Compiled by Umar Dalha Funtua.


🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *AUREN BAUTA*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(the amazing cook)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍢🥠🍥🍤🍣🍱🍲🍡



       By mmn walid and walida (mrs aliyu)



   Marubuciyar
*tawa kaddarar*
*dangin sa*
*uwata*
*rabo na ce* to be continued in shaa Allah



    Page 1🌹




 "Sai yanzu kika dawo ƴar iska tun ɗazu da aka aike ki ɗebo ruwan sai yanzu kika ga daman dawo wa kuma kina ji na nace miki sanwar wake da shinkafa zan ɗaura da ruwan shine kika je kikai zaman ki don kina min baƙin cikin kuɗin da zan samu ko, shegiya da fuskar kamar ta aljan"



   Duk wannan faɗan da inna harira bata taimakawa ƴar yarinyar da take ɗauke da ruwa akan ta, duk kuwa da ganin cewar yarinyar ta gaji sosai



   sai da tayi ta gama sannan ta sauke,
"kuma kije gonar malam ki wo min in kin ga dama ki daɗe kamar kinje lahira gaida iyayen ki"


    Ɗan ɗankwalin da take ɗauro karar ta ɗauka tayi waje da shi, directly gonar ta nufa wanda bashi da nisa da gidan ta ɗebo karar sannan ta kama hanyar gida tana yi tana nishi daga gani yunwa ce da kuma gajiya a tattare da yarinyar



  Da sallamar ta ta shiga gidan ta ajiye karar sannan ta zundumi ruwa a randa ta ɗan sha kaɗan bata san ta cikawa cikin ta ruwa



    "shiga madafi ki ɗauko ragowar ɗumame ki don yadda kike zaro min idandinan nan naki a cikin wannan baƙar fuskar taki ai wannan sai in mummunan  mafarki"




   Abincin ta ɗauko zata fara ci kenan inna harira ta kuma saka ta aikin hura wuta na wake da shinkafar da take saidawa



  A bakin murhun ta zauna tana hura iccen tana cin sandararran tuwon dawan da idan aka jefe ka da shi sai kaji ciwo saboda tsabar taurinsa



     Sai da ta gama girka wake da shinkafar tsab sannan ta kwashe a ƴar fantekar da ake kwashewa sannan ta gayaws inna harira ta gama


   "lantana lantana", inna harira ta kira ƴar ta da ke yi mata talla don kuwa asmau bata da kan inna harira tace yadda fuskar ta take baƙa haka ma kwakwalwar take sam babu haske a tattare da ita



     Asma'u ce ta ɗau fantekar inda lantana ta shige gaba suka tafi tallan haka suke yi kullum ita lantana itace me kan talla amma ban da asma'u



  Sai bayan sallah la'asar sannan suka dawo inda suka tarar da inna harira da baƙuwa a zaune a tsakar gida akan tabarma



  Ƙwalawa asmau kira tayi ta ƙarasa inda take sannan ta nuna wa matar asmau

"hjy kina ganin zatayi, don ni ƴar nan babu abinda take min anan, kullum sai dai taci tayi kashi kan talla babu shi yanzu in ta tashi aure wazai mata kayan ɗaki, ga shegen baƙi kamar kwalta"



   Matar da aka kira da hjy ta dubi asmau sannan tace

"to ba wai baza tayi ba kamar yadda na faɗa miki abuja ni fa nake kai yara aikatau, wannan kuma kamar yarinya ce"


 "ahap haka kike gani ai wannan in ta kama aiki kamar jaka haka take, reno shara wanki wanke wanke duk ta iya"



  Hjyr ta kuma kai duba asmau wacce kan ta yake a ƙasa sannan ita sam bata fahimci inda zancen su ya dosa ba


"ni dai da waccen ce" ta faɗa tana nuna lantana ƴar inna harira, inna harira sai tayi dariya irin ta basarwan nan


"haba bazaki so kiɗau wannan ba ai alanƙosa ake ce miki indai lantana ce ba abunda zata iya, yanzu tallan wake da shinkafar da take kai min ma tace zata dena tunda ɗan me gari yace yana sonta shi yasa nake neman hanyar da kuɗi zasu dinga shigo min, ga bikin lantana ban ajiye ba ban ba wani ajiya ba, kuma auren ɗan me gari kashe kuɗi gare"   ta faɗa tana ajiyar zuciya


 "to shike nan indai kince wannan ɗin zatayi ai shike nan, amma idan na tafi da ita kuma aka ƙi ɗaukar ta zan dawo miki da ita"


   "na yadda amma kice su fara gwadata tukunna kafin su yanke hukunci da wannan ɗan ƙaramin jikin nata shine yake sawa mutane suna yi mata kallon yarinya ce"



  Sukai sallama kan kashegari da asuba zata zo ɗaukar asmau zuwa garin abuja aikatau



 ***********************



 Asmau sunana na kasance ni kaɗai a wajen iyaye na babana ɗan nan garin ne azore wanda yake a ƙaramar hukumar minjibir ta jihar kano,



  Garin fulani ne sosai don gida tsilli tsilli zaku dinga gani in kun shigo sannan sai kuma gonar mutum a jikin gidan sa, irin dai ginin fulani, in kaga gida ɗaya sai kayi tafiyar mill kafin kaga wani



    Ban san iyaye na ba kasancewar sun rasu, mahaifiyata ta rasu lkcn haihuwar ƙanina, inda aka rasa aka rasa ɗan,

 

    Shi kuma mahaifina sai da na ɗan tasa kaɗan sannan Allah yayi masa rasuwa, sai kulawata ta koma hannun wan mahaifina



   Inda yake min rikon sakainar kashi, don kuwa babu ruwan shi da duk wani daya shafe ni duk abinda  matar shi zatai min baya cewa komai wannan shine taƙaitaccen tarihi na


  ******************




    Da sassafe hjy ta zo mukai sallama sannan muka kama hanya inda naci karo da wasu ƴammata waɗanda zamu tafi da su, amma duk sun girme ni don ni sai na zama kamar wata ƴar tsana a ciki su



 Sai da muka je gezawa sannan muka samu ƙaramar mota inda zata kaimu abuja, haka aka cunkusa mu a motar nan kamar dabbobi inda ita kuma hjyr ta zauna a gaba ita kaɗai



     Tafiya ce kamar ta yada shege ba ƙaƙƙautawa sai da muka je kaduna sannan direban ya tsaya muka fito muka ɗan huta, sannan muka kama hanyar abuja




   Lfy ƙalau muka isa abuja inda muka sauka a kubuwa, anan gidan hjy yake, ɗaki ta bamu guda, tace duk mu sauke kayan mu




      Ni dai kamar an min duka haka nake ji don kuwa a gajiye nake, kwanciya nayi sai bacci, inda ƴammatan da muka zo da su kowacce take ta buri tare da fatan irin gidan da za a kaita, ni dai tunda na samu bacci ya kwashe ni sai nace saba'ul khairi

  

👩🏽‍🍳 menu of d day👩🏽‍🍳
*wake da shinkafa served with local salad & zobo drink*


    🍲 ```wake da shinkafa```🍲


  ```ingredients```

```wake```
```shinkafa```
```gishiri```
```man gyaɗa```
```haɗin salad```


    ```method```


1) bayan kin gyara waken ki saki ki wanke ki ɗaura akan wuta, sannan ki bishi da ruwan kanwa (optional)

2)sai waken ya dahu, sannan ki ɗauko wankakkiyar shinkafar ki ki zuba ki juya ki saka ɗan gishiri sannan ki rufe


3) idan ya dahu sai ki sauke ki yi serving da soyayyan man gyaɗa, ko tankwa,  da yaji sai kiyi ganishing da salad  aci lfy


   *LOCAL SALAD*

    ```ingredients```

   cabbage
lettuce
carrot
cucumber
green pepper
lemun tsami
man gyaɗa
maggi


```method```

1) ki wanke lettuce, cabbage, cucumber, green pepper ɗinki, ki barsu su tsane sannan sai ki yanka su irin yankan da kike so




2)ki kankare bayan carrot sannan ki wanke shi daga nan sai ki gurza shi


3) ki ɗauko kayan haɗin da kika yayyanka ki haɗa da carrot sannan ki haɗe su waje ɗaya, ki ɗauko lemun tsami ki ɗiga kaɗan ba dagawa ba yadda dai zai miki sannan ki zuba mai ki zuba maggi ki juya sai ki juye a salad bowl sai ci

      


    *zobo drink*

 ```ingredients```

   Ganyen zobo
 Citta
 Kanunfari
 Abarba
 Cucumber
 Sugar
 Flavour


   ```method```

 1) ki ɗauko zobo sai ki wanke shi ki zuba masa ruwa ya sha kansa sannan ki ɗaura a wuta, tare da citta, ɓawon abarba, sai dakakken kanunfari ( ```sirrin daka kanunfari shine ƙamshin shi ya fi fitowa idan an daka shi akan a watsa shi haka```)


 2) idan zobo ya tafasa ya dahu sai ki sauke shi ki juye a babban mazubi yadda zai sha iska, kafin ya huce kuma bari mu haɗa ragowar

 3) ki fere yanka abarbar da cucumber ki ƙanana yadda dai zasu miki daɗi wajen blending sai ki markaɗa su kina yi kina tacewa kina ƙara markaɗawa har dai a samu yadda ake so

4) sai ki ɗauko wannan zobon naki ki tace ki ɗauraye ganyen ki kuma tace wa har sai maa shaa Allah, sannan ki haɗa da ruwan cucumber & abarbar nan


5) ki zuba sugar, flavour ki zuba a jug a saka shi a fridge yayi sanyi sai shaa


   👩🏽‍🍳 *Bon appetit*👩🏽‍🍳


  *ASMA'UN SABIT*
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)



 page 2 🌹






 Kashegari da sassafe aka tashe mu, koko da ƙosai aka bamu, muka karya sannan hjy ta tasa mu a gaba domin neman wa kowa gidan aiki



    Muka dinga zagaya gari zuwa gidajen masu hannu da shuni da kuma masu matsakaita ƙarfi ana ajiye mu da ɗai ɗai,



 Sai da ya rage mu biyu sannan muka hau mota muka nufi wuse zone 4 kamar yadda naji hjyr tace wa driver taxi ɗin da muka shiga



   A ƙofar wani restuarant muna sauka inda muka shiga ciki,




         Hjy ce ta nuna mana wani ɗan loko wai mu zauna a can kafin ta dawo, kusan minti biyu ta ɗauka sai gata inda ta kira mu muka bi ta cikin gidan



   Wata mata ce muka samu tana zaune a saman wata three sitter daga gani itace me wurin

"gasu nan kamar yadda na faɗa miki su biyu ne"   matar da ke zaune a ɗakin ta gyara ɗan glass ɗin da ke fuskar ta sannan ta kalle mu kamar ta ga wasu kashi ko abun ƙyanƙyami



  "me zanyi da waɗannan jariran" ta faɗa a wulaƙance

"na faɗa miki indai zaki kawo min ƴar aiki babba nake so amma me zan yi da waɗan nan, gwara ma waccen amma wannan kamar ba a daɗe da yaye ta ba"


  Ta ƙarashe zancen ta idon ta akaina


  "wallahi hjy munnira ƙaramin jiki  gareta amma da shekarun ta"
  



    Mahawara suka fara yi inda hjyr da ta kawo mu ta fi hjy munnira baki don haka dole hjy munnira ta yadda ta ɗauke mu bayan an sani shara nayi



    Sai da suka gama cinikin abinda za a dinga biyan mu a shekara sannan hjy tai sallama da mu, ita kuma hjy munnira ta kira wata laure wai ta tafi da mu ta nuna mana aikin daya dace mu



    Can bayan gidan muka je inda anan ake duk wani hada hada na girki, ƙaton kitchen ne, sai kuma wajen wanke wanke sai kuma wasu ɗakuna guda biyu da ke can gefen daga ƙarshen katangar inda anan akace mu ajiye kayan mu



   Kowaccen mu aka haɗa ta da aikin daya dace da ita, ni dai kitchen aka kai ni inda wacce muka zo da ita aka kai ta wajen wanke wanke




Ina shiga kitchen, naga girman kitchen ɗin, ban taɓa ganin irin wannan kitchen ɗin ba sai yanzu



  Girki ake yi kamar ba gobe, tsayawa kawai nayi ina kallon ikon Allah tare da ƙarewa kitchen ɗin kallo,



   "ke ya sunan ki" naji wata ta faɗa

 "asmau" na faɗa a hankali, kallon banza naga ta bini da shi

"ke amina waye yace a kawo mana ƴar jaririyar nan kitchen mu da muke  aikin wuta" ta faɗa kamar taga kashi


"hjy ce tace a kawo ta nan" inji wacce aka ƙira da aminar

"to sai sa ta tsabtace jikin ta don nan bama gayyata ƙazanta" sim sim sim na fice inda na nemi hanyar da ɗakunan kwana suke



    Ƴar jaka ta na ɗauko, sam babu wasu kayan arziƙi don duk kayan da nawan yawancin su ba wanki, wasu kuma a yayyage


   Zama nayi ina kallon ikon Allah, ban jima da zama ba sai ga wata ta shigo

"me kike yi a ɗakin nan bayan kowa yana waje yana aiki, kar dai bincike kike mana a kayan mu"


"wallahi ba haka bane, wanka akace inzo inyi in canza kaya kuma naga kayan nawan duk babu wanki" na faɗa d ido na duk ya kawo ruwa saboda banji daɗi zargin da tai min ba


   Jakar tawa ta zazzage a ƙasa ta fara duba kayan cikin ta, bakin ta a taɓe

"kije wajen wanke wanke ki samu ƙananan sabulai ki haɗa ki zo kiyi wanki"

 Miƙewa nayi na fita, nai mamakin dana ƙarasa wajen wanke wanke na samu sabulai, kamar ba da kuɗi a ka siye su ba, tsinta na fara yi har na haɗa iya wanda nasan zai ishe ni sannan na tafi ɗakin


  Kaya na na ɗiba sannan na je bayan ɗakin inda banɗakin mu yake na wanke kayana tas sannan na shanya



  Wanka na shiga da ragowar sabulun na saɓi jikina kamar ba gobe, don a



   Don kuwa a azore ban isa in samu wannan damar ba, sai dana gama wanka na sannan na fito



     Sai yamma sannan kayana suka bushe na kwashe, a ranar dai ban koma kitchen ba sai kashe gari


 Cikin hukuncin Allah na fara aiki a kitchen amma ba abinda nake yi sai aike, dauko wannan ɗauko wancen haka dai



   Kafin ka ce me wannan har na zama ƴar gidan, na son komai na kitchen, sannan na san inda ake ajiye komai


    Gidan cin abincin hjy munnira gidane da a kullum a ke dafa kusan buhu biyu na shinkafa da ta tuwo


 Babu irin variety na abincin da ba a yi, waina sinasir, alkubus fankaso, ta ɓangaren shinkafa ma


  Jollof rice fried rice, duk dai wasu sunfari na dafa abinci ana yi, ba wai duka a ke ci anan ba, akwai waɗanda ake fita da su,


  Don kuwa akwai certain hotels ɗin da suke zuwa suna yin order abinci anan gidan, ga kuma costomers da suke zuwa suna siya su tafi da shi



  Ga waɗanda suke siya su ci anan, akwai wasu mutane ma da ake musu abincin gidajrn su anan, kullum akwai abincin da za a dafa na certain gida akai masa



    Nakan yi mamaki amma dana ji cewar yawanci gidanjen ministers ne da house of reps da senators ake kai musu waɗanan abincin saboda mutanen da suke tarawa sai na daina mamaki duk da dai ban san ko su waye ba



    don haka aiki a gidan nan in aka tashi tun safe sai mukai ƙarfe 10 :00pm bamu gama ba


  Amma kuma mu girki ne kawai akwai ƴan wanke wanke, akwai kuma ƴan service, akwai masu kaiwa gidaje, group group ne kowa da group ɗin sa kuma kowa ya san aikin sa



   ******************



 *b̫a̫y̫a̫n̫ s̫h̫e̫k̫a̫r̫a̫ b̫i̫y̫u̫*




    Na zama ƴar gida yanzu don kuwa ba abinda bana shiga ayi da ni ta ɓangaren girki,


   A lokcn ne hjy munnira ta ƙara buɗa restuarant ɗinta inda yanzu babu abinda ba a yi, snacks ne ɗrinks ne, duk daia abinda kake so idan ka zo restuarant ɗin mu,


  Kuma kullum cikin hukuncin Allah ƙara samun costomers muke yi, yanzu ba a shakkar bani girki ko ya yake don kuwa a gaskiya na iya



    Kasancewar ni ce ƙarama a kitchen yasa kowa sai kaji yace asmau don Allah juya min kaza, kwashe kaza, wannan ne ya sa ni ko wane ɓangare na kitchen ina shiga


  Ba kamar cooks ɗin kitchen ɗin ba, yadda in a ɓangaren sarrafa shinkafa kake to ana zaka zauna, in a ɓangaren snacks kake to anan zaka zauna, haka ma in a ɓangare drinks kake ko miya ko salad ko wani abu na kitchen



  Ma'aikatan a rarrabe suke kowa yasan aikinsa, amma banda ni, ni ina kowane ɓangare kuma duk inda naje sai na tabbatar da cewar na koyi abunda suke


  Wannan ne yasa a kitchen ɗin nai fice tunda komai aka bani zan iya kuma zan yi shi kamar ba ƴar ƙaramar yarinya ce tayi ba



   *****************


   Sabit yana zaune a office ɗinsa cikin fararen yadinsa waɗanda kana kallon su kasan ba ƙananan kuɗi aka sa wajen siyan su ba, wayace a hannunsa yana ta danna wa


  Tun ɗazu yake kiran ta amma bata ɗauka ba, tsaki ya ja tare da ajiye wayar

"wallahi sam banga amfanin wayar mata ba ace mutum sai yai ta kiran ki a waya amma wai bakya kusa da wayar" be gama mitar sa ba sai wayar tashi ta fara ringing


  Tune ɗin daya saka mata kenan don haka wayar tana fara ringing ya gane ita ce, idon shi ya kai kan screen ɗin wayar inda aka rubutu *only u*


    Ɗan tsaki ya kuma sannan ya ɗauka a yangance kamar wani mace

" *SD* don Allah kayi haƙuri wallahi ina sallah ne ka kira" duban shi ya kai kan agogon bangon ɗakin inda ya ƙarfe 03 :15pm


 *only u sallah me  kike yanzu kar dai kice min azahar"

" wallahi *SD* na shiga meeting ne shiyasa ban samu nayi sallah akan kari ba, ya kake "


"amma meeting sai ya hana ki sallah wai sai yaushe zaki san mahimman cin sallah haba only yanzu haka zamu yi aure ki dinga nuna wa yaran mu, yanzu lkcn sallah bazaiyi ba a bar abinda ake yi a tafi ai sallah ba"

"  *SD* kasan matsalar bank fa su koman su a ka'idance yake kar ka damu in shaa Allah tarbiyya me kyau zan muyi wa ƴaƴan mu, kaji"


   Ta shiga kalailaye shi da kalaman da tasan suna kwantar masa da hankali kafin kace meye wannan har sun koma kamar ba abinda ya faru,



   Sai da suka gama shan soyayyar su sannan sukai sallama akan zai zo da daddare, daga nan sukai sallama kowannen su zuciyar su tana alfahari da kuma ƙaunar junan su





👩🏽‍🍳 *Menu of d day* 👩🏽‍🍳

🍲```Veg cous cous with kidney sauce``` 🍲


    ```ingredients```

   _Cous cous_
    _Butter_
    _Cabbage_
    _Peas_
    _Carrot_
   _Canned sweet corn_


    ```recipe```

  1) ki wanke carrot ki yanka shi size ɗin da kike so, sai ki wanke peas sai ki haɗa su ki tafasa su da ɗan gishiri, tafasa ɗaya sai ki sauke ki wanke su da ruwan pampo wannan wankewar zai sa su suyi shar kuma su rike kalar su sai ki ajiye a gefe


  2) a wanke cabbage a yanka sannan a ajiye shi aside, sweet corn ɗin shima a tsane ruwan shi a ajiye shi gefe


3) ki ɗaura ruwan zafi, idan ya tafasa, sai ki ɗauko cous cous ɗinki a cikin bowl, sai ki ɗan zuba masa dan ruwan zafin, ba dayawa ba ya ɗan sha, *a zuba yadda bazai yi wa cous cous yawa ba* sai ki ɗan bari ruwan ya tsotse

4) ragowar ruwan daya ke tasafa a kan wuta sai ki saka colander ```(in babu colander zaki iya yin na buhu amma a tabbatar da buhun be taɓa ruwan ba)```a kan sa, sannan ki kawo jiƙaƙƙen cous cous ɗin ki, ki zuba, ki kawo kayan peas da carrot ki zuba ki rufe ya turara


5) idan ya ɗanyi wani lkc kika buɗe kika ya dahu sai ki sauke, ki juye cous cous ɗin a wata roba, ki zuba melted butter, da sweet corn da kuma cabbage sannan a juya a zuba a food flask
~bon appétit~


    ```kidney sauce```


   ```ingredients```

 _Kidney_
 _Attaruhu_
 _Albasa_
_Maggi_
 _Man gyaɗa_
 _Tomato paste_
 _Curry_
 _thyme_


