[6/29, 11:00 AM] Muhievvert: 'YAR BARIKI

   ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

  (15)

"Kiyi tunani,matan aure nawa kika dauki hakkinsu wajen nasarar dauke hankulan mazajensu a kansu? Allah bazai kyaleki ba,da rai da lafiyarki muddin baki tuba ba sai kinga sakayya."

   Har zuwa yanzu da take kwance a gadon d'akin na hotel d'in,ita kad'ai. Wadannan kalaman ke yawo a kwakwalwarta. Damuwar da ta yawaita a zuciyarta ya hanata zuwa bangaren da ake fatin hibba,hakan yasa ta kama d'aki da zummar ta kwana da safe tayi gida. Batayi iya runtsawa ba kalaman Haris sun shigeta matuka. Ta tuno yanayin fuskarsa wanda ke nuni da tsantsar takaicinsa na halin da rayuwarta ke ciki. Bata taba cin karo da wanda ya nuna kyama a harkar rayuwarta ba kamar shi.

     "Nan da kike ganinsa ustaz ne,ya fiye takura kansa baison ya more rayuwarsa."

    Kalaman Kb akan Haris suka fad'o mata. Tabbas ta yarda da hakan,Haris kamilin mutum ne wanda bai sha'awar rayuwar da suke ganin itace ta arziki a garesu.

                    *****

    Da zarar ya runtse ido,ita yake gani. Bai manta sa'adda ta dubeshi fuska dauke da ruwan hawaye wanda yasan na munafunci ne. Amma meyasa ta kasa b'acewa tunaninsa,bai manta sadda ta fice a motar ba jiki a sanyaye. Toh hakan yana nufin taji nasiharsa ne ko kuwa? Amma ai inda ace ta dauki zancensa,babu abunda zaisa ta shiga hotel d'in. Ya dafa goshinsa yana mai runtse ido,bayason ya dunga tunanin wacce bazata amfaneshi da komai ba. Hakan yasa ya mike tsam yayo alwala ya soma nafila duk domin kaucewa tunanin wacce ko sunanta bai sani ba.

                   ******

     "Gobe zan koma Abuja,inaso muyi wata magana ne."

   Ya tsayar da rubuce rubucensa sannan ya dago fararen idanunsa ya saukesu akan Kb,fuska ba walwala.

     "Na'am,ina sauraronka."
[6/29, 11:00 AM] Muhievvert: 'YAR BARIKI

   ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

  (16)

Kb ya numfasa yana mai sassauta muryarsa,ba tare daya yarda ya dubi kwayar idanun Haris ba ya soma magana

     "Look Haris, nasan na aikata ba daidai ba. Nasan zuwa yanzu ka dauki zafi dani baka kaunar sanyani a idanuwanka ma,amma don Allah kayimin uzuri wallahi kaji na rantse maka babu macen da nake mu'amala da ita a waje idan ba Baby Tasleem ba."

    "Baby Tasleem."

  Haris ya nanata sunan a ransa,sai yau ma yasan sunanta. Kb ya cigaba da magana

    "Nasan ban kyautawa Yasmeen ba kamar yanda ban kyautawa kaina ba. Gaskiyar magana rabuwa da Tasleem abune mai matukar wuya agareni,shiyasa na yanke shawarar zan aureta a matsayin matata ta sunna."

    Wani mugun kallo da Haris ya watsa mishi ya sanyashi kauda kansa cikin jin nauyi,ya numfasa kafin ya cigaba

     "Yes Haris, kabar yimin irin wannan duban,raya sunnah nakeson yi ba wai zina ba. Duk da dai zuwa yanzu Baby tak'i bani had'in kai,ta nunamin babu abunda ta tsana kamar aure,wannan shine hakikanin damuwata. A matsayinka na amini kuma d'an uwana don Allah ka taimakamin da shawara."

     Ba tare da ya jira cewar Haris ba ya mike tsam ya nufi hanyar fita cikin jin nauyin amininsa. Saida yakai k'ofa sannan ya dakata ba tare da ya juyo ba

     "Ba hakan dana fada yana nufin na rabu da soyayyar matata ba,a'a. Inason Yasmeen matuka saidai inason raya sunna. Idan har ka amince da bukatana,ka taimakeni kayi jihadi wajen shawomin kan Tasleem domin cetomu daga wannan rayuwa please Haris. Goodbye."

