakko laptop yai joining Da laptop ya kunnan, sultan da sultana ya gani, haka ya zauna yai watching TV din sosai ya shiga rudani dama sultana ittace waccan sultana to taya hakan ya faru?amma yadda yaga abun sultan din bai gane me take nufiba,murmushi yayi finally nakawo karshen komai shikenan zan kawar Da komai Tashi daya ban damu Da insan taya ta zauna ba,turo kofan habib yayi Da sallama hakan yasa yai saurin rufe laptop din Dan ya lura Dan nashi ya canza kwana biyu ya rasa dalili, kallan shi Habib yayi me kake yi Dady? Ba komai lafiya?tabe baki yai Dady so nake aje a Sami mahaifan Zuwaira ayi maganar auren nan Baba duk canjinann Da kake gani wlh saboda in Sami martaba agun iyeyenta kuma wlh Santa nake, saboda ya matsu yace shikenan Zanyi magana Amman sai nan da sati daya, shikenan kawai yace sannan ya fita,.
Sultana kuwa bangaren mama taje,da sallama ta shiga,bayi suka amsa suna gaidata,dai dai lokacin mama taxo, gaida sultana tai ta amsa ba laifi sannan ta sanar mata gun Zuwaira tazo, mama ta sa aka kirata suka tafi baya danyin magana,.
By hajara Mami natty girl
[9/13, 9:57 PM] Hajaramami: 👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 74*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Fita wajen sukai, kallanta sultana tai yanzu Zuwaira ya kuke ciki Da Hafiz naga duk ya canza? Tabe baki Zuwaira tai nima ban saniba bafa, OK Amman zuwaira me yasa ba zaki soshiba maybe ta wannan hanyar sai kiga Allah ya shirya shi, jijjaga kai Zuwaira tai zan duba inga, murmushin jin dadi sultana tai Amman zanfi kowa jin dadi kinga shahada zakiyi ta haka sai kiga Allah ya shirya shi, Hmmmm kawai Zuwaira tace,yauwa Zuwaira plz ki fadawa Zulai tazo gobe bangaren momy zatayi magana Da itta, me Zatai mata kuma? Aikin Da nakeyi zata dauka OK kawai sultana tace sannan suka ci gaba Da hira kafin sukai sallama,.
Sarki Da yan aikin shi zaune gabanshi, inasan a sami baiwar Da zata je bangeren matar sultan kotasan yadda zatai tasa ta fice ku kuma ku kamata sannan ku kaimun ittq gun dana ajjiye wannan sarkin a nawa San zanso hakan ta faru Dan in kashe mahaifinta a gabanta Amman kuma in hakan bazai faruba inasan tasan yadda zatai tasa mata poising a abinci taci kawai ta mutu, jijja kai dayan yayi ranka ya Dade angama Amman abun Da kake so na farko shi zaa bi za,a San yadda zaai ta fito a kamata kawai, murmurshi yayi zanso hakan kuwa ya kasance, mikewa sukai suka fice,.
Yau Sultana fushi take da sultan KO yaki KO yaso ba zata kwana adakinshiba, wanka tai bayan tayi sallar isha kafin ta saka kayan baccinta ta kwanta tare da kashe wuta,.
Da sallama sultan ya shigo parlour tare da kallan parlour komai tsafa Amman ba kowa, sama yayi zuwa dakinshi, yai wanka sannan ya fito Dan zuwa yaga KO sultana ta sauka kasa, saida Ya sauka yaga bata nan, dakinta Ya koma Ya leka yaga wutan a kashe, hakan yasa ya koma yaci abincin sannan ya koma sama dakin sultana yai zaije Ya tasheta tazo suje su kwanta, sultana najinshi Amman tai shiru kunna fitilar yayi,hakam yasa Ta rufe ido Da sauri kusa Da itta yauna yana kallanta, Shafa kanta yayi yana kiran sunanta, sultana sultana,juyi tai irin tana baccinnan, ka barni plz yaya sultan kamanta abun Da kamun kenan,tai tsaki tare da juya baya, murmushi yayi Ya mike yaje gun fridge din dake dakin Ya dakko ruwa a ruba, ya bude ta kasan ido Tana ganin Da gaske zuba mata zaiyi hakan yasa Ta mike Tana kallan shi, yaya sultan me zakai hakan, ajjiyewa yai aina dauka ba zaki tashiba, ki taso muje mu kwanta, Dan tsaki taja ba inda zanje Yau a Dakina zan kwana hakama kullun kowa yai kwaciyarshi a dakin shi kallan ta kawai yake kawai burgeshi take da Tana Mai rashin kunyarma, murmushi yai naji zo muje in baki hakuri tunda fushi kike dani, tsaki taja tare da kwanta ta juya Mai baya, OK Ya fada tare da mikewa yaje Ya kashe wutan dakin Ya kulle kofa sannan ya dawo Ya hau gadon Ya kwanta, Da sauri sultana ta mike Tana kallan inda yake, yaya sultan me zakai hakan? Kwanciya zanyi mana naga dakin Matata tace ko banda laifi kuma KO? Niban yadda ba kawai kaje kayi kwanciyarka a dakinka,wlh anam zan gwana aiban Da laifi dan nayi hakan? Aa baka Da laifi Amman ni bari in sauka inbar maka kan gadon ta fada Tana shirin sauka yai saurin riko hannunta ta fada kanshi, sosai sultana ta tsorata dashi a yanzun meke damunshi kuma ta fada a zuciya, yaya sultan maye hakan plz ka Bari ta fada Tana shirin kwace kanta, juyar Da itta yayi Ya mayar Da itta Kasan ,sosai gabanta Ya Fara dukan hamshin hamshin me Yaya sultan yake shirin yi matane? A hankali Ya yara magana nace kiyi hakuri sultana KO zan biyaki abunki ko, sosai ta tsorata dashi hakan yasa tai saurin cewa na hakura plz ka Tashi yaya sultan babu kyau fa, babu kyau Dan na zauna Da Matata za muyi magana Mai mahimman ci kenan? Yaushe kuma na zama matar taka plz ka Tashi Yaya sultan, baice mata komai illah bata kiss dayai goshi sannan ya bata to both kumatunta sannan ya bata a haba sosai gaban sultana ke faduwa duk ta rasa yadda zatai gashi Ya hanata wucewa, plz yaya sultan....tun kafin ta karasa Ya Fara bata wasu kiss a lip Nata da yasa ta kasa yin komai sai runtse ido yai tare da dunkule hannu,saidai yai kissing Nata sosai sannan ya saketa Ya kwanta genta Sannan ya rada mata sweet dreams matar sultan, ittadai batace komaiba illah juyamai baya datai dan har lokacin bata jin bakinta normal gashi Ta kasa natsuwa, haka har bacci Ya dauketa inda sultan ya rungumeta,.
Kwata kwata yau sultan KO tashin darenma baiyiba
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 75*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Sarki zaune gaban su kawu sai dariya yake kamar wani mahaukaci, saida yai mai isarsa sannan ya Kalli abbahn sultana kasan wani abu?wlh na gano ta Na gano wacece yar taka kaga kuwa komai yazo karshe Ya fada yana dagamai gira, murmushin takaici Abbah yayi yanzu kan ka ganota yasa kake murna ka sani KO karshenkane yazo, hade rai yayi ai kawai karshen kune yazo badai nawaba Dan kuwa na da sati zan gama daku, ya fada Tare da mikewa Ya fice,.
Asubar fari sultana ta Fara Tashi kallan hannun sultan tai dake zagaye Da itta, kafin ta daga ido Tana kallan shi, jiya take tunowa tai saurin rufe ido me ya sami sultan kodai Ya Fara santa NE? Da sauri ta kawar Da zancen no kawai yana San yaudarata ne Da salanshi ta raya tare da shirin zare jikinta hakan Yasa sultan farkawa, Da sauri ta rufe ido dan yanzu kunyar shi kawai take yi inta tuna jiya tana zare Jikinta tai saurin ficewa daga dakin gaba daya Ma, murmushi sultan yayi kafin Ya fice daga dakin shima kasa sultana ta sauka, kallanta bayin sukai kamar batama haiyacinta, ganin suna kallan ta yasa ta koma dakinta, ganin baya nan yasa ta kulle kofan gaba daya ta shiga toilet ,.
Sultan kuwa wanka yayi kafin yai sallah,yahau shiri Dan yau Da safe zaije asibiti zaiyi wani aikine,. Yana gamawa Ya nufi dakin sultana, Da sallama Ya shiga, hakan yasa ta Mike da sauri daga gaban madubi duk ta baza kanta dan kuwa tajewa take zata gyara tayi wanka tasa kayanta kwalliyane kawai bataiba,.
Kallan yai kafin yai murmushi Ya ajjiye kayan hannunshi Ya nufi inda take,duk ta tsotara kawai dakewa take ta kasa matsawa daga gun, karbar comb din hannunta yayi kawo in tayaki ,Da sauri taja baya bana so Amman taki yadda su hada idoma, karbar comb yayi Ya Fara taje mata nifa ban ganeba naga sai wani sasanne kai kike KO lafiya, ya fada Tana kallan ta,batace mai komaiba illah juyar Da kai kawai Da tai ,ajjiye comb din yayi sannan ya dauki ribbon ya daure mata kai, An gama anya ba za,a rage wannan gashinba indai yana takurawa Matata, batace komaiba illah wucewa datai tare da fadin thanks sannan ta dauki dankwalinta tasa, daukan kayanshi yayi kafin Ya kalli agogan shi 6:30 Yau da safe zan wuce basai nayi break bama kinji ina Da wani aiki,a dawo lafiyq Allah ya bada Sa,a murmushi yayi Dan yaji dadin maganar na gode Ya fada tare da ficewa,.
Gun motocinshi Ya nufa Ya dauki wacce zai dauka sannan ya fita daga masarautar, abakin hanya Ya hadu Da wani abokinshi hakan yasa ya tsaya Dan su gaisa, suna tsaye yaga wata motar masarautar tazo ta wuce Da wani fuskarshi a rufe kallan motan yayi har ta wuce jikinshi bai kwanta maiba hakan yasa ya yayi sallama Da abokin nashi Ya shiga mota yabi Bayan waccan motan, sunyi tafiya kafin yaga motan tayi parking a wani uncompleted gida,gaba sultan yayi saboda kar a gane shi Yai parking sannan ya dawo Da kafa ,kallan gidan yayi babbane sosai sannan ya shiga,.
Tafiya yake baisan inda yake saka kafarshiba to ina mutumin yaje,.
Sarki kuwa abinci Ya kawo masu Dan yace yanzu shi zai dinga kawowa saboda suyi bankwana .
Sultan dake tafiya jin ana magana yasa yai labe sarki ke fadin ai kasheta zanyi Na aika asan yadda zaai a Sa Ta fito indai hakan yaki faruwa kawai asa mata poison a abinci, zaro ido sultan yayi to wa sarki yasa a kashe, kallan Da wanda yake magana yai idonshi Ya sauka kan abdulsalam, a dan razane yaja baya tare da fadin uncle abdulsalam, Da sauri Ya juya Ya fuce.
By hajara Mami natty girl
[9/14, 8:59 AM] Hajaramami: 👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 76*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Mota ya koma zauna duk Ya shiga rudani wai dama uncle yana raye ku kuma aljanune suka bude Mai ido KO fatalwarshi Ya gani, no Amman gashi naga daddy agun har yana Mai magana wannan real ne to taya akai dama bai mutuba daddy Ya buyeshi kenan,gudun kar daddy Ya fito Ya ganshi yasa ya tada motan Ya tafi, haka yaje asibitin kowa kuwa yazo Dan meeting zasuyi, karasawa gunshi habib yai Ya bashi hannu suka gaisa, ya amarya, Hakan yasa sultan yin murmushi, aboki you look same how kodai amarya ta bata maka raine? No aboki wlh ba haka bane, aboki dama mutun yana iya mutuwa sannan ya dawo KO kuma wai Da gaske dama akwai fatalwa, zaro ido habib yayi subhanallah ba wani fatalwa a duniyar nan sai IN mutun Ya mutu kadinga mafarki dashi Amman there no something like ghost, ka gane batun mutun Ya mutu kuma dawo babau saidai indai dama can bai mutunba,ammma kai kuwa maye namun wadannan tambayoyin, hmmmm aboki Wanda nake tunanin Ya mutune yau na ganshi kuma a raye har yana magana da baban Hindu abun yaban mamaki fa aboki since wajen 19years kaga yadda ya koma Annman a hakan Kana iya ganin kamannin shi I am so shock aboki, to Allah mai iko, bari in mun fito zamuyi magana a kai,, Da haakan suka shiga meeting din KO was wajen meeting din Ma hankalinshi kwata kwata baya jikinshi kawai yana zaunene,.
Sultana kuwa Bayan Ta gama abun Da take ne ta fito parlour zataje bangaren momy, anan taga sabuwar baiwa, abayinta nada wata ta duka ta fara mata bayani, wannam daga wajen sarki take shiya kawota amatsayin baiwar Da zata dinga tayaki wasu aiyukan, kallan ta sultana tai waye Ya kawota baku fada inda bayiba kumama bana San da yawa zan iyayin komai Da kaina, Matar ce tai saurin karba, ranki ya Dade aiba ta haka bane dolene ake ba KO wannne bangare baiwa kuma dole suke karba saboda daga masarauta ne koda kina Da wani sakon Da kike San akai masarauta shine aikin mu, kallan ta sultana tai kwata kwata batasan bayi Da yawa gashi Matar Ma bata mataba, ganin irin kallan Da sultana ke mata yasa tai kasa Da kai tare da fadin innayi laifi tuba nake ranki Ya dade sunana marka, ganin matar tayi giving up ( sarrander )yasa sultana sakin fuska na gode marka Allah ya bamu zaman lafiya, Tana kaiwa nan Ta Fara tafiya Dan ficewa,baiwa daya ta biyu bayanta dan rakata bangaren momy din haka har suka isa,.
Da sallama ta shiga wannan lokacin momy na parlour farko,da murmushi ta karasa ta durkusa ta dauki gaisuwa sannan ta zauna kusa Da kafar momy din haka sukai ta hira daga karshe sultana ta shiga kitchen dan tace yau itta zatai mata girkin safe, Da taimakon bayin bangaren ta gama ta saka Tray sannan tai saman parlour dan lokacin momy ta koma sama,.
Ajjiye abincin a dining sultana tai sannan ta shiga ta fadawa mom Ta gama hakan yasa suka fito tare, zama momy tai Tana cin abinci sannan sultana take sanar Da itta zuwan Zulai, shikenan in tazo za muyi magana,.
Bayan sun fito daga meeting ne shi sultan duk Hankalinshi yayi gida, hakan yasa habib bai tsayar dashiba yaka Kama hanyar zuwa masarautar, yana parking bangaren momy ya nufa yai sama, ganin bata parlour yasa yai dakinta Da sallama Ya shiga, sultana na kwance akan duguwar kujeran dake dakin tana danne danne a phone dinta, zama yayi kusa Da momy, momy sannu Da gida,yauwa son Yau ban ganka Da safe ba, wlh mom meeting ne damu shi yasa banshigoba wlh har yanzu ban wani yi karyawar kirkiba, eyyya ga matar ka can saita maka girki, kallan sultana yai wacce ta juya mai baya bata San su hada ido murmushi yai, mom wai dama mutun yana mutuwa Ya dawo kuma ne? Ko kuma fatalwa gaskiyane, murmushi tai saidai indai dama bai mutunba kuma ba wata fatalwa,me Yasa kkake wannan tunanin, idonshi NE Ya kada mom uncle abdulsalam fa na gani kenan bai mutuba kenan? Mikewa mom tai son ban gane me kake nufi bafa wlh mom uncle abdulsalam naga ni shiya buyeshi kenan,.jijjiga kai Mon tai anya kuwa ba gamo kaiba sultan
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 77*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Zauna kawai yayi baice komaiba, sultana ta mike ta kawo Mai abinci duk sai taje jin ba dadi Da taga baya walwala,haka yaci abincin sannan ya Tashi ya tafi bangaren su Dan akwai abun Da yake San zai duba, kallan sultana yai itta yake San yaiwa magana so yake tazo suje tare kuma baiga alamar tana San tashiba, kallan mom yayi kafin Ya kalli sultana kizo muje inasan zan nuna miki wani abune, kallan mom tai momy ma hankalinta baya kansu, mikewa tai tabi bayan shi suka wuce,.
Suna zuwa Da sallama marka dake tsaye bakin kofar kitchen ta karaso ta zube tana kwasar gaisuwa agun sultan, kallan sultana sultan yayi wace wannan kuma? Wai sabuwar baiwace daga masarauta aka aikota, ko ina aka kai KO iya nan ne Ya fada yana kallan marka din aa ai dama sudin suna dasu nan dinne dai babu, tsaki yaja kije masarautar kice bama bukatar wata baiwa indai ina San zan aika sako Da kaina zanje, afuwa nake nema ranka Ya dade Amman yace kar in sake inbar bangarennnan, hade rai yayi tare da fadin get out plz, ganin Yadda fuskarshi ta koma yasa ta Tashi ta tafice,. Sama yai sultana tabi bayanshi, kowa Ya shiga dakinshi,.