   ```recipe```

   1) a wanke kidney a cire tsakiyar nan don kuwa wataran har tsakuwa ake gani


 2)sannan sai ki tafasa ta da albasa da maggi da thyme, idan ya tafasa sai ki tsame ta a gefe


  3) a grating attaruhu da albasa, ki saka man gyada kaɗan a tukunyar ki sai ki dan bishi da albasa da tafarnuwa, idan man ya ɗau zafi sai ki zuba attaruhun ki da albasa a barshi ya soyu


4) idan ya ɗauko soyuwa sai ki ɗauko kidney ɗin nan ki saka ki ƙara maggi, tomato paste sannan ki sa curry sai ki rage wuta ki bar shi ya ƙarasa 
   
    👩🏽‍🍳 ```bon appétit```👩🏽‍🍳

     *ASMA'UN SABIT*
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)



   P⃗a⃗g⃗e⃗ 3🌹






           Badia ƴa ce a wajen alh hamza da matar sa hjy bilki, dukkan su ma'aikatan banki ne, inda alh hamza yake aiki a *CBN* ita kuma hjy bilki take aiki a zenith bank


   Ƴaƴan su uku mata biyu sai namiji 1 hauwa ita ce babbar ƴar su dr. ce a asibitin general hospital dake abuja tana da aure da ƴaƴa biyu


 Sai badia wacce a yanzu take aiki a zenith bank amma ba branch ɗin su ɗaya da mmn ta ba, sai ɗan autan su nura wanda yake karatu har yanzu a china



   Rayuwar gidan su badia irin rayuwa ce ta western style babu ruwan iyaye da matsawa ƴaƴan su duk abinda kayi dai dai don haka rayuwa ake yi ba kwaɓa balle harara



   Yo ina ma suka ga iyayen nasun balle su kwaɓe su in suna ba daidai ba, kuma cikin hukuncin Allah sai ya shirya musu ƴaƴan babu me abin ashsha masu zuciyar samun na kansu ne amma batu addini sai a slow



    Badia sun haɗu da sabit ne lkcn da ya zo bank ɗin su bayan ya samu matsala da master card ɗinsa sai ya kasance badia ce ta gyara masa matsalar
  


  Badia irin dogwayen matan ne masu ƙirar coca cola, fara ce amma duk da farin ta hakan bai hanata shafa man da zai ƙara mata haske ba, Allah yayi da son gayu, don haka take da manema dayawa, gayun ta da kyan ta da kuma iya ɗaukar wankan ta yasa take taƙama da kanta



   Tunda ta ɗaura idon ta akan sabit taga gaskiya wannan yayi mata don haka sai tai tayi masa salo salo daban daban ko zai taya, amma ga mamakin ta sai taga kamar ma tana yi da dutse ne



   Don haka sai ta kau da ƴar kunyar nan tamu ta mata tace masa suyi exchanging contact incase ko wani matsalar zai kuma tasowa ba sai ya sha wahalar zuwa bank ba



   Sabit be kawo komai ba don haka sai ya yadda da abinda tace, ko bayan da to koma gida ta ɗauka zai kira ta amma sai taji shiru, kwana da kwanaki kullum jiran call ɗin sa take amma shiru



  Rannan sai ta kira shi inda ga mamakin ta wai yama manta da ita, sam bata ji daɗin yadda yai mata ba amma kuma sai ta ɗau ƙudurin in shaa Allah daga lkcn ba zai kuma cewa ya manta da ita ba



    daga lkcn ta zama me kiran shi, tun yana basarwa har yazo yana ɗan dauka har kuma cikin hukuncin Allah suka fara soyayya har gashi suna shirin gabatar da junan su ga gabatan su don a tabbatar da soyayya su,



   ******************



    Sabit ɗa ne na huɗu kuma ɗan auta a wajen hjy fatima da kuma alh bashir, mahaifiyar shi shuwa ce mace me kyau da kwarjini ga ƙaunar ƴaƴan ta, ita bata damu ba ko zata ɓatawa kowa indai hakan zai farantawa ƴaƴan ta wannan soyayyar da ƙaunar da take wa ƴaƴan natan ne ma har yasa ta sa mijinta ya gina wa kowanne daga cikin ƴaƴan natan ɓangaren shi a cikin tafkeken gidan da suke,



    Sannan ƙwararriya ce wajen haɗa sanwa, idan ta shiga kitchen ta haɗa dinner sai mutum ya manta sunan sa saboda tsabar daɗi da kuma tsari, wannan ne ya sa ta sha alwashin duk ɗan ta daya yi aure matar bata iya girki ba sai ya ƙara kuma a hakan ake har yanzu



      Alh bashir mutumin adamawa ne fulani ne fari kyakkyawa da shi, wannan kyan na bayin Allahn nan yasa idan kaga ƴaƴan su sai ka saki baki barin ma ace sabit wanda kamar su da hjy fatee har ya ɓaci, don haka duk cikin ƴaƴan su ya fi su fari da kyau



     Ƴaƴan su huɗu isma'il shine babba, likita ne matan sa biyu, ta farkon auren soyayya ne, amma matar bata iya girki ba don haka sai ta saka shi ƙara aure inda ita ma ta biyu ya kasance da babu ce hausawa suka ce gwanda ba daɗi



   Wannan yasa har yanzu isma'il a ɓangaren iyayen shi yake cin abinci, na biyun su shine sulaiman shi ma matan sa biyu duk babu gwanda wajen girki sai na uku mansur wanda shima matan nasa biyun amma su da ɗan sauki sauƙi



    Sai auta sabit wanda ake ta shirye shiyen auren sa tooo shin badia ta girki kuwa bari dai mu bisu mu ji ita kuma ya nata yake



   ********************




 Sai ƙarfe 06 :30pm na yanna sanna ya shigo gida duk saurin sa na dawo wa gida da wuri don ya samu ya shirya ya tafi wajen badia amma hakan bai samu ba


  Wanka kawai ya shiga yana cikin wankan ne ma yaji wayar shi na ringing ko be gani ba yasan badia ce don ringing  ɗin daya saka mata ne



     Hankalin sa akwance ya ƙarasa wankan sa ya fito, yana fitowa wayar tana kuma shigo wa, towel ɗin da ke hannun sa ya ajiye sannan ya ɗau wayar

" *SD* sai yaushe zaka zo tun 05:00pm nake jiran ka amma shiru kamar bazaka zo ba"


"only yi haƙuri wallahi aiki ya tsare ni a office, more over ina son mu haɗu da alh ku don ina son jin yadda za a tsara wannan lamarin don na ƙagu in ganki a gidana"


  Ɗan dariya tayi irin na nuna jin daɗi sannan tace masa

"kamar kasan kuwa ya dawo shima, bari in gaya masa kana son ganin sa don kar ya fice"

"dats my only shiyasa nake son ki, kuma nake ce miki only don daga ke ba ƙari" ya faɗa hankalin shi a kwance don shi mutum ne da baya son tarkacen mata


   Tayi bala'in jin daɗin wannan maganar tasan wanda har ta kasa ɓoye murnar ta ta fara zuba masa shagwaɓa


    inda shi kuma wannan abun nata na bala'in birge shi yana bala'in son yaga mace ta iya shagwaɓa, haba me zakayi da macen da babu wani sanyi a tattare da ita, shi ya fi son mace faran faran wacce kullum zaka ganta very lively sannan wacce ta iya shagwaɓa


   Ta kasance fara doguwa kyakkyawa duk wannan abun daya ke nema a mace ya same shi a badia shi yasa yake tunanin daga ita babu ƙari, haba gashi fari kyakkyawa ai sai fara me kyau inji sabit



   Sauri yai ya ƙarasa shiryawa inda ya shiga masallacin gidan su yayi sallah magariba daga nan ya wuce gidan sahibar tasan


    A ƙofar gidan su ya faka motar sa sannan ya kira ta, tana zaune a gaban dressing mirrow ta gama tsara kwalliyar ta irin yadda sabit yake so taji call ɗinsa


  Ɗauka tayi a yangance sannan cikin shagwaɓa tayi masa magana

" *SD* sai yanzu ka zo duk na bushe kwalliyar da nai maka duk ta goge" ta faɗa kamar gaske, wannan maganar tata har cikin ranshi ya ji ta yadda ta kashe muryar ta sannan cike da shagwaɓa

"awa nawa kike ki sake min wata zan iya jira a waje"

"wasa nake maka bari insa a shigo da kai"

"ok " ya amsa tare da maida wayar aljihun sa sannan ya tsaya gana jiran ai masa iso zuwa cikin gidan, bai daɗe ba sai ga me aikin su ta fito inda ya bita har farfajiyar gidan inda suka saba taɗi ya samu wuri akan ɗaya daga cikin  fararen kujerun da suke wajen ya zauna



   Ko da ta gama kwalliyar tata da fesa duk wasu turakan da ta san masu ƙamshi ne sai ta ɗauko hijab ta saka, tana ta mita a ranta


  Ita ta rasa irin sabit, duk irin kwalliyar da tayi sai dai yace tabi kwalliyar da hijab, sannan kuma ya hana su taɗi a ckkin sitting room sai dai a waje yacce duk wanda zai shigo ko zai fita sai ya gansu, wallahi daba dan san da take masa ba da tuni sun rabu don wani lkcn abin nashi kamar ɗan ƙauye haka yake yi ba wayewa ta faɗa tana fita wajen sa




👩🏽‍🍳 *menu of d day*👩🏽‍🍳



       ```Alala```




Ingredients


_Wake
Kwai
Hanta
Dankali
Alayyahu
Oil
Maggi
 curry
Attarugu,
albasa
Leda


```method```



1) surfa waken ki saiki wanke shi sosai kisa attarugu , albasa da ki kaishi inji a Markado miki


2)  ki wanke hantar ki ki dafa ta da albasa,maggi thyme idan ta dahu saiki sauke ki aje gefe


3)ki fere dankalin turawanki ki yanka shi cubes ƙanana, sai ki yanka dafaffan ƙwan ki shima ƙanana, alayyahu a fara wanke shi sannan shima a yanka shi sannan a ajiye

4) sannan sai ki ɗauko  markaden ki saiki dauko mai ki zuba aciki kisa maggi da curry ki kara ruwa in ƙullun yayi kauri amma ruwan da kika tafasa hantarki kikara yanka albasa ki buga kullon ki ɗauko hantar ki da ƙwan ki, da dan kalin da alayyahu kixuba ki ƙara bugawa, sai ki ɗan ɗana, idan komai yayi sai ki saka cray fish (niƙaƙƙe amma optional ne)



 5) sannan kije ki ɗora tukunyar  akan wuta kisa ruwa bayan ki ɗora saiki zo kina ɗiban ƙullun kina sawa aleda kina ƙullawa kina sawa cikin ruwan zafin nan har ki gama ki rufe har ta dahu saiki sauke .


  *Minced meat sauce*


Niƙaƙƙen nama
Attarugu
Oil
Green papper
Maggi
Albasa
Tafarnuwa
   


```method```
1) ki ɗauko frying pan sai ki zuba ɗan man ki ki saka masa albasa kaɗan idan ya ɗan yi zafi sai ki zuba niƙaƙƙen naman ki  sannan ki ƙara zuba albasa, tafarnuwa maggi sai ki ta juyawa har sai ya koma brown, ba a ɗauke masa hannu don sai ya ƙone



2) idan naman ya koma brown sai a ɗan zuba ruwa a rufe ya dahu, ruwan kadan ba dayawa


3) idan naman ya tsotse ruwan sai a zuba niƙaƙƙen attaruhu, da albasa curry sannan sai a rage masa wuta har ya soyu, shima a dinga juyawa don kar ya kone

  Sai aci da alalan




 *Pineapple drink*

madara
sugar
abarba
flavour

1)ki fere abarbar ki ki markaɗa a blender sai ki tace saboda ba duka bane suke markaɗuwa ba


  Sannan sai ki ƙara mayar da wadanda basu markaɗu ba ki ƙara markaɗawa suma ki tace ki ci gaba da markaɗawa har dai ki samu yadda kike so

2) ki juye a cikin roba mai kyau sai ki ɗauko wannan madarah ki juye  a cikin wannan ruwan abarbar ki zuba sugar (amma nafi gane in dan tasafa sugar da ɗan ruwa idan ya narke sai ki sauke ki barshi ya huce) kisa flavour

3) a juye a jug a saka a fridge don ya yi sanyi sai sha 🍸


  👩🏽‍🍳 *bon appétit* 👩🏽‍🍳


   *ASMA'UN SABIT*
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)



   P⃗a⃗g⃗e⃗  4🌹



Da sallamar ta ta ƙaraso inda yake cike da tafiya cikin yanga da karairaya sai kace zata karye, iskar farfajiyar sai ɗauka hijabin da ke jinkinta yake inda ƙamshin turaren ta yai masa sallama


   A rayuwar sabit in akwai abinda yake so da badia be wuce ƙamshin ta da gayun ta ba ga uwa uba fara ce tas kamar jinin larabawa, ƙarasowa tayi cike da yanga da kuma shagwaɓa ya zauna kujerar da ke kallon tasa sannan tai narai narai da ido kamar me shirin yin kuka sannan tace

" gaskiya *SD* ka shanya ni, tun biyar nake ta jiran ka sai yanzu, kuma kasan dokar ka ta gama hira ƙarfe 08:00pm gashi yanzu takwas ɗin ta kusa" ta ƙarashe zancen ta tana kyakkyaɓe fuska kamar me shirin kuka



  Wannan abun da badia take yi shine abinda yake ƙara hargitsa wa sabit tunani har yake ganin kamar bazai iya rayuwa ba tare da ita ba


    Haƙuri ya shiga bata inda ya kuma kawo mata uzurin office ne ya hana shi zuwa da wuri, sai ya kawo mata zancen da yasan zatai farin ciki da shi na batun auren su



   Nan ta nuna murnar ta kamar ba gobe bata da wani ragowar buri a rayuwar ta daya wuce ace ta mallaki sabit a matsayin miji, miji na nuna wa sa'a, mijin daya ke kallon ta ya daki ƙirjin sa cewar daga ita ba ƙari, mijin da a kullum zai dinga saka ta cikin farin ciki



   Tattaunawar su suka ci gaba akan yadda za a gidanar da bikin da kuma shirye shiryen da zasuyi na bikin, har mahaifinta ya dawo sannan sukai sallama inda ya je domin su tattauna da shi akan magabatan sa da yake son turowa




Cikin hukuncin Allah sukai tsaida magana inda mahaifin badia yace wa sabit ya turo da iyayen sa sai a ƙarasa maganar tunda maganar ta manya ce


  Sabit cike da farin ya koma gida inda ya sanar da mahaifiyar sa,

  Mummy ta taɓe baki ta gyara zama, sarai ya san dalilin wannan abu mummy tana da wani aqida ne wai sai lallai mace ta iya girki, shi kuwa sabit ba shi da wannan tunani shidai kawai ya auri badia

 "auta kana ganin wannan me rawar kan da kake son ɗauko wa ta iya girki kuwa, ko in nemo maka wata in yaso dai ka haɗa biyu kamar ƴan uwanka"


 "mummy na ɗauka mun gama wannan maganar da ke,ni dai gaskiya bazan ƙara aure ba akan girki, kin yadda da wannan inda ni kuma na yadda bazan nemi aiki a ƙasar waje ba zan zauna kusa da ke"


   Ya faɗa yana kallon ta don ya son ba abinda mahaifiyar sa ta ƙi jinin ji daya wuce yace zai fita ƙasar waje neman aiki takance duk abinda baka samu a ƙasar ka ba to bazaka same shi a waje ba



   "to kuma me ya kawo wannan maganar, don kawai na tambaya ka a kan iya girkin ta"


 "mummy ma'aikaciyar banki ce don haka ko aure mukai ba zama za mu dinga yi a gidan ba, ita tana wajen aiki nima haka don haka karki damu"



  Taɓe baki tayi Sam ita ba haka take so ba, ta so ace sabit ya ɗauko macen da ta iya girki sosai tunda shi mutum ne me son girki different varieties amma wai ya ɗauko wani tsari wai aiki, duk cikin matan ƴan uwansa babu wacce take aiki sai matar shi kawai, lallai dole ne ta dakatar da wannan aikin taya ma za ayi ta iya kular mata da ɗanta bayan tana aiki



   Sabit yadda yaga mommy ta zurfafa cikin tunani yasan tasa saƙa wani abunne don haka sai yace mata

"mummy i hope u r not thinking about any strategy don mun riga mun gama yarjejeniya da ke akan baza ki shiga maganar aure na ba"


 "to me kaji nace, ni batun aikin nata ne kawai bana so"


"mum ki bar komai kawai mun riga mun gama tattaunawa da ita da aikin ta na ganta don haka bazan hanata ba, kuma aikin ta bazai hanata kula da ni ba" ya faɗa yana ficewa don yasan idan ya tsaya sai mummy ta kawo wani abun da bazai iya magance shi ba



   *******************



   Cikin hukuncin Allah aka kai kuɗin auren sabit inda da yake abin na manya ne aka saka wata biyu, ba abinda zamuce sai dai muce Allah ya kaimu



  ********************


    Asmau an ƙara wayewa ta ɓangaren girki, kullum ƙara gogewa take yi ta ɓangaren sarrafa abinci kala kala, wannan ƙwarewar tata yasa ya ƙara jawo wa restuarant ɗin su customers sannan restuarant ɗin ya kuma yin suna lungu da saƙo an san shi kuma ana zuwa ko cin abinci ko yin order



   Wannan iya girkin na asmau ne ya saka hjy munnira tura ta zuwa ga wani catering school don ta ƙara ƙwarewa, don duk wani abinci na zamani a restuarant ɗin sai a hankali sun fi siyar dana gargajiya



  Domin a ƙara haɓaka restuarant ɗin ya kasance duk irin sunfarin abincin da kake so akwai sai hjy munnira ta tura ta catering school inda taje ta fara koyan abincin na garuruwa iri iri kama daga na turai, larabawa, chinese da dai sauran su



  Shekarar asmau ɗaya tana karatu inda ta ƙware ta fi da ƙwarewa har ta kai duk restuarant ɗin itace chef de cuisine wato itace shugaban ƴan kitchen ɗin gabaɗaya duk da ƙanƙantar shekarunta



   Girki take fesawa na kece raini, babu wanda zai ci abincin ta baiyi santi ba, wannan ya sa restuarant ɗin ya kuma haɓa ka har hjy munnira ta ƙara buɗe branches inda duk anan ake yin girkin sai ana gama duk sai akwasa akai can branches ɗin



Duk wannan ɗaukakar da Allah ya bawa asmau me sa ta ta fara kula da jikin ta ba, tana nan baƙar wuluk kamar da fuskar ta ake girkin, ga rashin fara'a wannan ɗabi'a ce sam a lamarin ta ba fara'a



  Ga miskilanci sai ta wuni bata cewa kowa uffan ba, don haka da wuya kaji anyi faɗa da ita ko cecekuce, ita dai kawai tayi aikin ta ta koyi sabon girki sannan tayi kuma a yaba



   Rashin fara'ar da sakin fuskar ta yasa duk mazan da ke cikin kitchen ɗin suke ganin girman ta duk da dai a kitchen ɗin har yanzu ita ce ƙarama, don har yanzu batai 16yrs ba, ga ƙaramin jiki sai ka ɗauka ma she is only 13yrs amma sai shegen basirar sarafa abinci kamar da wannan hikimar aka haife ta




    ******************


    Ko da lkcn auren sabit da badia ya matso sai mummy ta zo restuarant ɗin hjy munnira akan tana son cooks waɗanda zasu dinga yi mata girki da bikin ko dan baƙin da zasu zo na kwana



   Ganin yadda mummy tace wa hjy munniran zata biya su labour ɗin su ne yasa hjy munnira amincewa har da saka asmau a ciki tunda girkin kwana uku kawai zasu yi anyi bikin an watse, don haka sai ta yanke hukunci tura asmau ita kaɗai tunda mummy tace akwai ma'aikatan da zasu taya su aiki, ita kuma hjy munnira bazata iya barin iyayen kuɗin nan da mummy take da niyyar biya ba




    Asmau bata san hawa bata san sauka ba kawai sai taji hjy munnira tai mata maganar tafiya gidan wata wai zata dinga abincin biki da taimakon wasu



  Fuskar nan tata da kullum take cunkushe ba fara'a ta ƙara tsuke ta sannan tace

"hjy ban gane ba, ai ni aiki na anan yake"


"can ma aiki zaki yi na kwana uku ki dawo, biyan ki nake yi don haka ina da ikon tura ki duk inda na ga dama, sauran inkin je ki ci gaba da wannan turɓune fuskar taki" ta ƙarashe zancen ta tana ficewa tare da barin asmau ita kaɗai a ɗakin



  Ran asmau yai mugun ɓaci wai taje wani gida aikatau duk da dai aikatau aka kawo ta amma yanzu ai ta wuce wannan matsayin amma shine matar nan take son kai wani gida wai ta zame musu cook ta biki, ƙara cunkushe wannan fuskar tata tayi sannan ta fito ta fara haɗa kayan ta




   A cikin restuarant ɗin taci karo da driver na gidan da zata yana jiran ta, inda bayan ta fito hjyr take ce masa

"gata nan ita kaɗai ce zata" bin asmaun yai da kallon raini inda ita kuma ta daka harara tare da ƙare haɗe ranta


 "hjy madam fa mutane uku tace ya zaki haɗani da wannan ƴar yarinyar" dariya hjy munnira tayi sannan tace


 "kace wa madam wannan itace best chef ɗin gidan nan shigasa na bata aron ta" ƙara kallon baƙar yarinyar yayi sama da ƙasa yadda ta wani haɗe ranta kamar an aiko mata da mala'ikan mutuwa ga ƙanƙanta amma wai ace ta fi kowa iya girki lallai ashe ma girkin ba wuya, ya faɗa a ransa


  "muje to da rabon madam ta dawo da mu"

"in bata yadda ba kace ta gwada giɗkin yarinyar kafin a dawo da ita" gyaɗa mata kai kawai yayi suka fice inda asmaun ta fice ba tare da tayiwa hjy munniran sallam ba don har yanzu haushin ta take ji




 Sunyi tafiyar kusan minti ashirin sannan suka ƙaraso wani tafkeken gida, tunda muka fito drivern nan yake min surutu iskar da ta kwaso shi ma ban shaƙa ba balle zancen sa ko da ya ga alamar banni da niyyar tanka masa sai ya ja bakin sa ya tsuke har uka isa gidan layi guda ya cinye, a ƙofar wani makeken get driver ya tsaya inda suka fito tare



    Tsayawa tayi tana ƙarewa gidan kallo dabadan hjy munnira ce ta ce mata ta biyo shi ba da ba abinda zai sata biyo shiva wannan gidan kamar na yankan kai



    Sai da suka ƙwanƙwasaƙofar sannan wani turƙeƙen arne ya leƙo

"who's knocking" ya tambaya da wata muryar sa wacce zata iya sawa mutum ya zura a guje, ganin driver ɗin ne yasa shi wangale baki wai yana murmushi



  Shi kanshi murmushin ƙara masa muni yake balle kuma, buɗe mana get ɗin yayi muka shiga, inda muka tasamma tafiya kamar zamu wata unguwa ba acikin gida muke ba



  Sai da mukai tafiya me nisa sannan muka isa wata ƙofa inda drivern ya danna door bell sai ga wat ƴar dattijuwa nan ta zo ta buɗe

 "mlm garba tun ɗazu hjy take ta jiran ka har ta gaji ta hau sama sai ku ɗan jira kaɗan sai ta sakko naga ma kamar ba a samu masu girkin ba ko, ai dama na faɗa wa hjy ko miliyan zata basu baza su bata wacce zatai mata daddaɗan girkin da take siyar wa ba ita dai tafi son kawai ai ta siya a wajen ta" duk wannan bayani tunda ta ɗauko shi bata numfasa ba sai da ta kai aya



   Wanda aka kira da mlm garban wato drivern bai ce komai ba sai kawai ya nemi waje ya zauna, ni bece min ga guri ba don haka sai na ci gaba da tsayiwa ta



 Ina da wani abu in ba bani abu kayi ba ko kuma ba nunain kayi ba bazan taɓa motsawa ba balle insan Allah ya yi ruwan abun anan



 Sai daya ga na daɗe da tsayuwar sannan yace min

 "baza ki zauna ba, ke gaki ƴar ƙaramar ki da ke amma zuciyar ki kamar ta kafirai tunda muke tafe nake ta miki hira amma kamar gunki yanzu kuma ki nemi waje kin tsaya an gayamiki hjy yanzu zata sauko ne"



  Iskar da ta kwaso shi ban kalla ba balle shi, ya buɗe baki kenan zai ƙara magana aka buɗe ƙofar falon wannan dattijuwar ce dak ta kuma fitowa


"hjyr ta sakko" tace da mu, tashi yayi yai gaba ni kuma ina biye da shi a baya muka shiga fatana Allah yasa hjyr tace baza ta karɓe ni ba




👩🏽‍🍳 *menu of d day*👩🏽‍🍳


    *chinese fried rice  served with russian salad & mixed fruit juice*


 
*chinese fried rice*

  ```ingredients```

-rice (a tafasa sannan aka wanke)
-eggs
-carrot( a kankare shi a wanke sannan a yanka shi cubes)
-peas
-green beans(a wanke a yanka shi kamar girman carrot)
-man gyaɗa
-tafarnuwa
-albasa
-curry
-nama tafasashshe shima a yanka shi ƙanana


1) ki haɗa carrot, peas, greenbeans ki dafa su da gishiri, idan sun dahu ki sauke ki wanke su da ruwa, (wannan yana sawa suyi retaining colour ɗin su)


2) ki ɗauko frying pan, ki zuba mai da ɗan albasa sai tafarnuwa, idan man ya ɗan fara soyuwa sai ki zuba naman, da kayan veges ɗin da kika dafa kiyi ta juyawa


3) idan sun ɗauko soyuwa sai ki matsar da gefe, sannan ki ɗauko kwai wanda kika fasa kika kaɗa shi sai ki zuba a gefen da ba komai ki bar shi ya ɗana fara soyuwa


4) da kinga kwan nan ya dauko soyuwa sai ki saka cokali ki fara dagargaza shi, kina yi kina juyawa haɗ ya soyu sannan ya zama dagargajajjen ƙwai, sai ki haɗe da ragowar veges ɗin da kika matsar gefe ki ci gaba da suya



5) idan sun soyu ko ince sun ɗanyi laushi, sai ki ɗauko shinkafar ki wacce kika tafasa ta kika wanke ta tsane sai ki zuba, ki zuba maggi curry da duk wani seasoning ko garnish da kike so sai ki cigaba da juyawa har sai ta soyu ita ma sai ki sauke a juye




