[1:50pm, 05/05/2016] 📓
📓01 *'YAR JAMI'A*📓📓
_By_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
_In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESAH ABUBAKAR RIMI*
*(ANEELURV)*
&
*UMMIEE ADNAN*
Gabatarwa:
Assalamu alaikum 'yan uwa da masoyana baki daya naga irin sakonnin ku naso da na ci gaba da rubutu akan littafina na 'yar jami'a hakan bai yiyu ba sakamakon rashin samun cikakken labarin daga wanda abun ya shafa!yanxu haka an samu gashi kuma xamu ci gaba!kamar kullum LITTAFINA YAR JAMI'A banyi don xagi ko batanci ga wata/wani ba sai don ya xama darasi garemu!allah ya bamu ikon anfana dashi ameen!!
Wattsapp:comment only 08103439416
Visit me @ herwwerhjidderh92.wordpress.com.
Hi Daddy shigowar tane yasa daddy da umma tsayawa daga hirar da suke da mai da kallon su gareta dariyar da daddy ya sakarmata yasa ta kara langwasar da jikinta ta hanyar fadawa jikin umma tana wani shashsheka kamar mai shirin kuka daddy xan wuce scul na ji ance jiya anyi lecture toh ai kinga irinta dama ai nasan xa'a rina kamar na sani nace jiya karkije airport tarar mahaifinki amma kika ki ji ki sani fa wannan makarantar ba kamar ta baya bace dole sai kin kula cewar umma tana kallonta fuska ba yabo ba fallasa tuni hajara ta mike daga jikinta tana bubbuga kafa a kasa tana daddy ka ganta ko ai bashiri daddy yaja hannunta fuuuu suka haye sama yana mai bata baki shigarsu dakinsa ke da wuya daddy yace beauty rufe idonki ki karbi tsarabarki amma fa bayawa kin san ba shiri kika sa na dawo dan naga murnar xagayowar haihuwarki gobe cikin sauri ta rufe tare da cewa toh na rufe daddy dakko min hannu yasaka cikin aljihun riga yaxaro karamar takarda ya bude hannunta ya saka mata yace gashi babu yawa kya iya bude idonki yanxu;ai kamar jira take ta bude me xata gani takarda(check)da rubutun kudi har naira dubu dari biyar,tace daddy wannan fa bade shine na kayan da xan siya na birthday na ba tana fadi tare da bata rai yace haba beauty kamar ni na baki haka a birthday"kawai na shiga scul ne dan ki farin cikin daddynki ya dawo" woooo" ihun da tasa ke nan tana mai rungumesa da fadin sai daddy na wallahi ko garin ba kowa amma fa ki kula maza kisaka a jakarki kafin......bude kofar da akai ne yasa ta yi saurin saka takardar a jaka da fadin bye daddy kam tayi bakin kofa ita bata wuce ba kuma batai magana ba har sai da daddy yace bata hanya fa kar 'yata tai latti matsawar umma yabata damar fita cikin sigar sauri batayarda tayi magana ba sai da takai bakin kofa da sauti mai karfi tana umma xan siya miki ice-cream rufe kofar tai da xura wa mijin nata ido sanin da abinda ya kawota yasa yayi azamar juyawa da bude kofar bandaki murmushi kawai ta saki tace kashiga kafito ina jiranka don akwai maganar da xamuyi!
Abangaren beauty kuwa kamar jira take ta karasa wajen aje mota tana dariya ta bude jaka ta xaro key ta bude motar tare da rufe ta tadau kusan minti biyar tana kallon kanta a madubin motar kafin tunaninta ya koma kan takardar daddy!yanxu toh yau me xanyi wanda yafi na kullum yanda xai sa na wuce duk wata kaza a scul din nan don allah yau sai an bini ko ba'a so hhhhhhhhh!jin dariya kawai kake na tashi kamar tana hira da wata karar wayarta ya katseta daga kogin tunanin data fada ganin wacceta kirata yasata saurin dauka da karawa a kunne tana fadin duk inda kike yanzu ki fito ki tsaya a bakin gate na scul dan yau akwai harka...
📓📓 02 *'YAR JAMI'A*📓📓
_By_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
Harka kuma?ka ga shegiyar gari waya gina ki haka ?gaskiya beauty ba kyau wajen samu kalaman matashiyar yarinya xee-xee kenan wacce ta amsa sunanta! Shike nan dama ina hanya na tsaya gidan mai ne amma yanxu xaki ganni,ok toh sai mun hade haka ta fada tare da kashe wayar tana maida numfashi! Cikin nutsuwa takunna motar tare da kara sautin wakar (u are my african queen) wanda ya bata damar juya kan motar tai hanyar gate gaisuwa baba me gadi ke kai wa da washe baki yana kokarin bude kofar!jaka ta bude ta zaro dubu hudu ta mika masa tai waje ai godiya da kirari wajen baba me gadi ba kama hannun yaro!!
Kofar shiga jami'a cike take da motoci,mashina,kekuna da kuma dalibai matafiya kasa kowa cikin layi don karbar takardar shedar shiga jami'ar(gate pass)hange take tayi ko ta gano inda aminiyarta ta tsaya amma yawan motoci sun hana dole ta kira ta a waya tasanar da ita inda ta tsaya!can gefen titi kadan da gate ta tsayar da motar!gano lambar motar yasa beauty tai saurin karasawa tare da tsayar da motarta,tsayuwarta ya ba xee-xee damar bude motarta da nufowa wajen beauty;ai kamar jira take ta shigo beauty ta saki wata dariya jikake tana fadin ai mun afuwa na jima ko? sarkin fushi kallon data sakar mata yasa tai ajiyar zuciya tare da fadin mene labari!
Sannin kanki ne xee-xee daga haduwarmu wancan satin xuwa yau mun shaku da yawa kuma tamu tazo daya dan haka ina so na ke ta raini a scul yau fiye da yadda na yi satin daya wuce don so nake na zama 'yar jami'a lamba daya da kowa zai so ni a makarantar nan duk da ana cewa sai ka gama tashenka wani bai san da zamanka ba!amma ni beauty kisani da ban nake kuma dole abi ni don salona daban yake tawan!!hhhhhh dariya xee-xee ta saki tare da kallonta tana fadin kina wuta beauty! Naga wani country mall wajen ya hadu amma fa ban taba lekawa ba kawai xamu shiga ki siya ki canja acan tunda akwai wajen sa kaya sai kuma nima asai min nawa ko kuwa??xee-xee tai furucin tana mai watsa hannayenta!hmmn kema kin san wannan ba matala bace ke dai shiga motarki ki biyo ni kawai!!
📓📓03 *'YAR JAMI'A*📓📓
*BY HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
Haj.Halima ce zaune bakin gado"wato umma tana jiran fitowar daddy daga wanka" tunani fal cikinta ta sak'a wan-can ta kunce wan-can" jin da tayi an watsa mata ruwa a fuska ana dariya yasa ta dagowa tana kallonsa"!har ka fito dear ta fada tana kauda kanta" !juyawa kawai yayi yana fadar ai tunda ba taimako ba dole nai saurin fitowa ba" don nasan ko fita ban gama yiba na fito !jin tayi shiru yasa shi juyowa tare da fadin ki tallafa min wajen shafa lotion mana uwar'gidan!mikewa kawai tayi ta dawo kusa dashi batare data bari sun hada ido ba"tahau shafa masa sai da tagama tsaf tana shirin tashi yace yau kuma fuskar laifi me tai miki kika barta?cikin halin ko in kula ta debo lotion din ta kai hannunta fuskar ke nan ya ruku hannun tare da fadin haba farin ciki na ki shafamin mai tare da kallon kwayar idona shine abinda nafi so sama da komai a yanzu dan nasan baki da musu.
Sannin halin matar tasa yasa ya dago fuskarta suna duban juna yace kiyi sauri mana ina so naji damuwarki fa kallon daya bita dashi ne yasa ta murmushi tana fadin dear kasan lagona da yawa duk damuwata ka iya da ita maza tashi kasa kaya muyi maganar!!murmushi ya saki ai kin san mata da miji sai allah tawan!
*******
Katon katafaren kantin nan na country mall beauty ta tsaya tare da fitowa cikin zumudi don taga lokaci na tafiya!besty yi sauri fito mu shiga ba lokaci fa cikin karamin lokaci suka shiga dauki wan-can aje wan-can" har sai da mai kula da wajen kayan mata ta karaso (area sider) lura da yadda suke bincike kayan tana tambayar baku sami abinda kuka zo nema bane?" naga tun daxu sai bin cike kuke? cikin sauri xee-xee ke labarta mata me suke so!murmushi kawai tayi tare da jan hannun beauty xuwa wani daki"daki ne madai-daici amma fal yake da kaya na alfarma"dubanta beauty tai cike da mamaki tace wow fantastic"nan matar ta dafota tana fadin wannan kayan da kika gani anan d'akin sai manyan mata ke sayansu ga k'yau ga kudi in zaki iya nasa ashirya ki a tailoring room dinmu" ya kika gani?baki kawai beauty ta bude tana kallon matar ai auntyn 'yan gayu kudi ba matsala ta bane ke dai ashirya ni kawai!auntyn 'yan gayu kuma kaji sabon suna cewar matar tana dariya"nan suka fito daga d'akin xee-xee de na tsaye tana kare ma wajen kallo auntyn 'yan gayu ce ta waigo tace kawar beauty ki zabi naki bari na kai ta ciki a gyara ta!toh kawai tabita dashi xee-xee tana kare ma wajen kallo lallai gaba da gabanta wai aljani ya taka wuta!
📓📓04 *"YAR JAMI'A*📓📓
_By_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRUNCESS'QUE~DEE*
Shalele na ya kika ga wannan shigar! dagani ba tambaya wannan shine namijin da baya tsufa!dariya suka saki a tare sannan ya dawo gefen gado kusa da ita ya zauna yana mai mata nuni da ta juyo inda yake!uwar gidana mata daya tal gare ni a duniya har lahira inshaallahu haleematu na gaya min damuwarki!Damuwata sanin kanka ne baza ta wuce taka da ta 'yarka ba wallahi dear ina shiga cikin wani matsanan cin hali idan naga yadda kake tafiyar da rayuwa hajara katuna yanxu ba da bace!ace yarinya tun tana karama sai abinda take so ake mata bata san fada ba!har tana ganin kamar kafi sonta akai na gaskiya dear da sake don haka kasan abinyi akanta!ya kamata muzauna muduba rayuwar yarinyar nan don nan gaba fa aure zatai haka zataje gidan mijin nata kuma har ta iya rike 'ya'yanta da wannan tarbiyyar hab.....ke!ke!ke dakata halima wannan ne daman damuwar naki ashe kuwa zaki jima cikinta ko dan bana miki magana kina gani ina kauda kai shiyasa yau kika biyo ni ta haka"?eeyee"?nayi zaton ma kina missing beauty ne din xata je scul ta barmu da kadai ci"ashe ke ba haka ba!toh idan ban nuna mata so ba wa zai nuna mata?ai wannan shine gata!"gata"?gata fa kace dear?wannan ba gata bane wallahi cutar kaine kuma ya kamata ace kasan da haka" inda nima haka aka kawo maka ni ai da nasan yanzu labari ya canja kafa tsaya ka duba maganar nan dear!"dubawar kenan kuma kisani rai na ya baci dan haka idan bazaki iya taimaka min akan tarbiyyarta ba ni zan iya ni kadai !kuma kar naji kar na gani bacin ranki akanta halimatu!
Mekewar da yayi ne yana neman fita rai a bace wai shi me 'ya yasata durkusawa gabansa tana mai sunkuyar da kai!dear dan Allah ka gafarta min kada fushinka yasa na samu fushin mahaliccina natuba kuma bazan sake ba amma na san da ranar nadama!hmmm tawan kenan tashi na ji ba komai kuma ya wuce amma ba ranar nadama!!cikin yanayin bacin rai ya fice tare da rufo kofar gammm kake ji !!tashi tai ta zauna tana kare ma dakin kallo!hmmn Allah gatan bawa ga dukiyar ga soyayyar ina samu amma tarbiyar 'yar ciki na an hana nabata wannan wace irin rayuwa ce da anyi magana ya hau fushi yana kururuwa kamar wani zaki wai shi me 'ya!"
hmm na biye ma tunani tabbas zan iya kamuwa da wata cutar bari kaga na tashi na leka kitchen naga me ladiyo ta ke yi!
(WANNAN KENAN)
📓📓
05 *"YAR JAMI'A*📓📓
_By_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
Bude kofar da akai ne yasa xee-xee saurin juyawa rike da wata hadaddiyar doguwar riga a hannunta da alama ita ta xaba xa ta saka baki bude tabi beauty da kallo!ya kika ganni?cewar beauty tana kara gyara xaman kayan jikinta!wani smiling xee-xee ta saki hade da fadin mace kamar hawainiya lokaci kankani haka kin canja gaskia dole akira ki da *beauty* kyau kamar ba gobe"bari kiga nima nai sauri na gyara sai mu wuce kin san fa wannan tsohon mutumin ne damu!"wanne farin ko bakin?!bakin dai mana nifa naga ko d'an sako wasa cikin karatunsa baya yi balle dariya!ke dai yi sauri shirya mu wuce tun da bai iya wannan ba ai zai iya kallo ko?cewar beauty tana wani karkada boobs nata"cikin sauri xee-xee ta shirya ta fito ta tarar da beauty na karbar receipt daga hannun auntyn 'yan gayu da alama ta biya kudin kayan ne!xamu iya wucewa kawai na gama!hmmn yarinya ga kyau ga diri kin fa fita da yawa cewar beauty tana danna waya!yawwa na shigar da nambar sai kin ji ni auntyna" dariya kawai ta sakar mata hade da sallama suka wuce!
Gudu take sosai da motar kamar mai shirin tashi sama har ta isa babban gate na shiga *Jami'ar* ta karbi takardar shiga(gate pass) ta wuce har takai *A.Bukar twin theatre*ji kake kiiiiiiiiii... ta ja birki! Ido kawai jama'ar wajen suka bita dashi atunanin su motar ta kwace ma ta ne!hankali kwance ta bude motar ta fito rige da karamar jaka a hannu!ta hau duba bayanta ko zataga motar xee-xee can ta hangota ta kusa karasowa ta ja wani karamin tsaki!cikin sauri xee-xee ta karaso ta fito tana nufota tana cewa lokaci ya wuce nasan ma yanxu ya shiga wallahi mu d'aga k'afa!ke dalla mene haka da kin san da haka kike tuki kamar 'yar koyo!wai yanxu karfe nawa ne?10.a.m fa xee-xee ta fada jiki a sanyaye ni naga ko a jikin ki beauty wai ke baki da tsoro ne?hmmm kin san lokacin da aka haifi tsoro ina bacci pls ki biyo ni kawai...
Bin ta kawai take amma hankalinta duk ya gama tashi!daliban dake wajen kuwa tuni kallo da hira ta koma kansu kowa na tofa albarka cin bakinsa!
Kofa ce a rufe da alama an rufo wajen ne!hannu ta saka ta bude tare da shiga sauri-sauri" gudu-gudu take taka matattakalar ta haye sama ta na duba wajen zama! Can ta hango wuri kusa da wani saurayi taje ta zauna tana fadin dan matsa na samar ma xee-xee waje!tuni ya matsa yana binta da kallo na mamaki!daga kan da zatayi ta hango xee-xee tsaye bakin kofa ta kasa shigowa! In ranta yayi dubu toh ya gama baci!cikin tsawa kake jin maganarta tana fadin kishi go malama kar a gama attendance bake....
*Get out of my class*"!!!(fitar min daga aji) Maganar prof.kAS kenan yana cire karamin gilashin dake manne idonsa!binsa tai da kallo kawai ba tare data motsaba!are you not hearing me?(bakya ji na ne?) I said leave...(nace ki fita...)sorry sir i didn't get u(malam ban fahimce kaba)!!tafada tana watsa hannayenta cike da raini"dogon tabur din dake gabansa ya kaiwa duka da hannu"kafin yace"toh dan ubanki zan miki da yaran da zaki gane fice min daga aji kuma kar na kara ganinki cikin class dina and u monitor ya nuna shi" let d attendance sheet go round"waigowa yyi ga xee-xee yace ke kuma da kike waje shigo!cikin nutsuwa ta shigo tana fadin thank u sir(nagode malam)!mikewa beauyy tayi tana wani yauki tace ga nambata bawan allah ko daattendance sheet yaxo kaina kai min"ke kuma zo ki zauna ga waje baiwar allah"tana fadin haka ta dau jakarta fuuu tai waje kallo gaba daya yana kanta!adaddafe ya karasa lecture din amma ransa in yayi dubu ya baci har ya saka kafarsa waje kome ya tuna yace captain biyoni da takardar data baka bakin mota ya juya yayi waje !mikewa al'ameen yayi ya bi bayansa
Tun da ta fita beauty take ta faman zagaye a bakin twin theatre din ta kasa zama jira kawai take taga lecturer din ya fito!kamar daga sama taji takun tafiya!me zata gani PROF.KAS da wannan bawan allahn har sun dan wuce inda take tsaye!ta d'an yi gyaran murya hade da d'an taku kadan ta cin musu"hannu ta nuna wa captain tace dan Allah je ka dawo ka fada min full name din malamin nan bawan Allah?"ai ba al'ameen ba har Prof.KAS sai da ya juyo!tsananin mamaki yasa yayi wani irin murmushi mai cike da mugunta ya juya hade da sa kai gaba ya wuce!ganin bai tanka ba yasa tai murmushi itama ta koma ta samu kujera a gefen wajen ta zauna!
Abakin motar ahi ya tsaya sannan ya juyo"kana jina ko captain wani satin sai 10.a.m zanzo ina ta uxuri sai ka sanar"ita kuma waccan ka fada mata sunan naga uban me xatai dashi! Susa kyeya captain yayi kafin yace"sorry sir ai ban san full name dinka ba!har ya bude mota ya shiga kamar bazai magana ba can kuma yace khaleed Ahmad sulaiman!Da haka ya kunna motar yayi gaba abinsa!"
📓📓06 *'YAR JAMI'A*📓📓
_By_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
D'aga kansa da xaiyi ne captain yaga duk anfito dalibai sun cika gaban theater din har baya iya hangota can yaji ana kiran malam kaganni nan! Hakan ya karasa da sallamarsa!ta amsa tana cewa zauna ga waje!tsayuwarsa ya gyara tare da fadin a'a nan ma ya isa!yauki tai da bakinta beauty tace"Yi hakuri ka zauna maganar da yawa!xama yayi yace"ok ina jinki!ko zan san sunanka naga kamar baka so ina kiranka damalam"!kallonta yayi aa nutse sannan yace sunana al'ameen!ok meenu kenan na gane",gaskiya meenu abinda ya faru yau banji dadi ba wannan tsohon yayi disgracing nawa a public kamar be san kiman mace ba"ai a xato na ai a xatona mace abin da xaai caring akaine ba ai harassing nata ba"cike da takaicin irin kalaman dake fita daga bakinta al'ameen ke kallonta"ganin yadda yake binta da kallo yasa ta dan shafi fuskansa da yatsunta"tace what meenu?ni bana son yawan kallo just gaya min sunansa da inda yake zama don naje musami understanding don next baxan d'oki hakan ba!buks nashi ya kara gyara xamansu kan cinyensa sannan yace gaskiya baiwar Allah bazan boye miki ba kin yi bade deba saboda wannan lecturern babbane a scul din nan kuma ko ba dan girmansa ba ai ubane be dace kina haka ba just kefa kina scul ne just to acquire knowledge and go"amma in kika biye wa lec....heyy...shout up...ni xakai wa nasiha?din kawai na baka damar xama dani?karka rslena min hankali malan"cike da fada take maganan"kabani sunanshi ka wuce period"ajiyan rai meenu yayi yace sunansa sir khaleed ahmad sulaiman!wani fari beauty tai da ido"what kHALEED AHMAD SULAIMAN?? Nice name"sai kuma ta toshe baki tana d'an fakar kallon meenu"au kayi hakuri fa ba santin malaminku nai ba"sunanshi kam yayi hakan yanzu kaga lecture ta yau ta wuce ni dan haka ina so ka zama mai taimako na wajen karatu in ba damuwa!karki damu yanzu ni zan wuce gobe in kin zo sai ki kwafi na yau don sauri nake xan shiga library research"!dariya abin ma yaba beauty yanxu ace duk lexturn har da shiga library"toh wane lokaci shakatawa xata samu kuma?tuninta ta katse ta dubeshi tace ai tun da aka fara lecture bana yi kai dai kawai bani nambarka mayi magana tunda sauri kake!ok gashi!nagode zankira sai kai saving!har ya juya zai tafi tace baka ji ba sunana Hajara Aliyu Mai-dollar!gyada kai yayi sunan yayi sai anjima,meenu ya fada yana tafiya!
Duk hirar da suke xee-xee na tsaye gyfensu tana jinsu!beauty ta juya ta kalle ta!hmm shegiya ga sangayu ka tsoro toh zauna kiji!xee-xee ta zauna jiki ba kwari menene kuma? ni fa yau na tsorata wallahi duk iskancina ina ragawa tsoho!!dalla yi min shiru sarkin tsoro ai nafiki girmama tsoho bazaki gane bane yanxu dai bari kiga!hannu beauty ta saka cikin jaka ta xaro wani karamin dairy(littafi)ta bude tace kalli nan zanyi tick(maki)anan!tanayi tace bari na fada miki mena rubuta a wajen "PLAN ONE" TASK COMPLETED"!!
Fuska yamutse xee-xee ta dubeta tace Ni fa ban gane me kike nufi ba beauty!hmmn karki damu zaki gane amma baki mamaki ba dazu dana kiraki baiwar Allah?? Toh saboda kar laifina ya shafeki"Ko da yake tashi muje nemansa!
wa din???xee-xee tai maganan tana zaro kayen ido!wannan farin tsohon na mana!!beauty ta fada tana wasa da mukullin motarta!
MUJE ZUWA!!!!
📓
📓07 *'YAR JAMI'A*📓📓
_By_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
Mota suka shige basu zame ko ina ba sai gaban wani gini inda aka rubuta faculty of economics da alama anan office dinsa yake tuna nin daya fad'o ran xee-xee kenan sakamakon dakatar da mota da beauty tai a wajen!fitowa tai daga motar ta karaso wajen xee-xee"ki jirani anan yanxu xan fito" ta fada tana mai juya baya zuwa kofar shiga wajen bude kofarta ke da wuya ta ci karo da mutum gabanta cikin razana ta ja baya amma ina tuni jakarta ta daki hannunsa har wayarsa ta fadi kasa ji kake rasssss!!! Ba shiri tai saurin durkusawa tana kokarin daukar wayar hankali a rude!muryarsa ta tsinkaya ciki-ciki irin na kasaita yake fadin badai ni zaki dakko ma wannan empty cell din ba?c'mon zaro min sim din ciki malama!jiki na rawa ta dauki wayar ta zare sim din! ga shi ta fada tana mai daga ido domin ta mika masa! Wani irin hallita mara misaltuwa ta gani gabanta ita hasken shima tsoro ya bata"kallon da take me ne"yasa ya katseta"hey my sim"a dakule ta saki ajiyar zuciya!susa kai ta d'anyi tana mutstsuka face ta mika masa"kayi hakuri ban.......karki kuskura ki apologising nawa kede kawai ki zama mai kamun kai!kalmar daya fada kenan ya bude kofar yayi waje!
tayi kusan minti biyar tsaye tana jin voice dinsa a ranta ita bama maganan ke damunta ba"but his lion voice" sai ta ji magana daga bayanta ana cewa what are u doing there?juyawa tai tana sorry sir i came to see malam umar but unfortunately i forget his office number!here i'm ya fada yana mai kokarin matsowa kusa da ita!'yammata taho muje office ai tsayuwa da irinku a waje hadari ne!binsa tai abaya tana ok sir!karamin office ne ba laifi sai takaddu daya cika kan tebur din nasa ga warin sigari sai tashi yake yi"!'yammata zauna ya fada yana bin ta da kallo me zan kawo miki ki sha? No! ka zauna kawai ba damuwa!kujerar dake kallonta ya zauna!toh ina jinki ki fadi damuwarki!
Murmushi ta saki kafin tace ba komai bane maganar da mukai a waya ne yanzu nazo akanta"!au dama ke ce mukai waya dake lallai Allah yayi halitta!ai dole kudinki ya karu yanzu duk aiki daya 50k!kin amince??hmmn amma ai ba haka mukai da kai ba?ada kenan wane malami zai ganki bai k'yasa ba ni ma dai...katseshi beauty tai saurin yi da hannu"kaga mubar wannan maganar yanxu dakko min task file d'ina sauri nake!tashi yayi ya dakko wani file yace gashi duk wani malami na department dinku akwai sunansa,lambar wayarsa kai har da ta mota akwai ciki"nagama nawa aikin saura naki!murmushi beauty ta saki alamun ta ji dadin aikin!to shike nan ga wannan 50k ne baya cikin kudinka kawai somin tab'i ne!ta ja kujerar baya ta mike tana fadin yawan aikinka yawan kudinka"so sai ka ji ni a waya!me yake yi malam umar in banda dariya ai karki damu beauty don kuwa aiki ai kin zo gidanshi" !kul karna kara jin wannan sunan a bakinka sunana *YAR JAMI'A* daga yau ko ka manta ga jami'ar nan a hannu na daga haka tabude kofar tai waje murna fal cikinta!!
📓📓
08 'YAR JAMI'A
_By_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
Da fara'arta beauty ta fito daga faculty din wajen xee-xee ta dosa bude motar tai ta shige"cike da son jin labari xee-xee ke tambayar irin wannan fara'a haka tawan kodai prof. Ya hakura ne?yamutsa fuska tai beauty lokaci d'aya tace pls kar fa ki b'ata min rai daga laifi d'axu se bada hakuri yanxu?dama nai haka ne kawai dan ki rako ni nan"ai shi ya kamata ya bani hakurin don shi yayi laifin ba ni ba" ya baki hakuri fa kika ce beauty?eh mana ko kina ganin hakan baxai yiyu ba?lallai baki san wace hajara ba ma"amma ina ganin wannan abin na hannuna shixe kara wayar miki da kai"kan sitiyarin motar xee-xee ta dafe ta mai da dubanta ga titi tace"agaskiya beauty kin yi min nisa kuma ina ganin tafiyarmu tare a jami'ar nan baxai yiyu ba"duk iskanci na baya wuce na cikin unguwa ko tare da wasu bebs da tsagerancinsu be kai naki ba"amma ke naga kamar kin aje karatu a side"kamar xe fi kyau ki kara duba class ko Allah xe sa ki samu dede ke"ajiyar rai beauty ta saki jin xee-xee ta kai karshen maganarta"hannu takai ta juyo da face dinta suna facing juna tace"xee-xee ashe kallon 'yar iska ma kike min wacce bata damu da karatu ba?kina tsammani ba karatu naxo yi ba?karki yaudari kanki toh wallahi karatu ya kawo ni amma ta hanya me sauki xan bi don na samu"sanadin ni da wahala bamu had'a hanya ba"se kuma wasu 'yan kananan dalilai nawa"so karki damu baxaki tab'a dana sanin kasancewa tare dani ba".
Yanxu haka kinga yinwa nake ji bari naje motana sai muje capteria xqki ji wani abu daga file din nan ko hankalinki ya kwanta"bata jira cewanta ba bude marfin motan tai waje xuwa nata".
*******
Waje ne ya cika da jama'a inda aka fi sani da *stop & chop*duk wani ko wata mai ji da kanta kai hatta wasu daga cikin lecturers sukan zo nan don cin abinci bude kofar tai suka shiga!kujera biyu ta gano a can front side da alama da mutum a zaune ya tashi don ga jakar laptop nan a saman table din!har wani sauri take ta cimma wajen ta isa wajen ta zauna!xee-xee ma taja d'ayar ta zauna!waiter!waiter!beauty ke kira tana d'aga masa hannu!ina xuwa ya fad'a yana tahowa!me kike so akawo?matso kusa kaji!matsowa yayi tsammaninsa fad'a masa zata yi!nan tace kaga so nake daga yanxu har ku rufe wajen nan yau duk wanda yazo cin abinci ka zuba masa kace ya bar kudinsa *'YAR JAMI'A* ta biya kuma ka tabbatar ka nunoni yayin da kake fad'a har nabar wajen!ga wannan naka ne!5k ta saka a cikin tissue wacce take ajiye a wajen ta mika masa!nawa ne??naka ne ta fad'a tana masa alamar ya wuce!!amma ka miko mana maltina musha!toh ya fada yana shigewa ciki!
Kusan minti uku da faruwar haka sai ga wani saurayi wanda bai wuce shekara 30 ba ya shigo ciki sanye da wani coffee brown suit!cikin sauri daliban dake wajen suka fara morning sir!wasu uku daga ciki suka biyo bayansa!tafiya suke basu tsaya a ko ina ba sai a gaban su beautyl!d'aya daga cikin daliban ne yace"excuse me gals ku d'an ba da seat wa sir zai zauna!har xee-xee na kokarin tashi beauty ta riko hannunta"ta murgude baki gefe tace ka fad'a masa *'YAR JAMI'A* ta zauna a wajen kuma ita bata tashi sai ta gama abinda take but in xai iya jira"better for him"kawai sai ta ci gaba da shan maltinan ta hankali kwance!a fusace wani student ya taso jin maganan beauty d'aga hannu yayi da zummar zai mareta cikin sauri Prince ya rike hannunsa!karka soma batta kawai fuskan nan cike da murmushi!karka damu kan ka amma ka fad'a mata ta zama mai kamun kai!cikin sauri ta dago kai don ta ga wanda ya fad'i hakan akaro na biyu kenan"amma ina tuni ya xari jakanshi ya juya ya fita! binsu tai da kallo su kuwa daliban suka juya suna ta cece kuce!xee-xee kawai binta tayi da kallo tana fadin kin burgeni wallahi na zaci zaki ce muta shi nai wani d'anyan aiki yanzu!ai da mikewa nai xan d'au jakar na buga masa a kai don atunani na ya samu mental problem"kinsan tunda kikace na saki jiki dake karatu xe xo min da sauki toh nasan xaki yi hakan"gauran numfashi beauty ta saki hmmn kema ai kinsan haka bazai taba faruwa ba!ace wai ni hajara ina xaune wani ya tashe ni a seat"haba never"!
*****
Dalibai kuwa duk wanda yashigo siyan abinci sai a xuba mishi a kuma ce yaje kawai *YAR JAMI'A* ta biya kuma a nunota abinka da dalibai ai kafin kace me waje ya cika makil! ganin haka yasa beauty kallon xee-xee toh yanxu zan iya baki kadan daga cikin labari na amma fa karki dauka komai"s dan ki xauna tare da ni" tunda hayaniya ta cika wajen ba mai jinmu!!
📓📓09 *'YAR JAMI'A*📓📓
_By_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
Ni dai sunana *HAJARA ALIYU KABIR MAI-DOLLAR* kamar yadda na fada miki ranar da muka fara haduwa!na kasance Yarinya d'aya tal ga mahaifina alh.Aliyu mai-dollar wanda ina ganin ba sai na gaya miki wanene mahaifina a jahar nan ba tunda shahararran attajirin d'an kasuwane kuma na hannun dama a gwamnatin kasa!Asalin mahaifina dai d'an garin yola ne wanda shine na 4 a wajen iyayensa!alh. kabir mai-dollar da hajiya ramatu madaki sune mahaifansa (Wato kakanni na) allah ya azurtasu da 'ya'ya hudu 3mata 1 namiji!aunty fatima itace babba!sai aunty khadija da kuma aunty Aisha!mahaifina shine auta acikin su ya samu cikakkiyar kulawa da gata daga iyayensa duk da wannan mahaifinsu baiyi sake wajen basu ilimin addini ba don dukkansu sunyi karatunsu a england in banda daddy wanda yake a china kasancewar kakus bai fiya zaman kasarba!Da zarar sun gama jami'a suke dawowa gida dan aure haka rayuwar gidan kakus ta ci gaba cikin farin ciki da jin dadi!har izuwa lokacin da ya kamata aunty aisha ta dawo gida don ta gama karatunta na jami'a anan ne tai burus da maganar kakus har take ikirarin can yafi mata nan hankalin kowa ya tashi a gidan nan musamman hajiya wacce sanadin hawan jininta kenan!alokacin daddy bai san abinda ke faruwa ba har sai da tayi shekara 2 acan wanda yayi dai-dai da kammala karatunsa!lokacin da ya dawo ne ya sami wannan mummunan labarin hakan yasaka shi kiran wani abokinsa da sukai makaranta tare dan kasar england da ya taimaka masa wajen sanin halinda take ciki sakamakon rantsuwar da daddy yayi bazai nemetaba tunda ya bata dukkan tarbiyyar da uba zai ba 'yarsa amma tai watsi da hakan!daddy ya shiga matsanancin hali da kiranda abokinsa yayi masa yana shaida masa aunty aisha tabi wata kungiya ta mawaka yanxu haka dasu ake damawa acan england!tunda Alh.kabir ya samu wannan labari yayi wa daddy gargadin idan har yakai 'ya'yansa mata waje toh bai yafe masa ba!
nan beauty ta d'an tsagaita da labarin nata ta dan surb'i maltinan gabanta ta ya mutsa fuska tace kinji fa abu irin na tsoho yaci duniyarsa dan bala'i baxe bari mu jikoki muci tamu ba".kina ji de ko xee-xee
A da daddy ya fara aiki a kamfanin kakus sai daga baya karfin kasuwancin yadawo kano inda daddy ke lura da kasuwancin kano!kakus kuma na can yola!da haka har kakus yabar masa kamfanin tunda bashi da wani d'a a gabansa"kin ga dai aunty fatima tayi aure har da d'anta itama aunty khadija tayi aure amma bata haihuba!kiga tun lokacin fa kenan gashi yanxu duk sun tara family nasu"! Karar wayan beauty ne ya katseta da hiran dole ta tsaya ta dauko wayan a jakanta"number ta gani kawai nan ta katse kiran ta dago kai tana kallon xee-xee da itama ita take duba tace wannan kenan amma
Kiyi hakuri xee-xee bazan iya baki labarin mahaifiyata yanxu ba da yadda mahaifina ya aure ta saboda baki da hurumi akai!kawai de nasan hankalinki yana ga file din da kika gani dazu na karbo a faculty!toh bari na shaida miki wani abu xee-xee tun lokacin da daddy yasama min admission a jami'ar nan nake jiran fara shigowarta don kuwa
Ranar lahadi da daddare wancan satin daddy yake shaida min zai yi tafiya ta sati biyu amma ya fada wa wani malami gobe zan fara shiga don an gama yi min registration amma zai bani wasu takaddu ya kuma bani file dina akan na kai department dinmu ya kuma she damin wannan mutum xe kara mun bayani sosai akan makarantar da haka kenan muka rabu yana min sai da safe!
📓10 *'YAR JAMI'A*📓📓
_By_ *HERWWERH JIDDERH*
*A K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
Safiyar litinin da misalin 9:a.m na shigo scul bayan daddy mun rakashi airport ni da ummah a inda ya bani lambar wayar malamin da xa xan nema!kira daya cikin ikon Allah ya dauka!nai masa bayanin kai na" cikin kankanin likaci ya gane!yaron office dinsa(massenger) ya turo ya tafi damu!
office ne babba muka shiga zaune yake dattijo d'an kimanin shekara 45 kansa kasa yana latsa laptop!shigowarmu ne yabashi ikon tsayawa da mai da dubansa garemu!'ya ta kin iso?haka yafada yana mai sakin murmushi a fuskarsa!eh na fada ina kallonsa!toh ga waje nan zauna!cikin nutsuwa na zauna!muka gaisa!sai naji yana cewa!mun gama magana da mahaifinki kuma nasan ya gaya miki!eh kawai nace!yawwa toh yanzu ga wannan takaddun ki hada cikin file dinki zan saka a nuna miki inda xaki kaisu!haka na karba na saka !yaron office dinsa ya kira ya kuma umarceshi da ya nuna min faculty dinmu da office din umar!daga nan nai masa sallama inda yake cewa in har kina da wata matsala karki nufi kowa kizo nan 'yata don bada kowa ake sabo a *jami'a* ba!amma kinsan kawai na ji shine xee-xee!
Baba habibu sunan masinjan nashi"gaskiya naji dadin hada ni dashi da yayi don ya nuna min komai wanda ya kamata na sani in banda malam umar da muka je baya nan !anan ne fa baba habibu yake ta maganganu ciki-ciki wai watakila yaje biyewa shashashan 'yan iskan yaran makaranta ne!wani abu ya faru baba?na fada ina mai da duba na gareshi!hmn ke dai 'yata ki kama mutuncin kanki kawai amma kinga *jami'a* mahadar gyara ko b'arna ce dole zaka zabi daya amma narasa dalilin da yasa yaran suke biye masa wajen ashararanci ga bala'in san kudi a cikinsa kamar dan kasuwa!dagaske baba?na fada ina zaro ido!kedai bari kawai ai shi jariri ma zai iya masa aiki indai zai biya shi cewar baba yana tab'e fuska!ni gaskiya baba har na tsorata dashi kawai ka bani lambarsa in na samu kawa a ajinmu sai ta rakani wajensa don kar naje kai file din ni kadai yazo min da wata maganar!da yake ranar babban mayafi na saka cikin ikon allah kuwa sai naga ya zaro waya!yana fadin kin san da yake duk yawancinsu ina da lambarsu kasancewar ni din na jima dasu anan!cikin sauri na dakko wayata na saka lambar !5k na zaro na mika masa amma kin san bawan Allahn nan sai yak'i karba sai da na nuna masa dan allah na bashi sannan mukai sallama dashi da haka na dawo gida!!
📓
11 *'YAR JAMI'A*📓📓
_By_ *HERWWERH JIDDERH*
A.K.A
*PRINCESS'QUE~DEE*
Nisawa beauty tai daga bada labarin ta dago kai tana kallon xee-xee tace
Bar batun haduwarmu da malam umar yanxu dai bari na bude file d'in nan na gano mana abinda ke ciki!kofin dake gabanta me dauke da maltina ta d'aga tasha sannan ta dauki file din!bismillahi xan bude sirrin jami'a ta fada tana kashe wa xee-xee ido d'aya!matso da kujerarta tayi ta hau nuna mata nan! kinga sunayensu ne da lambar wayarsu ke harda ta mota kin ga kuwa iyakar wayona iyakar nasarata!ko ba haka ba?Washe baki kawai xee-xee take tana fadin kice nima xa'a bani wadansu na lasa!hmmn yanxu ba lokaci bari naga wannan yaron sai mu wuce kin san fa gobe nake birthday na manta ban gaya miki ba don haka sai ki san da wane gayen zan ganki!don allah na ga bai min ba dauke kai zanyi kamar ban sanki ba!daga haka ta tashi tqna dariya ta shige ciki tana leken inda yake don tasan nawa zata biya!zaune ta ganshi gefen wasu mata suna had'a kayan girki!baka jiba" ta fada tana matsowa kusa dasu!cikin sauri ya mike yana fadin hajiya har kin gama ai da kin sa an kirawo ni"shigo mu karasa ga waje can ki zauna!no" ba sai na zauna ba fadi kudin kawai sauri nake!hajiya ai duka abincin wajenfa har ya kare!ai na san zai kare kudin na tambaye ka malam" ta fad'a cikin d'aga murya!gaba daya dubu sha uku da dari biyar ya kama!ok gashi amma gobe kukara hannu wajen girkin don zan baka na kwana biyu nan gaba dan bazan kara zuwa ba sai juma'a !hannu tasa cikin jaka ta zaro dubu talatin ta mika masa!ku nawa ne ma'aikatan wajen?mu biyar ne hajiya!ok ga wannan ka raba muku kuma ka kiyaye kada matar wajen taji don naji ance ba zama take ba!daga haka ta juya tayi waje!cikin mota ta tarar da xee-xee sautin waka ya cika motar!ta bude ta shiga tana kallonta!sai ina yanxu?beauty ke tambayarta"habeeb zan kai wa ziyara gidansa bayan la'asar sai na wuce!dariya kawai beauty tai ta fice daga motar!har ta juya kamar ance ta waiga cikin motar ta hangi hijab!wancan fa ta fada tana nuna mata!em!em !kin san baba sai a slow shiyasa nake yawo dashi da na shiga layi nake sawa kin san shi ba kamar mama ba"kinsan abin ne se kana basaja" koya kika gani?shegiyar gari ni na wuce ke dai ga son dadi ga tsoro kuma!dariya suka sa duka sukai sallama ta wuce!
Mota beauty ta shiga sai gida!horn take baba me gadi ya bude mata gate yana mika gaisuwa! Hannu kawai ta d'aga masa ta shige"cike da rera wak'a ta fad'a falon ganin ba kowa yasa ta hayewa sama!ta bude kofar falonta!me zata gani ladiyo ce ke tsaye tana goge tv!ke me kike min a falo?cikin sauri ta juyo tana kallonta!sannu da zuwa beauty dama umma ce tace....! Yi min shiru munafuka wallahi k'arya kike mata kawai halinki kika zo yi kuma wallahi yau zaki bar gidan nan bari daddy ya dawo!jiki a sanyaye ladiyo ta dauki tsimman nata tayi waje!cikin fushi ta shige d'aki!jakarta ta aje ta saka file d'in cikin drawer !yawwa bari nai wanka na kwanta na huta kuma"towel din dake sarkafe gefe ta janyo tayi bayi"lokaci kankani se gata ta fito"karamin riga ta xurq ma jikinta ta fad'a saman gado se bacci"!
📓📓12 *'YAR JAMI'A*📓📓
_By_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
Buga kofar da daddy yake ne yasa ta farkawa daga baccin da take"! sanin daddy ne kad'ai ke mata haka ya sata saurin bude ido"tace swit daddy gani nan zuwa! Karamar riga ce iya kar kwiwa ke jikinta ta bude kofar tana bude hannayenta!matsowa daddy yayi ya rungumeta jikinsa!daddynki yayi miki laifi beauty na!ya fad'a yana kama hannunta suka koma cikin dakin!laifin me kayi daddy na?Dama Na gayyaci 'ya'yan abokaina don su zo su tayamu murnar birthday dinki gobe mantawa nayi ban sanar miki ba d safe"!kara kwantar da kai tai jikinshi murya cikin shagwab'a tace ok"daddy ba damuwa hakan yayi ai ba laifi bane!
ehh toh dama bawai wannan ne kadai ba ibmn baki manta ba ina wannan aminin nawa alh.Mukhtar'wanda na tab'a baki labarinsa wanda yake abuja da zama!d'ago kai beauty tai tace eh daddy na ganoshi!
yawwa beauty dady ya fad'a cike da fara'a"shine d'azu ya kira ni yake shaida min d'ansa an turo shi service nan kano kuma ya kama gida"shine nafa be kamata ace ga gidana ace har yakai ga xaman gidan haya"duk da dai nasan bak'yasan ganin kowa gidan nan my beauty kiyi hakuri ya zauna damu just 4 a year kinji my bea.........saurin janye jikinta daga nashi tai ta hau buga kafa kasa tana fadin no!no!no daddy ni dai bana so kawai kaji daddy bana so kace ya je wani gidan ya zauna!beauty bazan iya ba aminina ne fa"nasan shi baxe nemi ya kawo shi ba amma tunda yace min yaronsa na kano ai ya kamata ni na gane me yake nufi"kuma ba anan zai zauna ba wancan bangaren zai zauna kinga bazaima takura miki ba kinji beauty!turo baki tayi ta wani had'e giran sama dana kasa tace'toh daddy zan yadda indai zaka kori ladiyo daga aiki!
ladiyo kuma? mai tai miki daddy ya fada yana mikewa tsaye!tana yi min sata a dakina!duk da daddy yasan ba halin ladiyon bane amma haka ya biye mata!basai na koreta ba amma yau zata gane kurenta na shigo miki daki!fita daddy yayi ya nufi kitchen ya tararda umma da ladiyo suna ta aikin kwashin tuwo ai ta inda ya ke shiga ba ta nan yake fita ba!sai da yayi mai isarsa sannan ya juya ya haye sama!kallo ummah kawai ta bishi dashi ita kuwa ladiyo tunda daddy ya fara kanta k'asa yake!
Kallo ummah ta kai gareta kafin tace ladiyo kiyi hakuri kinji!ummah ta fada tana mikewa zata bar kitchen din!
Kai sunkwi ta amsata da bakomai hajiya yarinta ce kuma zata daina!yarinta?wannan haukane ba yarinta ba!dan allah ke ma karki b'ata min rai cigaba da aikinki kawai!tana kaiwa nan ta nufi sashenta duk rai ba dad'i".
Ranar haka beauty ta wuni bata ko lek'o k'asa ba don bata son fadan umma!
📓
13 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE-DEE*
💕
Washe gari Tun bayan sallar asuba ladiyo ta hada kan sauran k'ananan ma'aikatan gidan don fara shirye-shiryen birthday na beauty kamar yadda daddy ya saka ayi,bayan data gama hada breakfast ne a dining table ta koma cikinsu dan cigaba da hidima!hayaniyar aiki kake ji ta ko ina a gidan sai gyara yake d'auka" a d'aya bangaren kuwa har daddy da ummah suka gama cin abinci beauty bata ko lek'o falo ba gudun fad'an ummah take!cikin tsanaki suka gama cin abincin nasu har ummah ta mike tsaye tana shirin shiga kitchen don kai flask na ruwan xafi! daddy ya kira sunanta! Ta amsa tana mai komawa ta xauna!fuska ba yabo ba fallasa yake kallonta"sai kuma yace"ina ganin lokaci yayi da zaki canja halinki don axama na dake sam ba haka kike ba"bansan yanxu waya d'oraki bisa wannan d'abi'arba?ace kawai dan nayi ma wata 'yar aiki fad'a shine kike fushi dani da 'yata ko?bama wannan ba ai ko ba komai yakamata beauty na'ta zama anan wajen!yanxu tana ina?nasan fad'anki ta gudar ma!ace 'yar cikinki baxaki iya sakar mata mara a duniyar nan ta huta ba"toh meye anfaninmu a gurinta banda ganin farin cikinta"baki ummah ta hau motsawa tana kokarin magana daddy ya katseta da hannu"kul ban son jin kome yanxu maxa aje kayan hannunki ki hau sama ki nuna mata farin cikinki da wannan ranar tata duk da nasan kin manta yau birthday d'in ta toh ni ban manta ba"dan na damu da kayana!toh kawai ummah ta amsa dashi ta mike ta nufi sama abinta!ta jima bakin kofar tana bugashi amma beauty bata bude ba!can take itakam beauty saman gado rik'e da waya tana ta faman chart da frnds suna tai mata murnar xagayowar haihuwarta"wasu kuma wanda tasan 'yan abi yarima asha kida ne se gayyatansu take xuwa shagalinta na ranar"!tunanin bugun baxe wuce na ladiyo ba shi yasa tak'i amsanta"!cikin k'aguwa tace"bacci kike ne hajara?ummah ta fada tana murda hannun kofar!tuni tai wurgi da wayan hannun ta gefe jiki na b'ari ta nufo kofa"a'a ganinan xuwa!cikin sauri ta taso ta bude kofar tana 'yan boye-boye jikinta"!ina kwana ummah!sakin fuska ummah tai ta amsheta da lafiya lau ya kika kwana?alhmdullah!ta fad'a tana d'an sakin murmushi!hannunta ummah ta kama ta had'e da nata tace ina miki murnar xagayowar haihuwarki ina fatan kuma xaki yi shagalinki cikin farin ciki!