Sultan kuwa kwantawa yayi yana tunani kowa sarki yasa a kashe, sultana ta fado mai kodai su sultana ta gani a dakin ajiya, no basu bane wannan aljanune,.
Haka yaita ta tunani har wajen sallahn mariba sannan ya tashi Ya wuce masallaci,.
Sultana kuwa hakan yafi mata kowa yai zamanshi a nashi banganren haka itta taita tunani KO ina su abbah suke yanzu Allah masani,.
Bayan sallar isha sultan yana tafiya yaji muryar Dady na kiranshi hakan yasa ya juya yana kallan daddy din gabanshi Ya fadi, bayi yace subasu gu hakan yasa suka bar gun,kalllan sultan yayi Nice akawo baiwa ka kureta bansan daliliba? Gyara tsayuwa sultan yayi saboda tsaro ban yarda Da itta bane saboda inaji akwai abun Da ake kullawa, kallan shi daddy yai kardai yasan me yake aikatawa, ban gane me kake nufibafa sultan, karka damu daddy ina binciken masu San kawo karshenmune ba wani abun daga hankali bane, sai safe Ya fada tare dayin gaba, Da kallo daddy Ya bishi kafin Ya gaba,.
Da sallama sultan ya shiga parlour lokacin bayin Sun tafi sultana ke zaune a parlour tana kallo, amsawa tai Tana kallan shi Ya zauna kusa Da itta tare da fadin washhhh na gaji sosai, mikewa tai ta nufi dining ta debo mashi abinci a tray ta kawo Mai ta ajjiye sannan ta zuba Mai, murmushi yai tare da fadin thanks, tai murmushi kawai hakan Ya gama cin abinci sannan ya zauna ayi kallan dashi.
Film din India ne na soyayya mata Da mijine ke soyewa hakan yasa sultana kasa nutsuwa duk tabi ta takura bata San kallan film din soyayya a gaban wasu duk kunya take ji, kallanta yayi ganin kamar ba a nutse take ba ,mutsawa kusa Da itta yai wannan film din Da ake kallo soyayyar Da zaa mun ake koya, abun saiya bata kunya yanzu zaice mata yar iska mikewa tai zata bar gun yai saurin riko hannunta Ya dawo Da itta, yaya sultan bacci nake ji, OK kije inasan ganin ki inkin gama akwai abun Da zan nuna miki, OK Ta fada tare da Tashi tai sama shima kashe wutan yayi yai sama,.
Wanka yayi Ya shirya Ya zauna yan jiranta,.
Itta kuwa sultana Data gama kamar ba zataba sai kuma ta tashi tasa hijab dinta tayi dakin,.
Da salllama, Ya amsa tare da nuna mata kusa dashi, dan can gefe ta zauna hakan yasa ya matsa kusa Da itta, hutan hannunshi Ya nuna mata wannan kika ga a dakin ajiya KO? Karbar hutan tai hutan abbah ta shine Yaya sultan ka ganshine,?
By hajara Mami natty girl
[9/14, 3:49 PM] Hajaramami: [9/14, 3:47 PM] Hajaramami: 👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 78*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
[9/14, 3:48 PM] Hajaramami: Duk tabi ta dameshi a ina kasanshi plz ka ganshine, karban hutan yayi Ya ajjiye a gefe sultana a ina kika sanshi fada mum?shiru tai tana tunanin me zatace mai, uhmmm ranarne na shiga dakin ajiya dana ganshi shida wani shine namai alkawarin zan fitar dashi a gun shine Na maka karya Da wannan wasikan to da muka je bamu gansuba shirt. Gashi kuma akwai record danai nasan sarkin kune Ya kullesu ina Da shaida a Cikin record din Amman ka batar mun ya zanyi, kallan ta yake Yi karban hutan yayi Ya juyo Da ittta tare da rike hannunta sultana kinsan waye wancan,? Uncle dinane fa kanin babane Ya dade Da mutuwa yajen shekara 19 kenan Amman yau na ganshi Da idona sultana da idona na ganshi abun yaban mamaki bansan bai mutuba ashe dama shike aiko Da wasika ban saniba sultana, Yaya sultan yanzu yana raye ne ka ganshine? Yana raye sultana a wani gu daddy Ya kaishi unguwar gaba Da tunfure can karshen garine bama a fiya zuwa gun ba Ma kuma gida dayane a gun shima incomplete ne, rirrike hannunshi tai Dan Allah Yaya sultan muje in gansu plz plz Dan Allah, no sultana ba yau zan kijeba gobema ni kadai zanje bana San ki biyuni zanje in fito dasu Da kaina kinji, hawaye ta Fara Ta rungumushi Tana kuka Dan Allah Yaya sultan zanje in gansu kaji kasan yadda nake ji kuwa, jijjaga bayanta yayi haba sultana keda baki Da relationship dashima nifa ina Da relationship dashi Amman ban damu kamar hakan ba hana addua kawai zakiyi kinji, daga kai Tayi alamar taji, good Ya fada tare da dagota ki kwanta Bari IN mayar Da hutunab na, zare joints tai ta koma ta kwanta Amman hawaye kawai take,har Ya ajjiye yazo Ya kwanta tare da kallan bayanta jin kamar kuka take hakan yasa ya matsa kusa Da itta tare da juyo Da itta, ai bazaki dena kukan ba? Nifa ban ganeba KO akwai abun Da kike buyemun ne?, Da sauri ta jijjaga kai alamar aa, murmushi yayi I will find it by myself ai, kokarin juyawa take Dan bata San abun Da ya faru jiya yauma Ya kara faruwa, Da sauri Ya rikota Maye hakan kuma ana zaune lafiya zaki Fara, yaya sultan ka sakeni kaida ba sona kake ba ka dinga mun haka niba Bana so, ka manta nidin baiwace? Wayece miki bana sanki inma ke baiwace ai Matata tace KO, uhmmm naji Amman plz ka sakeni,matso Da itta yayi sosai hakan yasa tai saurin rufe ido gabanta Na dukan hamshin hamshin, kiss Ya bata a goshi kafin Ya ce good night ayi bacci lafiya tare da mafarkina, plz yaya sultan ka bazan iya bacci a hakaba ai, no bazan sakiba wlh ya rage rikon dayai mata nasan Da adddare ina bacci zaki iya ficewa ban saniba ai, murmushi kawai tai Tana tunanin me Ya canza sultan a wannan lokacin kwata kwata bata gane kanshi yanzu, a haka kuwa suka kwana Tana ta tunanin ta yadda zatai gobe taje taga abbahn ta,.
Sarki ke jeka ka dawo adakinshi Ya zaiyi Ya Sa sultana ta fito gobe, gobe kawai yake San ya kasheta Ya huta, murmushin jin Dadi yai sannan ya dakko wayarshi Ya kira marka, gobe inasan Da zarar kinga sultan ya fita kije kice sultan ya aiko a dauki sultana akaita asibita zan aiko mai daukan Nata kinji, sannan a wannan lokacin nake San ki kira police Bayan an shigar Da itta Da minti goma kafin nan Na gama dasu kina ji, eh Na gane yadda kace haka zaai ta fada with due respect, sannan ta kashe wayan,.
Washe gari Da asuban fari sultan ya tashi Ya tafi masallaci sannan ya dawo saida Ya biya bagaren momy acan Ya zauna har wajen 8:00, mikewa Sultan yayi mom zan wuce, yauwa mom ina wannan sarkan dana taba siyowa nace ki ajjiye lokacinta zaiso itta nake San ki dakko, murmushi tai lokacin sultana NE yazo kenan? Murmushi kawai yayi,ta sannan ta Tashi ta dakko Mai ta mika Mai, sarka ce ta gold sai walwali take,.
Karba yayi Ya fice,.
Sultana kuwa Bayan Ta yi sallah ta koma ta kwanta sai wajen 9:00 ta Ta Tashi, wanka ta shiga Tana wanka ta fito daure Da towel, tana gaban madubi sultan ya shigo Da sallama' mikewa tai Tana kallan shi, murmushi yai mata tare da ajjiye kayan hannun shi Ya karasa gunta kasa tai da kai tana wasa Da zoben hannunta, uhmmm kan naki a jike? Ya fada yana gyara gashin kan nata, sultana zan tafi aiki daga nan zan biya wani gun karki sake ki fita kinji, daga kai tayi sarkar dake hannun shi Ya dakko a kwalinta gift zan baki sultana, kallan kwalin tai shima kanshi kwalin abun kallone balleh abun dake ciki kallanshi tai kallan irin Tana mamaki dinnan,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 79*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Daga mata gira yai alamar Da gaske, sannan ya bude idonta Ya sauka kan sarkar dake sheki, dasauri ta kalleshi, ciro sarkar bari insa miki, matsawa yai kusa Da itta Ya tattara gashin kan Nata baya, har hancinsu Na haduwa sultana kuwa mutuwar tsaye kawai tayi lallai sultan ya canza kodai Santa yake ne? Saka mata yayi sannan ya dago yana kallan ta kinga yadda ta zauna a wuyanki ki kuwa? Itta dai batace komaiba juyar da itta yayi tana kallan madubi tare da rungumeta ta baya kalli kiga matar sultan, daga ido tai Tana kallan sarkan sarkan tayi mata kyau sosai, murmushi tai tare da Sa hannu tana Shafa sarkan, a hankali ta furta Na gode Yaya sultan, dai dai kunnenta Ya rada mata no need my wife, runtse ido tai dan itta daya tasan yadda take ji, IN fada miki wani abu sultana, daga kai tayi alamar eh, a hankali Ya furta a I LOVE YOU SULTANA my wife inasa sanki sosai,da sauri ta bude ido Tana kallan shi ta Cikin madubi idonta Ya kada hawaye kawai take San Yi ta kuma rasa Na maye ne,no my wife banda kuka fa inna dawo zan miki magana sannan karfa ki fita juyo Da itta Yayi yana goge mata hawayen dukda bansan Na maye bane Amman Allah yasa na murnar Na furtane, murmushi tai hade Da dan kuka tai kasa dakai, shima murmushin yayi Ya dago Da fuskarta Ya Fara bata wani kiss bata hanashiba kuma ta rasa dalilin dayasa bata hanashinba (nidai nace kodaisultana nanma ta kamune? ) .
Dagowa yayi Yana kallan yadda ta rufe ido, murmushi yayi tare da fadin zan tafi, bata kalleshiba illah daga kai datai, kayanshi Ya dauka Ya fice kawai,.
Da kallo tabi bayanshi kafin ta Saki murmushi tare da juyawa Tana kallan sarkar daya Sa mata, wardrobe taje ta dakko kayan Da zata saka tasa sannan ta sakko kasa,.
Bayin ta gani suna aikinsu GA breakfast nan a kan dinning, zama tai taci sannan ta koma ta dauki Hijab dinta ta nufi bangaren momy a hanya suka hadu Da Zulai tare suka shiga tai introducing nata GA momy sannan sukai ta hira har wajen 11:00 itta Da momy, sannna tace zataje bangarenta sukai sallama Da momy ,.
Shigarta bangaren su keda wuya saiga marka ta shigo, nan take sanar mata wai sultan ya aiko a dauketa za,a kaita gun aikinshi abun Ya bata mamaki Amman saita hada hakan kan wani surprise zai mata, fuskarta kawai ta gyra ta sakko tabi Bayan marka ta nuna mata motan sannan ta tafi, saida ta tabbatar su sultana Sun tafi sannan ta shiga a daidaita tabi bayansu,.
Sultan kuwa yana fita wanna be gun ya nufa Dan yace yau zai dakko su abbah din, kuma yana fatan Ya hadu Da daddy dan inya nunamai wani abun Ya hadashi Da yan sanda in kuma yabi a hankali Ya bishi shima a hankali,.
Haka Ya shiga gun,
A wannan lokacin kuma su sultana sun karaso,.
Sarki Ya kira marka yace Da zarar 11:40 tayi ta kira police, Da haka sukai sallama,.
Marka Da taga wayanta agogan baya tafiyq dai dai ta tambayi mai a dai daita yace mata 11:30 abun Ya bata mamaki kodai sarki Ya rage Time dinne, tabe baki kawai tai,.
Sultana kuwa shiga take bata San inda take sa kafa ba,.
Sultan yana shiga yaga Da Daddy, kallan shi Da mamaki sarki yayi Ashe masu nutuwar nada yawa Ya fada yana murmushi, ba wannan bane a gabana ba kawai kaban uncle in tafi ta hakan zan iya rufa maka asiri, tsaki sarki yaja tare da jan gun din hannunshi ni gara in gama Da kai kawai in huta,.
Sultana dake bayanshi tai wani zuro zuro tai saurin daukan karfen kusa Da itta Da kwala Mai nan take Ya fadi yana rike Da kanshi, Da sauri ta karasa gun abbahn ta tana fadin abbah shi kuma sultan yai gun kawu Dan kunce shi dai dai lokacin kuma suka fara jin jiniya Na motan yan sanda, mikewa Daddy yai dukda yana jin jiki Ya dauki bindigar takan sultana zai Fara, bai jira wata wataba, ya saki alburushin bindigarshi wannan lokacin kuma yayi dai dai Da juyowar sultana, hakan kuma yayi dai dai Da fara shigowar police hakan yasa sarki harbin hannun shi shima, yai kasa irin dashi aka harba dinnan,.
Ku biyuni
By hajara Mami natty girl
Duk tabi ta dameshi a ina kasanshi plz ka ganshine, karban hutan yayi Ya ajjiye a gefe sultana a ina kika sanshi fada mum?shiru tai tana tunanin me zatace mai, uhmmm ranarne na shiga dakin ajiya dana ganshi shida wani shine namai alkawarin zan fitar dashi a gun shine Na maka karya Da wannan wasikan to da muka je bamu gansuba shirt. Gashi kuma akwai record danai nasan sarkin kune Ya kullesu ina Da shaida a Cikin record din Amman ka batar mun ya zanyi, kallan ta yake Yi karban hutan yayi Ya juyo Da ittta tare da rike hannunta sultana kinsan waye wancan,? Uncle dinane fa kanin babane Ya dade Da mutuwa yajen shekara 19 kenan Amman yau na ganshi Da idona sultana da idona na ganshi abun yaban mamaki bansan bai mutuba ashe dama shike aiko Da wasika ban saniba sultana, Yaya sultan yanzu yana raye ne ka ganshine? Yana raye sultana a wani gu daddy Ya kaishi unguwar gaba Da tunfure can karshen garine bama a fiya zuwa gun ba Ma kuma gida dayane a gun shima incomplete ne, rirrike hannunshi tai Dan Allah Yaya sultan muje in gansu plz plz Dan Allah, no sultana ba yau zan kijeba gobema ni kadai zanje bana San ki biyuni zanje in fito dasu Da kaina kinji, hawaye ta Fara Ta rungumushi Tana kuka Dan Allah Yaya sultan zanje in gansu kaji kasan yadda nake ji kuwa, jijjaga bayanta yayi haba sultana keda baki Da relationship dashima nifa ina Da relationship dashi Amman ban damu kamar hakan ba hana addua kawai zakiyi kinji, daga kai Tayi alamar taji, good Ya fada tare da dagota ki kwanta Bari IN mayar Da hutunab na, zare joints tai ta koma ta kwanta Amman hawaye kawai take,har Ya ajjiye yazo Ya kwanta tare da kallan bayanta jin kamar kuka take hakan yasa ya matsa kusa Da itta tare da juyo Da itta, ai bazaki dena kukan ba? Nifa ban ganeba KO akwai abun Da kike buyemun ne?, Da sauri ta jijjaga kai alamar aa, murmushi yayi I will find it by myself ai, kokarin juyawa take Dan bata San abun Da ya faru jiya yauma Ya kara faruwa, Da sauri Ya rikota Maye hakan kuma ana zaune lafiya zaki Fara, yaya sultan ka sakeni kaida ba sona kake ba ka dinga mun haka niba Bana so, ka manta nidin baiwace? Wayece miki bana sanki inma ke baiwace ai Matata tace KO, uhmmm naji Amman plz ka sakeni,matso Da itta yayi sosai hakan yasa tai saurin rufe ido gabanta Na dukan hamshin hamshin, kiss Ya bata a goshi kafin Ya ce good night ayi bacci lafiya tare da mafarkina, plz yaya sultan ka bazan iya bacci a hakaba ai, no bazan sakiba wlh ya rage rikon dayai mata nasan Da adddare ina bacci zaki iya ficewa ban saniba ai, murmushi kawai tai Tana tunanin me Ya canza sultan a wannan lokacin kwata kwata bata gane kanshi yanzu, a haka kuwa suka kwana Tana ta tunanin ta yadda zatai gobe taje taga abbahn ta,.
Sarki ke jeka ka dawo adakinshi Ya zaiyi Ya Sa sultana ta fito gobe, gobe kawai yake San ya kasheta Ya huta, murmushin jin Dadi yai sannan ya dakko wayarshi Ya kira marka, gobe inasan Da zarar kinga sultan ya fita kije kice sultan ya aiko a dauki sultana akaita asibita zan aiko mai daukan Nata kinji, sannan a wannan lokacin nake San ki kira police Bayan an shigar Da itta Da minti goma kafin nan Na gama dasu kina ji, eh Na gane yadda kace haka zaai ta fada with due respect, sannan ta kashe wayan,.