   *russian salad*

  ```ingredients```
  -Dankalin
-peas
-cucumber
-carrot
-green pepper
-egg
 - bama mayonnaise


  ```method```

1) Ki free dankalin  turawan yanka shi ƙanana sannan a tafasa shi a sauke a barshi ya huce)

 2) a kanakare carrot sannan ayi yanka shi kamar yankan da akai wa dankalin a haɗa shi da peas a dafa su (irin dahuwar da nake faɗa)


 3) a yanka cucumber irin yankan carrot, dafaffan ƙwai shima green pepper ɗin


 4)ki haɗa komai a roba, dankalin, carrot, peas, egg, cucumber, green pepper sannan a dan barbaɗa maggi saboda ɗanɗano sai a saka mayonnaise a juya sai a juye a mazubi



  *mixed fruit juice*

   ```ingredients```
 -Kowane kayan marmari da suke tashe

 -sugar
-flavour


 ```method```


1) ki haɗa kayan marmarin nan tas ki markada kina makaɗawa kina tacewa kin sakewa har a samu yadda ake so


 2) a zuba suga da flavour sannan a saka a jug a saka fridge don yayi sanyi sai sha


  👩🏽‍🍳 *bon appetit*👩🏽‍🍳



    *ASMA'UN SABIT*
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)



   P⃗a⃗g⃗e 5 🌹




Muka shiga falon ba abinda yake tashi a haɗaɗɗen falon sai ƙamshin turaren ƴan maiduguri da kuma sanyin ac



   Falon ya sha gyara sosai na kayan ƙawata falon, duk da dai ban taɓa shiga haɗaɗɗen falo irin wannan ba amma hakan be sani na fara ƙauyanci ba


  Kallo ɗaya nayi wa falon na ɗauke kaina inda kaina ya sauka kan wata farar mace kamar balarabiya tana zaune a kan couch ɗin da ke falon



   Fara ce tas da ita ta sha jan lalle wanda yake ƙara mata kyau da kwarjini, kana ganin ta kasan ta manyan ta amma gayun ta da ɗaukar wankan ta sai ya ɓoye mata tsufan nata



   kusa da ita mlm garba ya zube yana ɗiban gaisa inda nima na ɗan tsugunna

 "mlm garba ina masu girkin naga da wannan yarinyar"  ta tambaya

 "ai hjy babu yadda banyi ba akan ta bani masu aiki amma sai tace min sai dai mu tafi da wannan yarinyar wai babu wanda ya fi ta iya girki"


  Ina jin shin shi yana ta bayanin yadda sukai da hjy munnira ni dai ban tanka ba kaina a ƙasa, ɗago wa tayi ta kalle ni sannan tace

 "don ta raina min hankali wannan ƴar mitsitsiyar yarinyar me zata yi, duk irin kuɗin dabna bata na saka a jakar ta amma baza su sa ta bani su aro na kwana uku ba, shike nan ka mayar da ita kace nace wai ta baka kuɗin ka dawo mun da su na samu wasu cooks ɗin"


 Tana gama faɗar haka na miƙe don dama ni haka nake so

 "a a tsaya mana, hjy ita hjy munnirar tace ki fara cin girkin ta kafin ki yanke hukunci"



  Musu suka shiga yi da hjyr da mlm garba kasancewar yana shegen surutu yasa shi yin galaba akan ta don haka sai tace min in shiga kitchen ɗin ta mata abinci dare


   Miƙewa nayi sannan da dakakkiyar fuskata nace mata

 "ina kitchen ɗin yake"kallo ta bini da shi

"bakya fara'a ne, ko gidan ne bakya son zuwa" ƙara cunkushe fuskata nayi, don naga alamar waɗannan masu kuɗin da ka sakar musu fuska sai raini ko su mayar da kai wani ɗan iska, don haka sai nai shiru nayi kamar banji ta ba


 "hjy ina jin haka take don tunda muka fito banji tace ƙala ba, itama hjy munnirar da take mata magana bata kula taba" mlm garba ya faɗa



   Bata kuma cewa komai ba sai sallamar mlm garba da tayi sannan ta kira wannan dattijuwar akan ta nuna min kitchen



 INa shiga kitchen ɗin fridge kawai na nufa na buɗe, tsayawa nayi ina kallon abinda ke ciki, babu ba abinda babu ta ɓangaren nama da veges



   Kallon fridge ɗin kawai nayi na gane me ya kamata in dafa

 ``` chicken soup served with bread``` shine starter na

 Sannan nayi ```grilled catfish served with jollof spaghetti with side salad``` a matsayin main dish


 Sannan sai ```water melon cocktail``` a matsayin dessert
*zaku samu recipe ɗin a ƙasa page ɗin in shaa Allah*


   Na riga na saba da three course meal, duk ina in dai lunch ne kƙ dinner, ina gamawa nayk serving ɗin shi a kan dinning table sannan nazo nace mata na gama


  Ok kawai tace min bari inyi sallah magariba sai kizo kiyi serving ɗina,


  Ban tanka mata ba sai ta kira wannan dattijuwa akan ta nuna min inda zan yi sallah, bin ta nayi naje na gabatar da sallah magariba ta nai nafilar dana saba yi ta bayan magariba sannan nai addua ta dana saba akan Allah ya zaɓa min komai na al khairi sannan ya haɗa ni da miji na gari in dai ina da rabon aure



   Tunda gaskiya ni bana sha'awar komawa azore har abada, anan kuwa wa zai auri ƴar baƙa kamar ni




Sai da na idar sannan naji matar nan tace min hjy na kiran ki, ƙarasa wa nayi falon nata na shiga da sallamata, tana zaune ita da wani ɗan matashi,


 Bazan iya kallon fuskar sa ba saboda ya juya wa ƙofar baya itace ta amsa min inda shi kuma hankalin sa yana kan wayar sa yana ta daddanawa


 "kin ƙarasa ko zo kiyi serving ɗin mu don har na fara jin yunwa tun ɗazu ƙamshin abincin nan ya dame ni" ta faɗa da fara'ar ta wanda nima yakamata in mai da mata da martani amma sai na share ta kawai nayi wajen table ɗin



  "auta zo muyi dinner" naji tace wa saurayin ok, kawai yace sannan ya ajiye wayar ya ƙaraso wajen dinning kallo ɗaya yayi min inda ya ɗauke kansa dama ni can bashi nake kallo ba


 "mummy me kwashe kwashe ina kika samo ƴar somalia" ya faɗa yana ƙoƙarin zama akan kujera, dariya mummyn tayi

 "asmaun ce ƴar somalia, zo kiyi serving ɗinmu kinji ƙyale wannan he likes to joke alot"


 "sincerely  speaking mum am not joking, kamar aljana haka take ga baƙi ga fuskan ta sam ba fara'a balle annuri"



   Ga mamakina sai naji mummy na dariya har da ƙara kallo na na ɗauka ,zata kwaɓe shi amma sai naga saɓanin hakan wannan ne yasa na ƙara ɗaure fuskar tawa na fara serving mummy da soup ɗin wanda za a ci shi da bread



  Na gama sai na matso zanyi serving ɗin

"in kika taɓa bowl ɗin nan bazan ci abinci ba" naji ya faɗa, ai kuwa da sauri na na ɗauki bowl ɗin na zuba soup ɗin sannan na dangwarar masa a gaban sa



  Tsayawa sukai suna kallo na inda ni kuma na gyaɗa tsayuwa ta irin ta cooks waɗanda sukan abinda suke yi sannan na ɗauke kaina daga gare su



  Buɗe baki yayi zai yi magana sai naji mummy ta dakatar da shi

"asmau me yasa kika zuba bayan yace idan kika taɓa bazai ci ba" kallon inda take banyi ba balle in kula ta



   "mummy wallahi bazan ci abinda wannan ƙazamar yarinyar ta taɓa ba" ya faɗa yana miƙewa hana shi mummy tayi sannan ta ɗauko sabon bowl a kitchen ta sake zuba masa ta miƙa masa


 "mummy bazan ci abinci ba wannan abun tana nan don sai in ƙware"


 Mummy ce ta kira ni sannan ta sallame ni juyawa nayi zan fita inda naji yana cewa


 "haba mummy me zakiyi da wannan fuskar ta kamar ta aljanu, gata ƴar ƙarama da ita dai dai suffar aljanun wannan in ka ganta cikin dare ai sai ka zura a guje" yana ta kushe hankalin sa akwance kamar be san cewar ina ji ba inda ita kuma mummy abin yake ta bata dariya



  Takaici me kawai ya gama kamani ina fita na samu wani ɗan lungu na zauna sai kuka, mutum be sanni ba amma kalmar daya fara jifa na da ita shine kalmar kama da aljanu




 Sai da suka gama ya fita daga part ɗin natan sannan  ta kira ni na shiga, na tarar da ita tana waya daga ji da hjy munnira take don naji tana cewa


"lallai na yadda ƴar baiwa ce kinga yadda sabit yake ta santi wai ya ɗauka ni na girka" shiru tayi daga gani hjy munnira tana magana ne



 Ban hana su hirar su ba sai da suka gama sannan ta juyo gare ni


 "asmau sannu da ƙoƙari gaskiya naji daɗin abincin ki, kuma ina fatan har a gama bikin nan zaki ci gaba da kawo mana daɗaɗan abincin ki"



  Ban tanka ba ta ci gaba da min bayanin irin yadda take son abincin baƙin ya kasance, breakfast, lunch, and dinner duk ni zan dinga yi amma da taimakon ma'aikatan gidan



  Sai da ta gama bayanin sannan ta sa aka raka ni boys quaters inda main kitchen na gidan yake, na gani kuma naga komai sannan aka nuna min ɗakin da zan zauna wanda bashi da nisa da kitchen ɗin sannan anan ne ma'aikatan gidan suke



    Sallah isha kawai nayi na kwanta dama ni hira bata dame ni balle raba dare, ina kwanciya nayi addua sai bacci 😴🤤



    *******************



  Kashegari da sassafe na tashi na haɗa breakfast aka kai wurin mummy, sai gata ta aiko wai in zanyi lunch inyi dayawa domin yau za a fara zuwa



   Kasancewar bansan mutanen da zasu fara zuwa ba sai nayi waina da sinasir da miyar taushe me tantaƙwashi, domin kuwa ɗai ɗai ne za suce basa son waina



  Sai ƙarfe 01 :00pm sannan na gama inda aka zo aka kwashe, kafin kace me wannan an dawo da coolers ɗin wai a kuma ɗaura wani abincin akwai baƙi masu zuwa da yamma



   Haka na dinga girki in sauke wannan in ɗaura wancen kamar ba gobe, kusan duk ma'aikatan yan iska ne sai dai su saka min ido ni kuwa da ince wance zo kiyi kaza gwanda nayi da kaina



  Wannan ne yasaka bana samun zama kuma cikin hukuncin Allah kowane course a kan lkc nane gama shi,



 Abinci ne kamar ba gobe nake dafawa don ma banayi wani dayawa amma sai dai ina yin abinci kusa kala goma a lkc ɗaya banda soups, snacks drinks duk course sai na haɗa da waɗannan



   *******************



   Sabit ango sai ƙamshi ake ta zuba wa burin shi ya kusa cika ya mallaki macen da yake ganin kamar babu kamar a duk faɗin duniyar nan


  Duk wani preparation da za ayi na bikin anyi shi kuma an shiga bikin lfy, inda aka abokanan sa suka haɗa masa dinner a sheraton hotel, sannan akai arabian night sannan a kai mothers eve ranar kai amarya a nan gidan su sabit ɗin




  Duk wanda ya ga amarya badia sai ya yaba kyan ta don kuwa gaskiya ta ɗau wanka da gyara sai dai muce Allah ya bada zaman lfy



  Duk wannan abunda ake yi asmau tana kitchen tana ta faman sarrafa abinci kala kala wanda yake barin mutane da tanɗe hannu sannan ga santi


  Sai da aka gama biki sannan ta nemi tafiya, mummy sam bata so amsau ta tafi ba saboda ta riga ta saba da abinci yarinyar amma ya zata yi



 Ta haɗa mata kayan gara sannan ta saka driver ya kai mai da ita, inda ita kuma asmaun take jim kamar an mata bushara don kuwa gaskiya ba ƙaramin gajiya take yi ba ga rashin sabo da muatanen



  Duk da dai nan ma ɗin ba wani jan mutane take yi a jikin ta ba amma ai nan ta riga ta saba da nan ɗin,



    ****************



   Amarya badia ta tare lfy, to akwai wani al ada da suke yi a gidan inda ɗuk wacce ta shigo idan tayi sati biyu zatai girki duk a haɗu a babban falon gidan gabaɗayan su aci girkin amarya



   To itama amarya badia mummy ta aika mata da wannan saƙon cewar zatai girki, hankalin badia ne ya tashi domin ita tunda take tafasar ruwan zafi ma bata sani balle wani girki



  Bata ji komai ba ta kira sabit ta faɗa masa ita fa bata iya girki, sam sabit be ji komai ba, ai ba lalle ne ba ace mace dole sai ta iya girki

      shi wannan karin maganar da ake cewa ```women belong to d kitchen``` sam be yadda da ita ba taya zayi ace don namiji be iya girki ba ba komai kuma wai mace idan bata iya ba sai ya zama tashin hankali




   shi zai nuna wa duniya cewar matar sa bata iya girki ba kuma ba wani abu bane kawai ra'ayine kuma da ita kaɗai zai zauna har iyakacin rayuwar sa har illa maa shaa Allah




  waya ya ɗauka ya kira mummyn sa ringing ɗaya ta ɗauka

"yau matar ka ce da girki da fatan ka bata kuɗin da zatai cefane"


"mummy dama abinda yasa na kira ki kenan gaskiya badia bata iya girki ba kuma ni dama ban damu ba ace wai lallai sai mace ta iya girki don haka a cire ta a cikin wannan tsarin, waɗanda suka saba girkin su ci gaba don matata bata iya ba kuma ni ma nayi supporting ɗin ta ai ba dole ne mace sai ta iya girki ba"






 Mummy mamaki ne ya kamata har ta kasa cewa komai, har sabit ɗin ya kashe wayar, wai matar sabit bata iya girki ba kai wallahi da sake



   Nufin ta abincin masu aiki ɗanta zai dinga ci ko me, mitar ta ta dinga yi har ta gaji tayi shiru tunda babu me lallashin ta



  Takan yi takaicin rashin haihuwar ƴa mace da batai ba, don wani lkcn ƴaƴa mata ma daɗi gare su, barin ma a irin wannan lkcn da tana da mace da ba sakata ta mata maganin su ba



  Kuma gashi ikon Allah dukkan nin ƴaƴan natan ukun da suke da aure da ƴaƴa babu me ƴa mace, duk jikokin natan maza ne, kullum burin ta Allah ya bawa ƴaƴan ta ƴaƴa mata lallai da anga tarbiyya





👩🏽‍🍳 *menu of d day*👩🏽‍🍳

  ```chicken soup served with bread, grilled fish served with jollof spaghetti and side salad, melon cocktail```


 
```chicken soup```

  ```ingredients```

-chicken breast (tsokar naman na ƙirjin kaza)
-albasa
-tafarnuwa
-maggi
-curry
-flour



_method_

1) ki sami chicken breast din ki, sai ki wanke tas sannan ki yanka shi ƙanana yankan cubes


2) ki ɗauko tukunya  ki saka naman, maggi, tafarnuwa albasa, sai ki rufe don ya dahu


3) idan kazar ta hadu sai ki tsame naman sannan ki sai ki sauke ki tace, ruwan naman kawai ake so, sai ki ƙara mayar da tacecen ruwan namaki akan wuta don ya kara tafasa ki zuba naman kazar ki zuba curry


 4) ki dauko flour ki kwaɓa shi da ruwa kamar zakiyi wainar flour sai ki zuba a ruwan idan ya tafasa sannan ki rage wutar sai kiyi ta juya wa kar ki ɗauke hannu don sai yayi miki gudaji, idan yayi ɗan kauri sai ki sauke a ci da bread


   ```grilled fish served with spaghetti and side salad```


 ```Ingredients```

   _grilled fish_


-kifi
-albasa
-tafarnuwa
-citta
-attaruhu
-curry
-man gyaɗa


```method```

1) ki wanke kifin ki tas sannan sai ki ajiye shi a gefe

 2) ki ɗauko kaskon gashin ki sai ki ɗan goga masa mai, sannan ki saka kifinki,

3) ki barbaɗa masa maggi, ki yanka albasa slice, a jajjaga tafarnuwa da citta da attaruhu duk a zuba akan kifin sannan ki barbaɗa curry sannan a gasa a oven kar ki sakar mata wuta don sai ya ƙone idan ya gasu sai ayi serving


_spaghetti_

```ingredients```
-spaghetti
-kayan miya
-mai
-maggi
-curry
-albasa


1) ki zuba mai a tukunya  da ƴar albasa idan ya ɗauko soyuwa sai ki zuba kayan miyar ki ki ci gaba da soyawa


2) idan kayan miyar sun soyu sai ki zuba ruwa da maggi curry sai ki rufe

3) a wata tukunyar daban kuma ki zuba ruwa idan ya tafasa saiki zuba taliyar ki, kar ki bari ta dahu tafasa ɗaya biyu sai ki sauke ki tace sannan ki wanke ta (wannan yana sawa idan kin gama taliyar ki ruwan taliyar bazai yi kaurin nan ba)


4) idan ruwan kayan miyar ya tafasa ki ki zuba tafasasshiyar taliyar ki sannan ki rage wuta ki zuba lawashin albasa, idan ya ɗan kara tafasa sai ki sauke

_side salad_

```ingredients```
-tomato
-gwanda

```method```

1) ki yanka tomatoes ɗinki sannan ki yanka gwandar ki duk cubes zaki yanka sannan sai kiyi serving kusa da taliyar ki da kuma kifi