Cike da d'an guntun fad'uwan gabanta ta k'ara sakin fuskan tace
tnx ummah!sakin hannun nata tayi ta d'an gyara tsayuwanta had'e da dubinta"naga daddynki ya gama tsara kome naki da fatan de bakya bukatar wani abu daga gareni ko?eh ummah babu kome se de pls ke ma ki gayyaci frnds naki"naga daddy ya gayyaci nashi"kallo ta watsa mata me cike da tuhuma kafin tai k'arfin hali ummah tace xan duba na gani"!daga haka ta juya baya tai waje ba tare da ta jira wani cewa na 'yarta ta ba!dafe kai beauty tayi ta muxgune fuska"cike da tunani fal cikinta ta shiga hakaito wacce irin uwa allah ya bata haka?"wacce ita a lissafinta babu socialization ko kad'an"ganin bata da amsar hakan ya sata sakin rai ta shiga sabgar gabanta
Haka wunin ranar ya kasance beauty bata saka daddynta a ido ba har gashi ana maganar la'asar ganin haka ne yasa ta shiga neman number auntyn 'yan gayu kamar yadda suka tsara"bugu biyu ta d'auka"itama de wishes d'in tayi mata kafin beauty ta bata full address nata ta kashe wayan".
Sallah ta fara gabatarwa sannan ta shiga ta watsa ruwa"tun tana cikin toilet take wilk'iyo maganganu a d'akin nata cikin xumud'i kuwa ta sheka ruwa jikinta ta fito"auntyn 'yan gayu ce xaune cikin wasu kaya riga da skirt sun hadu sai wata bakuwar fuska gefenta"da fara'arta ta k'arasa wajensu suka k'ara gaisawa nan take shaidawa beauty cewa wannan itace me gyarata ga kuma kayan sawarta nan an tanada mata kud'i kawai xata bayar"tsalle beauty ta saki had'e da rungumota tana fadin ok! ba damuwa yanxu dai tashi a fara shirin nan k'adan xqki ji jama'a sun fara hallara"!.
📓📓14 *'YAR JAMIA*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
Gyal-gyali na wasu kyawawan ababan kwalliya kake iya ganowa ya cika ko ina na harabar gidan"ga kujeru da tebura an jera su da kaya na tand'e-tand'e da lashe-lashe"wasu kananan fitilu masu kala launin j'a da shud'i su ke ta walkiya a wajen"a hankali motoci na alfarma suke shigowa kowa ka gani cikin kaya na keta raini"daga maxan har matan sam babu na bari dan kowa yayi ma wannan ranar shiri na musamman"sanadin sanin waye Alh. ALIYU KABIR MAI DOLLAR" a gefe guda kuma makid'a ne ke ta sakin sauti a hankali irin me tsuma jiki din nan"sai masu rawa da suke ta nishad'antar da wajen"daddy da tawagar abokansa tuni sun hallara wajen"inda ummah na gefensa itama dai da nata xugar"shagali ake tayi ainun amma har kawo yanxu mai gayya me aiki bata k'araso ba".
Ummah ce ta d'an tab'o daddy da hannu tana nuna masa agogo da xummar lokaci na tafiya"kai ya gyad'a mata kawai ya nemi uxuri daga wajen abokan nashi ya nufi ciki"da saurinsa ya nufi sashenta nan su kai kicibis a bakin kofar'wow marvelous daddy ya fad'a yana shafo kumatun beauty'kauda kai tayi tace no daddy bana so u re late 2 wish....saurin toshe bakinta yayi da hannu yace so sorry beautynah kinsan fa yau ranar muce dole na shiga busy yanxu haka guri ya gama cika ke kawai ake jira"hannunta ya kama su auntyn 'yqngayu da wasu frnds din' na take mata baya"da haka suka karasa filin"
Koda isarsu tuni kid'i ya tsaya cak kowa ya mike ji kake raf'raf'raf"hannu na tafi ta ko ina dan nuna girmamawa ga celebrant"kujeran da aka tanada mata ne taje ta xauna"nan shagali ya fara inda akaji tak'aidaccen tarihin beauty da abubuwan da tafi so na rayuwa kai har da wanda bata so"duk wasu abubuwa na nishadi kam anyi su"nan aka bukaci gabatar da beauty da ta taso dan yanka cake dinta"daddy da ummah su suka rakata har gaban cake d'in cike da farin ciki ta yanka" nan ta gucuro ta manna ma daddy a baki saura ta saka ma ummah"!tuni ganin haka makid'i ya saki sauti daddy ya kamo hannun ummah da beauty su ka hau dancing abinsu"a kunyace ummah ke rawan duk ba dad'i take ji toh amma ya xatai da farin cikin mijin nata'kafin kace me jama'a sun fara yawaita a wajen" rawa ake tayi sosai'juyin da ummah xatai ne ta hango wani d'an abokin daddy rik'e da k'ugun beauty ga maxa duk sun xagayeta se rawa suke"cikin sauri ta doshe su" taji karaf an rik'o hannunta"cikin fushi ta d'ago kai dan magana taga daddy dauke da hannu bisa baki yana g'yada mata kai"matso da kunnensa yayi dede nata ya rad'a mata pls dear let her be"it's her day"dn't spoiled it 4 her"baki ga yadda ta girma bane by the way da haka xata iya samun guy".kallo ummah ta kara watsa masu taga still yaron na ri'ke da ita"cike da takaici tace ka gafa me suke yi kace wai i should leave her"why"why dear kake so mu bar yarinyarmu ta lalace a haka"xaro ido daddy yayi yana dubanta da maganan da tayi"kinji kuwa me kikace?ce mata fa ki kai yarinyar nan ko kin manta beauty ta xama cikakkiyar *'YAR JAMIA NE*Last year ai ba'ak haka ba so if this year nayi mata be kamata ki nuna damuwanki ba"any way mu bar maganan nan yanxu je ki wajen mutanenki ni ma bari na janyo nawa mu d'an rage jiki"dariya ya saki ya wuce yana d'an gyada kai alamun sauti na d'ibansa ya barta nan tsaye"
Itako beauty rawa take sosai abinta babu alamar damuwa tare da ita"xee-xee ta hango rike da wani guy se rawa suke nan ta tab'ota suka saki dariya ganin yadda beauty ta had'e ne wani guy ya matso kusa da ita ya rad'a mata chai gal u luk so take a way"kashe mata ido d'aya yayi nan ta saki murmushi ta mik'a masa phone nata ya shigar da number dinsa"!haka akai taro me cike da tarihi da k'ayatarwa aka watse"!kyaututtuka kam beauty an sha su"!lik'is tai ranar don gajiya don kuwa har 8:00p.m aka kai ana shagali"!ta rako xee-xee da yake itace karshen tafi parkin space ta ga alamar shigowar mota cikin gidan"tsaki ta saki tare da kwallawa me gadi kira jiki na b'ari ya nufo yace gani hajiyata"wa ka bude wa gate ba tare da ka fa'dan ba??emm.emm!!dama bakon daddy ne"bakon daddy kuma?beauty ta nanata tana jinjina kai"can maganansu da daddy na jiya ya fado mata"tsuka ta sake yi ta galla me harara tace ok jeka ashe mayen ne yaxo"ido bude xee-xee ke nanata kalman"nan ta katseta"ke manta dashi kawai shiga mota ki tafiyanki ni bacci nake ji xan shige gida"tana kai wa nan da magana beauty tai mata sallama tare da k'ara gode mata"
📓16 *'YAR JAMI'A*📓📓
_By_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
Yau da yake lecture ba na safe gareta ba sai ba tai wajen karatun nasu ba"da yake safiya ne se ya xamana ba wani jama'a sosai" tafe take a hankali cikin motanta har ta isa wani building dogo wanda kana gani kasan offices ne na malamai jeren mktocin data iske wajen taje itama ta jera nata cikinsu"xaune take kana gani kasan da abin da take jira sakamakon wai-waige da take yi"hango shawo kwanar wata had'ad'd'iyar mota kirar end of discussion tayi na hararo wajen parkin ma motocin'saurin sunkwi da kai beauty tayi ta manna shi ga sityari tana d'an kare fuskanta da wani guntun handkachef"cikin nutsuwa wani dattijo manne da gilashi saman fuskar cikin shiga na suit ga karamin jakanshi na laptop rike a hannu ya fito"key na hannunshi ya d'an latsa se ga motan yayi k'ara alamun rufewa"hankali kwance ya hau tafiya har ya cimma building d'in Nan security ya mik'e da saurinsa ya bude me k'ofa yana fad'in morning sir'!"
Jin babu alamar motsi a wajen ya bai wa beauty daman d'ago da kanta tare da sauke wani ajiyan xuciya" ba tare da b'ata lokaci ba ta shiga gyara jikinta ta k'ara feshe kanta da wani mayataccen turare me bala'in k'amshi"d'an karamin madubin dake gaban motan ta kai dubanta gareshi wani gwalalo ido tai cike da murmushi saman fuskanta tace wow wato Allah yayi halitta fa ajikin nan nawa"!dariya ta saki tana me bud'e k'ofan nata tayo waje"a bakin k'ofan shiga ta iske security wani wurgin kallo yaayi mata amma yadda beauty ke da wani irin haiba na ko kana son mata fad'a se kaji ka kasa!yasa shi yace" Baiwan Allah ina xuwa?eh xan shiga ciki ne dama!xaki shiga ciki wajen wa toh?bama haka ba kinsan dokace fa duk wani d'alibi baya xuwa da safe haka nan wajen se captains ko kuma da wani kwakwkwaran dalili"jin haka yasa beauty d'an rau da ido kalar tausayi ido ciki-ciki tace haba me sunan baba na me xe kawo ni wannan waje haka da sanyin safiya inba daliliba"ni nan daka ganni ma'abociyar guje ma mutane ce amma ya zanyi?tunda prof KAS yayi test bana aji ina can kwance gadon asibiti gashi ance baya sake wata shi yasa da naga shigowarsa yanxu nace bari naxo ko Allah xesa ya saurareni"!wa??? prof KAS wai kike magana toh malama in xama ki san inda dare ya miki tun wuri gara ki tafi don Allah ko ke 'yar gidan uban wace bare saurare ki ba"don munsan halin kayanmu"kinga dashi da wani sabon matashi nan guraren da be jima da xuwa ba ai na gaya miki basu da rangwami kome bisa doka suke binsa balle ke yanxu ki shiga office d'insa a haka wallhi inaga d'ankwalin kanki a hannu xaki fito da shi don takaici"
Tabbas kalaman security d'in sun ratsa beauty don taga ainihin wane prof KAS rannan ace mutum yaga mace kamar ita amma ya kauda kai ya koreta a aji ga wani ixxah da yake ji dashi"wai shi a dole na gari ko?xe sani ne"!xancen xuci take da murmushinta ta d'an k'ara rankwafi da kai tace toh bak'in jin maganar ka ba amma kasan ance se angwada akan san na kwarai da xaka lamince min minute 10 kacal na shiga da kaga sakamakon da zan fito dashi"!badan yaso hakan ba amma yana da yak'inin b'acin rai kawai beauty xata shanyo ta fito haka ya wangale mata k'ofa yana fad'in a fito lafiya amma karki ce ban gaya miki ba"!bata bi ta kansa ba in banda murmushin nan de data k'ara cilla masa ya cab'e da girgixa mata kai don mugunta"!har ta d'an ci taxarar tafiya sai ta waigo tace wanene office no nashi!"cikin sauri yace kina xuwa 2floor ki mik'e shine na k'arshe se ki fad'a da k'afa biyu ki fito da......hannu beauty ta d'aga mishi da haka ta nufi ciki gadan-gadan!.
Ab'angaren xee-xee kuwa koda ta iso jami'ar bata xame ko ina ba illah masallaci nan ta shiga kamar yadda ta saba ta hau fito da kaya daga jakanta"batai k'ok'arin sanya wa ba se data ga jama'an da suka shigo suma dan buk'atun su sun fita sannan ta shiga k'ok'arin sauyawa daga doguwar riga ta atamfa dake jikinta da dogon hijabin ta har k'asa xuwa wassu shegun k'ananan kaya riga da wando gara ma rigan iya kar kwiwace!gyale mara nauyi ta yale a kanta tare da k'ara 'yar powder da jan baki a bakinta"kafin kace me tsaf ta gama canja ma kanta halitta baka ce ita ka gani d'axu cikin kaya na mutunci ba"!me da wad'ancan jaka tayi nan ta kammala tsaf ta fito ta nufi lecture hall nasu kamar yadda ta kira aka sanar da ita a inda xasu yi ranar"jama'a ke ta shiga ciki hakan ya sa itama tai parkin car nata gefe ta xari wani k'aramin jotter na ta da biro se wayoyinta a hannu ta fito ta nufi ciki waje ta samu ta xauna kamar yadda ko wane d'alibi ke nema"bata wani jima da shiga ba se ga wani matashin malami ya shigo captain na biye dashi da kayan karatunsa"saman stage ya tsaya nan kaji ajin yayi wani irin tsit kamar ruwa ya cinye saboda shiru da akai"!kowa mamakin da yake toh ina prof KAS d'in bashi xe shigo mana ba?ko de an canja tym table ne?ko kuma yana da wani uxuri babba?amma kuma ai shi ba ma'abocin fashi bane"?"!
📓15 *'YAR JAMI'A*📓📓
_By_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
💕
Washe garin ranar beauty kwance take tana maida ramuwar gajiyar jiya ummah ta shigo ta sameta"tashinta ta shiga yi sanin tabbacin cewa batai ko sallar asuba ba"a hankali beauty ta shiga bud"e idonta"firgit tai ta mike xaune ganin ummah duk'e kanta"murxa idanu ta fara yi tana fad'in ummah ina kwana?ina kwana kuma kin yi sallah ne? Emm emmm ummah nima bansan lokaci yayi haka ba fa?oya toh maxa tashi ki shiga bayi abu har past 7;00a.m ace baki sallan asuba ba anya kuwa hajara kina son hutu cikin kabari kuwa"?fuska ya mutse beauty ta fara kallon ummah taji an fara maganan lahira wanda sam baya cikin abinda beauty ke so ana magana"hannu ta kai ta dod'e kunnenta ta mike ta nufi bayi"tsaye ummah tayi tana dubanta har ta rufe kofan sannan ta nisa tace oh ni kam Allah de ya shirya wallahi"ace yarinya kamar tashin gidan arna kwata-kwata lissafinta ba ibada in anyi magana shi kuma ubanta ya chafke da bala'insa shi a dole me san 'ya"tana sambatun ta ummah da haka tayi waje".
Har ta k'arasa d'akinsa nan ta iske dady xaune gaban mirrow yana taje kanshi daya ke daga wanka ya fito"karasawa tai gabanshi ta kai hannu ga Cumb nashi nan ya saki mata ta shi sharce masa kan a hankali tana shafanshi da hannunta cike da kulawa".ganin yadda take yi ne cikin burgewa daddy ya lalubo phone nashi dake aje saman mirrow d'in bata ankara ba taji k'es-k'es-k'es dady na snapping nata d'agowan da tai tana dariya ne ya k'ara yi mata wani se ya xamana duk yafi ko wannen ciki kyau"wow dear luk wannan pic d'in yayi kyau"duk'owa ummah tai itama tana kallo nan ya lakato mata hanci da kan phone d'in dady yace dix pic will be my new screen saver".dariya ummah tasa tare sa kamo hannunshi da alamun ya mik'e haka ba musu ya ko tashi ya biyo bayanta har gaban wardrobe d'insa nan ummah ta shiga nema masa kayan sakawa"cikin lafiyayyar shadda wacce tasha aiki ummah ya shirya dady ga hula ta kafa mai akai"ya fito fes"ware hannu dady yayi tako fad'a jikinsa ya manna mata peck a kuncinta yana fad'in dear banga macen data kaiki iya kula da namiji ba"kinsan kome na farin ciki naa".how i wish others will come and copy from u my dear"tana murmushi ta d'ago kai tace ok kar kai late maxa muje kai breakfast sarkin xolaya"har ta juya da xummar fita dady ya k'ara riko hannunta cak ta tsaya haka ya k'ara so gabanta ya wani langwabar da kai cikin nata yace Trust me dear Allah kin iya kome akaina".yanda yayi maganan ma abun dariya ya bata kamar wani k'aramin yaro nan umma ta saki dariyanta a fili"sosai suke dariya haka ta rike me hannu tana cewa ok i trusted your words swytynah let go".
Xaune take ummah gefen dady inda yake cin abincinsa ita ko tana taya sa hira!sakkowqn beauty suka hau ji daga saman matattakala tana ta rera wak'anta na "shakira i'm live"har ta k'araso dinning d'in da gudu ta nufi dadynta ta fad'a kanshi har se da kujeran ya d'an ja baya"cikin sauri ummah ta mike ta daka mata tsawa"ke meye haka?bakki da hankali ne?hannu dady ya d'aga mata da xummar ta yi shiru amma ummah sam tak'i jinsa"baxa ki tashi daga kansa ba wai?kaga shashashar banxa?haka ake gaisuwa a garinku?ni na rasa wallahi yaushe yarinyar nan ta xama haka?
A hankali beauty ke raba jikin nata dana dady ga hawaye nan shar ya gama cika kuncinta"nan ta d'ago kai tana kallon dady can ta nisa cikin kuka tace"dady u see ko?kuma bara kace komi ba ?in na nuna caring akanka ai min fad'a?in nayi ignoring mayi maka magana kai kuma kace i hated u?so ya kuke so nayi?bata jira maganan shiba ta juya baya da gudu rike da karamin jaka a hannunta se file nata tayi waje tana wani kwarma ihu kamar wacce aka daka".cikin sauri dady ya mike ya biyo bayanta har wani tuntube yake yi a kofa yana kiran beauty?beauty?pls beauty nah wait kinji ba haka bane?amma ina kafin ya kai ga cimma parkin space tuni beauty ta fixgi motanta tayi waje" dafe kai kawai dady yayi cike da takaicin abinda ya faru"shi ya rasa ma me xeyi wa ummah ya huce"ga wani irin gudu da yaga 'yar tasa nayi"Allah yasa de kar wani abu ya same ta"tunani ne ya fad'o masa hannu ya saka cikin aljihu ya xaro waya nambar beauty ya shiga nema amma gashi yana ruri tak'i d'auka"ran nan nashi gaba d'aya ba dad'i".cikin murya k'asa-k'asa yaji kamar daga sama ance dady ina kwana?waige ya kai gun se lokacin ya tuna da jiya fa cikin dare yayi bak'o d'an amininsa".murmushin dole ya k'irk'iro ya jefa masa nan suka gaisa yake tanbayarsa akan mahaifin nasa".lura da yanayin da dady ke cike yaso yi nan ya ke tambayar dady ko lafiya?ehh toh ka gane dama beauty ce ta fita da mota a guje kuma bana son tana irin wannan gudu kar wani abu ya sameta gashi ina ta kiran nambarta tayi fushi tak'i picking call na"bansan ya xanyi ba".cike da mamaki matashin ke kallon dady yadda duk ya damu akanta"ajiyan rai ya saki kafin yace ok dady ka sake trying layin nata mana"no baxan sake ba nasan bara ta d'aga ba i know her se de ko na baka nambar se kai ka kira tunda bata san namber naka ba"?jinjina kai yayi nan ya xaro phone nashi ya shiga karb'ar lambar".kira biyu yayi mata amma duk da haka batai picking ba".idan ran dady yayi million toh ya gama b'aci k'arfin hali kawai yayi yace masa ka wuce wajen aiki kawai ba damuwa bari na shiga ciki"yana kaiwa nan ya nufi ciki".
Cikin mota ya shiga yana k'ok'arin tada mota yake wata xuciyar ke raya masa ya k'ara gwada layin mana ko xe samu"a hankali ya danna nambar"kara yake yi sosai har gashi ya kusa katsewa se jiyayi karaf an d'auka".
Toh me ma xan ce mata?abinda ya fara sak'awa a rai kenan!hello who ix on d line?beauty tai maganan cikin fad'a"jin yanayi da ta karb'esa yasashi watsa mata magana shima cikin fad'a"STOP D CAR"I said STOP IT" keeeee... kake iya jiyowa alamar tsayiwar mota cikin waya"wata ajiyan rai me k'arfi ya saki jin haka kafin ya nisa' jin shiru ya biyo baya ne yasa ya d'an katse shirun tattausan voice nashi me cike da ixzah ga haiba ya fara riskan kunnen beauty inda ya fara da"pls take it easy mana wannan speed da kike gudu dashi haka yayi yawa"ko bak'ya son ran kine?so in bak'ya so ki aje shi akwai masu so"yanxu ina so ki tafi a hankali har ki k"arasa inda xaki kinji beautyn dadynta".?tsintar kanta tai da amsa shi da toh"yana jin haka kuwa ya kashe wayan yana wani murmushin jin dad'i ko ba kome ya san dady xe ji dad'i in ya fad'a masa ta rage gudun".
Abangaren angel kuwa ita abin ma mamaki ya bata wai ya akai ma ta d'aga kiran unknown number ita da bata haka kuma har ake bata command tana amsa"can kasan ranta kuma tace no ba command bane may be ya hange ni ina gudu ne yaga baxe iya bari na naci gaba da hakan ba se yayi protecting na"but ina ya sami number na kuma waye ma?tambayar kanta ta shiga yi amma ta kasa samo amsa tuna cewa akwai aiki babba da xata gudanar yau a scul d'in yasa ta tsaida tunani ta lalubi wayan nata ta kallon number d'in kafin ta shiga contact nata tai saving no da *MY PROTECTOR* haka tai saving badan wani abu ba se dan kariyar da take kawowa ya bata a yanxu".mukullin motar ta tayar ta shiga tuki abinta a hankali kamar yadda *PROTECTOR* Ya nema har ta isa bakin kofar JAMI'AR.
📓19 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE
Da isarta gida ummah ta tarar zaune a falo rik'e cajbi tana lazumi se gwaggo atika da ke zaune k'asan kafet tanai mata gyaran k'umba(farce)"--daddy wanna beat me bcox i gonna party"--shine baitin wak'an dake d'auke bakin beauty da haka ta shigo falon tana ta faman gyad'a kai uwa wata shurwa"gaba d'aya juyowa sukai suna bin ta da kallon mamaki"har tsakiyan falon ta k'araso rik'e da waya a hannunta se airpiece data sak'ala a kunne"
Hannu tasa ta zare shi a kunne sannan ta k'araso gaban momyn a kasalance ta zauna gefenta tace umma na dawo".toh sannunki"ummah ta amsata a tak'aice"sanin halin ummah ya sa ta mik'e ta nufi sama abinta" hooo hooo hoo!!Allah de ka shirya wallahi yanxu kai magana cibi ya zama k'ari"cewan ummah tana me allah wadai da hali irin na 'yar tata!"ameen de gwaggo atika dake duk'e ta fad'a".
Da shigarta d'aki ruwa kawai ta iya watsawa nan ta haye gado hannu d'auke da file nata".zama tai a tsakiyan gadon nan ta shiga bud'e file d'in a hankali tana nazarin sunayen data gani a ciki"gefe guda kuma ta janyo wayanta ta shiga laluben number datai mata aciki".sai da ta kira lecturers har tara(9) aciki"abin jin dad'in sai gashi duk 'yan kamun ludayi ne kowannen su yayi na'am da batu na beauty"dan Allah ya bata baiwar iya sarrafa harshe sosai".wasu a ciki kuma koda tai saving number d'insu a phone nata se ta lura da suna chart ai ko nan da nan ta yi musu magana suka ko biye mata(abin nema ya samu).kamar yadda malam umar ya sanar da ita cewa duk halayensu d'aya ne na bin mata in banda dattijon nan prof.KAS se ko gashi hakan ne". Ko me ta tuno kuma se ta shiga ci gaba da binciken file d'in wanda har ta k'arashe bata gani ba"!kallo ta kai ga madubin dake lik'e a bango a d'akin sannan tace toh in de haka ne wannan file d'in is incomplete tunda ban ga number sir.prince ba kamar yadda naji zee-zee ta ambaci sunansa d'azu"toh ko de shi ba na faculty namu bane borrowing d'inshi akai daga wani deparent din?any away zuwa dare naji daga bakin dattijon can".ruri wayan ta ya d'auka tana dubawa ko taga saleem ne wani d'an abokin dady ne wanda suka had'u ran birthday nata "da murmushi d'auke samalan fuskanta ta amsashi a waya nan hira ta b'arke tsakaninsu har kana iya jiyo dariyanta sosai a wayan da alama de hira yayi dad'i" a karshe ne ya ke nuna mata yana son had'uwarsu a wani guest house na mahaifinshi ba musu kuwa ta amince da buk'atan nasa don dama haka take so badan komi take son mu'amala da saleem ba se dan ko a 'yq'yan masu hannu da shuni su kansu suna fad'ar kud'i da jan aji na saleem se de shi matsalarsa d'aya bin mace me aji".bayan ta katse wayan ne beauty tai wani d'an k'aramin shewa cike da murna tana fad'in ko banza de duniya zata sanni da kai kuma se na tabbatar da na raba ka da kowace mace se ni d'aya tilo".
◆Wannan kenan◆
_Daren ranar:_
Zaune yake a d'aki saman kujera ya d'an kishingid'a kai kamar me nazarin wani abu se yaji an bud'e k'ofan nan hankalinshi ya koma ga k'ofan dan ganin waye" dady ya gani ya shigo cikin manyan kanya"da saurinsa ya mik'e zaune cike da kunya ganin yadda dady ya same shi daga singlet se short"kai sunkwi yayi yana d'an sosa k'eya har dady ya k'araso ciki".
Ina wuni daddy??ya fad'a da fara'ansa.lafiya lau sameer ya zaman kad'aici da kuma aikin naka hope de baka facing wani problem ko? Eh daddy babu ko d'aya se de wallahi daddy garin nan ya cika zafi".da dariyarsa dady yake kallonsa jin maganar da yayi yace toh in banda abin sameer ai ko ina kake da air conditioner kaga de d'akinka,falo cikin mota kuma na tabbata office d'inka ma da akwai"ido ya d'an kaikaici daddy da kallo da sigar na'am da batun nasa yace eh daddy amma weathern mu yafi na nan dad'i d'azu dawowa na ai ina tsakar gida shan iska"!
Jin yadda sameer ya kira tsakar gida hankalinsa a kwance yasa daddy sauyawa gami da neman guri ya zauna"haka shima sameer ya nemi gu ya zauna".
Emm sameer"dady ya kiraye shi" dama ina so mi wata magana da kai".kana ji ko d'ana?eh sameer ya fad'i yana me k'ara gyara zamansa sosai" ka gane dama ba wani abu bane'illah kaga ita beauty wallahi mace ce wacce bata son ganin jama'a hasali ma bata son jin hayaniya ko wanin bak'uqar fuska"tun tashinta haka take yanxu zaman ka a waje ze iya janyo min matsala ko ma yasa ta fushi"kasan rigimar yara"shine nace wai ko in ze yiyu kawai se kana zaman ka d'aki ko falo koma kai fitanka wajen shak'atawa tunda muna dasu anan kam da yawa"kaji d'ana na kai na"murmushi dady yake haka shima sameer ya me da me cike da mamakin maganan dady yace ba komi dady zan kiyaye"
Har suka gama hiransu dady ya yi me sallama ya fita amma sam sameer hankalinsa ya kasa kwanciya tunaninsa d'qya maganar dady"yanxu dan yarinya k'arama bata son jama'a se dady ya hau ya zauna bama yayi mata fad'a ko neman hanyar gyara ba"toh amma kuma ai ummah ba k'arama bace bara ace tana da k'aramar yarinya kode jika ce a gidan dady ke nuna mata so haka?hala shiyasa da na nuna ina son mu gaisa da ummah dady ya hana?Ganin bame amsa masa tambayoyin nasa yasa shi tashi ya rage wutan d'akin yabi lafiyar gado".
📓18 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
kamar yadda kullum wajen yake cike da jama'a toh yau ma de haka"bata wani b'ata lokaci ba da isarta wajen ta nufi wajen waiters d'in abincin wajen ta k'arashe siyawa gaba d'aya kamar yadda ta saba ta kuma umarce sa da yau ma duk wanda yaxo a bashi abinci kyauta a kuma sheda masa da *'yar jami'a*ta riga ta biya kud'in,take away tayi itakam dan cunkoson wajen baze barta ta iya cin abinci wajen ba"ta fito a wajen kenan ta waiga ido a car nata me xata gani?wani car yayi blocking nata a wajen"cikin b'acin rai ta dawo cikin restaurant d'in rik'e da key nata ta na gyad'awa!
Waiter! Waiter ta kira sunan a tsawace"fahimtar muryan wace yasa shi saurin fitowa a wajen nasu rik'e da serving plate yayo wajen ta yana fad'in hajiya wani abu kike so"?
Wani kallo ta wurga me cike da tsiwa tace wani blind man d'in ne mara ganin komi yayi wrong parkin a waje?cike da rashin fahimta waiter ke kallonta can ya nisa yace wallahi hajiya ban sani ba amma bari na tambaya"duk abin nan da ake jama'an wajen naji abin ka da d'alibai da son gulma"se k'us-kus suke suna tambayan juna ko de wannan ce 'yar jami'an da ake fad'i?wasu ko na cewa ai kam ta cika sunanta da gani akwai naira se de ba tarbiyya".ganin ze b'ata mata lokaci a gun yasa ta sauke wani gauran numfashi ta kallo shi tace look waiter kayi saurin nema min blind man d'in da yayi min blocking ma mota na ina jira a waje".tana kaiwa nan ta fice"
Cikin sand'a waitern ya lek'a waje ko ze gane motan waye"ai ko da alama ya fahimci me ita"rik'e baki yayi cike da mamaki na yadda ze je ya samu sir. prince yace gaya masa sak'on da aka bashi".
Waige ya hau yi gefe ai ko can gefe ya hango wani student wanda akasari kullum shike rik'e da jakan sir. prince inde xasu shigo wajen da saurinsa ya k'arasa wajensa ya d'an tab'o shi da hannnu"dan Allah malam minti d'aya yayi maganan yana matsawa gefe ba musu kuwa ya taso yaxo wajen shi yace ok ina jinka"dama kaga motan sir. ne a waje kuma ya rufe ma hajiya hanyar fita shine nace toh ko za kai mai magana ya d'an janye"ido d'alibin ya zaro don sanin ainihin waye sir.prince amma ya zai yi dole ya d'an sauke kai ya maida dubansa ga sir.wanda tuni yana zaune a can kujeran gaba hankalinsa kwance yana rik'e da phone nashi yana dannawa ga d'ayan hannun nashi rik'e da coke yana sipping passionately".kallo ya k'ara maidowa ga waiter d'in duk suka dubi juna"ka taimaka pls wallhi da hajiyar nan yanxu nake samun alheri mara musaltuwa"jin haka daga waiter yasa d'alibin gyad'a kai da alamar amincewa ya nufi sir.prince".
Salamu alaikum sir"wa'alaikassalam"sir ya fad'a had'e da d'ago kai yace"ya akai ne abdul"
Eh dama sir wai motanka ne toh....de"what's dix abdul?kai magana strightly mana. Wai dama motanka yayi blocking wani car ne shine....saurin dakatar dashi sir yayi".
Ohhhh bade yarinyar da ta shigo nan yanxu ana shouting ma waiter dani take ba"?shine har aka aikowa na janye mota"?well xan janye but she should bear it in her mind cewa se tai dqna sanin min hayaniya in public"..maganan zuci.
Mik'ewa kawai prince yayi ya janyo key nasa dake gefe kafin ya juyo ya kalli abdul ya ce seat here'i wll be back soon" da haka ya fice"
Tsaye take gaban mota se girgid'a k'afa take dan haushi duk wannan mutumin ya gama b'ata mata lokaci".jin alaman motsin mota tai bayanta ai ko da saurinta ta juya taga ana gyara parkin d'in da yake motan bak'i ne sosai se bara ta iya gano wanda ke ciki ba"kwafa tayi da sauri ta shige nata motan ta tayar"wani ja da baya tayi da motan har se da ya riski motan sir.prince na baya fitilan baya kake jin kwassss......na fashe wanshi".dariya beauty ta saki ganin b'arnar da tayi me ta k'ara sa kai gaba a motan ta ta fice a wajen tana fad'in maganin blind man kenan gobe ma ka sake wrong parkin".
Shiko sir du da abin ye me ciwo amma se yaa kasa komi agun ga jama'an dake bakin wajen duk sun ga abinda ya faru dole ya kasa fita a motan ya kira abdul daya mik'o masa kayansa a table.nan ya mik'o masa kawai ya bar wajen rai b'qce".
A wani gaban print container beauty ta tsaya ganin motan zee-zee a gun laluban wayan ta ta shiga yi"kira biyu kuwa ta d'aga"shegen kaya kina ina haka? Eh gani a print place ina printing wasu papers"ok in kin fito ina bayanki ki k'araso"toh zee-zee ta amsata dashi da haka ta kashe wayan".
Tana zaune cikin motan nata taan cin take away da tayi ne se ga shigowan zee-zee kallo beauty ta kai gareta aiko suka sa dariya baki d'aya wow k'awana amma fa kin sha kyau"maganan zee-zee kenan "ina kyau d'in yake ai ban kai kiba".
Shiru ya biyo baya kafin tace Yau fa beauty ban ganki a lecture ba kuma nai trying ma layinki off ko lafiya?
Eh toh kusan de lafiya amma baza ki sake gani na ma alecturen yau ba don na gama da lecturen"
Hhhhhhhhh shigiya beauty bade kina so kice min prof. KAS Yaxo hannu ba?"eh toh kusan de yaxo hannu amma saura kad'an"
Ban tari lumfashin ki ba fa amma ina ganin kamar an canja mana lecturen 1301 saboda yau wani sabo ne yaxo kin ganshi yaro matashi daga gani huta ya xauna jikin nan"wai shi sir prince baki ga yadda matan nan ke ta admiring nashi ba fa"
Cikin halin ko in kula beauty ta juyo tana kallonta can kuma tace kee kinga koma sir king ne ba prince ba shima xe mik'o kai"don haka kiban wani labarin ba wannan ba"
Nisawa zee-zee tai tace ke k'awa jiya fa k'iris ya hana baba ya kamani ba hijab"ina karyo layin gidan mu zan kai motata inda na ke ajeta kinsan be san Alh.bushasha yase min ba kawai se na ganshi yana k'okarin shiga gida"ai ba shiri na canja hanya da sauri"kinga yau ma dan kar ya gane wani abu dole se da nazo school na canja"
Wani uban dariya beauty tasaki had'e da kaima zee-zee duka a hannu tace'shegiyar gari ga son jin dad'i ga tsoro amma fa gaskiya baban nan yana kwafsa miki kamar ba uban zamani ba?"kinga niko daddy wani abun ma shi yake siya min duk da ummah bata so"
Ke ni kuma mama na so amma baba ke min cikas zee-zee ta fad'a tana tab'e baki".
Ok dear kar ki damu da baban nan ke de ki iya takunki kawai se kiga munci duniyar mu da tsinke'ki bari ma zuwa dare zan duba file d'ina duk lecturen da naga bashi da wani anfani a wajena zan turo miki number nasa"yanxu de kije kawai later zaki jini"
Cike da jin dad'i haka zee-zee tai sallama da beauty.daga nan ko beauty ta nufi gate abinta tai wajen a school d'in..
📓
17 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
A hankali take knocking kofan office d'in amma shiru kake ji kamar ba alamar mutum ciki har tana k'ok'arin tura kofan kenan taji ance yes"ai ko cikin sauri ta tura k'ofan amma se ta tsinci kanta da kasa shiga ciki dole ta d'an tsaida nutsuwarta waje d'aya sannan ta shiga ciki"taku take cikin wani salo na kwarkwasa ga yadda sanyin office d'in ke ratsata ta ko ina"wani irin annashuwa taji ya dirar mata duk da bata san dalilin hakan ba"har ta cimma gaban table d'in nashi kansa juye yake yana tsaye gaban wani k'aramin drawer nashi wanda ke cike da buks da alama wani research book d'in nashi yake nema"ganin haka ya bata damar kyara kujeran wajen sosai ta xauna ta had'e k'afa d'aya bisa d'aya"tare da kura ma inda mutumin nan yake da kallo"can ya nisa ya juyo rike da wani k'aton littafi ya shiga kad'eshi saboda k'ura"yana fad'in pls i'm so sorry for keeping u.....ai be k'arashe maganan da yayi niyya ba idanunshi ya dira ga beauty" tuni ya shiga tambayar kansa toh me ya kawo yarinya k'arama haka offince d'inshi?ko de sabuwar d'aliba ce tayi missing office d'in da take nema?k'are mata kallo yayi tsaf yaga de tabbas shigar jikinta babu alamar tarbiyya ko kad'an aciki"!dole ya dawo da nutsuwarsa sosai gareta tare da d'qn b'ata fuska yace wani abu ya kawo ki nan?jim baeuty tai da jin yadda yayi tambayar cike da manyance".leb'e ta d'an cije a lokaci d'aya ta mik'e tana k'ok'arin k'ara sowa inda yake".
Hannu yayi saurin d'aga mata"da alamar dakatarwa yace ke ina xaki?kuma me ya kawo ki nan?"share tambayar tayi"inda taci gaba da takowa" wani wawan tsawa daya daka mata se da gilashin idonsa ya zame Allah yasa da igiya a jiki".duk da razanar da beauty tai da tsawansa hakan be bata damar nuna masa ba"amma tunani take ta faman sak'awa a rai ta yadda zatai dealing da prof kAS cikin sauk'i ba tare da tasha wahala ba".
Agogon hannunta takai ma kallo taga har minti 4 ya tafi a cikin minti 10 data nema daga security man".karaf taji wata idea tazo mata cikin sauri tai juyi da baya kamar wacce ta tuna wani abu tai hanyar k'ofa" hannu takai ga mukullin k'ofan ta danna shi ciki had'e da murd'a shi ta ke kake jin k'ofan ya rufu gam"zare mukullin tai ta shiga gyara gaban rigarta ta jefa shi a rigar mama(bra nata)juyowa tai ta kwashe da wata irin dariya na k'eta lalle beauty ta cika shu'uma toh me take shirin aikatawa?
Cikin halin ko in kula prof KAS ke kallonta dan abinda take sam baya bashi mamaki don ya sha tsallake farmaki na 'yammata da zaurawa kai wasu ma matam aurene"balle wannan k'aramar yarinya a tunaninsa".ganin ta ci gaba da tahowa wajensa yasa shi harzuk'a ainun gaba d'aya jijiyoyin kansa suka d'aure"magana ya hau yi cikin fad'a".
Ke dan ubanki fice min a office kafin na sab'ar miki"!duk tashan balagar iskancin naki kirasa inda ze k'are se a kaina wato kin tsallake shashashan yaran makaranta kin taho garemu".dan tsabar rashin kunya bama yaran cikinmu ba ni zaki kawo wa shirmen banza cikin office".toh yau xan koya maki tarbiyya bari kiga"!hannu ya kai cikin aljihu yana laluben waya".
Wayar ya xaro nan ya shiga laluben number a ciki har beauty ta k'araso daf dashi nan ta ja birki ganin yadda duk ya wani kid'ime wai shi a dole ransa ya b'aci da hakan".nan ta watsa masa wani dogon numfani data saki tace":
Sorry sir' ni fa bana zo nan dan wani abu bane kawai nazo miyi hoto ne dan naga kana kama da daddy na"jin maganan da tayi ne yasa shi d'ago kai inda yayi dede da kashe masa ido d'aya da tayi"!
Hoto?hoton ubanki xaki d'auka dani"ke kinsan kuwa da wa kike magana?".jin yadda yake magana cikin fad'a ne ya k'ara tunzura beauty"
Enough! nace enough!!wanna hayaniyan naka ya ishe ni haka ko an fad'a maka ni ma ban iya bane?da na zaci xami abu cikin sauk'i mu gama ashe ba haka bane"toh wallahi kaji rantsuwa d'aya kenan koka amince muyi hoton nan ko kuma yau na nuna maka wace *'Yar Jami'a* don se na maka abinda duk wanda ya ji labari akanka se yayi Allah wadai da halinka"se kuma nayi silar barinka wajen nan in kuma kana ganin wasa nake toh ka gwada jayayya dani" ni kuma in nuna maka kaidin mata".
Tana kaiwa nan a zuciye ta nufi saman table dinsa inda ta d'ora jakanta hannu takai ciki ta zaro wayarta a fusace tayo kansa"tunani,bacin rai,ga wani azababban ciwon kai sun hadu sun cure masa aka"wai yau shine zai fad'a tarkon mace ko me?".ganin yadda Take nuni tabbas yasan yarinta na matuk'ar damunta kuma kome tace tabbas ita me iya aikatawa ce" be an kara ba cikin tunaninsa yaji kyas"kyas kyas !! har sau uku an d'auka"jikinsa har wani b'ari yake na ganin wani sabon abu yau a tattare dashi".bakinsa na rawa ya kallo ta kawai yace 'yar nan kiji tsoron Allah".ganin burinta ya gama cika gashi ta barshi tsaye da waya a hannu shi be kira ba kuma shi be aje ba yasa ta sakin wata irin muguwar dariya tace zuwa dare zan kiraka muyi magana so ka aje phone naka kusa da kai".
Daga haka beauty bata jira cewan saba ta xare jakanta tai bakin k'ofa hannu takai ta zaro key d'in daga bra nata ta bude k'ofan tai waje hade da janyo masa ita".
ya salam! ya salam!! furucin prof KAS kenan inda yake k'ok'arin durk'ushewa a k'asan kafet"inda tuni hawaye ya gama cika fuskansa ace wai yau 'yar cikinsa ke masa barazana da jikinta"yarinyar da bata wuce sa'ar autar 'yarsa ba".toh yanxu wani cikin makaranta yaji wannan labari ai ya kunyata duk kaffa-kaffan da yake da kame kansa amma yau babu".haka ranar ya wuni cikin mawuyacin hali duk aikin office d'in ya gaza yi".
Itako tun fitar ta cikin sauri ta k'arasa bakin k'ofan shiga wajen inda ta tarar da security man a zaune rik'e da radio yana sauraron shirin *RAI ANGIN GORO* Se wani lumshe ido yake hannu ta tafa ba shiri ya d'ago ganinta yasa shi rage sautin radion yana fad'in wai har kin fito"?kallo kawai takai ga agogon hannunta se kuma ta d'ago tace me acikin minti goma daka bani naci tara"shima dubi yakai ga nashi inda ya tabbatar da hakan"
Bata jira cewan saba nan ma de ta hau laluban zif na jakanta ta bud'e wani k'aramin dairy buk d'inta ta zaro nan ta shiga bude page har takai inda aka rubuta PLAN 2:PROF KAS nan ta duba gefe cikin wani karamin box da akai tai alamar mark" na gama aiki"kafin ta d'ago kai tace TASK COMPLETED".
cikin rashin fahimta ya bita da kallo inda ta maida buk d'in jaka tai mai sallama ta doshi motanta da niyyar tafiya capteria duk da taga alamar lokacin shigarta lecture hall yayi amma yunwa take ji".
Cikin nishad'i ta kunna motar inda tai hanyar Stop and chop"..
📓📓20 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE
A B'angaren beauty kuwa sam daren ranar bacci k'aurace mata yayi don kwance take hannunta naga phone nata ta k'urawa agogon wayanta ido"tqna jiran lokaci kamar yadda ta tsara" diqq...diqq...diqq...bugun alarm kenan da yayi na nuni da 12:00a.m cikin wani matsanancin farin ciki beauty ta kai hannunta ga d'aya daga cikin sunanyen contact nata" MY KAS sunan da ke bayyane akan screen nata kenan"laluban wayan na shi ta shiga yi"har sau biyu yana shiga amma ba'a d'au ka ba"m'ikewa tai daga kwanciyan da take tare da cunkud'e fuska tana mai ci gaba da latsa wayan nata"Allah yau kam ko asuba xa tai min se na tabbatar da ka..... ba ta kai k'arshen maganan zucinta ba ta ji takkk....alamun d'aukan waya"wani gauran numfashi ta saki tare da manna wayan akunnenta"
Amincin Allah ya tabbata a gareka jarumin jarumai"
"Shiru"
Sorry fa na hanaka bacci"
"Shiru"
Nasan tabbas kana ji na but ba wai maganan na ka ne abin so na a yanxu ba,abinda zan gaya maka shine abin so na da kai ka ji"
"Duk da haka de Shiru"
A zahirin gaskiya na yaba da kamala irin ta kwarzon dattijo kamar ka,don naji kowa yakan yabe ka,sai de ni na kasa gaskata hakan,ko meye dalili?nasan de bazan tab'a samun had'in kan ka ba,bawai dan bazan iya ba,ko banda hanyar yi,nop ko d'aya sai dan ba wannan buk'atar ce a wajena ba"
Prof.KAS abu ne k'arami a wajena amma bansan yadda kai zaka d'aukeshi ba"wato na tak'aice ma de course naka da kake yi wato 1301 nake so naga correct A1 a result d'ina"
Yin hakan gareka kamar taimakon kai ne kaga ni na samu jarabawa na, kai kuma ka tsira da mutuncinka,in kuwa ka bijire wa buk'atata toh wallahi abinda zai biyo baya se yafi haka zafi da muni dan ko sai na sa an yad'a min kai a jami'a da hoton da mukai na cewa ka nemeni a office naka nak'i baka had'in kai,kasan de sharrin 'ya mace saurin karb'uwa ne dashi dan haka sai ka zab'a aciki!".
Hankali kwance beauty ke maganan har ta k'arashe alamun da take gani na kamar baze tanka taba ne yasa tai k'arfin halin sai-saita dariyan da take tace"prof.nasan tunanin da kake na matarka da 'ya'yanka kai har ma da sauran jama'ar gari yadda zasu kalleka ko"?so just think about it wisely".
Emmmm by the way sir d'axu baka zo lecture ba wani yaro ka turo shi wannan ya sunansa?
"Shiru"
Bacci ya fara d'aukana pls ka fad'a min mana"
Sunansa _*SAMEER ALK'ASEEM MAJI-DAD'I*
Dan Allah yarinya ki ji tsoron Allah ki fita harka ta duk da nasan ban nemeki da sharri ba wallahi ban tab'a aikata abu makamancin haka ba"ban tab'a injustice ko ba wani marks free ba se yau kike so na da hakan why?baza kije ki karatu ki ci marks d'in da kanki ba"duk yadda na kai ga wulak'anta mata masu zo min da buk'ata irin naki na kasa miki haka"toh meyasa kema baza ki fita a harka na ba pls"ko ba dan komai ba ki duba girman shekaruna da iyalina mana".
Heeeeyyyyyyy ix ok sir bana son wani surutu haka"wa'azi zakai min?toh ka de ji abinda nace ni ban nemanka da sharri ba kawai de kabi dokar *'YAR JAMI'A*
_So just go and sleep and i wish u a colourful night_
Tana kaiwa haka ta katse wayan abunta"tai wurgi da ita gefe".