    Ya fice cikin sauri ba tare da ya juyo ba ballantana ya lura da irin firgicin dake akan fuskar amininsa.

     Rike kai yayi yana mai runtse ido,gabansa na duka da sauri da sauri. Aure?!! Tsakanin Kb da baby tasleem?!!

    Ya nanata a zuciyarsa,kafin ya kwantar da kansa akan kujerar ya runtse ido. Toh menene matsalarsa? Me zaisa zancen nan ya dameshi? Amma kuma dole zai dameshi ai,ko babu komai,kanwarsa ce fa Kb ke shirin yiwa kishiya da karuwa! Dole yaji tsanar auren,dole ne ya taya 'yar uwarsa kishi. Kishi mai tsanani.

     Ya bud'e ido,kafin ya hasko halittar Baby da wayewarta sannan ya dawo ga kanwarsa wacce baby bazata nunawa kyau ba saidai ta fita a halittar jiki da kuma barikanci. Ita d'in ta kasance saliha,domin ko a gida bata fiye magana mai tsawo ba,sam, bata da hayaniya tamkar Haris d'in take. Wannan yasa duk cikin kannensa yafi tausayinta yafi sonta tasu tafi zuwa d'aya. Anya kanwarsa zata iya kishi da gogaggiyar mace irin Tasleem? 

"Idan har ka amince da bukatana,ka taimakeni kayi jihadi wajen shawomin kan Tasleem domin cetomu daga wannan rayuwa please Haris."

    Ya tuno zancen Kb,wannan ya nuna kenan yayi kokarin shawo kan Tasleem domin ta amince da bukatarsa na suyi aure amma sam,tak'i aminta.

    Haris ya girgiza kai cikin takaici da bacin rai

     "Tabbas Kabir bashi da kunya."

    Ya fad'a a fili. K'arar wayarsa ta katseshi,ya duba yaga sunan Daddy. Da sauri ya d'auka. Bayan sallama da gaisuwa ne Daddy ya sanar dashi ya shigo yazo ofishinsa yana nemansa. Ya amsa kafin ya tashi a hanzarce ya nufi ofishin director kuma uba a gareshi,Alhaji Idris.
[6/29, 11:00 AM] Muhievvert: 'YAR BARIKI

   ©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)

  (18)

Shewarsu ta katse mata tunani,hibba tace

     "Allah Sarki uwata,hauka nakeyi zan mance da ita? Karki ganni anan, duk wata saina tura mata kud'i ta account kawata Balaraba. Ba don wannan mugun uban nawa ba ai da wataran saidai ta ganni naje ziyara. Kunsan dai duk iskancina bana manta MAHAIFIYA."

    Baby tayi shiru,jikinta a sanyaye. Ita kam yaushe rabonta da tata uwar? Shekaru biyu kenan,gwara ma mahaifinta,tana da masaniya akansa,ta tsaneshi shima ya tsaneta,wannan dalilin ne yasa babu wanda ya taba yunkurin neman wani a cikinsu. Amma mahaifiyarta fa?      

Dalal tace "Ai gwara a dungayi ana tuna asali,nikam saidai nace Allah Ya jik'an nawa iyayen. Ita kuwa Gwaggona da ita muke ci da sha. Ina yawan zuwa gidanta a Kano,kuma kun sani."

   Ga mamaki sai sukaga Manal na hawaye tace

   "Gwara ku, kuna da iyayen. Nikam idan baku manta ba tsintata akayi a bola,sai ya zamana wanda ya daukeni ya rikeni har girmana,shine mutumin farko daya soma aikata masha'a dani."

    Tayi shiru tana sharar kwallah,kowannensu jiki yayi sanyi na tuno abubuwan daya shud'e a rayuwarsu. Baby daga kwance itama hankalinta taji ya tashi,babu wacce ta tsaya a ranta kamar mahaifiyarta. Taji gaba daya tanason taje duba lafiyarta. Manal ta share hawaye ta mike

     "Yan iska zaku tunomin bakin labarin rayuwata,ku tashi muje shan ice cream. Yau jakata a cike take."

  Sukayi murmushi don babu wacce keda kuzarin dariya,Manal ta dubi Baby.

     "Zakije ne?"