_melon cocktail_

```ingredients```

-kankana
-sugar syrup


_method_

1) ki yanka kankanar ki cubes ƙanana bayan kin cire ƙwallayen,

2) ki zuba sugar da ruwa a tukunya ki ɗora a wuta idan ya tafasa sai ki sauke idan ya huce sai ki juye a kan cubed kankanar ki ki saka a fridge idan yayi sanyi sai ayi serving a ci da spoon


 👩🏽‍🍳 *bon appetit*👩🏽‍🍳



   *ASMA'UN SABIT*
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)



   P⃗a⃗g⃗e⃗  6🌹




 Mummy rasa yadda zatayi da sabit gashi kowa ga san ran girkin matar sabit gashi shi kuma ya kira yace baza tayi girkin ba


 Ita ba wannan ne ya fi damun ta ba tunda yarinyar nan asmau mara fara'a ta tafi abincin gidan kamar cusa shi take sam bata jin daɗin sa



  Juyi ta dinga yi akan gado tana ƙarawa daga ƙarshe ta tashi ta dauki land line na gidan ta kira kitchen knda ta shaida musu suyi musu dinner gabaɗaya gidan


 Abin yabawa ma'aikatan mamaki saboda da safe ta kira tace karsuyi amma kuma yanzu ta kira tace suyi


  Sai da yamma tayi kowa ya dawo daga aiki duk an hallara wajen cin abinci za a fara ci sai mummy

"to amaryar sabit dai bata iya girki ba kuma mijinta ya ɗaure mata gindi yace shi ba komai ai ba sai lallai mace ta iya girki sannan za a zauna da ita ba"


  " haka ne mu ba kowacce mace ce akayi ta domin kitchen ba" maganar nan tayi bala'in ɓatawa mummy rai inda ta kai masa harara


"to daga yau sai ku dinga cin abinci a part ɗinku in cook zaku ɗauko bismillah amma mun daina ciyar ku"


  Babu wanda ya kuma cewa komai mummy ta so daddy ya mara mata baya amma sai taji yayi shiru dama shi mutum ne me bin ra'ayin ƴaƴan sa


  Sai da suka gama cin abincin ne sannan mummy ta kuma nanata musu akan su nemi me ciyar da su don ta tsame su daga waɗanda zata dinga ciyar wa, ko a jikin su daga badiar har sabit ɗin suka kama hanyar part ɗin su



   Kashegari badia ta kira mmn ta ta faɗa mata abinda yake faruwa da kuma hukuncin da suka ɗauka na ɗauko cook,

 

   Mmn badia ta sha alwashin sai ta nemo musu cook ɗin da ita kanta mummyn ma a wajen su zata dinga kwaɗayi



  Cikin hunkuncin Allah aka samo musu wata agnese kafira ce, amma tsohuwar cook ce abincin ta da daɗi kasancewar ta daɗe tana yi


  Kafin su tashi da safe ta haɗa musu breakfast haka ma kafin su dawo da yamma ta ajiye musu lunch haka ma dinner akan lkc wannan ne ya kwantar da hankalin ma'auratan ya kasance ba abinda suke yi daga aiki sai soyayya 😍



  Ana haka ana haka badia ta samu ciki, me shegen laulayin tsiya ga miyau, ga shegen kwaɗayi, rannan da sassafe ta na tashi wa alala zata ci, don haka sai sabit ya sauko ƙasa don gayawa agnese tayi mata alala



  Me zai gani agnese ce a kitchen hannun ta a hammat sai faman susa wa take yi, tana gamawa ta saka shi a hanci ta shinshina yana gani yadda ta ɓata rai daga dukkan alamu bata ji daɗin warin da hammatar ta take badawa ba sannan ba wanke hannu kawai ta koma ta ci gaba da girkin ta



  Jun shi yayi kamar zai yi amai tunanin girkin ta daya dinga ci yayi, ji yayi gabaɗaya zuciyar shi na tashi, be yi ƙasa a gwiwa ba yana zuwa ya gayawa badia abunda ya gani



 Aikuwa itama sai amai anan inda take, abu goma da ashirin ya haɗu ya haɗar wa sabit, shi yayi aikin aman sa don ba ba komai a aman sai ruwan da tasha



  Badia da kanta ta kori agnese sannan ta kira mmn ta akan a nema musu wata sabuwar cook ɗin ko da mmn ta tambaye ta ina agnese sai ta faɗa mata abinda sabit ya faɗa mata



 Ita kanta mmn ta koka da wannan abu inda tai mata alaƙawarin sake neman wata me aikin, too fa aiki ya dawo sabit sabo, ya je aiki a hanyar shi ta dawo wa doƙe ya tsaya a restuarant ya sai musu abinci kafin ya dawo



  Wani lkcn in ya makara sai dai ya kira badai ta siyo musu haka suka dinga jaurar siyan abinci sune shiga wannan restuarant fita wancan don siyan abinci



 Rannan sai ya kama ranar da badia zata siyo abinci ne amma sai ta manta sabit ya dawo gida gajiye ga yunwa ko da ya tanbayi abincin sai tace masa ba kak bane da siyowa



  Ranshi ne ya ɓaci don abun nata kamar da rainin wayo,

"so nawa zan siyo jiya ba ni na siyo ba" ya faɗa ranshi a bace, ɗaga kafaɗar ta tayi alamar bata damu


"na manta na ɗauka kai ne yau ma" ranshi ne ya ƙara ɓaci wato ita sam bata ma san laifi tayi ba ko, nan da nan ya hau masifa inda itama ta biye masa sukai ta bala'i



   Wannan shine faɗan mu me girma na farko tun aurensu amma sun yi faɗa kamar ba gobe daga ƙarshe kowa yayi zuciya ya kama hanyar ɗakin sa baza a kwana tare ba, a daren badia tai ɓari



 Sabit be sani ba sai da safe da ya fito ya ganta a falo da akwati tana ta ja ita zata tafi gidan su kamar ya share ta sai kuma dai ya tambaye taa

"ina zaki da akwatin nan haka"


 "gidan mu zan koma tunda wanda ya ajiye ni be damu dani ba har nayi miscarriage be sani ba"




 Kalmar miscarriage ce kawai ta dawo da shi daga tunanin da yake

 "what, me kika ce" ya faɗa yana kara matsawa kusa da ita cike da tashin hankali maimai ta masa tayi tayi ɓari



 Jikin shi har rawa yake ya sunkuce ta sai mota yana ta adduar Allah yasa ba gaskiya bane cikin daya ƙwallafa rai da shi za a ce ya zube subhanallah



  Gudu kawai yake falfalawa domin son zuwa asibiti sai da badiar tai masa magana ma akan ya rage gudun sannan ya rage burin shi su je asibitin ace bai zube ba


  Cikin ikon Allah suka iso asibitin da badia ke awo suka shiga wajen ganin dr. binciken farko ya nuna ciki babu shi



 Sabit kamar yayi kuka a rayuwar shi yana son yara barin ma ace yadda badia ke da kyan nan a haɗa da nashi ai Allah ne kaɗai yasan irin kyan da ƴaƴan su zasuyi



  Hankalin sa ne ya tashi sosai inda duk ya bi ya tsagwami kansa don shi a tunanin sa faɗan da sukai jiya ne ya zubar mata da cikin





Badia sam hankalin ta be wani tashi ba kamar yadda sabit ya tashi nashi hankalin daga ƙarshe ma sai ita ce ta koma tana lallashin sa

" haba *SD* kar ka damu in shaa Allah we will try again, kuma cikin be fi wata biyu"

"only kin kuwa san yadda na ɗaura raina akan cikin nan wallahi nagi nake yi kamar fault ɗina ne da bamuyi faɗa ba da ƙila cikin bai zube ba" ya faɗa da alamar tausayi a tattare da shi



  Lallashin sa ta dingayi, bayan an basu magani an sallame su sai ta saka rigimar ita gida zai kaita har ta warke


  Ba haka ya so yaso ace ta dawo gidan sa tayi jinya amma ganin bata da lfy ya shi ƙin cewa komai kawai yai hanyar gidan su da ita



 Yana ji yana gani ya kai badia gidan su ya baro ta acan don ta samu ta ɗan huta, kuma ta samu sauƙi, ko da ya dawo gida ya faɗawa mummy abinda ya sameta



  Sai mummyn ta jajanta masa sannan tai masa ƙorafin zuwan badia gida, kyakkyaɓe mata fuska yayi kamar zai yi kuka, wannan ne ya sa ta jan bakin ta tayi shiru


 

   ********************


  Sai da badia tayi wata guda a gida sannan ta dawo shima sai da sabit yai ta safa da marwa yana roƙon ta sannan ta dawo anna wannan karan ma da sabuwar cook ɗin su



  Me suna kulu, to ita matsalar klu bata iya kowane abinci ba sai tuwo da dai dangin na gargajiya bayan kuma su sabit ƴan zamani ne ba son tuwon suke ba



 Wannan dalilin ne ya sa kulu bata daɗe ba suka sallame ta, suka koma take away daga restuarant

  

    Duk abinda ke faruwa a part ɗin sabit mummy tana sane ta ƙyale shi ne kawak don taga iya gudun ruwan sa



  A ka ci gaba da yin take away har Allah ya kuma haɗa su da wata sabuwar cook ɗin, ita kuma sata duk abinda ta gani sao ta ɗauka ta ɓoye da taga lkcn ba mutane sai ta fice daga gidan



   Rannan sai ta ɗauki agogon sabit ya ajiye akan dinning table yana breakfast kawai ya shiga ɗaki  ya fito ya nemi agogo ya rasa



  Tun yana nema shi kaɗai har badia taji suka shiga nema tare, abu kamar wasa agogo yayi ƙafa ya gudu


  Sam basu kawo ita ta ɗauka ba don har da ita ake ta nema, sai badia ce kamar ance ɗaga idon ki ki kalle ta sai taga gefen zanin ta yayi wani ƙulili

 Tambayar ta tayi

"ke meye a jikin ki haka" nan da na sa jikin yarinyar ya ɗaurawa, badia kuwa ta kwacume ta ta kwance mata zani sai ga agogo



  Shidai sabit tunda ya ɗauki agogon sai ya fice ya barsu inda badiar ke ta dura mata zagi, daga nan ita ma ta kore ta,



   Abinfa ya fara isar sabit wai duk masu girkin da aka samo musu sai sun samu matsala ne me yasa baza su samu cook ɗaya ba mtsss Allah dai ya kyauta



  Kuma neman wata cook ɗin sukai inda aka kawo musu wata tivi, kana ganin ta kaga rashin tsabta, har wani tashi take don tsabar tsamin da ke fita daga jikin ta



  Sabit sam hankalin sa be kwanta da ita ba don shi mutum ne me shegen ƙyanƙyami don haka ko tayi abinci baya ci sai dai yai ta raɓe raɓe yau shine cin abinci anan gobe a can



  A maimakon shi da yake da mata a ganshi ya murmushe sam sai ma wani ramewa yake yi, ya ya bazai rame ba sam baya samun kulawa ko ta ɓangaren cin abinci balle kyakkyawan kula daga matar sa



  Sun tashi da safe sun fice gabaɗaya idan sun dawo da yamma kowanne su a gajiye yake don haka kowa ta kai ta kai yake balle badia ita bata san wani wahala da wani ba balle tace wannan mijinta ne ai ba yaro bane zai iya kula da kanshi haka take cewa



   Tun mummy na ɗauke kai har abin ya zo ya fara damunta ta kasa shiru kun san tsakanin ɗa da mahaifi balle kuma mummy me shegen son ƴaƴa



  Don haka rannan da ya shigo da safe gaishe ta sai ta gabatar masa da abinci be ji komai ba ya zauna ya takr cikinsa kamar wanda ake wa horon yunwa


"yanzu sabit rayuwar da ka ɗaukar wa kanka kenan ta horƙn yunwa, baza ka zauna ka faɗawa matar ka gaskiya ba ta tashi ta zama mace ta iya girki don ka dinga ci amma sai ka dinga ɗaurewa karya .....🙊 kullum kai kenan zama da yunwa wai akai a matsayin na me mata to meye amfanin auren kenan"



  Ta ɗauka zai tanka ko ya kare matar tasa sai taji yayi shiru yana gama ci sai ya miƙe

"mummy don Allah ki neman mana cook me tsafta wacce zata dinga mana girki" yana gama faɗar haka yai ficewar sa maganar tayi mutuƙar ƙona wa mummy rai wato har yanzu shi ba daddara ba




👩🏽‍🍳 *menu of d day*👩🏽‍🍳


   ```danbun shinkafa served with offal pepper soup and kunun zaƙi```


  ```danbun shinkafa```

_ingredients_

-shinkafa
-zogale
-gyada
-mai
-maggi
-cabbage
-carrot
-green pepper
-albasa
-attaruhu


 1)ki ɗauki tukunyar ki ki zuba mata ruwa ba dayawa ba idan kina da colander ki ɗora idan ba colander kuma sai ki saka murfin tukunya wanda zai shige cikin tukunyar a tabbatar ruwan yana ƙasan  murfin yadda idan an saka buhu ruwan bazai taɓa shi ba,  ki ɓarza shinkafar ki sai ki tankaɗe ta ko za a samu gari a yi amfani da barjajjen kawai, ki wanke sai ki zuwa a buhu ko colander, sai ki saka a tukunyar sai ki rufe

2) ki samu zogalen ki (idan ɗanye ne ki zuge ki wanke, idan bushash she ne sai ki jiƙa shi da ruwan zafi ki ajiye shi)

3) ki ɗauko gyaɗar ki ki ɗan daka ta sama sama kar ta dake

4) idan shinkafar ta fara tirira sak ki sauke ki juye aroba ki zuba zogale gyaɗa ki juya ki ɗan yayyafa mata ruwa si ki ƙara mayar wa


 5) ki wanke cabbage,  green pepper, carrot (bayan kin kankare shi) sai ki yanka yadda kike so ki ajiye,

6) ki yanka albasa manya manya, jajjaga attaruhu duk ki ajiye, idan shinkafar ta tirara sosai sai ki sauke ki juye a roba ki zuba ƙayan cabbage ɗin nan albasa attaruhu maggi mai, gishiri ki juya a ɗanɗana idan komai yaji sai a ƙara yayyafa mata ruwa a kuma mayar wa a buhu a mayar tukunya sai a barshi ya tirara sosai har sai komai ya dahu sai a sauke ayi serving

*p s* a dinga yi ana duba ruwan ƙasan tukunyar idan ya ƙone sai a ƙara, ga masu amfani da buhu kenan



_offal pepper soup_


```ingredients```

-kayan ciki
-dankali
-attaruhu
-albasa
-maggi
-curry
-thyme


  ```method```
1) a wanke kayan ciki tas da kyau yadda za a cire duk wani ƙazanta da ke tattare da su sai a ɗora a tukunya a sakar masa ruwa sosai ya sha kansa, a zuba thyme albasa tafarnuwa, maggi sai a rufe a barshi yai ta tafasa


2) ki fere dankalin turawanki ki yanka shi irin yankan da kikai wa kayan cikin sai ki ajiye a jajjaga attaruhu, a ƙara yanka albasa sai a ajiye su


3) idan kayan cikin ya dahu sai ki zuba dankalin ki da albasa da attaruhu da curry da maggi in baiji ba ki ƙara ruwa sai ki rufe ki rage masa wuta ya ƙarasa dahuwa a hankali idan ya ƙarasa saiki sauke sai aci shi da ruwa ruwan sa da danbun shinkafa



 *KUNUN ZAKI*


*ingredients*

 _Gero_
 _Citta_
 _Sugar_
 _Lemun tsami_
_Flavor_
_kanunfari_
_kimba_


*method*





1) Ki jiqa geronki a ruwa tare da in da hali da daddare kafin safiya ya jiƙu


2) ki wanke a ki haɗa da citta kanunfari da kimba a markado ki tace. Sai ki dibi kadan ki dama koko  dashi ki ajiye shi ya huce



3) idan ya huce ki zuba ruwa ciki, Kisa sugar da flavour da ruwan lemun tsami kisa a fridgeyayi sanyi, idan an tashi sha sai an ɗan juya shi kafin shaa🍸


   👩🏽‍🍳 *bon appetit*👩🏽‍🍳


 *ASMA'UN SABIT*
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)



   P⃗a⃗g⃗e⃗  7🌹









Duk a tunanin sabit mummy zata nemo musu cook amma sai yaji shiru kamar an shuka dusa don haka sai ya yanke hukunci tunkarar ta ya tambaye ta



  Ai kuwa yana kawo mata zancen cook ɗin ta rufe idon ta tai masa tas tai masa wankin babban bargo sannan ta kore shi jikin shi a saɓule haka ya fita daga part ɗin nata



  Shi sam ya kasa gane mummy to menene don macr bata iya girki ai shi be ga wani abu ba ace mace bata iya girki



 Shi wai ace ai wacce ta iya girki shi sam abin baya birge shi, ko yaga abokan sa suna kurin matan su sun iya girki shi tausayin matan ma yake ji gani yake yi kamar an tauye wa matar haƙƙin ta



 Don haka in shaa Allah zai ci gaba da neman cook har su dace amma badiar sa fara tas da ita ga gayu ai kitchen be dace da ita ba



  *******************



    Bayan kwana biyu sai mummy ta tashi da zazzaɓi me zafi inda aka kai ta asibiti bayan test ɗin da akai mata sai aka gano damuwa da kuma rashin bacci yake damun ta



  Haka ƴaƴan suka tasa ta a gaba sukai tai mata faɗan wai me ta rasa, aka bata magani aka sallame ta, ko da ta dawo gida sai ta kasa cin komai duk abinda aka bata sai tace baza ta iya ci ba haka suka yi da ita har ta kwana bata ci komai ba ciwo kuma sai ƙara gaba yake



 Kashegari tana tashi sai taji sha'awar wani pepper soup da asmau ta taɓa yi lkcn zamata da bikin sabit don haka sai ta faɗawa sabit akan ya je yasa a yi mata


 Be wani ɓata lkc ba ya karɓi address ɗin restuarant ɗin  hjy munnira, yana zuwa ya ci karo da hjy munnirar ashe ma mummyn ta kira ta faɗa mata har tasa asmaun ɗaurawa



 Don haka bai daɗe ba ya karbo ya taho, ko da ya kawo yadda ya ga mummy tana shan pepper soup ɗin nan ya saka shi ma ɗan zubawa don sha



 Ai kuwa daga ƙarshe tas ya shanye har mummy na cewa ya bar mata na anjima, sai a lkcn ya faɗa mata ai ya shanye

"ai yarinyar ce ta iya girki ga ƙanƙanta amma girkin ta ko babba sai haka" shi dai sabit don santi ko tankawa be yi ba


 Tun daga lkcn ya zama daily customer na restuarant ɗin kuma yana zuwa zaice a sa yarinyar da mummy take son girkin ta tayi masa



  Tun daga lkcn ya kasance kullum shi yake zuwa yana yi musu order shi da badia



   Baya iya cin abincin ko ina sai na restuarant ɗin safe rana yamma kullum yana hanya



  Rannan sai yaje da safe wurin mummy tana zaune ta gama breakfast, tayi masa tayi sai ya ƙi ci, gyara zama yayi sannan ya fara koro mata bayani



 "mummy tunda mun neman cook me zai hana kije restuarant ɗin nan kice su bamu cook ɗaya ta dinga mana girki, wallahi kullum na fita daga gidan sai na cen cin abinci


 Kuma idan aka taso haka har na fara gajiya"


 Taɓe baki mummy tayi sannan tace

"yo me kake son inyi maka tunda kai ka riga ka yadda matar ka ba matar kitchen bace ai sai kaje kai ta muku order ɗin tana zaune ba abinda take yi" ta faɗa tana mikewa don barin wajen



 Binta yayi yana mata magiya tare da faɗa mata irin wahalar da yake sha wajen yin order ɗin kullum


 Buris tayi da shi kamar bata ji ba duk da dai abinda ya faɗa mata ya taɓa mata zuciya sosai, amma saboda tana son ya gane kuskuren sa sai ta yi kamar bata san yana yi ba



  Magiyar yaci gaba da yi mata kamar zai yi kuka kun san tsakanin ɗa da mahaifi ai kuwa nan da nan zuciyar ta ta tsinke inda tai masa alƙawarin zuwa da yamma



 Murna yayi mata sosai hadda bata kuɗi wai ko da za abuƙaci payment a take kuma cash, tausayin sa ne ya kamata, ohhh Allah Allah be haɗa shi da mace da ta san darajar aure ba ga shegen ra'ayin shi na ƴan boko ta faɗa tana mita





    Sai bayan la'asar sannan mummy ta saka driver ya kaita wajen hjy munnira, don ta gabatar mata da buƙatar ta na son karɓar asmau a matsayin cook




 Kasancewar mumy ta nuna wa hjy munnira ƴaƴan banki ya sa maganganun nasu basuyi wani tsaho ba hjy munnira ta yadda da zata ba mummyn asmaun inda za adinga ba hjy munnira kuɗin aikin natan



   Asmau bata san hawa ba bata sauka ba kawai sai ce mata akayi ta haɗo kayan ta, ta ɗauka azore za ta koma har ta fara jin ba daɗi,



 Ko da suka fito ta ci karo da mummy sai ta ƙara haɗe wannan fuskar tata da sam ba fara'a, mummy tana hango ta ta saki murmushi duk da dai asmaun ranta a haɗe yake


 "wai ni hjy munnira yarinyar nan bata fara'a ne", mummy ta tanmbayi hjy munnira dariya kawai hjyr tayi bata tanka ba don itama bata taɓa ganin murmushin ta ba balle dariya, babu bayanin da hjyr tayi wa asmaun kawai dai tace mata zaki koma gidan hjy ki dinga musu girki



   Ƙara haɗe girar ta tayi wai me yasa mutanen nen suka son mai da ni wata mara gahilu ne daga ni ce nan sai nice nan


  Gani bata tanka musu ba yasa mummy ta miƙe


"to hjy mudai mun tafi fatan mu Allah ya bamu damar riƙe wannan amanar"

"to hjy na gode ai asmau bata da matsala sam baza ki ji ta tana cecekuce da wani ba magana ma bata dame ta balle kuma faɗa"


"ai ba sai kin faɗa ba daga ganin yanayin ta" sukai sallama sannan suka kama hanyar gida



 Ko da suka iso gida sai mummy ta sa aka bata tsohon ɗakin da ta zauna lkcn biki sannan mummyn tai mata bayanin yadda take son abincin ya dinga kasancewa



  Tun daga lkcn asmau ta fara girki a gidan breakfast lunch dinner kullum ba fashi, da farko daga mummy sai ɓangaren sabit kawai take wa abinci amma da ragowar ƴaƴan suka gano daɗin abincin sabuwar cook ɗin duk sai hutash she da matan su



   Tun daga lkcn duk abincin gidan asmau ce take yi, kowa ya saba da cin daddaɗan girkin ta me sanya mutum santi, kafin kacr meye wannan sabit ya murmure yayi ƴar kiba yai fresh da shi abin shi kamar ba shi ba wannan abun yasa kullum mummy take godewa Allah daya haɗa ta da asma'u  a matsayin cook ɗin su



  Ba sabit ba gabaɗayan yaran ta duk sun saba da wannan girkin da baiwar Allahn nan take yi sam babu wanda ya taɓa sawa a ransa cewar wataran zata bar gidan kunji ɗan adam





 *BAYAN SHEKARA BIYU*



  Ba abinda ya canza a rayuwar gidan su sabit sai lalacewar matan gidan, yo lalacewa mana don yanzu kowacce ta sakankance da asmau



  Duk wani abu da suke so daga sun ɗaga waya sun kira kitchen sun faɗa nan da nan za a kawo musu


  Ta ɓangaren sabit kuwa sau biyu badia na kuma samun ciki yana zube wa inda daga ƙarshe aka gano cewar indai har suna son ciki ya zauna a marar badia sai da ta ta samu cikin ai mata ɗaurin mahaifa


 

  Ga sabit da shegen son ƴaƴa duk inda yaga ɗa sai ya ɗauke shi barin ma ace ɗan fari ne, shi dai yana son mutum fari duk munin farin mutum baya gani


  Haka zalika duk kyan baƙin mutum sabit baya gani sai yace ak shi wai baƙin ne yake kare masa ganin kyan, sai yayi taji ana cewa black beauty black beauty amma shi sam be taɓa sanin me kyau a baƙi ba



   Har musu suke yi da abokan sa musammam masu baƙaƙen mata akan ɓaƙi ma yana da nashi kyan amma sabit sam be gane wannan karatun ba shi dai in kai baƙi ne to kawai kallon muni yake maka



  Duk da dai yana da son yara amma baya son baƙin ɗa gashi mataɗ shi Allah ya haɗa ta da matsalar haihuwa inda suke ta fafutuka, Har yanzu a wannan halin suke inda sabit ya biya musu ummara suka kama hanyar ƙasa don su roƙi haihuwa



  Ita badia sam abin be damun ta dama can ita ba child person bace ita ba mace bace me son yara ba don haka abin ko a ƙarƙashi takalmin ƙafarta wai rashin haihuwarta sam be dame ta ba




👩🏽‍🍳 *menu of d day*👩🏽‍🍳


   *cornflakes crispy cake, miyar gyaɗa with tuwon shinkafa, coconut drink*


  *cornflakes crispy cake*

 *ingredients*
-corn flakes
-chocolate bar
-butter
-sprinkles (ko wane iri)
-marshmelow (optional)
-vanillah extract
-salt

 *method*

1) ki narka chocolate da butter ko  a micro wave ko a kan wuta amma pls kar a sakar masa wuta


2) idan sun narke sai ki juye su a roba sannan sai ki zuba vanilla da ɗan gishiri kaɗan


 3) ki rugurguza cornflakes ɗinki da hannu ƙanana sannan sai ki zuba ki juya sai kasance kamar tuwo ne, irin zasu cure ne waje ɗaya amma duk da haka cornflakes ɗin zai kasance da ƙarfin sa


 4)sai ki ɗauko cupcake case ɗin ki ki dinga ɗiban haɗin nan kina sawa kina ajiyewa, idan kin gama sai ki bi kowanne da marshmelow sannan ki watsa sprinkles ki saka a fridge domin yin sanyi sai aci




*tuwon shinkafa served with migar gyaɗa*


*ingredients*

- farar shinkafa ta tuwo

-gyaɗa
-tomatoes
-attaruhu
-albasa
-tafarnuwa
-citta
-wuyan rago
-curry
-alayyahu
-thyme
-maggi & salt

  *method*

1) ki haɗa naman,maggi, gishiri, albasa, tafarnuwa sai ruwa a cikin tukunya ki dora ki barshi yaita dahuwa


2) soya gyaɗa sama sama ta yadda ɓawon gyaɗar zai fita, sai ki surfa ki cire ɓawon sai ki daka ko kiyi blending, ki haɗa tomatoes da attaruhu kiyi blending shima

3) idan naman ya ɗauko dahuwa sai ki zuba kayan miyar ki da soyayyan man da kike so amma kaɗan kasancewar gyaɗar itama zata fitar da nata man


3) idan sun ɗan tafasa sai ki dama dakakkiyar gyaɗar ki da ruwa ki zuba, ki ƙara ruwa iya irin ƙaurin da kike son miyar sannan ki ƙara maggi in baiji ba ki rufe ya ci gaba da dahuwa


4) idan ya dahu kin tabbatar da komai ya dahu, sai ki ɗauko alayyahun ki ki wanke sannan ki yanka sai ki zuba a miyar ki gare mata wuta ki bashi minti 1 sai ki sauke


5) ki wanke shinkafar tuwon ki ki jiƙa ta

6) ki zuba ruwa a tukunya wanda zai ishi shinkafar sannan sai ki rufe, idan ruwan ya tafasa sai ki tace jikakkiyar shinkafar ki ki zuba ki rufe don ya dahu


7) idan shinkafaɗ ta ɗauko tsotsewa sai ki rage mata wuta ya koma low saboda ta ƙarasa tsotsewa a hankali,


8) idan bayan ta tsotse sai kika ji bata dahu ba sai ki ƙara mata ruwan zafi amma karki taɓa ta ki barta haka akan low heat har ta shanye ruwan sai a tuƙa a kuma rufewa akan low heat ɗin


9) idan ta turara sai ki kwashe


*P S* ki sani dahuwar shinkafa ko ta ci ce ko ta tuwo ce ta fi son wuta kaɗan kaɗan da ta ɗauko dahu




 *coconut and banana milk shake*

*ingredients*

-ruwan kwakwa
-ayaba
-ice cream ko madara
-sugar
-ƙanƙara


*method*

  1) bayan ki markaɗa kwakwar ki kin tace ruwan to  ruwan kwakwar shi zamuyi amfani da shi

2) ki yanka ayaba ƙanana ki haɗa da ruwan kwakwa ice cream ko madara sai sugar sai ƙanƙara sai kiyi blending ɗin su


3) idan suka marƙadu sai ki juye a cup ko jug sai ki ƙara yanka ayaba a kai ayi serving


👩🏽‍🍳 *Bon appetit*👩🏽‍🍳


  *ASMA'UN SABIT*
[4/17, 2:24 AM] 🥦: 🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)



   P⃗a⃗g⃗e⃗  8🌹





Mummy tana zaune rannan da yamma sai ga hjy munnira sam mummy bata kawo komai ba, suka zauna suka gaisa sai hjy munnira tace


"hjy takakkiya nayi, wallahi iyayen asmau sunce a dawo da ita lkcn aure yayi"


 Mummy ji tayi kamar hjy munnira ta soke ta ita sam bata taɓa kawo wa cewar wai asmau zatai aure ba, ta gama sakankan cewa kaji san kai


 Gyara zaman ta tayi don wannan magana ce da a za yi ta sosai asmau zata tafi bayan sun gama sakin jiki da girkin ta ai da sake



   "hjy munnira ya baki taɓa min wannan maganar ba sai yau" inji mummy

"yo hjy sai na gaya miki ai kema kinsan mace ce kuma wataran dole ne tayi aure ko ba haka ba" shiru mummy tayi don kuwa zancen hjy munnira gaskiya ne



  Tattaunawa suka shiga yi inda daga ƙarshe aka yanke hukunci mummy zata neman mata miji a cikin ma'aikatan gidan tunda ko taje can ma sai Allah ya haɗa ta mijin


 A haka sukai sallama akan idan mummy ta samo mata mijin zata kira hjy munnira



   Mummy ta tara ma'aikatan ta maza sannan ta musu albishirin akwai yarinyar da take son aurar wa cikin su ko akwai me so



 "kar ku damu sadaki da kayan aure duk ni zanyi"


  Kusan mutane biyar suka amsa suna so amma tunda mummy ta ambaci sunan asmau sai kowa ya janye


Mummy ba yadda batai da ma'aikatan ba amma kowa sai ya ƙi, kowa sai ya dinga kawo uzurinsa


"wa zai auri wata asmau ga baƙi ga rashin fara'a" inji driver, babu yadda mummy batai ba amma fafur suka ƙi haka ta sallame su suka watse



  Duk wannan abun da ake yi asmau bata san wainar da ake toyawa ba, hankalin mummy ne ya kuma tashi don duk yadda ta ɗauki abun ba haka yake ba


  Shawara ce ta faɗo mata sai ta tara ƴaƴan ta ko akwai wanda zai auri asmaun in yaso sai ta zauna amatsayin cook ɗin daga baya idan ta girma ta mallaki hankalin ta a san yadda za a yi



  Bayan duK sun taru amma banda sabit wanda yake ƙasa me tsarki shida matar sa, mummy ta gabatar musu da maganar da kuma hukuncin da ta yanke na ɗaya daga cikin su ya aure ta in yaso daga baya a san abin yi amma yanzu wannan shine kawai shawara



 Shiru sukai kowannen su na jimamiba wanda yake son auren asmau, da babban ɗanta tafa ra


"isma'il me kake tunani"


"gaskiya mummy bazan aure ta ba saboda kwananan zan sake aure ƴar meduguri ce magabata kawai zan gabatar a fara shirye shirye"



  Ako koma kan na biyu sulaiman shima ya kawo uzurinsa, mummy tana kallon muktar ɗan ta na uku yace


"gaskiya bazan iya ba matana sun iya girki"


   Tooooo faaaa abu ya taru ya haɗar wa mummy

"yanzu duk cikin ku babu wanda zai auri yarinyar nan na wani ɗan lkc haka kune son yarinyar nan ta tafi, a banza a wofi" ta faɗa ranta a ɓace



   Kowannen su ɗauke kansa yayi mummy ta dinga faɗa kamar ta ari baki dukkan su suka tsuke baki can sai sulaiman yace


 "mummy ai mu mun matan mu sun iya girki, ɗan autan ki ne matar sa bata iya girki ba kuma yarinyar nan kamar saboda su take zaune me zai hana ki aura masa ita"



   Dukkan su suka amsa da haka ne kam shi kaɗai ne ma mata ɗaya


 mummy shiru tayi tasan halin sabit da rigimar sa zata iya lanƙwas kowanne su amma banda shi,


 "kun san halin sabit zan iya lanƙwasa ku amma banda sabit taurin kansa yafi komai"


  "mummy ba sai ayi auren ba kafin ya dawo sai dai kawai ya dawo ya tarar da amarya" muktar ya faɗa yana d ariyar mugunta don ba ƙaramin rigima za a sha da sabit ba idan ya dawo ya tarar da ya angwance 💑




 Babu yadda mummy ta iya haka ta ɗauki shawarar ƴaƴan ta dole ne ta aurawa sabit asmau kafin ya dawo in yaso idan ya dawo ayi duk waccd ayi da shi ita dai ta riga ta gama



 Bata ɓata lkc ba taje ta faɗawa mijinta batun auren sabit ɗin da asmau amma bata faɗa masa dalilin auren ba



  Dady sai yace
" to shikenan dama gobe zani kano ɗaurin aure sai kawai mu ƙarasa can garin su yarinyar sai a ɗaura mata tunda kince ya dawo kike son ayi"



  Mummy sai taji daɗin yadda sam dadyn be yi tambayoyi akan auren ba


  Aka gama shirye shiryen auren duk mutanen gidan suka dunguma sai kano auren sabit da asmau har da asmaun wacce sai a mota sannan mummy tai mata bayanin auren



  Da yake da ƙuruciya a tattatare da ita sai ta yadda, lfy suka isa kano suka sauka a hotel ɗin tahir guest palace suka kwana



  Kashegari suka kama hanyar azore, kasancewar ba a san da zuwan su ba don haka suna isa suka sauka a gidan me garin na fulanin



  Suka gabatar da abinda ya abinda ya kawo su sam me garin be gane asmau ba sai da tayi bayani sannan ya gano ta



  Nan da nan yasa aka kira kawun na tan ya zo shima aka gabatar masa da maganar auren



  Mummg tayi mamaki da taji cewar basu suka tura hjy munnira ba da maganar auren suka ce musu su rabon da hjy munnira ma ta bada kuɗin aikin yarinyar har sun manta



   Ko kaɗan dady be ji daɗin wannan abun ba yarinya tana aiki amma sam iyayen ta basa samun ladan aikin ta, sai da ya biya su kuɗi a madadin na aikatau ɗin ta sannan suka kuma gabatar da aurawa ɗan su asmau



  Babu wani ja'inja wan mahaifin asmau ya yadda inda atake a ka ɗaura auren sabit da asmau akan sadaki mafi ƙanƙanta



    Baffa wan mahaifin asmau shi aka ba sadaki amatsayin sa na uban ta, daga nan daddy ya shiga rabon kuɗi



   Mutanen gari sai turuwa suke suna ƙara ƙaruwa kamar sallah ana cewa ai asamau ta je binni ta haɗu da me kuɗi




    Baffan ya so su kwana amma sai suka kawo masa uzurin zasu koma ne kasancewar kashegari ake sa ran tasowar ango sabit 😂




      Amma sai da suka ƙarasa gidan baffan suka ga gidan sannan suka kama hanyar kano inda suka sauke daddy a kano sannan suka kama hanyar abuja



  Mummy kamar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha ganin ta mallaki asmau yanzu asmau ta zama mallakin ta, kuma babu abinda zai raba ta da ita