******
Haka rayuwa ga beauty taci gaba cikin jin dad'i da kwanciyar hankali duk wani abu nata da take buk'ata na rayuwa tana samu ga mahaifinta"in kuma batun makaranta ne data buk'aci wani abu zata kira wanda abun ya shafa"dan jami'ar ma yanxu ta tsaya da zuwa sai dai lokaci-zuwa lokaci wani uzuri nata ya kaita"sosai mu'amala ta goge tsakaninta da lecturers d'in nan yadda take so haka suke mata"wanda duk yaso shiga harkar ta ko a school tuni zata sa a dakatar da mutum a karatu"shaharar beauty ta kai inda takai"dan kowa yasan wace *'yar jami'a* babba ko yaro"
Duk inda ta wuce nuna ta ake"b'angaren zee-zee ma de abin ba'a cewa komi duk da takan shiga lectures amma dai suna ne don yawancin yanzu tare suke zuwa yawonsu sai can dare ko yamma lik'is sukan koma gida.
Koda ummah ta tambayeta game sa canjin lokacin na dawowarta yanxu kam cewa tai an gyara musu time table ne,duk da ba wani gamsuwa tai ummah da hakan ba amma ya zatai dole ta barta a hakan!"gudun fad'an dady!"
A b'angaren Sameer kuwa tun randa dady yazo mai da maganar baya son ganinshi a harabar gidansa se ya zamana kullum yana sashensa"don k'arfe 6:00a.m yake fita waje baya kuma dawowa sai 9:00p.m tunda Allah ya had'ashi da wani frnd Ameenu shike nan ya samu gidan zama!"
[1:50pm, 24/11/2016] Salaha: 📓📓21 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
Kamar kullum dai yau ma prof KAS zaune yake a faffad'an office nashi"kansa duk'e yana bitar wasu takaddu wanda da alama suna da matuk'ar anfani a gareshi yaji an bud'e k'ofa".ko da ya d'aga kai da murmushinsa ya sauke ga bak'on nasa"matashi ne ajin farko wajen iya shiga da haiba" wato Sameer kenan"k'ofan ya me da ya rufe ya k'araso ciki"cike da girmamawa ya gaishesa kafin ya nemi ixinin zama".hira suka shiga yi sosai irin na d'a da uba,inda prof ke ta zubo masa tambayoyi game da jami'ar don jin ko yana fuskantar wani k'alubale"hakan kuwa sameer yace babu don tun fara aikin bautar k'asan sameer a makarantar babu wata 'ya mace data samu damar masa magana duk da ana yawan yabawa da komai nashi amma sam yak'i bada fuska"kasancewar shi mutum ne mara son rai ni ko kad'an".daga haka prof ya d'an k'arayi ma sameer wasu 'yan nasihohin duk de akan sharrin mace"abin har yakai yana ba ma sameer mamaki yadda prof ke masa nasihan" don shi tun tashinsa mace ma bata gabansa balle har yayi tunanin biye mata"haka de yabi prof da toh kafin daga bisani yayi masa godiya da nasihan".
Long sheet dake gabanshi a hankali prof yake kallonta can ya nisa ya ce wannan fa result ne na yaran can da ake k'ok'arin kafe musu yau kasan sati uku baya sukai jarabawan"
D'ago kai sameer yayi yana mai bin sheet d'in da kallo sannan yace but sir ande samu gud performance nasu ko? Ehh toh gashi nan amma de.....
Bud'e k'ofan da akai ne ya hana prof kasa k'arasa magananshi"hantar cikinsa ce ta bada wani irin k'ara cike da razanin halittar da ya gani gaban k'ofarsa"cikin isa da tak'ama ta k'araso har gaban tabur d'in nasa daf da kujeran da sameer ke zaune taja kujeran gefe d'aya ta zauna"kallo duk suka bita dashi musamman sameer da be tab'a tsammanin ganin wata mace a office na prof ba"musamman irin wannan matan"sam mace ba kamun kai"ga jiki kusan tsirara har kana iya hango kalar bra din jikinta don tsananin hasken kayan data sa" kai k'asa sameer yayi don baze iya jure ma ganin abu irin wannan ba"
Shirun nasu ta katse cike da shauk'i beauty ke fad'in
Morning sir"ka ganni se yanxu ko bacci ya d'auke ni da yawa" by d way bade wannan ne result d'in namu ba?let me see?hannu ta kai ga sheet d'in hankali kwance ta rabo shi da ita"
Shiko ji yake prof kamar ya bud'e k'asa ya shige a ciki dan kunya"yanxu da wane ido zai d'aga ya kalli sameer?yanxu fa yake masa fad'a kan bin ashararan matan jami'a gashi tun ba'a je ko ina ba shi ya kamasa da irinsu".
Wow good job dad'i na wallahi da mutane na saurin d'aukar darasi kaga de kowa yasan hak'k'in d'an uwansa"but second class kuma?"yamutse fuska beauty tai can kuma ta saki tana fad'in i will just manage it bari naga na k'awas d'ina" nan ta shiga duba na zee-zee"
Hhhhh dariya"shegiyar gari wallahi ta haye kalli wannan gaye d'in ma da tace course na shi da wahala se gata da B2 da alamun ya bada kai kenan"?
Ke wai me haka kike yi ne?cikin zafin nama da rashin jin dad'in abinda beauty take sameer ke maganar". A raunane beauty ta d'ago kai cike da mamaki ta wurga masa wani wulak'an taccen kallo tace and who are yuh? Kake min tsiwa baka bari uban gidan naka yayi?ko kuwa wani sabon iskanci ne hakan?".
Be kai ga magana ba prof yayi saurin dakatar dasu" wai what's going on ne haka? Kuyi shiru mana"magana prof yake duk a kunyace"ya ma rasa me xaiyi"
Kasa jurewa abin yayi sameer lura da yadda yanayin prof duk ya canja yasa shi mik'ewa tsaye a fusace ya hau dubanta yana gyad'a yatsa"
Surely u dn't know who i'm"
But i sameer d son of Alkhaseem cn't take all these of your nonsensity"
In kuma kinyi denaying haka wait and see"bugun da yakai ga tabur d'in yayi dai-dai da juyawansa don fita".zafin naman itama de beauty ta nuna inda ta cakulo wuyansa tana me wurgi da sheet d'in waje guda tana wani zare ido kamar mayunwaciyar zakanya cike da huci ta fara fad'anta"ni kake ma shouting akai?baka san wace *'Yar jami'a*ba ko?ka rubuta ka aje wa'adin aikin ka yazo k'arshe".
Sake mai kwalan riga tai ta juya a fusace da yake ba komi hannunta dama ta shigo haka tai waje abinta"
Karo na farko da wata 'ya mace ta tab'a matsowa har kusa da sameer haka sai gashi abin ya kai ga cakumar riga?"kan ubancan"
Yayi maganan a fili yana kallon prof da tuni idonsa ya gama cika da kwalla" dan takaici"abinda yake gudu kar wani yasani yayi masa kallon ashararan mutum yau ya tabbata"
Hannu ya k'ara kaiwa ya bugi tabur d'in cikin tsiwa sameer yake fad'in ashe kuwa yarinyar nan ta taro match se na nuna mata ya ake rayuwar jami'a"bade tai ikirarin ita *'yar jami'a*bace? Be jira cewar prof ba ya juya a fusace yayi waje"ji kake garrrrraaaammm na rufewan k'ofa"!
[1:50pm, 24/11/2016] Salaha: 📓📓23 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
Bata jira ji daga gareshi ba beauty cikin zafin nama ta mik'e had'e da sauke wata nannauyar ajiyar zuciya,tai hanyar fita,cigaba malam umar yayi da kiran sunanta abin tin yana k'asa da voice nasa har ya k'ara raising nashi amma sam beauty tak'i sauraronshi."
Cikin b'acin rai na rashin samun mafita da haka ta baro office d'in nan ta nufi hanyar barin jami'ar" gudu take sosai abin ta har ta cimma babban gate d'in kamar baza ta tsaya ba kuma kome ta tuno ai ko ta saki uban birki a bakin wajen ji kake keeeeeeeeeeee"na k'arar tsayuwar mota"cikn sauri mutanen dake bakin wajen kowa ya dawo da hankalinsa gareta don ganin ko lafiya?hankali kwance take bud'e glass na motan tare da fiddo hannu rik'e da k'aramin kati(exit) a hannunta ta mik'a ma security man d'in"tun tsayuwar motar agun duk ma'aikatan gurin sun fahimci motar wace shiyasa ma basu wani d'aga hankali da abun ba don inda sabo su kam sun saba"hannu ya mik'o had'e da amsa da haka ta maida glass nata sama ta ja motanta gaba".
******
Mutumi na kana ina ne?cewar sameer wanda yake zaune cikin mota yana tuk'i ga waya a manne a kunnensa yanayi hankalinsa a tashe kana gani kasan cike yake da damuwa"daga d'ayan b'angaren aka bashi amsa sannan yace owk toh gani nan k'arasowa ina hanya".katse wqyan nashi yayi ya ci gaba da tuk'insa,kusan minti goma kenan da yin haka sai gashi a bakin wani makeken gida"horn biyu yayi mai gadi ya lek'o gami da bud'e gate d'in fahimtar wanda ya zo da yayi",a parking Space na gidan yaje cikin jerun motocin gurin ya aje nashi gami da fitowa ya nufi cikin gidan".a falo ya tarar da mama wato mahaifiyarameenu inda cikin girmamawa ya gaisheta sannan ya nemi izinin shiga cike"cikin wannan takun nasa na isa da tak'ama yake takawa kamar wani wanda ke tsoron k'asa haka ya riski d'akin".da sallamarsa sameer ya bud'e d'akin"amsanshi ameenu yayi a nutse"amma sameer ko ta kansa bai bi ba ya nufi gado abinsa"kwanciya yayi ya juya baya had'e da rufe ido kamar wani me bacci"
Ameenu Dake zaune saman 2 seater rik'e da magazine yana karantawa, cike da mamakin yanayi irin na aminin nasa dole ya ajiyeta gefe guda ya nufo gareshi"
Prince lafiya? Meke damunka haka?mtsssssss......... wani dogon tsaki da sameer ya saki ne ya k'ara tabbatar masa cewa da abinda ke damunsa"hannu yakai ya d'an dafa kafad'ansa a hankali ya shiga bubbuga masa ita yana fad'in pls be lyk a man"fushi fa ba naka bane"koma waye ya b'ata maka just forget about it & let us chill like nothing do you man pls"wani wawan juyi sameer yayo nan take kuma yabi shi da kallo cike da b'acin rai kafin ya iya mosa lips na shi a hankali yace"kasan kuwa me kake cewa?kana so kace na manta da abinda ya faru yau?that is unbearable"ba ran iya hak'ura ba wallahi"nan da nan kuma yanayinsa ya canja jijiyoyin gaban kansa duk suka riga suka mik'e cikin zafin nama ya d'ago jajayen idanunsa yace"se na koya mata hankali"sena tabbatar mata cewa jami'a ba gidan iskanci bane gidan koyan karatu da ladabtarwa ne" wai ni sameer yau wata banza har zata kalleni ta fad'a min magana"by the side ita 'yar gidan uban wace take jin kanta haka?
Sai a lokacin ameenu ya fahimci inda sameer ya dosa"duk ta k'are dama yasan hakan na iya faruwa'don ba yarda za'ai matashin namiji kamar sameer ace bai samu matsala da mata ba"sai gashi yau yazo masa da zancen"murmushi mara sauti ya yi kafin ya kai dubansa ga sameer ya iya cewa"calmdown prince yanxu akan wata mace kake d'aga voice naka haka?kamar ba sameer d'in dana sani a baya ba wanda kullum kake cemin mace bata gabanka yau kuma ya abin ya canja?ko de ka fad'a mata wani secret na mind d'in ka tayi rejecting ne?fad'amin naji wace lucky gal ta yi nasara akanka haka?"cike da zolaya yake maganar"mugun duka sameer ya kai masa a cinyarsa ji kake d'asss..dan maganar tai mai ciwo"stop it kaga bana cikin wasa yanzu"ko zakai min wasa karka k'ara had'ani da wannan 'yar iskar wacce bata ma san ciwon kanta ba"may be ma iskanci akai da uwarta aka haifeta shiyasa itama take haka amma kana dangantani da ita?ganin yadda sameer ya d'au zafi na ruwan bala'i yasa ameenu sassauta murya ya hau masa nasiha"
Kaga de prince ba'a haka a rayuwa duk laifin da mutum yayi maka baka ai batashi haka don baka san wanne baiwa Allah ya aje a tattare da shi ba"duk da na fahimci akan mace kake wannan fad'an toh ina so ka sani ita mace k'ara min tunani gareta abu k'an k'ani na iya saka ta ga tafarkin dai-dai haka zalika abu k'arami yakan iya jefata ga halaka"saboda su mutane ne masu rauni"idan mace tai maka ba dai-dai ba rabuwa kake da ita sai kai mata addu'ar shiriya".
Addu'ar shirya?shirya fa kace?lallai baka san yarinyar nan ba kenan? ai ba zata tab'a shiryuwa ba" illah kawai na samu hanyar da zan lalata mata rayuwa ta gane cewa tayi kuskure a rayuwarta data d'auki jami'a tamkar gidan b'atanci zalla"kaji de na gaya maka"yana wani gyad'a masa hannu alamun gargad'i".
Toh naji but meye sunanta?
Cike da harara sameer yake kallonsa" kamar shi yayi masa laifin can kuma ya saki wani dogon tsuka yace" i don't care to know that"all what i know de ana kiranta da *'yar jami'a* kaji wani banzan suna"sameer ya fad'a yana watsa hananye"shide ameenu binsa kawai yake da ido kafi ya nisa ya ce toh Allah de ya sawwak'e amma yanzu muci abinci ka huta se na rad'a maka wata sauk'ak'ak'kiyar hanya ko zaka iya binta may be da haka ka rama wanna abun da tai maka"
Jin haka ba k'ara min kwantar ma sameer rai yayi ba don shi babban burinsa dama be wuci yaga ya rama abinda beauty tai masa ba musamman ya samu hanyar korarta a karatunta".
Haka suka zauna gidan bashi ya koma gida ba se can bayan 10:00p.m.koda ya koma watsa ruwa kawai yayi tare a jero nafilfilinsa na dare sannan ya haye makwancinsa".
📓22 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE
Tun fitowar beauty bata zame ko ina ba sai office d'in malam umar ko da ta isa ta tarar da dashi tare da bak'o"dole ta d'an dakata a waje"kusan minti goma da haka sai ga shi ya fito don raka bak'on nasa ai ganin beauty tsaye gaban office nasa sai kai kawo take a wajen kamar wata zautacciya"dole yayi sallama da bak'on nashi ya k'araso gaban ta cikin sauri"
"Yar jami'a lafiya?
Da saurinta beauty ta juyo daga zagayen da take yi se wani ajiyan xuciya take saki tace"mu shiga ciki wannan ba maganar waje bace"
Gaba ya wuce tana biye da shi a baya har suka k'ara office nashi"tsaye tai gaban kuje ran"yayi yayi ta zauna amma sam beauty tak'i"
Dole shima ya taso ya dawo kusa da ita ya shiga magana cikin tattausan lafazi don ya lura tabbas yau ran mutuniyar tasa b'ace yake"
Pls kyakykyawa ki d'an saki fuskan ki daga wannan cukulewan wlhi sam be dace dake ba"
Wane abu kike so a makarantar nan baki samu ba?
Ina ce na baki file me d'auke da komai na jami'ar nan'kuma da bakinki kince min kingama samun komi naki"
Wait malam kar ka sake cewa ka bani komi"baka bani ba ni zakai ma wayo"cike da tsiwa beauty ke maganan"
Wallahi a iyakar sanina na gama baki komi, amma fad'a min me kike so yanxu?
Kallo me cike da raini beauty ta wurga me dole ya d'an kauda kai"kafin can ta d'ago kai tace:
"Ina so ka gaya min game da wani wai shi sameer alqaseem"tell me waye shi?kuma d'an gidan uban waye a garin nan da har ze zage ni a gaban prof KAS"?
Wqni gauren numfashi malam umar ya saki cike da fargaban sunan da yaji beauty ta kira nan ya ja kujerar dake gefensa ya zauna dan samun cikekken nutsuwa"
A hankali ya matso da wata kujera dake gefensa kusa dashi yayi ma beauty nuni data zauna ba musu kuwa da zauna ta maido dubanta gareshi tana saurare"
Wato kina ji ko 'yar jami'a bazan b'oyr miki komi ba dan nasan mun zama d'aya kuma ko wane abu zaki iya yi a makarantar nan amma bazan tab'a lamunce wa kaina baki damar shiga harkar wannan bawan Allahn ba"dan shi ba malami bane"aikin bautar k'asa ne ya kawo shi nan garin kuma yanxu yaci rabi zuwa k'arshen shekara zebar wajen nan"ki rabu da shi kawai in ma abu yayi miki kiyi hak'uri a karo na farko de pls"!!
What malam umar kasan ko me kake cewa?ai gara kace min baza ka iya ba kawai na nemi wata hanyar amma ba ka tsaya min wa'azi ba"dan ko wallahi ka rubuta ka aje korarsa za'ai a jami'ar nan confirm".
📓24 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
Ta b'angaren beauty kuwa ranar tun komawarta gida d'aki ta nufa ta kulle kanta haka ta wuni ciki"tun abin be dami ummah ba har yakai ga ya fara don sam beauty bata fiya jimawa haka a d'aki ba ko da kuwa baza ta fito parlo ta zauna ba amma dai ta kan lek'o tym to tym sab'anin yau'se de ko da ummah taje ta tambayeta se ta nuna mata ba komi"
Da misalin k'arfe 8:00p.m daddy ya shigo gida sashensa ya wuce inda ya iske ummah tsaye rik'e da garwashi na turaren wuta tana turara falon"wani a jiyar zuciya dady ya saki sakamakon wani daddad'an k'amshi daya doki hancinsa"cike da murmushi umma ta nufo shi tana me ajiye garwashin gefe guda"
Rungume juna sukai na d'an tsawon lokaci wqnda hakan ya nuna tsantar kulawa da missing na junansu da sukayi"umma ce ta shiga janye jikinta a hankali tare da amsan jakan dake d'auke a hannunsa"
Sannu da dawowa dear"
Yawwa umman beauty"ya kula da gida da kuma kanki hope de baki wahalar min da jikin nan naki sosai ba?"daddy ya fad'i idonsa k'uru bisa nata"
Haba dear kaima kasan ba yadda za'ai na wahalar maka da jikin nan naka da yawa,zaka sameshi yau fiye da kullum"
Allah umman beauty??cewan dady yana washe baki.
Sosai ma kuwa! se de fa wani hanzari ba gudu ba yau na kasa gane kan yarinyar can tun dawowqrta a makaranta take d'aki".what??? Amma kuma kike cemin gida lpy?yoh ba gwara komi ya hargitse ba da b'acin ran gudaliya ta"bari naje naji me ke damunta"cikin matsanancin damuwa daya riski daddy lokaci d'aya haka ya nufi sashen beauty"
Knocking......yes daddy come in"beauty dake kwance can saman gado ta juya ma k'ofa baya tai maganan sanin cewa daddy ne kad'ai ke mata irin wannna knocking d'in"
Bud'e k'ofan yayi had'e da kiran sunanta yana mai k'ara sowa cikin d'akin"k'aramin teddy nata dake mak'ale a jikinta ta janyo gami da wurga ma dadmdy shi kamar yadda ta saba in tana matsanancin fushi irin wannan tace pls daddy go away ni bana son ganin kowa yanxu"just go"tai maganan tana turo baki waje"be biye ta nata ba dady ya haye gadon daf da ita ya zauna tare da sak'ala hannunta cikin nashi ya juyo da fuskanta gareshi murya ciki-ciki dady ke tambayan beauty na waye ya b'ata miki rai ki gaya min ko waye shi & i promise u cewa zan dealing nashi kowaye pls my one and only one"lura da yadda daddy ya damu sosai da halin da take cike da yadda dady ke fad'in ze dealing ma damuwanta yasa ta d'an saki ran nata kad'an ta shiga magana uwa tana rad'a"dady wani lecturer ne baya son cigaba na a school d'in nan duk yabi ya dameni yau fa har ikirari yake wai se ya koreni don kawai na samu result me kyau so shine nake so dady ka saka a koreshi kafin shi ya aiwqtar da nashi akaina"
Jim dady yayi a fari da jin batun da beauty ta zo mai dashi yana tunanin hanyar da zai magance damuwan nata"
Beauty meye ne had'inki da wani malami a makaranta kinsan fa duk wani abu dazai janyo na samu nak'asu a har kar kasuwancina beauty bana so"bana so in ji kina rigima da wasu don duk wanda yasan cewa ke 'yata ce zai so kuyi kyakykyawar mu'amala ba mummuna ba"inda san samu na ne har ki gama karatunki ba wanda zai san ki in ba 'yan ajinku ba"suma d'in se dan ya zama dole amma yanxu ni naje nasaka a kori wani ai se a watsa a kafafan yad'a labarai wanda hakan ba karamin zubar min dq k'ima ze yi ba"pls beauty dadynki na baki hak'uri da ki bar maganar nan tunda kince kinyi nasara a jarabawarki watak'il abu kika mai ba dai-dai ba kawai ki bashi hak'uri duk randa kuka had'u kuma ki fita a harkarsa,kinsan fa bana so ummanki ta fahimci wani abu so nake ki bata mamaki duk da tana ganin bazaki iya karatun nan ba ki taimaka mu bata mamaki"ki fita da flying colours se mu had'a wani gagarumin shagali"koya kika ce beauty??fuska ba yabo ba fallasa beauty ke bin dady da kallo duk da hakan da ya fad'a sam be yi mata ba toh ya ma za'ai kamar ita ace ba wanda zai santa sai mate d'inta ashe bata cika *'yar jami'ar*ba,banda cincirun don malamai gogaggu da beauty ke harka da su"dariyan yak'e ta sakar me tare da langwab'ar da kai a jikinsa ta lafe tace ok dady na ji ba komi zan fita a har karsa amma kai ma de kasan bazan je na bashi hak'uri ba but believe me duk randa ya k'ara shiga har kata Se ka d'au fansa daddy"
Dady promise me mana kayi shiru"
Sanin rigima irinta beauty dole dady ya amsa mata da yes"da haka ya kamo hannunta suna ta hira abinsu duk da beauty ta gama k'udurta bin wata hanyar don ganin ta muxguna ma sameer da haka suka sakko dinning inda ummah ta gama jera kayan abinci nan suka zauna don cin dinner"
Sosai beauty ke cin abincin don wata irin matsananciyar yunwa data wuni da ita nan ummah ta samesu itama tai joining d'insu"bayan sun gama ne dady ya k'ara jan hannun beauty falo inda sukai ta kallo suna hira ala dole dady naso ya ga ya kawar ma beauty da damuwarta"
K'arar horn na shigowan mota suka ji dady ne yace toh ga d'an albarkan nan ya dawo"
Hmmm kai da ka sanshi ba? ace yaro tun zuwanshi gidan nan ban tab'a saka shi a ido na ba"ko tunanin yazo ya gaishe ni be yi ba?cewan momy tana kalon dady"beauty ko kamar jira take nan ta soma"ai wallahi umma shiyasa ni tun farko nace ban yarda kowa yazo mana gidan nan ba don duk basu da tarbiyya dady ya nace se yazo".
Hannu dady ya kai ga bakinta yayi saurin tsayar da ita a magana yana cewa kai beauty na kin manta ke kika ce min kin yarda yazo amma bakya son ganinsa a hara bar gidan nan"shine fa nai masa iyaka da cikin gida dan kar yazo ya damar mun ke".
Dariya sosai kake gani d'auke saman fuskar beauty sorry dady kaga na manta,gaskiya dady na k'ara tabbatar wa kana so na fiye da tunani na me too luv you dady"peck ta kai masa a kumatu' nan suka hau dariya na jin dad'i abinsu nan-da-nan beauty ta shiga yi mai surutai kala-kala wani abun ma duk shirme kamar ba wacce ta mallaki hankalin kanta ba"
Mik'ewa ummah tai don takaicin yadda suka maida ita gefe guda suka watsar suna ta hirarsu"duk abin duniya ya isheta ita ba abin tai kishi da 'yar cikinta ba'dole ta nufi sama abinta ta bar su nan falo zaune"
Ba ita ta shiga d'aki ba beauty se wajen 12p.m haka watsa ruwa tare da haye wa gado"wayarta ta janyo ta shiga laluben numbers na wasu daga cikin lectures din abokan harkarta"a inda duk wanda takai ma batu na korar sameer daga aiki se a nuna mata gazawar hakan,wasu kuma su nuna mata yiyuwar hakan amma indai har zata kai musu ziyara a wajen had'uwarsu"dole take amsa musu da eh tunda bata da wani buri yanxu wanda ya wuce taga ta kori sameer daga jami'a kafin shi yayi kamar yadda ya furta mata".
📓📓25 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
💕
Yau take litinin wanda yayi dai-dai da dqwowar d'alibai daga hutun sati biyu da aka basu na gama zangon karatu na farko (wato first semester),kowa ka ganshi cikin shirinsa tsaf na komawa karatu wasu fuskoki na shek'i na samun nasarar jarabawar baya wasu kuma akasin haka"
Zaune take a bakin wata theater rik'e da takadda a hannu"ta na yamutsa fuska xee-xee ta d'ago kai ta dube ta".wai beauty lapiya naga duk kin wani had'a fuska?banxan kallo me cike da jin zafin tambayar beauty ke kallonta dashi can kuma ta kai ajiyan lumfashi tana fad'in ai dama ke baxa kiga komi ba" amma fa ki kalli time table d'in nan har da statistic bayan kinsan bana son harkar calculation"ni wallahi duk naji karatun ya fita a kaina"baki xee-xee ta bud'e cike da mamaki toh da har wani karatu ma beauty ke yi a haka?a xahiri kuwa tace haba beauty ke da jami'a ke hannunki ai bake ba har ni xan so A1 ko ya kikace kawai first lecture d'in xamu shiga da haka xamu gane wa xe d'auke mu in me xafin kai ne na bar ki dashi in kuwa ruwa-ruwa ne ki watso min number d'insa"
Tabbas beauty na matuk'ar jin dad'in yadda xee-xee ke yawan yabonta haka'suna cikin haka sqllama suka ji an sakar musu cikin wata siririyar murya"yi sukai uwa basu jiba haka aka k'ara rangad'a sallamar cikin kasalanci xee-xee ta d'ago kai tana kallonta"matashiyar yarinya ce kana ganinta kaga kamilar mace me cike da addini basai an gaya maka ba"don sanye take da atamfa d'inkin riga da skirt ga doguwar hijab har k'asa"sannan k'afafun nan an suturcesu da safa"
Sannunku"matashiyar ta fad'a"
Yawwa meke faruwa kika xo saman kanmu kikai mana inuwa kamar wata ice?xee-xee kenan tana magana tana wani taunar cingom"cikin halin ko in kula matashiyar ta saki wani k'aramin ajiyan zuciya tace eh dama naga kamar kuma class d'inmu d'aya kuma naga yawanci duk ba'a da time table shine nace bari na tambaye ku? D'agowa tai cikin sauri beauty daga jinginar da tai da kujera ta d'ago kai a karo na farko tana dubanta"
Me kika ce?time me??time table?? Eyyee kaga director kai koma ince rector saboda ga sa'anninki ko?duk fad'in makarantar nan baki ga maraina wayonki cikin sanyin safiyar nan ba se mu ko?bakusan ku yak'in nema ba se an samu kuyi photo copy ki??toh ga time table d'in a hannu na xo ki karb'a?cikin fad'a-fad'a beauty ke maganan tana gyada k'afa"
Jin yadda beauty ke magana yasa matashiyar k'ara san yaya murya tace kiyi hak'uri ni ba fad'a nazo yi ba"k'ok'arin juyawa ta shiga yi don barin wajen don tasan tsayuwarta kan iya haifar da wani abun" wani dogon tsaki mtsssss... xee-xee ta saki a gurin tare da k'ara kare wa matashiyar kallo ta baya"dubeta kucakar banxa ko an gaya mata nan tsangayace ko xauran wa'axi da xata xumbulo mana hijabi luuuuuu....se kuma ta katse maganar sakamakon wata muguwar dariya da taji ta kufcewa beauty"da sauri ta d'ago tana tambayar lpy de?se da tai dariya me isarta beauty sannan ta waigota tana nuna ta da hannu cike da mamaki"
Dilla can kin ganki wai har kura ce xata cewa kare maye" ko kema ba hakan kike tahowa daga gida ba ki shigo mana jami'a uwa matar malam se an xo abi lungu a canja"se kuma ta k'ara tuntsurewa da dariya tana fad'in gaskiya duk ranar da na ganki cikin kayan zafin can dole na ja ki miyi selfie"
Yanda take dariya abin ya matuk'ar bawa xee-xee haushi"wannan ma ai cin fuska ne"cikin fushi ta mik'e wqnda tuni beauty ta rik'o hannunta nan ta shiga bata hak'uri"zama ta koma tai fuska ba yabo ba fallasa take fad'in ok komai ya wuce yanxu ina ki kai?
Yamutsa fuska beauty ta d'anyi kafin ta saki tace'gida xan wuce dama kinga abinda ya shigo dani ta nuna time table"yanxu haka kuma xan fitq a school sede hanxari ba gudu ba yanxu ma na koma gidan ummah ta hau jero min tambayoyin na dawo da wuri"kai duniya wannan wacce irin uwace"?dafe kai beauty tai cike da damuwa kafin ta nisa tace any way daddy ai nasan be fita ba tunda yanxu 9:00a.m be yiba barq nai sauri na koma na samu me karemin"xumbur beauty ta mik'e had'e da sak'ale jakanta a wuya ta juyo ta kalli xee-xee tace kin gane xan wuce se munyi waya"a haka suka rabu beauty ta shige mota ta fice a jamiar ta nufi gida!.
📓📓26 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
Da isarta gida q haraba ta tadda motar daddy ali driver na wanke masa cike da murna ta k'ara so ciki"falo ta dosa kai tsaye tana shirin bud'e labule ta ji an bud'e cikin hanzari ta ja da baya ta tsaya"ummah ce ta fara fitowa rik'e da brief case"daddy na biye da ita"hajara lpy kika dawo gida yanxu ko kin yi mantuwa ne?cewar ummah tana dubanta fuska had'e" dama tabbas tasan haka xe faru beauty don haka tai saurin kai idonta ga daddy inda tai nare da su"gyaran murya daddy ya saki tare da kamo hannun ummah kad'an ya ja da alamun ta sauke idon ta haka daga kallon da take wurgar beauty dashi"burus ummah tai tambar bata ji shi ba inda ma ta sake jefo mata tambayan"da ke fa nake kikai min shiru ko?? Ganin yadda ummah yanayinta ya sauya ya baiwa beauty damar daurewa murya cike da sark'ewa tace emm..emm dama yau ba lecture se gobe bayan munje ne monitor ya sanar"
Badan ummah ta yarda da xancen beauty ba amma dole yasa ta shareta lura da sauyawar fuskar daddy".
"Beauty nah tafiya ce fa ta kamani yanxu haka,bayan fitar ki d'axu governor ya sanar dani wani taro da zashi jarmany na harkar farfad'owar tattalin arxikin kasuwanci"ya kuma nemi dana shirya muje tare yanxu haka jakata na mota xan wuce"
Yeennnnnnn.....kuka beauty ta saki tuni ta shiga buga k'afa tana wani langab'ar da kai da hannu ta hau magana a shagwab'e"yanxu da bandawo ba haka dady xaka tafi ban sani ba"toh Allah nima ka tsaya na had'o kayana mu tafi tare"yunk'urawa tayi da niyyar shiga ciki dady cikin sauri har yana tuntub'e da labule ya biyo bayanta yana kiran sunanta"
Ya ilahi"me xan gani haka?allahu qadirun ala man yasha'u"ita abin ma dariya ya baiwa ummah yadda dady ke biye ma beauty uwa wani rak'umi da akala ganin da gaske sun haye sama sun barta tsaye bakin k'ofa yasa ta dawowa ciki ta nemi kujera ta xauna tana fad'in kuyi ku gama kwa iske ni nan"ba inda xan biku na tadda takaici"
Beauty kam bata zame ko ina ba se gaban wardrobe d'inta ta tsaya saurin rik'o hannunta dady yayi inda ta fincike da k'arfinta tana murgud'e baki tace"ni allah kar ka ce min wani abu se na bika baran zauna ni kad'ai se ummah a gida ba nasan ba fad'a ba wataran duka na zatai"cike da tashin hankali dady a karo na biyo ya k'ara kai hannunshi ga beauty ya rik'ota"
Murya can k'asa uwa me shirin kuka ta shiga bata baki"_beauty na ki yi hakuri ki banni na tafi ni kad'ai kinsan fa wannan ba personal tafiya bane balle nace zani da ke kuma duka-duka fa bazan wuce 1week ba,bqtun ummah kuma tun da naji maganar tafiyar nan na ja mata kunne sosai akan kar ta takura min ke,kinji ko ki dai na damuwa indan wannan ne"da alamun yarda da maganan daddy'beauty ta gyad'a kai tace are sure daddy kai mata fad'an?yes my daughter believe me nai mata"yanxu de gaya min me kike so na baki kafin na wuce"abin ne ma ya samu ga beauty washe baki tuni ta shiga yi nan ta fara zayyano buk'atunta wanda duk basu wuce kayan sakawa ba"nan daddy ya lalo kud'i himili guda ya aje mata wanda ita kanta se da kud'in ya firgitata don bata tab'a ganin dady ya bata kud'i masu yawa haka ba"wani wawan hugging ta kaima daddy cike da jin daddy tana fad'in thank yuh my amaxing dady yanxu kam xance maka safe journey"
Dariya sosai suke abinsu nan dai su kai sallama dady ya fito ya nufo falo nan ma dai jan kunne sosai ya k'ara ma ummah kafin tarakashi har mota suyi sallama cikin alhini da nuna tsantsar missing ma juna da haka sukai bankwana"ali driver ya tada mota se government house"
📓27 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
Tsaye take bakin window tana lek'en dady har ya fice kafin ta maida wata nannauyar ajiyar zuciya ta maido dubanta ga d'akin"gefen gado ta taka a hankali ta zauna tare da kai hannunta ga ajiyar da dady yayi mata ta janyo su ta shiga k'irgasu"ta k'arashe lissafasu had'e da kwarma wani uban ihu na farin ciki can kuma tai saurin toshe bakinta da hannu tana sak'awa arai"_kai ashe fa dady baya nan nake sakin wannan shewar kar na jama kaina fad'a"a fili kuwa ta furta N200,000 cab lallai yau akwai shiga mall bara na kira xee-xee"nan ta mik'a hannu a haka ta xaro waya ta shiga lalubar number xee-xee"k'ara biyu wayan ta saki kafin daga bisani xee-xee ta amsa wayan da fad'in kina wuta tawan"murmushi beauty ta fara saki sai kuma ta amsata itqma da kema haka k'awas yanxu de ba lokacin hira bane ki shirya bayan sallar la'asqr xanxo har gida na d'aukeki muje shopping dan haka se ki min text na address d'in gidanku" jimm xee-xee ta fara yi a farko dan sarai ta san halin gidansu da yadda mahaifinta yake gashi da xarar anyi sallar la'asar yake dawowa gida,in yazo yaga beauty a gidansu me xe ce don tana da tabbacin da irin shigar da beauty xata xo gidan nasu"toh amma ai mama na nan kuma nasan bazata hanani zuwa ba don haka ba damuwa"nan ta amsa wa beauty da toh se na ganki"sun d'an tab'a hira ba wani sosai ba da haka sukai sallama"
_Yammacin ranar:_
4:15p.m
Tsaye take bakin k'ofar d'aki rik'e da jakar hannu,jikinta kuwa ta zumbula wani dogon hijabi har k'asa"taji sallamar mama d'aki"wai har yanxu k'awar taki bata xo bane zainab?eh mama amma na kira ta tace min ta kusa tana hanya"toh gara dai kuyi sauri dan kina ganin lokaci yanxu gyaji sallamar mahaifinki" ya mutse fuska xee-xee tai tace wallahi mama nima abinda nake ta ji ma tsoro kenan nasan yanxu yana xuwa fitar nan ta fasu"kuma ze iya wulak'anta min k'awa ko ya koreta"saurin katseta mama tayi da inah yaushe xan bari haka ta faru ya korar miki k'awa ba ita ce wacce kike ban labari 'yar babban mutum nan ba?eh mama ita ce"toh kinga ko in zaki huld'a da 'ya'yan masu hannu da shuni a hankali mijin aurenki ma ta nan tsatson xe fito ke dai kawai ki bar min komi a hannuna bari naje na k'arasa wasu ayyuka a can d'aki na" toh xee-xee ta amsa da tai waje"
Zagayen d'aki kawai take tana duban agogo kamar daga sama taji k'arar horn na mota ai cikin sauri-sauri gudu-gudu ta fito a d'akin ta nufi wajen mama ta shaida mata ta k'araso"nan mama ta nuna mata tai sauri toh su wuce dai kafin baban nata ya dawo" da saurinta ta fito inda ta iske motar beauty kafe bakin gate d'in gidan nasu nan ta nufota"
Zaune take beauty cikin mota cikin wasu arnan kaya riga da skirt sai wata k'aramar hula data sak'ale kanta dashi"idannunta kafe a gidansu xee-xee nan ta shiga xancen xuci'gaskia ba laifi gidan yayi duk da dai unguwar lunguna sunyi mata yawa ga hayaniyar jama'a amma ade xaman gidan k'aramun ma'aikacin kwamnati ba laifi yayi k'ok'ari"tana cikin tunani taji an bud'e mota an shigo se a lokacin hankalinta ya dawo jikinta ta maida dubanta ga k'ofan"me zata gani?xee-xee murk'ushe cikin k'aton hijabi har k'asa" ai beauty bata san lokacin da dariya ta kwace mata ba ta nuna ta da yatsa tana fad'in me xan gani haka xee-xee kode kema kin koma matar malam ne?"cikin wasa xee-xee ta watso mata harara tana ci gaba da k'ok'arin yaye hijabin jikinta da yake motar me duhu ce tana fad'in banda lokacin ki ni dai yanxu yi sauri mu fita a layin nan koma meye kya tsokane ni dashi"batabar dariyar ba dai haka ta kunna motar tahau tuk'i'dai-dai kwanar hawa babban titi suka ci karo da baba cikin motarsa honda 307 yana k'okarin karyo kwana"
Na shiga uku"xee'xee ta fad'a tana b'oye kanta k'asa"me ya faru ne?ko kin manta na waje baya ganin na ciki?beauty ke tambayarta"se alokacin ma xee-xee ta tuna da hakan nan dai ta d'ago kai ala dole ta sha mur don kar beauty ta tsokaneta"tace ai na sani kawai de tsohon nan ne se a slow yanxu haka se kiji yace jikinsa ya basa ina cikin motar nan"na rasa me yasa sam ya kasa yarda dani"kome nawa se yasamin ido,ko shi haka akai masa da yana saurayi oho?itade dariya kawai beauty take har sukai nisa da unguwar sannan ta iya cewa dama dady ya auri mamanki se umma mu had'ata da baba suje suyi ta wa'axinsu mu kuma muna jin dad'in rayuwarmu koya kikace k'awas?dariya itama xee-xee ta saka tace ehh wallahi da mun huta da b'acin ransu duka"se de nasan baba ko ana muzuru ana shaho baxe saki mama ba kamar wanda akai wa asirin natau da ita"ke nima fa haka umma ke nanik'ewa dady na ko de su ustaxannan shigewa mutum suke? Xee-xee ta amsata da oho musu su suka san kayansu"har suka cimma shopping mall d'in nan hirar nan dai d'aya ita suke!
📓📓28 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
Katafaren kantin country mall dai-dai nan beauty ta tsayar da motarta tare da fitowa,haka xee-xee ta biyo bayanta,ciki suka shige abinsu nan suka shiga b'angaren kaya suka jidi kaya na axo a gani designers kala-kala don yawancin kayan komai kala d'aya suka d'auka abinda ya kama jaka da takalmi kai harda jewelries abindai ba'a cewa komi ranar kud'i ya sha kayi"ma'aikatan wajen su kansu beauty bata barsu a baya ba se datai musu kyakykyawar sallama bayan sun kawo mata kaya har mota"basu suka isa gida ba sai gab da sallar magrib inda ta sauke xee-xee a k'ofar gida,nan ta janyo hijabinta cikin jaka ta xumbula tare da janyo ledar kayanta ta nai ma beauty godiya ta fita har ta cimma gate beauty ta manna mata horn ta juyo bak'ar leda ta hau nuna mata dake ajeyi a bayan mota,hakan yasata dawowa tana fad'in kinga na manta kayan da kika ce a baiwa mama ko"nan ta karb'a tana mai k'arai mata godiya ta wuce"hakanan yasa itama beauty ta tada mota ta nufi gida"
Kamar yadda ta saba haka yau ma ta shiga gida mota sautin kid'a se tashi yake haka tai parkin a wajen aje motoci tare da manna horn da gudu mai gadi ya taho rik'e da buta a hannu ya xube gefen marfin motar,booth tq bud'e masa ba magana ya nufi wajen dan yasan aikinsa,da haka ta fito ta nufi cikin gida"falon shiru ba alamar motsin kowa hakan ya tabbatar mata da umma da ma'aikatan gidan kowa na wajen sallah sashenta ta nufa itama"murd'a hannun k'ofarta yayi dai-dai da fitowar ummah daga sashenta rik'e da caxbi tana laxumi"daga ina kike?tambayar data fito daga bakin ummah kenan"cikin sauri beauty ta juyo dan har ta tsorata da jin murya bayanta"tuni ta saita nutsuwarta ganin ummah tace shopping naje nayi" shopping??shopping fa kikace awannan lokacin?in har da gaske kike ina kayan da kika siyo"kafin beauty ta iya cewa wani abu baba me gadi ya hawo sama nik'i-nik'i da kaya cike bisa hannu"sanin ummah cewa dady ya d'aure wa beauty bayan rashin aiki se dai ma'aikata suyo yasa bata tanka mata akan hakanba"gaisheta baba me gadi yayi inda beauty jiki sanyaye ta shige d'akinta yabi bayanta"gefe guda ya aje mata kayan ya fice"
Sallah ta fara yi duk da dai cikin sauri aka kaita ana ta d'okin bud'e kaya"tana sallamewa ko addu'a bata samu damar yi ba ta doshi kayan"a hankali ta hau fiddo kayan tana k'are musu kallo"hannu ta kai ga wata doguwar riga kalar sky blue da ratsin bak'i ajikinsa ta d'aga ta sama tana k'are mata kallo se kuma can ta nisa tace tabbas wannan rigar dake xa'ai harka gobe tunda inaga muna da statistic kamar yadda na gani a time table se de kuma long slip ce" ta nisa kamar me tunanin wani abu se kuma ta basar kawai taci gaba da duban kayanta"k'ara wayanta ya shiga yi nan ta mik'a hannu ta d'akko a jaka"xee-xee kuma toh lapiya?tambayar datai kenan sannan ta d'auka"
Beauty dama mama ce tace na kira mata ke a waya"cewar xee-xee"ok toh wani abu de ko?eh godiya dama xatai miki gata ma kusa bari na bata"nan mama ta karb'i waya suka gaisa da beauty godiya ta inda ta shiga ba ta nan take fita ba har ta kai ta ga fad'in ai kullum in kina son rakiya unguwa zainab tana da cikakken lokaci kixo kuje"itade beauty toh shine kad'ai amsarta har sukai sallama mama na ta shi mata albarka kafin xee-xee ta amshi wayar su ci gaba da hira"bayan ta kashe wayar ne ta shiga gyaran kayan ta jere su a wardrobe bayab ta fitarda complete kayanda xata saka gobe a shiga *jami'a* d'aukar lecture!
📓📓29 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
💕
Zaune take bisa stool gaban madubi se shafe-shafe take da alamar fara'a ainun d'auke sama fuskarta"ta d'au lokaci tana ta kwalliya kamar me shirin xuwa wani party ko dinner"bayan ta gama ne ta nufi wajen kayan data aje saman gado ta janyo su ta saka kamar yadda ta ware su daga irin kayan data siyo a fitar su da xee-xee jiya"da kokawa da nishi doguwar rigar nan ta shige jikinta"se faman haki take kamar wacce ta sha wani aiki"rigar tsaf ta amshi jikinta sosai duk wasu sak'o da loko na jikinta ya bayyana matuk'a gashi tai mata cif-cif kamar an aunata"haka ta zura d'an kunne,tare da jaka da takalmi harda k'ara min veil duk black tunda rigar sky blue ce"ko da beauty takai kallonta ga madubi wani irin ihun jin dad'i ta saki don ita kanta tasan yau kam abin ba'a cewa komai"gefen gado ta k'arasa ta bud'e k'aramar drawer dake wajen ta ciro wata jotter me sak'ale da biro ta xura a jaka"sannan ta matsa gefe wajen ma'ajiyar tirare nan ma tai ruwansa ajikinta"kafin ta zari key na mota ta fito kunne dod'e da earpiece se kad'a kai take na jin dad'in yadda kid'in ke tsima ta" a falo suka had'e da ummah cikin sauri ta tsaida kid'an tare da gaisheta a ladabce"da fara'arta ummah ta amsa mata kafin ta nuna mata dinning table dake cike da kayan bud'e baki"fahimtar abinda ummah ke nufi beauty tai ba musu ta nufi wajen nan sukai karin kumallo" bayan ta gama tai ma ummah sallama ta fito"
Ko da beauty ta shigo jami'ar office din malam umar ta fara wucewa sai dai ina lokacin bai k'araso ba da yake safiya ce sosai dan ko 8:00a.m batai ba"dole ta hak'ura bayan ta tura masa sak'on yanemeta in yaxo da haka ta nufi venue d'in su na ranar"ta jima cikin mota zaune tana ta kallace-kallacen jama'a mai shiga dame fita se sak'a zancen zuci take"cikin waigenta ne idonta ya kai ga captain d'insu tuni ta wangale gilashin motar ta shiga kiran sunansa"meenu!meenu!
Da farko ameenu bai lura da kiran da take masa ba sai da wani d'alibi da suke tafiya tare ya ce masa wai ameenu ba sunanka nake jin 'yar jami'a na kira ba da yake kowa yasan beauty yadda ya kamata" hakan ya sashi mik'a ma d'alibin takaddunsa akan ya wuce masa dasu ciki kafin shi ya k'ara so"wajen beauty ya k'arasa nan suka gaisa sai kuma ta nisa tace haba meenu ka shigo mota mi magana mana xakai tsaye a waje"da farko ya d'an yi shiru kamar baxe shiga ba sai kuma ya xagaya ya bude motar ya shiga"
A nutse meenu ya d'ago kai ya dubeta yace toh ina jin ki wani abu ne?ita abin ma dariya ya bata se yayi ta wani mata magana sauri-sauri aduk sanda suka had'u besan yaga suna jimawa a hira"itama kallon nasa tayi cike da murmushi tace ba wani abu bane illah aikin da kaimin watannin baya yau ma shi za kai min"wane aiki kuma?cewar ameenu"sunan malamin da zai d'aukemu statistic nake son ji" wata ajiyar zuciya ya sauke na jin dad'i da Allah yasa ba wani abun zata sakashi ba don shi sam be son abinda zai had'ashi da ita musamman yanxu da kowa yasan wace ita a jama'iar"
Saukar lumfashinsa yaxo dai-dai da bata amsa"ehh toh nima dai bansan shiba amma dai dana tambayi wani tsohon lecturer anan yace d'alibai dai na kiransa sir prince but tak'amai-mai sunansa se ya shigo lecture zai fad'a mana don haka yake yi kafin ya fara darasi"jin-jina kai beauty tayi kamar me wani naxari tana k'ara maimaita sunan a zuciyarta"sir prince"sir prince" ina kuwa na tab'a jin sunan nan a baya?ina ne kuwa?kai bazan iya tunawa ba"may be ma shima na harka ne ban sani ba"
Ganin yadda ta duk'ufa da tunani ne yasa meenu ya d'an buga kujeranta yace zan iya tafiya ko?firgigit ta jiyo tana fadin yes meenu zaka iya tafiya nima ai yanxu xan shigo ka samamin seat kusa da kai bara naje na siyo orbit chewing gum a caferia"toh kawai ya amsa ta ya fice a motan ita ko ta tada mota ta nufi caferia"
A wani k'aramin kanti ta siyo shi tana k'okarin kunna mota kenan ta bar wajen taji ance adawo lapiya?saurin juyawa tqi taga wanda ke mata magana"murmushi ta saki ganin sir Mutallab tsaye a gefen motan ta"wanda yake d'aya daga cikin malaman department d'insu kuma na hannun dama a wajenta dan kuwa lokaci-xuwa lokaci sukan had'u" dole ta fito suka tsaya nan fa hira ta b'arke tsakaninsu har beauty ta manta da wani abu wai shi lecture!