Washe gari Da asuban fari sultan ya tashi Ya tafi masallaci sannan ya dawo saida Ya biya bagaren momy acan Ya zauna har wajen 8:00, mikewa Sultan yayi mom zan wuce, yauwa mom ina wannan sarkan dana taba siyowa nace ki ajjiye lokacinta zaiso itta nake San ki dakko, murmushi tai lokacin sultana NE yazo kenan? Murmushi kawai yayi,ta sannan ta Tashi ta dakko Mai ta mika Mai, sarka ce ta gold sai walwali take,.
Karba yayi Ya fice,.
Sultana kuwa Bayan Ta yi sallah ta koma ta kwanta sai wajen 9:00 ta Ta Tashi, wanka ta shiga Tana wanka ta fito daure Da towel, tana gaban madubi sultan ya shigo Da sallama' mikewa tai Tana kallan shi, murmushi yai mata tare da ajjiye kayan hannun shi Ya karasa gunta kasa tai da kai tana wasa Da zoben hannunta, uhmmm kan naki a jike? Ya fada yana gyara gashin kan nata, sultana zan tafi aiki daga nan zan biya wani gun karki sake ki fita kinji, daga kai tayi sarkar dake hannun shi Ya dakko a kwalinta gift zan baki sultana, kallan kwalin tai shima kanshi kwalin abun kallone balleh abun dake ciki kallanshi tai kallan irin Tana mamaki dinnan,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 79*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Daga mata gira yai alamar Da gaske, sannan ya bude idonta Ya sauka kan sarkar dake sheki, dasauri ta kalleshi, ciro sarkar bari insa miki, matsawa yai kusa Da itta Ya tattara gashin kan Nata baya, har hancinsu Na haduwa sultana kuwa mutuwar tsaye kawai tayi lallai sultan ya canza kodai Santa yake ne? Saka mata yayi sannan ya dago yana kallan ta kinga yadda ta zauna a wuyanki ki kuwa? Itta dai batace komaiba juyar da itta yayi tana kallan madubi tare da rungumeta ta baya kalli kiga matar sultan, daga ido tai Tana kallan sarkan sarkan tayi mata kyau sosai, murmushi tai tare da Sa hannu tana Shafa sarkan, a hankali ta furta Na gode Yaya sultan, dai dai kunnenta Ya rada mata no need my wife, runtse ido tai dan itta daya tasan yadda take ji, IN fada miki wani abu sultana, daga kai tayi alamar eh, a hankali Ya furta a I LOVE YOU SULTANA my wife inasa sanki sosai,da sauri ta bude ido Tana kallan shi ta Cikin madubi idonta Ya kada hawaye kawai take San Yi ta kuma rasa Na maye ne,no my wife banda kuka fa inna dawo zan miki magana sannan karfa ki fita juyo Da itta Yayi yana goge mata hawayen dukda bansan Na maye bane Amman Allah yasa na murnar Na furtane, murmushi tai hade Da dan kuka tai kasa dakai, shima murmushin yayi Ya dago Da fuskarta Ya Fara bata wani kiss bata hanashiba kuma ta rasa dalilin dayasa bata hanashinba (nidai nace kodaisultana nanma ta kamune? ) .
Dagowa yayi Yana kallan yadda ta rufe ido, murmushi yayi tare da fadin zan tafi, bata kalleshiba illah daga kai datai, kayanshi Ya dauka Ya fice kawai,.
Da kallo tabi bayanshi kafin ta Saki murmushi tare da juyawa Tana kallan sarkar daya Sa mata, wardrobe taje ta dakko kayan Da zata saka tasa sannan ta sakko kasa,.
Bayin ta gani suna aikinsu GA breakfast nan a kan dinning, zama tai taci sannan ta koma ta dauki Hijab dinta ta nufi bangaren momy a hanya suka hadu Da Zulai tare suka shiga tai introducing nata GA momy sannan sukai ta hira har wajen 11:00 itta Da momy, sannna tace zataje bangarenta sukai sallama Da momy ,.
Shigarta bangaren su keda wuya saiga marka ta shigo, nan take sanar mata wai sultan ya aiko a dauketa za,a kaita gun aikinshi abun Ya bata mamaki Amman saita hada hakan kan wani surprise zai mata, fuskarta kawai ta gyra ta sakko tabi Bayan marka ta nuna mata motan sannan ta tafi, saida ta tabbatar su sultana Sun tafi sannan ta shiga a daidaita tabi bayansu,.
Sultan kuwa yana fita wanna be gun ya nufa Dan yace yau zai dakko su abbah din, kuma yana fatan Ya hadu Da daddy dan inya nunamai wani abun Ya hadashi Da yan sanda in kuma yabi a hankali Ya bishi shima a hankali,.
Haka Ya shiga gun,
A wannan lokacin kuma su sultana sun karaso,.
Sarki Ya kira marka yace Da zarar 11:40 tayi ta kira police, Da haka sukai sallama,.
Marka Da taga wayanta agogan baya tafiyq dai dai ta tambayi mai a dai daita yace mata 11:30 abun Ya bata mamaki kodai sarki Ya rage Time dinne, tabe baki kawai tai,.
Sultana kuwa shiga take bata San inda take sa kafa ba,.
Sultan yana shiga yaga Da Daddy, kallan shi Da mamaki sarki yayi Ashe masu nutuwar nada yawa Ya fada yana murmushi, ba wannan bane a gabana ba kawai kaban uncle in tafi ta hakan zan iya rufa maka asiri, tsaki sarki yaja tare da jan gun din hannunshi ni gara in gama Da kai kawai in huta,.
Sultana dake bayanshi tai wani zuro zuro tai saurin daukan karfen kusa Da itta Da kwala Mai nan take Ya fadi yana rike Da kanshi, Da sauri ta karasa gun abbahn ta tana fadin abbah shi kuma sultan yai gun kawu Dan kunce shi dai dai lokacin kuma suka fara jin jiniya Na motan yan sanda, mikewa Daddy yai dukda yana jin jiki Ya dauki bindigar takan sultana zai Fara, bai jira wata wataba, ya saki alburushin bindigarshi wannan lokacin kuma yayi dai dai Da juyowar sultana, hakan kuma yayi dai dai Da fara shigowar police hakan yasa sarki harbin hannun shi shima, yai kasa irin dashi aka harba dinnan,.
Ku biyuni
By hajara Mami natty girl
[9/15, 8:18 AM] Hajaramami: 👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 80*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Still sultana tai a tsaye saida nerves nata suka kaiwa brain Nata sannan brain Ta bata response na harbin Da akai mata nan take taji wani zafi ta taba gun jini ta gani, abbahn ta dake bayanta yai saurin rikota ganin layi Na Neman daukarta, shikuwa sultan ya kasa ta buka komai yama rasa wannne brain dinshi zata bashi, Da sauri Ya karasa gun Nata yai saurin rikota ganin tana yin kasa,idonta Ya kada yayi jajur sai lumshe su take, jijjaga sultan yake yi yana kiran sunanta, Da sauri Ya dakko wayarshi Ya kira habib ka aiko min da ambulance yanzu Yana kaiwa nan ya kashe wayan .
Police da suka shigo sudai basuga Wanda yai harbin ba Amman sunji kara kuma baici ace har Wanda yai harbin Ya gudu ba sannan GA gun din a can wani gun da ban, Da sauri daddy Ya mike Ya nufi police din sai marka dake bayan su, wlh ya gudu Wanda yai harbin Ya gudu tacan Ya nuna musu window dake dauke Da Jimi tacan yabi kuma naso in harbeshi Amman inajin Na sameshi shiyasa Ya zubar Da jininshi a can din, kallan shi kawai abbahn yake yama kasa magana lallai yayan nashi babban mayaudarine, sultan kuwa bai San abun Da ake ba, karasawa gun su sultan police din yayi,ittama Ya harbeta ne?budar bakin Da abbah zaiyi dan yayi magana yaji muryarshi taki fitowa abun Ya bashi mamaki, yana San yai magana Amman taki fitowa, kallan gun da daddy yake yai yaga yana Mai wani murmushi, juyar Da kai kawai abbah yayi yai shiru, xukunnawa police din yayi kusa Da sultan dake hawaye yana kiran sultana,dafa kafadarshi police din yayi karka damu koma waye zamu gano shi, kallan police din yayi wannne ganoshi zakuyi banda ku tafi dashi kawai, wa zamu tafi dashi? Gashi can yai nuni Da daddy, Da sauri Daddy Ya karba karka damu office yana cikin shock ne saboda yaga nai harbi dole Ya dauka nina harbeta karka damu komai zaiyi normal,.
Jin karan ambulance yasa sultan baibi ta kanshiba Ya dauki sultana a hannu suka fito inda daddy yabi bayansu, kusa Da marka yaje taya zaai ki kiramun police a cikin 5min haba keda sai 30 kafin ki kira, ranka Ya Dade kaifa kace Da 40 zan kira, OK dakko wayarki karfe nawaa yanzu?data duba 12:00 har tayi shi kuma a tashi wayan a lokacinma 11:40 din tayi, nan Ta gane agoganta ne baya tafiya dai dai,.
A ambulance din Sultan ya sata, ganin daddy nasan shigowa yasa Ya sha kwalarshi wlh ba inda zaka shiga kuma wlh sai ma shiga court da kai mugu azzalumi, Da kyar police din suka kwace Da daddy sannan aka dauki daddy a motanshi aka tafi dashi hospital,.
Ana zuwa akai emergency da sultana, su abbah kuwa akai wani gun dasu Dan duba lafiyar su gashi kuma Sun kasa magana . Tare da sultan suka shiga emergency Dan cecu rayuwar sultana,.
A masarauta kuwa marka taje ta sanar hankalin su hafix Ya tashi Da ce musu akai garin sarki yai taimako An harbeshi,..
Momy haka aka ce musu an harbi sultana, a gigice momy ta shirya itta Da Zuwaira Da Zulai dan cewa sukai sai sunje haka suka Kama hanya,.
Da aka cirewa sultana bullet din numfa shinta yaki tsaya duk sultan yabi Ya daga musu hankali hakan yasa suka fita dashi a baki kofa Ya ga momy Ya rumgunmeta tare da fashe mata Da kuka
By hajara Mami natty girl
[9/15, 6:40 PM] Hajaramami: 👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 81*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Rumgume momy yai yana kuka sosai kamar wani yaro, momy sultana mutuwa zatai ta barni wlh nunfashinta yaki tsayawa mom ya zanyi, dagoshi mom tai ba zata mutuba kaita mata addua kaji ka daina kira mata mutuwa kaji son, daga kai yayi yana hawaye su Zuwaira kuwa tsayawa suka suna kallan yadda sultan ke kuka kamar wani yaro, zama tai ta zaunar dashi, Ya akai abun Ya faru kuma sultan?mom duk laifin sultana nane dana fada mata cewa ga abun Da na gani Da zan fita saida nace karta fito bansan me ya fito Da ittaba abun mamaki har gun wai ta sani bansan taya tai hakan dana fada Mata gun bai cancanci ace Ta ganeba, rike mom yayi mom uncle abdulsalam bai mutuba bafa yana raye wlh, kallanshi MOm tai da gaske sultana ta fada mun Amman ban yarda ba ashe Da gaske take abun daya kawota wannan masarautar kenan fa, mom ban ganeba, ai ba zaka ganeba, sultan Waya harbi sultana kuma?mom wlh daddy ne a gabana Amman dad Ya nuna bashi bane banda shaida tunda abbah Ya kasa magana bansan Ya zaai ba shida Wanda suke tare ya zanyi mom, Danna gashi memory da sultana tai record ya Bata nasan bazan rasa shaidaba, sarki dake baya Ya tsaya yana jin me suke cewa memory kuma Ya fada da mamaki, Hmmmm kawai yace sannan yai sallama hakan yasa sultan mikewa yana kallanshi meye kuma me ya kawo ka nan? Murmushi sarki yayi yi a hankali mana aiba abun zafi bane kasan yanzu ba Wanda zai yadda dakai Ya fada a hankali yadda ba zasujiba, murmushin takaici sultan yayi wlh saina shigar dakai kara bazan barka a hakaba kaidin wa wlh saina tuna maka asiri, wlh Hmmmm kawai daddy yace sannan ya karasa gun mom, Ya mai jiki ba laifi ta amsa Da jiran sako meke murmushi kawai yayi baice kkomaiba Da hannunshi dake dauke Da bandage,.
Sultan Ne yai magana dama ai ba zakace Allah ya bada lafiya ba tunda burinka ta mutu ni bansan Me ta tare maba kuma saina daukar mata FANSA (NOVEL DIN AISHA)hafiz dake gefe Ya matso kusa Da sultan malam ka iya bakinka dan Ma ya taimaki matar taka stupid, kallan sama Da kasa sultan yamai kai kasan abun Da ya faru NE idiot kawai, nan suka fara shirin fada mom taiwa sultan magana sannan ya daina shima Hafiz sarki Ya mai magana, fitowa habib yayi Ya sauke ajiyar zuciya faukarshi dauke Da murmushi Ya rungume sultan aboki komai yayi dai dai farfaduwarta kawai muke jira,dariya hade Da murna sultan keyi, sarki kuwa mutuwar tsaye yai yanzu duk abun Da yai ace bai kashe koda mutun dayana tsaki yaja a ranshi yana aiyana dolene Ya kashe su duk a wannan asibitin,hafix kuwa shima yayi murna Da jin an daidaita koba komai Zuwaira zatai murna hakama sultan zai daina jin haushin baban shi,.
Momy Ta karasa gun habib zamu iya shiga mu ganta? Eh mom Amman banda hayaniya, Da sauri tai gaba inda sultan yabi bayanta hakama Zuwaira, Zulai zata wuce habib Yai saurin shan gabanta za muje ki karbo abu ki kawo nan din, kallan shi tai kafin ta Kalli su Zuwaira har sun shigema, dan Allah sofa nake inganta, ai zaki ganta abun Da zaai Mata amfani zaki dakko ai, badan tasoba tabi shi,suna tafiya yake tambayarta unguwarsu ta sanar mashi Da dadalinta Na zuwa masarautar kan rashin kudi sosai ya tausaya mata yaji kuma Santa Ya kara karuwa a kanshi,.
Abu Ya dakko su drip suma Dan kawai Ya rasa me zai daukane, itta Zulai burinta taje ta gansu,.
A hankali suka shiga sultana dake kwance kam gado cikinta yaci uban bandage sai dan jini daya batata kadan nunfashi take Amman duk tayi haske idonta a rufe an baza kashin ta baya, zama mom tayi kusa Da itta ta Shafa kanta tare da Matata adddau Da fatan samun lafiya, hakama Zuwaira, sultan kuwa hawaye kawai yake shidai Baisan meya fito Da sultana Na shida yace karta fito haka su Zulai suka shigo itta ta ganta, kallan shi habib yai kaje kaga conditions din uncle fa dam doctor mb yace yana San ganin ka, jijjaga kai yayi habib Ya ajjiye abun Da zai aajjiye suka fita tare
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 82*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Da sallama suka shiga office din doctor mb, suka gaisa kafin suka zauna, kallanshi mb yayi gaskiya your patients are under critical accident, Dan wlh nayi bincike iya abun Da nagani shine nasan ansa musu poison a abinci sunci waanda yai blocking speech dinsu daga fitowa actually abun dana yanke kawai we should referred them to abroad I think it will be easy,ajiyar zuciya sultan ya sauke hakan zaai saboda I need my uncle wlh, wanne hospital kake ganin zaa kaisu? India zan tura su kawai kaje kai musu visa gobe su wuce, OK Amman Kana ganin bazan hada Da sultana ba hankalina bai kwanta anan wlh, OK as you wish wannan aikin habib ne, da haka sukai sallama kafin yaje Ya sanarwa mom yadda ya yanke ittama tafi yarda Da hakan, sannan tace Da itta zaa je Zuwaira ta nemi alfarmar Rakiya,zulai Ma haka Amman habib yasan yadda zaiyi Ya hana wai zaau yawa, itta dai Zulai duk taga yabi Ya wani takura mata hakan yasa Ta Fara hade mai rai, hafiz Da yaji bai wani musuba Dan har GA Allah yana San sultana tai Sami sauki,.
Daddy kuwa bai San abun dake faruwaba yana can yana hada yadda zaiyi, Ya kira marka kan ta nemomai wannan memory din a dakin sultana,.
Sultan zaune a dakin sultana yasakata a gaba kamar Tv, mom dake kan sallaya ta kalleshi son magariba fa tayi bakaje masallaciba gashi kaki tashi kaje kayi sallah, mom bana San barin sultana itta dayane shi yasa fa ina tsoran a kara kawo mata hari, OK ni ban iya kula Da itta bako tashi kaban gu kaje kai sallah, mikewa yayi Ya fice yana dan maganganu,.