```ni kuwa mmn walid nace anya kuwa sabit zai yadda ya zauna da baƙar mace amatsayin matar sa mutumin da baya son baƙi```



 ******************




    Cikin hukuncin Allah sabit da badia suka dawo gida lfy sai da mummy ta kwaɓi dukkan ƴaƴan ta akan kar wanda ya faɗa masa maganar auren



  Don haka ko daya sauka sam be sani ba hidimar sa kawai ya ci gaba tare da kwasar girkin wacce a yanzu take a matsayin matar sa



  Itama mummyn ko da suka dawo bata ce asmaun ta bar inda take ba tunda auren ai kamar suna ne, don kawai asmaun ta zauna a nan wajen su



  Sai da suka huta suka nutsu sannan mummy ta kira shi da matar sa badia da kuma asmau dukkan su ta tara su a falo



 Sabit da badia da mummy suna zaune a kan kujera inda asmau take zaune a ƙasan carpet fuskan nan tata sam ba annuri don kuwa tasan kiran menene



  Sai bayan da kowa ya nutsa sannan mummy tace

"sabit bayan ka tafi matsala ta taso ta yadda dole ne a aurar da asmau don haka sai nai mata aure"


  Kallon mummy yayi

"yo mummy ina ruwana da auren ta ai aiki aka ɗauke ta kuma ake biyan ta idan zata iya aikin da auren to idan kuma baza ta iya ba ta ƙara gaba ai ba ita kaɗai ce ta iya girki ba sai mu nemi wata"


  "ai kai ne mijin" tsab sabit yaji abinda mummy tace amma sai yake jin kamar kunne sa ne yake masa kuwwa



 "mummy me kinace" bata maimaita ba face idƙ da ta zuba masa


"kamar naji kince nine mijin wannan abun koo" ya faɗa yana nuna asmau


"ashe kaji kuma wallahi da wasa ka sake ka furta mata kalmar saki wallahi sai nayi mugun ɓata maka wallahi sai kaga ɓacin raina tunda auren ka da asmau babu wanda zai taimaka sai kai


  Tunda de duk ƴan uwanka kowannen su yana da mace biyu kuma acikin biyun akwai wacce ta iya girki amma kai kana zaune da ɗaya ɗayar ma wacce bata san darajar aure ba balle wani miji"



   Faɗa mummy ta dinga yi ta inda take shiga ba tanan take fita ba tsab ta san halin sabit in tak masa lako lako sai ya watsa mata ƙasa a ido gwanda tai masa ta ruwan zafi in yaso duk a dafe a tare




   Sabit shiru kawai yayi yana saureran mummy wannan shine wai a dake ka a hana ka kuka, ita kuwa badia tana zaune a gefe ta cika tayi fam kamar zata fashe wannan shine ga mari ga tsinka jaka



  Ga kishiya ga kuma kushen ta da mummy take yi wai bata iya girki ba


"amma mummy duk a gidan nan a rasa wanda za a haɗa da wannan halittar sai ni" ya faɗa ran shi a ɓace kalmar nan ta daki asmau sosai wai halitta



  Ɗagowa tayi ta maka masa harara sai kace ita cewa tayi tana son sa ai ko maza sun ƙare a duniya ya rage daga ita sai sabit baza ta so shi don ta fahimci ɗan renin hankali ne



 "mummy kin san tsari na na mace ɗaya sannan kinsan ni ba me son mu'amala ne da baƙin abu ba balle wai ace matata ce baƙa" ya faɗi kalmar ```matata``` kamar wanda yake da kashi a baki



  "gaskiya mummy da sake ya za ayi in shigo in kalli wannan baƙin abun a ɓangare na ai wannan ma sai ta saka ni in ta firgita cikin dare, in matsala bata sa zuciya ta bugawa ba wannan halittar zai sakani" ya faɗa yana ƙara nuna asmau cikin tsana





 Asmau iya ƙulewa ta ƙule ƙarshe ita tunda take ba a taɓa ci mata mutunci ba kamar yadda sabit yai mata *shin wai baƙi muni ne* ta tambayi kanta



   shiyasa fa ita tunda taji da wannan ɗan rainin hankalin za a haɗa ta dashi shi taji sam bata san abun amma kasanceqar bata da mafita yasa ta yadda da lamarin



  Sabit ya cigaba da kushe asmau kamar ba gobe inda mummy ta tsaya ta barshi ya gama faɗin abinda yake son faɗa sai daya zage ta tas sannan yai shiru yana huci



 "to in banda abin auta ai na faɗa maka dalilin auren ko ba haka ba, kuma ba wani da zai haɗa ka da asmau tana can boys quaters tana aikin ta kai kuma kana ɓangaren ta me zai haɗa ka da ita, da matar ka ta iya girki shi kenan sai in raba auren itama taje ta auri wani"



  Jin cewar akwai lkcn da auren zai yi expire ne kuma ga yadda tsarin auren yake na asmaun baza ta dinga zuwa ɓangaren sabit ɗin ba ya sa shi kwantar da hankalin sa



    Ya kakkafa asmaun doka na in ta ganshi ta canza hanya don baya son yana cin karo da mummunar fuskar ta sannan kar ya sake ya ga ƙafarta a ɓangaren sa duk aka gama maganar kowa ga san matsayin sa sannan mummy ta sallami kowa



 Sam badia ba haka ta so ba taso ace sabit ya bijirewa mummy amma sai taga saɓanin hakan



  Ko da suka koma ɓangaren su sai faɗa, wai dama ƙila ya so auren ne shi yasa ana faɗa masa ya hau borin ƙarya in da da gaskene ai da sai ya saki asmau



  Yai mata bayani yai mata rantsuwa amma ina sam ta ki yarda kawai sai ya share ta yayi wucewar sa ɗakin sa shima yaje yaji da abinda ya dame shi
[4/17, 4:50 PM] 🥦: 👩🏽‍🍳 *menu of d day*👩🏽‍🍳


   *brown rice served with liver and egg sauce, Apple milkshake*


  *brown rice*

*ingredients*
-shinkafa
-man gyaɗa
-maggi
-curry
-green beans
-carrot
-peas
-attaruhu
-albasa
-tafarnuwa

  *method*

1) ki wanke shinkafar ki tas sai ki shanya ta don ta bushe, idan ta bushe sai ki ɗauko tukunya ki zuba mai sosai sai ki saka tafarnuwa da albasa amma kaɗan

2) idan suka ɗan ɗauko soyuwa sai ki zuba shinkafar ki ki ci gaba da soyawa, kina yi kina juyawa har sai tayi brown sosai sai ki sauke ki tsane man

3) ki yanka attaruhu da albasa yankan cubes, sai ki zuba a tukunya da ɗan mai, sai ki cigaba da soyawa, idan sun dauko soyuwa sai ki zuba ruwan da zai dafa miki shinkafar ki



 4) ki zuba maggi, curry thyme da duk wani seasoning da kike so, idan ya tafasa sai ki zuba shinkafar ki tafasa ɗaya sai ki zuba carrot, peas, green beans ki rage wuta, idan ya dahu sai a sauke


*liver and egg sauce*

*ingredients*

-tomatoes
-attaruhu
-albasa
-hanta
-kwai
-curry
-thyme



  *method*

1) ki wanke sai yanka hanta ƙanana sannan ki tafasa ta da maggi, thyme, tafarnuwa, albasa


2) idan ta dahu sai ki sauke, ki jajjaga attaruhu, tomatoes albasa da tafarnuwa


3) ki zuba mai a kasko sai ki ɗan saka masa albasa ko tafarnuwa don yayi zafi, idan yai zafi sai ki juye jajjagen nan a ci gaba da suya, a zuba maggi a cigaba


4) minti ɗaya biyu sai ki zuba hanta a ci gaba da miya, idan miyar ta ɗauko soyuwa sai ki matsar da miyar gefe ki zuba kaɗaɗɗan kwai a gefen da ba komai ki barshi sai ya ɗauko soyuwa sai ki fara dagar gaza shi

5) idan ƙwan ya soyu sai ki haɗe shi da miya ki ɗan ƙara bata tsoro sai ki sauke sai a ci da brown rice


   *Apple milk shake*

  *ingredients*
1)apple
2)dabino
3)cardamon powder
4)sugar

*method*

1) ki yanka apple ɗinki ƙanana, ki cire ƙwallon dabinon ki, idan dabinon bushash she ne ki jiƙa shi

2) ki haɗa apple, dabino, cardamon powder amma kaɗan, madara da sugar sai ki markaɗa


3) ki saka ƙanƙara a jug ko cup ɗin da za ayi serving ki juye milk shake ɗin ki


👩🏽‍🍳 *Bon appetit*👩🏽‍🍳


*ASMA'UN SABIT*
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)



   P⃗a⃗g⃗e⃗  9🌹







 Har garin Allah ya waye sabit da badia basu daina fushi da junan su ba, haka kowa ya shirya ya kama hanyar office cike da jin haushin ɗan uwan sa



    Sai da suka dawo badia taga sam sabit bashi da niyyar lallashin ta kamar yadda yake mata ada idan sun yi faɗa yasa ta zuwa ta tsara wanka da kwalliya irin wacce sabit ɗin yake so


  Sai da akai sallah magariba ya dawo daga masallaci ya zauna a falo yana kallon news sannan ta fito tana karairaya


  Ɗago ido yayi yakalle ta sai ya kasa ɗauke kanta, badia ta gama karantar sa tsab wani, dai da taje har kusa da shi sannan ya ruƙo hannun ta ya zaunar da ita akan cinyar sa


 "ya dai my only wannan wankan yayi da me zan biya ne" ya tambayeta yana kashe mata ido


  Fari tayi da idon ta wanda ya sha lashes na kanti

"haba *SD* sai kace baka san matsalar da muke ciki yanzu bane na auren ka da wannan yarinyar" ta faɗa fuskar ta kamar me shirin kuka



  Sabit jinta kawai yake yi amma gabaɗaya ta gama da shi

"yanzu don Allah *SD* na dace zama da kishiya kalle ni fa"


  Ta faɗa tana miƙewa tare da jujjuya jikin ta gaban sa ta yadda zata ƙara rikiɗa shi,

 "only wannan salon naki yana ƙara rikita ni, zo nan in ji ɗimin jikin ki da nai missing jiya" ya faɗa yana kai hannun sa don ya jawo ta, sulalewa tayi ta ƙara nesa da shi inda shi kuma ya koma kan kujerar ya zauna yana kallon ikon Allah

 " *SD* kalle ni fa so kake friends ɗina da ƴan uwana suyi min dariya kayi min kishiya ni me kurin baza ka ƙara aure ba" ta faɗa tana jujjuga jikin ta ya yadda zai ƙara ƙare mata kallon, sabit dai yana zaune kamar mutum mutumi sai kallon ikon Allah


 "only ki zo nan muyi maganar mana zan fi ganewa" ya faɗa yana me niyyar kamo hannun ta wanda ta miƙa masa sannan ta taho da cat walking sai girgiza take yi inda gaba ɗaya duk wani lissafin sabit ya gama kwance wa



  Sunkutar ta tayi sai bedroom ɗin su,


  Tana kwance akan gadon su inda ta rufe jikin ta da bed cover, a haka sabit ya fito daga toilet ya same ta,

"only dia na ɗauka zakiyi joining ɗina a toilet ne" ya faɗa yana goge kansa, ɗan ƙaramin tsaki taja sannan tace

 " *SD* naga alamar kamar wannan auren da akai maka da sanin ka kana so shiyasa sam baka son mu samu mafita"


  Ajiye towel ɗin yayi ya ƙaraso inda take zaunawa yayi a kusa da ita inda ya riƙe mata hannun ta sannan yace mata

"haba only ya zaki dinga abu kamar baki sanni ba, dia kin sam taste ɗina kin san koman da nake kin san yarinyar nan gabaɗayan ta ba taste ɗina bace


 Mace me kamada namiji namijin ma kamar ɗan prison, me zanyi da ita sam bata da girly personality, kuma kin san nafi son mace me koman ta na mata ne, amma wannan kamar wani namiji fa haka nake ganin ta"



  Badia taji daɗin yadda ya kushe asmau sai ta ƙara narkewa sannan tace

" yanzu *SD* yaushe zaka sake ta"

 "dia kin dau ji abinda mummy tace sai kin iya girki don haka sai ki dage ki koya"

  A firgice ta ƙwace hannun ta daga cikin nasa wanda hakan ya barshi da sakin baki

" *SD* kana nufin kana goyon bayan in koyi girki kenan, kuma kasan ni am not a kitchen person" riƙe ta ya ƙara yi


 "na sani only dia amma kinga abinda mummy tace idan kin koyk girki mun huta nima sai ki koya min in yaso sai mu dinga sharing duty yau in kikai girki gobe sai inyi kinga mun huta da cin abincin da bamusan tsabtar wanda yayi ba ko"



    Ya dinga kamale ta yana rarrashin ta har ta yadda zata fara koyon girki, suka gama haɗa plan cewar a waje zata je koyon girki ta yadda sai dak kawai mummy taga ta iya girki haba ai da ta ƙware da wannan ƴar iskar yarinyar tayi waje va sakinta kawai sabit zaiyi ba sai ta saka shi ya kore ta ma



 *******************


   Hjy badia ta je ta sai form a wani cooking class zata ta fara koyon girki, ranar da ta fara zuwa ta ga yadda ake abinci kamar tayi amai



  Babu abinda yake tayar mata da hankali kamar nama ɗanye, tunda ta bar cooking tace bazata ƙara komawa ba saboda basu da tsabta



  Sabit sam be damu ba don haka sai ya kuma samo mata wani cooking class ɗin shima duk sammakar ce wai basa wanke nama ya fita tas suke ɗaura wa



   Cikin wata ɗaya sun zageye kusan dukkan cooking class  ɗin da suka sani amma duk cikin su babu wanda ya iya girkin irin wanda badia take son yi babu yadda ta iya haka ta haƙura da koyon girkin



  Sabit ne ma ya dinga matsa mata akan ta kuma dubawa, ko da faɗa masa matsalar ta na ƙyanƙyamin naman da basa wankewa sai yace mata


 "me zai hana ki nemi wannan yarinyar ta koya miki kinga ita ta ƙware kuma daga gani tana kula da tsabtar abincin ta"



  Sam badia bata yadda da wannan shawarar ba ai bada kaine ma yarinyar da aka aura mata mijinta itace zata ce ta koya mata girki ai ta faɗi ƙasa ba nauyi



  Ƙiri ƙiri tace bata yadda ba inda daga karshe har ta kai su da faɗa wai sabit yanzu ya fara son asmau, shi kuma ya dinga rantse mata ba abinda yake haɗa shi da ita, faɗa sukai da gaske




 Ganin sabit bashi da niyyar sakkowa ne ya sa badia shiryawa domin zuwa wajen asmau koyon giki ```tirƙashi koyon girki wajen kishiya amma an faɗi ba nauyi```



    Asmai tana zaune ta gama lunch kenan duk an rarraba kowane ɓangare tana shirin hutawa kenan sai taji wata yarinya asabe da ke aiki a kitchen ɗin gidan ta shigo


 "anty asamau wai inji wannan farar matar me iyayi tace kije" tsayawa nayi ina tunanin wace farar mata ce ko dai mummy ai asabe ta san mummy


  Tashi nayi na ɗauko hijabi na na fito, ina fitowa naci karo da badia sai wani yatsine fuskar tar take yi kamar wacce taga kashi


 "ke da a wannan ƙazamin wurin kike mana girki kina aiko mana da shi, meye amfanin ɗauko ki aiki ko ba biyanki ake yi ba, don me yasa baza ki dinga sakawa ana gyara wajen ba" ta faɗa



  Ƙarewa wajen kallo nayi babu abinda ya same shi yanzu yanzu nan suka gama share wa amma ƴar rainin hankalin nan zata wani ce wai datti


  Samun gefe tayi ta kyafe sannan tace

"ki dauko tsintsinya ki ƙara share wajen don nazo ne zanyi wa sabit girki bazan iya ciyar da mijina abincin da aka dafa a wannan ƙazamin wurin ba"



   Ban ce mata komai ba kawai nai shigewata ciki nai kwanciya ta har yanzu bata san wace asmau ba bata san ko wannan koɗaɗɗan mijin natan bai isa ya sani ba balle ita



    Ganin na daɗe ban fito ba ya sata shigowa ɗakin ganina a kwance ya sata fara masifa


 "lallak ma yarinyar nan kinci kin ƙoshi shiyasa har na saki aiki amma kika ƙi yi"

  Iskar data kwaso ta ma ban shaƙa ba balle ita, masifa ta dinga yi tana gaya min magana wai ƴar ƙauye ta zo birni, ganin bazan iya shiru ba yasa nace mata


 "to wai in girki zakiyi na ɗauka part ɗin ki ma akwai kitchen meyasa ba zakiyi a can ba" na faɗa kaina tsaye


  Masifar dai ta ci gaba da yi kamar ba gobe sai da ta gama sannan ta ɗauko wayar ta ta fara dailing



  Ana ɗauka na ga tafara magana

" *SD* ai ma faɗa maka yarinyar nan ƴar rainin hankali ce kagan ni a kitchen ɗin amma tana kwance sam ban san me take nufi ba"  ban san me yace mata ba sai kawak ganinai ta miƙo min wayar


  Daga ita har wayar na doka wa wata harara sannan na kuma mai da kaina na gyara kwanciyata ta,


 Wani zagi na ji ta ɗura wanda sai da na toshe kunne na saboda tsabar girman sa

" ikon Allah *SD* wallahi ta ƙi karɓa," ban san me ya faɗa mata ba sao dai naji ta kashe,



 Intercom ɗin da ke kitchen ɗin aka kira ban da niyyar tashi sai dana ga dama har ta kusan tsinkewa sannan naje na ɗauka, ashe mummy ya kira shima mummy's boy 😁


     Ana take gaya min wai in koya wa badia girki ban musa mata ba kawai dai na dawo nace wa gwanar ta zo muje kitchen ɗin