📓📓30 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
Kimanin minti 30 beauty na tsaye da sir mutallab suna hira can ya nisa yace au kin ga kin sha'afantar da ni da dad'ad'an kalamanki ko? gashi kinsa nayi late a lecture da zan gabatar"sai a lokacin beauty ta tuna da ashe itama fa tana da lecture dole sukai sallama a gurguje ta hau mota ta nufi venue "wayam kake ganin wajen nan ba alamar mutane kowa ya shiga ciki hakan ya tabbatar mata da an fara lecture"motar xee-xee ta hango can gefe guda, haka ga kuma wasu motoci nan sunyi jeri a gefe d'aya"tsakiyar cikinsu inda yayi dai-dai da wata mota ash colour tasha wanki nan ta aje motan nata ta d'akko jakanta ta fito"
A bud'e ta samu k'ofan hakan yasa ta tura kai ciki ta shige"
Juye ta riske shi ya maida kai ga allo yana ta xuba uban rubuta d'alibai na kwafa"don haka bata jira wata-wata ba ta shiga taku cikin gadara ji kake kwas-kwas takalmi na k'ara"markern dake rik'e a hannunsa sir prince ya tsayar da rubutun tare da juyowa yana kallon ikon Allah"inda tuni hankalin beauty ita ko yayi nisa a neman meenu se can ta hangoshi saman theater ga wata mace a gefensa"sauri beauty ta shiga yi don taje tai mata masifa na ta zauna mata a waje"kamar daga sama taji ance"hey lady where are u going there?ba tamabayar ce ta bata mamaki ba sai dai muryar wanda ta ji"don tabbas ko a mafarki taji wannan voice d'in xata gane shi bare a fili"juyowa tai don k'ara gaskata abinda taji"kwatsam sukai ido hud'u da prince"kusan mutuwar tsaye tayi a gun shiko me zai yi prince in ba k'ara had'e fuska ba ya k'ara jefo mata wata tambayar"tell me about your wristwatch?banbara kwai taji tambayar aiko me xatai in ba k'udurta raina masa hankali ba nan ta gyara tsayuwarta sosai ta kai dubanta ga agogon dake sak'ale a hannunta ta shiga magana cikin izzah"wow my wristwatch ix unique and fashionable"as u guys normally call it one in town"& i'm quite sure small money inside a small pocket can't afford to handle it"tana kaiwa nan ta d'ago kai cike da murmushi saman fuskarta tana dubansa"me yarinyar nan take nufi ni talaka ne kome?wato ina tambayar ta lokaci shine zata juya min da haka aiko zata ga dixgi"xancen da prince ke nanata wa kenan arai"ganin yadda aji kowa ke jiran jin me xai ce ma ta"nan ya k'ara matse fuska tamau kamar be tab'a dariya ba sai kuma ya d'an saki murmushi na gefen fuska ya shiga kad'a marker dake dauke a hannunsa yana fad'in alright class let us solve a small work here before moving to our main topic of discussion"ido kowa ya bishi dashi ana kallon ikon Allah"a inda prince ya koma gefe da rubutun shi na farko yayi wani k'aramin arithmetic yace waze iya min solving"wani d'alibi a gaban seat ya d'aga hannu yace sir let me try"prince yace ok come and try"haka d'alibin ya taso ya karb'i markern a hannunsa ya shiga solving"bai d'auki wani lokaci sosai ba sai gashi ya gama ya fitar da amsa da yake d'alibin shi ke d'aukar overall a class din"yace sir na gama"duban board d'in prince yayi a nutse yaga tabbas abinda yake so ya gani yaron ya rubuta"nan yace ko zakai min bayanin yadda akai ka samo amsar"tiryan-tiryan d'alibin yayi bayani abin yayi matuk'ar burge prince nan ya kallo class yace alright class kun gane me yayi ko?class kowa ya d'auka da yes sir"in banda wata matashiya dake gefen dama gareshi wacce ta amsa da no sir"dama abinda yayi tsammani za'a samu me fad'a kenan dan yasamu yayi nasa bayanin nan kuwa ya kallo ta cike da samun karsashi a jiki yace ok lady let me repeat it clearly"gaban allo ya koma ya shiga nunawa yana bayani daya ke quadratic equation ne sai da ya gama bayani tsaf sai yace mata ko kinsan dalilin da yasa x=0 & y=10 nan ma dai ta kara bashi ansa da no sir sai yace toh bara nai miki example da hausa yadda xaki gane sauran aji ma su k'ara fahimta sosai dan nasan akwai wanda ko an bud'e brain d'insu an zuba karatu kan bazai d'auka ba"
📓📓31 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
💕
kallo ya k'ara kai wa sir prince ga sauran d'alibai dake zaune suna jiran cewarsa cikin sarrafaffiyar muryar nan tasa mai cike da kwarjini had'i da izzah haka ya fara magana" Hak'ik'a nin gaskiya ba ya cikin tsarin karatuna yin bayani da hausa don ya zama dole ne shiyasa yau zan mu ku,kun fahimce ni ko?sauran aji suka amsa da yes sir,sannan yaci gaba da magana"yana kai nuni da hannu izuwa ga allo"a duk lokacin da ku ka tashi lissafin irin wannan aiki toh ku d'auki x amatsayin mace mara kamun kai, ita kuma y amatsayin mace mai kamun kai"a yayin da x mara kamun kai ta gama zagayen ta na duniya zakuga ta tara kud'i masu d'umbin yawa (anan yayi nuni ga inda x ta samu maki100 a yanda calculation d'in ya nuna) ,har ta dunga jin cewa kamar ta fi kowa kud'i jama'ar gari kuma suyi ta bibiyarta don neman abun hannunta,har ta kai wata rana kwatsam sai a wayi gari wannan kud'in nata ya k'are a lokacin da zaton mutane bai kai ga haka ba"nan ya sauke hannunsa a inda rubutu ya nuna=0, ita kuma y mai kamun kai za kuga tana ta faman wahala a duniya( ya saita inda aka rubuta y=0) jama'a ko ta kanta basa bi don a tsammaninsu sam babu wata daraja a tattare da ita har sai an cimma gab'ar da zatai arziki alokacin ne jama'a zaka ji suna yabo gareta na k'iddige muku sai ta kai ta kawo wannan x d"in na bibiyar y don samun dacewar rayuwa"don haka jama'a wannan labari dai na san kun fahimce shi don nai muku shi dalla-dalla"bai kai ga rufe baki ba waje gaba d'aya ya d'auka da tafi ji kake raf-raf had'i da ihu kai har da shewa na jama'a,kowa na tofa albarkacin bakinsa akan wannan labari,beauty dake tsaye gaban desk k'afafunta sun kasa rik'eta ga wani matsanancin sarawa da take ji kan ta ya fara duk don wannan d'an iskan labarin da sir prince ya bayar ta san ba makawa labarin nan da ita yake"ganin tsayuwar baza tai mata ba ne yasa ta fara takawa a hankali tana dafe kai kamar wata 'yar giya ta nufo k'ofa dan barin theater d'in,tana takowa dai-dqi da inda yake tsaye nan ta d'ago fuska cikin zafin nama ta shiga k'ok'arin yin magana amma ta kasa sakamakon rad'ad'in da kanta ke mata"saurin duk'ar da kanta k'asa tayi sai ji tai kamar daga sama yana fad'in pls among u ladies someone should help her out kafin ta fad'i anan may be cough syrup ne ya fara mata aiki,ai ko kamar jira suke class suka d'orar da wani sabon ihun kafin kace me wajen ya karad'e da hayaniya,xee-xee da ke can saman theater cikin sauri tai k'arfin halin tasowa ta nufo wajenta nan ta rik'eta adaddafe har wajen mota, bud'e motar xee'xee tayi ta sanya ta ciki tana mai cewa zaki iya tuk'in ko kuwa?hannu beauty ta d'aga mata kawai da alamun ta bar ta haka ta koma ciki"ba dan taso ba haka xee'xee ta barta xuwa ciki don tasan halin beauty indai ta kafe a abu to abarta kawai"
Tunani sosai su kai ta ziyartar beauty ta sak'a wannan ta kunce wancan duniyar duk ta gama yi mata zafi,sam ta rasa me ke mata dad'i a duniyar nan ace wai yau har ita jama'a zasuyi ma ihu duk shaharar da tayi a haka zai k'are inaaa wallahi da sake hakan bazai tab'a faruwa da ni ba"duka takai wa sityarin motar tata da hannu kafin ta kunna motar cikin b'acin rai ta nufi gate ta bar makarantar!Bayan kimanin awa biyu da faruwar hakan ne sauran d'alibai suka fara tururuwar fitowa bayan da sir prince ya rufe karatunsa na ranar inda kowa ka ganshi labarin nan dai d'aya shi ake nanatawa na dizgin da akai wa 'yar jami'a da sanyin safiyar yau, shi ko prince wani dad'i ne ya lullub'e shi tun bayan fitar beauty daga theater d'in yasan ko ba komai yau burinsa ya fara cika akanta!
📓📓32 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
💕
Horn! Take ta faman yi amma ba taga alamar mutum a wajen ba"fitowa tai ta nufo gate d'in ta bude k'aramar k'ofar ta shige ciki tabar motar a nan waje,d'akin baba mai gadi ta nufa nan ta shiga yaye labulen k'ofar!me beauty zata gani? baba ne kwance saman tabarma sai faman gurnanin bacci yake abinsa daga gani kasan baccin nasa yayi nisa"dube-dube ta soma yi can ta hango buta a kusruwar d'akin,da saurinta ta k'ara sa wajen ta janyota,ruwa ne cike cikinta haka ta nufo baba"shaaaaaa kake ji ruwa na malala saman fuskarsa"firgigit baba mai gadi yayi ya mike zaune yana nanata kalmar shahada"cilli beauty tai da butar gefe sannan ta fice a d'akin tana gungunin cewa gobe ma ka sake baccin rana mu gani"bai iya cewa komai ba baba mai gadi illah cire kayan nasa ya sauya da wasu!
K'ofar falo ta murd'a a zuciye ta shiga da mamakinta sai ji tai an fincikota da k'arfi k'asa ta fad'i saman kafet ta inda ake shiga bata nan ake fita ba saukar duka take ji ta ko ina"kuka beauty ta shiga rerawa tun kana iya jin k'arar sautin kukan har ta daina"sosai ummah ta farfasa mata jiki"tana fad'in sakaryar banza da wofi,uban wa zaki kawowa raini a gidan nan? ko dan kinga ana zuba miki ido shiyasa ko?toh wallahi baki isa ba,baxaki sanadin shigata wuta ba,dan nasan alhakin tarbiyyarki na hannuna,bakya ganin kowa da gashi se ubanki ko?shi baba mai gadi sa'an ki ne?toh bari kiji daga yau har ran da uban naki zai dawo shima ya same ni duk na tanadar muku sai dai ki silar mutuwar aurena,amma tabbas ko kin k'i ko kin so sai ki kyaru"shasharar kawai"maganganun da ummah ke yi kenan tana ta haki inda su ko masu aiki ke zagaye da ita sai bata hak'uri suke"sam ummah bata bi ta kansu ba har sai da tayi dukkan don kanta ta gaji ta haye sama ta barsu anan,carko-carko sukai gaban beauty don ba damar lallashi"don sarai sunsan halin ta yanzu ta huce akansu"
Kuka beauty take yi wi-wi kamar an aiko mata da mutuwa haka tai mai isarta tayi shiru dan kanta,ko da ta tsagaita da kukan sai ta mik'e don falon shiru kake ji su kan su ma'aikatan sun koma bakin aikinsu,ta nufi sama,d'akinta ta bud'e ta shige"bata zame ko ina ba sai saman gado"ta fad'a nan ta ci gaba da kukanta har bacci yayi awon gaba da ita!can cikin bacci ta ji kamar ana tashinta"k'ara gyara kwanciyarta tayi sai taji an kai mata duka a k'afa cikin sauri ta bud'e ido"nan sukai ido hud'u da ummah"ina mukullin motarki?tambayar da ummah ta fara mata dashi ke nan" murya can ciki-ciki beauty ke fad'ar yana cikin motar"bata tanka ta ba ummah daga jin haka tayi waje"beauty na nan kwance ta ji alamar bud'ewar gate tare da shigowar mota"wanda hakan ya tabbatar mata da akwai abinda ummah ta shirya da hakan!duk da ciwo ga rad'ad'i da jikinta ke mata haka ta k'ok'arta ta mik'e ta shiga bayi tayo wanka" bayan ta fito tana zaune gaban mirrow tunani ya fad'o mata na jakarta da wayoyinta da ta bari a cikin mota"haka tai sauri-sauri ta shirya ta nufi hanyar fita daga d'akin har ta isa falo kenan tunaninta ya kai ga mukullin motar"jim beauty ta yi na wasu 'yan dak'ik'a kafin tayi k'arfn halin koma wa sama ta doshi sashen ummah!k'ofar d'akin ta murd'a a hankali ta shiga da sallamarta"ummah ta amsata kai duk'e ga wata jarida dake hannunta"hajara lafiya dai ko?ummah tace"cike da tsoro beauty ta amsata eh dama umma key na motana ina son d'aukar kayana aciki? Daga jin haka ummah ta d'ago ka tana dubanta tace Key na mota kuma?da munyi dake zan dawo miki da shi ne da har zaki biyo ni d'aki?shiru beauty tai cike da mamaki ta na jin ummah inda taci gaba da magana"eyyeh tambayar ki nake?toh wai da wace tsiyar kika aje a motar in banda wayoyinki da jaka?sukansu na karb'e ran da duk kikai hankali na baki"sannan kuma kina jina ko daga rana irin ta yau kar na sake ganin kin bai wa maaikata wanki sunyi miki"tunda kema macece kamae kowa dole ki koyi wanki don gidan wani zaki"kina jina ko?ido cike da hawaye beauty ta d'ago kai tana gyadawa da zummar ehh!k'ok'arin barin wajen beauty tayi ummah ta kira sunanta ta juyo"ina zaki kuma?ai ban gama da ke ba"don na fahimci zaman kad'aici ke saki koyon wasu munanan d'abi'un dan haka wuce can ga wuri ki zauna'tai mata nuni da kujera"jiki na kyarma haka beauty ta shigo d'akin ta nufi kujerar da ummah tai mata nuna ta zauna!
📓📓33 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
💕
Tun bayan fitowar sameer daga jami'a bai zame ko ina ba sai gidansu abokin nasa ameenu"kamar yadda ya saba"yau ma dai zaune ya tarar da ameenu rik'e da jarida yana bibiyar kanun labaran ciki"cike da farin ciki d'auke saman fuskarsa ya nufo shi"daga sallamarsa kad'ai zaka ji ka tabbatar da yanayin da yake ciki mai dad'i ne"ameenu ne ya katse shi da tambaya"gaskiya yau dai prince akwai magana bakinka ko? Murmushi sameer ya saki tare da jinjina kai da zummar haka ne kafin ya samu waje ya zauna ya maido kallonsa ga ameenu yana fad'in wato yau na ga ribar hak'uri"ribar hak'uri?na me kuma?ameenu ya tambaya,kasan fa abaya nayi niyyar bin duk wata hanya don naga na kori yarinyar nan a jami'a amma ka hanani toh yanzu maganar da nake yi maka tazo hannu don kuwa ni nake d'aukarsu statistic yau baka ga wulak'ancin da nai mata ba"
Baki bud'e cike da mamaki ameenu ke kallon sameer shima dai farin cikin yake da wannan labari na abokin nashi haka sameer ua ci gaba da zayyano masa duk kan abinda ya faru a jami'ar, yinin ranar gaba d'aya anan sameer yayi ta kamar yadda ya saba yi,wanda hirarsu ta yau bata wuce akan beauty bane,bayan sun dawo daga masallaci ne sameer yayi sallama da ameenu akan zai wuce gida har ameenu na tsokanarshi ko dai wajen wata zashi haka ya fake da tafiya gida da wuri don sanin kansa ne kullum basa rabuwa sai 9 koma fiye da haka na dare"haka nan dai su kai sallama shi dai sameer bai biye ta ciwarsa ba" ya nufi gida abinsa"
Kamar yadda ya sabayi kullum haka yau ma yayi, yana yin horn d'aya baba mai gadi ya fito ya bud'e masa gate,cike da girmamawa sameer ya gaishe shi kafin ya shigar da kan motarsa zuwa parking space na gidan"jakar aikinsa ya d'akko ya fito aciki ya rufe motar ya shiga waige-waigen gidan don yau ya ga sabon al'amari na rashin tashin kid'a daga sama kamar yadda ya saba ji kullum,se yaji gidan duk ya sauya masa"tambayar ko lafiya yake yi a zuciyarsa amma sanin cewa bazai samu amsar tamabayar tasa bane yasa shi sauke wata guntsuwa ajiyar zuciya tare da fad'in toh Allah yasa dai mutanen gidan yau lafiya suke da haka kuma ya nufi sashensa"
Wanka ya fara yi sannan ya d'auro alwala ya fito,nafilfilinsa na dare ya shiga jerawa ba shi ya gama ba sai wajen 10 saura,yana cikin addu'o'i ne yaji wayarsa ta fara k'ara,wanda ko dama abinda yake jira kenan,da saurinsa ya k'arasa ya d'auko wayar ya kara akunne cike da shauk'i yace sweet momy nah"daga d'ayan b'angaren ma aka amsashi da my prince"wani sassanyan murmushi sameer ya saki don ba abinda ya fi so kamar ya ji momy ta kirasa da my prince,cike da kulawa suka gaisa yana ta faman nuna yadda ya ke kewar momyn tasa itama haka don kuwa akwai shak'uwa mai k'arfi a tsakaninsu"bayan sun d'auki tsawon lokaci suna hira ne momy ke tambayar sameer akan lafiyar mutanen gidan"shiru ya biyo baya hakan ya baiwa momy damar sake tambayar nasa"nan ma dai ba amsa,sameer!momy ta kira sunansa"amsata yayi muryan nan k'asa-k'asa,sai tace ko dai ba lafiya bane sameer naji ina ta tambayar ka mutanen gidan amma kayi shiru"daga jin haka sameer bai b'oye wa momy komi ba tsakaninsa da su da mutsnen gidan akan yadda daddy ya hanasa ko da lek'owa harabar gidan "sosai momyn sameer tai mamakin abin don har tana nuna masa ko dai zai samu wani masaukin kawai in nan bai masa ba"nuna mata yayi babu komai zaman nasa da ya kusa zuwa k'arshe ,don a lokacin sameer bai wuce 'yan watanni ya gama bautar k'asarsa ba"ba don ta so hakan ba amma ya zatai da ra'ayin prince dole ta hak'ura ta bishi a haka"sun tab'a hita sosai kafin yayi sallama da ita ya kashe wayar"
Kayan bacci ya iya canjawa tare da gyara komai na d'akin yayi tsaf-tsaf don ya zaman to d'abi'a ta sameer kullum kafin ya kwanta sai ya gyara muhallinsa tun agida"bayan da ya gama ne ya rage wutar d'akin tare da bin lafiyar gado!"
📓📓34 *'YAR JAMI'A*📓📓
_BY_ *HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
💕
Misalin k'arfe bakwai na safe sameer tsaye yake gaban motarsa yana k'ok'arin bud'eta ya shiga ya ji kamar daga sama an kira sunansa da alamar manyance,saurin juyowa yayi cike da mamaki ya dawo da dubansa ga inda sautin kiran ke tashi,ido ya kai ga dattijuwar dake tsaye bakin k'ofar sanye cikin dogon hijabinta fari fat, tunani ya fad'o masa kan tabbas ko bai tambaya ba wannan ita ce hajiyar gidan,cikin sauri ya k'arasa har inda take ya russuna yana gaisheta kai a k'asa,sosai ummah ta ji dad'in yadda ya gaisheta'amsashi tayi kafin tai masa nuni daya mik'e tsaye"kasa mik'ewa sameer yayi se ma shiga susa k'eya da yayi yana fad'in ba damuwa hajiya nan ma yayi,murmushi ta k'ara saki wanda ke nuni da farin cikinta gareshi tace dama magana ce zamuyi amma kaje in ka dawo daga aikin sai muyi"toh kawai sameer ya amsata dashi da haka ya mik'e ya nufi mota ita kuma ummah ta shigo ciki"
Da yake daren jiya beauty na tare da ummah don a d'akin ta ma tai bacci sai ya zamana yau tashin wuri tayi,saboda tun kiran sallar farko ummah ta tasheta haka zalika bayan sun idar da sallah ta mik'a mata al'qur'ani nan beauty ta shiga karatun dole ba don taso hakan ba,har wajen shida na safe sannan ta rufe shi ta nufi gado ta kwanta"dawowar ummah cike ne ya batar damar komawa d'akin nata ta tashi beauty da tai d'ai-d'ai saman gado tana bacci"har a sakko daga gadon ba alamar motsi a leb'enta"hakan ya baiwa ummah damar kallonta cike da takaici tace ita addu'ar tashi daga baccin ni zan tofa miki ko kuwa ya akai?cikin mawuyacin yanayi beauty ta ji tambayar"ita mamaki abin ya bata yanzu ace har da wata addu'ar tashi daga bacci"amma gudun fad'an ummah hakan yasa tilas badan taso ba ta hau mutsu-mutsu da bakinta kai kace da gaske adduar take har ta bar d'akin"
Ba ita ta gama shirin taba sai kusan tara na safe sai gata ta fito cikin wasu matsatstsun kaya riga da wando wacce rigar bata wuce gwiwa ba"sai wani yalelan gyale da ta rufe kanta dashi wanda dashi da babu duk d'aya ne"ko takan breakfast bata bi ba don yanzu duk abinda zau had'ata da ummah bata so don ko jakar makarantar yau wata sabuwar ta d'akko,sand'a ta shiga yi a hankali har ta sakko daga sama ta kai bakin k'ofar fita daga falo kenan ta tuna da key na motar da ke wajen ummah"dafe kai beauty tai kamar zatai kuka don takaici amma ya ta iya dole hakan zata koma"kallo ta fara kaiwa ga suturar dake jikinta tasan tabbas ta je wa ummah da wannan shigar baza su rabu ta dad'in rai ba"shiru tayi kamar me nazarin wani abu se can dabara ta fad'o mata"yes!yes ta fad'a cike da murna cikin sauri ta haye sama ta nufi sashenta" drawer d'in ta na kaya ta bud'e ta shiga lalube"tsohuwar ajiyar da tafi shekara uku a ajiye ta janyo wani dogon hijab da tun zuwan daddy dubai ya siyo mata akan tana sallah dashi ta d'akko cikin murna da wannan shawara data samo ta saka shi cike da yiwa kanta dariyar abinda tayi ta nufi wajen ummah!!
35 *'YAR JAMI'A*
_BY_ *HERWWERH~JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS'QUE~DEE*
💕
Beauty cikin nutsuwa ta tura k'ofar d'akin ummah ta shigo,zaune ta tarar da ita saman kujera hannunta rik'e da remote tana k'ok'arin sanya channel d'in MBC 4,ciki-ciki kamar mai koyon magana beauty ta shiga tambayanta key,banza tai da ita kamar ummah bata san da mutum a wajen ba har sai da beauty ta k'ara nanatawa sannan ta d'ago fuska a dak'ile ta k'are mata kallo tas,tai mamakin yadda taga shigar 'yarta ta yau amma a hakan ta cije ta b'oye narkakken farin cikin dake kwance saman zuciyarta na ganinta haka, tace gashi can saman madubi wuce ki d'auka,gefe kuma ga wayar ki can ki d'auki babbar ki anfani da ita kuma da zarar kin dawo ki maido min key d'in nan!toh kawai beauty ta iya cewa jiki na rawa ta d'akko su ta fito had'i da janyo mata k'ofa ta rufo,tana fad'in yes!yes!!cike da murna beauty ta sakko ta nufo waje!A gaban motar beauty ta cire hijab d'in ta bud'e ta wullashi ciki,kallon motar ta sake yi,sosai motar tayi kyau yadda taga an wanke ta sosai ta fita"haka ta shiga yau kam ba yabo ba fallasa gaisawarsu da baba mai gadi bayan sallamar kullum ta kud'i da tai masa"ta wuce abinta sai makaranta"!
Da yake batayi wani breakfast ba ta fito dole tana shigowa ciki ta wuce STOP & CHOP,shiru wajen yau yake tunda safiya ce sai ma'aikata da suke ta faman kai kawo suna gyaran wajen"da shigarta kowa ya yo kanta suna kwasar gaisuwa,meenu kamar yadda take kiran yaron nata na wajen haka ta kirashi bayan ta zauna ta zayyana masa abinda take buk'ata ba'a d'auki wani lokaci mai tsawo ba sai ga shi ya dawo cike da kayan abinci da na sha haka ya jere mata su gabanta beauty ta shiga ci hankali a kwance"bayan data gama ne tana k'ok'arin fita daga wajen bayan da su kai mata total na duk abincin da su kai na ranar ta biya su kud'in da zummar ayi yadda aka saba na raba wa d'alibai da sunanta"wasu mata ta gani su hud'u kana ganinsu kaga rik'ank'un mata masu zaman kansu"don lalatattun shigar dake jikinsu kad'ai ya gama fassarasu"takowa su kai suka shigo har gaban beauty sannan ko wacce ta ja kujera ta zauna"!
*'Yar Jami'a*!!sunan da d'aya daga cikin matasan kenan ta kira beauty dashi wanda hakan ke nuna itace gaba da su"
Ya mutse fuska beauty tayi tana kallonta kafin ta amsa mata da lafiya dai ko?ki ke kiran sunana da sanyin safiyar nan??
K'ara gyara zama sosai matashiyar tayi saman kujerar ta fuskanto beauty sosai sannan ta hau magana" A gaskiya wato kin gane kina d'aya daga cikin matan da muke yawan jin labaranki daga maza kai har da mata na jam'ar nan akan yadda kike rayuwarki cikin jin dad'i da gogewa"sai muka ga abin ya burge mu shine muka yi tattakihar cikin makarantar nan don samun damar ganinki,amma ko da muka nemeki sai aka shaida mana baki shigo ba sai dai aka nuna mana aminiyarki"ita ta shaida mana kina nan"toh agaskiya dai 'yar jami'a duk da ban san ya zaki karb'i abun ba amma mun zo miki ne da tayin wani babban rabo"wanda muke ganin zaki iya"wannan abin ba komai bane illah muna so ki shigo cikin k'ungiyarmu wanda take da reshe da yawa a sassan jahar nan,muna so ki zama cikin ta biyar agaremu,kinga taron sati da za'ai a gidan uwar d'aki sai mu gabatar dake"yanzu dai tare dani wannan ta hannun damar tawa sunanta nusaiba amma anfi kiranta da nusy,wannan kuwa ta gefen hagun sunanta shamsiyya wato shamsy kenan!sai kuma ta gefenta surayya ko kice sury daga haka sai ni mai gayya mai aiki miss lollipop wato lawiza"bata kai ga aje numfashinta ba lawiza kamar yadda ta fad'i sunanta beauty ta katse mata hanzari da hannu tana fad'in toh kin gama?caraf sury ta amshe maganar don taga kamar beauty baza tai na'am da buk'atar su ba"tace ehmm kina jiko 'yar jami'a ba wai muna nufin da ordinary men fa zaki na harka ba nooo!ba haka bane manyan Alhazawan k'asar nan ba ma jaha ba duk namu ne sai wanda kika zab'a in ma kince ba da maza zaki harka ba, suma matan akwai su kala-kala(wa'iyazubillah)sai kin zab'a kin darje,ta k'arashe maganar surry tana wani kashe wa beauty ido d'aya!kafin beauty ta samu damar yin magana har shamsy dake can gefe ta ciro wani k'aramin kati mai d'auke da suna har da lambobin waya ta aje gaban beauty"tace kar ki saurin yanke hukunci ki je ki nazari,wannan lambobin mu ne,don haka sai mun ji daga gareki,muna fatan kuma baza ki bamu kunya ba!mik'ewa sukai a tare suka fice"ido kad'ai beauty ta iya binsu dashi wai gaba da gabanta aljani ya taka wuta"yanda beauty ke ta faman had'a zufa ze tabbatar maka da shigar sabon abu cikin kwakwalwarta"a sannu ta kai hannu kan katin ta d'akko shi a hankali ta shiga juyasa a hannu!toh wad'annan mutanen me suke nufi da hakan? Na fara mu'a mala da wasu mazaje a waje ko me??? Wannan itace tamabayar da take ta faman kaikawo a kan beauty!
36 *'YAR JAMI'A*
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
💕
Cike da matsananciyar damuwa d'auke saman fuskar beauty haka ta daddafa ta fito daga cikin stop & chop sallamar da take musu in zata fita yau ko ita basu samu ba"mota ta nufa ta zauna tare da d'aura kanta saman sityarin motar"muna fatan kuma bazaki bamu kunya ba?"wannan maganar ta shamsy itace take ta faman kai komo a zuciyar beauty"A zahirin gaskiya bazan so ni kai na na baku kunya ba,kuma bazan so wannan damar ta wuce ni ba ta k'ara shiga cikin wasu wayayyun mutanen"toh amma ai babu wannan tsarin a cikin file d'ina hasali ma ban tsara wannan rayuwar ta zama abin dawwama a gareni ba,sai gashi yau kwatsam kun shigo min rayuwa da wani sabon abu mara misaltuwa"yanzu meye mafita???yanda ta lula kogon tunani beauty ba kama hannun yaro,fahimtar daga k'arshe baza ta samu wata mafita bane yasanya ta dole ta hak'ura akan in ta koma gida ta yanke shawara".motar ta kunna tare da sakin sauti ta nufi lecture hall d'insu na ranar"duk da an kusa cimma k'arshe lecturen haka beauty ta banka musu ciki tsagal-tsagal ba ko kunyar suturar jikinta,kallo ta kai ga lecturern da yake tsaye rik'e da wata k'aramar takadda a hannunsa yana bayani tace morning sir,tana maganar ne a sa'ilin da duk wata gab'a ta jikinta ke motsi"tana wani kwarkwasa kamar mai shirin b'allewa"washe baki lecturern ya shiga yi da ganinta tuni ya taho yana mai laluben biro a aljihunsa yace ina kika shiga tun d'azu 'yar albarka gashi har anyi attendance?abinci naje ci! Ok toh ai ba damuwa dama shi gane karatu ai sai ciki ya k'oshi maza amshi sa sunanki daga k'asa!ba musu beauty ta k'arba ta rattaba sunanta ta mik'a masa tare da sakar masa wata kasalalliyar dariya tace"thank you sir,gaba d'aya theater tayi tsit ko wane d'alibi da d'aliba zaune suke suna kallon ikon Allah,ace duk irin zafi na malamin nan da rashin yarda a shigo masa bayan ya shigo yau shi har yake lallab'a wata"a gaskiya 'yar jami'a ta cika shu'umar kanta!cike da fara'arta ta mik'a masa takardar had'e da bironsa ta haye sama"har tayi kamar zata shige can sama sosai ta hango mace da hijabi gefenta babu kowa!da saurinta ta k'arasa wajen ta zauna"satar kallon yarinyar dake zaune gefenta tayi"ta tabbatar da farin hijabin dake sanye jikinta"leb'enta na sama ta shiga ciza da hak'oranta kafin ta janyo wayarta daga jaka ta shiga wajen aika sak'o"
I need red pen!!
Sak'on da ta rubuta kenan tare da lalubo lambar xee-xee ta aika mata"
Xee-xee na zaune taji alamar shigowar sak'o da kamar baza ta d'auka ba don tasan halin MTN da turo sak'o kamar ka sa su!can kuma wata zuciyar ta bata ta duba haka ta bud'e ta karanta"cikin ikon Allah kuwa tana da shi haka ta nad'e jan biro a tissue ta bayar ma ta gefenta ta mik'a wa beauty!murmushi ta saki bayan ta amsa!taci gaba da latsa waya abinta tana game yayinda ko wane d'alibi yayi nisa cikin rubutu saboda dictation yake musu"lura da shagaltuwa da su kai hakan ya baiwa beauty damar d'akko biron nan a hankali ta bude shi,nan ta shiga hura ink d'in biron a hankali yana d'iga jikin tissue d'in har ya k'are"haka ta kaikaici idon mutane ta wullar ya zama saura tissue hannunta"hannu ta zura ta baya ta dai-daici k'asan farar hijab d'in baiwar Allah nan ta shiga goga mata shi a hankali,sai da ta tabbatar da gaba d'aya k'asan hijabin ya gama b'aci da jan biro sannan ta dawo da hannunta a hankali ciki ta cukuikuya tissue d'in ta wullar k'asan seat!
Karatu ake sosai ba alamar shirin tashi gashi duk ta k'agu tabar wajen dole ta d'aga hannu tace excuse me sir!"kamar jira yake daga can k'asa inda yake tsaye yana koyarwa yace yes go ahead!narkar da murya beauty tayi"duk wani kalar tausayi ya bayyana fuskarta tace"ciwon kai nane ya tashi please sir kai min izini wannan baiwar Allah ta rakani zuwa mota na tafi gida bazan iya zuwa ni kad'ai ba"cikin hard'ewar murya yake amsata da toh kuje ai ba komai Allah ya k'ara lafiya!
37 *'YAR JAMI'A*
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
💕
Badan ta so ba haka d'alibar ta kama beauty dake dafe da kai tana cuskune fuska ita ala dole mara lafiya!da taimakonta haka suka shiga sauka daga matattakalar wajen suka nufo k'asa!huuuuuuu huuu!!! Shewar maza kenan da kake ji tana tasowa daga can saman theater! Kafin kace tak gaba d'aya wajen ya cike da hayaniya"tun lecturern yana buga tebur d'in gabansa yana tsawatar musu har ya kai ga abin ya k'ufular da shi,yayi shiru ya zuba wa sarautar Allah ido,har beauty suka cimma bakin k'ofar fita gaba d'aya hankalin d'alibar bai kai akan su ake wa dariya ba,sai da suka k'araso kofa sai karaf idon lecturern nan ya kai ga hijabin jikin d'alibar yaga duk ya gama b'aci da jini wannan ne ya k'ara tabbatar dashi cewa shine abinda yasa mazan nan dariya"duk sai yaji wani iri don ganin kamilar mace abu irin wannan ya sameta a bainar jama'a!gashi d'aliban mata suna son sanar da ita amma babu hali sakamakon d'abi'ar lecturern da indai an fita toh babu dawowa ciki"dole yasa suka hak'ura,amma abin suma bai musu dad'i ba don ciwon mace na 'ya mace ne"
Cika min jiki dilla shashasha"!abinda ya fito kenan daga bakin beauty inda a lokaci guda kuma take k'ok'arin raba jikinta dana d'alibar"cikin rashin fahimta d'alibar ke kallonta don ko ba komai ai ta gode mata da taimakon da tai mata bata saka mata da zagi ba"kafin ta kai k'arshen tunanin nata taji an finciko ta da karfi har tana kai tuntub'e kan k'aramin dutsen dake gabanta,beauty ta shiga jijjiga mata dogon hijabin dake jikinta tana fad'in!ustazu uwar imani!kina gaba maza na bin ki a baya suna yabo!wai ke 'yar gidan malam me dogon carbi ko? Toh yau naga abin so a jikinki,ko an gaya miki ana ja da 'yar jami'a da zaki saka malami ya wulak'anta ni gaban aji wancan satin wai har kina ikirarin baki gane calculation d'in kan allo ba ko?toh tunda baki gane wancan ba ai nasan zaki gane wanda ke bayan hijab d'in ki ko?tana kaiwa nan beauty ta cika mata hijabin nata ta bita da wani banzan kallo!mai cike da jin dad'i"duk da har yanzu d'alibar bata gama fahimtar kalaman beauty ba amma jin ta ambaci hijabi, haka ya baya damar shiga laluben jikinta cikin sauri, gaban hijab d'in ta fara kaima kallo taga tsaf yake hakan yasa ta juya bayansa!
Kasa yarda da abinda idanunta suka nuna mata tayi!jan abu ta gani gaba d'aya ya gama b'ata mata farar hijab d'inta"bata ankara ba taji kamar daga sama ana magana!hak'ik'a wannan shine sakayyar duk wanda yace zai shiga harkata"yanzu kinga sai ki koma cikin theater maza su ci gaba da miki dariya ko kuma ki nufi toilet kafin ki je can kuma mazan makaranta sun gama shan kallo"sai ki zab'i d'aya"
Cike da muguwar dariya beauty ta k'arashe maganar tana watsa hannaye sama ta wuce zuwa motarta!
Wasu irin zafafan hawaye ne suka fara kwaranya a fuskar d'alibar wanda ita kanta ta rasa dalilin hakan"durk'ushewa tai k'asa ta shiga rera wani sabon kuka tana tariyo abinda ya faru yanzu na yadda maza ke shewa suna ihu da ganinta haka!yanzu ina zata?tunanin daya fara kawo mata kenan,ta jima tana tunanin mafita sai kuma can dabarar kama wajen ta rike da hannu ta yadda zai b'oye jan dake wajen ya zo mata"haka kuwa akayi ta kama bayan hijab ta rik'e ra nufi bayi ta cire sannan ta nemi taimakon wata d'aliba data shiga masallaci ta d'akko mata hijab dake rataye na sallah ta saka"bayan data gama gyara jikin tane batai wata-wata ba ta fice daga jami'ar duk wani karatunta na ranar haka ta rasa shi!
38 *'YAR JAMI'A*
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
💕
_Luv is so sweet when u meet the right person to show it out yeeeee! Oh yeeee!_
Wak'ar da beauty ke rerawa hankali kwance kenan cikin mota,hannu ta kai ga jakarta ta zaro wani k'aramin dairy nata,wani shafi mai cike da Manyan rubuta ta bud'e nan da nan ta kai hannunta ga wata da'ira da akai a wani k'aramin akwati da aka zana tayi tick aciki!alamun yiyuwa na cimma wani abu!bayan da ta gama ne ta kalli agogon hannunta taga har lokacin 12:00p.m ba tayi ba!Tsaki ta saki had'i da kunna motar tata, ta sureta da gudu kamar mai shirin tashi sama tai hanyar fita daga jami'ar!anan ne ta gamu da wani malami wanda ya d'auke su a zangon karatunsu na farko,wanda shima ba laifi d'an harka ne don ko ba komai ya bata marking da ta gamsu dashi"hakan yasa ya haska mata fitila itama ta haska masa na alamun dakatawa"waje ya samu gefe yayi parking itama ta samu tayi sannan ta fito tayo wajensa"da yake motar tasa itama bak'in gilashi ne haka ya bud'e mata motar ta shige ciki ta zauna!gaisawa sukayi tare da maida bayan saduwa"sun d'au lokaci mai tsawo suna hira abinsa kai kace don ita ya shigo"daga bisani ta nemi tafiya amma sam yak'i bari ta tafi,sai ma shiga bata wasu labaran yayi masu matuk'ar tasiri a zuk'ata"
kwan! kwan! kwan!k'arar bugun gilas kenan suka ji daga b'angarensa,ba tare da nuna alamar damuwa ba"ya kalle ta ya sakar mata wani kasalallen murmushi itama ta watso masa sannan ya iya sauke gilas d'in motar k'asa".
Baki bud'e har kana iya hakaito hasken fararen hak'oransa ya ji ance c'mon! malam bani laptop d'ina da aikin da zanyi da ita ka barni ina jira ka taho nan wajen......kalaman sameer kenan wanda bai kai ga k'arashe su ba idanunsa suka sauka ga macen dake gefen kujera zaune,wanda itama dai daga b'angaren nata shi take kallo"dimmm lokaci guda suka ji wani irin matsananciyar bugawar zuciya"kasa danne yanayin da yake ciki sameer yayi dole ya katse maganarsa ta farko ya fito da yatsa waje ya shiga nuna beauty yana fad'in"me wannan yarinyar take maka a mota kamal?d'auke da wata siririyar dariya saman fuskarsa malamin wanda aka kira da kamal ya kai duba a karo na biyu ga beauty kafin ya juyi gareshi yace wai wannan?ehhh ita!!sameer ya bashi amsa a tak'aice"ko da yake ka gane ba na buk'atar ma na sani don nasan abinda ya kori shaho daga shek'a bazai wuce yunwa ba!bani laptop d'ina na wuce"cikin fushi kake jin zafafan kalaman sameer na tashi!da yake yasan halin mutumin nasa kamal don ko suna office wani lokacin in ya d'au zafi ba mai iya masa sai in don kansa ya saki!haka ya mik'a hannu kujerar baya na motar ya janyo jakar laptop d'in ba uhmm balle um'um ya mik'a masa"karb'a sameer yayi duk da haka cikin fushi ya sunkuyo da kai cikin glass d'in yana kallonta yace wallahi i hate u to the extend level baki da hali,baki da hali banza mara kamun kai"!bai jira cewar su ba ya sa kai yayi gaba"
kamar a mafarki haka beauty ke jin kalaman sameer na dokar kunnuwanta"duk wasu k'ofofin tunaninta sun riga sun kulle ruf,k'afe ido tai ga sararin wajen da sameer ya bari tamkar mai wani nazari,can kuma sai ji tai ta saki wani irin k'aramin yak'e wanda ya fi kuka ciwo,bata jira jin wani abu daga bakin kamal ba, ta bud'e k'ofar tana shirin fita,cikin sauri kamal ya rik'o hannunta yana fad'in please dear wait ki ji wani abu"cikin zafin nama beauty tai wurgi da hannunsa gefe ta fito da sauri daga motar ta nufo tata"a fusace haka ta fad'a cikin motar kamar wacce hankali yabar jikinta haka ta finciki motar tayi waje!
39 *'YAR JAMI'A*
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
💕
Zaune yake cikin office d'insu da alama aiki yayi masa yawa yadda ya duk'ufa sosai akan laptop d'insa dake ajiye saman tebur d'in gabansa yaji an turo k'ofa,sam bai damu da sannin wanda ya shigo ba don kuwa su uku ke zaman office d'in,sallama yayi kamal yayi sannan ya shigo ciki,kujerar dake kallon ta sameer ya zauna yana d'an gyad'a k'afa,alamun daya gani daga sameer na bashi da niyyar kulasa ne yasa shi k'ara gyara zamansa yace"amma dai kaji shigowa ta ko?eh kuma na amsa maka sallama ba!sameer yayi maganar kansa na sunkuye a laptop!murmushin k'arfin hali kamal ya saki sannan yaci gaba da maganarsa"wai shin kuwa sameer ina kasan 'yar jami'a naga tun da ka ganta d'azu tare da ni duk ka sauya gashi kamar ni d'in ma fushi kake dani!
Banza sameer yayi da shi tamkar bai ji me ya ce ba har na kusan minti uku sannan ya d'ago raunanan idanunsa da tuni sun gama k'ank'ancewa saboda gajiyar aiki ya sauke su saman nashi"malam aiki fa nake ka zo zaka dameni,ina ruwa na da kai da ita,tunda kai ma ka zama mai biye ma shashashan mata ai se kaje kai tayi,kar fa ka manta tare muka zo aikin bautar k'asa jami'ar nan kuma ni baka ga ina biye musu ba toh ni ma kenan dana tashi cikin hausawa,nasan illar abin ina ga kai daka tashi a birnin kudu,ya ci ace yanzu kasan me kake,basai an gaya maka ba,amma fa shawara ce bazan hanaka jin dad'inka ba sai dai ka sani yarinyar dana ganka d'azu da ita tun ran da na fara zuwa jami'ar nan na fara had'uwa da ita duk da bata gane ni a lokacin ba amma ni na ganeta saboda mummunar shigar dake sanye jikinta"don haka ina shawartarka please kaje kai dukkan abinda kake so amma ka rabu da wannan yarinyar wallahi bata da tarbiyya!cikin wani irin mawuyacin hali da yanayi sameer ke magana,kana ganinshi zaka fahimci tabbas duk kan abinda yake magana akanshi ba mai dad'i bane!
Ba don kamal ya ji maganar abokin nasa ba amma ya zai yi dole ya nuna masa ya gane komai kuma zai gyara da haka suka rabu kamal ya koma tebur d'insa ya fara aiki shima sameer ya d'ora daga inda ya tsaya!
****
Misalin k'arfe hud'u na yamma 4:00p.m, kenan a agogon dake sak'ale a hannun sameer"ajiyar zuciya ya saki lura da yadda lokaci ya tafi haka"kafin daga bisani ya had'a kayansa ya fito,a harabar office d'in nasu yaga an had'a jam'i ana k'ok'ari tada sallah haka ya aje kayansa gefe yabi jam'i sannan ya shigo motarsa ya fito daga jami'ar!
Tafiya yake hankali kwance har ya kai ga kwanar da zata sada shi zuwa gidan aminin nasa ameenu kamar yadda ya saba wuce wa can kullum sai kuma dare ya koma gida"maganar ummah ce ta fad'o masa na cewa bayan ya tashi daga aiki zasuyi magana"dole ya juyar da kan motar tasa sanin cewa in bai je lokacin ba dare zai zamanto dare yayi nisa watak'il ma tayi bacci a sa'ilin,haka ya d'auki hanya sai gida!
Horn biyu yayi baba mai gadi ya fito don ganin wane ne da mamaki sai yaga motar sameer!har ya bud'e masa gate suka gaisa ya shigo gaba d'aya baba mai gadi mamaki bai sake shi ba!tunani ya shiga yi Allah yasa dai lafiya ya dawo yau da wuri!ko da sameer yayi parking haka ya fito ya k'ara gyara zaman darkblue suit dake sanye jikinsa"sannan ya zura phones nashi a aljihu ya nufi hanyar shiga babban falo!
Assalamu alaikum!Assalamu alaikum! Sallamar da sameer yake yi kenan amma da alama babu motsin kowa a falon"ganin ya d'au lokaci tsaye ya sashi yanke shawarar ya wuce d'akinsa kawai zuwa an jima sai ya dawo"ya yunk'ura kenan zai juya yaji an bud'e k'ofar!dawo da kallonsa yayi wajen,inda hakan yayi dai-dai ga kallon ummah gareshi tace"aufff ashe kai ne? Eh ummah! Ina yini!cike da girmamawa sameer ke gaisheta!haka ummah ta amsa masa da lafiya lau!sannan tayi masa iso da ya k'ara so ciki! Cikin nutsuwa sameer ke bin bayan ummah har suka k'arasa cikin falon, kujera tai masa nuni da ya zauna!