Bayan yayi sallah Ya nufi dakin Da ajjiye su abbah Ya tura Da sallama Ya shiga kowa Na kwance a kan gado, zauna abbah yai yanawa sultan murmushi hakan yasa sultan kirkirar Na karya Ya Karasa kus dashi ya zauna, biro Da takarda Ya dauka Ya rubutaa mai Ya jikin yata Da fatan koma lafiya?
Karantawa sultan yayi Ya rubuta lafiya gobema zaku koma india har itta,.
OK kawai abbah yace sannan Ya rubutamai kawu shine wanda Ya rike sultana,.
Shidai sultan bai gane komaiba Ya dauka shakuwa yasa abbah ke kiran sultana da yarshi,.
Gun kawun yaje suka gaisa irin Ta kurame kafin Ya dauki hutunan su yai musu Saida safe,.
Gun sultana yaje lokacin mom Na toilet Ya zauna kusa do sultana gobe zakuje abroad ni kuma zan dauki fansarki wife Na miki alkawari, idonshi Ya sauka kan sarkar daya Sa mata dazu akan trolly din kusa Da gadonta Ya dauk yana kallah sai hawaye yana tuna sanda Ya Sa mata,.
Mom ce ta fito, aaa dama baka tafi gida ba? Mom anan zan kwana, tsaki taja Allah baka isa ba,duk yadda yai Amman mom taki dole Ya hakura,
Saida Ya bata kiss a goshi gaban momy sannan Ya tafi,.
Haka Ya karasa bangaren su jiki ba laka,..
Kallan marka yayi Da take tafiya a hankali akan stair kamar wata muna fuka ta takalmi a hannun, Cikin daga murya Ya furta keeeee, sosai ta razana har Tana zubar Da takalman hannunta ji take kamar ta saki futsari
By hajara Mami natty girl
[9/16, 11:32 PM] Hajaramami: 👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 83*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Karasawa gunta yai ranshi a daure, malama me kike anan gun? Bayan kowa Ya kama ganshi uban wama yace kisake dawowa wannan bangaren ban korekiba? Ranka Ya dade kayi hakuri wlh dama dakunan naga abude gashi ba kowa shine zan rufe, kallan ta yai kallan tsana babbace amma duk yaji ya tsaneta saboda abun datai, murmushin yai kafin Ya kalleta mun gode zaki iya tafiya malama,kasa tai na gode sosai, Tana kaiwa nan Ta fice,,.
Daknshi Ya shiga yai wanka Ya zauna abakin gado kawai tunanin ta inda zai bullo yake gobe su sultana zasu wuce zai San yadda zaiyi yaga Ya tunawa sarki asiri, wayarshi Ya dakko Ya kira habib, hello aboki plz ina San kasamun barrister da zai kareni a court,kara zan shigar I know Hafiz ne zaice zai Kare babanshi you know shima barrister ne babbama kuwa, OK angama aboki Da haka sukai sallama,.
Mikewa Sultan yai yaje dakin sultana, Ya zama dole IN nemo memory dinnan dan in samu abun kare kaina if not nine zam fadi daddy mugune yasan ta yadda yake tafiyar Da abunshi, dakin yahau dubawab iya Dubenshi bai ganiba saima gajiya dayai GA wata yunwa Da yake ji hakan yasa yaje dining yaci abinci sannan Ya koma daki yai alwala yai ta nafila yana rukawa sultana sauki Da uncle dinshi,haka yaita yi saida yaji ya fara gajiya sannan Ya hakura Ya kira mom KO sultana tai farka Amman ina Da haka sukai Sallama Ya kwanta,.
Hindu kuwa Da taji labari har ta fara shiri kan cewa tana San tazo taga lafiyar mahaifinta garin taimako zaije Ya kashe kanshi, Hashim ma yace tare xasuje, Da haka ta fara shiri,.
Washe gari asubar fari Bayan sultan yaje yai sallah yau bai tsayaba Ya nufi airport yai musu visa daga nan yaje Ya shigar Da kara, sannan Ya wuce asibiti lokacin har 9:00 tayi Da sallama Ya shiga, momy Ta amsa,.
Ina kwana mom? Lafiya qlau son mom ya jikin nata? Son gashi nan dai amma bata farka ba, you don't worry mom 11:00 zasu wuce Bari inje gun su uncle Ya ajjiye take away sannan Ya dauki nasu kawu, bayan sun gaisa Ya ajjiye musu yake sanar dasu cewa zasu tafi anjima Da haka sukai sallama ,.
Da sallama Ya koma, yauwa son ka zauna ina San zanje gida akwai abun Da zan dakko daga Nan zan tahu Da Zuwaira, OK mom saikin dawo, Da haka ta futa bayi Na biye Da itta,.
Zama kusa Da sultana sultan yayi Ya daura kanshi a kafadarta, wife ki sauri ki tashi plz I need you by my side I promise zan daukar miki fansa, sannan zan nuna miki yadda nake sanki wife Allah ya baki lafiya haka Ya zauna yana tai mata surutai ,.
Hindu kuwa 10:00 suka karaso dan flight suka bi, duk tabi ta damu taganta agaban babanta, suna zuwa tai bangaren shi danshi yana gida saboda ciwon is not wost, akwai doctor dake dubashi,. Hafiz da mama taga agunshi, nan Hashim ya gaidashi ana hakane, police suka karaso sukace akaisu GA sarki wazirine Ya kai su sannan yai sallama Da sarki,duk tare suka fito mama, Hashim Hafiz da Hindu sukabzauna Bayan sun gaisa,.
Mikawa Hafiz takarda sukai wannan takardar shigar Da karace, sultan Ya shigar Da mai martaba kara kan shi Ya harbi matar shi sultana sannan Ya buye sarki abdulsalam Na wasu shekaru, ka iya bakinka jami, I kasan Da wa kake magana kuwa cewar waziri, kallan sarki dpo yai kayi hakuri ranka Ya dade haka aikin namu yake sannan shari,a gobe zata Fara saboda yace baya bukatar a jata Da da yawa, zamu wuce, sannan suka tafi..
Hindu idonta ne Ya ciko Da kwallah yanzu abunda sultan zaiyi kenan tsanar har takai haka, Ya shigar Da mahaifinta daga taimako, murmushi kawai sarki yayi, kafin Ya daur KO tashi kuje ku duba matar tashi suna asibiti
By hajara Mami natty
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 84*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Hindu ce ta karba haba daddy kalli abun dayai mana sannan Kana cewa wai muje mu duba shi haba daddy, plz mana Hindu karkiji komai insha Allah komai zai daidai plz kuje, kallan hashim tai da duk jikinshi yai sanyj muje, mikewa Hafiz yayi nima zanje ina San zanyi magana Da sultan, Da haka suka fice,.
Dai dai zasi shiga mota momy Ta fito itta Da Zuwaira, kallan Hafiz Zuwaira tai da gani ranshi a bace yake, kome Ya bata mai rai kuma oho ta fada a ranta suka shiga motan su sannan sannan suma suka shiga tasu,.
Haka suka nufi asibitin, suna shiga dai dai lokacin habib yazu , kallan Zulai yayi uhmmm zaki tayamu daukan kaya,hade rai tayi hannuna na ciwo,eyya sai muje office na duba ki bata saurare shiba tabi Bayan su momy sukai ciki, Da sallama suka shiga hakan yasa sultan mikewa tare da kallan agogan hannun shi 10:30 yanzu zamu wuce, dai dai lokaci su Hindu suka shigo suka duba sultana, kallan sultan tai munga takarda mun gode gobe kuma xamu shiga court, murmushi yai mine da godiya,.
Kallan shi hafiz yayi maika tanada na shaida,?wannan kuma bai dameka ba cewar sultan, hmmmm wlh sultan kaban mamaki Ashe baka dauki daddy tamkar mahaifinka tunda har zaka iya shigar dashi Kara, taya zan dauki Wanda yake kukarin kashe mun mata as my father, inda ace yau daddy shiya kashe mun Baba bansan yadda zanyi acting ba da dakaina zan kasheshi inyaso nima a kasheni, gadan gadan Hafiz yai kanshi hakan yasa habib shiga tsakani, sultan ne yai magana banda Time dinka malam ka Bari sai naji Da lafiyar yata tukun, dai dai lokacin su abbah suka shigo Sun gama shiri, kallan Hindu da Hafiz yayi Ya sakar musu murmushi hakan Yasa sukai kasa dakai Dan Sun ganeshi,.
Haka suka wuce airport saida sukaga tafiyar su sannan sultan Da habib Da Zulai suka dawo, a hanya sultan ke fadawa habib su wuce gidansu kawai dan acan xai zauna bayasan komawa wannan masarautar amma su biya su sauke zulai haka kuwa akai suka sauketa sannan suka kama hanya ,.
Kallan shi habib yai aboki wannan barrister dinfa macece daga katsina zatazo nasan inajin yanzu Ma tazo, OK Kana ganin zata iya ko? Aa mai zai hana, OK Allah ya bamu sa,a ,.
Suna zuwa suka tadda tazo kuwa, harta huta a gun maman habib Da sallama suka shiga parlour suka amsa musu, mamin habib taiwa sultan wa,azin Ya kara hakuri saida suka huta kafin Ya zauna Da barrister dan tattau nawa,.
Sunana barrister zarah, habib was my friend so ya fada mun case dinka, Amman inasan ka fada mun abun Da ka sani gam da wannan abun,nan Ya sanar mata komai, Bayan Ta gama ji OK shikenan Amman karma tabbatar komai haka yake Dan banasan azo ana fadamun abunda ba haka ba, haka barrister, OK yanzu dai bamu Da shaida gashi ka shigar Da kara gobe Amman ba matsala zan duba inga, Da haka sukai sallama,.
Hafiz shima Bayan Ya gama abun Da yake yaje Ya Sami sarki,.
Daddy so nake ka fada mun gaskiyar yadda abunnan yake, a take daddy Ya hada karya Ya bawa Hafiz, ka tabbatar hakane daddy Ya daga kai alamar eh, mikewa yai Allah ya kaimu goben zamu hadu Da haka sukai sallama.,
By hajara Mami natty girl
[9/17, 12:02 PM] Hajaramami: 👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 85*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Washe gari
sarkine a dakinshi Ya dauki Waya Ya kira marka, bayan sun gaisa, wai Ya ake ciki kin Sami memory din? Dan bansan meye a cikiba kuma ina Da Bukatar Sani, tuba nake ranka ya Dade wlh ranar zuwa Yai Ya sameni ya kureni yanxuka bangaren a rufe yake Dan ba kowa a ciki, tsaki yai tare da kashe wayan, Da sallama Hafiz Ya shigo ban taba ganinshi a wannan shigar Ta barrister ba sosai yai kyau zanso Zuwaira taga yadda yai wannnan shigar, daddy ina kwana? Lafiya qlau Hafiz ka shirya kenan? Eh dad kasan 10:00 zamu shiga gashi lokaci yanzu Ya jaa ka shirya dad and dad plz ka fadi gaskiyar abun Da ka Sani bbanda fadan rashin gaskiya, OK kawai sarki yace yai sama abunshi, shi kuma Hafiz Ya fice,.
Sultan ne zaune akan gado baganshi laptop ce suna magana Da momy Ta video call,mom Ya jikin an fara bata kulawa KO? Eh son sunce nan da 2 days zata iya tashi su uncle dinka kuma akwai abun Da suke basu suna sha sance suma nan bada dadewa zasu dawo normal suma, OK allahamdullilah Allah ya basu lafiya ta amsa Da Ameen,.
Habib ne Ya fito daga toilet kaje kayi wanka mu shirya plz kaga lokaci Na wucewa gashi ko break bamuyiba, OK Ya fada tare da mikewa Ya shige sannan Ya fito Ya shirya suka kama hanyar dining, a parlour sukaga zarah har ta gama shiryawa taci abinci Tana duba laptop dinta, suka gaisa sannan suma suka nufi dining din,.
Bayan sun gama suka mike sannan ittama Ta tashi suka fita a tata motan tabi bayansu har suka isah, suna isa su Hafiz Ma Na isowa, kallan sultan Hafiz yai kafin zarah Ta fito Tana kallan court din sosai tai mata kyau, Hindu da zuwanta kenen itta Da Hashim, tana sakkowa Ta nufi gun sultan, yaudai zaa shiga Amman ka sani dole sai an daukar mana mataki a kanka na tuxarta mana mahaifi dakai, tsaki sultan yayi Ya kalli zarah barrister zamu iya shiga ciki, murmushi tai thanks, but ina San zan danyi call Ta fada tana danna Waya mom dinta Ta kira take sanar mata zasu shiga tana Neman adduarta aikuwa mom dinta tai mata sosai ,har taji dadi,bayan Ta gama Ta kalli sultan,.
Kace sarki guda kake kara, murmushi kawai yai Kalli Hafiz tai daga nesa wancan shine Wanda zamu fafata kene, daga mata kai yayi OK Bari inje mu gaisa bata jira cewarshiba tai gaba, Bayan Ta gaida su mama ta Kalli Hafiz sunana zarah jibo wacca zata kare Wanda yake kara Allah yaba mai rabo sa,a ,zarah jibo Ya maimaita tabbas yasan sunanan,ameen kawai yace sannan yai gaba Dan an Fara shiga ittama tai gaba Dan shiga court din,.
10:00 dai dai aka shiga court inda alkali Ya shigo aka mike sukai abun Da zaai sannan Ya zauna, nan ne wani ya yashi ya fara yau 11/11/2015 yane kuma aka shigo Da kara inda sultan ke kekarar sarki kan yana San kashe mishi mata sannan Ya buye sarki har na wasu shekarau, bayan Ya gama ya zauna sannan Hafiz Ya gabatar Da kanshi kan Kare Wanda ake kara hakama zarah kan mai kare Wanda yake Kara,.
Nan alkali Ya bukaci ganin sarki a kan stage wanna ya kara konawa hindu rai wai sarki babanta kuma ne anan gun, hawaye kawai ta goge zuciyarta Na tafasa,.
Kallan sarki alkali yai Da fatan mai martaba zaiyi hakuri haka abune yake dole yai hakuri Da abun Da zai biyo baya Dan munsann shima Mai yanke hukunci Da kanshi ne, daga kai kawai sarki yai, kallan shi alkali yai Da fatan kaji akan abun Da yasa ake karar ka ,daga kai yai alamar eh, nan alkali Ya juya ga du zarah KO mai kareh Wanda yake kara Tana da abun Da zata tambayi mai martaba? Tashi tai kwarai Ma kuwa ranka ya dade, koto ta baki dama, mikewa tai ta nufi sarki,sunana barrister zarah jibo Mai kare Wanda yake kara, Da fatan kaji akan abun Da ake karar ka, eh naji OK yanxu me zaka ce game da wannan karar Da ake maka? Ni abun Da zance kawai shine ba nine naso kasheta ba hasalima ni taimakonta Na so yi, gyara tsayuwa Zarah tai ko zaka fada ma Yadda abun ya kasance?
by hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 86*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Eh sanda abun zai faru ni inasan zanje ran gadine nazo wucewa daga garin naga wannan gun shine naje acan naga kanina Wanda ake ce mana Ya mutu abun yaban mamaki, to shine nace zan daukesu ina cikin hakane naji kamar Da mutune shine Na buye sukazo sukai abun Da zasuyi suka bar daya, ana hakane sultan yazo yace su bashi uncle dinshi inba hakaba zai hadasu Da police to ni Da naga mutumin nasan ya harbi sultan din shine nai niyar fitowa dai dai lokacin kuma sultana tazo bansan ta yadda akai Na ganta agunba, shine ta kwadawa mutumin karbe taje zasu kunce baban nata shine da naga mutumin zai yi harbi kafin in fito har ya harbi sultana shine ni kuma Na dauki bindigr zan harbeshi dai dai lokacin mukaji motan Yan sanda mutumin yazo guduwa ta window Na harbeshi shima ya juyo shine ya harben a hannun, Ta sanadin hakan ne sultan Ya dauka nina harbi matar shi,. Kallan sarki zarah yadda yake maganar Ma ya tabbatar mata karya ne OK, Amman me yasa da zaka tafi ran gadi baka dauki bayi ba da dogarai kuma Da sassafe baka tsoran lafiyar ka? Mikewa Hafiz yai ya mai girma mai shari,a barrister zarah Tana wucewa inda baa kaitaba, korafi bai kwarboba cewar alkali muna San sanin dalilin Da yasa sarki ya tafi shi daya,. Na gode ya mai shari,a cewar zarah kafin ta kalli sarki muna jinka,.
Abun Da yasa na tafi ni daya inasan zanyi badda kama ne saboda zan shiga gari inga yadda mutane ke tafiyar Da abun su, jijjaga kai zarah tai, kafin ta Kalli alkali Da wannan zan tafi yamai shari,a Amman inasan wnannan koton tai duba sosai babu wani sarki daya taba ficewa shi daya sannan koda zaiyi baddakamane yana yafiya Da bayine suma suyi badda kama din Amman shi yace shi daya yaje hakan yana nufin abun dayai a sirrine baya San a kamashi, na gode ya mai sharia,.ta koma ta zauna,.
Alkali yai rubuce rubucen shi sannan Ya ya tambayi Hafiz ko yana Da tambaya yace bashi Da dashi,.