   Dagewa tayi wai bazai tai girkin ba har sai na saka yara sun ƙara gyara kitchen hmmm lallai baki san wace asmau ba na faɗa, neman wuri nayi na kuma kwanciyata



 sabit ta kuma kira ta kuma faɗa masa ai na kuma kwantawa shi kuma ya kuma ƙara kiran mummy ko da mummy ta kira tsab nai mata bayanin abin da ke faruwa bata ce ko mai ba kawai ta kashe wayar



   Allah ne kaɗai yasan me tace aa sabit ɗin sai gashi ya kira ta wai muyi girkin a haka wannan abun ya bala'in ɓatawa badia rai



 shigewa tayi kitchen ɗin inda na bita a baya don fara girkin fatana dai Allah yasa har mu
 gama bamu ƙona kitchen ɗin ba don na fahimci ƴar rainin wayo ce to nima duk all d same ne ai




 *Parpesun naman kaza zatai masa da jollof rice sai cole slow da kima fruit salad*  ```recipe yana ƙarshen page ɗin in shaa Allah```


   Ita me koyon girkin tana zaune akan wani stool na kitchen ɗin nice nake komai, naman kazar nan an wanke shi ya fi so goma


  Ni dama tunda na wanke tace be mata ba sai na dangwarar mata da shi,

"kiyi irin wanke war da kike so idan kin gama na ɗaura" na faɗa mata na cigaba da haɗa ragowar abincin


 Asabe ta kira ta sata ta wanke hannun ta yafi a ƙirga sannan ta saka ta wanke naman


  Idan ta wanke sai ta kawo mata da ta kalle shi sai tace

"je ki ƙara wanke wa har yanzu be dena ƙarni ba" lallai manya na girki nace a raina


 Girkina kawai nake tayi amma ita uwar iyayin tana can a kan kaza har na gama jollof ɗina da taji kayan lambu ba a gama wanke kaza ba 🤔


    Komawa gefe nayi ina kallon ikon Allah duka an gama wanke zaƙin kazar ma ko wane zaki zatayi oho, sai da ta gaji don kan ta sannan tace a bani in tafasa ta, duk wannan fa acikin koyon girki ne lallai mata nada aiki a gaban su


  Tafasa ɗaya kazar tayi duk na gama haɗa mata kayan ƙamshi sai tashi suke yi amma baiwar Allah nan abinda zai fito daga bakin ta shine


 " ki kashe gas ɗinnan ki sauke kazar na ki ƙara wanke ta sai ki mayar da ita don wannan ƙarnin natan in ba an kuma wanke ta ba bazai rabu da ita ba"


 Matsawa nayi na bata wuri sannan nace mata

"zo ki sauke ni bana taɓa abu idan yana tafasa aljanuna basa so" tsorata tayi sai kuma tai gum da bakin ta


 Sai can ta kira asabe wai asabe ta sauke, ganin yarinyar zata cutu ya sani na sauke da kaina a guje ta fice daga kitchen ɗin wai kar aljanuna su tashi da ita



  Tukunya kawai na canza na ƙara kayan haɗin na ƙarasa kazar sai da aka gama tas sannan ta shigo ta saka yaran wajen binta da abincin part ɗin ta ina jinta tana kiran mijin wai ta gama amma fa ta wahala ashe girki da wuya


  Ban san me yace mata ba naji dai tana dariya sannan tai masa fatan dawowa lfy sukai sallama ni dai asmau nace to ayi dai mu gani in man kitso zai soya ƙosai











 👩🏽‍🍳 *menu of d day*👩🏽‍🍳


   *chicken pepper soup, jollof rice served with cole slaw,  fruit salad*





 *chicken pepper soup*


*ingredients*
-chicken
-attaruhu
-albasa
-thyme
-curry leaves
-lawashin albasa
-green pepper
-maggi
-tafarnuwa
-egg


  *method*
1) a wanke kaza sai a saka ta a tukunya a saka curry leaves, thyme, maggi albasa da tafarnuwa sai a rufe a barshi ya ta tafasa, a sakar mata ruwa


 2) ki jajjaga attaruhu da da albasa, idan kazar ta ɗauko dahuwa sai ki zuba attaruhu ki ɗan ƙara maggi sai ki rage wuta ki rufe


 3) ki yanka lawashin ki da koren tattasai sai ki kaɗa kwai ki ajiye


4) idan kazar ki ta dahu sai ki buɗe ki zuba ruwan ƙwan amma ki taɓɓatar da ruwan yana tasafa, kar ki juya


5) idan kwan ya dahu sai ki zuba lawashin da kika yanka ƙanana da koren tattasai ki rage wutar gabaɗaya ki rufe, idan ya dahu ki sauke ya kasance yana da ruwa ruwa



   *JOLLOF RICE SERVED WITH COLE SLAW*


*ingredients*


-rice
-tomatoes
-attaruhu
-albasa
-tin tomatoes
-stock fish
-nama
-maggi
-curry



  *method*

1) ki gyara stock fish a cire duk dattin da kashin sannan a jiƙa shi a ruwan zafi


2) ki tasafa shinkafar idan ta tafasa (per boil) sai ki sauke ki wanke ta

3) ki wanke naman da stock fish ɗin ki sai ki zuba a tukunya ki zuba maggi tafarnuwa da albasa ki rufe



4) idan ya tafasa sai ki markada, sai ki sauke ki juye, ki zuba mai a tukunya da albasa da ƴar tafarnuwa don ya ɗan soyu,


5) ki markaɗa tomatoes da attaruhu da albasa sai ki zuba akan man nan, idan ya tafasa sai ki juye naman nan da stock fish ki barshi ya tafasa



3) idan sun tafasa sai ki ɗan ƙara ruwa kaɗan ki zuba tin tomatoes, curry ki ƙara maggi in be ji ba sai ki zuba shinkafar


4) idan shinkafar ta ɗauko tsotsewa sai ki yayyaɗa mata yankakken green pepper da kuma lawashin albasa sai ki rage wuta ki rufe ya dahu sai ki sauke




 *coleslaw*

*ingredients*


 -cabbage
-carrot
-peas
-green beans
-kidney beans
-egg
-mayonnaise



 1) ki haɗa kayan veges ki wanke ki gyara duk ki yanka na yanka wa ki haɗe su waje ɗaya, ki yanka da daffaffan ki ki haɗa ki zuba mayo ki juya ki serving

*PS* ki tabbatar da veges ɗin sun tsane in so samu ne ma su bushe  kafin a zuba mayo ɗin


  *fruit salad*

Ingredients


 -kankana
-gwanda
-abarba
-ayaba
-sugar syrup ( ki tafasa ruwa da sugar idan sugan ya narke sai ki sauke ya huce)
-foster clark (pine apple and ginger flavour)


 *method*



1) ki gyara fruit ɗinki ki yanka su ƙanana amma banda ayaba

2) idan kin yanka su sai ki zuba sugar syrup ɗin ki, sannan ki zuba foster clark a cup ki ɗan zuba masa ruwa sai ki juye a salad ɗin ki zuba flavour indan kina so ki saka a fridge

 Idan an tashi serving sai a yanka ayaba akai a ci


  👩🏽‍🍳 *BON APPETIT*👩🏽‍🍳


   *ASMA'UN SABIT*
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)


*ina jidda mmn surayya nayi breaking record ɗinki ko 💃🏼💃🏼💃🏼 to ga page nan naki ne u alone, zan ce miki naji daɗin ciran tutar nan taki 🏳 zan maƙala shi a goshina har in gama littafin nan jzk ga page nan naki ne dedicated to u sannan recipe ɗin ƙarshe da fatan za a birge bbn surayya da shi na gode*



   *Hishma ya karatu nace kije school kiyo yo karatu kizo mu raba ilimin 🤣 don inji daɗin rattabo wani sabon littafin bayan wannan*


   P⃗a⃗g⃗e⃗  10🌹






 Ko da sabit ya dawo da daddare yayi wanka ya shirya badia ta gabatar masa da abinci ci yayi har da santin sa


  Girkin badia kamar girkin yarinyar can, inji

"gaskiya only ban taɓa sanin cewar u r gifted ba sai yanzu, girkin ki na farko kamar wacce ta ƙware, kina nufin da kanki ki kai wannan girkin"


  Rausayar da kanta tayi tare da yin fari da wannan fake lashes ɗin da ta saka sannan tace

" haba *SD* ya za aiyi ince maka ni na yi amma ka tsaya ka na tambaya ko kana ganin kamar bazan iya bane"


   Shiru yayi kawai ya kai lomar rice yana ƙara gyaɗa kansa, matsalar girkin ɗaya taste ɗin abincin yarinyar yake yi, ya riga ya saba da cin girkin asmau don haka duk lkcn  da ya ci abinci in ba nata bane ya sani sannan baya wani ƙoshi



 Amma wannan kamar ita tayi, ko dan ita ta kowa only ɗin nasan shiya sa girkin na only ɗin yake tasting kamar nata


  Kai amma in only ɗin shi ta iya irin wannan girkin me daɗi taste ai ya gama more wa ```ni kuwa mmn walid nace ko ina ra'ayin shi na rashin damuwa da macen da bata girki ba oho```



   Tas ya cinye abin sa yana ta santi, ita da yake mara kishin kai ce sai ta dinga yi masa dariya a ɓoye


  Haka badia ta cigaba da zuwa wajen asmau koyan girki amma tun lkcn da ta je sau ɗaya taga ana yi bata kuma zama a yi agaban ta ba, sai dai ta ɗauki waya tai ta chatting in an gama ta sa a ɗauko mata a kawo mata part ɗin ta



   Ana haka badia ta kuma samun ciki, wannan cikin da tsirfa ya zo ga kwaɗayi, don haka sai aiki ya kuma ƙarar wa asmau



  Wani sabon salo ma da suka ɗauko shine wai asmaun ta dinga zuwa part ɗin sabit ɗin tana aiki don yanzu badia baza ta iya ba



  Mummy ce da bada wannan umarnin, ƙiri ƙiri asmaun tace gaskiya bazata iya ba ita girki kawai zata yi amma sai mumy tace ko taje tafara aikin ko a sallame ta gaba ɗaya



  Ganin cewar bata da tsuntsu bata da tarko ya sa ta haƙura amma da ta tara kuɗin da tasan zasu ishe ta yin rayuwar ta zata bar gidan




   Ranar da ta fara zuwa part ɗin taga abu, im banda ƙarnk babu abinda falon yake yi, haka ta tsiri gƴara sai yamma ta gama, ɗakin su falo kitchen, toilets ɗin ma kamar an shekara ba a wanke ba saboda tsabar dauɗa



   Kallon gaye take wa sabit ɗin amma tunda ta zo ta ga irin wurin da yake sai ta rena masa ashe ma ƙazami ne ta faɗa a ransa



    Sabit sai yamma ya dawo yadda ya ga part ɗin nasa ya canza ya sa yaji daɗi a ransa, kitchen ɗin ya kira ya buƙaci asmau ta zo, ƙin zuwa tayi sai da ya kira mummy ta kira ta sannan ta tashi ta shirya ta je tana shiga falon ya hauta da faɗa


 "ke wai don ubanki ba biyanki nake yi ba da zan ce ki zo kiƙi zuwa har sai na kira mummy sannan zaki zo" fuskar nan tata da kullum take a cunkushe ita ta ƙara cusheta kamar wacce bata taɓa fara'a ba wannan abun shine yake ƙara ingiza sabit yake kuma ƙara tsanar ta wai ace mace sam a lamarin ta ba fara'a




  sai da ya gama zage ta tas sannan ya saka aiki wai ta haɗa masa dinner, cikin kitchen ɗin ta shiga ta haɗa masa taliya me ruwa sosai ta kawo masa



    yana buɗewa yana gani. abinda ta dafa ya antaya mata shi a jikin ta, wani irin ihu ta saki inda ta fara sosa hannun ta da ƙafar ta daya ƙone




  "don ubanki ance miki ina cin taliya ne kin taɓa ganina na ci taliya, tashi kije ki kuma dafo min wani abun useless kawai"




   duk dakiya irin na asmau sai da ta tsorata da lamarin sabit, ta ɗauke kayan jiki na ɓari tayi hanyar kitchen,



   tana shiga ta rushe da kuka, ita sam bata ma san me zata dafa masa ba, ga hannun data ƙone da shi sai raɗaɗi yake mata




 Jin takun shi tayi wanda hakan ya firgitar tar da ita ta ɗauki tukunya tare da zuba ruwa tana shirin ɗorawa a kan gas,

"me zaki dafa min" ya faɗa da husky voice ɗin nan nasa


"doya da miya" ta faɗa a firgice, wani ɗan iskan kallo ya watso mata,

"kinga alamar ina cin doya ne, wai me yasa ke daƙiƙiyace, tun ɗazu nake jin yunwa amma ki bani abinci abun ya gagara sai kace ba biyan ki nake yi, shike nan dafa min doyar amma bana son miya ki kawo min ita haka gaya"



  Abin yai mutuƙar bata mamaki amma kuma sai ta dafa masa


  Tana gamawa ta juye a plate ta fita, yana zaune yana shan furar sa, ta ajiye masa

 "je ki ɗauko min abin kwashe sharar can, (parker)" bata kawo komai ba ta tafi ta ɗauko masa


   Tai mamakin da taga ya juye doyar akai, sannan ya miƙe ya zare belt ɗin jikin sa, guda ɗaya ya sakar mata tai wani tsalle ta dire sannan yace mata

"oya maza ɗauki doyar nan ki cinye ta a haka in ba haka ba wallahi yau sai dai gawar ki" ya faɗa yana gyara belt ɗin hannun sa



   Kallon doyar tayi wacce take a cikin parker idon ta na hawaye ta ɗauka ta dinga cusawa ba miya ba ruwa haka ta dinga cusa doyar tana rawar jiki


   Gashi a ƙoshe nake, gani ba masoyiyar doya ba, ga doya ba miya haka azzalimin nan ya dinga saka ni ina ƙasimar ta ina haɗiya da kyar ga belt a hannunsa



   Amai ne naji yana taho min inda na fara yunƙurin yinsa, saukar belt kawai naji a bayana wanda ya kuma saka ni tsalle tare da haɗiye wata ƙatuwar doya wacce ban tauna ba

"idan kika sake kika min amai sai na karya ki, daga yanzu idan na kuma buƙatar abinci daga gare ki kika kuma kawo min abinda bana ci zaki ga abinda zan miki, da wata fuakar ki kamar ta aljanu baƙa ƙirin" ya faɗa



  Sai dana cinye doyar nan tas sannan ya saka ni dafa masa tuwon shinkafa miyar kuɓewa ɗanya


 Ba ni na gama girkin ba sai ƙarfe 02 :54am na tsakar dare duk na gaji har wani dishi dishi naƙe gani saboda tsabar baccin da nake ji



  Ina fitowa baya falon kuma ƙofar falon a kulle take da mukulli, na rasa yadda zanyi, ɗan zama nayi a ƙasan tiles ɗin falon don injira fitowar sa har bacci ya kwashe ni be fito



    Ruwan sanyi kawai naji ana zuba min ina cikin bacci na a zaune wanda ya farkar dani




 Bayan ruwan zafin nan sai naji an take min hannu na dana ƙone wani zafi daya ziyarce har sai dana kusa yin pitsari



   Kukan azaba na saki tare da riƙe masa ƙafar daya take min hannun nawa ina roƙon ya ɗaga min hannu na


"waya baki damar yin bacci ko an gaya miki bayi nayi bacci ne ba tare da izinin iyayan gijin su ba" ya faɗa yana ƙara take mata hannun nata



 Kuka na saki sosai tare da yiwa wannan mutumin Allah ya isa, sai da ya gaji don kansa sannan ya ɗaga min hannun wanda naji kamar an min gafara


 "kuma ki haɗa min breakfast" ya faɗa yana wucewa, kuka na saki kamar ba gobe, na miƙe na wuce can inda nake da zama BQ kenan



 Sallah na farayi sannan na fara haɗa breakfast yanzu tsoron sabit nake ji ban taɓa tunanin akwai mutum daya iya zalinci ba kamar sabit



  Sai da na haɗa breakfast aka rabo kowanne part sannan na samu nutsuwar duba ciwo na, ya kunbura, ga raɗaɗi da azaba da yane min



  Hawaye ne kawai naji suna zuba daga idona masu zafi, wai sai yaushe zan samu ƴan cin kai ne, yaushe ne nima zan san jin daɗin a duniyar nan



    Magani ma samu na saka a hannu na inda na ƙone da ƙafata, sannan na samu na kwanta, ban daɗe da bacci ba naji call ɗin intercom ɗin kitchen


   Kasancewar bani kaɗai bace yasa na share kawai, ganin sai ringing take tayi ba a ɗauka ba ya sani miƙewa na je na ɗauko, sabit ne jin muryar shi sai daya sa zuciyata bugawa


 "ina asmau" ya tambaya da muryar nan tasa me rikita min ƴaƴan hanji

"nice" na faɗa jiki na a sanyaye

"na fahimci har yanzu baki yi hankali ba, iskancin da ke kanki har yanzu be ragu ba kizo part ɗina ina jiran ki yanzu kika ɓata min lkc zaki san sauran"


Katse wayar yayi kafin in masa complain ɗin hannun nawa, hannun nawa na kuma dubawa yadda yake shirin chaɓewa inban yi hankali ba



  Hijabi na kawai na ɗauka nayi part ɗin nasan ina takaicin wannan rayuwa, ina shiga yana ,zaune shida sahibar tasan suna kallo



  Da sallamata na shiga sallamar da ba wanda ya amsa min kamar ba musulmai ba

"shiga kitchen kiyi mana abinci" ya faɗa ba tare da ya kalli inda nake ba


 "hannuna ciwo yake, ƙonewa nayi in ban kula da shi ba sai ya fara ruwa"


  "Muga hannun" ya faɗa kamar gaske, nuna masa nayi sai ya miƙe ya shiga kitchen sai gashi da wata baƙar leda


 "nannaɗe hannun ki da wannan ledar sai kiyi mana girkin bana son cin ƙazantar ki" ya faɗa saboda tsabar mugunta



Hawaye ne ya fara zubar min na karɓi ledar zan fara ƙullawa a hannuna sai naji badia tace


" gaskiya *SD* bazan iya cin abincin da yarinyar nan tayi ba yama nake cin abincin ta balle kuma da wannan jagwalon a hannun ta" ta faɗa fuska a yatsune, sallamat sukai inda nai ta wa Allah godiya don ina da tabbacin idan na cigaba da girki akai akai ciwon zai iya kuma chaɓewa







 Ina fita daga nan part ɗin mummy na nufa na gaya duk abinda ya haɗa mu da shi, kallo na tayi sannan tace


 "to in banda abin asmau ai *AURE BAUTA* ne, duk abinda kika ga ya faru a cikin aure ki tabbatar yana daga cikin ƙaddarar ki sannan bauta kike yi kije kiyi ta haƙuri har Allah ya kaimu lkcn da badia zata gama koyon girkin ta sai a raba ku amma yanzu biyayya shine naki"


  Wani baƙin ciki ne ya zo ya maƙale min a ƙirjina wato *AUREN BAUTA* ke nan nake yi, na zama baiwa kenan, na yadda duk *AURE BAUTA* ne amma ba irin wannan bautar ba



  Ganin bani da wata mafita yasani tafiya ɗakina na kwanta ina me roƙon Allah ya saka min da gaggawa



   ******************


  Bikin isma'il ne ya taso inda zai yi aure a maiduguri ta uku ce, sai shirye shiryen tafiya suke yi harda mummy balle kuma ƴan uwan sa


  Buri na da fatana ace sabit ya bar gidan don yanzu wata baiwar ba tafi ni ƴanci indai aka ce sabit yana gidan, mugunta kala kala yake gwada min kamar wani mara imani


  Banda wahalar gyaran part ɗinsa da ya zame min tilas kullum don matar sa tana da ciki mtssss



   Ranar friday da yamma suka shirya domin zuwa maiduguri biki inda shi angon ya rigasu tafiya tin da safe, wannan uban rigimar ina kitchen yasa aka kira ni sai dana bushi iska sannan nazo



  Abinda ke haɗa mu da sabit kenan ya fi san daya kira ni in zo ni kuma gani da shegen taurin kai, kusan kullum da muguntar da zai gwadamin amma gobe bazan daddara ba


  Ina shiga sai da sha ruwan takalmin sa ya doddoke ni da takalmin sa ni kuma na bishi da Allah ya isa a zuciyata



   sannan ya sani gyaran kayansa sai kace wata matar sa ooops na manta ashe da aure tsakanin mu ko, sai da na gama haɗa masa kayan sa sannan ya sani fitar masa da akwatin


  Kinkimar akwatin nayi na fita ina ja da ƙyar, a ƙofar get ɗin gidan naci karo da daddy har ƙasa na durƙusa

 "daddy ina kwana" sai daya kalle ni ya gama ƙare min kallo sannan yace

"kar dai matar sabit ce wannan" ya faɗa yana nuna ni, mummy da ke gefe ta murmusa sannan tace

"itace asmau kenan ƴar baiwa" murmushi yayi yana gyaɗa kansa irin nasu na manya, a wannan lkcn sabit ya ƙaraso

"sabit kasa matar ka ta haɗa kayanta sai muyi tafiyar da ita tunda a hotel zamu sauka kaga itama taga gari" sam ban kawo da ni ake ba shima sabit ɗin sam be kawo ni ba ya ɗauka badia don haka sai yace


 "daddy ai bata jin daɗi kuma dr.  yace ta daina nisa da gida" kallona daddyn yayi sannan yace

"asmau me ya same ki" ɗagowa nayi na kuma kallon sa sannan na girgiza kai alamar ba komai, kallon sabit yayi sannan yace

"kace bata da lfy" sai a lkcn na gane wai dani da yake shima sabit ɗin sai a lkcn ya gane


"a a daddy ba sai naje ba anty badia bata da lfy ni nake kula da ita" na ƙarashe zancen


"zancen banza kenan kishiyar ki zaki kula da ita ko mijinki, maza kije ki haɗo kayanki muna jiran ki" 


 Kallon sabit nayi wanda ya haɗe ransa kamar an aiko masa da mala'ikan mutuwa sannan na duƙar da kaina mummy ce naji tace

"muje in taya ki haɗa kayan nakin" ƙafafu wana a sage na ja su sannan na bi bayan mummy a zuciyata bace dady ka ba sabit license ɗin cin ƙwal ubana






 👩🏽‍🍳 *menu of d day*👩🏽‍🍳


  *yam balls, potato pancake, fish cake*


  *yam balls*

*ingredients*
-yam (doya me gari tafi daɗi akan me danƙo)
-eggs (dafaffe da ɗanye)
-attaruhu
-danbun nama ko kifi
-albasa
-curry
-maggi
-garin bushash shen burodi


*method*

1) ki fere doyar ki sai ki ɗora ta a wuta ki bi ta da sugar da gishi, sugan ya ninka gishirin yawa

2) bayan doya ta dahu sai ki sauke ta ta huce, ki ɗauko wankekken turmin ki ki zuba albasa da attaruhu ki jajjaga sai ki kwashe a roba


3) ki zuba doyar itama ki daka ta ba kirɓawa ba ki farfasa tasai ki sauke ki haɗe da kayan attaruhun

4) ki zuba maggi da curry danbun ki sai yanka ƙwai ƙanana a ciki ki ƙara sai ki duddun ƙula kamar ball 😁 Kamar fuskar na

5) ki zuba mai a kasko ki dan saka albasa sannan ki barshi ya huce, ki fasa ƙwai a roba ki zuba maggi da albasa isashshe sannan ki kaɗa


6) ki dinga ɗaukar ƙwallon doyar kina sakawa a garin burodin kina tsomawa a ruwan ƙwai sannan ki soya har sai yayi brown sai a kwashe a barshi ya tsane