K'ara gaisawa sukai kafin ummah ta umarci akawo masa abin tab'a wa baki!
Duk da ba wani iya cin komai yayi ba don sameer bai saba da cin abinci gaban mutane ba"in ba dole ba, musamman ma yau da ya kasance gaban ummah!haka ya aje juice cup d'in dake rik'e a hannunsa a centre table"ya d'ago kai yana kallonta da alamar son jin wani abu daga gareta"matsakaicin murmushi ummah ta saki sannan tayi gyaran murya tace!
D'azu nace in ka dawo kazo ina nemanka"saboda a ganina yaci ace kawo yanzu nasan da wane irin mutumi muke zaune a cikin gidan nan!jinjina kai sameer yayi da nuna gamsuwa da furucin ummah!sunkuyar da kai k'asa yayi sannan ya fara motsa leb'ensa!
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: *'YAR JAMI'A*
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
40-45
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Ni dai sunana.......pinn pinn...k'arar wayar ummah kenan da ta fara ruri a lakacin wanda hakan ya ba sameer damar tsayawa don ta amsa wayar!hannu takai ummah ga wayar dake aje gefenta ta janyota!ta duba sunan wacce ta kira"yagana kuma?ba d'azu muka gama waya ba?ganin kiran yana daf da katsewa yasa ta tayi saurin d'aga kiran ta kara a kunne!k'ara gaisawa su kai amma duk yanayin da ta tsinceta tabbas a lamar tambaya!lafiya dai ko? Jimmm yagana tayi na wasu 'yan lokaci sannan ta nisa tace jikin malam ne ya k'ara tashi yanzu gashi babu wani babba a gida sai ni kad'ai!innalillahi wa innah ilaihirraji'un"toh yanzu yana ina?ummah tayi tambayar,gashi nan a gida na jik'a masa saiwa yasha ya d'an samu bacci!sosai jikin ummah yayi sanyi da jin rashin lafiyar mahaifinta,cikin k'arfin hali tace mata yanzu gashi baya gari kuma waya dashi sai dai cikin dare don aiki yawa yake musu,amma zan gani zuwa anjima duk yanda na yanke zan kira!toh yagana ta amsa dashi kafin nan sukayi sallama t ma kashe wayar!
A sulale wayar tabi jikin ummah ta sauka kan cinyarta inda tuni ruwan hawaye ya gama cika idon ummah"damuwa tsagwaronta kake gani d'auke saman fuskarta"yanayin da ta shiga yasa sameer bin ta da kallo a hankali ya iya furta,lafiya dai ko ummah?sam hankalin ummah ya gushe a kanshi har sai da ya k'ara nanatawa,sannan ta juyo guntun hawayen dake mak'ale a fuskarta suka gangaro,a rud'e sameer ke fad'in"subhanallahi dan Allah ummah menene ke faruwa?naga daga d'aukar wayarki haka ta faru ko dai anyi rashi ne,girgiza kanta ummah tayi sannan ta share hawayen nata ta d'ago kai a dak'uke tana kallonsa,can kum tace ba'ai rashi ko d'aya ba sameer k'anwar mahaifiyata ce ta kirani akan rashin lafiyar mahaifina;yanzu haka yana can kwance jikin ya k'ara tashi kuma ba kowa a wajensa sai ita sa yake mahaifiyata ta rasu,kuma dangin namu mazan ba masu d'aukar zumunci da wani abu bane,shiyasa kaga duk na damu,in dama ace daddyn hajara na nan da da sauk'i zan iya tambayarsa gobe na shirya naje,toh baya nan ita kuma waccen shashashar yaushe zan tura ta jinya,ita da ko hankali bata cika ba,!dafe kanta unmah tayi don wani irin sarawa da taji yayi kamar zai bar jikinta hakan yasa sameer saurin fad'in ya isa haka ummah ki daina damuwa kar kema wani abun ya sameki,yanzu shi yana ina da zama?yana nan kano cikin local government d'in minjibir!minjibir?sameer ya nanata sunan wajen,a gaskiya ummah bansan wajen ba amma in bazaki damu ba ni ki wakiltani indai kinga ba wani abu sai naje ni!da sauri ummah ta d'ago kai tana kallonsa!ajiyar zuciya ya sauke yace eh ummah ni zanje in har kin amince min sai ai mun kwatance!toh sameer Kar na takura maka aikin naka fa?haba umma karki damu da wannan zan sanar kuma ko bana nan akwai masu tallafa min don haka ki kwantar da hankalinki,toh shike nan hakan yayi na gode amma kaga da waccen malalaciyar zata iya ai da kun tafi tare tunda ta san wajen ba sai ka wahala ba!yamutsa fuska sameer ya d'an yi jin an ambaci mace yace wace kuma ummah?hajara mana,kai dai Kawai Allah ya sawak'e ma wannan yarinya wallahi ban tab'a ganin mace sakara irin taba duk ubanta ya gama d'aure mata sai yadda take so ina duniya zatayi dad'i a haka?cikin fad'a-fad'a ummah ke maganar!wani dogon gauron numfashi sameer ya sauke lura da yadda ummah ke zayyana halayem yarinyar sak irin na salaha k'anwarsa,toh amma ya akai duk da jarunta da nake ganin yanzu tattare da ummah ta kasa gyara 'yarta?toh yanzu mene abunyi?ko dai na tallafa wa ummah ne tunda ga dama ta samu daddy baya nan?
Sameer lafiya dai ko naji kayi shiru haka?jin ya lula wata sabuwar duniyar yana tunani yasa ummah tamabayarsa!cikin jin kunya irin nasu na maza nan ya shiga susa k'eya kamar mara gaskiya sannan yace babu komai ummah amma in babu damuwa sai mu tafi tare da ita kawai yadda nima bazan wahala ba,kuma kinga itama ai taga jikin nasa!sosai hakan yayi wa ummah dad'i nan da nan ta amsa masa da ai kuwa hakan za'ai bara ta tashi daga bacci sai na sanar mata zuwa safe sai d'au hanya"kai Allah dai yayi maka Albarka ashe kai rahama ce a gareni amma k'ememe daddy Ya hanaka shigowa ciki,ai daga yau ka zama d'an gida kuma ana tashi daga aiki ka yo gida nan ne mahallin cinka da shanka,ni na tsaya maka naga kuma wanda zai canja hakan!dariya sameer ya saki na jin dad'in kalaman ummah nan yayi mata godiya da hakan ya kuma nemi izinin wucewa sashensa,ba musu ta yarje masa har da kiran ma'aikata da'a mik'a masa abinci sashensa!
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: *'YAR JAMI'A*
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
46-50
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Misalin k'arfe 9:00p.m kenan a agogon bangon dake mak'ale saman d'akin ummah kallo ta kai gareshi sannan ta nisa,juyowa tai gefe ta ga hankali kwance beauty na rik'e da waya sai latse-latse take yi?me kike yi da wayar??ummah ta tambayeta,cak beauty ta tsaya da charting d'in da take ta d'ago kai a hankali tace ummah gaisawa muke da daddy!daddy kuma?me kike ce masa?shiru beauty tai ba emm ba em em,toh ki ce masa ya kirani zami magana,toh ummah sannan beauty ta samu damar ci gaba da latsa yawar ta sanar masa,daga haka ta kashe datan nata ta sauka akai gaba d'aya,gefen kujera ta maida wayan ta aje don tasan halin ummah yanzu k'iris take jira ta kwace ta,ba'a d'auki wani tsawon lokaci ba sai ga kiran daddy ya shigo wayar beauty,hannu ta kai ta d'akko wayar ta ga sunan daddy a jikin wayar,juyawa tai ta kalli ummah tace daddy ne ya kira!wani dumm ummah taji kanta yayi mata yanzu kenan bazai kirata a wayar ta ba sai dai ta 'yar ta!haka ta danne damuwarta ta sa hannu ta karb'i wayar!gaisawa sukai kafin nan suka shiga hira ainun suna k'ara nuna wa juna tsantsar kulawa da rashin juna da sukai!acikin hirar ne beauty dake can gefe zaune taji ummah na sanar da dady zancen tafiya har tana ce masa beauty ta rok'i bak'on gidan nan ya kaita ta dubo jikinsa,da mamaki beauty tabi ummah da kallo har ta kammala wayar,ba abin tai magana ba sai kallo da ido,ke lafiya kika kafe ni da ido haka?cewar momy"nasan dai kin ji me nake cewa sarai toh dan haka ki shirya gobe da sassafe zaku tafi minjibir!minjibir kuma ummah?eh minjibir kuma wallahi naji kin kira dady kin gaya masa wani abu ni dake ne,don haka sai kije ki fara shiri tun yanzu don bansan kwana nawa zai ce kuyi ba!ba shiri beauty ta mik'e tsaye ta amso wayarta a hannun ummah ta fice a d'akin!
Da gudu beauty ta fad'a d'akinta kuka sosai ta shiga yi ba ji ba gani sai wani shure-shure take da hannu ita ala dole an b'ata mata"teddyn ta dake ajiye tsakiyar gado ta d'auka tai cilli dashi saman mirrow duk wasu kayan kwalba suka zube k'asa,tun tana kukan da sauti har ta gaji ta fara tsagaitawa dan kanta"kalaman ummah ke ta faman mata yawo akai toh yanzu haka kawai zata bi wani bak'o k'auye bata ma san waye bane,don kawai an ga daddy baya nan,har kusan sha d'aya na dare beauty na kwance sai faman mirgine-mirgine take saman gado"
Can wata dabara ta fad'o mata"tabbas zan had'a kayana da zarar mun fara tafiya sai na nemi na bashi kud'i kawai ya sauke ni a wani hotel d'in in yaje ya dawo sai ya biyo ya d'auke ni mu tafi!!yes yes beauty ta mik'e tsaye tana murna ta nufi drawer d'inta,duk wani abunda zata buk'ata sai da ta kammala su a jerin akwati biyu don ko ta batun karatunta bata yi sanin dama can baya gabanta!
Kiran sallar asuba na farko beauty ta tashi"ita da sallah sai gari ya waye take yi,wanka ta d'auro kafin nan ta fito ta shirya tsaf ta nemi hijab tai sallah"tana zaune kan dadduma kamar daga sama ta ji ta fara tariyo abinda ya faru jiya a stop and chop,yanda matan nan su kai mata tayin shiga k'ungiyarsu,tunani sosai tayi har dai daga k'arshe ta yanke shawarar in har ta samu zuwa hotel an jima zata kirasu ta shaida musu amincewar ta akan buk'atarsu!
Duk yadda tayi saurin lokaci yayi ummah ta kirata sai gani take lokacin baya ja,sauka k'asa tayi ta nemi breakfast tayi amma har yi war haka 7:00a.m batai ba, tsuka ta saki ta k'ara haye wa sama"tana zaune saman stool tana k'ara gyara kwalliyar fuskarta taji turowar k'ofa,ummah ce ta shigo dan haka cikin ladabi ta gaisheta!shigar jikinta ummah ta k'are ma kallo"doguwar riga ce light pink sai yalolan gyalan rigar data nad'e kanta dashi"jinjina kai ummah tayi sannan tace tun d'azu fa ya fito yana mota ke yake jira"jin haka yasa beauty cikin sauri ta aje lip stick d'in dake hannunta kamar ba ita jiya ke b'ata rai ba,ta shiga jan akwatinta,don yanzu ummah ta hana kowa yi mata aiki a gidan in banda wanki da guga,ummah ce ta taya ta da d'ayan akwatin har bakin mota inda ya ajiyeta saitin fitowa daga falo,bud'e taga booth d'in don haka suka zura akwatunan ciki,jiyowa tai su kai sallama da ummah sannan ta nufi k'ofar gaba na motar ta bud'e,da yake motar dimm take da duhu ko ina bak'i ne in banda side mirrow na waje baya ganin na ciki,shiko sameer rik'e yake da waya yana fama zuma revenge game da yake mayan game ne kawai yaji wani k'amshin turare ya doki hancinsa daga bud'e k'ofar!!!
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: *'YAR JAMI'A*
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
51-55
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
A hankali sameer ya d'ago dara-daran idanunsa ya sauke su akan k'ofar motar har lokacin beauty na tsaye tana k'ok'arin gyara doguwar rigarta don ta zauna,zanen rigar ya k'ura ma ido yadda yake ta shek'i na tamabarin tauraro(star) sosai ya shagala da kallon zanen kamar daga sama yaji k'arar demmmmm...Alamun an masa game over kenan, saurin sauke kansa yayi a phone d'in inda hakan yayi dai-dai da shigowar beauty had'e da tsayuwar ummah a bakin k'ofar tana fad'in toh sameer Allah ya tsare hanya,da saurinsa ya d'ago kai sama don baiwa ummah amsa!dass yaga idon mace kafe saman nasa wanda tun kiran sunansa da ummah tayi hakan yasa ta waigowa taga wannan waye abokin tafiyar tata,what??abinda sameer ya iya fad'a kenan yana nuna ta da yatsa, beauty da tai saroro kamar wata dutse tana kallonsa,can kuma cikin razani lokaci guda ta turo k'ofar motar har tana bige ummah da marfin motar haka tayo waje sai faman haki take kamar wacce tai tseren gudu!ido waje take kallon ummah da take tsaye tana luliye inda ta bug'e tace ke lafiya haka?bata iya cewa komai ba beauty sai nuni da ta ma shiga yi da motar!ganin ta kasa cewa ko uffan yasa ummah sunkuyar da kai cikin motar don ganin ko wani abu ya faru ciki!zaune ummah taga sameer ya dafe kai da hannu!cikin rashin fahimta ummah ta k'ara nanata maganar ga sameer shima dai yayi shiru!k'ok'arin komawa ciki beauty tayi,ai kuwa cikin sauri ummah ta rik'o hannunta!ina zaki?tambayar da ummah ta jefo ta dashi kenan?cikin dak'ilewar murya beauty ta amsa ta da ciki zan koma ummah wallahi na fasa tafiyar nan ya fito min da kaya na kawai!ciki kuma?akan wane dalili?kafin beauty ta iya bata amsa suka ji bud'e k'ofar sameer daga d'aya b'angaren yana fad'in emmm ummah dama ba komai kawai tayi mamaki ne jiya na d'an daki motar ta ban sani ba har ta kasa hak'uri ta fito tanai min fad'a,sai kuma gashi yau Allah ya had'amu amma babu komai,cikin k'ik'ina da sark'ewar murya sameer ke maganar!kana ganinshi kaga wanda ke b'oye da wani abu a rai,k'ara yunk'urowa beauty tai zatai magana nan ma ya k'ara tare ta da cewa,ina ga ummah in ta shirya kawai mu wuce don kar muyi latti ko?jin an ambaci latti yasa ummah saurin kallon beauty tace kin de ji kunya wallahi ko ina se kin nuna halinkina rashin hak'uri yanzu gashi dara ta ci gida,sai ki wuce yanzu ku tafi ai,kasa ko da kwakwkwaran motsi beauty tayi,duk wasu jijiyoyin kanta sun gama tsayawa cak da aiki,tunani fal sun gama cika kwanyar kanta,toh yanzu dama wannan shine bak'on dady?wanda ya gama tozartani a bainar jama'a?anya kuwa burin dana cimma yau zai iya bari na cika shi?toh yanzu ya ma za'ai na iya binshi mu tafi daga ni sai shi?bata dawo daga duniyar tunanin data shiga ba kamar daga sama taji wuf an finciki hannunta da k'arfin tsiya an wullata cikin mota,an maida k'ofa an kulle da key,a razane beauty ta hau jijjiga k'ofar da k'arfi ita ala dole sai ta bud'e,tana kallo haka cikin sauri sukai sallama da ummah ya shigo motar,bai bi ta kanta ba ya hau kunna motar,batai wata-wata ba ta jiyo kamar wata zararra ta rik'o hannunsa da yake kan key tace wallahi ka bud'e min motar nan,kar ka kuskura ka fita a gidan nan ba tare da ka sauke ni ba na dai gaya maka,sauke idanunsa sameer yayi a karo na farko a hannunsa yaga hannun beauty saman nasa,wani irin kukan kura yayi kamar wani mayunwacin zaki yayi wurgi da hannunta gefe,yanda taga jikinsa na wani kyarma tamkar mayak'in soja yasa ta shiga taitayinta ta fara rok'onsa Allah,da annabinsa ya sauketa,da yake motar duhu gareta sai ya zamana ummah duk wannan dramar tasu ba wadda ta gani haka ya tada mota hankali kwance ya fice daga gidan yana gyad'a kai!
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: *'YAR JAMI'A*
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
56-60
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Wallahi ka sauke ni, zan maka ihu, Allah zan juyar da kan motar nan kowa ya mutu,wai ba da kai nake magana ba ka mai dani wofi,kana jina fa? Nace ka tsaya na fita,surutai sosai beauty keyi,tun tana gunguni har takai ga samun sararin d'aga murya,ganin har lokacin sameer tafiya yake bashi kuma da niyyar tsayawa yasa ta kwarma wani uban ihu da bashi ba ita kanta sai data firgita,lura da lokacin ya fita daga wajen mutane ya fara yankar daji yasa shi jan birki ya maida motar gefen titi ya tsaya,kana ganin sameer kaga wanda yake cike da b'acin rai basai an gaya maka ba,wani wawan kallo ya jefe ta da shi mai cike da tsana,kusan minti 2 yana mata shi ganin hakan bazai gama isar da sak'onsa ba yasa shi magana"tur da wayewar gari irin wannan a wajena,ina ma ace mafarki nake,wallahi da tuni na farka na shiga gari na hau sadaka,don wannan munin mafarkin yakai matuk'a!kaicona sai gashi wai a zahiri ne,ni ne yau kusa da mace fasik'a,fajira,wacce bata san k'ima da mutuncin kanta ba,balle kai tunanin samun tsarki tattare da ita,nikam Allah wadai da mace 'yar Allah bani musha kunin kanwa,wai ya ma akai kika zama 'yar ummah?how??duka yakai a sityarin motar rai b'ace cike da nadamar hakan!
Tun tana danne zafafan kalaman dake fitowa daga bakin sameer har abin ya fara kai ta mak'ura gashi yak'i ci gaba da tuk'in kuma yak'i yarda ya sauketa,wasu zafafan hawaye ne suke k'ok'arin gangarowa kumatun beauty cikin sauri ta sharesu dan kar sameer ya ga lagonta ko kasawarta,juyowa tai cike da tsiwa tace ya isa!ya isa haka malam,ka ishe ni da surutai nace ka sauke ni ko dole ne sai ka tafi da ni?
Cikin huci sameer ya amsa ta"dole sai na tafi dake,ke kanki kinsan hanyarmu ta sha ban ban in banda k'addara!hayaniya sosai suka shigayi ya fad'a ta fad'a kamar wasu karnuka,har takai ga ta big'e masa hannu don masifa,kan uban can!ni kika bige ma hannu?ai sameer be jira ta bashi amsa ba ji kake fau fau ta ko ina dukanta yake kamar an aiko shi,duk da wuyar dukan da take sha amma hakan baisa bakin beauty ya rufu ba,sai da yaga yayi mata lilis sannan ya kyaleta,nan ne kuma tai lamo saman kujerar mota tana maida ajiyar zuciya!
Sai a lokacin ya janyo goran ruwa dake sak'ale a marfin motar ya sha,sannan ya bud'e motar,hannunsa ya wanke kafin nan ya maida k'ofar ya rufe yata nanata astaqfirulla,shi ala dole ya tab'a mace(kun ji sameer fa)wata doguwar tsuka ya saki yana fad'in ni dai duk iskancin mace da makircin ta na fi k'arfinta don ni ba ta shin shaid'anu bane,in ma sune ke bibiyarki gara ki gaya musu su barki dan nan baza ku sami waje ba,sai a bari sai an koma *'jami'a* sai a ci gaba,yana kaiwa nan yayi saurin kai hannunsa ga cd rom d'in motar, kaset d'in qira'a ya kunna, a hankali kake jin muryar sudais na tashi aciki,cikin sanyayyar muryarsa mara sauti haka ya shiga raira qira'an yana wani kwantar da kai saman kujera,sannan ya tada motar yaci gaba da tafiya!
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: *'YAR JAMI'A*
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
61-65
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Duk da ba wani bacci beauty take ba amma haka tai shiru itama dai tana sauraron qira'ar da haka har bacci ya d'auketa!lura da yadda ta makure kanta waje d'aya sameer yayi,nan da nan ya k'ara k'arfin ac d'in motar inda ta ko ina kake iya jin sanyi,shi kansa sanyin yayi masa yawa amma don mugunta haka ya hak'urar ma kansa,can cikin bacci beauty ke jin sanyin a jikinta, juyowa tai ta kai hannu ido a rufe tana laluben makunnin ac,d'all...taji an kai mata duka a hannu,wani irin zugi taji hannunta ya d'auka ba shiri ta bud'e ido,kansa na a titi amma yasan tabbas shi take kallo yace,kar ki kuskura ki bari najasa ta tab'a tsaftataccen abu in ko ba haka ba,yanzu ki sake shan wani dukan!
K'ara gyara zamanta sosai beauty tayi har tana wani bank'aro k'irji waje ta murgud'o mai baki tace bismillah d'an halak ka fasa,
Kallo d'aya sameer yayi mata ya k'ara sakin wani tsakin yace kaga balama,wato na dake ki d'azu kin ji dad'i hankali ya kwanta,har da lumshe ido shine yanzu kike so jikina ya k'ara tab'a naki ko?toh na gano ki!gaskiya ke akuya ce ko wacce harawa ci kike!God forbid! Wannan irin rayuwa taki yarinya kamar tashin getto!
Marairaice murya tayi beauty uwa mai shirin kuka take nuna kanta da yatsa tace,ni nake son ka tab'a ni?kai kuwa kasan ni wacece?cikin tsiwa shi ko sameer ya dawo mata da amsa"ahaf ni ko nasan ko ke wacece,ko ba kece wannan karuwar malaman jami'ar ba? wacce sunanta yayi k'auri a wajen d'alibai kai har da malamai ko ina ka zagaya *'yar jami'a* duk mutumin banza ya sanki!bayan wannan sanin akwai wani sani da zan miki ne?don haka ina gargad'inki in kina son tafiyarmu ta k'are lafiya toh ki iya bakinki kuma ki nisanci zama a inda nake,bata jira taji k'ashen maganar tasa ba ta juya masa baya har da cire gyalen data yale kanta dashi ta rufe fuskarta!
Murmushin gefen kunci sameer ya saki me cike da mugunta yace dad'in ta dai kin ji a jikinki don haka in kunne ya ji,toh gangar jiki ta tsira,yana kaiwa nan ya basar da ita ya shiga bin qira'arsa yana tuk'i!
Har suka isa garin minjibir beauty kwance take fuska rufe,gashi yana son tambayar ta inda zai shiga amma zuciya tak'i barinshi,can dai da yaga ba haza dole ya k'ara d'aka mata wani dukan,beauty dake kwance tunani duk ya gama cikata ta sak'a wancan ta kunce wance,tai firgigit ta d'ago fuska tana cire gyalen fuskarta,dilla malam ni kar ka sake duka na ai ba jaka bace,shiru yayi mata don yanzu bashi da lokacin biye mata haka,ina zamuyi?ya tambayeta kansa na kalon gaba,karkato hannunta tayi tana nuna masa kwanar data yanki gefensa cikin saurin yayi baya da jikinsa sameer can kuma ya kallota yace ke dilla ba sai kin kara kanki da ni ba da baki zaki min magana!wani abu taji ya kawo mata wuya beauty wai shin me ya dauke ta haka yake ta wulak'antata?kwanar yasha ya shiga tafiya a hankali don sun shigo gari baya so ya wuce wajen!tafiya suke tayi ba tare data k'arayi masa magana ba sai ma chewinggum data fito a jakarta ta jefa baki,ta shiga tauna, har sameer ya kai k'arshen titi beauty bata tanka masa ba,a k'ufule ya juyo don yaga babu wani sauran gida gma inda suke sai gonaki na mutane, yace ke wai ina zami yi ne kuma?kwai beauty ta sakar masa ji kake k'as-k'as sannan ta saki wani kasalallen murmushi tace inda waccen akuyar take nan zaka bi!waige sameer ya shiga yi amma sam wajen baiga wata alamar ko kaza a wajen ba balle akuya,lokaci d'aya ya fahimci beauty bak'ar magana ta yi masa,juyowa yayi a b'ace yaga ta k'ara sakar masa wani kwan k'ato,ai bai san sameer lokacin daya cafko hannunta ya murd'a shi da k'arfin tsiya ba,ihu sosai beauty ta saki har da d'aga k'afa d'aya sama bayan ido data zaro waje,ji kake tana cewa wallahi baya ne,kwanar da muka baro ne,waccan kwanar ce fa ta baya,amma ina sameer k'af yak'i kulata sai da yaga ta ji jiki sannan yayi wurgi da hannun ya juya kan motar suka dawo baya,rik'e take da hannun tana juya shi da haka tayi ta masa kwatance a nutse har suka isa k'ofar gidan nan tace toh ka tsaya haka mun zo!
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: *'YAR JAMI'A*
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
66-70
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Yi yayi sameer kamar ba ze amsata ba, sai kuma can ciki-ciki uwa mai gunguni yace toh!k'ok'arin bud'e k'ofa beauty ta shiga yi ta fita don taga alamar sameer bashi da niyyar fita, taji yace toh sai a kama kai nan dai gidan tsoho ne ba gala ba,wani miyau mai mugun zafi beauty ta had'e ta gyad'a kai ta fice abinta,kamar jira yake ta fito shima ya fito ya biyo bayanta, zauren gidan suka shiga tana gaba yana biye har suka cimma tsakar gidan sallama beauty tayi shiru ba motsin kowa sai data k'ara d'aga sautin nata fiye da wancan sannan ta ji daga can d'akin dake kallin kusruwar gidan wata dattijuwa ta amsa!
Wana ke ji kamar muryar jikalle?
Eh tsohuwa me ran k'arfe mune!
Toh! yagana ta fad'a tana yaye tsukakken labulen dake sak'ale a k'ofar tana fad'in lalle marhabun k'araso ciki!ta kai ayar maganar kenan kanta ya kai ga sameer wanda ke mak'ake bayan beauty!.
Auf ashe da bak'o kuke tare!hannu baba yagana takai saman katifar da ke shinfid'e tsakar d'akin ta janyo gyalenta ta yale akanta dashi sannan ta k'araso waje,cikin nutsuwa sameer ya tsugunna ya gaisheta ta amsa hannunta d'auke da tabarma!
Ashe ana ganin ku mutanen birni?cikin farin cikin ganinsu baba yagana ke jefo mata tambayar!
Hmm kaji baba ai yanzun ma wajen tsoho na zo ba ke ba!tana maganar yayin da take tallafamata wajen shinfid'ar tabarmar!
Yunk'urawa beauty tayi zata zauna baba yagana ta jefota da wani irin mugun kallo tace na bige ki anan guraren,ke zan wa shinfid'a ko siriki na?gafara can ki ba bak'ona waje ya zauna yau ta shi nake bake ba!"
Ba beauty ba hatta sameer se da maganar tayi masa mugun nauyi a kai!siriki kuma?nanata kalmar yayi cike da rashin fahimta,haka nan dai ya iya dai-daita nutsuwarsa ya nemi waje ya zaune,k'ara gaisawa sukayi nan kuma hira ta b'arke inda sameer ya ji komai game da raahin lafiyar tsoro dake can cikin k'uryar d'aki ya samu bacci!
"Gafara dai masu gida!e Muryar wani matashi kenan wanda a tsawo bai wuce na sameer ba ya shigo tsakar gidan rik'e da kekensa mai cike da damin harawa!
Baba yagana ce ta amsashi da gafara dai!tana kallon shi cike da nuna sanayya!
K'eeee.. suka ji ya saki keken k'asa ya shiga nuno su da yatsa yana fad'in kan uban can wazan gani zaune kamar hajjo?
Sororo hajjo tai tana kallonsa kamar zata iya tuno shi amma ina rashin zuwanta yasa ta kasa tuna shi!!
Ganin tayi shiru ya sashi k'arasowa ya nemi waje gefen sameer ya zauna nan ya mik'a mai hannu sukai musabaha sama-sama amma duk hankalinsa naga beauty,baba yagana ce ta katseshi da hannu tace kai wannan kallo haka d'an ladi kamar baka san taba?washe baki ya shiga yi yana kai hannu k'eya yana susawa yace"ai baba hajjon ce duk ta canja tayi fari tai gyau wallhi hala tana shan lemon birni(apple) ne?
dariya duk suka sa har da beauty!jim suka d'anyi da sigar shiru hakan ya baiwa sameer damar kai kallonsa ga bak'ar agogon dake sak'ale a hannunshi ya duba lokaci inda ya nuna 9:30a.m da sanyin jiki ya d'ago kai ya kalli baba dake jn gene da garu yace ina ganin baba yagana ya kamata a tashi tsoho haka yayi kumallo mu je asibiti ko? Don kar lokaci ya k'ure mana"baki sororo baba yagana ta bud'e baki hangam tabi sameer da kallo can kuma ta nisa tace kai d'an nan rufa min asiri ina yabon ka sallah kar ka kasa alwala mana,mu yanzu ina mu ina zuwa wani wajen asibiti kayan yahudu da nasara bakaji jami'an su ana kiransu likita bokan turai ba?wannan ai sai ka saka mu zama abin fae'e a yankin nan,toh bada niba wai shiga d'akin mayya!fad'a-fad'a,tsiwa-tsiwa haka baba yagana ke maganar kafin ta kai ga cigaba d'an lami yayi caraf ya karb'e maganar!
Ai dama wallahi baba ni nasan da walakin goro a miya tunda na yanko kwanar layin nan naga an kicciye mota gaban shagon sale me rake nasan cewa wa'adin tsoho yazo don na tabbatarda wannan d'an farin(nan ya nuna sameer da yatsa)uwa aljani ba haka nan yazo ba,toh wallahi ahir d'inka tsoho sai ya ga aure na don baza kai min haramiyar damun hatsin daya tanadar min ba yazama na magada!jin yarda d'an ladi ke ta zuro bayani ba ko tsagaitawa yasa beauty rai b'ace ta daka masa tsawa!
Kai dalla can kai wa mutane shiru,ashe kai har yanzu sokancin nan dai baka bar shiba?har kana wani d'aga wa mutane murya?toh bara kuji zuwa kamar anyi an gama"
Kin yi kad'an wallahi kin yi tsararo baki isa kizo cikin sanyin safiyar nan ki d'aga mana hankali ba,ko uwarki ina magana bata ja balle ke!
yau naga waze raba ni da d'an uwana"tana kaiwa nan a magana sai ta b'arke da wani irin kuka mai cike da k'ara baba yagana kenan, kai kace wani mugun abun akai mata!
Ganin yadda hayaniya ke tashi sosai ga kuka da baba ta saka yasa sameer matsowa kusa ita ya saisaita muryarshi k'asa-k'asa uwa mai rad'a ya shiga aikin lallashi! Da kyar baba yagana ta hak'ura ta tsagaita da kukan wanda lura da hakan ya baiwa sameer damar fara yi mata bayani!
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
71-75
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Ina so kisan wani abu baba mak'asudin zuwan mu gidan nan ba don komai bane illah mu nema wa tsoho lafiya,babu yadda za'ai muna ji muna gani mu kai shi inda zai wahala,tunda mu musulmai ne,bisani ma wannan jikarsa ce,maganar asibiti kuma da kika baba shekara nawa kuna zaune gida ana yin na hausa,wane sassak'e da mad'acin ne ba'a bashi yasha ba?ina ce duk an gwada amma jikin jiya i yau,kinga kuwa bazamu zuba ido ace haka za'a barshi cikin wahala ba dole a samu abin yi!kuma ina ganin son da zaki nuna wa tsoho shine ki barshi muje mu jarraba na baturen ko Allah yasa a dace!
Jimm baba yagana ta d'an yi uwa mai nazarin wani abu kowa ita yake jiran jin abinda zai fito daga bakinta,kwatsam suka fara jin k'uhul...k'uhul...k'uhul....alamun k'arar tari na tasowa daga d'akin dake gefensu,cikin sauri baba yagana ta mik'e suka rufa mata baya sukai cikin d'akin!
Kwance suka iske shi yana yunk'urin mik'ewa amma ba hali don wani matsanancin rawa da jikinsa ya soma va shiri sameer ya k'ara suka dashi bai jira cewar suba yadda yaga jikin tsoho na gyargyarwa ya sungume shi yayi yayi waje dashi,haka suka k'ara d'ungumowa gaba d'ayansu suka yo waje banda kuka da kururuwa babua binda baba yagana ke sumbud'awa"
Abakin k'ofar zaure ne suka ci karo da malam sale mai shago wanda kukan baba da ya jiyo yasashi shigowa ba shiri,ganin yadda aka fito da tsoho ranga-ranga yasa shi shima kwarma uban salati ya ja gefe ya tsaya,ba wanda ya iya bi ta kansa suka haura sukai waje,cikin aljihu sameer ya fiddo key ya mik'a wa beauty nan ta bud'e motar ,gidan baya sameer ya zauna shi da tsoho d'an ladi na k'ok'arin turo kai ciki ya dakatar dashi yace a'a ka zauna gida ka kula da baba yanzu zamu dawo,badan yaso ba haka d'an ladi ya ja gefe yayi turus!
Juyawar da sameer zai yi ne kicib'is suka had'a ido da beauty dake gefen baba tsaye hannu rike da mukullin mota"cikin tsawa ya furta mata" ke dalla malama ki shiga ki drivern namu kikai tsaye akan mu kamar sanda,ba ta bi ta maganar saba duba da yadda jikin tsoho ta tsananta ta nufi driver seat da sauri ta shiga ta kunna motar,ta nufi asibitin dake k'auyen!
Da idarsu asibitin waje beauty ta samu ta aje motar wanda har lokacin numfashin tsoho ya kasa dai-daito cikin sauri sameer a bud'e k'ofar ya d'akko tsoho suka fito beauty na take musu baya,cuncurundon jama'a kad'ai kake hangowa ta ko'ina acikin asibitin ga hayaniya na mutane duk inda ka juya mara lafiya ne zaune,abinka da ba'ai saba shiga waje haka ba kafin kace me duk sameer ya rikice ya rasa ina ma zai yi dashi,waje ya gano gefe da wata mata dake goye da yaro ba kowa cikin sauri ya isa wajen ya zaunar dashi juyowa yayi ya kalli beauty rai b'ace yace ki kula dashi ina zuwa kuma banda nuna hali!yana kai wa nan sameer ya sakai yayi gaba" sakayau beauty ta bishi da kallo fuska yamutse uwa mai shirin kuka ta shiga zancen zuci"toh wai shi wannan me ya d'auke ni akuya ko kuwa tunkiya da duk inda naje sai na bi maza?ba takai ga baiwa kanta ansa ba ta jiyo tarin tsoho ba shiri ta katse guntun tunaninta ta nufi wajensa ta na mai sannu!
Bai wani jima da tafiya ba sameer sai gashi ya dawo gefensa wani matashi da alama likitane sai wasu samari suma dai cikin fararen kaya dake nuna jami'an lafiya ne,ko da suka k'araso samarin nan cikin sauri da nuna gogewar aiki haka suka janyo gado a wani d'aki dake gefe damu suka d'aura tsoho suka nufi can wani sashen na asibitin,biye muke binsu har suka isa wani b'angare da hayaniya ta tsagaita a wajen,office dake ciki suka nufa muna k'ok'arin biyo su ciki likitan dake biye damu ya d'ago musu hannu badan sunso ba dole yasa suka dakata anan!
Waige sameer ya shiga yi ko ya samu wajen zama can ya hango wasu kujeru da basu wuce 4 a jere a k'arshe wajen ba take ya nufi wajen yazauna itako beauty ta shiga sintiri tana kai kawo a wajen!
Har kimanin minti 30 babu alamar motsi ko fitowa daga ciki! gajiya beauty tayi da zagayen dole ta nemi gefen wata window dake nan ta jingina tana kallace-kallacen jama'ar waje!
Can suka fara jiyo taku na tahowar mutum ido duk suka k'ura wa k'ofar sai gashi d'aya daga ciki samarin nan ya fito hannunsa d'auke da takarda!mik'ewa sameer yayi da sauri ya nufoshi inda itama beauty ta yo kansa tana fad'in dan Allah malama ya jikin nasa?bai iya tanka mata sai ma kallo da yakai ga sameer yace yallab'ai dr.ya rubuto allurai da ruwa da za'a siyo,karb'ar takardar sameer yayi k'ok'arin yi sai yaji yace dashi,a'a yallab'ai ai wannan aikin ba naka bane kadai bayar a siyo,lummm sameer ya d'anyi sai kuma can ya wuce gaba yace muje toh wajen!
tafiya suka shiga yi har sun kai k'ofar barin wajen sameer kamar wanda yayi mantuwa ya juyo ya kallo beauty wacce itama dai su take kallo yace toh sai ki samu waje gashi can ki zauna a bar lek'en taga don babu abin gani kuma dai a kama kai don nan gidan HIV ne,yana kaiwa nan yasa kai ya fice abinsa!beauty dake tsaye hannu sak'ale da k'aramar jakarta bata ankara ba taji wasu zafafan hawaye sun fara kwaranyo mata a fuska wanda sam batasan dalilin hakan ba!
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
76-80
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Kusan minti biyar kenan da fitar su sai gasu sun shigo rik'e sa ledoji biyu,office d'in saurayin ya shige shi ko sameer ya dawo nan ya nemi waje ya zauna!
Kawo lokacin beauty na zaune saman kujerar ta duk'e kai k'asa tana nazarin halin da tsoho ke ciki,
Sallama har sau biyu sameer yayi amma ina beauty tayi nisa a tunani"wasu dai anyi asarar kud'in tara wallahi ace sallamar ma basu iya amsawa ba"furucin da beauty kenan ta tsinta daga sameer hakan ya tabbatar mata da sun dawo don haka ta d'ago kai tana kallonsa"kafin daga bisani ta saki doguwar tsuka had'e da tab'e baki ta d'aura k'afa d'aya kan d'aya ta juya masa gyeya! Dariyar k'arfin hali sameer ya saki mai cike da tuhuma sannan ya furzar da wani zazzafan iska waje yace"Wato in aka ce dai akuya wallahi an gama da kai,don kuwa ita ko ina sai ta nuna halinta sai dai in bata samu waje ba! Bai kai ga sauke lumfashinsa ba kamar wacce aka mintsina beauty ta juyo a kufule ta shiga gyad'a masa hannu taba magana"kai malam shiru-shiru fa ba tsoro bane gudun magana ne,ko dan kaga tun d'azu ina raga maka shiyasa kake ganin kai ka isa,toh wallahi ina yi maka kashedi na k'arshe ka fita a harkata tun kafin na nuna maka kaina a zahiri"
A razane sameer ya mik'e tsaye ya dafe k'irje had'e da fad'in wa iyazu billahi yanzu banda wannan munanan ayyukan da kika shahara dau kina so kice min har akwai wasu na xahiri?ehh toh lallai ke tashin shuri ce don daga gani bade rainon mutim basai dai aljani!
Ganin yadda sameer ya samu damar ci gaba da gaya mata magana son ransa yasa itama ta mik'e tsaye ta shiga jijjiga jiki uwa mai shirin dambe kana tace na lura kana wasa dani ko?da sigar ko in kula sameer ya bata amsa da,ni kuwa yaushe zanyi wasa da wacce tayi ikrarin kiran kanta da sunan 'Yar jami'a ai ban isa ba tunda ban tab'a bin wani malami tsoho mai nauyin shekaru ya prof KAS na buk'aci b'ata masa mutunci ba,ban kuma tab'a nuna tsiraici na afili don samun distinction ba kin ga kuwa baxan tab'a had'a kanki da ni ba!
Hucin da beauty ke fitarwa kad'ai zai zayyanar dakai irin halin da take ciki na k'unar rai na lura da duk wata gab'a da tabi don taga ta d'au fansa sameer ya kasa bata wannan damar! Awulak'anceta watsa masa wani mugun kallo had'e da sakin wani mugun zagi ta koma ta nemi waje ta zauna jiki ba kwari"abubuwa kala-kala ta shiga sak'awa a zuci ganin yadda ko da sau d'aya zatai nasara akan sameer amma nazarinta ya kasa bata,dole haka ta hak'ura na lokacin ba don ta janye k'udurinta arai ba dai don ta gama da jinyar tsoho tukunna!
shi ko sameer lura da yadda ta yi lagwas yayi don haka ya shiga murmushin mugunta ala dole ya iya furta hmm kad'an kika gani yarinya in dai kin ce ke 'yar jami'a ce toh mu masu gyara jami'a ne kuma dole ki ladabtu ko kin k'i ko ki so!daga haka shima ya nemi can nesa da ita ya zauna tare da janyo waya a aljihunsa ya shiga yin game na zima revenge ko ya samu sauk'in rai!
Haka sukai zaune har wajen azahar kafin nan dr ya fito hannunsa rik'e da wani abin kwajin numfashi ya nufosu,ko da sameer ya hangoshi tashi yayi fuska a sake ya nufi wajensa yana fad'in dr. Ya jikin nasa?murmushin k'arfin hali ya saki kafin nan yace c'mon down prince ba wani abu ne na tada hankali ba jimawa da yayi a gida ba tare da an kawo shi asibiti ba shiya haddasa masa hawan jini amma yanzu cikin ikon Allah mun samu munyi controlling nasa sai dai tarin da yake ne wannan sai a hankali kuma ana shan magunguna,yanzu haka yana ciki ya samu sauk'i sosai don nayi masa allurar bacci zaku iya shiga ku ganshi in har jikin naga ba matsala zuwa yamma kafin na tashi a aiki na sallame ku!
Amsa masa sameer yayi da toh sannan ya k'ara gode masa da namijin k'ok'arin da yayi yabar duk wani aiki nasa yayi nasu!musabaha suka yi kafin ya basu izinin shiga ciki shiko ya wuce waje,jami'an lafiyar da suke tare suka mara masa baya!
Duk bayanin dr. a kunnen beauty ake yi duk da tana can zaune amma hankalinta na kansu haka bata jira cewar sameer ba duk da tasan ba wani abu zai ce mata ba yana shiga d'akin ta biyo bayansa ta shiga!kwance suka iske tsoho yana bacci hannunsa d'auke da ledar k'arin ruwa da aka saka masa,cikin sauri beauty har tana bige kafad'ar sameer ta k'ara gefen gadon ta rik'o hannunsa cike da tausayin halin da yake ciki ts shiga rero kuka!.
Cike da b'acin rai sameer ke binta da wani wulak'antaccen kallo shi ala dole ta buge masa jiki gashi yak'i jinij yaga mace tana kuka balle wannan daya lura kamar ita jin dad'in kukan ma take,tsawa ya daka mata a tsawace yace dalla malama ki wa mutane shiru uban me akai miki da zaki cika mana waje da k'ara?wannan shegen kukan naki ai se ya tashe shi"
Bata iya tanka masa ba beauty illah tsagaitawa da kawai ta iya yi da kukan!ta nemi waje gefe dashi ta zauna ta k'urawa tsoho ido, a sukwane shima sameer ya koma can baya ya jingina da bango tare da hard'e hannayensa biyu a k'irjinsa cike da damuwa ya ke kallon yarda robar ruwa ke d'iga cikin kwaroron robar hannunsa!
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
81-85
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Har wajen k'arfe d'aya na rana tsoho na kwance bai tashi ba,jin kiran sallah na tashi daga cikin masallacin ya baiwa sameer damar fita ya barsu anan,yana sa kai ya fita beauty ta waigo ta k'are ma wajen daya tsaya kallo nan ta saki wata doguwar tsuka tare da fad'in"aikin banza ai na zaci bara kaje sallar ba gafin mu zaka zauna yi ka wani kafe mutane da ido uwa soja gona,tsukar dai ta kara saki don yadda duk take jin ta atakure ita bata saba wannan zaman ba musamman ma na asibiti ga yunwa data fara addabarta,k'are ma wajen kallo tayi tas taga dai babu wani abun ci a wajen balle tai tunanin ci,ga babu bayi da xatai alwala ballantana daddumar sallah cike da b'acin rai beauty ta shiga gunguni wanda ita kanta baza ta tantance abinda take fad'i ba do takaici!
Tana haka taji an turo k'ofa an shigo, sanin wanda zai shigo yasa ko takan k'ofar bata bi ba da mamakinta sai ta ji muryar mace,hakan ya bata damar d'ago kai ta kalle ta"
Sannu dai" jami'ar asibitin ta fad'a, yawwa sannunmu,bata k'ara tankawa ba matar ta shiga jere mata kayan dake d'auke a hannunta,ledojine guda hud'u bak'ak'e sai sallaya da hijabi data mik'a mata sannan ta iya cewa dama yallab'ai ne yace a kawo miki kuma in kina son wani abu ga d'aki nan na kusa da wannan kina fita daga hannunki na dama sai ki min magana"murmushin karfin hali da jin dad'i beauty ta sakar mata don ko ba komai tasan dai abinci ke cikin ledojin nan don haka ta ce toh nagode amma ina bayi yake?hannu jami'ar takai ga wani labule da ke manne a saitin gadon tace gashi nan madam"madam kuma? Abinda beauty ta furta kenan a ranta,toh me yace musu game da ni?kar dai fa ya gaya musu wani abu na b'atance don k'aramin aikinsa ne?ciskune fuska tayi na dole ba don taso sunan ba tace ok zaki iya tafiya yanzu,da haka jami'ar ta fice tare da janyo mata k'ofar!
Bayin ta nufa ta d'oro alwala ta fito,inda ta aje hijab d'in je ta janyo ta ta saka dogone har yana d'an ja mata k'asa,haka ta janyo sallayar da shirin sallah sai kuma tayi turus tana bin d'akin da kallo ?can kuma ta nisa tace wayyo ni ina ne yanzu kuma gabas d'in?ganin ba fahimtar hakan zatai ba yasa ta yanke shawarar zuwa ta tambayo matar,aje sallayar tayi ta doshi k'ofa don fita,tana murd'a k'ofar taji an murd'o ta daga waje an turo,saurin matsawa da baya tayi don kar ta bige,har ya shigo kallo,sameer kallo ya bita dashi cikin hijab kwanan sha'awa kamar tayi ta zama kullum haka sai kuma can ya basar ya juya kai gefe cikin izzah ya jefota da tambaya,ina kuma zaki?ita madai kauda kai gefe tayi uwa bazata amsashi ba sai kuma can ciki-ciki tace gabas zan tambayo,kamar be jita ya tab'e baki yayi mata nuni da hannu,kalli nan! Kallo ta kai wajen,bai k'ara tanka mata ba ya nemi guri ya zauna!
Bango ta kai wa harara beauty kamar yana kallonta ta juya ta zare sallayar cikin fushi ta shinfid'a ta fara sallar!