   Baby ta girgiza kai

   "Banajin fita ne."

   Sun lura jikinta yayi sanyi, tausayinta ya mamayesu musamman ma Manal wacce anan duniya ita kadai tasan wacece Baby Tasneem. Ita kadai tasan tarihin rayuwarta. Don kafin ta hadu da kowacce cikinsu,Baby tasleem ta soma haduwa da ita harma ta sauketa a gidanta. Haka suka fice suka barta a gidan. A ranar Baby taci kuka sosai,ba don komai ba sai don rashin sanin halin da mahaifiyarta ke ciki. Karshe ta mike ta shiga daki ta kwanta ba don tanajin bacci ba. Sai don kawai tunanin rayuwarta.

                    *****
     KWANA HUDU BAYAN HAKA
  Tafiya takeyi da baya da baya tana kallonta,yayinda ita kuwa ke kwance duk fuskarta ya baci da kuraje,hannu take miko mata alamun tsayar da ita tana ihun kuka

      "Ya d'iyata,kada ki gujeni! Karki barni cikin wannan halin! Ki dawo gareni!"

  Maimakon ta dawo,sai ta juya a guje zata tafi, karar da taji uwar tayi ya sanyata itama kwala ihu kafin tayi wuf ta fada wata rijiya a wajen."

    A tsananin firgici Baby ta tashi sakamakon wannan mafarki mai rud'arwa,gumi ya wanke fuskarta duk da Ac dake a kunne. Sai haki takeyi tamkar wacce tayi gudu. Ta sanya hannu ta dafe kirjinta dake dukan uku uku. Can kuma tayi wuf ta sauko daga gadon. Wani d'an karamin akwati ta dauko ta bud'e. Hoto ne a cikin (envelope),nan da nan ta zaro tana duba. Dattijuwa ce tare da yarinya mai shekaru uku,sai dan saurayi mai kimanin shekaru goma sha daya a hoton. Dukkansu suna dariya. 

    Ta rungume hoton a kirjinta yayinda hawayenta suka karu. Tausayin kanta ya dabaibayeta,taji nan duniya bata sha'awar komai daya wuce na zuwa kauye ganin Mahaifiyarta. Tun hirar da sukayi tare dasu Manal,hankalinta yake a tashe. Ta amince bazata taba samun nutsuwa ba har sai ta dangana ga duba lafiyar mahaifiyarta.

                    ******
   Karfe goma na safiyar Asabar,ya shirya tsaf cikin kananun kaya ya feshe jikinsa da turaruka. Bai dauki komai ba sai karamin trolley dinsa inda ya shirya kayan sawarsa. Saida ya soma zuwa gidansu yayi sallama da Daddy,kafin yaje gidan Abba. Nan ma yayi musu sallama,mahaifiyarsa ta bashi sako a kaiwa uwarta,wato kakarsa. Daga haka ya kama hanya.

                    ******
   Zaune suke suna karyawa,basu ankara ba suka ganta ta fito tana jan akwati. Ba jan akwatin ne yafi basu mamaki ba,tunda sun saba tafiye tafiyensu. Shigar dake jikinta ne ya burgesu kuma ya basu mamaki. Doguwar rigar atamfa ce, anyi mata dogon hannu three quarter,maimakon ta dora dankwalin saita yafa karamin mayafin (pashmina) a kanta. Saida tazo kusa dasu sannan ta dubesu fuskarta babu wata kwalliya ta daukar ido sai hoda da jan baki mai kalar ruwan hoda(pink). 

      "Zanyi 'yar tafiya ne,amma in sha Allah bazata wuce kwana uku ba. Amanar gidana yana hannunki sister."

   Ta dubi Manal. Murmushi manal tayi kafin tace

    "Karki samu damuwa baby,shigarki tayi mana kyau,tamkar bake ba."

   Tayi murmushi batace komai ba ta nufi waje. Babu wata wata,ta fada motarta ta shiga. Duk da dai bata taba karambanin tuk'i mai nisa ba,yau kam tanason yi. Dole taje ga mahaifiyarta ta duba lafiyarta. Tsananin kewarta yana neman hanata sukuni,ga fargabar abunda zata  tarar sskamakon mafarkin da tayi a daren jiya......!




Download Ýar Bariki Littafi Na Biyu Complete