*potato pancake*

*ingredient*




-dankali
-albasa
-attaruhu
-maggi
- mai

*method*

1) ki fere dankalin turawan ki sannan ki gurza shi, itama albasar ki gurzata

2) ki jajjaga attaruhunki sannan sai ki haɗe da dankalin da albasa sai ki saka maggi, idan yayi ruwa dayawa sai ki ɗan ɗaure da flour, (ni dai nafi amfani da potato flour)


3) ki zuba mai a kasko idan yayi zafi sai ki zuba kullin dankalin ki ki soya idan ɓangare ɗaya yayi brown sai ki juga ɗayan idan ya soyu sai ki sauke


  *fish cake*

*ingredients*

-kifi (kowane iri ne)
-shrimps
-squid
-attaruhu
-albasa
-maggi
-mai
-flour da corn flour


*method*
1) ki gyara kifinki ki cire ƙaya in me ƙayar ne, ki gyara shrimps da squid sannan ki saka su a food precessor ɗin ki, ki haɗa da albasa, attaruhu, corn flour da flour sai ɗan mai kaɗan sai ki rufe ki kunna

2) idan baki da food processor, sai kiyi blending kifin da shrimps da squid, albasa attaruhu ɗin sai ki juye a roba sannan ki haɗa kayan flouɗ ɗin da maggi da ɗan mai


3) in babu blender sai ki tafasa su sannan ki daka su kafin ki haɗe da kayan flour ɗin

4) kaɗan zaki saka flouɗ ɗin yadda dai kwaɓin zai ɗinga danƙo a hannu bi ma'ana ya dinga kama hannu ba da tauri ba


6) bayan kin gama haɗa komai sai ki zuba mai a kasko sannan ki dinga ɗiba kina sakawa a cikin man kina  soyawa har ya soyu sai ki kwashe


👩🏽‍🍳 *BON APPETIT*👩🏽‍🍳


   *ASMA'UN SABIT*
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)




  *ina masu cikin mu 🤰🏻🤰🏻da mmn .....reeda da real me ........... Ban kama suna ba 🤣🤣🤣 duk ina muku fatan sauka lfy*



Page 11🌹



 Part ɗin mummy muka je itace ta bani ƴar ƙaramar jaka, sannan na wuce ɗakina, kayana na haɗa sannan na fito zuciya ta sai dukan uku uku take na san akwai rikici tsakanin mu da sabit



     Motar da mummy take ciki nan na shiga kusa da mummy na zauna na tsuke fuska don kar ace in fita in koma motar da sabit yake, ilai kuwa sai sulaiman wansa yace

"asmau ki fito ki zauna kusa da mijinki don daddy ne ze zauna" kau da fuska ta nayi kamar banji ba har daddyn y ƙarasa sai yace

"ke me kike yi anan ga mijinki can ya shiga waccen motar maza wuce kije wajen mijinki ni ma ki barni da matata" kunya ce ta kamani na tashi na fita daga motar na wuce motar da sabit yake zaune


   Shi kaɗai ne a bayan motar, rasa ina zan shiga yayi, gaban motar zan shiga ko bayan motar,

"bazaki shigo bane ko so kike a zauna ai ta jiranki gimbiya" sabit ya faɗa cike da takaici, kusa da shi na shiga na zauna inda ya matsa can ƙarshen sai kace wacce zan goga masa cuta



   Muka fara tafiya, har muka je airport ba wanda ya tanka wani, muna sauka na gudu wajen mummy ni wallahi yanzu sabit tsoro yake bani





 Private jet ɗin daddy zamu shiga don haka babu wani ɓata lkc ko duba passport, muka hau, ina shiga na fara dibi dibin gurin zama, muryar daddy naji yace

 "sabit kama hannun matar ka ka zaunar da ita kusa da kai naga kamar first flight ɗin ta ne"


  Jinayi cikina yai ƙululu ban ankara ba naji ta damƙi hannu na, tare da matse min shi yacca har ƴar ƙara na saki


  Sakin ƙarar ne ya shi take min ƙafa wanda zafin takalmin nan nashi kamar na ƙarfe ya shige ni kamar an ɗaura min dutse a kafar



   Toshe baki na nayi inda wasu hawayen azaba suka fara sauka daga cikin idona, jaa na yayi ya zaunar dani a kan kujera sannan ya fara kiciniyar saka set belt ɗin sa



    Har lkcn ban dawo daga duniyar zafin takanin da yayi ba don haka sam ban ma san ana saka wani belt ba


   Sai da mummy tace "sabit asmau kuwa ta saka set belt" sannan na lura da cewar ana sakawa


Yunƙurowa yayi jikina domin ɗauko set belt ɗin inda ya saka gwiwar hannun sa a kan cinya ta tare da danna na gwiwar sa


    Cinyar tawa kamar zata tsage don azaba haka naji wani irin kuka na saki wanda hakan ya janyo da hankalin duk wani wanda yakd cikin jirgin


   Daddy ne ya fara tambayar lfy, kafin in bude baki ba tuni sabit ya yi magana

 "daddy wai tsoron flying take ji" sakin baki nayi ina kallon babban mutum da ƙarya

 "karki damu asmau ga mijinki a kusa da ke ba abinda zai same ki, kai kuma ka lallashe ta" daddy ya faɗa cike da kulawa sannan ya juya


   Kukana na cigaba tare da yi masa Allah ya isa, mintsini na kuma ji ya mannara min cizo sosa wurin na kuma yi tare da ƙara furta kalmar Allah ya isa da ƙarfi Ƙwafa yayi sannan yace

"zaki gane kuren ki idan mun sauka zaki san baki wayo"


   A haka flight ɗin ya tashi, don tsoro gaskiya na tsorata amma sai na dake don bana son wannan ɗan rainin sence ɗin ya samu damar ta


   Lfy ƙalau muka sauka a maid.  daga nan motoci suka kuma zuwa ɗaukar mu wannan karan da sauri na shiga kusa da mummy sannan na kyafe, ko da daddy ya zo sai be ce infita ba sai kawai ya shige gaban motar har yana tsokana ta wai yaga nafi sabawa da mummy akan sabit, murmushi kawai nayi na jin kunya



   A wani hotel muka sauka inda bayan an kai mu ɗakunan da muka kama, nayi mamaki ko ince nai takaicin da aka ce wai ɗaki ɗaya zamu ɗauka da sabit 🙆🏼‍♀



   Ai nasan cewar na kaɗe daga ni har ganye na,  Muka shiga ɗakin yana ɗan girma sosai, muna shiga ya faɗa banɗaki, ni kuma na samu wuri na ajiye jaka ta sannan na ɗan rakuɓe na zauna, bai daɗe ba ya fito da towel a jikin sa daga gani wanka yayi



   "oya maza tashi ki shiga toilet ɗin nan ki zauna a ciki ko kina tunanin tare zamu zauna a nan ɗaki da ke, ai rayuwar banɗaki zakiyi"


  Sam ban fahimci abinda yake nufi ba sai dana ga ya hankaɗa ni cikin toilet ni da jakar tawa sannan na fahimci ashe a toilet yake nufin zan zauna yau naga ta kaina Kan toilet sit ɗin na koma na zauna na zuba uban tagumi ina kallon ikon Allah, rasa yadda zanyi nayi, ƙarewa toilet ɗin kallo nayi yana da ɗan girma ba laifi,


   Bath ne babba sai sink sai toilet sit, sai ɗan space haka


   Zama nayi na zuba tagumi da na gaji da zaman sai na ɗauro alwala, na fito duk dai jarabarsa ai baze ce in sallah a toilet ba ko  Yana  yana gaban laptop ɗin sa yana ta danne
 Ƙarasowa nayi ɗakin sannan na tsaya ina tunanin ina ne gabas, ɗago kai yayi yana kallo na inda ni kuma nayi kamar ban ma san yana yi ba

 "uban me ya fito da ke bana ce ki zauna a toilet ba" ya faɗa fuskar nan tasa a murtuke

"naga alamar kina son zama kusa da namiji Allah dai yasa ba kin saba bin su bane shiya duk inda nayi kina biye da ni, inda wata macen ce me kunya yadda ta ganni daga ni sai gajeren wando ai kunya zata ji amma ke ko a jikin ki"


   Kallon shi kawai nayi wani takaici ya rufe ni

"sallah zanyi ko itama sallah inyi ta a banɗaki ne" na faɗa kaina tsaye

"ni na isa ince kiyi sallah a toilet kije can kiyi amma kina idar wa ki koma toilet don bazan iya zaman ɗaki ɗaya da ke ba, naga ke kina son mood ɗin na ganin mu tare amma ni ko a ƙafa aka ɗaura min sai na yanke na gudu" ya faɗa yana maida kai tare da ci gaba da abinda yake yi



   Zuwa nayi inda ya shinfida sallaya na tada sallah, sai da na idar sannan na miƙe na koma toilet, yunwa ce kawai take cina ina zaune akan toilet sit ɗin sai naji an buɗe ƙofar


  Wata leda ya wullo min ɗaukar ledar nayi na buɗe, kaza ce a ciki da yoghurt, kasancewar toilet ɗin ba wani ƙazanta a ciki ga kuma yunwa ya sani buɗewa na fara ci



  Sai da naci na ƙoshi sannan nai brush zani na na ɗauko na shiga bath ɗin na shimfiɗa da niyyar kwanciya sai naji ya hankaɗo kofar



  Maza fice min da gani zanyi fitsari inyi alwala in kwanta, shiru nayi kamar bacci nake yi, shima sai ya ɗauka da gasken baccin nake yi don haka sai ya saki jiki ya fara fitsarin sa


  Sai da naji ya fara yi sannan na tashi zinbir zanyi waje, a guje ya nemi ƴar kaciyar tasa ya mayar wando be gama fitsarin ba ni kuma nai waje da gudu


   Sai daya gama sannan ya fito

"meye na fitowa da gudu bayan kin saba gani, nawa ne dai sai dai kiyi fata amma yafi ƙarfin ki"


  Ni dai ban kula shi na raɓe shi na shige naje na shiga cikin bath ɗin na kwanta, wayyo Allah kamar ina kwance akan ƙashi juyi nake amma bacci yaƙi zuwa



   Can na kasa bacci sai na tashi na fito daga toilet ɗin, ɗakin ya ɗau sanyi sannan an kashe fitilar lallaɓawa nayi naje kan gadon na kwanta sannan na rakuɓe ƙarshen gadon don kar in tada shi



  Ban daɗe da kwanciyi ba bacci ya kwashe ni,



   Kiran sallah naji sai na ƙara juyi tare da ƙara duƙunƙune wa saboda sanyin da ake yi, sannan na kuma komawa bacci na me daɗi na sakankance ina bacci kawai naji an haɗaka ni na faɗo ƙasa tim


  A guje na tashi inda shima ya biyo ni ze dake ni, toilet na faɗa na saka key na kulle, dukan ƙofar a ya shiga yi yana cewa in buɗe



  Kin buɗewa nayi, har ya gaji ya dena nasan duk wanda ɗakinsa yake kusa da namu yaji don yadda yake bugun, a zuciyata nace mugu ai na waye na daina barin ka kayi min mugunta



  Can aka fara kiran assalatu, nan ma yazo ya fara bugun in buɗe masa zai yi alwala a zuciyata nace sai dai karkayi sallah, sai daya gaji da bugun sannan ta tafi



   Jin buɗe ƙofar ɗakin ya sani ni ma na buɗe toilet, sai da na gama fitowa sannan mukai ido huɗu da shi ashe be fita, na juya zan koma ya damƙo ni,


    Tsalle na dinga yi ina ihu ai na waye yanzu wallahi sabit bazan kuma bari ka kuma duka na ba, tsaya wa yayi yana kallo na yadda na daddage sai tsalle nake yi



   Belt naga ya ɗakko wanda hakan ne ya sani na ƙara ƙwala ihu wanda ban daɗe da kwalawa ba sai ga knocking a ƙofar mu, shi yaje ya buɗe



   Mummy ce ina jin tana tambayar lfy da yake bashi da kunya sai yace


"mummy ba komai kawai faɗa tsakanin mata da miji, daɗi ne yake sata wannan ihun amma in shaa Allah baza ta kuma ba"


  Sam be bari ta shigo ba balle in gaya mata Itama mummy da yake ta iya ɗaurewa ƙarya .......🤭 sai ta juya ta tafi, dawowa yayi na ɗauka wajena zai yo har ina shirin wage baki 😱 sai gana yayi hanyar toilet


  Alwala yaje yayo sannan ya fito yai sallah asuba lkcn gari har ya fara wayewa a zuciyata nace ba lada, yana idar wa ya tasa ƙeyata na koma toilet sannan yaja ƙofar wai ni a toilet zan dauwama ne


  Ina zaune bacci ya fara ɗauka ta, sai na fara gyangyaɗi a kam toilet sit ɗin, ƙarar buɗe ƙofar naji wanda hakan ya tabbatar min da shi don haka sai na tashi


  Harara ya doka min sannan yace

"maza tashi ki fice wanka zanyi" sim sim sim na fice na bar masa toilet ɗin, ina fitowa naci karo da breakfast an kawo, daga dukkan alamu ya ci


   Kallo ɗaya nayi wa abincin na ɗauke kai ba a bani ba duk da dai nasan hadda ni aka siyo amma ba a bani ba bazan ci ba,


  Yana fitowa ya kora ni toilet, inda shikuma ya hau shiri, har cikin toilet ɗin ina jiyo ƙamshin turaren sa daya ke fesawa sai bayan daya gama sannan ya leƙo

"ki fito ki karya kuma da kingama ki koma toilet, kar inzo in same ki a ɗakin nan" yana gama faɗar haka ya fice


  Sai da na tabbatar da ya daɗe sa tafiya sannan na fito nai break fast inda na samu chips da kwai sai pepper soup na hanta wanda yaji curry


  Sai da na ƙoshi sannan na tashi na koma toilet don bana son abinda zai kuma haɗa mu da sabit,


   Zama nayi a toilet na rasa abinda yake min daɗi ga bacci ina ji amma babu comfortable guri na kwanciya, duk inda na juya ba daɗi, miƙewa kawai nayi na fito ɗakin na saka key sannan na kwanta akan gadon ai ko ya dawo sai yayi knocking kafin in buɗe



    bacci na nasha sosai sai la'asar sannan na tashi kuma har lkcn be dawo ba alwala nayi na zo na tada sallah ina cikin sallah sai gashi ya shigo



   Ganin yadda gadon yake a hargitse ne ya tabbatar masa da ankwanta

"wato ke bakya jin magana ko, nace miki kar ki kwanta sai da kika kwanta ko" kasancewar sallah yake yi ya sa shi saurara min



  Ni kuwa ganin yana jiran in idar yaci zalina ya sani na sake sabon kabbara tare da tada wata sabuwar sallah


  tun yana jirana a tsaye har ya gaji ya zaune, ko dana fuskanci hankalin sa yayi wajen tuni na zura a guje sai toilet na rufe, nai mamakin da be biyo ni ba



  Sai magariba sannan na buɗe yana zaune akan sallaya na raɓa ta gefen sa na wuce na gabatar da tawa anan na zauna har akai isha nayi sannan na tashi zan fice daga ɗakin


"ina zaki" naji yace min

"ɗakin su mummy zanje yunwa nake ji"

"ai dama an saba ci ki cika plate da uban abinci ki wuni kina ci ba abinda kika iya sai ci ko kwalliya irin taku ta mata ma baki iya sai gayyar ci, zo ki wuce ki ke can ga abinci can ki ɗauka ki ci kar kije ki tona min asiri"


  Wuce wa nayi na ɗau abinci na zauna naci na ƙoshi sannan na kama hanyar toilet, ina shiga naji an rufe ni ta waje, hmmmm komawa kawai nayi na yi shimfiɗa ta a cikin bath na kwanta na daɗe sosai sannan bacci ya kwashe ni



   Da asuba ina bacci a cikin bath naji ruwan sanyi a jikina a firgice na tashi ganin sabit ne ya sani yin Allah ya isa a raina


"fita ki bani waje zan yi alwala" fita nayi sai da yayi ya fito sannan nima na shiga don yin alwalar








 👩🏽‍🍳 *menu of d day*👩🏽‍🍳

   *coconut rice, with  fried chicken vanillah smoothy*


*coconut rice*

```ingredients```
-rice
-coconut
-tattasai (green & red)
-albasa
-maggi
-mangyada
-carrot
-peas
-tomatoes



  *method*

1) ki yi per boiling shinkafa sannan ki sauke ki wanke
2) ki pasa kwakwa sannan ki gurje baƙin bayan, daga nan sai kk yanka ƙanana sai kiyi blending ki tace ruwan

3) ki yanka carrots, da peas ki tafasa su, sai ki yanka tomatoes, tattasai koren da ja, sai ki yanka alabasa ki ajiye

4) ki zuba mai kaɗan a kasko sai kibi man da albasa kadan, idan man ya ɗan yi zafi sai ki zuba yankakkun kayanki duka banda koren tattasai


5) idan sun tafasa sai ki zuba ruwan kwakwa sannan ki zuba maggi saboda taste idan ruwan ya tafasa sai ki zuba shinkafa sannan ki rage wuta ki ƙara albasa


  6) idan shikafar ta dahu sai ki zuba yankakKen koren tattasai ki kashe sannan ki sauke


  *fried chicken*

```ingredients```

-kaza
 -maggi
-garlic
-thyme
-baking soda
-flour
-corn flour
-mai
-egg
Salt

*method*

1) ki wanke kazar ki sannan ki tsane ta sai ki zuba mata maggi, thyme, tafarnuwa da duk wani spice da kike so sai kiyi ajiye ta a frigde kamar awa ɗaya

2) idan yayi awa sai ki ɗauko ki tsane sannan ki zuba flour, corn flour, baking soda da kuma kwai sai ki jujjuya har sai ko ina yaji sannan ki ajiye a gefe

3) ki ɗauko kasko ki zuba mai idan yayi zafi saki dinga saka kaza ɗaya da ɗaya kina soyawa amma karki sakar mata wuta

4) idan ta fara jaa sai ki kwashe ki bar ta ɗan yi minti ɗaya sannan saki sake mayar da ita har ta ƙarasa sai ki sauke