Nan alkali Ya shaida ya daga karar zuwa gobe,. Daga haka aka fice, ruwan sanyi Da lemon sultan Ya siyawa zarah ya kai mata, nagode ta fada sannan zamuyi magana a jida Ta shiga motar ta suma suka bi bayanta,.
Sarki Na fita Hindu ta rungumeshi Tana kuka Tana bashi hakuri shima Yana lallashinta,.
Kallan Hafiz sarki yai wai wace wannan zarah din ta fiya kwakwa gashi na fada mata gaskiya Amman tana San raina mun hankali,?karka damu za muyi winning, Allah yasa kawai yace sannan suka shiga mota,.
Bayan sunje gida sun huta ne zarah ke tambayar sultan Wanda ya kira police, yace bai saniba Amman yana tunanin sarkinne yasa, daga kai kawai tai, .
Bayan sun gama ya kira mom ya fada mata yadda sukai sannan tayi musu addua,.
Washe gari a court .
Hafiz ne a gaban sultan, ko zaka fadawa court Yadda abun yake nan ya sanaf Da gaskiyar abun Amman Hafiz Ya nuna krkirane kawai sultan yayi,.
Amman malam sultan ko zaka iya fadawa court dalilin Da yasa ka tura sultana waje alhalin itta zata bada shaida KO kuna tsoran zata tunama asirine saboda tasan sharri zakaiwa Wanda yke tamkar uba agunka? Zarah ce ta Mike yamai sharia abokin aikina yana kawo wani abun daban basaida lafiya zamu samu itta taba Da shaidarba, barrister Hafiz koto nasan Na gyara bakinka, nagode yace sannan Ya kalli sultan ko zaka iya nunawa court halin da matarka take itta Da mahaifinta, eh kawai yace yaje ya dakko laptop dinshi ya kunna ya nunawa,aka karba sannan aka juna sultana na kwance gatanan dai rai a hannun Allah sai su Abbah Da akeba magani Da haka aka kashe ,.sannan Hafiz yace ya gama ya koma ya zauna zarah ta mike ta shaidawa court tana San ganin dpo din Da aka kira sosai gaban sarki ya fadi Dan ya manta baisa Da marka a zancen shiba
By hajara Mami natty girl
[9/18, 11:55 AM] Hajaramami: 👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 87*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Nan DPO ya Tashi yaje ya tsaya, ko zaka iya fada mana w ya kiraka Wannan lokacin? Eh wata matace sanda muka jema tana gun,kallan alkali tai yamai girma mai sha,ria inasan court ta kira wannan matar IN kuma ba bazata fitoba aba DPO dama ya nemomin itta saboda akwai tambayoyin Da zan mata, court Tana neman wacce tai kiran police a wannan lokacin, mikewa marka tai sannan DPO ya koma ya zauna itta kuma ta maye gurbin shi,.
Kallan ta Zarah tai ko zaki iya fadawa court wacece ke? Eh ni baiwace a wannan masarautar, OK zaki iya fadawa court abun Da yasa kika fita a wannan ranar? Eh dama kamar yadda na fada miki cewa nima baiwace,to a wannan ranar naga lokacin Da shi mai martaba ya fice ganin shi daya ya fice hakan yasa nabi bayan shi Dan kare lafiyar shi,to danabi bayanshi ne naga yaje wannan gun, har zan bishi shine naga wasu mutane sun shiga sannan Sun fito Amman ba mutun daya bayan sun fice ba dadaewa ba Na Fara jin harbi hakan yasa na kira police sanda nukaje naga sarki Da itta matar sultan a kwance, kinji yadda abun ya kasance, OK na gane Amman meyasa Da kikaga fitarshi baki kira wani namijinba kika tafi ke daya,? Hafiz ne ya mike yamai girma a jawa abokiyar aikina kunne Mace nada power din Da ittama zata iya kare uban gidanta, barrister Zarah ki gyara zancen ki, na gode yamaisl shari,a shikenan abun Da zan tambayeta sannan inasan court ta kira doctor dayai bincike game da bindigar Dan muga hannun waye ,.
bayan doctor din yazo ya sanar cewa hannun Da yaga guda biyune daya Na sarki daya kuma baisan Na wayeba, daga haka ya koma ya zauna, alkali yai rubuce rubucenshi sannan Ya shaida ya daga kara zuwa kwana uku Wanda a wannan lokacin zai yanke hukunci ,sannan Ya Mike ya fice hakama mutane,.
Bayan sun fito, Hafiz Ya nufi gun zarah dake tsaye ittada su sultan kallan ta yayi shawara zan baki tun kafin kiji kunya garama ki kama gabanki ki daina biyewa wannan banzan ya nuna sultan saboda babu wata shaida Da kuka taba munawa nacewa sarki shine yai wannan abun, gyara tsayuwa Zarah tai kasan wace zarah kuwa? Zarah bata Gudu a sha, ria sannan bata fuduwa daga yadda naga mahaifinka yana magana Na tabbatar Da cewa bashi Da gaskiya ina fahimtar haka sannan zan baka shawara yafi maka kawai kai ka Kama hanya Dan wlh ina Mai tabbatar maka a wannan ranar zan nunawa mutane kan cewa waye sarki kuma mu zuba n,ida kai ,sosai ranshi ya baci har yana San Ya mareta sultan yai saurin rike hannunshi yai wulli Da hannun sannan suka shiga Mota suka bada mai kura sukai gaba, sosai ran Hafiz Ya baci dole Ya dauki nataki,hakaa ya wuce suka tafi,.
Bayan Zarah ta gama abun Da take ne ta yi parlour inda su sultan ke zauna, zama tai, sultan kasan bamu Da shaida KO dayaba ko sannan anzo karshen karar saboda haka musan abun Yi, barrister wlh sultana itta kadaice shaida Amman akwai wani Memory dayaba bata a dakinta inajin shi zanje In duba, OK gobe za muje tare, insha Allah zamu ganshi ,Da haka suka yanke decision,.
Sarkine shi Daya a dakin shi kamar Wanda aka ciza yai saurin daukan wayar shi marka ya kira yai mata godiya sannan yace gobe tazo ta karbi wani key Na bangaren su sultan tamai bincike Dan yasan yanzu akan wannan memory din zasu dukufa,.
Sultan yana kwance a daki abun duniya ya dameshi,kallam shi habib yai aboki ka daina wannan tunanin zai iya saka ka cikin wani hali fa, ba doleba aboki inaji ina gani zaa bawa Sarki gaskiya alhalin Bashine Da gaskiya ba ya zanyi gashi sultana bata farka ba, kafadar shi habib ya rike karka wani damu komai zaiyi Normal wayar sultan ce ta hau ruri, ganin mom Yasa Ya dauka yasa juna a laptop sannan Ya kunna fara,ar daya gani fuskar mom tasa jin sanyi mom me Ya farau naga kina fara,a ,son saika ban goran albishir tukun, marai raicewa yayi plz mom mana, juyar Da laptop din tayi zuwa GA sultana dake zaune ana bata tea wata doctor Na gyara drip din dake hannunta, dariya ya saki tare da rungume habib
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 88*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Wallahi ta Tashi ya fada yana kara rungume habib, kallan shi sultana Tai duk sai taji kunya ganin yadda yake ta murna, murmushi tai kawai,. Tare da kallan wacce ke bata tea din am OK, OK nurse din ta fada sannan Ta mike, juyo Da laptop din mom tai Tana tambayar sultan yadda abun ya kasance yau, nan ya sanar mata sannan yace gobe zaije su duba memory din sannan gashi sultana Taiwan tashi itta zata bada shaida koda ta laptop ne tunda yasan ba zaa sallameta yanzu ba,da haka sukai sallama sannan yace ta mikawa sultana wayan saida ta zare sannan Ta mika mata karba sultan tai ta kara a kunne,.
Shiru yai ittama tai shiru shi dindai ya Fara magana, sultana ya jikin naki? Da sauki, hmmm to na gode Allah Matata ta samu lafiya jibi zamu koma court zaki bada shaida a wannabe ranar kuma ina jin zanzo gun Matata in kuma banzo ranarba sammako zan biga saboda inasan ganin fuskar Matata, murmushi kawai tai, kinsan me? Aa Ta fada so nake ki koyamun wannan harbin naki Da kika yi ranar so nake in kuya,ok saidai Na dawo no basai kin dawoba nan zanzo muyi honnymoon dinmu anan,uhmmmm kawai tace, sannan kimun addua gobe zanje duba wannan memory din naki, haba Allah yasa Ka ganshi Dan nasan ba zaka rasa shaida acikiba Ta iya yuyuwa Ma inna bayar nida kaina ace hada baki mukai Amman inka nuna wannan bamai maka musu saboda video ne,ok Allah yasa in gani my wife all I need is your prayer,murnushi kawai tai haka yaita mata fira har saida Ta gaji Da tace bacci take ji sannan Ya barta ,.
Washe gari
Da safe bayan sun gama shirya suka nufi dining,sukaci abinci sannan sultan yace Zarah tazo suje, habib tare suka tafi a mota daya sukaje,.
Parking sultan yayi a harabar masarautar, bayi sukazo kwasar gaisuwa yana amsa musu, Hafiz daya zo wucewa ya gansu hakan yasa Ya karasa gun da suke yaba habib hannu suka gaisa sannan Ya kalli sultan me kuma aka zoyi anan,zanzo gidanmu sai ana tambayata dalilin zuwana,aa ai gani nai Da anbar mana gidan mu kasan wannan MASARAUTAR MUCE shine nake tunanin Ko ka tafine gaba daya, tsaki kawai sultan yaja a ina ta zama masarautar ku koka manta Mai kujera ya dawo kuma dole a bashi gunshi mutanema sunfi sanshi maye nakama Na zakewa Bayan mahaifin naka cell zai tafi, kanshi Hafiz yai habib yai saurin shiga tsakiya, sannan yaja Hafiz baya plz mai yasa kuke hakane babu kyaufa, tsaki Hafiz yaja sannan Ya Kama gabanshi. Kallan Zarah yai muje barrister karki damu,murmushi kawai tai tabi bayanshi,.
Abun ya bashi mamaki daya tura kofan yaga Ta bude alhalin yasan a kulletake, kallan habib yai duk yadda akai akwai wani acikin gidan nan kuma koma waye yana Da hannu a wannan harkar saboda haka zamu kamashi shima zai zama shaida,.
Daga kai kawai habib yai suka shiga ciki, marka dake daki Tana bincike jin an shigo yasa gabanta faduwa Ta rasa ya zatayi, gabanta Na dukan hamshin hamshin, dasauri Ta shiga toilet har ta manta wayarta akan gado, sultan kuwa yana shiga yaga alamar an shiga dakin,jijjaga kai yayi kawai sannan Ya kalli habib aboki mufa Fara duba abunnan plz inaji a jikina akwai Wanda ya shigo wannan gun,gun wardrobe Zarah ta nufa shi kuma habib ya Fara duban kasan carfet, dubawa suke sosai Amman bashi babu dalilinshi,.
Mikewa Sultan yayi ya nufi bedside drower din daya ajjiye mata ranar ya jawo Amman babu komai zama yai akan gadon kamar yayi kuka dan bakin ciki, kamar an mintsileshi kuma ya dakko drower din ya juyar Da itta akan gado idonshi ya sauka kan memory din daya makale a jikin drower din ya shiga sosai kadanne ya rage bai gama shiga ba.,
Ga number gamasu San mun magana for correction KO comment
08032464246
By hajara Mami natty girl
[9/19, 9:43 AM] Hajaramami: 👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 89*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Dedicated to Miss Salsabila ml naruwa gumel (my partne)
This page Is indicated to you AISHA JAFAR UMAR LADY &FA,IZA IBRAHIM
Dasauri ya zauna a kan gadon,gashinana ina jin, dasauri suka karaso gunshi suna kallan, ahanlali ya zaro memory din, tsabar dadi har wata dariya ya saki, zarah Ma murmushi tai, bari Musa muga ni, wardrobe Ya bude ya dakko modern dinshi sannan yasa Ya juna ajikin TV din dake dakin, Zarah taja kujeran madubi Ta zauna sukuma suka zauna akan gado, video biyu ya gani a video da yake wayar sabuwace ba komai a ciki sai wannan video din, Na farko yasa, nan sukaga video din Da sultana Tai lokacin Da yasa aka kamo kawu,kallan sultan Zarah tai kaga wannan Ma zamu iya bada shi a shida tunda gashi Ya fada akaishi gun uncle dinka, sana gaba muga, ba musu kuwa yasa, .
Record din dataine a dakin a jiya yau sultan Ya shiga tashin hankali, hawaye kawai yake tare da rike hannun habib ganin hakan yasa zarah cirewa Ta rike shikenan komai yazo karshe,dama daddy ne ya kashe mun mahaifina dama duk sharrrin shine akan wani banza mulki abun Da zaka tsaya agaban Allah kayi bayani Maye abun kisa a ciki ya karasa tare da fashewa Da kuka, sosai Zarah taji tausayin shi hakama habib duk jikinshi yayi sanyi, wayar dake gefensu Ta marka itta Ta katse musu komai suka maida kansu gun wayar, dakkowa habib yayi ya kalli wayar Mai martaba ya ga an rubuta, kallan sultan yayi ya nuna mai karba sultan yayi ya kuna tare dasawa record kuma yasa a handfree, sarki naji an daga baima jira Mai zatace ya Fara haba marka wai har yanzu baki fito ba gashi Hafiz yace mun yaga Sun shigo KO so kike asirina ya tunu, Amman wlh in aka kamaki Karma ki ambato sunana,kuma ki fito yanxu, baima jira Mai zatace ya kashe yana tsaki sai jeka ka dawo yake adakin,.
Kallan wayar sultan yayi,kafin ya mike Ya nufi toilet direct Dan yasan iya nanne gun maboya a dakin, jin ana shirin bude toilet din yasa marka tsurewa Ta ina zatabi inane hanyar Da zatabi Tafice gashi babu gun buya,gara kawai tayi giving up hakan yasa Ta tsaya Bata motsa KO ina ba, sultan Na budewa ya ganta, ranshi a hade ya kalleta fito kawai yace tare da komawa ya zauna, a hankali Ta fito duk hankalinta ya Tashi yanzu ya zatai Amman duk runtsi ba zata fadi gaskiya ba,kallanta habib yai kafin ya kalli kalli Sultan wace itta? Itta zataba Da shida ittama muguwa ce ai, kallan ta Zarah tai ai ittace wacce naiwa tambaya a court, eh ittace karya Ta fada miki, jijjaga kai kawai zarah tai kafin suka mike we have to go, kallan Marka yayi wuce muje, haka suka sakata a tsakiya sannan suka fito, sarki dake fitowa zaije fada dashi da wajiri idonshi ya sauka kan marka Da ke Ta wutsi wutsi Da ido, sosai gabanshi ya fadi Yana gani suka sakata mota sannan suka shiga suka ja ta suka Kama hanya, wayarshi sarki ya dakko Ta turawa mutanen shi Text kan cewa su tare hanya susan yadda zasuyi su kashe marka yasan ba abun Da zai hanat fadan gaskiya (Dan adam bulune wlh ).
Tafiya suke a mota ba Wanda yake cewa kala,kawai sukaji motan su na kara Irin na faci hakan yasa habib dake tuki tsayawa suka fito motan yayi faci ya fada tare da dafe kai, gashi gun ba wasu mutane sosai, fitowa sukai shida Sultan inda aka bar Zarah da marka amota, Bayan motan ya zaga ya dakko wata tayan suka Fara cire waccan,.
Mutanen sarki dake can nesa suna zaune Sun saida bindigarsu kawai fitowar marka sukw jira su gama Da itta Amman bata fitoba, saida su habib suka saka dayan tayar suna daurewa Zarah ta cewa marka su fito saboda zafi hakan kuwa akai,.aikuwa nan danan suka kara saita bindigar, sultan daya dago idonshi ya sauka kansu Da suke shirin sakin bullet din Da, sauri Ya karasa gun su yai kasadasu saijin karar bindiga sukai, ahakan ya bude musu mota suka shige sannan suma suka shiga, duk yadda motanen sukai basu samesu ba Amman suka yanke hukuncin zasu cewa sarki sun gama Da itta haka kuwa akai suka fadamai sannan hankalin shi ya kwanta
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 90*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
Dedicated to Miss Salsabila ml naruwa gumel (my partne)
This page is for you,FATIMA MUHAMMAD MIKA,IL& FATIMA MUHAMMAD SANI HADEJIA
Haka suka karasa gidan sosai hankalin marka ya tashi Dan itta bata taba jin karar bindiga ba, wani daki Sultan Ya sata tare da kallan ta ko kifadi gaskiya gobe KO karki fada ya rage miki dan dole gobe asirinku zai tunu sannan kuma gashi nan nasan shi zaisa a kasheki saboda kar ki fadi gaskiya ki zauna kiyi tunani ya kaiwa nan ya rufe kofan Da key sannan Ya fice, sosai ranta ya baci dama shine yasa a kasheta, shikena su kasa zata gani,.