Tana idarwa kenan ta fara azkhar ta ji k'arar wayarta cikin jaka,kallo ya bita dashi sameer ya na jiran yaga cikin biyu wanne zatai azkhar ko waya,da mamakinsa sai yaga ta share wayar taci gaba da addu'ointa,k'arar da cikinta ya bayar da k'aramin sauti yasa ta dole badan taso ba tsagaita adduarta ta shafa,wani abu ta ji ya tsaya mata a rai kuma gashi dai tana son janyo ledojin abincin amma kunya ta hanata don yadda k'afafunsa suka tokare ledar" jim ta d'anyi tana nazarin abin amma lura da yadda yunwa ke nuk'urk'usarta yasa ta dole ta maze had'e da tsuke fuska uwa wata 'yar dambe ta saka hannu ta shiga janyo ledojin,karaf ledar k'arshe ta buge masa k'afa, ai kamar jira yake sai ji kai d'asss.. ya kai ma hannunta duka da k'arfi,ledar beauty ta saki a razane ta d'ago kai ta kalle shi,me kuma nai maka?cike da mamaki take tambayar,mugun kallon nan dai nashi ya k'ara jefo mara ya galla mata wata harara yace"ehh lallai kam tunda kin maida tab'a jikin namiji abincin ki ai baza ki san me kikai min ba,toh wallahi na bar kyaleki kina tab'ani kina cin na jaki banza akuya,zunbur beauty ta shiga yi har tana hard'ewa da hijabin jikinta ta mik'e tsaye ta kama k'ugu ta rik'e tana wani karkad'e-karkad'e tace kasan Allah wannan abin naka ya ishe ni ehe,don ba jaka aka kawo maka ba,mutum sai bala'in naci da shishshigi idan baka son alak'ata dakai tun farko wane karanbanin yasa ka neman tahowa dani? Me yasa baka jefar dani a hanya na san inda dare yayi min ba?ko an gaya maka bani da wajen zuwa?meya hanaka zaman wajen da ka dawo yanxu tunda ban kama hannunka nace zo zauna kusa dani ba?toh dan haka malam kasaurara min ko na ci uban.....ba ta k'arasa k'arshe zagin nata se ji kake fau..fau..fau wasu zafafan mari har biyar da sameer ya sauke mata a fuska,bai jira wani abu ba yayi wulli da ita gefe har tana karo da bango ya zari sallayar dake shinfide a k'asa ya shiga jibgarta da ita,kiciniya suka shiga yi sosai dukkan ninsu a wahalarce musamman beauty dake kwance k'asan tiles jiki duk shatin duka,shiko haki ya shiga furzarwa na wanda bai saba shan wahala irin hakaba!
Ganin yadda ta galabaitu yasa sameer dakatawa da dukan yayi cilli da sallayar gefe ya nunota da yatsa yana maida haki yace"wallhi duk randa kika kuskura kika k'ara magana irin wannan sai kin raina wa aya zak'inta mutuniyar banza kawai,har ni zaki kalli mahaifina ki zaga wanda ya bani cikakkiyar kulawa da tarbiyya?toh baki isa ba wanda duk kike tunanin ya tsaya miki shima bai isa ba,da kuma kike cewa na takura miki,eh naji na takura miki don bazan zauna ina kallo karuwa ta lalatamin rayuwa ba,don haka ki kama kanki!
Yanda take kwance k'asa tana maida numfashi haka ta shiga nuna kanta da yatsa tace,ni ka kira da karuwa?karuwa fa?k'ok'arin mik'ewa zaune tayi amma ina jikin yayi tsami dole ta komar da kai ta kwanta k'asa wasu mugayen hawaye suka shiga anbaliya a kuncinta!
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
86-90
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Yarda take maida hak'i na kuka haka sameer ke maida hakin wahala suna haka sai rurin waya ya k'ara tasowa daga jakar beauty,sai alokacin ta tuna da d'azu an kirata tana addua haka da janjiki ta isa gaban jakar ta sa hannu ta fito da wayar,lambar zee-zee ta gani rass gabanta ya fad'i ba tare da wani dalili ba,d'aukan kiran tayi ta kara akunne tana fad'in hello"murya k'asa-kasa beauty ke amsa ta can kuma kome zee-zee ta gaya mata sai cewa tayi what??kina so kice min yau akayi test d'in?toh ba cewa akai se last week ba?har nawa akayi?biyu?wanne da wanne?sir p... maganarta yayi dai dai da kallon sameer wanda ke zaune gefen tsoho ya dafe kai da alamar damuwa tare dashi,a sanyaye ta k'arashe wayar sukai sallama da beauty duk jiki ba kwari,tana kashe wayar ta k'ara sulalewa k'asa ta kwanta,tunani kala-kala tun tana iya danne zuciyarta har ta gaza a fili ta shiga dukan tiles din dake shinfid'e k'asa tana fad'in mugu,mugu,azalimi wallah Allah sai ya sakamin!
Tana cikin wannan hali taji daga sama rurin wayar sameer dole ta tsagaita da kukan ta maida kanta ta had'e da gwiwoyinta, zaro wayarsa sameer yayi daga aljihu ya amsa kiran bai wani jima ba ya gama wayar,wata lambar ya shiga laluba beauty na kwance taji cikin wayar yana fad'in kamal yanzu za'a zo a kawo maka test d'ina pls ka adana min kafin na dawo! Da haka suka ci gaba da hira har ya gama,aje wayarsa ke da wuya yaji alamun motsi daga bayansa,da sauri ya juya idonsa ya ci karo da tsoho dake kwance yana k'ok'arin tashi,k'arasawa sameer yayi ya tallabo shi yana tai masa sannu,wanda hakan ne ya tabbatar ma da beauty cewa tsoho ya tashi ,a hankali ta d'ago ta zauna,dishi-dishi haka ya shiga bud'e idonsa har Allah ya saka ya bud'e su gaba d'aya,alama ya fara nuna masa da yana buk'atar ruwa don haka cikin sauri sameer yayi waje don kiran dr.
Sameer na fita tamkar ya baiwa beauty damar k'arasowa wajen tsoho ne cikin jan jiki haka ta k'araso suna had'a ido suka sakar ma juna dariya haka ta rungume shi da haka ta hau masa sannu!suna haka sai ga sameer ua shigo tare da dr.dole ta basu guri dr yayi 'yan bincike-bincikensa ya gama da yake ruwan hannunsa ya kai k'arshe zare masa yayi kafin nan ya rubuta masa magunguna yace su zauna nan ya k'ara samun k'arfin jikinsa zuwa anjima sai a sallame su!dad'i sosai ya lullub'e jn yadda cikin k'ank'anin lokaci tsoho ya samj sauk'i,takardar maganin dr. Ya mik'a wa sameer sannan ya basu waje,ledae dake aje sameer ya hau bud'ewa har ya gano wacce ke dauke da ayaba,hannu yakai ya d'ebk yadawo gefen tsoho a hankali ya shiga bashi yana ci har ya gama dai tsoho ba emm ba em em duk tunani ya gama cika game da dabuwar fuskar daya gani tare da jikarsa amma lura da yadda beauty ta kasa sakin jiki suyi hira sosai kamar yadda suka saba sai yayi zaton ko kunyar had'uwarsu da sirikinsa yasa ta shiru(loh tsoho bai sai su beauty duka aka sha ba)da haka ya kauda tunanin a rai"!
_4:30 na yamma:_
Tsaye suke bakin asibitin rike da takardar sallama inda sameer ya rik'o hannun tsoho duk da jikin da kwarinsa sai dan bashi kulawa kawai,ita ko beauty tafe take nik'i nik'i da ledoji ,baya ta bud'e ta shiga inda sameer ya sanya tsoho gaba ya zagaya ya shiga motar suka fita a asibitin!
Tun saka kan motar sameer a layin tururuwar jama'a kad'ai kake gani ta ko ina ana biye dasu ana ihu na farin cikin tsoho ya dawo,yara ko se d'ane motar suke da yake yamma tayi duk wasu magidanta sun dawo k'ofar gidan tsoho mak'il yake haka suka tsaida motar,inda da kyar Sameer ya iya bud'e wa tsoho k'ofa ya fito dan jama'a,k'ok'arin bud'e marfin motar beauty ta hau yi don ta fito taji an buge hannun daga waje,sanin waye yasa bata ma bi takai ba da sauri ta bud'e k'ofar ai ko yayi saurin maida marfin motar ya kulle kafin ya fidda tsoho yasa mata lock,tururuwar taron jama'ar data gani shi ya hanata magana dole ta koma ciki tai zaune ta bi su da ido har suka shige cikin gida!don tasan sarai sameer na iya dizgata gaban bainar jama'a!
Juyi da murna babu irin wanda baba yagana batai ba,sam zama ya gagareta,d'akko wancen aje wannan shine kad'ai aikin kai kawo da take wa sameer sai da ta tabbatar ta cika masa gabansa taf da kayan abinci da fura sannan ta iya samun waje ta zauna,baba yagana sameer ya kalla yace baba wai ina d'an ladi kuwa?nisawa tayi kafin nan tace ai d'an ladi ya tafi gona tun bayan tafiyarku watakil ma yanxu duk inda yake yana hanya,wani abu zai yi?a'a dama maganin tsoho zai rakani na siyo cikin gari"sameer ya fad'a"
K'aramin murmushi baba ta saki sannan tace ai ban baka labari ba d'azu bayan tafiyarku drammer aka sha ni da shi,wai ala dole anyi masa haramiyar jin rab'ar mota,da gunguni haka ya fita ko ta kansa ni kam ban bi ba ina tunanin yadda tsoho zai samu lafiya duk na gama tada hankali,tunani ya kasa yarda cewa zai dawo da rai sai gashi ya shigo da k'afafunsa kai amma fa mungode da wannan taimako naka!
Ba komai baba ai yiwa aki ne yanxu dai ki sama wa tsoho wani abu yaci kafin ya dawo mu siyo maganin"haka baba ta amsa da toh ta mik'e ta nufi cikin uwar d'aka!
Hankali kwance sameer ya gama cin tuwon alkama miyar gyad'a da baba yagana tai masa ya bishi da fura wacce tasha kindirmo,ya jingina kenan da bango yana son abincin ya ratsa masa yaji maganar d'an ladi yana shigowa"
Maimakon ya shigo da sallama sai 'yan wake-wake da yake sakin kamar d'an makid'i har ya zauna dariya kawia sameer yayi masa sannan yace,har ka dawo daga gonar?banza yayi dashi kamar be ji shiba da haka sameer ya ci gaba,dama kai nake jira ka dawo muje mu siyo wa tsoho magani a mota,da jin haka cikin sauri dan ladi ya waigo yana kallon sameer yace wai da gaske kake zaka shigar dani mota?gyad'a kai sameer yayi da zummar eh,ai lokaci d'aya d'an ladi ya saki fuska hira ta b'arke tsakaninsu ta inda yake shiga bata nan yake fita ba,har da alk'awarta wa sameer yau zai had'a masa taro mai kyau a dandali suje kallo,da haka dai sukai ta hira,sai can da hira ta nisa d'an ladi ya waiga ya kalli sameer yace wai kuwa ina hajjo?sakin baki sameer yayi cike da kid'ima bai jira basa amsaba ya mik'e ya zuri takalmi da sauri yayi hanyar zaure".
Koda ya isa gaban motar kwance ya Taradda beauty sai had'a zufa take kana ganinta kasan ta galabaita,cikin sauri ya bud'e k'ofar ya shiga lek'enta!..
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
91-95
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Lura da alamun bacci da ta shiga yi na wahala yasa sameer bubbuga gefen kujerar yana fad'in ke!ke!firgigit beauty tayi ta mik'e zaune kana ganinta kasan ta wahala,fuska cuskune ta kallo shi babu ko kwakwkwaran nauyi a jikinta ga tsamin duka da jikinta ya riga yayi,koma wa da baya yayi sameer wanda hakan ya bata damar fitowa a motar a daddafe ta maida k'ofar ta rufe,cikin sanyin jiki haka ta shiga tafiya sai yaji duk babu dad'i abin bai masa ba,amma dole ya dake ya kallota ta wutsiyar ido yace ke!kike wani cilla k'afa uwa summy cillare(Loh) in zaki saki jiki gara ki saka in ko ba haka ba na fasa kwai yau kowa na k'auyen nan ya san halinki,da sauri beauty ta d'ago raunannun idanunta ta kallosa cike da takaici,murmushin mugunta ya sakar mata had'e da kashe mata ido d'aya yace kinsan dai xan iya don haka sai ki zab'a yana kaiwa nan yayi gaba abinsa ya shige ciki ya barta nan tana jan jiki uwa wacce kwai ya fashe wa a jiki!
A cikin zaure beauty ta tsaya nan ta k'ara gyara jikinta sosai,cikin k'arfin hali kuma ta saki fuska ba yabo ba fallasa ta nufi cikin gida,Da sallamarta ta shigo tsakar gidan babu kowa sai k'arar muryar d'an ladi dake tashi duk ya karad'e gidan da surutu shi ala dole labari yake ba sameer,muryar beauty da yaji yasa shi tsagaitawa da hirar ya juyo baki a washe yana kallon k'ofa,har ta k'araso wajen sameer bai d'ago kanshi daga duk'en da yayi ba tun jin sallamarta,cikin k'arfin hali beauty ta kalli d'an ladi tace ina tsoho yake,yana d'akinsa"d'an ladi ya bata amsa,bata k'ara cewa komai ba ta sa kai ta wuce su zuwa d'akin,yadda ta gifta ta gaban sameer haka ya d'ago kai ya bi bayanta da kallo,k'arewa tafiyar kallo yayi sam babu wani alamar sauyi ko canji daga tafiyarta,murmushin gefen kunci sameer ya saki a kasalance ya raya a zuciyarsa"lallai yarinyar nan a iskanci ita yarinya ce har da take tsoron k'aramin k'auye kamar wannan susan sirrinta,toh ko dai tsoho ne bata so ya sani? Bai kai aya a tunanin nasaba yaji an tab'o shi a kafad'a,a d'an tsorace ya juyo,lafiya dai ko bak'on birni?tambayar da d'an ladi ya jefo masa kenan,gudun kar d'an ladi ya fahimto abinda yake kallo yasa shi kauda kai gefe ya d'an ja numfashi yace ai da kaga na kau da kai ba wani abu nake mazari ba illah b'aci da rai na yayi ace yadda kake suburbud'amin wannan labari ka kasa bani labarin budurwarka?(kwana ba sai a mota ba)bud'e idonsa sameer yayi da sigar son jin wani abu ya k'ara langwab'ar da kai gefe sannan yace toh ko dai baka da ita ne?
K'afa d'an ladi ya d'aga sama ya dire a kan tabarma sai kuma ya kwashe da wata irin muguwar dariya mai cike da mamaki,sai da yayi ma'ishiyarsa sannan ya d'ago kai a gadarance yana wani faffad'a kafad'a yace Wato d'an birni ni d'in nan da kake gani na duk ranar da naje dandali sai 'yan mata sunyi fad'a akai na,shiyasa kaga samarin garin nan duk kishi suke da ni don mero 'yar gidan mai gari wancan satin da naje dandali baka ga yadda take nuna kauna k'arara akai na ba,har wani kod'a ni take wai tana son tsagun fuskata,amma ni duk basa gabana ,jin maganar d'an ladi na k'arshe yasa sameer k'are wa bak'a k'irin d'in fuskar d'an ladi mai cike da tsagu kallo,jinjina kai yayi cike da mamaki,ganin yadda d'an ladi ke ta faman kod'a kanshi ba ji ba gani,surutan 'yan mata barka tai yasa shi d'aga masa hannu yace toh suda sarkin magana yanzu dai gaya min wace zab'inka acikin nasu?cikin sauri d'an ladi yayi hanzarin kai hannunsa ya rufe fuskarsa shi ala dole yaji kunyar tambayar"
Murmushi sameer ya saki ganin yau ya had'u da wani garan yace sai kuma can yace haba d'an ladi meye na rufe fuska kuma kai dai gaya min ko wace zan baka shawarar yadda zata so ka fiye da tunaninka, jin haka tuni d'an ladi ya zare hannunshi yace wai da gaske?eh mana kai de gaya min,turo baki gaba d'an ladi yayi uwa mai shirin surb'ar koko yace bawata bace illa haj...hajj...sai kuma yayi shiru! haba kai kuwa meye haka ka fad'i sunan sosai mana ni ban gane wannan yaren ba, jin hak a kunyace d'an ladi ya nok'e kai ciki-ciki yace ni fa hajjo nake so tun dana ganta d'azu"
Hahahahahahahahaha!wata irin muguwar dariya sameer ya saki wacce shi kansa bai ma san lokacin data kwace masa ba don kid'ima da abinda yaji,ido waje ya zaro yana fad'in wace hajjon?ba dai hajjo ta birni ba?washe baki d'an ladi yayi don jin dad'in yadda sameer yayi saurin gano shi yace alqur'an ka gano ni sarkin wayo!k'ara kecewa sameer yayi da wata muguwar dariya ta k'eta ganin bazai iya dai-daita kansa da dariyar ba yasa shi mik'ewa da sauri ya kamo hannunsa yana fad'in kaga taho muje a siyo maganin,a can ma tattauna komai,ba shiri d'an ladi ya mik'e ya bishi sukai waje!
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
96-100
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Tun bayan shigar beautu d'aki hira kawia suke da baba yagana don abincin ma kasa cinsa tayi don yunwar taci ta har ta cinye,duk da kuwa ta jin zugin jikinta,a tsammaninta su sameer suna zaune a tsakar gida,shiko tsoho na kwance yana bacci tun bayan abincin da baba yagana ta bashi,jin kiran sallah da baba yagana tayi ya sata mik'ewa da sauri tana fad'in yau naga yarinyar kawai duk na biye miki da hira gashi ko abinci ban aje miki balle na baki ruwan wanka,dariya beauty ta saki sannan tace ai dama ba sona kike ba yanzu dai bara nai sallah sai ki bani jagolgolon da kike yiwa tsoho na ci,dariya duka suka saki kafin nan baba ta fita ta barta anan!
Gyalen data yale kanta dashi shi ta cire ta k'ara gyara tukkuwar gashin kanta sosai sannan ta janyo wani k'aramin d'ankwali data gani nan gefen shinfid'ar tsoho ta d'aure kanta dashi ta nufi tsakar gida!wayam taga wajen babu alamar mutum wanda hakan ya tabbatar mata cewa su sameer sun tafi sallah ne!k'aramar tsuka ta saki cike da b'acin rai ta furta d'an masifa kawai mutum kamar maye se shiga harkar mutum gaskiya ya kamata ko ba komai na gaya wa daddy abinda duk yake faruwa tunda nan ummah bata nan balle ta tsawatar min in ma dawowa zai yi gara yayi amma duk mutanen nan biyi sun takura wa rayuwata kamar ni kad'ai ce mutum a duniya?wata tsukar ta k'ara saki cike da cin haushi haka ta nufi bakkin tijiya da zummar kafin tai bacci daren yau zata sanarwa dady duk kan abinda ke wakana bayan tafiyarsa,butar dake gefe sanye da ruwa ta d'auka ta nufi bayi!
_8:00p.m na daren ranar!_
Ruwa ta watsa beauty ta shigo d'akin baba yagana wanda ke jere da na tsoho,zaune ta isketa saman gado tana k'idayar kud'i, eyyeemba su baba an yi arzik'i irin wannan kud'i ince dai kayan d'aki zaki saya mini dasu?tayi maganar tana yarfe ruwan hannunta,dariya baba yagana ta saki nan ta d'ago kai tace mata toh sarkin son banza wannan ba kud'in tsoho bane balle a jere miki d'aki da kumbo wannan kud'in dashi ne da muke yi jiya aka kawo min d'ibata ko k'idayasu banyi ba don dama na maganin gargajiyar tsoho nake tari sai gashi yaron kirki yazo ya share mana hawayenmu,abinda shekara da shekaru ake magani yau lafiya gobe babu amma kiga jikinsa yau har da cin abinci da shigowa gida da k'afafunsa aiko lafiya ta samu,jinjina kai beauty tayi had'e da tab'e baki ta kauda kanta gefe,tana rayawa azuciyarta"lallai baba baki san wanene shi ba da har kike yabonsa mutum mugu azalumi wanda babu tausayin 'ya mace a zuciyarsa,da har zai mun dukan ajali kusa!
Gafaranku dai masu gida,maganar d'an ladi kenan wacce ta dawo da beauty cikin hayyacinta ta k'arasa shigowa da sauri ta nemi gefen gadon kusa da baba yagana ta zauna! Waige ta shigayi ko ta samu abu ta rufe jikinta don zanin atanfar baba yagana ne d'aure a k'irjinta,sai alokacin ta tuna da akwatin kayanta na motar sameer da suka zo basu fito da kayan su ba haka suka tafi asibiti,bata an kara ba taji an yaye labule sama, cikin rawar jiki,ido na kyarma ta d'ago ido sama me zata gani?d'an ladi rik'e da hannun sameer tsaye a bakin k'ofa!yarda ta matsar da kwayar idonta akan d'an ladi sai gashi ta kasa sauke idonta daga kallon da suke mayarwa da juna ita da sameer!ko wannen su da abinda zuciyarsa ke raya masa,cikin k'arfin hali da mazantaka sameer yayi saurin sunkuyar da kansa gefe tare da jan hannun d'an ladi cikin zafin nama yace fito nan waje musha iska mubarsu ciki!bai jirayi amsar d'an ladi ba sai ganinsa d'an ladi yayi an finciko shi da k'arfin tsiya tsakar gida,inda farin wata ya haske su!
Duk kan abin nan daya faru akan idon baba yagana dake rik'e da kud'i a hannu ta tsaya da k'idaya tun shigowarsu!juyowa tai sosai ta fuskanci beauty wacce ke zaune kanta a duk'e ta zuba wa zanen ledar tsakar d'akin ido,wanda ita kanta bata san dalilin yin hakan ba taji baba ta dafo kafad'arta! Da yake hankalinta ya d'an gushe zuwa tunani sai ya zamana a tsorace ya d'ago kai ta kalli baba!murmushi mai cike da fassara baba ta saki sannan ta saukw ajiyar zuciya ta kira sunanta!hajara! Beauty ta amsa kanta na k'asa!
Allah yasa ayi damu!
Me za'ayi daku baba?ido waje ta d'ago kai tana tambayar,jin baba tayi shiru tana dai 'yan murmushin nan nasu na manya da suka san me duniya ke ciki!nan ta ci gaba da magana Allah kuwa baba ki yara da n... bata iya sauke lumfashin ta ba baba ta tsayar da ita ta hanyar nuna ta da yatsa tace kul hajara naji kince wani abu!ki tashi ki shirya ki sallah kawai shi ya fi miki ga kuma tuwonki can rufe a tasa!daga haka baba yagana ta mik'e ta maida kud'inta ma'ajiyarsu tayi waje abinta!
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
101-105
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Cikin sark'ak'iya tare da b'acin rai haka beauty ta mik'e ta shiga zagayen d'aki kai kawon da take ne ba tare da samun wata mafita ba yasa ta tsagaitawa da zagayen nan ta shiga laluben d'akin,a saman wata ghana most go taga sallaya tare da hijab ai kuwa cikin sauri ta janyota ta zunbula har tana jan k'asa nufo k'ofa tayi da niyyar fita,amma ina tana kaiwa bakin k'ofa sai tai turus ta tsaya jin sautin hirar da suke a tsakar gida shi ya bata raunin gwiwar fita,ta d'an jima nan tsaye sai kuma can dabara ta fad'o mata labulen k'ofar ta janyo ta bud'e shi kad'an ta lek'a kanta ta shiga magana da k'ara tana cewa"d'an ladi ka je mota ka duba jakata na ciki ka d'akko min!
Hira suke sosai abinsu su sameer su kaji kamar daga sama ana magana!jimmn sameer ya d'an yi kad'an kafin nan ya tuna ashe kayansu na mota!d'an ladi ne ya fara cewa murya k'asa"d'an birni kaji wai jakar gimbiya na mota,murmushi sameer ya saki da jin kalmar gimbiya sai kuma yace toh je ka d'akko mata!kallo ya watso masa yace ai kasan ban iya aiki da na'urar bud'e mota ba!auff ashe fa haka ne muje toh,haka suka mik'e sameer na gaba yana biye dashi suka fita ba'a wani jima ba sai gasu da kaya nik'i-nik'i sun shigo,mai makon jakar beauty ta kasance a hannun d'an ladi sai gata a hannun sameer,yana k'ok'arin wucewa d'akin baba da k'aramar jakar sameer don ya kai mata sameer ya tsaida shi yace a'a wannan fa malam tawa ce kai min ita d'akin ka bara na mik'a mata tata!toh kawai d'an ladi yace ya wuce, shi ko sameer ya nufi k'ofa, a bakin k'ofar shima dai ya tsaya amma bai kai ga d'aga labule ba,wanda har lokacin beauty na tsaye wajen sai dai ta saki labulen ta jingina da bango ta ji sautin magana!
Tabbas mai hali baya tab'a canja halinsa,a gaskiya dai anyi asarar shekaru,girma ya fad'i,wallahi ina mamakin kasancewarki tsatson wannan dangi na mutunci da girmamawa,sai dai kuma ta wani fannin ba laifi bane don naga haka don ko 'YAR JAMI'A shahararriyar karuwa ce!mai neman maza,wacce bata son kamun kanta ba,wacce take ikirarin kanta da beauty ma'ana kyakykyawa ko?toh Allah dai ya raba mu da kyawun d'an miciji!ameen! Yana kaiwa nan da maganarsa sameer ya wulla mata jakar ciki da k'arfi har ta kai ga buge k'afarta!amma ba yadda ta iya dole ta toshe bakinta da rad'ad'd'in da k'afarta ta bayar lokaci d'aya!
Sameer ko daya wurga mata bai zame ko ina ba daga nan sai d'akin d'an ladi,itako beauty abinka da wacce rai bai saba b'aci haka ba komai ace dady sai ya zamana sabon abu a wajenta,haka ta daure ta ja k'afar da tuni dama ta gama tsami don dukan da ta sha da rana a asibiti,ta k'arasa gefen akwatin ta bud'e wata doguwar rigar kalar ruwan toka(ash)dai ta k'ara janyowa ta zura da yake duk dogayen rigunan ta kwaso don tasan halin tsoho sarai tun tana yarinya ba'a shigo masa ita gida da k'ananan kaya!
Haka ta kammala shiryawarta tsaf tayi sallah sannan ta ci tuwo,Alhamdullah ta fad'a bayan ta gama cin abincin, duk da ba wani cin kirki tayi masa ba!abinka da ba'a saba ci ba! Tana k'ok'arin hayewa gado ne taji muryar baba yagana tana fad'in toh ina kuma kuke shirin fita haka,ko wacce amsa suka bata sai ji tayi tace toh ku jira ku kai min kifin rijiyata yawo tun zuwanta ba inda ta lek'a,
Kafin ta iya wani kwakwkwaran motsi ina har baba ta shigo,yi tayi kamar bata ji shigowarta ba ta ci gaba da hayewa gado,ke meye haka kuma hajara?bacci tun yanzu?ai kuwa baki isa ba tasowa zaki ku tafi,kai baba mu tafi kuma ina? Fuska sake baba yagana tace dandali mana kije kisha kallo in da rabo sai ki sama wa d'an ladi mata daga nan ma! Don naga da alama ruwan ido ya masa yawa!cuskune fuska beauty tayi kamar me shirin kuka tace dan Allah ni dai su je kawai gajiyar hanya tayi min yawa gobe naje ni,had'e girar sama data k'asa baba yagana tayi ta matso saitin kunnenta tace mata kaga ja'irara banza mara wayo,ki shigo da yaro santalele fari sol wannan k'auyen ko kishinsa bakya yi ai ya ci ace duk motsinsa kuna tare,haka d'azu fa ina kallo suka fito ko ki bi su,saurin katseta beauty tayi ta shiga bubbuga k'afa na shagwab'a tana cewa ni wallhi baba yagana ki shiru don tsakaninmu ba dangin iya bana baba kawai had'in ummah ne tace ya rako ni!
Janyo ta baba yagana tayi cikin fushi ta tsaya k'em a tsaye sannan tace toh yi maza zura takalmin ki mu wuce,yadda taga baba tayi fuska ba annuri yasa ta tilas ta zuwa suka fito daga d'akin a jere da juna!
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
116-120
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
A daddafe beauty ke binsu da kallon mamaki, to shin me d'an ladi ya shirya musu haka?kallo takai ga inda su d'an ladin suke nan taga sameer tsaye gefen dama sai wani matashi wanda da alama shine d'an mai garin, a hankali ta k'arasa inda suke badon taso ba haka ta koma gefen sameer ta tsaya don ta tabbatar ta tsaya d'ayan gefen sai ya mayar mata da magana!
Tun tsayuwarta a wajen wasa ya fara kad'e-kad'e da wak'e-wake ke tashi sosai,a inda ko wane makad'i ke baje irin nashi basirar a salo na gargajiya,murna da farin ciki sosai kake iya ganowa a fiskokin kowane saurayi dake wajen inda kuwa 'yan mata ke cikin fili suna taka rawa d'an ladi da d'an mai gari sunai musu lik'i,wayarsa sameer ya fitar daga cikin aljihunsa a yayinda ya shiga vedio ya hau yo saboda wannan shne karonsa na farko da yaga abun gargajiya irin haka,sai ya zamana abin ya k'awatar da shi nesa ba kusa ba,beauty dake gefensa tana tsaye jugum tana binsu da kallo sosai ta shagala da kallo bata ankara ba taji an janyo hannunta cikin tsakiyar fili,d'ago kai tayi don taga wacece ai kuwa tayi ido hud'u da wata matashiyar bafulatana fuskarnan cike da fara'arta ta shiga juya mata hannu da nunin su yi rawa,duk da yadda rawa da wak'a suka zama jiki a wajen beauty sai gashi yau ta tsinci kanta da jin kunyar hasali ma duk sai take jin nauyin kasancewarta a filin,haka bafulatanar nan ta ci gaba da juya mata hannu amma sam tak'i yadda ta taka,ganin haka d'an ladi jiki na rawa yayo kanta ya shiga yi mata lik'i,can gefe guda kuma ya hango sameer tsaye sai d'aukar su yake a waya ai da saurinsa ya k'arasa ya kamo hannunshi sameer na kaucewa amma ina sai da ya kawosa cikin fili,kunya ya aje gefe sameer ya kamo hannun d'an ladi suka sha rawarsu suna yiwa juna lik'e,haka dai sukai ta sharholiyarsu a ranar abinda aka jima ba'a yi irinsa a dandalinba,sosai daren ya k'awatu ga kowanne saurayi da budurwa,ba su suka tashi a dandali ba sai 12:30,da haka ne kuma kowa ya kama hanyar gida inda su sameer suma suka nufo gida,beauty kuwa anyi k'awa bafulatana don har k'ofar gida ta rakota anan sukai sallama ta kuma shaida mata sunanta ladiyo!
suna shiga kai tsaye d'akin tsoho duka suka wuce,beauty da ge gaba ita ta fara shigewa ciki inda ta iske d'akin cike da mutane har kawo wannan lokacin ga tsoho na kishigid'e gefe yana dariya wanda hakan ya nuna abin dariya akayi,sallamar tace ta katse su don haka suka juyo baki d'aya zuwa ga k'ofa,a d'an razane beauty ta ja da baya sanadin fuskar data gani yana dubanta,jiki na gyarma ta zube k'asa ta shiga gaisuwa,Alhaji ina wuni?
Fuska d'aure wanda ta kira da Alhaji ya amsa da lafiya lau! ya wajensu ummantaki?
Duk suna lafiya!sannan ta iya gaishe sauran bak'in dake wajen wanda da alamun Alhaji ne da iyalansa suka shigo don dattijuwar mace ke gefensa da matashin yaro!baba yagana ce ta katseta da tambayar ina kika baro mazan kuma? Nan ta amsata da gasu nan tsakar gida tsaye!bata kai ga rufe baki ba Alhaji ya jefota da tambayar ke wane maza kuma?yarda take mutuwar tsoron Alhaji yasa ta kasa basa amsa sai baba ce ta tari numfashinsa da cewa loh ai su d'an ladi ne sai kuma bak'on da suka taho dashi daga birni,bara na kira ku gaisa,nan take ta kwala musu kira suka shigo cikin girmama wa dukkan ninsu suka gaisheshi kafin nan tsoho cikin murya k'asa-k'asa yace sannu dai d'an nan naga magunguna dazu bayan fitarku yagana ta kawo min kuma nasha kamar yadda kayi mata bayani,ubangiji Allah yayi maka tukwici da gida ln aljannah yasa kaima kasamu mai yi maka!d'aki kowa ya amsa da ameen!
Alhaji ne ya nemi su tashi su tafi tunda ya zama kamar al'ada duk dare sai sun raba hira a gidan k'anin nasa!haka sukai sallama suka fita har Alhaji ya kai bakin k'ofa ya juyo ya kalli beauty ake zaune manne da bango yace zuwa gobe sai ki shigo da bak'on naki waje na ina nemanku!mutuwar zaune kusan beauty tayi don da an auna jininta awannan lokacin babu shakka ya daskare!tsawa ya doka mata sosai yace baki jini bane, asukwane ta amsa da toh sannan ya fita!
Mtsss kai Allah dai ya shirya wannan muguwar zuciyar taka wallahi ace mutum zafi kamar zaki,tsoho yayi maganar yana k'okarin mik'e,da sauri beauty ta taso ta fad'o jikinsa ta shiga rero kuka don tasan yadda ya yink'ura d'in nan wajenta yake son zuwa,babin lallashi da bada hak'uri sabo tsoho ya bud'e inda duk suka zama 'yan kallo a d'akin!can beauty ta tsagaita da kukan ta d'ago kai tana ajiyar zuciya tace wallahi tsoho shiyasa ko ummah tace nazo bana son zuwa kai kana sona amma Alhaji baya sona kullum fad'a se duka!janyota tsoho ya kuma yi ajiki yace yi hak'uri mutuniyar maza ce yagana ta kai ki d'aki kiyi bacci gobe in jiki na ya k'ara sauki zaki sha labarai!murmushi beauty ta sakar masa sannan ta tashi ta bi bayan baba yagana suka fita,inda suma dai su d'an ladi sukai bankwana dashi suka nufi d'akinsu!
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
121-125
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
_Karfe 07:00 na safe!_
Zaune take beauty ta gama cin karin kumallo kenan bayan wanka data gama,tashi tayi ta janyo wata jar doguwar riga mai ratsin fari a ciki ta saka kayan masha Allah abinka da farar mace sun karb'i jikinta ainun,k'aramin gyalen kayan ta yale kanta dashi kamar yadda ta saba ta shirya tsaf,baba yagana dake kwance saman gadonta na k'arfe tace sai ina kuma?fari beauty tai mata da ido tace sai d'akin tsoho kema dai kinsan wannan kwalliyar tsoho ce!dariya baba yagana ta kwashe da ita sannan tace ja'irar banza kya dai gyara zancen naki,don kin rai nani zaki ce haka mana tunda jiya da murnarki kika dawo daga dandali,toh kar dai ki manta da zuwanku gidan Alhaji,lokaci guda beauty ta d'aure fuska ta juyo ido narke tace dan allah baba yagana ki wani abu akai wallahi ni bana son zuwa don nasan tabbas fad'a kawai zan sha kinsa fa halinsa!fuska baba ta yamutse da jin maganar beauty sannan ta iya cewa toh ni me zance akai bayan kinsan halin kayanki,yanzu dai tsoho bacci yake don tun safe ya ci abinci yasha magani ya kwanta,ki tashi ki yiwa bak'onki jagora ki tafi can gidan tun safe kafin ya fita gona don kinsan ya d'akko zafin gona kanki zai huce!dariya duka suka saka tare sannan beauty ta zari takalmi da jakarta tayi waje!
Tsaye take beauty bakin k'ofa ita bata shiga ba kuma bata koma d'aki ba,can dai ta lura tsayuwar nan ba yi mata zatai ba dole ta matso daf da k'ofar ta manne jiki da bango murya k'asa-k'asa tayi sallama,d'an ladi ne ya amsa mata amma da mamaki sai gani tai sameer ya bude labulen k'ofar ya fito,kallo d'aya yayi mata ya kauda kai,ita d'in ma dai kauda kan tayi k'asa tana son gaishe shi amma tana tsoron dizgi,dole ta iya bakinta ganin bata da niyyar magana yasa shi tamke fuska a kasalance yace zaki iya wucewa mu tafi ko?ba tare data tanka masa ba beauty ta shige gaba abinta ta nufi hanyar fita waje,bin ta tayi a baya,haka suka yi ta tafiya da yake safiya ce babu duk jama'a sai harkokinsu suke yi haka har suka isa k'ofar gidan, anan ne kuma ta ta tsaya a tafiyar ta juyo ta kalleshi tace nan ne gidan!wani kallon raini sameer ya fara binta dashi kafin yace in nan ne gidan ni zan shiga nai miki iso ki shiga kome?ta ji haushin kalamin nasa sosai duk da dama tasan bai zama lallai ya bata kyakykyawar amsa ba haka ta saka kai gaba ta shige gidan!kusan minti uku da shigarta sai gashi ta fito tace da sameer wai yace ka shigo! Kallonta kawai yayi ba tare daya ce uffanba, da haka ta fahimci abinda yake nufi ta shige ciki shi ko yabi bayanta!
Alhaji na zaune tsakar gida rike da ludayi a hannunsa sai gabansa da kwanon koko ya cika shi taf,a hankali yana surb'ar kayansa yana had'awa da k'osai ya ji sallamar sameer!ludayin hannunsa ya maida cikin kwanon lokaci guda kuma ya shiga gyara babbar rigar dake sanye jikinsa,zama na kamala da manyance Alhaji yayi kafin yayi wa sameee iso daya zauna dama dashi,k'ok'arin zama beauty tayi kafin kace wani abu Alhaji ya da mata wata uwar tsawa ke shige ciki ki baiwa mutane waje, jiki na gyarma haka beauty ta afka cikin d'aki!kallon sameer Alhaji yayi akaro na farko ya sakar masa murmushi inda sameer ya sunkwi da kai cikin jin kunya a ladabce ya gaishe sa,amsa Alhaji yayi da fara'arsa har yanayi masa tayin koko,cikin dariya sameer ya amsa masa daya gode,shiru ya biyo baya na 'yan wasu lokaci sannan Alhaji ya nisa yace yaro ya sunanka?cikin nutsuwa ya amsashi da sameer!
Jinjina kai Alhaji yayi na gansuwa da hakan kafin yace toh malam sameer tak'aitaccen tarihin rayuwarka nake son ji,sannan ka sani a hira dani ba'a k'arya don haka sai ka kiyaye,tom sameer ya amsashi sannan ya k'ara gyara zama sosai ya shiga motsa leb'ensa!
Da farko dai sunana Sameer Al-qaseem maji dad'i ni haifaffen garin yola ne mahaifina Alh.Alqaseem maji dad'i ya kasance k'asaitaccen d'an kasuwa a garin yola gashi kuma d'an siyasa,bayan sarautar gado da muke da ita ta maji dad'i da aka nad'a masa,hakan ne yasaka bayan zab'en da akai shekara uku baya muka dawo garin abuja da zama sakamakon zab'arsa a kujerar senator da akayi,mu uku ne a gurin mahaifina,na kasance babba sai k'anne na biyu mata aysah da salaha wanda duk suna zaune yanzu haka da mahaifana a garin abuja suna karatu,ni kuma nayi karatuna tun daga matakin karatu na primary kawo yanzu dana kamala jami'a nake bautar k'asa da nake yanxu a garin kano,gaba d'aya nayi a garin abuja wajen yayan mahaifina Alh.Aliyu maji dad'i da yake shi can yake zaune sai ya zaman to tun tashi na babana ya maidani wajensa saboda Allah bai bawa matarsa haihuwa ba sai dai in anyi hutu naje wajensu!bayan karatu na kuma a b'angaren kasuwancu yayan mahaifina tare muke harkokin company d'insa dani yanzu haka jira yake na gama bautar k'asa d'ina takaddun company daya bud'e min yana nan a garin lagos inda zan fara jan ragamar kula dashi dazarar na gama bautar k'asa! Wannan dai shine tak'aitaccen tarihin rayuwata!
Ajiyar zuciya ta gamsuwa da abinda ya fad'a Alhaji yayi,yadda ya lura da tsantsar hankali da nutsuwa irin ta sameer yasa shi umartarshi daya rubuta masa lambar wayar mahaifin nasa dana yayan mahaifinsa a takarda,haka kuwa akayi sameer ya janyo wani k'aramin memo daga aljihunsa na gaba tare da biro ya rubuta masa,karb'a Alhaji yayi ya linke takardar ya zura a aljihu,da haka suka shiga 'yan k'anan hirarsu wacce duk bayanine akan sameer da zuriyarsa!
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
126-130
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Duk labarin nan da sameer ke labartawa Alhaji akunnen beauty dake mak'ale baki k'ofa tana jinsu da yake d'akin bak'i ne sai ya zamana babu kowa ciki,shiru ya biyo baya nan take kuma ta shiga nazarin rayuwar sameer da yadda taji tsantsar nasaba da girma irin na gidansu,lallai wannan mutumin mai girma da karamci ne dole ya ki ni da duk wata halayya tawa toh yanzu da ace yana nan akai birthday d'ina inda muka sha rawa da maza a lokacin ai da bansan daga jiya zuwa yau wane irin zagi da tozarta zansha ba!tana cikin wannan tunane taji kamar daga sama Alhaji yana magana,lallai indai wannan itace rayuwarka ka tashi gidan girma da mutuntaka kuma ka dace duk inda kaje kaga abu kuma har ka yaba dashi toh abaka,don haka yanzu inaso ka gaya min gaskiya domin Allah daga saninka da hajara zuwa yau wane irin halayya ka fahimta tattare da ita!
K'ululu.....k'arar cikin da sameer ya bayar kenan don shi kam anyi masa tambaya mai matuk'ar tsauri wanda shi kansa bai ma san ta ina zai fara ba inda akan rayuwar beauty ne,a yayinda beauty tuni ta gama daskarewa jikin k'ofa tana jiran shigowar Alhaji tasha duka don tasan yau kam kashinta ya bushe, jin yadda sameer yayi shiru yasa Alhaji k'ara jefo masa tambayar ta wata siga,yace kar ka d'auka na tambayeka haka da wata manufa ne a'a illah dai kawai ya kamata ace kasan wacece hajara sosai don kuwa ni azamana da ita akwai matsananciyar soyayya dana lura a tsakaninta da mahaifinta wanda hakan ya sanya ta sangarta mafi muni,har ya janyo bata ganin kowa da gashi ga shiga mara ma'ana amma zuwansu na k'arshe garin nan na horar da ita mafi k'ololuwa don a lokacin tana gab da fara shigarta jami'a don haka nake rok'onka daka gaya min meke wakana tun yanzu na gyara ta basai tayi aure abin yafi k'arfi na ba!duk da haka shiru sameer yayi don duk wasu k'ofofin kansa ji yayi an gama kulle masa su wai yau shine ake wa tambaya akan beauty haka?kafin yayi wani k'wak'wk'waran motsi suka ji sallama daga waje!tuni sameer ya sauke wata nannauyar ajiyar zuciya don kuwa yasan neman Alhaji akazo yi! Yun k'urawa Alhaji yayi yace ina zuwa daga haka yayi waje!bai jima ba sai gashi ya dawo nan ya nufo sameer ya zauna yace kaga abokin tafiya ta gona wato makwabcina yazo don haka zan baka damarka ka je gida yanzu,bazan d'au lokaci da yawa a gona ba saboda wannan muhimmiyar maganar dazarar na dawo can gidan malam zan nufa sai mu k'arasa maganar tamu!
Cike da murnar zuci sameer ya amsa shi da toh Alhaji,
Kwalawa beauty kira Alhaji yayi cikin sauri sai kuwa gata ta fito hannu rik'e da takalma don rikita,kallonta yayi yace ki mai dashi gida zuwa anjima zan shigo bai jira cewar taba ya nufi hanyar fita ya fice abinsa bayan daya d'auki kayan aikinsa a gona yayi waje!
Duk da jikinta ya gama bata sameer ita yake kallo a lokacin amma sam ta kasa d'ago kai ta kalleshi balle kwakwakwaran magana, takalmin dake mak'ale a hannunta ta zaro ta saka sannan ta nufi hanyar fita!ba tare da shima ya damu da hakan da tayi ba sameer ya bi bayanta!
Shigarsu zauren gidan ne kuma labari ya canja don beauty ta gama fahimtar tabbas sameer zai tona mata asiri dole ya yanke shawarar ta sauke koda kad'an ne daga cikin girman kan da take ji ta nemi gafararsa!don hakan ne kad'ai zai ceceta yau a hannun Alhaji,yanke hukuncinta yayi daidai da tsayuwarta haka kuma sukwane ta juyo har suna kusan cin karo da juna ta tsaya, shima dai tsayawar yayi da sauri ganin yadda jikinsu ke kusan had'uwa yace lafiya dai?? Murya can k'asa beauty ta kira sunansa"ya sameer!! Shiru yayi yana bin ta da wani wulak'an taccen kallo har sai da ta k'ara kiran sunan nasa"ya sameer fa magana nake"anan ne ya iya samun bakin magana ya amsata"ya sameer kuma?yaushe na zama yayanki?ko kuma ince yaushe daddynki ya gaya miki bayan ke ya haifa miki wani d'an uwa sameer? Bata damu da zancen da yake ba haka taci gaba da magana,ya sameer don girman Allah kayi hak'uri da duk wani abu daka sani nayi maka ko kaji labari nayi ma wani wallahi sharrin shaidan ne!!what?? Kinsan kuwa me kike fad'a 'Yar jami'a??shaid'an fa kika ce?yarinya karki kuskura kiyi wa shaid'an k'azafi don kuwa bai miki komai ba!ganin yadda sameer lokaci guda ya tada jijiyoyon goshi yasa beauty sulalewa da gwiwoyi k'asa ta d'ago hannayenta sama tace ba don hali na ba ya sameer don girman mahaliccinka ka taimaka ma rayuwata,wallahi kana son jefa min rayuwata acikin mawuyacin hali!
Dariya sosai sameer ya sakar mata har yana sark'ewa,sororo beauty ta bishi da kallo don tasan tabbas hakan zai faru dama!ke malama ki tashi muje ki nuna min hanya na koma gidan tsoho na jira Alhaji acan lokaci na k'ure min!cewar sameer yana gyad'a kai na mugunta!narai beauty ta kuma yi da ido tace haba ya sameer yanzu lokaci kake dubawa ba hatsarin da rayuwata take ciki ba?yanzu ashe yadda kake kiran sunan Allah dama duk a baki ne?ya sameer ka tausaya min mana!ganin yadda beauty ta duk'ufa da rok'onsa yasa shi had'e rai a karo na biyu ya daka mata tsawa"wai ke wace irin mace ce? nace ki tashi muje ko in baza ki ba just tell me sai na nemi mafita ama ba ki tsaya kina min wani zance mara anfani ba!
Ajiyar zuciya beauty ta saki can kuma ta mik'e jiki ba kwari ta kad'e k'asa da ta shafi kayanta ta shiga tafiya,bin ta sameer yayi tayi yana kuma k'ara gane hanya sosai har suka iso,har ta sa kai tana k'ok'arin shiga zaure taji yace ke? Da sauri ta juya kamar dama jira take tace na'am ya sameer!wani irin duka ya kai ma bango a zuciya kafin nan ya d'ago kai da tuni sun rud'e sun ja jur yace ba na ce karki k'ara kirana da ya sameer ba?call me wit my real name sameer don bana karb'ar tuban d'an muzuru,sannan kisani in har kina so asirinki ya rufu sai kin min Alk'awarin zaki sanar min da duk wani labari naki da dalilin da yasa kike wannan mummunan halayyar taki!saurin d'ago kai tayi jiki na b'ari beauty ta amsashi tana nuni da hannu wallahi duk abinda kake son ji zan gaya maka amma ba yau ba sai ana gobe zamu koma kaga yanzu lafiyar tsoho ya kamata mu kula da ita,kai kuma in Alhaji ya kiraka sai kasan abinda zaka gaya masa wannan shine kad'ai alfarmar da za kai min!
Kallo mai cike da buk'atar amsa sameer ya jefeta dashi ran nan sam babu alamar annuri haka yasa hannu ya tureta can gefe daya ya shige gida abinsa!
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
136-140
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Bai takura mata sameer ba har sai da tayi kukan ma'ishinta don kanta ta tsaya,sannan ta d'ago kai a hankali ta kalle shi,har lokacin sameer kan shi na gareta don haka ya kauda kansa a sanyaye ganin yadda beauty tai narai da ido,murmushin k'arfin hali ta saki mai cike da tambaya sannan ta dai-daita nutsuwarta ta shiga magana,"yau zata zamo rana wacce ban yi tsammanin kasancewarta a rayuwata ba,sai dai ina k'addara ta riga fata,babu yadda na iya dole na bud'e sirrin da bai kamata na bud'e shi ba don kuwa bani da wata mafita,ya sameer kamar yarda kasha kirana da sunan karuwa ban tab'a inkari akan haka ba, don duk wanda yasan hajara da halayya irin tawa dole duk sunan da aka kirani dashi na amsa,sai dai abinda baka sani ba koma ince jama'a basu sani ba game dani shine,wannan d'abi'a dole ta sakani yinta ba don naso ba!don kuwa na samo wannan halin ne"
Adalilin principal d'in makarantarmu ta secondary school,da jin haka k'ara gyara zama sameer yayi sosai yana fuskantar ta don jin abinda ta ambata,nan ta ci gaba da magana,eh haka ne magana ta ba k'arya principal d'inmu itace ummul abaisi na duk rayuwar da muka tsinci kanmu aciki,sanin kan kane dai dady bazai sani makaranta mai arha ba,makaranta ta ajin k'arshe wajen tsadar kud'i wanda duk 'ya'yan masau kud'i yawancinsu nan suke yi anan nayi primary don haka bayan na gama na d'ora secondary,anan ne kuma wata rana muna zaune a aji da yake mun zo s.s.s3, bazan tab'a mantawa ba muna karatun geography sai ga discipline master yazo har aji ya kiramu mu uku,jiki na gyarma muka bishi duk mun gama bayarwa dukanmu zaiyi,sai bayan da muka fita ne yake shaida mana cewa principal ke nemanmu,haka ya samu gaba har office d'inta,bayan daya kaimu ne labari ya fara canjawa dayake mace ce principal d'in tana washe baki ganinmu ta shiga zayyana mana buk'atarta ta hanyar wayo da dabara"ta shaida mana cewa yanzu mune ajin k'arshe sannan tasan fatan kowannenmu shiga jami'a nan ta cigaba dacewa ita jami'a ba'a shigarta haka nan sai an shirya haka dai taitayi mana bayani muna ganewa ta kuma shaida mana da tazab'e mu muyi mata wani aiki ne saboda tasan 'yan gidan masu hannu da shuni kamarmu babu zancen takurawa ko matsantawa ta iyaye a tattare damu!bamu gama gane inda ta dosa ba sai da discipline master ya k'ara wayar mana da kai da cewa duk kanmu yana so mu kar muyi applying makaranta d'aya ta yadda zamu cimma burin janyo hanakalin malamai maza,ko wacce d'aliba ta yi k'okarin kawo nata toh darajarta zata k'aru sannan akwai wasu mak'udan milliyoyin kud'i da bayan shekara hud'u za'a bata!jin yadda suke jaddada miliyoyin kud'in anan yasaka kowannen mu amincewa,hakan ya saka bamu tashi a wajen ba duk sai da aka bamu somin tab'i na naira dubu d'ari biyu da hamsin!tare da yarjejeniyar ya zama sirri a tsakaninmu,toh tundaga wannan ranar kullum sai mun je office d'in principal bayan an tashi a makaranta ta k'ara wayar mana da kai yadda zamu janyo hankalin malaman jami'a yayin da muka shiga!
Hankalin ummah ya fara tashi in ban manta ba tun daga ranar data fara ganin d'abi'u na da tarbiyyata ta canja duk da dama ba wani tsauri nake samu ba tunda dady na nan kuma baya son b'acin rai na,kullum rigimar daddy da ummah bata wuce akai na,haka har mukayi jarabawar waec da neco amma duk ummah ta lura ba wani karatu nake ba illah dai kad'e-kad'e da wak'e-wak'e da suka zama jikina,ga kud'i da nake kashewa baji ba gani,wasu dady ke bani wasu kuma principal ke turamin ta account tunda duk ta bud'e mana account,wata rana dana karb'o kud'i daga banki ko dana shigo gida na taradda dady a parlo dole nima na zauna,dana tashi mik'ewa ne tsautsayi hannun jakar ya bud'e wasu mak'uden kud'i suka zubo,wato a lakacin ba ummah da dady ba harta ni kai na sai da gaba na ya yanke ya soma gyarma,amma da yake dady baya son ganin laifi na sai yayo sauri mik'ewa ya fara kwasar kud'in ya mayar min jaka sannan ya kamo hannu na mukayi d'akina,turani ciki kawai yayi shi kuma ya wuce nashi d'akin a ranar ne ummah ta fara gaba da ni wai na fara samun kud'i daga waje,wanda ni kuma tun daga lokacin na fahimci ummah bata so na,bata son cigaba na arayuwa daddy ne kad'ai ke so na!
Haka rayuwa ta jin dad'i da daula taci gaba da wanzar min har ya kawo lokacin da na samu admission zuwa jami'a ranar ji nayi tamkar na zama millioner gani nake nesa tazo min kusa,da murna haka na kira na shaida musu,wanda suma murnar sukai tayi min!
Tun kafin sati d'aya da fara shigowata jami'a tuni na ziyarci duk wani kanti na kaya,mak'il haka na cika drawers dina kaf da k'ananan kaya,takalma da jakunkuna,duk da naso siyan gyale ko da k'anana ne amma principal ta hanani acewarta zasu rage min kwarjini kuma zasu b'oye min kyaun halitta!
Shiru beauty tayi da ta kawo nan a hirarta ta kai hannu fuska,mak'alallen wahayen dake shirin sauka a kuncinta ta goge had'e da jan majina!tsintar kanta tayi beauty ta k'in ci gaba da labarin har sai da ya nemi da taji gaba sannan tayi gyaran murya taci gaba!
Tun daga ranar dana shiga jami'a tunani na bai wuce ta wacce hanya zan samu na cimma burina cikin sauk'i ba,sai kuwa gashi na samu malam umar,mutum na hannun dama a b'angaren neman mata da kud'i na iya samo kanshi don na sakar masa kud'i iyakar sakarwa kafin ya had'a file guda na duk wasu sirrika na malaman makarantar ya bani,ita kuma k'awata zee-zee tunda na fahimci 'yar abi yarima asha kid'a ne sai na rik'eta na fara sakar mata kud'i don sune matsalarta duk da agidan ma bata tsiraba,mahaifinta mutumin kirki ne ga kula da hak'k'in iyali amma mahaifiyarta 'yar Allah bamu musamu ce,ita dai a bata kud'i shiyasa kullum cikin samari masu mota take wai a haka baban na sa ido kenan!
Ina ganin wannan shine abinda kake son ji ko?
Tana tambayar ne tare da maida dubanta ga sameer tana kallo!d'ago kai yayi shima dai ya kallota don abinda yake da muradin ji har kawo yanzu bai jiba nan take kuwa ya fara jefo mata tambayoyi!
"Daga shigarki jami'a zuwa yau malamai nawa kika had'ata dasu?kuma ke nawa ne sukai anfani dake?
A kid'ime beauty ta zaro ido cike da mamakin tambayarsa ta k'arshe inda shima ya zaro mata nasa da zummar eh amsarta yake jira!tab'e baki beauty ta yi sannan ta kauda kai gefe guda cikin murya can k'asa tace mutum goma na kai mata,ni kuma babu,ban gane babu ba?babu me?sameer ya tambaya! sunkwui da kai sosai beauty tayi don tasan bai zama lallai sameer ya yarda da amsarta ba ta k'ara nanata masa da babu d'a namiji ko d'aya da muka tab'a keb'ewa ko ta minti biyar a wajen makaranta dukkan ninsu a waya muke magana bayan na fahimci yanayin mutum toh sai na bashi address nata,wannan shine silar da ya saka ko wane course bana fad'uwa tun shigata jami'a kawo yanzu!
Shima prof KAS da kaga abu ya had'amu na zagaya kuma na zagayo na ga babu wata hanya da zan iya samun makin da nake so dole sai nayi masa abinda nayi masa shiyasa hakan ta faru,bata kai ga rufe baki ba wata tambayar tabiyo baya"toh abincin da kike rabawa na stop and chop shi kuma sadaka ce ko kuwa zakkah?kai duk'e tana kallon k'asa tace shi kuma neman suna ne kawai da son shahara don sun tabbatar min hakan zai saka kowa ya san da zamana a jami'a!
Shi kuma kamal dana ganku tare a mota wancan satin darasi yake koya miki?
a'a beauty ta bashi amsa sannan tace shima munje can sau biyu!
Wani gauran numfashi sameer ya saki mai cike da tuhuma ta b'angare d'aya kuma yana jin dadin yadda yake kallon gaskiya tsagoronta a idanun beauty !dole ya danne yanayin da yake ciki kwallon hannayensa wanda yake wasa dasu ya watsa mata su cikin zafin nama wanda hakan ya matuk'ar raxanata ta d'ago kai a tsorace ta dubeshi"ta mau fuskar nan babu alamar wasa balle murmushi haka ya shiga binta da wani mugun kallo sai can kuma cikin dakewar murya ya shiga magana yana nuna ta da yatsa"kin cuci kanki wallahi,banza, wawuya, asharariya,wacce bata san ciwon kanta ba balle na wasu shin kina tsammanin da haka zaki samu kud'i da wannan mummunar d'abi'ar,amma dai tur da halin kawaliya mace mai neman maza a gari tana kai wa wata can!kin zama akuya mai komai tq samu ya zama nata!don haka ina so ki sani wannan labarin naki karki tsammani abin so ne a wajena,babu abinda ya haifar miki illar tsantsar k'iyayya a fili wanda in kin lura zaki ganta cikin kwayar idanuna!kuma da kike batun kina samun nasara a jami'a toh ki rubuta ki ajiye wannan semester d'in sai kin samu matsala da course d'ina,don na d'au alwashin haka tun ranar da kika tozarta prof a gabana,kika wulak'anta tsohon da bai ji ba bai gani ba!maganata ta k'arshe a wajenk kuma sak'oni d'an ladi ya bani cewar yana sonki da aure,kuma a matsayina na wanda Alhaji yake ganin girma har yakan zauna muyi wasa da raha na furta masa na bashi ke,sai dai kuma kash ina ji masa takaicin namiji salihi zai auri mace mai hali irin naki wacce take wa kanta kirari da 'yar jami'a!
Yanda ya gama lura sameer da k'ofofin kan beauty sun riga da dun gama kullewa da munanen kalaman da yake jefarta dasu ga wasu zafafan hawaye da suka kasa tsayuwa a kumatunta ya sashi mik'ewa a fusace har yana buge k'afarta ta hagu yayi gaba ya barta nan jikin bishi cike da damuwa!
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
141-145
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Cike da damuwa tare da danasani haka beauty ta mik'e ta nufi gida cikin mawuyacin hali"shiru ta samu gidan wanda hakan ya tabbatar mata cewa tsoho sun fita da Alhaji zagayen yamma don ya motsa jikinsa, bata zame ko ina ba sai d'akin su d'an ladi a ganinta wannan shine mafi kyawun lokaci daya dace ta yi magana da sameer,sallama biyu tayi amma duk ciki babu wacce ya amsa mata,ga kuma takalmansa a bakin k'ofa wanda hakan ya k'ara tabbatar da ita cewa yana ciki,ba ta damu da jin haka ba sai ma kamo labulen d'akin tayi ta rik'e ita bata shiga ba,ita kuma bata lek'a ciki ba ta fara magana cikin murya k'asa uwa mai rad'a"nasan ya sameer duk abinda ka kira ni dashi wallahi na cancanta amma kayi wa girman Allah wannan magana ta zama sirri tsakanina da kai don idan har sirrina ya tonu a gidan nan wallahi na mutu,nasan dai zuciyarka akwai Allah a ciki,kaji k'aina ya sameer tunda kaga dai ban b'oye maka komai game da ni ba,kai ma ka tausaya min!dariya sosai ta juyo daga ciki har kana jiyo shak'ewarsa saboda dariyar mugunta can kuma sai ya nisa yace ho ho ho gaskiya yaro a kullum dai yaro ne,ke baki ji kunyar aikata laifi ba sai ni kike rok'on naji kunyar tona miki asiri,ai ki d'auka asirinki a fili yake,yanzu dai ki shirya karb'ar hukunci daga Alhaji kawai!cikin wani mawuyacin hali na jin sunan da sameer ya ambato yasa ta yaye labulen da saurin ta ta afka cikin d'akin tana fad'in kayi wa Allah kayi hak'ur.... chak ta tsaya tsaye idanunta suka kafe waje d'aya sakamakon toxali da idonta yayi da sameer kwance saman katifa daga shi sai vest da k-aramin short,kasa dauke ido daga kallonsa tayi wanda shima a tsorace ya tashi zaune yana d'an kare jikinsa da hannu!ganin abin bana k'arewa bane haka yasa shi saurin mik'ewa ya nemi jallabiyarsa ya zura sannan ya juyo a fusace ya wurgo mata wani mugun kallo yace lafiya zaki shigo min d'aki ko sallama babu!a sanyaye beauty ta iya sauke kanta k'asa don bata da abinda zata iya cewa yanzu!komawa sameer yayi gefe da gadon ya zauna yad'anyi shiru!
Dan girman Allah ya sameer kayi hak'uri mana tun d'azu fa nake baka hak'uri ko dan kaga ana lallab'aka shine kake ta wani ja min rai"cike da b'acin rai beauty ke d'aga murya tana maganar!bata tsaya nan ba taci gaba abinta,toh wallahi kaje duk wanda zaka fad'a mawa ka gaya masa tunda kai baka da tausayi,kaje kai tayi,juyawa tayi ta nufi k'ofa sai faman banbami take ita ala dole rai ya b'aci!tana kai k'ofa bakinta ya furta"bama Alhaji ba kaje ka gaya wa mai garin garinnan shine zaka nuna min cewa kai sunanka sameer!
Yaye labulen d'akin tayi a zuciye zata fita taji tayi karo da mutum tsaye!k'ara kai hannu tayi beauty ta yaye labulen baki d'aya!karaf ta dawo a baya ganin tsoho tayi tsaye gefensa Alhaji duk kanninsu fusa babu annuri musamman Alhaji,k'arasowa cikin d'akin sukayi baki d'aya kafin kowa ya ankara ji kake tasss ... Alhaji ya kaiwa wa beauty wani zazzafan mari! sululu beauty tayi nan wajen ta zube k'asa sumammiya!wani irin tsalle sameer yayi sai gashi gaban beauty yana jijjiga ta!amma ina babu alamar motsi take duk wani launi na sameer ya rikid'e daga fari zuwa ja don rikita,ganin yadda ta kafe bata motsi yasa tsoho fashewa da kuka yana fad'in wallahi zuciyarka ta sa yau ka kashe min jikata d'aya da bani da kamarta a doran duniya!kuka sosai tsoho ke yi yana sambatu,lura da haka da sauri Alhaji yayi waje bai jima ba sai gashi rik'e da butar ruwa a hannu baba yagana na biye dashi domin bacci take tayi abinta kukan tsoho ya tasheta!ruwan sameer ya karb'a ya shiga yayyyafa mata inda baba yagana ke jijjigata,wani gauran numfashi na wahala beauty ta saki a hankali kuma ta fara bud'e idonta wani dishi-dishi ta fara gani har ta kai ga bud'e idanunta gaba d'aya"sannu kowa ya shiga yi mata ita dai ba magana sai gyad'a kai,hannun Alhaji tsoho ya kamo yace tashi muje waje mu basu waje,ba musu haka ya tashi ya bisu ya rage saura su uku,baba yagana itama mik'ewa tace bara je na samo miki ruwa ki sha!tana fad'in haka ta fice!k'ara lumshe idonta tayi can ciki-ciki ta ji sameer ya ce sannu!ido rufe ta amsa shi,daga nan kuma shiru ya biyo baya!
_08:00p.m(na dare)_
Tsoho ne zaune gefensa Alhaji sai sauran mutanen gida in banda d'an ladi da duk yammacin yau baya gida!gaba d'aya suna zaune a d'akin tsoho kamar yadda ya umarta!bayan da suka gabatar da sallar isha'i!" Sallama da salati ga fiyayyen halitta ya farayi wanda hakan ya ke nuna akwai wata muhimmiyar magana da zaiyi sannan ya fara da"na taraku ne ba don komai ba sai dan abinda ya faru ga jikata hajjo,duk da dai bamuji komai akan hirar da kuke d'azu ke da yaron nan sameer ba amma tunda har kike rok'on kada Alhaji ya sani hak'ik'anin gaskiya abin bazai xamanto mai kyau ba,don haka baza mu takura ku da sanin wani sirri game daku ba sai dai yana da kyau duk yanda nake ji dake hajjo in naga kinyi wani abu ba dai-dai ba na tsawatar miki don hakan shine mafi k'ololuwar soyayya da zan nuna miki! haka tsoho ya cigaba da yi musu nasihohi masu tsuma jiki da sanyayasu,bayan ya gama ne Alhaji ya d'aura daga inda ya tsaya duk da Alhaji kusan duk fad'a ne nashi da jan hankali,sosai nasihar ta shige su musamman beauty da taron don ita ne! Inda daga k'arshe tsoho ya rufe taro da addu'a yana musu albishir da su xauna cikin shiri gobe akwai abin al'ajabi A k'auyen nan!Dariya duka suka saka inda anan beauty ta samu bakin magana tace watak'il in tsoho zai raka mu mota in zamu tafi zai mana rawa da k'afa d'aya don ya tabbatar mana ya samu lafiya!baki daya suka k'ara kwashewa da wata dariyar tsoho yana mai bata amsa da in har ta kama gobe na juya jiki ai sai nayi!cikin raha,da wasa da juna haka suka rabu kowa ya nufi d'akinsa don kwanciya shiko Alhaji yayi sallama dasu ya fice!
[10:15am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
146-150
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Bayan fitar Alhaji da kusan awa guda sai ga d'an ladi ya shigo hannunsa rik'e da bak'ar leda guda biyu,zarcewa ya yi d'aki inda ya iske sameer kwance akan katifa yana waya da ummah waje ya samu ya zauna har ya gama sannan sameer ya jiyo yace haba mutumina yau ina ka shige haka daga cewa ka bani waje na kafa soyayyarka azuciyar yarinyar nan kawai sai ka b'ace sai yanzu?murmushi d'an ladi ya saki yana d'an girgid'a kai ya d'ago idanunsa sama yace ai yau babbar rana ce agareni kaga kuwa bai kamata nayi wasa da ita ba,tun bayan rabuwarmu dai ban zame ko ina ba sai wajen aminina d'an mai gari can naje muka sha hira duk na baci labarin komai game da hajara kai in tak'aice maka labari shine ya bani naira d'ari biyar da na siyo mana wannan naman!janyo ledar d'an ladi yayi ya mik'o d'aya yace kaga wannan shine namu shi kuma wancan daka ganshi a k'ulle na gimbiya ne"dariya sameer ya saka can kuma ya nisa yace Allah mutumina?kace yau dad'i zamu ci,ai tana can shiga ka mik'a mata kafin tai bacci,washe baki d'an ladi ya shiga yi yana k'ara gyara zaman hularsa akai sannan ya d'akko ledar ya jiyo ya kalli sameer yace ya ka gani d'an birni!jinjina kai yayi da zummar gamsuwa da yadda ya ganshi yace wannan kwalliyar tayi mijin hajjo!cike da jin dad'in sunan da sameer ya kirashi dashi haka ya bar d'akin!
Wai wa yaga 'Yaar jami'a an yi auren k'auye??ai kuwa da musamman zan d'auki katin d'aurin aure na kai jami'a ko dan asha dariya!maganar da sameer yayi kenan cikin raha bayan fitar d'an ladi!
Kwance take beauty duk da ba bacci take ba, amma kana ganinta kasan hankalinta baya tattare da ita tuni ta lula duniyar tunani,har d'an ladi ya zaune nesa kad'an da ita amma bata san da zaman saba,sunanta daya kira ne ya maido da ita hayyacinta,a d'an tsorace ta d'ago kai gani d'an ladi zaune gefenta yasa ta saki wata k'aramar tsuka ta koma ta kwanta!gyaran murya ya fara yi sannan ya mik'o mata ledar!ganin bata karb'a ba yasa shi aje mata ledar ya mik'e zai fita kenan yaji tace ka dawo ka d'auki ledarka na k'oshi!bai bi ta kanta ba d'an ladi ya fice abinsa yana mai cike da farinciki na ko ba komai dai ta kalleshi kuma yasan abun sune kawai na mata na filako amma tana da buk'ata!
Baba yagana dake kwance can lungu da gado ta rufa da abin rufa ta bud'e tace in kin k'oshu ji mik'o min na lashe tunda abin wariyar launin fata ne bai kawo min ba ya biye miki!yamutsa fuska beauty tayi sannan ta mike zaune ta janyo ledar ta bud'e nama ta gani sai k'amshi ke tashi nan tai faro da ido tace loh tashi baba mu ci nama ne ashe!haka baba yagana ta sakko suka nad'i namansu tas suka cinye shi,ruwa suka sha suka koma gado anan ne kuma hira ta b'arke tsakanisu,tun fara hirarsu babu abinda baba yagana ke wa beauty nasiha dashi in banda sirrin zaman gidan aure,duk wasu hanyoyi na tarairayar miji da neman soyayya wajen mai gida babu wanda baba bata labarta mata ba,har takai beauty na mamakin yadda baba tasan wad'an nan bayanan ita da take k'auye,basu suka tsagaita da hira ba sai can tsakiyar dare suka samu suka bi lafiyar gado!!
_11:00a.m(na safe)_
Tsoho ne tsaye bakin k'ofar d'akinsa shirye cikin farar shadda da malin malin waxce tasha guga,Alhaji yayi sallama ya shigo cike da girmamawa haka suka gaisa suka nufi hanyar fita waje har sun kai zaure Alhaji ya dawo ciki ya nufi d'akin su d'an ladi suna zaune suna hira shi da sameer koda ya shiga suka gaisa nan ya kalli d'an ladi yace maza ka tashi ka shirya ka sameni kai d'aya a babban masallacin juma'a na tsakiyar gari!toh d'an ladi ya bisa dashi da haka Alhaji yayi waje ya basu waje!
A b'angaren baba yagana kuwa tun tashinta asuba take tsaye gaban murhu sai girke girke take yi ga wata tukunya can k'arama da lokaci zuwa lokaci takan bud'e ta motsata,bud'ewar da tayi ne na k'arshe taga tukunyar tayi don haka ta juye ta a k'aramin kwano ta nufi d'aki da ita!
Tana shiga ciki zaune ta tarar da beauty tayo wanka tana kwalliya sosai yau kwalliya take cab'awa abinta na komawa gida,kallo d'aya baba yagana tayi mata ta saki dariya tace lallai yau ana gayu anan ita kuma wannan kwalliyar fa?juyi tai da ido beauty tana d'aure d'an kwalin doguwar riga pink data saka,tace wannan kwalliyar komawa gida ce don ni duk na k'agu mu tafi na huta da surutunki!kwanon baba yagana ta ajiye gabanta sannan tace bari zumud'i nan da awa biyu zuwa uku zaki tafi gida nina na huta yanzu dai gyara zamanki kici wannan!yamutsa fuska beauty tayi sannan takai hannu ta bud'e kwanon,kaza ta gani ciki tasha kayan had'i ga romo jikinta sam babu kayan miki,d'ago kai tayi ta dubi baba tace wannan kuma meye?kaza ce mana!ku kuma haka kuke dahuwar kazarku anan toh ni dai d'auki kayanki na k'oshi,da jin haka baba yagana ta samu waje ta zauna,ai kuwa baki isa ba nai miki dahuwa kice kin k'oshi ko ya ya ne sai kin ci,cewar baba!ba don ta so ba haka beauty ta zura hannu cikin kwano ta d'an d'eb'o kad'an ta saka baki!cauu...taji abu ya kama bakinta,su beauty abin nema ya samu ai tuni ta gyara zamanta ta fara kwasar romanta,sai da taci kusan rabi da kwata na kazar nan banda romo da ta sha ta k'oshi sannan ta ture kwanon gefe guda tace Alhamdullah,cike da jin dad'i baba ta janye kwanon daga gabanta ta fice abinta ba tare data tanka mata ba!
12:00p.m( na rana)
Busa sarewa da ganguna kad'ai ke tashi ta ko ina,duk unguwa ta karad'e da hayaniya,ko da sameer ya lek'o ya tambayi baba ko lafiya sai ce masa tayi itama bata sani ba jiran dawowar su Alhaji take!
Ba'a yi minti 30 da maganar ba sai ga tsoho ya shigo gida da sallama cikin sauri ya nufi ma'ajiyar tabarma ya d'auka yayi waje"zaure yajeya shinfid'a wa manyan bak'i sannan ya dawo ciki,sunan yagana ya shiga kira haka ta fito a d'aki da sauri tana lafiya?abincin bak'i zaki mik'o da alamar fahimta haka baba yagana ta nufi inda ta jere kayam abinci data gama ta jidi mik'a masa yana fitarwa waje har ya gama!
Bayan wasu mintina da basu fi goma ba sai ga Alhaji ya shigo gida yana kiran sunan sameer,sameer dake tsugunne gaban k'aramar jakarsa ta kaya yana k'ok'arin zuge zip d'inta don ya gama shirya kayansa tsaf ya ji muryar Alhaji,amsa shi yayi ya fito hannu rik'e da jaka"sororo Alhaji yayi yana kallonsa sai kuma can yace ina zuwa haka?susa gyeya yayi sannan yace dama zan kaita motane kafin ku dawo muyi sallama!ahiyar zuciya Alhaji ya sauke sannan yace toh ajeta anan gefe kazo muje zaure ana buk'atarka acan!umarnin da aka bashi yabi haka ya bi bayansa bayan a jae jakar suka nufi zaure!
[10:25am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
156-160
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Daga fitar baba yagana bata zame ko ina ba sai d'akinta inda ta tarar da beauty kwance tana ta waya abinta dariya sosai take yi da alamar wayar da take tana jin dad'inta,waje baba ta samu ta zauna tana jiran gamawarta,ba wani lokaci mai tsawo ta d'auka ba sai gashi tayi sallama sa wadda ta kira da zee-zee sannan ta kashe wayar,kallo ta kai wa baba sannan tace ma,aikaciyar tsoho ya kayi ne?harara baba yagana ta watso mata sai tace saboda kin rai na ni nice ma'aikaciyar tsohon?dariya beauty ta maida mata ba amsa,gyara zamanta sosai baba tayi sannan ta juyo ta fuskance ta sosai,sunanta ta kira,beauty ta amsa tana k'are wa wayar ta kallo"hajara ina so ki nutsu kuma ki saurareni da kyau kisan cewa ita wannan duniyar kome muke aikatawa dama muk'addari ne daga Allah sannan mafiyawancin abubuwa na rayuwa da muke ganinsu ba alkhairi bane toh sune mafi Alkhairi a wajenmu amma mu bamu sani ba,don haka ina yi miki umarni amatsayi na na 'yar uwar mahaifiya a wajenki wacce nasan ko ita mahaifiyar taki zan gaya mata taji,daki ji tsohon Allah a zamantakewarki ta rayuwa,sannan yi biyayya ga na gaba dake domin abinda suka hango miki na ci gaban rayuwa ke bazaki tab'a hango shi ba,nasan yanzu baza ki fahimci me nake nufi ba Amma in kika koma gida ummanki zatai miki cikakken bayani,a k'arshe ina miki addu'ar Allah yayi miki albarka! Beauty ta amsata da ameen!
Tana kaiwa nan a maganarta baba yagana ta mik'e ta nufi jerin samirunta dake mak'ale a cikin kwabot ta zaro wata k'aramar samira bud'eta tayi ta janyo k'ullin dake ciki a rufe a bak'ar leda,beauty dai na biye da ita da ido har ta dawo ta zauna,hannun beauty ta riko ta saka mata shi sannan ta maida ta rufe nan tace hajara ki adana wannan zai miki anfani duk ranar da Allah yasa kika tarr a d'akin mijinki ko bayan rai nane kafin mu'amala ta auratayya ta had'aku ki tabbata kin jik'ashi da ruwa kin sha"hannu ta kuma kaiwa k'ark'ashin gado inda ta janyo wani farin mayafi ta yafawa beauty sannan ta saki murmushi tace toh haka yau zaki komawa ummanki nasan zatai farin ciki in ta ga wannan gyalen jikinki!
Kalaman baba yagana duk sun gama d'aurewa beauty kai inda kunya ta gama lullub'eta dan jin maganar baba ta k'arshe na abinda ta bata,don duk wasansu basu tab'a magana irin haka ba!
Suna cikin wannan hali ne suka ji shigowar tsoho da Alhaji,sunan yagana suke kira baki d'ayansu dan haka cikin sauri ta fito tana tambayar ko lafiya?Alhaji ya tambaye ta ina yaran suke?suna cikin d'aki! Yana jin haka ya shiga kiran sunayensu a tare,sameer ne ya fara fitowa d'an ladi na rik'e da hanunsa gaba d'ayansu fuskokin nan babu alamar annuri,sai can ga beauty ta fito rike da jaka a hannu,tsoho na ganin yanayin beauty sam babu alamar damuwa ko b'acin rai a tattare da ita cike da zolaya yace lallai yaran zamani wato ke farin cikin tafiya ma kike ki barni ko?itama dai cikin wasan ta maida masa da ehh mana ni daman duk a k'age nake na koma garin mu,dariya tsoho ya saki sannan ya tsagaita tak'aitacciyar nasiha yayi musu sosai mai tsuma jiki inda duk ciki jan hankali ne da hak'uri ga al'amuran rayuwa sannan ya sanar dasu cewa basu kad'ai zasu tafi can ba har da Alhaji da wasu mutanen!toh kawai suka amsa da shi sannan suka fiddo kayansu baba yagana na rik'e da hannunta har suka fito waje!
Cincirindo na mutane da motoci,beauty ta soma gani tun fitowarta inda nan take gabanta ya yanke ya shiga fad'uwa cike da d'unbin mamaki ta kalli baba tace wannan mutanen fa haka baba?da yake baba yagana ta shirya ma amsa wannan tambayar tuntuni don tasan ba makawa sai ta afku nan take ta bata amsa da nad'in sarauta akayi shiyasa kika ji unguwar ta rikice Alhaji aka baiwa muk'ami don haka in kunje can gida an nutsu sai ki masa tayin murna!toh ta amsa ta dashi da haka ta kaita har inda motar sameer take ta bud'e ta shiga gidan gaba ta zauna,haka tana kallon Alhaji ya shiga wata mota doguwa fara tare da wasu jama'a kana ganinsu kaga mutane 'yan alfarma,inda d'an ladi ya rako sameer har bakin mota sukai sallama beauty na masa bankwana amma yadda yayi shiru uwa bai ji taba don haka itama ta basar don ta lura da yanayin nasu gaba d'aya yai sai a hankali,ko b'acin ran rabuwa da juna ne oho musu!
Tafiya suka shiga yi cikin nutsuwa haka yake tuk'in inda motoci uku ke bayansa a jere,tun bayana shigarsu mota babu wanda ya iya ko da kwakwkwaran motsi baran tana magana,dukkan ninsu tunani tsagwaronsa ke cinsu sak'a wannan kunce wancan haka har suka yi nisa sosai a tafiyarsu,k'ishi daya taso masa ne ya janyo ruwa faro dake gefe dashi ya bud'e a hankali ya shiga sha,d'agawarsa ta k'arshe ne yasa shi kwarewa da sauri ya sauke ruwan ya shiga tari,jin yadda yake ta faman tari da alama ya kware da yawa ya saka beauty d'ago kai ta sauke dara-daran idanunta akanshi ba tare da wani tunani ba tace masa sannu ya sameer!banza yayi da ita uwa bai ji mai take cewa ba yaci gaba da tarinsa,ko zaka tsaya da motar ya fad'a maka?a raunane ya d'ago kumburarrun idanunsa ya sauke su akanta,kallon da yake watsa mata kad'ai ya isa ace tasha jinin jikinta,d'auke kai tayi daga kansa ta maida kan titi wanda hakan baisa ta tsaya da maganarta ba taci gaba,hmmn yanzu dai ba da bane da zaka kashe mota ka jibgeni,kuma kar kai tunanin abinda kai min abaya yanzu zan d'auke shi,wallahi bazan k'ara tsayawa wani namiji ya tab'a lafiyar jikina ba,kar kaga na saurara maka dama can saboda tsorona da Alhaji ne amma kaga yanzu yadda na d'akko hanyar gidan nan komai ta fanjama-fanjam,cikin b'acin rai da d'acin zuciya haka kalaman beauty ke dokar kunnuwansa,wato wani wawan damk'a daya kai hannu yayi mata saman kanta cikin zafin nama ya kai gab da gaban motar kenan zai buga,kamar daga sama ya ji maganganun baba yagana na dawo masa ....kaji tsoron Allah kuma ka sani hajara ta zama abin kiwo a wajenka......a sulale ya iya zare hannunshi daga kanta wanda tuni beauty ta gama sakin jiki taji inda kanta zai kasance taji an sake ta,hannunsa ya buga jikin sitiyarin motar yace"wallahi an cuce ni"an cuceni"why me? Dariya beauty ta saki ganin yadda yake ta faman haki kamar wani mayunwacin zaki,fari tai da ido kamar yana ganinta tace Allah dai ya kiyaye maza basuyi abun kunya ba,in banda matsoraci wake dukan mace?dariya ta k'ara sakar masa,inda abin duniya ya gama cika sameer CD na motar ya kunna ya k'ure k'arar motar k'ira'ar sudais ta hau tashi sosai ya shiga binsa ko ya samu sassauci a zuciya!
[10:25am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
161-165
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Misalin k'arfe 12;00p.m(na rana) a agogon hannun sameer wanda yayi dai-dai da shigowarsu gidan dady a parking space ya aje motar haka sauran motocin suma suka aje nasu!bara dai na wullar da kwallon mangwaro na huta da k'uda haka beauty ta fad'a tare da bud'e marfin motar ta fita abinta,hanyar shiga babban falo ta bufa ta kai hannu kenan zata bud'e k'ofa taji an riga ta turo k'ofa matsawa tai da baya gudun kar ta bige ta tsaya tana jiran ganin mai fitowa,ido ta zaro waje da gudu kumaa ta fad'a jikinsa dady ta gani tsaye ai kuwa ta shiga rero kukan shagwab'a tana bubbuga k'afa a k'asa,idan ran dady yayi dubu tuni ya gama rikicewa don babu abinda ke dagula masa lissafi irin kukan beauty,tambayarta ya shiga yi ko lafiya amma sam tak'i tanka masa,Alhaji da mutanen wajen haka sukai sororo suna ganin ikon Allah ganin abin nasu ba mai k'arewa bane yasa Alhaji yayi k'arfin hali ya k'araso wajen ya daka mata tsawa don yanzu ba halin dukan matar wani,dole ta janye jikinta daga na dady tabi gefe ta shige gida da gudu,babbar rigar jikin dady ya shiga gyarawa yana cike da fara'ar gani amininsa mahaifin sameer da d'an uwansa har da wasu mutum uku daga danginsa,cikin girmama juna haka ya k'arasa wajensu suka gaisa tare da yiwa juna murnar abinda ya had'a tsakani,haka sameer shima ya fito kai a k'asa ya gaida dady ya amsa,iso dady yayi musu dasu k'araso ciki nan suka d'unguma suka nufi falo,sameer dake tsaye yana k'ok'arin yin sashensa kamar yadda ya saba yaji Alhaji ya rik'o hannusa yana nuna masa hanyar falo dole ba don yaso hakan ba ya bi bayansa suka nufi ciki,ji yake a halin yanzu babu abinda yafi buk'ata irin kad'aituwa ba tare da wani ya shiga lamarinsa ba amma ya ya iya da lamarin Alhaji!.
A babban falo suka sauka nan hira sosai ta b'arke a tsakaninsu bayan nan ummah ta fito suka gaisa da yake tun safe tana kitchen da ma'aikata ana had'a abincin tarbar bak'i,nan da nan kuma aka shiga jere kayan ciye-ciye da tand'e-tand'e,sameer dai ido kad'ai yake iya binsa dashi don gaba d'aya tunaninsa baya wajensu,ga wani uban tagumi daya dasa kamar wanda akaiwa mutuwa,lura da hakan dady yayi nan ya kalloshin sosai yace sameer ki zaka je ciki ka d'an watsa ruwa ne?dady bai gama rufe bakinsa ba kamar dama jira yake sameer yace ehh dady!yana kaiwa nan ya mik'e ya nufi waje sai sashensa!
_4:00p.m (na yamma):_
Sameer ne kwance saman gado ya rufa da bargo duk da ba bacci yake ba amma dai idonsa a rufe yake,ya ji an bud'e k'ofar d'akin an shigo,bargon dake rufe a jikinsa yaji an yaye an shiga daddab'ar shi a hankali ya bud'e idanunsa karaf ya sauke su akan na Alhaji,cike da mamaki Alhaji ya k'ara kai hannunsa a wuyan sameer inda yaji zafi, meke damunka sameer?tambayar da yayi masa kenan!lumshe ido sameer yayi nan take kuma ya bud'esu ya sauke akan Alhaji, ya bashi amsa da babu komai!jinjina kai yayi na alamun bai gamsu da maganar sameer don haka yace toh tashi zaune muyi magana,ba musu sameer ya zauna ya zuba ido yana sauraronsa,sunansa ya kira samee sannan ya ci gaba da magana, A hak'ik'a njn gaskiya sameer na lura da rashin amincewarka da wannan abin alkhairi da nayi,tunda duk cikinmu ba yara balle su kasa gane halinda kake ciki,amma kasani banyi haka don na muzguna ma rayuwarka ba a'a sai dan na inganta ta,duk da nasan halayyarka da hajara ba d'aya bace sai dai kuma kai kad'aine zak iya zama da hajara a halin da ake ciki,don kuwa in har zaka iya rik'e sirrinta toh mene kuwa baza ka iya jura nata ba"ka d'auka wannan aure da aka had'a cigabane na rayuwarku baki d'aya kuma in har kayi hak'uri nan gaba zaka ji dad'in abin!
Shiru dai sameer yake,kai k'asa yana jinsa don haka ya ci gaba"sameer a yanzu ne ake auren soyayya mu da mukai namu ina muka san wata aba soyayya ai sai wacce iyaye suka zab'a maka amma kai fa har halayyarta ka sani kuma nasan duk wani abu nata ba wanda baka sani ba ciki da bai,sai dai bazan tauye maka hak'k'in ka ba sameer kai ma d'ana ne yanzu kamar yadda hajara take 'ya a wajena,gaya min meke saka kuka da har damuwa takai ka ga zazzab'i don daga jin jikin nan naka ba lafiya!
Mai makon sameer ya bashi amsar tambayarsa sai hawaye da suka fara bin kuncinsa,nan Alhaji yayi juyin duniyar nan amma sameer ya k'i magana har sai da yaji yace bari ya kira masa mahaifinsa ko shi zai iya gaya masa sannan yayi k'arfin hali murya can ciki yace Alhaji ni fa ina zargin hajara kuma kaga aure ai bazai yiyu da zargi ba?cike da mamaki Alhaji ya ke duban sameer had'e da nanata kalmar zargi a cikin ransa, dayake Alhaji bana yau bane kuma yasan halin da duniya ke ciki nan ya kamo hannun sameer yace,hakane maganarka d'ana aure baya yiyiwa da zargi amma ina rok'onka wata alfarma,nan sameer yace wace irin alfarma kuma alhaji?gyara zamansa yayi yace ina neman alfarmar ka tare da hajara a gidan nan kuma yau d'in nan idan har ka sameta yadda kake so toh shike nan idan kuma ka samu aka sin haka wanda bana fata toh ni zan baka alk'ami da takadda ka rubuta mata saki uku kwarara"d'ago kai sameer yayi yana kallon Alhaji yadda yake maganar da sigar gaskiya ainun!shiru yayi kafin nan ya gyad'a masa kao da niyyar amincewa sannan ya k'aro wani k'orafin yace"a aure na na ci burin yin shagali na gani na fad'a gashi hakan bai yiyu ba!nan ma dai murmushi Alhaji ya sakar masa sannan ya kuma ce waya gaya maka burinka bazai cika ba? Ai tun shekaran jiya dady ya dawo garin nan kuma na labarta masa komai ta wayar mai gari,kuma ni na umarceshi da karya sanar da hajara har sai ta dawo gida ta ganshi,yanzu haka maganar da akeyi yana can ya tarasu ita da mahaifiyarta ni yake jira mu sanar da hajara halin da ake ciki!da zarar ta sani zuwa dare dadynta da mahaifinka sun had'a k'ayatacciyar walima ko dinna ko me?a wani k'aton waje kuma duk sun gama gayyatar duk wasu wanda ya kamata a halarta kaga bayan daren yau duk shawarar daka yanke,inda yiyuwar ka tsara naka walmar daga baya kun tsara kai da matarka!yanzu dai bara naje can naga yadda zamu kasance!yana kaiwa nan ya tashi yayi waje ya bar sameer da wani sabon tunanin!
[10:25am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
166-170
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Beauty dake zaune gefen dady ta d'aura hanneyenta saman cinyarsa yana matsa mata su a hankali sai ummah dake gefe guda saman kujera inda ta bisu da kallo da haka suka ji sallamar Alhaji,k'ara so wa yayi ya samu waje shima ya zauna,wanda hakan ya dawo da beauty cikin hankalinta,take ta janye jikinta ana dady tanutsu sosai kamar ba ita ba,k'ara gaisawa Alhaji yayi da ummah sannan ya kalli dady yace masa toh Alhaji ai ina ganin sai ka sanar da ita komai ko!wasu k'anana muzurai da ido dady ya somayo alamun Alhaji yayi magana kawai shi basai yayi ba,don haka ya d'ora daga inda ya tsaya"hajara"Alhaji ya kira sunanta,cikin sanyayyar murya beauty ta amsashi tana sauke kai k'asa,Alhaji ya soma magana,wannan zama da mukayi anan ko kuma ince wannan taro da kike ganin ana ta yin shi tun daga can k'auye har kawo nan ba ana yi don kowa bane sai don ke"cike da mamaki beauty ta d'ago suka had'a ido da dady nan take dady ya kauda kai gefe,wanda hakan ya baiwa Alhaji damar cigaba a magana ina so ki saurare ni da kunnen basira kiji me zan gaya miki,a matsayinmu na iyayenki wanda suka gi cancanta da mu gina miki rayuwarki kuma mu zab'a miki mijin aure don haka yau mun sauke hak'k'inmu akanki mun had'a ki aure da d'an uwanki sameer !firgigit beauty tayi take kuwa ta mik'e tsaye cikin d'imauta tabi Alhaji da kallo idanunnan sun gama cika da hawaye amma sun kasa samun muhallin zuba k'asa,dumm...taji kanta yayi mata ta yadda take ganin abin uwa mafarki,lokaci d'aya kuma ta saki wata irin k'ara ta shiga shure-shuren k'afa uwa zararriya,dady ne ya yunk'ura zai yo kanta Alhaji yayo saurin tsaidashi da hannu badon ya so ba haka dady ya tsaya shima tuni hawaye ya gama cika idanunsa na tausayin 'yar tasa,wata irin gigitacciyar tsawa Alhaji ya watso mata take ta shiga hankalintabta tsaida shurin k'afar amma ta kasa dai na wayayen don tasan basu tab'a wasa irin haka da Alhaji ba,abinda ya faru tun daga had'uwarsu da sameer,zuwanta k'auye,kai kawo yai da zasu bar garin minjibir babu wanda ya k'ace mata a tunani,yadda baba yagana ta gaya mata nad'in sarautar Alhaji ashe duk ba haka bane,kukan da ya sameer yake yasan da aure na dashi ne?toh waye ya k'ulla abin nan,sameer?Alhaji ko kuwa tsoho?tunani sosai beauty ta duk'ufa yi ganin ba mafita yasa ta sulale wa kasan kafe ta shiga maida ajiyar zuciya mai cike da kukan zuci,ba ummah ba hatta shi kan shi alhaji sai daya tausaya wa halinda take ciki mazantaka kawai ya nuna don yasan aikin gama ya riga ya gama,a karo na biyu ya k'ara kiran sunanta,shiru ta bishi dashi,don haka sai bai damu ba ya ci gaba da magana cikin fad'a"aure d'aurashi yau akan sadaki dubu d'ari,wanda tuni na damk'asu ga mahaifinki,sannan ki zauna da shirin biyayyar aure ba hauka ko wauta ba,in kuwa naji wani abi sab'anin zaman lafiya, zan wanko k'afa har muhallinki na baki mamaki,kin dai san ni sarai?sannan daren yau ki shirya za'a yi walimar biki akai ki d'akinki!
Ko da Alhaji yazo nan a maganar shi sai ji tayi beauty ta kasa d'aukar girman maganar,ace yadda zamantakewa tasu take da sameer yau ita za'a kai d'akinsa?ai tuni ta mik'e wiwi ta shiga kuka tana buge-buge surutai barka tai marasa kan gado,sosai beauty take sharar kukanta kowa ya ganta a halin da take ciki dole ya tausaya mata,kasa jure hakan dady yayi da saurinsa ya k'arasa gabanta bai bi ta kan Alhaji ba tsum ya rungumota ta fad'a jikinsa ta shiga rero wani sabon kukan,kasa danne zuciyarsa shima dady yayi kafin kace me sun had'a kai da juna suna kuka,
Sororo Alhaji yayi yana kallon abin mamaki,takaici duk ya gama cika shi na yadda dady ya gama sangarta beauty,wani dogon tsaki ya saki tare da fad'in toh Allah dai ya kyauta,da haka ya nufi hanyar fita yayi b'angaren bak'i inda aka tanadar wa mahaifan sameer!
Bayan fitar Alhaji ne kuma ummah ta mik'e jiki ba kwari ta nufi wajen da su dady ke tsaye rungume da juna,hannun beauty ta rik'o a hankali ta d'ago kai tana kallonta,janye ta ta shiga yi daga jikin dady nan tayi hanyar d'akinta da ita amma har lokacin hawaye bai bar zuba a idon beauty ba"
K'ofar d'akinta ta bud'e tare suka shiga ciki, ta nufi bakin gado ta zaunar da beauty k'aramar kujera dake sak'ale gefen gado ummah ta janyo ta jinginata gaban gado ta zauna suna kallon juna!