Yau sakoko Sultan yake, haka yai komai, kallan shi habib yai aboki you look Some how kayi hakuri komai yazo karshe ai kayi Ta addau zamuyi winning by the name of Allah, kasawa ranka ruwan sanyi kodan lafiyar ka, hmmm habib dama daddy ne ya kashe mun abbah me yasa banyi tunaniba amma gaskiya ni banzane badan sultana tazo wannan masarautar ba kenan haka zan zauna yaci bulus kenen, Ya fada tare da hawaye a face dinshi,da kyar habib ya lallabashi yai shiru, sannan Ya kwanta yau kwata kwata bayajin zai iya wayama Da sultana din,. Ittama kuma acan Tana xaune tana jiran kiranshi Amman shiru hakan yasa tai addua Allah yasa lafiya Dan har yanzu bata Fara tashiba,.
Sarki kuwa jinshi yake on top tunda ance mai an kashe marka aiba komai hakanma yayi, Da haka ya kwanta babu KO dar a tare dashi (eyya daddy yazo karshe )
*washe gari*
Yau da sassafe Sultan Ya Tashi yai wanka yama riga habib Tashi, sanda habib ya tashi lokacin harya fito daga toilet, kallan shi habib yai aa kaga yau wani dadi akeji kenan har an rigani shiryawa kenan? Murmushi yai ka tashi karma shirya plz, mikewa habib yai yaje ya yai wanka Tare suka fito, dinning kamar kullun har Zarah tayi break su kawai take jira
Haka suka gama suka kama hanya ba tare da bata lokaciba suka shiga karar,.
Bayan anyi bayane bayane ne, alkali Ya kalli, Zarah KO mai kare Wanda ake kara tana Da abun Da zata fada KO kuma Wanda yake Kare wanka ake kara, nan Hafiz yace baida shi,zarah Ta Mike tare da ficewa,. Ta kalli alkali,inasan koto taban dama IN nuna shaidata Ta farko, aka bata dama, nan ta kira marka sosai hakalin sarki ya tashi, kallan marka tai zaki iya fada mana abun Da kika Sani, nan Ta fadi abun Data sani sannan, ta koma Ta zauna, kallan alkali Zarah, nasan court zata iya cewa mun siyi wannabe matarne tunda Da farko ga abun Da tace Amman shaidar tawa bata tsaya anan ba, Ta karbi laptop ta bayar ka juna a TV sannan aka nuno sultana Data Sa Hijab nan Zarah tai Mata tambaya sultana Ta fadi komai Da yadda akai Ta fice sanda Marka Ta kirata, kallan alkali Zarah tai nasan abokin aikina zai iya cewa hada baki mukai Da itta sultana Amman ina Da wata shidar nan taba Da record din Da sultan yai jiya ga marka,wani murmshi Zarah tai saki ta Kalli sarki nasan Mai martaba zai iya cewa muryarshi muka kwaikwaya amma ina Da wata shidar nan Ta bada video din aka,juna kowa ya gani sarki gabnshi yahau rawa inda Yan sanda suka zagaye gunda yake zaune saboda tsaro
by hajara Mami natty girl
[9/20, 8:40 AM] Hajaramami: 👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 91*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Sarki yai tsuru tsuru kamar ba sarkin Da aka saniba, kallan shi mutane suke suna kus kus inda alkali yai kasa dakai yana rubuce rubuce, Sannan Ya buga Dest alamar ai shiru nan kuwa gun yai tsif daga Hindu har Hafiz sunyi shiru jikinsu yayi sanyi kamar basuba abun yazo musu a un expected,nan alkali Ya bukaci ganin sarki a stage haka yahau abun duniya yamai yawa duk kunya Ta kamashi, kallan shi alkali yai kaga abun aka nuna shaida kuma a iya bincike mun gano gaskiyane, saboda haka mu yanke maka hukunci, kallan court yayi court ta yanmai hukun ci dai dai abun dayai a tsarin wannan court din duk Wanda yai kisa hukuncinshi kisa to Amman shi yayi kisa sannan Ya rufe mutun Na shekaru saboda haka court ta yanke mai hukuncin kisa wani sati sannan kafin satin Yazo za,a hukuntashi Da hukunci mafi tsauri yana fadan haka ya Mike inda police suka wa sarki ankwa sannan suka tsaya abayanshi,alkali yana ficewa aka Fara surutai inda police suka saka sarki gaba, Hindu kawai ficewa tai bata San ganin daddy Nata, gun Motansu Ta tsaya kuka kawai take bata San haka mahaifin Nata yakeba, Hafiz ne ya karasa kusa Da daddy din yana kallan shi, daddy Da gaske hakane abun Da na gani kuma naji? Shiru yai kansa kasa hakan ya tabbatarwa Da Hafiz gaskiyane, da sauri ya fice saboda hawayen Da yaji yana San zubuwa, gun Hindu yaje ya tsaya wadda take tsaye itta daya Hashim kuwa har ya tafi ranshi ya baci ashe haka surukinshi yake bai saniba duk sai yaji yana daya sanin aurenta dayai,kallan Hafiz tai Yaya kagafa Hashim fushi yake dani yama tafiyarshi wlh yaki kulani, rumgumeta yai yana lallashinta, haka sunaji suna gani aka wuce Da daddy dinsu, Hafiz ganin Zarah ta fito yasashi saka Hindu a mota ya nufi gun,.
Da murmushin yake yake kallanta, congrats gaskiya na gingina miki Na gode sosai. Kallan sultan yayi duk sai idonshi ya kawo kwalla bazai iya Kallan sultan ba kunyarshi yakeji yanzu hakan yasa Ya juya kawai, sultan Ya bishi Da kallo KO daya bayajin haushinshi tunda bashi yamai laifiba Tashi daya yaji tausayinshi shida Hindu yanzu basu Da uba, mama kuwa tunda taji abun daya faru zuciyarta ke mata soya Tana mota a zauna itta tasan yadda take ji,.
Sanda Hafiz Ya shiga motan yaga halin Da take ciki Dan har hawaye take sosai hankalinshi ya tashi muje asibiti kawai yace mata ba musu kuwa suka nufi asibitin,.
Suna zuwa gida Zarah ta Fara shirin tafiya Dan yau tace xata koma, bayan Ta gama Ta fito parlour, har kin shirya cewar sultan? Eh yanzu mukai magana Da mamana zan wuce, shida habib suka rakata Dan amotanta zata wuce, sosai suka mata sallama hakama Maman habib Ta hada mata goma Ta arziki,.
Bayan sun koma Sultan Ya kira mom tan take sanarmai su abbahma fa Sun dade Da samun sauki kawai boyemai tai sannan tace gobe zasu dawo anbada feedback a gama Da result din sultana din Sun dawo dasu Nigeria kan cewa a cigaba Da kula Da itta a asibitin Nigeria din, sosai yai murna gobe zasu dawo Amman yaso ace yaje can sudan huta shida sultana dinshi acan .
Mama kuwa Da sukeje asibitin sai abun daya karu dan kuwa nafashinta sai Sama yake yaki tsayawa hakan yasa hankalin Hafiz Tashi duk ya rasa meke Mai dadi ,abun duniya ya taru yamai yawa Da wanne xaiji, doctor ne ya fito ya kalli Hafiz Da fuskar tausayi,kaje mun samu mudan dai daita mata Amman wlh tana under wani condition, baigama jin Abun Da doctor zaiceba ya wuce ciki shida Hindu ,mikawa Hindu hannu mama tai taje Ta zauna kusa Da itta hakama Hafiz Ya zauna Ta dayan bangaren, a hankali Ta Fara magana,kunga abun Da mahaifinku ya jawo muku kenan, yanzu ya jawo muku bakin jini yanzu kuwa zai gujeku Amman kuyi hakuri komai dan lokacine bansan ya akai har mahaifinku yai wannan abunba baiyi tunanin irin wannan ranarba, gashi Ya jawo mana rashin martaba a idon mutane, Amman kuyi hakuri ninasa karshena yazo, jin hakan yasa Hindi kara fashewa Da kuka nikam dai Na yafewa mahaifinku, nasan dai yau zan tafi, kuka sosai Hindu take inda Hafiz Ya juyar Da kai zuciyarshi Na tafasa, jin shirun momy yai yawa yasa Ya kalleta bakinta mutsi yake a hankali hakan yasa yakara kunneshi, fada Mai take Ya nemar mama yafiya a gun sultan, Sannan Ta Fara salati nan tace GA garinku nan, m
Managed kafin anjima
By hajara Mami natty girl
[9/21, 1:46 PM] Hajaramami: 👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 92*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Kuka kawai Hindu take kamar ranta xai fice, ganin mama ta mutu yasa Hafiz dagata ya fice Da itta sannan Ya kira doctor nan aka basu gawarta suka tafi Da itta gida,yan masarautar Na basu girmansu Kamar yadda waziri ya fada masu nan ya kira sultan Ya Sanar dashi,sosai hankalin sultan din ya Tashi hakan Yasar babu shiri ya nufi masarautar sanda yaje ana mata wanka dashi akai komai aka kaita makwancinta, bayan sun dawo suna karbar gaisuwane, sultan Ya kalli Hafiz ina Hindu tunda naxo ban gantaba bafa? Hindu duk ta daga hankalinta KO abinci takii cima Tana dakinta, mikewa sultan yayi ya nufi cikin masarautar direct bangaren su ya nufa, har dakinta yai knocking jin shiru ya sashi shiga ciki,Tana kwance a kan gado kuka kawai take, zama yayi a kan bedside drower, Hindu ya Kira sunanta Da sauri ta Mike dan bata sanya shigoba, Yaya sultan yaushe ka shigo ban saniba ta fada Tana goge hawayen fuskanta, foodflask din kusa dashi ya dakko yazuba abinci ya mika mata maza cinye wannan abuncin kafin in bata miki rai ya fada tare da hade rai, mikewa tai tashi Tana kallan abincin kafin ta kalleshi yaya Dan Allah kayi hakuri bansan daddy abun dayai nakaba kenan Dan allah ka yafe mana, fa Tana hawaye, kauda fuska yayi ci abinci sai muyi magana tukun, haka taci kadan sannan Ta ajjiye, Hindu karki sa komai a ranki aiba komai nibake kikamun laifiba saboda haka karki takura kanki nidan uwanki ne Na jini a KO ina saboda karki najin wani dar game damu kin gane? Daga kai tayi tare da share hawaye, OK ina Hashim nifa ban ganshiba, yace wai in zauna a gida saiya nemeni ta fada a hankali, ban ganeba? Eh nima hakan yace mun, tsaki yayi zan kirashi muyi magana musan inda ya dusa dan bazai tuzartamun kanwa ba ya fada tare da mikewa ya ficeb, da kallo Hindu ta bishi kafin ta kwanta Dan Kanta ciwo yake mata, .
Sultan bai fadawa so momy mutuwar mama ba Dan Karma su gane yai musu shirin tarba hakama masarautar sun shirya tarbar sarkin su Nada wanda zai dawo gobe, dukda suna jimamin mutuwar mama,.
Washe gari Da farin ciki sultan Ya Tashi yau zaiga sultana na dinshi jikinta yayi sauki,.
Hindu kuwa kwana tai tana nafila tana rukawa mama ta rahama hakama Hafiz duk Sun koma abun tausayi,.
11:30 sultan Ya gama shirinshi Na tafiya gun su sultana Dan motan asibine zasu daukesu tunda baa sallamesu Amman zai ruki a sallamesu sai a basu nurse mai kula dasu,.
Dai dai sultan Ya fito Hafiz ma ya fito yayi shirinshi shima kallan shi sultan yayi ina zuwa kuma? Taro su sultana mana, aaa bazamuyi haka dakaiba nasan kawai karfin hali zakai saboda haka kayi zamanka kawai, no wlh ba haka bane kabari inje, aa Hafiz naga akwai masu zuwa gaisuwa saboda haka ka zauna plz, no sultans ina San zuwafa, suna haka habib ya shigo nan yasa baki Dan sunsan Hafiz kawai daurewa zaiyi yaje, hakadai ya hakura ya koma,.
12:00 girjin su sultana yai landing a airport sultan dake ta hange GA bayi a bayanshi idonshi ya sauka kan momy dake sakkowa fuska dauke Da murnushi sai Abbah Da kuwa abayanta suma suna murmushi, kallan sultan momy tai tana mashi murmushi Amman shi bayanta yake kallo yaga ta inda zata bullo, aikuwa idonshi ya sauka kanta Da wata nurses Na rike Da itta Tana tayata takawa, wani murmushi ya Saki tare da kallan habib gatacan ya fada yana shirin wucewa, da sauri habib ya rikoshi kai afa gaban mom kake bama kaje guntaba kake shirin tafiya gun matarka ko,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 93*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Murmushi yai sannan yai gaba hakama habib yabi bayanshi, yana zuwa ya rungume mom dinshi tare da fadin welcome home my mom, sannan Ya bufi Abbah rumguneshi ya jiki my uncle?shafa kan sultan yayi Da sauki my son sannan kuma my in law,murnushi sultan yayi ya karasa gun kawu ya gaudashi sannan Ya kalli sultana wacce take magana Da nurse din karasawa gun yayi suka gaisa Da nurse din kafin yace ta matsaya zai dauki sultana din, Dan zaro ido sultana tai Yaya sultan gafa su momy anan, aa to taya zan bar Matata dake fama Da jikinta ta wani taka dakanta, kallan mom yayi Mon wai bazata Bari intaimaka. Mataba kuma ta gaji, kallan sultana tai kekuwa ki Bari Ya tayiki mana, baijira cewar sultana ba yauke ta hannun, kallan shi mom tai kafin tai murmushi Dan vata kowa daukarta zaiyiba, abbahma murmushi yai kawai, har motan asibitin ya kaita sannan Ya shiga motan Dan ya dage dashi zaa je,.
Asibitin sukaje akai rubuce rubucen abun Da zaai sannan aka sallamesu tare da nurse,.
haka suka nufi masarautar,akai parking, kallan masarautar anbah yai tare da sauke ajiyar zuciya wai yana masarautar nan har na wani lokaci sai gashi Yau Allah Ya fito dashi, fitowa yai inda bayi ke kwasar gaisuwa gamai kirari a kusa Da waziri sai zubawa yake,murmushi kawai abbah keyi yana jin dadin kasancewar shi Da al,ummanshi,sultan Da kanshi yamai jagora zuwa bangaren shi nada dayasha gyara, kallan bangaren yake nan take fatima ta fado Mai hawaye ya faki idonsu ya goge sannan yai cigaba Da kallan bangaren,.
M
Sultana kuwa suna gfitowa aka taimaka mata suka kaita bangaren Nata har dakinta, kwanciya tai dan tayi bala,in gajiya hutuwa kawai take San ta yi, hakan yasa suka fice suka bata gu, Dan ta huta din inna huta sai taje taci abinci,. Hafiz kuwa saboda Zuwaira Ya fito Amman abun ya bashi mamaki KO kallan inda yake bataiba Dan itta yanzu haushinshima take ji shima din duk Da bashi Da laifi,.
Ganin Ya kasa sakewa yasa Ya ya koma bangarensu dakin Hindu, Da sallama ya shiga ta kalleshi ta amsa tare da mikewa daga salllayar, zama yayi kusa Da itta kafin ya kalleta kukan kika ci gaba dayi ko? Aa yaya kawai idona kemun ciwo Ta fada Tana murza idon, OK Hindu kodai Hashim din sakinki yai? Kallan shi tai me yasa kace haka to? Aa ganinai kowa yanzu ba Ya wani shiga harkar Mu kowa gudunmu yake shine nake tunanin KO kema ya sakeki ne? Aa yaya kawaidai yace saiya nemenine shiyasa Amman ba komai,ok kawai yace haka ya zauna yana debe mata kewa Dan gani yake ta fishi damuwama,.
Sultan kuwa Da kanshi ya hadawa abbah abinci ya nufi dakinshi dashi da sallama, amasawa yai yana fadin sannu dana, ajjiye abincin yayi uncle kazo kaci abinci kagafa baka wani jin dadi ya kamata kaci abinci, OK Ya fada tare da zama banda abun son aina koshi aa uncle ka Fara ci plz haka yasashi a gaba saida yaci,. Sannan sultan ya sanarmai mutuwar mama sosai abun ya bashi tausayi, kallan sultan yayi ina Hafiz din Da Hindu inasan ganin su jeka kiramun su, mikewa sultan yayi ya fice,.
Da sallama ya shiga bangaren nasu ya gansu suna hira, da murmushi ya kallesu uncle nasan ganinku fa, kallan shi Hindu tai saboda me? Saboda ya isa daku ya fada yana kallan su, mikewa Hafiz yai hakan yasa hindu mikewa tasaka hijab dinta sannan suka bi Bayan sultan din, bamai magana har sukaje bangaren Da sallama suka shiga yana parlour, yana jiransu, da murmushi ya amsan yana kallan su kafin ya ce ku shigo mana yayana,jin haka yasa suka karasa ya zaunat Da Hindu kusa dashi kafin su sultan suka zauna,.
Naji abun Da ya faru Amman Dan Allah ina rukanku Da ku daukeni tamkar mahaifinku duk wata matsala taku ku sanar dani zan muku shi sannan ku dauka kamar yadda sultana take ya aguna Yar dana haifa kuma haka kuke a guna, kallan shi sultan yayi uncle ban ganeba, shima Hafiz kallan rashin fahimta yake mai hakama Zuwaira, ganin hakan yasashi, kallan su AI baku San sultana yata bace ittace wacce fatima ta haifa kafin ta bar masarautar nan, zaro ido sultan yai abun kamar a mafarki by how,.
By hajara Mami natty girl
[9/22, 6:21 AM] Hajaramami: 👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 94*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Abunma mamaki yaba suktan to bama sultan kadaiba harda su hindu abun yag basu mamaki dama sultana yar uwarsuce basu saniba,haka nnah yauta lallabin su hindu har saidyaga sun d n saki jikisannan yacezasu iya tafiya sannna suke fice dan zuwa karbar masu gaisuwar mutuwa sultan kuwa bangaren su ya nufa dan yanasan sultana ta kara mai bayani,da sallama ya shiga bayin dake aiki suka amsa suna gaidashi ya amsa tare da yin sama,tunda ya bude kofar ya hangota kwance tana bacci abunta murmushi yai tare da karasawa dakin ya zauna akan gado yana kallata yadda numfashinta ke fita,kusa da itta ya kwanta yana kallanta kafin yasa hannu yana gyra mata gashin kanta, she is my first love shiyasa naji ina santa ittace yarinyar dana so tun tana ciki saigashi Allah ya kawo min itta thanks god bansha wuya wajen nemantaba, surutanshi yake shi daya kafin ya mike saboda karya tasheta tana baccinta dagani kuma na wahalane, sannna ya fice.
Haka sukai ta karbar gaisuwar mutuwa kafin can dare kuwa ya nufi nashi dakin bayan sallar isha,i.
Da sallama sultan ya shiga bangaren nasu dakin shi ya nufa direct saida yai wanka sannna yai shirin bacci ya nufi dakin nata,da sallama ya shiga magunguna ne a hannun nurse din dake kula da itta, karbar maganin yai mungode da kulawa yanzu yaci ace kina gida mun gode sosai,murmushi tai thanks doctor kaima zaka iya kula da itta ai ni zan wuce har bakin kofa ya rakata ta fice sannan ya rufe kofan paurlour din sannnan ya koma dakin tana zaune yadda ya barta murmushi yai tare da k asawa k an gadon sannnan ya dakko magungunan, kalllan magungunan tai kafin ta kalleshi yaya sultan wlh waddan magungunan dacine dasu plz abarni bana sami saukiba, kallanta yai kafin ya saki murmushi plz aunty sultana kiyi hakuri kisha karki sani a cikin wani hali plz kinji kallanshi tai yaya sultan yaushe ka koma haka kamar wani yaro kake shagwaba ta fada tana juyar da kai,murmushi yai kawai sannnan ya dakko maganin ya zuba haaaaa to bude bakin, tana yamutsa fuska ta bude ya bata sai yamutsa fuska take bayan ya gama ya ajjiye a gefe to saime kuma yanzu, shikenan saikaje ka kwanta a dikinka ta fada tana gyra gashin kanta da sauri ya rike hannun let me plz bana san inga kina aiki da yawafa, ya fada tare da zare hannun ya fara gyra mata gashin ya hadeshi gu daya kafin ya hade fuskansu gu dayab,yana kallan idonta ittta kallan nashi tai ganin kallan da yake mata yasa ta fara kokarin dauke fuskanta ina ba zata iya kallan idonshi for some time hakaba, da sauri ya rike habart da hannunshi aa my wife banda ruwar fuska kinsan halin dana shiga lokacin da kika tafibana ganin fuskarki ya fada dai dai kunnenta sosai jikinta ya hau rawa sultan nasan rudata,kiss ya bata a kumatu kafin ya bata a goshi ganin kissing nata yake san yi yasa tai saurin fadin yaya sultan fitsari nake ji, dagowa yayi ya kalleta ganin idonta a rufe yasa yai murmushi sannnan ya dauketa yai toilet da itta.
Kalllanshi tai yaya sultan to ka fita mana ta fada tana kallanshi uhmm ya fada tare da ficewa, tai murmushi sannnan tai uzurin gab anta, shikuwa daya fito kayan da zata sa ya dakko mata ya ajjiye sannna ya zauna yana jiran fitowarta, ta fito tana dafa bango, kayan ya bata tasa sannna ya kashe musu wuta suka kwanta ya rumgumeta a jikinshi a haka sukai baccin,,.
Washe gari waxirine zaune a kusa Da sarki, rankaa ya Dade yaushe zamuyi bakin dawowar sannnan mu nadaaka a kan mulki kallan waziri yai uhmm sai Bayan an gama jimamin mutuwar Maman Hafiz tukun sannan kuma Ma banajin ni zan hau Hafiz KO sultan zan daura, jijjaga kai waziri yai Dan Yasan mutane Sun fi san sultan,.
Da sallama Hindu ta shiga dakin sultana, Ta amsa Tana kallan Hindu din, sama hindu tai kusa Da itta Ya jiki sultana,?Da sauki Hindu nan kuma kowa yai shiru,ganin shirun yayi yawa yasa Hindu kallanta, plz sultana kiyi hakuri akan abubawan Da suka faruwa Dan Allah kiyi hakuri Da sauri sultana Ta rike hannunta no karkice haka yar uwa AI ba komai yanzu komai Ya riga daya wuce,murmushi Hindu tai tare da rumgume sultana din ittama Tana murmushi suka rungume juna,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 95*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Hafiz yana tafiya sauri yake zaije kiran Da Abbah kemai yau kwana 20 kenan Da mutuwar mamansu kuma An riga Da an yankewa daddy dinsu hukuncinshi,. Sannan sultana take warke sosai kamar ba ittaba .
Zuwaira Data tahu sukai kicibus har takusan faduwa yai saurin rikota, Da sauri Ta baya, Zata wuce yai saurin shan gabanta, wai Zuwaira menai mikine saboda me zaki dinga dauremun fuskane? Uhmmm dacan din sakin maka fuska nakene kaga Dan Allah ka Rabu dani banaso ana dolene TQM fada Tana kallan shi ganin itta yake kallo Da mamaki hakan yasa Ta raba Ta gefenshi Ta wuce, ajiyar zuciya Ya sauke sannan yai gaba ,.
Da sallama Ya shiga bangaren abbah din, sultan Na zaune suna hira zama yayi, abbah gani Ya fada dadan damuwa a face dinshi sharewa kawai Abbah yai, to dama ina tunanin kunsan cewa wannan kujera ba kowa saboda Da haka nake San ku sasant kanku Wanda kuke ganin zaihau mulki danni bazan hau mulkiba Na riga dana gama nawa aikin a yanzu kamata yayi ace ina hutawa, Da sauri Hafiz Ya karba aiba Wanda baisan sultan shine zaihau mulkiba shi Ya dace yahau shima sultan Ya karbe amma abbah ai babba aka sani Da mulki KO, ko agida naga babba ke mulkin karami, as Hafiz Ya fada wlh bazan hau mulkinnanba kwata kwata ban dace dashiba Kalli abbah yai abbah sonake ni zanma tafi waje saboda IN Sami salama Da abun Da zuciya Ta take ciki, Kallan shi Abbah yai dama tunda Kwan shigo naga alamar kana Cikin damuwa maza dana fada mun meke damumka indai har ka daukeni uba zaka fada mun,.
A gaskiyq bazai iya buyewa abbah komai ba Nan ya fada mai komai game da Zuwaira Da San Da yake mata itta kuma bata sanshi gara yaje waje KO zai sami sawaba,wace itta inasan ganinta, zan mata magana, aa Abbah kar aimata dole kawai abarta, hmmm kawai sarki yace kafin Ya kalli sultan kaine zaka hau kan mulki ka shirya jibine bakin hawarka, zaku iya tafiya Ya fada yana kallansu, murmushi sukai tare da rumgumeshi suka fice,.
Kallan Hafiz sultan yai ka tabbatar wannan yarinyar Na sanka Da? Nidai bansan mataba Amman nidai gani nake tanq sona, OK kawai yace haka har kowa Ya nufi nashi bangaren,.
Sultana na daki hakan yasa yai daki, zama yayi akan gado yana kallanta tana daurin Dan kwali murmushi tai kafin Ta zauna kusa dashi me ke faruwa shiru yai yana kallanta kawai sanki nake Da yawa Matata, murmushi tai nima ina..... Sai kuma tai shiru Tana shirin mikewa Da sauri Ya rikota plz karasa inasan inji daga bakinkil kinsan baki taba cewa kina sona ba kuwa, xama tai uhmmm ai naga nima din ina sanka gashi na fada, OK say it again, I love you Yaya sultan murmushi yai hade Da dariya yama rasa Ta ina zai Fara fada mata yadda yake mata nashi San, batsammni tajiya Fara bata wasu hot hot kiss Ta KO ina, hakan yasa Ta kwace Ta fice Tana murmushi, shima murmushin yai tare da kwanciya akan gadon yana San sultana kuma yana sha,awarta Amman baisan Ta inda zai Fara fada mataba, a haka har bacci Ya daukeshi .
Sultana na fitowa dai dai lokacin Zuwaira Da Zulai suka shigo,murmusji tai tare da fadin welcome,zama sukai suna amarya a gidan mijinta, hmmm kawai tace kafin Ta Kalli Zuwaira, Ya kuka Kare da Hafiz ne? Hmmmm so nake kawai in horashi shiyasa har yanzu nake mai jan aji,aikuwa ajin yanzu zai tsinke saboda dole kije daxun Abbah Ya kirani yake tambaya wace Zuwaira Hafiz nasanta Amman bata sanshi har yana fadin zaiyi tafiya saboda samun saukin kanshi
By hajara Mami natty girl
[9/22, 6:24 AM] Hajaramami: 👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 96*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Zaro ido Zuwaira tai shi sarkin Ya kiraki, har abun yayi zafin Da Hafiz zaikai karata kawai Dan ina danmai wasa kuma maye na cewa zai wani bar gari Ta fada Tana turo baki ,dariya Zulai tai wannan shagwabar aiba mu Ya kamata aiwaba Hafiz Ya kamata kiyiwa,kallanta sultanq tai Amman aiku kun dai daita Da habib KO, daga mata kai kawai Zulai Tana murmushi, mikewa Zuwaira tai ina zuwa, Da sauri Zulai Ta karba kice dai zakije gun Hafiz eh din Ta fada Tarw Da ficewa,suna mata dariy kafin suka ci gaba Da hirar su ,.
Da sallama Zuwaira ta shiga bangaren nashi yana parlour yana duba abu a laptop dinshi, Kallanshi tai tunda Ya amsa sallamar Ya dauke kai, ajiyar zuciya Ta sauke Ta nufi Fridge ta dakko lemo sannan Ta shiga kitchen ta dakko cup sannan Ta yanka fruit Ta fito dasu a tray ta ajjiye agabanshi sannan Ta dauke laptop din ance bakaci abinciba shine akace in kawo Maka. Kallant yai ban laptop dina baxan iya cin abinciba yanzu saboda raina a bace yake zama tai a kasa kusa dashi Waya bata Maka rai dazai hanaka cin abinci? Wacce nake so NE bata sona saboda gara IN mutu kawai IN huta murmushi tai kayi bincike ka tabbatar Da bata sankane Da zaka dinga kaita gaba? Eh nayi bincike mana saboda na gani a idonta ,murnushi tai ka tabbatar Da hakan, shiru kawai yai mata hakan yasa Ta kalleshi itta yake kallo, dauke kai tayi nidai bance bana sanka kawai ina maka hakane saboda inna tuna bin matan dakai Da sauri Ya katsata dane wannan Zuwaira yanzu Na tuba wlh, murmshi ittama tasan Da hakan Ya tuba itta zata bada shidar hakama, kaci abinci nizan wuce Ta fada tare da ajjiyemai laptop din,to yanzu kina sona? Batace komaiba Ta Fara tafiya saida Ta kai kofa Ta juyo kafin Ta furta ina sanka Hafiz sosai kuwa Da sauri Ta fice Ta barshi Da mutuwar zaune kafin Ya saki murmushi aikin dabai karasaba kenen,.
Kusan magariba sultana tai sallami masu aikinta yau Da kanta zata hadawa mijinta abinci haka Ta shiga kitchen ta hada masa haddun abinci sannan Ta jere a dining ta nufi dakinta tai wanka Ta tsara kwalliya Ta gani Ta fada sanda taga kanta a madubi saida tasan itta Ta gama gadewa sannan Ta nufi parlour Bayan tayi sallah, a parlour din tai isha sannan Ta kunna Tv Tana kallannta, har Bayan sallah isha,i.
8:30 dai dai Ya dawo gidan Tana jin sallamarshi Ta Mike ta nufi inda yake Ta rumgumeshi tare da fadin sannu Da zuwa,shima Ya runguneta tare da fadin sannu Da gida,sakinshi tai muje kai wanka sannan kazo kaci abinci babu musu yabi bayanta suka nufi dakinshi, Ta taimaka Mai yai wanka sannan Ta ba shi gu Dan shiryawa,.
A parlour Ya sameta Ya sakko yana zuba kamshi, Kallanshi tai kayi kyau Yaya sultan saura kaci abinci kuma, Ya zauna a dining ta zuba mai abinci Saidayaci you koshi sannan Ya cika plate Ya saka a gaba saida Ta cinye,.
Suka koma parlour suna kallo har wajen 10:00 sannan sultana tai dakinta wai bacci take ji shima Ya kashe kayan kallo, suka nufi daki kowa yai nasa dakin, wanka sultan Ya Fara yi Ya shirya hakama sultana Tana shirin kwanciya text dinshi Ya shigo wayarta, kizo ina San ganinki kawai Ta gani murmushi tai Dan dama ba zata iya kwanciya Baba sultan dinta a kusa Da itta ba hakan yasa Ta saka hijab Ta nufi dakin nashi,.
Parlor din babu kowa hakan yasa tai sama zuwa dakinshi Da sallama Ta shiga dakin duhu, Yaya sultan Ta kira sunanshi Tana tafiya, rungumeta yayi Ta baya tare da fadin gani Matata sultana sannan kuma kanwa a guna, murmushi tai tare da juyawa Tana kallan shi, gani yaya mezaka fada mun kake kirana?
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 97*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
Kawai ina San ganin Matata a kusa danine shi yasa, Hmmmm kawai tace Dan ta gane inda Ya dusa, daukan Ta yai yakainta kan gadon kafin Ya kalleta sultana ina Da bukatar kine Amman saida amincewar Ki. Duk Da kirjinta Na duka hakan Ta dake batace Mai komai itta yau tayi alkawarin farantawa mijinta, kin amince kenan tunda kinyi shiru ko sultana. Nanma shiru murmushi yayi kafin Ya fara kissing Nata duk tabi Ta rikirkice (to dai kunsan ni daga haka bana kara gaba dukda nasan nafisah isah Da yahanasu sunanan sun zuba ido to Amman fa saidai kumin sorry)saida yai romancing nata sosai har itta Ta fice hauyacinta kafin kuma Ya Fara shirin maida sultana dinshi babbar mace a wannan rana wato cikakkiyar matar aure, ganin hakan yasana jawooo kunsan sauram wato na jawo kofa duk nafi na jana karmu fice Amman Saida nafi karfinta muka fice bama mu zauna a gidanba masauarautar muka Bari gaba daya,.
Wannan dare Hafiz yayishi cikim jin dadi tunda Zuwaira abar sanshi Ta amince dashi maiyafi ranta, Hindu kuwa ittama kamar yadda Hashim baya kirant hakama ittama bata kira tunda ba abunda tarasa gun Abbah dinsu wato babaga sultana,.
Yau daga sultan har sultana din saida suka makara sai wajen Bayan asuba sannan sultan Ya Tashi Da adduar Tashi daga bacci maizaiba sultana tukucin Abun Data Mai sosai yaji yana kara San matarshi, baccinta take da gani na wuyane, kiss Ya bata sannan Ya Tashi yaje toilet yai wanka sannan yai sallah Ya koma Ya hada mata Nata ruwan,.
Kusa Da itta Ya zauna taya zai fara tashinta badan sallahba barinta zaiyi tasha bacccinta inama anayiwa wani Sallah Da ba abun dazai hanshi yi mata Tata. Dai dai kunnenta Ya Fara kiran sunanta a hankali. Haka har ta fara motsawa kafin Ta bude ido Ta sauke akanshi, Da sauri Ta rufe ido tuna jiya yadda sultana ya koma mata kamar bashiba harda mata kuka, murmusui yai Dan yasan wai kunyar shi take ji, bai tsaya biye mataba Ya dauketa Ya kaita Toilet Da taimakonshi tai wanka sannan Ta fito Ya shinfida mata sallaya tai sallah saida tai azkar dinta tai komai sannan Ya maida kan gadon shima Ya kwanta kusa Da itta, a hankali Ya furta thanks habibti ina sanki Da yawafa, murmushi inaso Bayan ana wahalar dani,aaa habibti aurenfa kenan fushi kike dani turo baki tai tare da daga kai, zaro ido yai mai zanyi Dan in fanshi kaina aimun afuwa,saika mun waka, dariya Yai kice mawaki kike San IN zama daga Mai kai tayi OK to wacce wakar kike so? Mai dadi zaka mum, juyo Da itta yai kafin yai gyaran murya Bari in Fara kinga gari yayi haske inasan zanje muyi magana Da waziri Ma, Amman bari in rairawa habibti waka Mai dadi,.