Sunanta ummah ta kira,cikin kuka beauty ta amsata"nan kuma ummah ta fara magana"ya kamata ace kin tsaya da kukan nan hajara don bazai anfanar dake komai ba,tunda Alhaji ya zartar da hukunci,duk da d'an uwana ne amma a zahirin gaskiya ban ji dad'in sigar da yabi ya sanar dake wannan al'amari ba,sai dai ki sani hajara mu iyayenki muna sonki kuma baza mu tab'a aurar dake ga mutumin banza ba!amma abu d'aya da na lura dashi daga ke har sameer d'ib babu mai farin ciki da wannan abu,kamar yadda na lura da ranar tafiyarku minjibir karo na farko da kuka had'u a tsakar gida razanar da ki kayi bayan kin ganshi ce ta tqbbatar min da kun san juna a baya,don haka hajara ina miki magana a matsayina na mahaifiya agareki da ki ji tsoron mahaliccinki ki sanar dani shin meke tsakaninki da mijinki sameer??!!.
[10:25am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
171-175
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Meke tsakina da mijina sameer kuma?yanzu shike nan kowa kallon matar sameer zai na yi min?zancen zucin da ya k'are zagayensa cikin zuciyar beauty kenan,jin kuma ummah ta tab'ota da hannu yasa ta dawowa daga matsakaicin tunanin data shiga,hawaye na bin kuncinta haka beauty ta shiga zayyano wa ummah duk abinda ya faru bata b'oye mata komai ba kama daga kana principal d'insu har zuwanta k'auye'salati da sallallami ummah ta shigayi bayan da beauty ta gama bata labarin cike da mamakin yadda d'iyar cikin jal a duniya wannan abu ya faru da ita,abinda take ji a gari yau gashi a gidanta,ganin hakan bazai anfana mata da komai ba yasa ta share mak'alallen hawayen dake manne idonta ta d'ago kai tana duban beauty kafin daga bisa ni ta ci gaba da magana"hak'ik'a hajara na so tarbiyyarki ta k'arfafu fiye da yadda kike zato,na so na baki soyayyar da ke kanki sai kinyi alfahari dani nan gaba,amma ina kaddara ta riga fata,mahaifinki ya d'auki son duniya ya d'aura miki inda har ya cusa miki wasu d'abi'u da har kike ganin tamkar na tsaneki,baya son ganin laifinki akan komai,yanzu wa gari ya waya?ke kuka shi kuka,don ma Allah ya taimake mu raya sunna zaki ba wani abu ne maras kyau ba hajara da ya zami da kanmu,yanzu kina ganin da wanda zai miki kallon mai mutunci a jamiar da kike ikrarin wai ke 'yar jami'a!hak'ik'a ban ga laifin sameer don yayi kuka da aurenki ba!don shi ya san mai ya gani na aibu game dake!sai dai kuma koma meye hannunka baya lalacewa ka yanke ka wurgar dole nid'in nan dai nice uwa wacce kukan ki dana mahaifinki ya zama dole na share muku,zanyi anfani da kowacce irin hanya ta gari naga na dawo miki da martabarki ta 'ya mace wacce nasan shi kanshi sameer zai dawo yayi alfahari dake!
Yanda kuka ke bin kuncin beauty haka dariya ya bayyana saman fuskarta,da sauri ta matso gaban ummah ta rumgumeta ta shiga wani sabon kukan tana mai jin son uwartata sosai a rai!
_8:00p.m(na dare)_
Bugun k'ofar da ake a cikin gidan ne ya sanya sameer da ke kwance lullub'e da bargo fitowa daga ciki ya nufo a tsammaninshi zai ga Alhaji,saurin ja da baya yayi abin da ya gani yayi matuk'ar d'aure masa kai,amininsa ameenu ya gani tsaye cikin wata dakakkiyar shadda,fuskar nan d'auke da fara'a,dariya ameenu ya saki ganin yadda sameer yayi sororo yana kallonsa,tureshi ya d'an yi da hannu da zummar ya bashi waje ya shigo,haka ya matsa masa ya wuce ciki ya bar shi nan tsaye!kunya duk ta gama cika sameer ga mamaki tsagwaronsa da yake yi ta yadda ameenu yasan gidan dady,dole ya katse tunaninsa a daddafe haka yabi bayansa!zaune ya sameshi gefen gado don haka shima ya nemi waje ya zauna,kana ganin sameer kallo d'aya zakai masa kasan damuwa ta gama cika shi,fahimtar haka da ameenu yayi ne yasa ya kira sunansa a sanyaye ya amsa ba tare da ya kallo shiba,bai jira cewar ameenu ba ya yi gaggawar furta,wallahi ameenu ni kam an cuce n....hannu ameenu ya kai ya toshe bakinsa yace kar ka yi sab'o ko ka zargi iyayenka sameer,dady yayi min bayanin komai game da lamarin kuma ni banga wani ai bu ba tunda iyaye sun aminci wannan gyaran tsakaninku zaku yi shi,ba tare da wani yaji kanku ba,ka d'auka duk abinda ya faru tsakaninku a baya k'adsara ce da silar ganawa,wasu zafafan hawayen bak'in ciki ne suka fara kwaranya fuskar sameer,sosai ameenu ya tausaya masa amma ya zaiyi dole ya danne damuwarsa akai yayi masa nasiha kamar yadda dady ya umarce shi,nasiha da lallami sosai ameenu yayi masa wanda tun yana kukan harvya fara sauka a hankali yana biye masa a maganar,in da a k'arshe ameenu ke shaida masa ya rok'i dady da ya janye maganar dinner daya shirya a daren zuwa wani lokaci ba da jimawa ba ta yadda za'ai abu kowa na so ba ana ganin bak'in juna ba" haka kuwa dady ya amince,ya mutsa fuska sameer yayi kawai bai tanka saba don shi baya tunanin da ranar da zai iya son beauty a ransa!haka suka ci hirarsu ta ranar wanda duk akan maganar aurensu ne har dare ya fara ratsawa ameenu yayi sallama da sameer akan gobe zai dawo da yamma!!
[10:26am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
176-180
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Ko da ta fito beauty cikin kaya na atamfa riga da skirt d'inkin umbrella shape kayan sunyi matuk'ar karb'arta sai wani d'an yalelan gyale data bi jikinta dashi bayan jaka da takalmi k'irar vinci data cakare jikinta dashi, cikin nutsuwa da jin kunya haka ta k'arasa bakin motar da taga alamun mutum aciki duk da bata tab'a ganin motar a gidan ba da alama ya nemi anfani da itane don kar a gane suna tare, wanda ta ke da tabbacin tuni yana ciki ita yake jira,a hankali ta bud'e marfin motar,jikinta har wani gyarma yake wanda ita kanta ta rasa dalilin hakan ta shiga ciki ta rufo k'ofar,wani sanyin dad'i daya doki hancinta na turarensa yasa ta lumshe ido a hankali kuma ta bud'e su,ya sameer ina kwana,abinda ta iya furtawa kenan murya can k'asa!shiru taji tare da tada mota kamar bazai amsa ta ba har suka isa fita gate sannan taji yace lafiya,daga haka bai k'ara cewa komai ba har suka yi nisa da tafiyarsu amma da mamakinta maimakon su nufi hanyar jami'a sai taga ya karya kan motar ya shiga wani titi,zagaye ya shiga yi yana 'yan dube-dube da alama wani abu yake nema can taji yace yes tare da take burki,gaban wani kanti da aka rubuta womens parlo a saman shi,fita yayi ya nufi kantin, haka bai wani jima sosai ba sai gashi ya dawo hannunsa d'auke da leda mai layi-layi,haka ya shigo yaci gaba da tafiyarsa,bai zame ko ina ba sai bayan ZAHRAIN TWINS THEATER inda yasan yau lecture d'inta ana zatayi,waje ya samu ya tsaya tare da bud'e ledar kallo d'aya yayi mata yaga kalar kayan dake jikinta don haka wata hijab pink colour ya zaro ya wulla mata,kallonsa kawai tayi ba ikon magana don haka ta d'akko hijab d'in ta bud'e tare da sakawa,duk abin nan da take idon sameer na kanta har ta gama ta shiga k'ok'arin bud'e k'ofa zata fita,ke???ya fad'a wanda ya tabbatar da ita yake,tsayawa tai ta juyo ta kalleshi,kansa ya mayar a titi duk da duhun motar yace ki aje wayoyinki cikin motar kafin ki fita sannan in kin gama ki same ni anan sannan ki saka a zuciyarki yanzu ba da bace!daga haka bai sake cewa komai ba,ganin haka yasa beauty zaro jakarta a hankali tayi kamar yadda ya umarta sannan ta fita!.hannu sameer ya buga da k'arfinsa a kan sityarin motar had'e da cije harshe yace u re my destiny!can kuma kome ya tuno a hankali ya shiga jero addu'oi kafin ya kunna motar ya wuce office d'inshi!
Duk wani iri take jin ta cikin hijab karo na farko kenan da ta tab'a shigowa jami'a da hijab,duk inda ta waiga sai gani take kamar kowa kallonta yake duk ta gama tsarguwa da kanta,haka ta nufi cikin theater d'in can lungu haka ta manne jikin ta da bango,ta kuma kwantar da kai a jikin tebur d'in wajen,ba ita ta d'ago kai ba sai da taji alamar shigowar malami ciki,tana juyo fuska ido hud'u su kai kicib'is da wata d'aliba wacce idan bata manta ba a wasu lokutan baya itace wacce ta watsa wa jan biro jikinta sakamakon yabonta da sameer yayi,saurin kauda kai tayi zuwa gabanta nan ma dai idonta ya sauka akan lecturern da ya shigo Prof KAS ta gani sanye da tabaronsa hannu rik'e da marker yana 'yan dube-duben wasu takaddu,tun da tayi tozali da wad'annan abubuwan biyu beauty ta sadda kanta k'asa a kan wata k'aramar jotter dake gabanta ba ita ta d'ago ba sai da ta tabbatar da an rufe darasin d'alibar gefenta na shirin tashi rik'o hannunta tayi ta zaunar da ita,hak'urin abinda ya faru a baya beauty ta rok'a tare da nuna nadamarta akan hakan,da ya ke yarinya ce mai sauk'in kai nan take ta yafe mata,su beauty dai har da karb'ar lambar waya kafin su rabu!
Kayan karatunta beauty ta had'a itama ta nufo waje da shirin fita inda anan ne kuma kowa ya fahimci wace acikin hijabi sakamakon shigowarsu ba d'alibai kamar yanzu da yawa kafin kace me,cece kuce da gulmace-gulmace suka fara yawo,kowa na tofa albarkacin bakinsa,wasu dan tsabar gulma har lek'e suke dan tabbatar da abinda suke zargi,ganin haka cikin sauri beauty har tana tuntub'e haka ta fito a ciki ta nufi bayan theater kamar yadda sameer ya shaida mata,can gefe ta hango motarshi don haka ta nufi wajen,tana k'ok'arin bud'e motar taji kamar daga sama an kirs sunanta cikin kid'ima ta juya me zata gani? K'unyar nan da suka sameta wani lokaci a baya a stop and chop har sukai mata tayin shiga k'ungiyarsu,take suka shiga nuna mata wani mugun salo suna kashe mata ido,bata jira wani abu ba tai azamar bud'e k'ofar kamar wacce aka wullo ciki haka ta fad'o ta rufe k'ofar tana ta faman mai da numfashi!
K'arewa 'yan matan nan kallo sameee yayi tas sannan ya dawo da kanshi wajenta,ita dai kallon nata yayi bai iya ce mata komai ba ya tada mota ya bar wajen,cikin nutsu haka yake tuk'in motar yana zagaya makarantar har ya kai ga muhalin da yake son zuwa,waje ya samu ya tsaida motar ya fito a ciki sannan ya sunkuyar da kai yace mata fito,haka beauty ta fito don ta fahimci inda ya kawota ta bi bayansa suka nufi ginin dake gine a wajen,basu tsaya ba sai da sameer ya kai ga office d'in Prof KAS,nan yayi sallama aka basu izinin shiga suka shiga,zaune suka sameshi ciki kamar kullum yana nazarin littafi,gaisawa sukayi cikin girmamawa amma fuskar beauty ta kasa b'oyuwa a gareshi,duk da sameer ya bashi labarin komai da safe,don haka sai bai yi mamakin ganin 'Yar jami'a cikin wannan shiga ta kamala ba,sameer ne ya juyo cike da izzah ya watso mata wani irin mugun kallon da ya sa tuni tasha jinin jikinta,sunkwi da kai tayi kafin yace baki iya bada hak'uri ba ne? A sukwane beauty ta zube k'asa ta shiga rok'on Allah prof ya gafarta mata abinda ya faru a tsakaninsu,cike da mamaki prof yake girgiza kai na jin dad'in Alk'awarin da sameer ya d'auka masa na cewa sai ta durk'usa da k'afafunta ta nemi gafararshi,yau ga 'yar jami'a k'asan gwiwoyinta,haka dai prof ya amsa mata sannan yayi musu nasiha sosai game da zamantakewar aure,bayan nan kuma suka fito zuwa gida inda a kan hanyarsu na koma gida ne sameer ke tambayarta akan 'yan matan da ya gani,beauty bata b'oye masa komai ba haka ta kwashe labarinsu ta bashi,tab'e baki kawai yayi da jin haka ya ci gaba da tuk'insa!
Haka rayuwa ta ci gaba tsakanin beauty da sameer kullum shi yake kaita makaranta kuma ya d'akko ta tun jama'a basu gano komai tsakaninsu ba har suka gano,bayan da kuma ya nema mata malamin islamiyya kullum bayan sallar magriba yake zuwa nan gida suyi karatu,haka takan ware wani yanki na dare tana bitar karatunta,duk da babu wata kafa tayin anfani da waya gashi yanzu zee-zee ta daina shugowa makaranta kuma sameer ne ke kaita ya kuma dawo da ita babu damar ziyararta don ba wani hira ke shiga tsakaninsu dashi ba!a b'angaren ummah kam abin ba'a cewa komai don kullum da had'i na musamman da ake wa beauty hakan yasa duk ta ciko tai wani haske abinta!
A kwana a tashi ba wuya, yau ya zama ranar da su beauty zasu farar jarabawar k'arshen zangon karatu (wato 2 semester exams),tun safe ta gama shirinta tsaf,haka suka tafi a mota tana ta bitar karatunta sosai sameer yake yaba kwazo irin na beauty,kullum haka take fama da wannan karatun indai zasu tafi don ranar da bashi da aiki a jami'ar dole don ita yake shiga,da haka har ta gama jarabawarta!
[10:26am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
181-185
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Wayewar garin yau ta kasance asabar,sameer na zaune saman kujera cikin d'akinsa daga shi sai singlet da short yana zuma revenge game hankalinsa sosai ya raja'a a game d'in yaji knocking,k'afa ya d'na buga k'asa da alamun rashin son tsayuwa a game d'in sannan ya danna pause ya mik'e kanshi tsaye ya nufi bakin k'ofar don yasan bazai wuce Ali driver bane da yake jininsu yazo d'aya yanzu kusan kullum suna tare a d'aki yana masa tad'i,hannu yasa ya bude k'ofar lokaci guda kuma yana fad'in you are late... bai iya tsaida numfashinsa ba karaf idanunsa suka sauka akan beauty dake tsaye cikin kamala hankalinta naga hijabin da take 'yan wasanninta dashi,jin an bud'e itama yasa tai saurin d'ago kai,sak'onni suka fara saukarwa junansu ta ido cike da mamaki,har wani kyarma jikinta yake sanin bata tab'a ganin sameer cikin yanayin irin haka ba yasa tayi saurin kai hannu fuska ta rufe tace kazo dady na kiranka!tan kaiwa nan da gudu beauty ta ruga ciki cike da jin kunya,kamar wanda aka tsayar sameer ya bita da kallo har ta shige ciki sannan ya maido da dubansa anan murmushi ya saki mai cike da d'unbin tambaya yana susa kai,komawa ciki yayi ya zuro jallabiya a sama sannan ya fito!
Kwance beauty take saman cinyar dady yana wasa da gashin girarta,inda ummah na gefensu zaune tana binsu da kallo,sameer yayi sallama fallon ya shigo kai k'asa ya k'araso ciki,gefe ya tsugunna ya gaishesu kafin nan dady yayi masa iso daya zauna a kujera!bayan ya zauna ne dady ya kira sunansa a hankali sameer ya amsa shi cike da ladabi,cigaba dady yayi da magana" Dama na kiraka ne badan komai ba sai dan na ji meye shirye-shiryenka game da beauty nah saboda a halin da ake ciki ta gama jarabawa kuma kamar yadda mahaifinka ya shaida min da zarar ta gama zaku tare,wannan shine mak'asudin kiran naka!
Eh dama dady ina shirin da nake nayi sallah azahar dama na shigo nan domin na sanar maka akan cewa sati mai zuwa zamu wuce abuja tunda ranar asabar mukayi passing out na bautar k'asarmu, cewar sameer da har kawo yanzu kansa na duk'e k'asa!jin jina kai dady yayi sannan yace toh Allah ya kaimu lokacin!ummah ta amsa shi da ameen,shiru dai beauty take duk jinta take wani iri tun bayan shigowar sameer wanda kawo yanzu hira suke tayi a tsakaninsu banda ita can taji dady ya lakato hancinta yana fad'in yanzu zan huta da rigima,sai kije can kiyi ta masa shagwab'ar taki!cuno baki gava tayi uwa mai shirin kuka tace dady ni d'in ko?yadda tayi maganar a shagwab'ance yasa dukkansu sakin wata dariya,sameer ne ya mik'e yana k'ok'arin barin waje dady ya kira sunansa,har lokacin dariya na d'auke saman fuskarsa yace tsaya ta biyo ka can ku bamu waje muyi magana da mahaifiyarku!hannu yasa dady ya shiga d'agota tana nok'e kai wani kallo da ummah ta watso mata yasa tuni tasha jinin jikinta tayi tsum ta mik'e tana wani cuno baki gaba ta bishi sukao waje!
Tafiya yake sameer tana biye dashi har ya shiga d'akinsa gaban gado ya samu ya zauna ya barta anan tsaye,ganin bai yi mata tayin zama ba yasa itama neman waje gefe k'ad'an dashi ta zauna har lokacin hannunta na rik'e da gefen hijab d'inta tqna 'yan wasanninta dashi!
Wayarsa sameer ya janyo yaci gaba sa game d'inshi wanda a zahirin gaskiya kana ganinsa kansan hankalinsa da inda ya raja'a yana cikin haka yaji an masa game over,take ya saki wani guntun tsaki yayi cilli da wayar saman gado,sai kuma shiru ya biyo baya!ganin wannan shine karo na farko da masoya biyun suka tab'a keb'e kansu sai ya zamana fargaba ta mamaye su,k'arfin hali sameer ya d'anyi ya katse shirun nasu da cewa?kin yi shiru kamar bakya magana?ganin yadda yayi maganar cike da izzah yasa ta maido masa amsa dai-dai da tambayarsa"ai naga wajen daga ni sai kai kar nai magana yau ma ya zama laifi,shiru sameer yayi maganar ta d'an so ta dake shi don ya fahimci inda ta dosa haka ya ci gaba da magana yana fad'in"ai yanzu kin girma baran dake ki ajiki ba sai dai a zuci?baki bud'e beauty ta juyo tace a zuci kuma?ai dad'in ta dai ita zuciya ba'a ganinta bare ka illata min ita"har wani yamutsa fuska take yayin maganar"wanda hakan ya baiwa sameer damar sakin wani guntun murmushi sannan yace ni ko a gani na kafin na kai hannu jikinki zuciyarki na fara kaiwa,domin idan baki manta ba ranar da kika fara shiga lecture a jami'a bayan kin gama kin shiga econs faculty wanda har ki ka fad'arwa wani kyakykyawan matashi wayarsa,alokacin basarwa kawai nayi na wuce sanin cewa dana jima tsaye zaki iya suma don azabtaccen kamun da nai wa zuciyarki,haka ne?yanda yayi tambayar yasa beauty tsuke fuska tamau tamkar bada ita yake ba, tabbas ta tuna yadda taji lokacin da tayi karo dashi don har tana iya kwatanta kyawun fuskarsa a idonta!dariya sameer ya soma sosai ganin ya gama gano lagwanta,da haka kuma sannu a hankali hira mai k'arfi ta fara shiga jakanin masoyan biyu,damar da sameer ya samu ne yasa shi labarta wa beauty abinda ya faru cikin satin inda ya shaida mata cewa an kori malam umar daga jami'a sakamakon wata sabuwar d'aliba da yayiwa ciki,iyayenta suka k'i yarda sannan ya sanar mata yasa an chafko principal tare da discipline master yanzu haka suna hannun jami'an tsaro kafin a tura su kotu!
Shiru beauty tayi tare da juyar da walwalarta zuwa fushi,tausayi tsagwaronsa kake iya hangowa a idanunta ga wani mak'alallen hawaye dake shirin zubowa!
Take sameer ya dawo gabanta ya tsugunna had'e da tarba hannunsa a fuskarta yayi sauri tarbar hawayenta a hannunsa,a hankali ya shiga share mata yana lallashinta,sai daya tabbatar da samun nutsuwarta sannan ya tallabo kumatunta ya shiga magana"Ban yarda a gaban idona ko abayana ki zubar da hawaye ba,kamar yadda ban yarda ki sake wata rayuwa nan gaba ba tare da ni ba, a baya na jahilci kai na game dake ashe abin ba haka yake ba,shiyasa a kullum nake d'aukar abinda ya faru akanki matsayin k'addara a gareki,a kullum ina godewa Ameenu don ya zamanto aboki na gari shine yayi ta nuna min yin hak'uri da juriya don samun alkhairin abu,yanzu princess d'ina gani tsugunne gabanki ina neman yafiyar laifina!
Da jin haka beauty tayi saurin rik'o hannayensa ta shiga yi masa nuni da ya tashi amma sam sameer ya k'i ala dole ta iya furta masa ta yafe!
godiya sosai yayi mata sannan ya shiga yi mata nasiha"inda aciki yake cewa" hajara yau na kira sunanki akaro na farko ba dan komai ba sai dan na sanar dake abinda jami'a ta k'unsa,ki sani ita jami'a da aka kira sunanta mahad'ace ta kowanne irin abu hala mai kyau ko akasin haka,muhalli ne na kazo nazo da mutumin kirki da na banza duk zuwa suke kuma kowa da manufarsa,yawancin iyaye ko jama'ar gari sukan kawo cewa a jami'a ko wane masha'a da alkhaba'i ke faru,wanda ba hakan take ba,tarbiyya ana fara tane tun daga gida,rashin samun kyakykyawar tarbiyya kamar wata k'ofa ce na bud'e b'arna ga al'umma,kinga wasu matan sukan yi anfani da jikinsu,wasu kuma suyi an fani da kud'i haka ma daga mazan yake shiko malami buk'atarsa d'aya kuma da ya samu toh ya wuce wajen,amma kinga duk da haka akwai na Allah wad'anda a komai nasu tsantsar gaskiya da rik'on amana suka saka a gaba,kamar dai Prof KAS,saboda haka na yanke shawarar canja miki jami'a sakamakon fahimta da nayi yanzu kin kasa sakewa da nan d'in,mutanen ciki kamar dodonni kike ganinsu,sanadin canjawa da kikayi kina ganin kamar kowa na miki kallon 'yar jami'a ta baya,bayan mun koma abuja zaki ci gaba da zuwa jami'a kuma karatu zaki yi har sai kin gaji tun da dai matar tawa ta kira kanta 'yar jami'a!duka na wasa beauty ta kai masa yayin da yayi saurin gocewa yana dariya!jan hankali sosai sameer ya yi mata kafin ya canja labarin zuwa yadda shagalin dinner d'insu zai kasance wani satin!
[10:26am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
186-190
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Kome aka sa wa lokaci toh alal hak'ik'a sai yazo,yau take asabar wanda shirye-shiryen tafiya tsaf sun gama had'uwa,a inda dady yayi musu jagoranci,ali driver ya kai su airport suka wuce abuja,ko da suka isa can sameer ne yayi wa dadynsa waya aka zo aka d'auke su,sai dai ummah tuni ta gama tsara inda zasu sauka gidan babbar aminiyarta inda a can ne 'yan uwanta da abokan arzik'i zasu taru,dole ba don yaso rabuwa da beauty ba sameer ya sauke su acan kafin ya wuce gida,bayan isarsa gida ne sameer ya iske ameenu da tun ranar litinin ya taho don ya shirya masa yadda dinner zata kasance,wanda ya tarar tuni an gama komai lokaci kawai ake jira!
_8:00p.m(na dare)_
Dandazon motoci ne na alfarma kana ganinsu kaga zallar ajiyar naira aciki ke ta faman tururuwar shigowa gidan can tsakiyarsu wata doguwar mota ce bak'a tasha wanki sai kyalli take wanda da alama ango ne aciki,haka suka jero suka yada zango a tsakar gidan,yadda abokansa ke fitowa daga motoci cikin kaya na alfarma wanda suma dai sukai ankon shadda blue wanda ita kad'ai zai gaya maka cewa bikin manya ne,hira da dariya kawai kake iya jiyowa ta kowane yanki,sameer dake cikin mota zaune ne ya fito a tare wani irin ihu suka sake ganin ango yasha wanka na had'uwa shadda black ce sanye jikinshi tasha zubin aiki golden colour d'an senegal,sai hula da takalminsa duka baki,hannun nan sanye da agogo itama golden,tattare a lallausar farar fata irin ta sameer abin dai ba'a cewa komai,zagaye shi suka zo sukayi kowa da irin tashi salon tsokanar can ameenu ya lek'o ta cikin mota da yake shi ya tuk'o sameer yace ango lokaci na tafiya fa akira amarya ko naje na fito da ita!wani kallo sameer ya wurga masa sai kuma can yace toh ai sai kaje ta fito da ita mu gani,gaba d'aya waje aka sa dariya wasu na fad'in jealousy!! Abin shina sai ya dawo yana bashi dariya dole ya zura hannu cikin aljihu ya fiddo waya ya shiga laluben lambarta,bugu biyu ta d'auka nan ya shaida mata zuwansu,ko me ta fad'a daga d'aya b'angaren ya bata amsa da ok my princess;da haka ya kashe wayar aka ci gaba da hira ana jiran k'arasowarsu!
Wani lokaci kad'an bayan wannan hayaniya ce ta 'yan mata had'e da gud'a kake jiyowa wanda duk dangin ummah ne na yola da ta sanar dasu bikin suka xo sai kuma 'yammatan gidan da suka fito ga wani k'amshin turare daya lullub'e gidan tun bayan fara fitowarsu,inda 'yan matan amarya suka sanya beauty a tsakiyarsu duk kan ninsu sanye da anko,baka iya hango komai daga shigarta,tafiya suka shiga yi basu zame ko ina ba sai jikin motar sameer inda suka zagaya suka shigar da ita sannan suma suka nufi sauran motocin suka shiga,duk wani zumud'i da rikicewa sameer ya gama yinshi burinsa kawai yayi ido hud'u da gimbiyar tasa don haka cikin sauri shima ya bud'e motar ya shiga" watabarakallahu ahsanal khaliqeen"abinda sameer ya iya fad'a kenan jikinsa na kyarma ya matso daf da beauty ya kai hannayensa biyu ya d'ago ta daga sunkwi da kai da tayi,karaf suka had'a ido wani shu'umin kallo suka shiga jefar junansu dashi inda ko wannensu baki d'auke da murmushi na farin ciki" a haka ameenu ya ja motar saura na biye dashi suka bar gidan,yayin da a hankali beauty ta maida dubanta k'asa tace ni kam ka bar kallo na haka"daga k'asan zuciyarsa ya sako wata dariyar had'e da k'ara matsowa sosai ya matse jikinta da nashi,shinshina k'amshin jikinta ya shigayi,yanda yake bin wuyanta da shinshina yasata fara janye jikinta tana tureshi taji can kamar mai rad'a yana fad'in ki barni naji k'amshin matata ko kuma yanzu labari ya canja,ya zatayi da sameer ta san halinsa idan ya fad'i magana dole ba dan taso ba ta barshi ya ci gaba da abinda yake inda sak'onsa ke ziyartar kwakwalwarta tana karb'a!
Karya kwanar da akai ne aka shiga wani k'aya taccen hotel ya tabbatar da beauty da an k'araso wajen inda cincirindo na motoci suka rigaya suka cika wajen,a bakin event hall d'in ameenu ya tsaida motar a inda sameer ya fito ya zagayo ya bud'e waa beauty k'ofa ya rik'o hannunta k'am kamar wacce za'a kwace masa take masu nan da nan aka fara ruwan d'aukar hoto sai alokacin sameer ya iya k'are mata kallo wanda ita ma dai doguwar bridal gown ta saka bak'i wuluk ta bi jikin nan nata,sai head d'in ta golden da takalminta,sosai beauty tayi kyau,don duk yawancin hotunan sameer na kallonta ake yi,lura da haka yasa ta d'an b'ata fuska tanai masa rad'a ka kalli mai camera mana !shima ya rad'a mata nak'i wayon!dariya suka sa a tare kamar daga sama taji ana mata magana ta baya inda akace amarya ta sha k'amshi,muryar data doki kunnenta yasa ta saurin juyawa don tabbatar da zargin da zuciyarta ke yi mata,nan tayi tozali da zee-zee dake tsaye cikin ankon da ita kanta bata san dashi ba don ta lura kusan kowa yayi ankon,a d'an rikice ta kira sunanta tana nunata da yatsa,cike da jin dad'i zee-zee ta matso tace mata juya bayan dinner mayi magana,haka beauty ta juya sameer ya k'ara manna hannayensu suka nufi ciki!
Sabon kid'a aka saki inda jama'a kowa ya mik'e don tarbar ango da amarya a nutsu suka nufi ciki k'awaye da abokai na take musu baya har suka k'arasa mazauninsu daga nan ne kuma shagalin biki ya fara a yanayinda kake iya hango abokan ango da danginsa suna zubar kud'i sam babu k'anshin tausayin naira tare da su,haka daga b'angaren dady da ummah kowa ya baje kwanintarsu ga 'ya d'aya tilo da suka mallaka a duniya,taro yayi taro can ummah ta hango dady na kwaso shoki na kud'i yana sauke wa a goshin 'yar tashi,dariya kawai ta saki cike da jin dad'i don in da sabo ummah ta saba da halin mutanen nata biyu,jama'ar waje kowa ya gani dariya yake,haka shagali ya ci gaba har kusan 11:na dare inda daga haka jama'a suka shiga watsewa,shima ango ya rik'o amaryarsa suka shiga mota zee-zee na biye da su!hira akai tayi cikin motar ana maida zancem dinner haka har suka k'araso gida nan ne zee-zee tai sallama da ameenu itama dai haka sukai sallama da sameer har ta juya zata tafi ya kira sunanta murya a k'ank'ance yace pls kar ki late bacci nake ji" a kunyace beauty ta shige gida da gudu zee-zee ta bi bayanta,a tare suka saki wata irin dariya sameer da ameenu ganin abinda ya faru da haka suka shige mota suka fita a gidan!
[10:26am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
191-195
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Tun bayan shigar beauty gida basu zame ko ina ba sai d'akin da aka ware mata inda ta shigar da zee-zee ta kuma kullo k'ofar,saman kujera suka zauna beauty duk ta gama d'okin ta ji labarin,sai kuma ta ji zee-zee tayi shiru tab'o ta tayi da hannu tace wai ke dilla ki fara bani labarin mana,murmushi zee-zee ta saki sannan ta gyara zamanta sosai tace,toj sarkin son labari bud'e kunnenki kiji da farko dai kamar yadda na labarta miki a waya nayi sabon saurayi mai kayan harka,toh wannan yaron kusan shine silar duk wani abu daya faru domin kuwa bayan sati da had'uwarmu ya min kyautar mota ta azo a gani dole na je inda nake aje waccan tsohuwar motar wacce nace miki itama bani akai amma ba wanda ya sani a gida bayan mama,na had'a su biyu yau na hau wannan gobe na hau waccan,fantamawa kawai abuna nake har ta kai a unguwa kowa yasan da sake mota ta,ana haka kwatsam na dawo daga jami'a wata rana ina shiga ma'ajiyar motar kwatsam muka ci karo da baba wanda nasan ba makawa ni yake zaman jira,ranar nan k'arshen danasani sai da nayi ta,don dukan da nasha ranar kamar bazanyi rai ba ga horo mai tsanani na ya cireni daga jami'a babu inda nake zuwa kullum ina gida zaune,na tak'aice miki labari mai kai bolar gidan mu wato almajirin layi ya fini daraja a gidan nan,ba anan abin ya tsaya ba har mama sai da ya shafa gida baba ya turata a karo na farko azamantakewarsu halin yanxu dai bai jima da dawo da ita ba,maganar bikinki kuma lamba na gani an kira ni a waya koda naji namiji ne da kamar bazan magana ba saboda 'yar jami'a na wahala....kul kar ki sake ce min 'yar jami'a kirani da sunana hajara,beauty ta katseta!dariya zee-zee ta saki tace shegiyar gari wato kin ji jiki ai na samu labarin komai ke dai bari na gama miki,haka taci gaba da cewa bayan na amsa wayar ne ya labarta min komai cewa shi abokim sameer ne wanda zai aure ki kuma yana da buk'atar mu had'u da yake hajara na shiryu sam banji nauyin b'oye masa komai nawaba don kar yaga na hana sa gamuwa dani yayi zaton ko wulak'anci ne bayan ya gama ji ne yace ma bashi lambar baba,duk da ina gudun yim wani laifin amma daya matsa dole na bashi,da haka mukai sallama!
tun lokacin ban sake jin shiba sai lahadin data wuce ina zaune tsakar gida ina wankin kayan yara naji shigowar baba kallo d'aya yayi min ya kauda kai sai ji nayi yace kiji waje da bak'o zakuyi magana,wani rass gaba ya fad'i sanin cewa bazai wuce cikin abokan baba yake son had'ani da wani don ya zama horo a gareni ashe abin ba haka bane sai dana fita muka gaisa naga saurayine kuma ba laifi kallo d'aya na yaba dashi amma dana ji shine ameenu da mukai waya a baya sai na saki jiki mukai magana ya kuam shaida min da baba ya amince kuma akan gobe litinin tare zamu taho anan abuja na yi wasu shirye-shiryen biki,da yake had'uwar farko ce sai na kasa sakewa dashi sai da muna kan hanya zuwa nan yake shaida min cewa ya nemi aure nane a wajen baba duk da bai ganni ba amma ya yarda da nadamar da yaji daga gareni,tuni na shiga godiya ga mahalicci na hajara na k'ara yadda cewa Allah na tare da mai tuba yayin laifi,toh tun daga haka kawo yanzu wani son shi nake ji har bana son naji bana tare dashi,ai kin gane,k'arashe maganar zee-zee tayi tana kashe mata ido na wasa haka suka wkashe da dariya a tare,suna haka suka ji ana bugun k'ofa beauty ce tace waye?can suka ji muryar yarinya tace wai aunty hajara ke zo d'akin sama ana nemanki!toh kawai beauty ta amsa da sannan ta mik'e tace ina zuwa da haka ta nufi hanyar fita!
D'aki ne cike da iyaye mata hira sosai suke yi haka beauty tayi sallama ta shiga can tsakiyarsu ta hango ummah don haka ta nufe ta,ummah gani ta fad'a kanta a k'asa,kafin ummah tayi magana Aunty balaraba tace tashi ki shiga bayi gani nan zuwa"toh kawai tace nan ta mik'e ta nufi bayi,waje ta samu a ciki ta tsaya tana 'yan dube-dubenta ciki taji shigowar aunty,wankan magarya tare dana turaren mata aunty tayi mata duk wan sak'o da lungu na jikin beauty sai data tabbatar data wanke shi tas sannan ya samh turare, bayan sun gama ta rik'o hannunta suka fito wani k'aramin labule da ke sak'ale a d'akin suka nufa suka shige ba wani abu cikin banda kayan mata da turaruka ga wata drawer can ta kaya nan ta ciro mata kayan da ummah ta tanada mata lace ne dark blue tasaka sannan ta d'aura mata alkebba d'inta bak'i a sama,k'arshen kyau beauty tayi shi ita kanta dubin kanta amadubi ta hau yi,sai data gama shirya caf bayan kayan shaye-shayen data bata,kafin nan suka fito,gud'a tsofaffin gurin suka hau yi ummah dake zaune tabi 'yar tata da kallo don sosai tayi kyau tankar ba ita ba,tasan cewa tabbas yanda taso ta aurar da 'yarta hakan ya kasance, tsakiyar d'akin aunty balaraba ta zaunar da ita sannan ta samu waje itama ta zauna,nasiha da fad'a haka mutanen nan suka shiga yi mata tun tana iya jure hawayenta har suka fi k'arfinta,suna haka suka ji alamar bud'e k'ofa wanda hakan ya tabbatar musu cewa dady ne ya dawo tare da mijin aunty balaraba,kuka ne ya k'ara ciyo beauty sanincewa dady ne da kansa yace zai kai ta d'akinta,mik'ewa tayi da gudunta ta fad'a jikin ummah ta shiga rero wani sabon kukan,tsintar kansu sukai daga ita har ummah cikin kuka,can aunty taga wannan kukan nasu ba mai k'arewa bane dole ta rabo beauty da ummah tayo waje da ita,a bakin motar dady beauty ta iske zee-zee na ta kukan rabuwa da k'awar tata nan itama ta k'ara kecewa da wani kukan dady dake gaban mota zaune tuni ya fara matsar kwalla jin rurin kukar 'yar tasa,da haka tana kuka tana ihu aka sata mota suka tafi!
A tsadadden gidanta wanda a hak'ik'anin gaskiya sameer yayi k'ok'ari matuk'a wajen tsara shi dady ya kai beauty har d'akinta sai dai sam ya kasa ko kwakwkwaran magana sai kuka da suka d'unguma sunayi rarrashin duniya mijin aunty yayi amma ina sam sun k'i ji dole ya kamo hannj dady tare da rufo mata k'ofa suka fito!
Sameer dake sashensa zaune shin da ameenu da jin k'ugin tashin motar su dady wani tsalle ya doka yana fad'in yes ta shigo gidana!tuni ya soma sauri yana shiryawa,wanka yayo har da d'oro alwalarsa sannan ya fito shadda brown colour ya saka ya feshe jikinsa da turare sannan ya d'ago kai yace da ameenu ya ka gani?jinjina da hannu ameenu yayi masa sannan yace gaskiya mutumin ba k'arya yau zaka koya wa 'yar jami'a hankali,wani mugun kallo sameer ya watso masa,take ameenu ya saki dariya yace sorry aboki mantawa nayi princess,mik'ewa tsaye yayi daga zaman daya ke yace to ni dai baru na wuce tunda an kawo mana ita but pls kabi ta a hankali kasan ita fa yarinya ce kar la sauke mata nauyi,wani wawan duka sameer ya buga masa a baya har yana duk'adda da baya ameenu yana dariyar mugunta yayi waje yana fad'in sai mun had'u gobe, bai amsa shi ba sameer sai ma wata nannauyar ajiyar xuciya daya sauke ya k'ara duban kansa a madubi sosai sannan ya fito ya nufi sashen beauty!
[10:26am, 16/01/2017] Àúńţý jîđđĕřh: 📓 *'YAR JAMI'A*📓
_BY_*HERWWERH JIDDERH*
*A.K.A*
*PRINCESS QUE~DEE*
*THE END*
💕In Devotion to yuh my Dearies:
*ANEESA ABUBAKAR RIMI*
*(NEESAHLURV)*
&
*UMMEE ADNAN*
*(TAWAN)*
Ko da ya isa bakin k'ofa sameer turowa yayi ya shiga inda ya sameta can zaune tsakiyar gado ta had'a kai da gwiwa da alamun kuka take,sallama yayi sannan ya k'arasa ciki saman gadon ya nufi a hankali ya shiga yaye mata alkebbar daga fuskanta,d'ago fuskanta yayi cike da tausayi ga kuma wani sonta da yake fizgarsa a halin yanxu ya shiga share mata hawaye yana manna ta a jikinshi,sai da ya tabbatar tayi shiru sannan ya d'ago fuskarta ya sakar mata murmushi,a daddafe itama ta mayar masa sannan yace my princess yau bani da sauran magana tunda Allah ya mallaka min ke don haka tashi muje mu fara gabatar da sunnah sai mu dawo nan,ba musu ya rik'o hannunta suka tashi bayi ya shigar da ita tayo alwala sannan suka gabatar da sallah,gaban kanta ya kama kamar yadda yake yayi mata addu'a sannan ya mik'e ya fita bai jima ba sai gashi ya dawo rik'e da tray na kayan tab'a wa a baki,ba wani sosai ta ci ba haka ya d'auke kayan yana mai ce mata ki shirin bacci bara na kai kayan waje,yana fad'in haka ya fice!
Tashi tayi beauty ta shiga cire kayan jikinta zuwa na barci kamar yadda aunty ta nuna mata night gown d'in da zata saka wata light pink iyakar gwiwa haka ta janyota ta saka hannu ta saka tana d'an janyo rigar k'asa amma ina tak'i sauka,beauty take taji duk kunya ta gama kamata can kuma ta tuna da wani abu da sauri ta nufi wata k'aramar jakarta dake nan ta fiddo wani k'ulli neman ruwa tayi ta rasa nan ta bud'e k'aramin fridge da ke d'akin ta janyo ta zuba a cup,k'ullin maganin da baba yagana ta bata ne ta tuna don haka ta d'akko ta kad'a a cikin ruwan ta shanye,haka kuma cikin sauri ta maida ta ajiye ta nufi gado,bargon dake linke a saman gadon ta shiga yaye shi kwanciya tayi ta rufa ruf har kanta!
Tana kwance har bacci ya d'an fara fizgarta taji alamun bud'e k'ofa shigowa sameer yayi amma ganin har ta kwanta yasa shi laluben madannin wutar ya rage hasken d'akin, kafin ya wuce can d'ayan gefen gadon ya kwanta,koda ya kwanta sunanta ya kira amma da mamaki yaji shiru,jim ya d'anyi sanin cewa ba bacci take ba yasa shi murginawa a hankali har inda yake,hannu ya kai ya sak'alo bayanta dashi take ya sauke ajiyar zuciya"jin har lokacin babu alamar zata motsa yasa ya maida hannunsa saman kanta,hular dake sanye akanta ya zame take ya hau shafar suman kanta a hankali uwa mai neman wani abu aciki!
Yadda yake wasa da gashin kanta sosai take jin tsigar jikinta tayi yarr ta tashi,saurin kai hannunta tayi saman nashi tajanye,ya sameer ka bannj ni bacci zanyi,haka ta fad'a tana maganar uwa wacce ta fara bacci,k'ara matsowa sameer yayi sosai har yana iya jiyo saukar lumfashinta haka ya kara bakinsa saitin kunnenta ya fara magana yana ci gaba da shafar gashin nata,my princess bazan hanaki bacci na kinji amma yana da kyau ki min abinda zanyi marking dix night as my best night ever kinji,na son kina so na kuma zaki iya sadaukar da komai naki domin ni pls baby ki bari ko tab'a jikin ki nayi na samu relief,kin ji?em em ni ka rabu dani ya sameer bacci zanyi?beauty ta fad'a har lokacin tana k'ok'arin raba jikinta da nashi amma ta gaza hakan,can ya nisa yace ok naji but atleast tell me something pls,nan ya matso da kunensa saitin bakinta yace all ears dear?duk a takure beauty take jinta yadda ya ke shige mata se take jin duk ba dad'i haka ta rad'a masa in na fad'a zaka sake ni nayi bacci na? Da sauri ya bata amsa da yes dear had'e da ci gaba da shafan kanta!
Da jin haka a hanakali beauty ta shiga juya harshenta tana fad'in:
_To night i feel so happy,i feel that i have not reached any where in my lyf,i have not made my goals,my dreams,i feel that i was just born again,that i have to start over,and it makes me a little scared bcox i have never comes across such moment in my lyf till now,and i have never thought i would feel this way;you have showed me all over wit ur luv and carez thanks yuh so so much my prince!_
Wani wawan hugging sameer ya kai mata yayinda ya k'ara manne jikinta da nashi sosai yana fad'in
_My angel u must be a fantastic runner bcox now u are always running in my mind before i neva thought sameer will fall this way but now i do so for dat pls permit me 2 know more of u!_
Yanayin da sameer ke maganar kad'ai ya wadatar ya gama kashe wa beauty jiki take ya fara aika mata wasu irin zafafan sak'onni tun tana kauda kai tana janye jikinshi daga nata har ya kai ta fara karb'a tana maida martani,take jikin sameer ya hau kyarma yamda yake jin beautu sosai tare da shi,labari ya soma canja wa laluben jikinta ta ko ina yake har ya cimma burinsa,kuka da ihu babu irin wanda beauty batai tun kana iya juyo sautin kukanta har muryar ta ya dishe dan azaba sosai sameer ya shigeta,haka daren sababbin amaren biyu ya zama cike da jin dad'i!
Bayan da sameer ya dawo daga sallar asuba ne ya shigo d'akin wanda har lokacin beauty kwance tale tana maida baccin wahala,gabanta sameer ya je ya zauna tare da yaye bargon da take rufe da shi can kuma wata zuciyar ta shiga raya masa abinda ya wakana daren jiya k'arar kukan beauty kawai yale tinowa yana dariya summ haka ya rungumota jikin nan nata gaba d'aya ya gama d'aukar zafi ya shiga fad'in thanks yuh so much my princess u make me feel morethan my expectation!k'ara matseta yayi gam jikinsa kamar wacce za'a kwace masa ya fad'a da k'arfi;wallahi alhaji beauty tayi ba kad'an ba ni da ita kuma mutu ka raba!k'ara k'are mata kallo yayi kafin yakai mata hot kiss a baki yace i luv yuh *'YAR JAMI'A* bayan nan ne kuma ya tashe ta domain sallah wanda haka rayuwarsu ta ci gaba cikin so da girmama juna!
*TAMMAT BI HAMDULLAH!*
```Godiya ta tabbata ga ubangijin halitta daya bani ikon kammala wannan littafi nawa na 'yar jami'a wanda ya zamanto k'irk'orarren labari,sannan ya zaman sadaukarwa ga masoyana biyu wato ANEESAH ABUBAKAR RIMI TARE DA UMMIE ADNAN! Na k'addamar da wannan littafi domin ya zama darasi ga 'yan uwa mata sannan ya zama hujja abin duba ga iyayen wannan zamani,fata na dai har kullum Allah yasa in an karanta ayi anfani da sak'on dake ciki ameen ya rabb!```
```Kunfi kowa bibiyar littafin nan;
Asma'u maman yasmeen
Fiddausi rabiu
Innah
Maman sadiya
Salaha fallata
Da wanda ban samu damar fad'a ba!```
```JINJINA DA GODIYA GA DUKKAN GRPS DA NAKE CIKI:
◆NAGARTA WRITERS ASSOCIATION
◆EXCELLENT HAUSA WRITERS
◆HAUSA ONLINE WRITERS GRP
◆WRITERS PLANET
◆HERWERH JIDDERH FANS
◆DANDALIN FEEDOO-DEEDO
◆HAUSA NOVEL GRP2
◆HAUSA NOVELLA HOUSE
◆.MUSAN JUNA GRP
◆.MATAN KWARAI GRP
◆DANDALIN SADY JEGAL AND MUM FATY
◆FUTHA LURV GRP
◆HUMMY BEE GRP
◆AYSHA GANA GRP
◆PBENA GRP
WANDA BASU JI SUNAN NASU BA SUYI WA HERWWERH JIDDERH UZURI JAMA'AR NE DA YAWA!!```
TAKU HAR KULLUM
HERWWERH JIDDERH
A.K.A
PRINCESS'QUE~DEE!
Download Ýar Jami'a Littafi Na Daya Complete
0 Comments
Thank you for this comment