Zan rayuwa dake
Zan mutu dake
Abanda dani dake zamu zauna
Indan nace ni ina nufin ke idan nace ke ina nufin ni,
Dariya tai Yaya sultan a ina ka iya waka? Ai wannan ba komai bace barima kiji wata ,.
Ciki Da zuciya sultana sanki
sultan yayi zurfi inama
Ace sultana bazanyi rabo dakeba
Dariya tai sosai ya zuba mata ido yana kallanta sosai santa ke kara shigarshi, habibti kina San wata wakar ne? As Ya isa haka my golden and star husband, dariyar murna yai tare da rungumeta yi baccinkin ki huta haka suka kara komawa baccin,.
We have rish to the end of novel sister saiku Fara shirin bankwana Da masarautar muce,
By hajara Mami natty girl
[9/22, 11:53 AM] Hajaramami: 👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 98*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
This page is for you KHADIJA SALIM GHALIB & AISHA LUKMAN ISAH
Sanda sultana ta Tashi,bataga sultan ba mikewa tai ta zauna dukda jikin yanzu Ya rage mata zafin sakamakon ruwan zafin Da ta shiga, toilet ta shiga Ta kara gasa kanta sannan Ta fito Ta karasa gaban madubi Ta zauna kallan kanta dai dake jike ruwa na zubuwa, dryer Ta dauka Ta Fara drying bashi, Da sallama sultan Ya shigo Da abinci akan Tray kallan shi tai kafin Ta dauke kai bata San su hada ido dashi murmushi yai, wai kunyar shi take yi, karasawa gunta yai Ya karbi dryer din Ya ajjiye sannan Ya juyo Da itta duk Da haka taki yadda su hada ido, nifa ban gane wannan sussunne kan ba aiyanzu bai wani kunya tsakanina dake sultana munfa riga mun zama daya,kallan shi tai ganin itta zai kallah yasa tai saurin shirin dauke kai ya riko habarta haba habibty Dan Allah ki bari, mikewa yai Ya dauki dryer din Ya fara Mata yana mata hira itta dai daga uhmm sai uhm uhm ne nata amsar, bayan Ya gama Ya je Ya dakko mata kayan Da zata saka saida kwalliyarta sannan Ta dauki kayan Ta shige toilet Ya bita Da murmushi, tana fitowa taga har ya hada mata tea din Ya zuba mata dankalin Da komai Da komai, zama tai da kanshi yai feeding Nata,.
Bayan Ya gama yace mata zaije suyi magana Da waziri yace yana San za suyi magana Da shi, kallan shi tai wai yaya ba zakaje office bane? Aa fa nina dauki hutu zan huta Da mamata NE Ya fada yana murmushi ittama murmushin tai bari inzo muje daga nan zan wuce gun momy, tare suka fita har bangaren momy Ya raka Ya gaida mom din sannan Ya wuce,.
Kallnta mom tai yatA kinfa gujeni kwana biyan nan, aa wlh mom kawai dai kinsan jikinne bamu Dade da samun lafiya ba, daga kai mom tai gaskiyane, suna hira Hindu ta shigo Da sallama, kallan ta mom tai da murnushi zo yata kema ki zauna, zama tai tana murmushi, kallan mom Hindu tai mom plz ki fadawa Abbah ya kira Hashim ya sakeni kawai yabarni anan ga cikin dake jikina mom ko kirafa bayayi, kallan tausayi mom tai mata aa abun baikai ga har sakiba zaizo za muyi magana kar ki kara zancen saki kinji, daga kai tai tana goge hawayen face Nata sosai taba sultana tausayi har tasa Ta itta ta zubar mata Da hawaye,.
Sultan ne Da Hafiz a zauna kusa Da abbah sai waziri dake lissafa abun Da zaai gobe na daurashi a kan mulki, yanwancin komai Hafiz ne ya shirya, Bayan sun gama waziri Ya tafine, abbah Ya kalli Hafiz, wai yaushe dana zai kai kayan aurene yamun suruka, murmushi Hafiz yayi ai mun daidai Ta itta yarinyar Da sauri sultan Ya karba wani satin habib zaikai kayan bikinshi gidan su zulai mai hana tunda kawar matar habib dinne muma mukai tare inyaso sai asa ranar tare, daga kai Abbah yai hakanma zaa yi zansa akawo kayan bikin Da haka suka Yanke shawara, Bayan nan sarki Ya kalli Hafiz ban number din Hashim dinnan yazo Ya sakar mun mata bana San rashin mutuci taya zai wani ajjiye mun Ya haka wannan haukane, bashi number din Hafiz yai Ya karba,.
Suna gun yai dailing number dun bugu uku aka daga,.
Da sallama sarki Ya Fara Hashim ya amsa,ni baban sannan kuma uncle din Hindu inasan kaban mahaifinka za muyi magana, sosai gaban Hashim ya fadi Allah Ya gani yana San Hindu Amman kawai haushinta yake ji saboda mahaifita Yai, to yace sannan Ya mike ya nufi masarautar tasu Da sallama Ya shiga sannan yaba daddy din nashi gashi zakuyi magana,karba yai Ya kara a kunne bayan sun gaisa Abbah yamai bayanin kanshi kuma Ya ganeshi, dama Hashim ne ya ajjiye Hindi a gida shibai saketa ba sannan bai zo Ya dauketa abun tun baya damunta har ya Fara damunta sannan GA ta da ciki kuma kasan baa San mace mai ciki Da tunani shine nake tunanin KO zai fada mana abun daya yanke KO sakinta zaiyi ko maidata saboda Ta samu saukin zuciyarta, hakuri Baban Hashim ya bashi Dan tunba yauba yake fama Da Hashim din Amman wai saiyace yana bata punishment itta Da bata itta tai laifiba sannan Ya shaida mai gobe zasuzo su tafi Da itta Da haka sukai sallama, baban Hashim ya mika sannan ka shirya gobe zamuje ka taho Da matarka, murmushi Hashim yai tare da fadin Allah Ya kaimu ,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 99*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
THIS PAGE IS FOR YOU HAJARA IBRAHIM & MARYAM MUHAMMAD KANO
Kallan abbah sukai Abbah me sukace? Gobe zasu zo su tafi Da itta sosai Hashim yaji dadi Amman bazasu fada mataba haka suka mike sukaje bangaren mom din akai Ta hira dasu,. Haka yau Ta kasance musu duk a Cikin dadi suke,.
Da daddare hindu Na zaune akan gado chatting take wayarta Ta Fara ringing, Hashim ne saida gabanta Ya fadi kin dagawa tai haka yaita kira so yake Ya sanar mata gobe zasuzo Amman taki dagawa, hakan yasa jikinshi yai sanyi lalllai tafi fushi dashi sosai,.
Da sallama sultan Ya shiga dakin sultana, zama yai Ya mika mata ledar hannunshi ga wannan gobe itta zakisa muyi anko nida Matata, kuma gimbiya Ta, murmushi tai ta karba Ta bude wata haddadiyar gown ce tai bala, in yin kyau, kallan shi tai tayi kyau Yaya ina San rigar, to taya zan gane rigar Ta miki Ya fada yana kallan ta, murmushi tai kafin Ta matsa kusa dashi Ta bashi kiss, aa fa habibty wannan bashine zai nuna Ta miki ba,murmushi tai kafin Ta Fara bashi hot hot kisses, duk Ta rudar dashi gaba dayansu sunma fita a haiyacinsu hakan yasa na rufe musu kofa nai tafiya Ta dan nima bacci nake ji,.
Washe gari masarautar Sun taashi Da aiki Dan yaaune za ai nadin sarauta,yau sultan Da wuri Ya fice saboda yana Da ai yukaa a ganshi hakama uban gaiya Hafiz Dan iyaa cewa shine ya hada komai saboda haka komai a gunshi yake, bangaren mom aiki ake hakama bangaren sultana aabun saini danaa gani,.
3:30 dai dai aka gama hade masarautar tayi mugun hadewa, a gajiye sultan Ya shiga banagaren nasu sultana dake kitchen Tana hadaa abubuwa ganin shigarshi yasa tabar WA masu aikin tai dakinshi a kan gado Ta ganshi kwance,sannu Ta fada tare da zama kusa dashi aikin kenan wani abunma sai mun baka sarautar, murmushi yai tare da jawota Jikinshi ai zaki dinga tayani? Ni aa inanan ina zaune Amman zan dinga kiranka ina maka kalaman soyayya murmushi yai tare da bata kiss Ya Mike Bari inje in yi wanka 4:00 Za,a fara kema kije ki shirya yanzu, OK Ta fada tare da mikewa Ta fice,.
Hafiz dake tafiyaa so yake Ya hadu Da Zuwaira Ya Bata kayan Da zata saka Dan suma anko zasuyi, kamar daga sama Ya hangota tana sauri zata je gida yau, dasauri yasha gabanta har ta tsorata harara shi tai kafa ban tsoro, sorry ya fada yana hade hannunshi gu biyu, murmushi tai zan wuce, holding arm yayi to ni Na hanaki ne,? Murmushi fadi abun Da zaka fada, kayan Ya dakko Ya mika mata, kallan shi tai maye wannan kuma, hade rai shikenan baazanwa Matata kyautaba saita tambayanei maaye,shikenan Ya fada yana shirin tafiya Da sauri tasha gabanshi to yi hakurk tasa hannu zata karba Ya rike hannun nata
By hajara Mami natty girl
[9/22, 11:57 AM] Hajaramami: 👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 100*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
THIS PAGE IS FOR YOU FIRDAUSI IBRAHIM & NASIBA ABBAS AMRAH
Da sauri Ta kalleshi, marairaicewa yayi wai Zuwaira hannunma baa zaki bari in rikeba, Hafiz babu kyaune yau inda muna Da aure aibazaaan hanaka ba, sakinta yayi yaana murmushi Allah Ya bashi uztajiya, wannn zakisa muyi anko kinji, daaga kai Tana kaallanshi, zan tafi OK ya fada har taste juya zata Ya kirata Zuwaira inaaa sanki, murmushi tai, nima ina sankaa Da Gudu tabaar gun Yasar bita Da murmushi,.
Dakin Hindu yaje yaga tana cin Dan wake tabe baki yai masu ciki da kwadaayi Yaa fada, gashi wannan kayan zaki saka kinji KO? Kallan kayanta tai OK naaji kowa Da nashi mijin Da budurwarshi yake anko ni kuma banda kowa, murmushi Hafiz yaii Dan kuwa Hashim NE two sashi Ya siyo musu kaya iri daya Da itta Amman yace karya fada Mata,.
Sosai gun ya ciki Da mutane, zuwan su sultan Da sultana, Da Hafiz ake kawai sai su habib,.
Dakin sultana sultan Ya shiga Ta gama shirin sarka take sakawa, karba yayi Ya saka mata tare da ja mata alkabbar sannan suka fito motocin sune Da bayi masu take musu baya, Hafiz Ta gani Da Zuwaira sai Zulai Da habib duk sunyi anko, nan take nafisah Ta fado mata taji ina ma Tana gun,. Da haka suka kama hanya,.
Hashim dake dakin Hafiz yana shiryawa dan Sun Dade da zuwa yace suyi gaba zasu biyosu daga baya, yana gamawa Ya nufi dakin hindu Ya shiga parlor ba kowa, hakan yasa yai dakinta Ya tura kofa tana kwance akan gado, kawai bata jin dadin fitar itta daya zataje shi Yasa Ta yanke shawarar sai An kusa gamawa zataje, hawayen fuskanshi Ya goge kafin Ya karasa kan gadon dake tayi zurfi a cikin tunaninta batasan Ya shiga ba saiji tai an rumgumeta Da sauri Ta dago Tana kallan shi, kamar a mafarki, Da sauri take San zare jikinta Amman yaki sakinta sorry, Hindu kiyi hakuri zuciya ce, Da kyar Da komai Ya shawo kanta Ta hakura sannan Ya tayata Ta shirya kallan kayanshi tai Irin Nata nan yai mata hayani, haka suka nufi gu, kuwa yaji dadi Da suka shirya,.
Anan aka nada sultan akan sarauta kowa Ta shaaida, bayan an gamane sultan Na karbar kyauta Ya riko haannun sultana zo kiga wani habu, binshi tai suka shiga taron, tun daga nesa Ta hango wata kamar Nafisa, saida sukaje daf Da itta,da murna ssultan ta karasa gunta suka rungume juna kafin suna kallan yaushe gamo, nan nafisa take nunawa sultana mijinta Wanda Ya kaasance aboki ga Hafiz, sosai sultana Tai murna Da hakan, haakaa aka gama komai kuwa Ya kama hanyar gida inda Hashim ya tafi Da matar shi nafisama suka koma ,.
Haka rayuwa ke tafiyaa komai yana tafiyaa with year, months, weeks, days, minutes, seconds har gashi Allah yasa kaawo mu wannan lokacin,.
By hajara Mami natty girl
👑🕍👑👑🕍👑👑🕍 🕍👑🕍👑👑🕍👑👑
🕍👑👑🕍👑👑🕍🕍🕍👑🕍👑👑🕍🕍👑
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍🕍
👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑👑. * *MASARAUTAR MUCE 101*
🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍
👑👑👑👑👑🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑
🕍🕍🕍🕍🕍👑👑👑👑🕍🕍🕍
FANTASTICS START WRITERS (F S W)
```INDICATED TO MAMAN SHUKRAH AUNTY UMMI```
THIS PAGE IS FOR YOU SA,ADATU GARBA KAZAURE &HAFSAT ABDULKADIR TOGETHER WITH NAFISA AHMAD AHMAD
bayan wasu shekaru,.
Sultana ce zauna a parlour Tana duba jarida, da guda yaran suka fada kantaa, momy mun dawo daga wanjen grandma, ajjiye jaridar tai tana kallansu to sannunku Da zuwa Ya kuka GA grandmaa din naku, Tana lafiya mun, yaran Da ba zasu wuce shekara bakwai bakwaibaa suke fada mata yadda sukaa tadda mom, dash sallaama sultan Yaakov shigo Da kaya hannunshi, washhh Ya fada tare da zama wannan yaran naki suka barni Da diban kaya,murmushi tai tare da fadin sannu Bari inba jakadiyaa saita kai masu daaki, kayaan su teddy NE dai kayan wasan yara, dauka tai ta sauka kasa taba jaakadiya kafin Ta dawo suna gun sultan sun dameshi, ganin hakan yasa Ta karasa gunsu,ku tashi muje kuga kayan wasanku, Da Gudu suka mike suka fice, Ta bisu Da murmushi, riko hannunta sultan yai zaunar Da itta gaskiya in zakki sake ban yara Mata zakiban masu Kama da ke kigafa Ashraf dashing ashrim dani suke kama, murmushi to shikenan karka damu Ta fada tare da jan haancinshi, ashhh Ya fada hakaaan yasa taSa dariya ka fiya raki Yaya sultan, kawo in miki kiji inba zafi, Da saauri Ta Mike tare Gudu yabi bayanta,..
Su habib sunsha biki Dan har su Zulai Nada ciki hindu Ma ta haihu lafiya abunta,.. Gashi sultana ma ta haihu Yan biyu sukaci sunan, baban sultan Da Baban sultana,.
To ALHAMDULILLAH ANAN NAKAWO KARSHEN LITTAFINAN MAI TAKEN SUNA MASARAUTAR MUCE INA ROKAN ALLAH YA YAFEMUN KURA KURAN DANAI, AMEEN,.
*SADAUKARWA*
HAUWA MUHAMMAD FALALU
HAFSAT MUHAMMAD FALALU
AISHA MUHAMMAD FALALU
SADIYA MUHAMMAD FALALU
AND MY DAUGHTER
ZAINAB NURA ADO GWARAM TOGETHER WITH MY SON
AL,AMIN AUWAL GOMBE,.
MY PARENT YOU ARE THE BEST I.E MAMA AND BABA
YOU ARE THE BEST
HAUWA UMAR ALPHA
FATIMA SALEH AHMAD
HAJJARA HARUNA
AISHA RUNKA
ZUWAIRA MUHAMMAD
MY AUNTY
AUNTY UMMI
AUNTY HURAIRA
MAMAN MAHMDU
MRS MALEEQ YOU ARE THE BEST
YOU ARE SPECIAL SISTER HAKEEY .
GREETING TO ALL MEMBERS OF COLLEGE OF NURSING AND MIDWIFERY BIRININ KUDU YOU ARE THE BEST
INA GAIDAKU FRIENDS DINA WANDA NA SANI DA WANDA BAN SANIBA I REALY LOVE YOU SO VERY MUCH
DAGA TAKU HAR KULLUN
HAJARA MUHAMMAD FALALU (MAMI NATTY GIRL)
BY HAJARA MAMI NATTY GIRL
Download Masarautar Muce Complete Book Here
0 Comments
Thank you for this comment