 *vanillah smoothy*

```ingredients```


-yoghurt
-dabino
-vanilla extract
-madara

*method*

1) ki jiƙa dabinon ki ya juƙu sai ki cire ƙwallon

2) ki haɗa yoghurt, dabino, vanilla da madarar da sugar sai kiyi blending sai ki saka ƙanƙara a cup ko jug sannan sai a juye smoothy a kai sai a shaa 🍸


  👩🏽‍🍳 *BON APPETIT*👩🏽‍🍳


   *ASMA'UN SABIT*
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)



   P⃗a⃗g⃗e⃗ 12 🌹









 Yana idar da sallah yace min in kunna masa water heater, yi na yi kamar naji sai na wuce toilet nayi zamana


 Can sai gashi nan ya ƙwanƙwasa min toilet buɗewa nayi a zuciyata nace kamar gaske

"tara min ruwan wanka kuma da zafi nake son ruwan"


Sai a lkcn na tuno da kunna heater, ruwan na tara amma na sanyi sannan na fice naje na zauna a ɗakin, ina kallon sa yana ta shirye shiryen kayan da zai saka na ɗaurin aure


  Sai daya gama komai sannan ya shiga toilet ɗin, a tsorace nake nasan abinda zai biyo baya, can sai gashi ya leƙo jikin shi duk kunfa

 "shine dana ce ki kunna min heater ashe baki kunna ba ko" ya haɗe girar sama da ta ƙasa, tuni ciki na ya bada ƙululululu nai tsuru tsuru

  Kwafa yayi sannan yace

"zan kama kine" komawa yayi toilet sannan ya ɗauko bucket ya wullo min

"ɗauki maza kije ɗakin su mummy ki karɓo min ruwan zafi sauran ki bari in ta jiranki"


   Ɗaukar bucket ɗin nayi na fice ina shiga ɗakin mummy naga daddy ma har ya shirya yana shirin fita


  Gaisheshi nayi sannan na samu wuri na shantake ina sane da sabit kawai dai na share shi ne don Allah kaɗai yasan abinda zai min idan ya fito me ze min



   Itama mummy tana kwance akan gado inda ni kuma nake zaune akan kujera ina kallo, can kusan awa ɗaya sai ga sabit ya shigo duk a firgice, jiki sai ya fara rawa na ɗauka dukana zai yi mummy ce ta fara tambayar

" sa auta lfy kuwa"

"mummy ina lfy badia ce ta ƙara yin miscarriage" ya faɗa rai a jagule, a zabure mummy ta miƙe


  "me ya kawo ɓarin"
"oho wallahi mummy ban sani ba kinga na riga na gama haɗa kayana ma abuja zan wuce Allah dai yayi bazan samu ɗaurin auren ba kya gayawa daddy ga matsalar da ta sameni"


  Har ya fita mummy ta kira shi, sai daya dawo sannan ta kai duban ta gare ni

"shirya kibi mijinki" a zabure na juyo na kalle ta, shi ma sabit ɗin sai yace

"wallahi bazan tafi da wannan ƙazamar ba, duk inda na shiga ana kallo na" takura masa mummy tayi da kyar ya yadda


  Miƙewa nayi jikina a sanyaye Allah ya kawo min ɗauki, cikin hukuncin Allah muka kama hanyar abuja a jirgi, duk abinda nake tunanin sabit zai min sam be min ba don ko ta kaina ma be bi ba yana ta matar sa da ta kuma rasa babyn su



    Muna isa gida muka raba hanya inda ni nayi BQ shi kuma yayi ɓangaren sa shi ke nan na huta da jarabar sa


  ********************




 Mummy sai da tayi kwana uku sannan ta taho da amarya wacce ta tare a ɓangaren mijin ta,  a lkcn na sha hidimar abincin saukar baƙi kamar ba gobe amma cikin hukuncin Allah kowa ya watse ya rage sai ƴan gidan kaɗai


  Wai ina batun koyon girkin badia ne oho mata tunda ta samu ciki shike nan ta watsar da shi dama can ba koyo take ba, ya kasance ni nake giirki hankalina a kwance



  Rannan ina kitchen ina ta shirye shiryen dinner sai ga wata kyakkawa cikin shiga irin ta ƴan kanuri wato laffaya sai ƙamshi take yi daga ganin ta nasan amarya ce



   Da fara'ar ta ta shigo wanda ni kuma hakan yasani ɗan sakar mata fuska

"sannu zuwa nayi inga inda ake mana girki gobe zan fara girki shiyasa nace bari inzo inga abinci wa nake ci ashe ma yarinyace  amma gaskiya kin birge ni da ƙanƙantar ki amma kina zuba girki kamar ba gobe wannan in kikai aure mijinki ya huta"


 Dai da ta kai aya sannan ta nunfasa ikon Allah ni ban saba da zance ba balle kuma masu surutu don haka sai na rasa amsar da zan bata

 "me kike dafawa ne" ta tambaya tana ƙarasa shigowa kitchen ɗin, ban ce mata komai ba sai ma cooker da na nuna mata bi ma'ana ta gani da kanta




    Buɗe buɗen tukwane ta fara yi kowanne ta buɗe sai ta tambayen ni meye a ciki kuma ya dafa wa


   Ido kawai nake bin wannan baiwar Allahn da shi don ni ban taɓa ganin mutum me surutun ta ba, kamar wasa sai naga ta cire laffayar ta ta saka apron ta ɗau girki


  Ban tanka mata ba amma kuma dana ga alamae da gaske girkin take son koya sai na ɗan sakar mata jiki na har ina ɗan nuna mata yadda za ayi next



   Cikin ikon Allah muka gama tas ita ta fara tasting, nan ta hau zuba kamar ƴaƴan kanya, kasancewar hausar tata bata gama nuna ba ya sa wani abun inji wani kuma bana gane wa kuma ban damu ba


  Sai da taci abincin ta na dare anan sannan ta tafi inda kafin ta tafi ta ke sanar da ni sunan ta  *FANNAH*


_(ban sani ba ko fannah ma ta hikima haka take da shegen surutu shiya sa wannan ma take haka, abinka da barebari ba abinda suka sai 🗣 ko fannah)_ 😜





    Tun daga lkcn anty fannan ta zama regular costomer a kitchen ɗina, kullum sai ta zo tun ban saba ba har ya kai na fara sabawa da ita har nakan ɗan saki jiki da ita mu sha hira



  Duk wannan abun da muke bata san ko ni wacece a gidan ba ta ɗauka kawai cook don haka kullum sai tayi ta kurantani wai idan nayi aure mijina zai more da girki



   Wai in na yadda zata haɗa ni da ƙanin ta aure, kau da zancen nayi ban tanka mata ba don nafi son mu tafi a yadda ta ɗauke ni, ni ba mutum ce me son tona asirin rayuwata ga mutane ba




   shikenan kullum in dai nayi girki sai ta yaba kuma sai tace ƙanin ta zai more da mace n da ta iya girki  Hmmm shine kawai abinda nake binta da shi, sannan kuma sai ta dinga cewa wai ina da kyau *KUT* wannan jin sa nake yi kamar zagi


 Domin ta ina za aga kyau na wannan baƙin nawa ya rufe shi, ni dai bana tanka mata sai dai intayi abin dariya in ɗan yi mata murmushi


   Takan bani mamaki yadda take iya wuni a ɗakina ko a kitchen muna girki, tace ita bata yadda ba wai ace kullum mijinta abincin cook zai ci


  Don haka in aka ce ranar girkin ta ne da kanta take masa varieties daban daban sai dai in taimaka mata tunda bata iya namu sosai ba



  Ga wani shegen ƙamshi da kullum ta zo tana zuba shi kamar daga kwalbar turare take fito, ni ba mutum ce me son turare ba amma zama da ita ya sani son nima in dinga sakawa


  Rannan tazo koyar girki sai nace mata

"anty fannah kullum in zako zo kitchen sai kin fesa turare ne" nai mamakin dana ga tana shinshina kanta sannan ta girgiza shi tare da cewa

"ban sa turare ba kin ji ƙamshi ne" ko da dai bana kusa da ita tsab ina jiyo ƙamshin ta amma wai zata rena ni

  Taɓe bakina nayi sannan nace mata

"kema ai kin san kin saka don gashi ƙamshin turaren ki ya cika kitchen ɗin" murmushi tayi sannan tace

 "ko kaɗan ban saka ba turare yana da wani abun idan ka juri saka shi ƙamshin yakan kama jikin ka kaji ko baka saka ba kana wannan ƙamshin, kema idan na haɗa ki da ɗan uwana aure zan baki wannan sirrin"


 A matsayi zolaya ta min sai taga na ɓata rai tare da cewa

"anty fannah ina fa da aure kawai dai maganar auren nawa ne bana so don *AUREN BAUTA* ne"


  "ban gane ba" ta tambaya sharewa nayi sannan na shiga sabgogi na, itama da fahimci bana son zancen sai ta sako min abinda nake so wata labarin girki


 Nan na saki jiki muna tayi har Allah ya taimake mu muka kammala da ya ke ita ce da girki sai bata daɗe ba tana gamawa tayi pary ɗin ta wai zata gyara kafin mijinta ya ƙaraso


 Ina mamakin wannan gyarawar tata kullum mace cikin ƙamshi amma kuma wai duk da haka bai yi mata ba sai ta ƙara _kya je ki shaƙe mijin naki da ƙamshin da yafi ƙafin sa, don shi be saba da ƙamshin nan daga wajen matan sa ba_ na faɗa a raina



Sai da daddare da isma'il ya dawo fannah ta gabatar masa da kaɓakin da ta haɗa masa sannan ta zauna inda ya fara ci yana zuba santi sai da yayi nisa a cin abincin sa sannan fannah tace

"habibi wai meye tarihin yarinyar nan asmau, wallahi tausayi take bani kuma jiya muna hira da ita naji tace min tana da aure sannan ta haɗe rai kamar bata son zencen"

    Sam be mata nauyin baki ba ya sanar da ita komai akan abinda ya sani akan asmaun sakin baki tayi tana mamakin wannan abu wai sabit baya son asmau saboda baƙa ce


  Bayan asmaun kana kallon ta zaka gano tsabar kyan ta, sai dai baƙin daya ɓoye mata kyanta, kuma baƙin natan rashin kula ne da ta sami man da zai karɓe ta baƙin nata zai gyaru ya dawo me kyau


    Lallai ma sabit ɗin nan shi sam be san



Me ake cewa mace ba, yanzu wa zai ga asmau ya raina ta a matsayin ƴa mace don kawai Allah ya haɗa shi da ƙyal ƙyal banza  sai gayu amma sam ba a san yadda  za a kula da miji ba



 Aikin banza Allah yayi masa kyauta na mace kamar asmau amma sam be ganiba saboda tsabar shi bashi da nazari shine yayi watsi da rahamar ubangiji ya rungumi waccen jaja amalen macen da ba abinda ta iya sai ƙyalƙyali


   Wani tunani tayi sai tayi ƙwafa zai gane bashi da wayo ne, har ta gama abinda take yi ta kwanta tana tunanin wai sabit ne  da wannan aika aikar lallai ma bashi  da wayo
[4/23, 6:55 PM] Oum Haidar: ********************


  Kashegari sai ga anty fannah ta shigo kitchen ɗin tare da ita muka gama abincin rana sannan muka shiga ɗakina don muci


  Tare muke cin abinci in dai a nan zamu tare, sai da muka zauna muka fara ci sannan tace min

"asmau wai me yasa ba kya son gyara ko don ki jawo hankalin mijin nakin" tsayawa nayi kawai ina kallon ta,


 "ya akayi kika san mijin nawa" na tambaye ta don abin ya bani mamaki

"yo abin duniya yana ɓuya ne, ni dai ina tambayar ki me yasa ba kya son kwatar kanki ƴanci Kina matsayin matar aure amma kin mayar da kanki baiwa" tsame hannu na nayi daga plate ɗin sannan na ce mata

"anty fannah ni fa ina da class kuma gaskiya bazan iya abinda zai sani ƙasƙantar da kaina saboda namiji ba"

"ai ba ƙasƙantar da kai bane, kowace mace ai ƴar kwalliya ce, mu samu mu gyara miki wannan baƙin naki ke ma zaki ga canji"


 "wallahi anty fannah bazan yi bleaching akan wani namiji ba wanda be ma san darajar mace ba" dariya ta dinga yi, inda ni kuma na tsaya ina kallon ta


 "ba bleaching nace kiyi ba, baki ganin fata ta yadda take baƙi amma kuma kowa ya ganni ya san ni macece ko kema abinda na ke son in gani a tattare da ke kenan ki zama ƴar gayu yadda sabit zai rena kansa akan yadda ya mai da ke cook ɗin gidan"


  Taɓe baki nayi sannan na gyaɗa ka   na kuma cewa

"ni dai wallahi bazan gyara ba indai saboda wani sabit ne in zai soni yadda nake too in kuwa bazai soni ba ai duniya da faɗi in wani ya ƙi ka ai dubu sai su soka"


  Tsayawa tayi ta saki baki tana kallo sam bata ɗauka zan mata girman kai ba, don ta ɗauka zata juya ni yadda take so, duk yadda ta juya sai na juyo mata cewar ban yadda ba ni dai bazan gyara ba saboda sabit ba


 "to shike nan mu bar wannan zancen ba kince kina son ki dinga ƙamshi kamar ni ba" ƙara shinshina ta nayi sannan nace

"ina sooo"

"to shike nan muje part ɗina sai in baki turaren da zai karɓe ki duk inda kika ratsa kina ƙamshi har kike ki ratsa zuciyar sabit"


"ai kuwa indai don sabit zaki bani bana sooo" dariya ta saka

"wallahi ba dan shi bane ta so muje" miƙewa mukai muka kama hanyar part ɗin su







👩🏽‍🍳 *menu of d day* 👩🏽‍🍳


   *brown mac, served with short ribs soup and beef pancakes*


   ```brown macaroni```

 _ingredients_
-macaroni
-mai
-carrot
-peas
- albasa
-maggi
-curry
-tomatoes
-attaruhu


_method_

1) a zuba mai a tukunya sai a ɗan saka ƴar albasa har ta ɗan suyo, idan man yai zafi sai a zuba macaroni a rage wuta sai a soya ta sama sama don kar ta ƙone har sai tayi brown sai a sauke a tsane man


2) a zuba mai ɗan kaɗan a wani tukunyar sannan sai ki yanyanka tomatoes ɗinki da attaruhi ki zuba, idan ya soyu sai ki zuba ruwa ba dayawa ba domin ba a son mac ɗin ta tayi romo haka ake yin ta ƙamas


3) bayan an zuba ruwan sai ki wanke carrot da peas ki yanka carrot ɗin yadda kike so ki zuba a ruwan a zuba maggi da curry sannan a rufe a barshi ya har ya tasafa idan ya tafasa sai a zuba soyayyar mac ɗin nan a rufe sannan a rage mata wuta ta dahu a hankali sai a sauke



*short ribs soup*

_ingredients_

-naman haƙarƙarin rago, har da ƙashin
-dankalin turawa
-ƙwai
-albasa
-attaruhu
-maggi
-indomie/spag


*method*

1) ki samu naman haƙarƙari ki yanka su yadda kike so sannan ki dora a wuta sai ki zuba maggi, tafarnuwa albasa sai ki rufe


2) ki fere dankalin ki sannan sai ki yanka irin girman da kike so, idan naman ya dahu sai ki zuba dankalin sannan ki zuba yankakken attaruhun ki sai ki ƙara ruwa yadda dai zai sa shi yin ruwa sosai


3) ki fasa kwai ki soya, amma in kin tashi soyawa idan kika zuba mai a kaskon in yayi zafi sai ki goge man da tissue sannan ki rage wutar sai ki zuba ƙwan ki kar ki bari yayi jaa fari ake so idan bangare ɗaya yayi sai ki juya ɗayan ɓangaren bayan kin gama sai ki sauke ki bar shi ya huce sai ki nannaɗe shi kamar tabarma sannan sai ki yanka shi ƙanana


4)ki ɗauko i domie ɗinki ki dafa ta a ruwa amma karta dahu sai ki sauke ki tace ta ki ajiye ta



5) idan naman ki da dankalin ki sun dahu sai ki sauke, ki tabbatar da akwai ruwa sosai ko kuma yadda kike so amma miyar nan me romo ce sosai

  Idan an tashi za a ci sai a zuba soup ɗin a bowl ki zuba taliyar ki a saman sannan ki zuba yankakken kwanki kiyi masa kwalliya sai a gabatar wa da oga


ps: Idan kuma oga baya son indomie za a iya amfani da spaghetti amma a tabbatar sirara ce kuma ɗan kaɗan ba dayawa ba


 
*beef pancake*

_ingredients_


-naman sa (tsoka zalla)
-maggi
-tafarnuwa
-mai
-flour
-kwai
-albasa


*method*

1) zaki yanka nama yankan slice ko ince kamar yankan kilishi sai ki jera su akan chopping board ɗinki

2) ki barbaɗa musu maggi sannan ki yanka tafarnuwa ƙanana, sai ki gurza albasar ki duk sai kibi ki yaryaɗa akai


3) daga nan sai ki yaryaɗa man gyaɗa akai sai ki ba saka hannun ki ki daddake su, da tafin hanunki yadda haɗin zai shige su sai ki bar su kamar zuwa minti 2


4) sai ki ɗauke su ɗaya bayan ɗaya kina baɗe su da flour, ki samu kaskwan suyar ki sai ki zuba mai ɗan kaɗan kamar zaki soya ƙwai idan yayi zafi, sannan sai ki kaɗa kwai ki saka masa maggi sai ki dinga tsomawa kina sakawa a kan kaskon nan


5) ki rage wuta baya son wuta dayawa, idan ɓangare ɗaya ya soyu sai ki juya ɗayan ma ya soyu bayan sun soyu sai ki sauke


 👩🏽‍🍳  *BON APPETIT*  👩🏽‍🍳


*ASMA'UN SABIT*
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)



*Aisha ibrahim maina (mmn mummy) ga page ɗinki nan takanas na ta tashi na hana kaina bacci nayi typing ɗin shi saboda ke, don haka ashaa karatu lfy, ga girki nan a ƙasa da fatan za a ƙawata bbn mummy da shi*


  *my asmy i lobe u cikin kwanon shaaa*😘 🤣🤣🤣🤣


 
*amrath amrath & asmau ta hikima grp asmaun sabit na miƙo miki 😘, my asmy ba ke ba ɗayar Allah yasa ta gane kanta*

   P⃗a⃗g⃗e⃗  13🌹






Ɗakin anty fannah na bita inda ta haɗa min turaruka masu kyau sosai, daga nan sai tace min wai zan rakata shopping, kasancewar bana fita yasa ni yin murna sannan na sanar da mummy abinda mummy tace shine

"ki dawo da wuri saboda ɗora abinci" naji daɗin yadda bata hanani fita ba ko tace sai na tambayi ɗan renin hankalin can


   Kuɗina na wajen ta na karɓa kasancewar kuɗin aiki na a wajen ta yake na fito sai ɓangaren anty fannah inda na tarar da ita ta gama shiryawa muka kama hanya



   Shoprite muka nufa don yin siyayyar mu, wurin man shafa wa muka je sannan sai wurin turaruka, sutura, nai mamakin irin kuɗin da anty fannah take kashe wa kamar bata san ciwon su ba



    Rasa me zan siya na yi, sai dana ga alamar muna neman hanyar fita sannan nace wa anty fannah


"ni fa ban siya komai ba kuma ga kuɗina na zo da su" kallo na tayi sannan tai murmushi


"ai duk wannan siyayyar taki ce, jiya isma'il ya bani kuɗi kuma ba abinda zanyi da su don haka sai nace bari kawai in kashe miki su"


  Riƙe baki nayi ina kallon ikon Allah ni na rasa bakin gode mata ma, can dai sai na ɗan buɗe baki sannan nace mata "na gode"


   Yi tayi kamar bata ji ba, muka je counter ta biya sannan aka loda mana kayan mu a boot ɗin motar  muka kama hanya


  Na ɗauka gida zamu wuce sai kawai ganin mu nayi a saloon, muka shiga, ba kowa don haka muna zuwa aka hau yi mana gyaran kai, inda hair dreeser ɗin ta buɗe kaina wanda ya kusan sati uku da wata shegiyar kalba da nayi wa kaina



 Sai da ta tsefe min sannan tai min steaming ɗin sa tunda bana retouching kan nan nawa ya sha gyara dama gani da gashi, don ma bana kula da shi,


 tuni ya sauko har baya na, su ma kansu mutanen shagon sai yaba gashin nawa suke anty fannah ce ta kalle ni sannan tace


"kin ga waɗan nan ma sun yaba balle sabit" haɗe gira ta nayi

"ni wallahi anty fannah indai don sabit kike min wannan gyaran gwanda ma ki daina don ni ba san shi nake yi kuma babu abinda zai haɗa ni da shi"


 "ko kaɗan ba don shi nake yi, asmau buri na ki zama mace yadda ko sabit ya sauwaƙe miki zaki zama me class yadda samun namijin da zai soki bazai yi wuya ba, kinga maza ba abinda suke so kamar mace me gyara, gyara shine mace


   Amma dube ki dubi fuskar ki tukunyar kitchen ɗin ma tafi fuskar ki samun kulawa, haba asmau in ba kya son sabit mu bar zancen shi a gefe akwai wani ƙanina wallahi irinku yake so, ke dai kawai abinda nake so da ke shi, duk abinda na siyo miki kiyi amfani da su har ki goge wannan baƙin naki me dusashewa ya koma baƙi me kyau a lkcn zan sa sabit ya sake ki sannan in haɗa ki da ƙanin nawa wallahi zaki sha gata"



  Ta ƙare zancen ta da murmushi daɗi ne ya cika ni ganin zan samu wanda zai soni, amma ni da sabit haihata haihata, har aka gama mana gyaran kai da kuma pedicure da manicure tana bani duk wasu tips na gyara mace inda ni kuma nake recording a ƙwaƙwalwata



  Sai gab da magariba sannan muka koma gida, don haka kawai sai na ɗora wa gidan jollof na spag ɗuk da de na san sabit baya son



  A zuciyata nace in bazai ci ba matar sa ta dafa masa wani ai tana koyon girki (a ƙaryar ta) anty fannah ce ta tana ni muka gama sannan ta sani yin wanka na shafa sabon man data siyo min tare da turare na kwanta



  Dama haka ƴan gayu suke ko ba miji a kusa da kai sai ka baɗe jikin ka da turare ka nemi lfyr katifa ka kwanta hmmm nima in shaa Allah sai na zama ƴar gayu sai na kwatar wa kaina ƴanci daga wajen sabit sannan sai na auri mijin da zai ji dani murmushi nayi dana tuno da ƙanin anty fannah



  ********************



  Cikin hukuncin Allah nima na fara canza wa, wannan baƙin nawa wanda yake tsokane idon mutane ya fara kyau inda na koma chocolate colour sannan ƙamshi ya fara ratsa ni amma duk da haka sai anty fannah tace be mata ba don haka sai muka fara shirin zuwa maiduguri wai zata ganin gida inda ni kuma zan mata rakiya


   Da ƙyar aka shawo kan mummy ta yadda muje muyi kwana uku, inda anty fannah tace

"taga tafiyar dawowa ba sai lkcn da muke so ba"


  Ban sani ba ashe ta samu sabit sai tayi masa zancen tafiyar tamu buɗar bakin sa sai yace


"in ta tafi wa zai dinga mana girki
Wai yarinyar sam bata san aikin ta bane, bata san biyan ta ake ba zata wani tsiri tafiya to ban yadda ba in kuwa ta sake ta biki wallahi sai na zare a albashinta" ya faɗa a fusace


 "sabit matar ka ce faa kana nufin ba ka hanata bane saboda matar ka ce a a ka hanata ne saboda abincin da take maka anya kasan haqqin aure kuwa"


 Wani banzan kallo ya bita da shi sannan tace

"itace ta ke gaya miki ni mijinta ne, bata gaya miki sharaɗin auren namu bane, wai yarinyar nan me take nufi ne, ni me zanyi da ita Allah ya sauwake min zama da baƙar mace ai ni sai fara kamar yadda nake farin nan"



  Babu yadda anty fannah batai ba akan ya gaya mata yadda asmaun take a wajen sa amma duk kalmar da zata fito daga bakin sa game da asmaun ta ashsha ce da kuma yi wa kansa Allah ya tsare shi da baƙar mace


 "shike nan tunda ka rainata saboda baƙa ce ka bata takarda ta inya so sai ta samu wani ta aura wanda zai so ta"



Nuna mata yayi ko a jikin sa sannan ya ƙara gaba, tsayawa tayi tana ƙare masa kallo lalle ma sabit ɗin nan ashe haka yake,


  Shi ya ɗauka kyan mace a fuska ne kawai be san duk kyan mace in dai bata haɗa abubuwan da ake so na zama cikakkiyar mace hoto ce kawai kuma na wani ɗan lkc ne da an ɗan zauna an zama jiki shike nan sai kyan ya gushe kuma sai a koma zaman gaskiya zaman da ba kwaskwarima ba ƙyalƙyal banza


  Amma shi sam kamar be fahimta ba shike nan mu zuba ido ni da kai sabit zamu ga wa zai zo nan gaba yana ƴar murya, lallai ma sabit ɗin nan ta kuma maimaitawa tana yin gaba abinta



   Shiri muka soma yi na tafiya, ni dai murnata ɗaya zan huta sannan zanje in haɗu da wanda zai soni kamar yadda nake so, sannan in samu kulawa



    Cikin ikon Allah muka kama hanyar maid. ni da anty fannah tafiyar da ta canza min rayuwa, wacce ta fidda ni ƙuncin nan sannan ta saka ni cikin wani hali da babu abinda zance sai godiyar Allah



Muna sauka muka wuce gidan su anty fannah, babban gida ne nayi mamakin irin girman gidan su, sassane daban daban, family house ne wanda yake cike da iyalai daban daban


   Mahaifin anty fannah shine babba a gidan kuma shine me abin hannun gida duk da dai kowa yana da nashi amma nashi ya fi na kowa


  Ɓangaren su ƙato inda mahaifiyar anty fannah ce kawai mata a wajen bbn su, tunda muka sauka nake zare ido inga ko zanga ƙanin natan  da take cewa zata haɗa ni, wayaga azarɓaɓi



   Sauka ta musammam akai min, kasancewar yaren su na kanuri suke yi yasa sam ban ma gane me suke nufi ba amma kuma kamar da ni suke don naga alamar sukan ɗan saci kallo na sannan su ci gaba



  Kunya ce ta kamani, ko anty fannah tana wa mmn bayanin nice wacce za ta haɗa da ƙanin ta Allah ya sa na faɗa a raina cike da kunya




 Sai da suka gama tsab sannan anty fannah ta ja ni zuwa ɗakinta muka ci abinci inda take gaya min cewar zamu koma gidan ƙanwar mmn ta da zama acan za ai mata gyara jiki ne in ina so sai in faɗa sai ai min



  Ganin cewar jikina a haka is ok ya sani cewar bana so nafi son gani na a haka, sam bata tanka ba ko ta musa min sai da muka gama komai sannan muka shirya inda muka kama hanyar gidan kanwar mmn tata



Mun isa gidan ana kiran sallah la'asar gida ne de irin namu na mutan kano, tsarkar gida ne babba sosai sai ɗakuna da suka zagaye gidan sai banɗaki sannan wani tafkeken kitchen



 Kusan rabin tsakar gidan cike yake da shirgi, da tukwane waɗanda duk aka ajiye su, sai uban itatuwa a buhu buhu sai kace ƴar me magani



  Gidan banda ƙamshin turare babu abinda yake yi kamar ma'aikatr sarrafa turaruka, mata ne sun kai kusan 20 kowacce da abinda take yi, daga masu haɗa turare sai masu sassaƙa icce ko dai wani abu.


   Suna ganin shigowar mu su hau yaren su, wanda sam bana ganewa amma daga dukkan alamu murnar ganin anty fannah suke, kayan mu suka karɓa, sannan suka shigar mana da shi wani ɗakin inda muma muka shiga bayan mun gama gaisawa



  Wata mata ce zaune a kan tafkeken carpet ɗin daya malale ɗakin tana ta magana a waya wanda sam ban san me take cewa ba, amma fuskar ta taf da fara'ar ganin mu sannan sai ta dinga ma na nuni da hannu na alamar mu zauna


  Wuri muka samu muka zauna sai da ta gama tsab sannan ta juyo gare mu, inda anty fannah ta ɗan kƙara durƙusawa tare da gaishe ta da yaren su ni ma durƙusawar nayi amma sai nayi gum



  Anty fannah ce take mata bayanin gaishe ta nake, da hannu ta saka ta yafito ni inda ni kuma na tashi na ƙarasa kusa da ita


   Yaran su ta dinga yi tare da ƙare min kallo ido na kai kan anty fannah sai take cewa

"tace kina da kyau" kunya ce ta kamani na sunkuyar da kaina


  Wani ɗan mai ta ɗakko kusa da ita a wata ƙatuwar roba ta kwaɓa min a fuskar ta ba abinda man yake sai ƙamshi


  A hankali ta fara shafa min shi sai daya game fuskar tawa gabaɗayan ta sannan ta soma murza min kamar nayi kuka don zafi amma sai na dake


 Sai da ta gaji don kanta sannan ta dena ta juya tayi wa anty fannah yaren su wanda anty fannah tabi matar da murmushi nuna jin daɗin ta



Wai magunguna ta ɗauko sannan ta kira wata mata inda ta dinga ɗiba tana yi wa matar bayanin yadda za ai amfani da su ni dai ko kalma ɗaya bana fahinta,


  Sai da ta gama sannan anty fannah tace min

"tashi ki bita ita zata miki gyaran jikin" tsayawa nayi na saki baki sai da ta ƙara maimaita min sannan na tashi na bayan mayar


 Wani ɗaki naga mun shiga wanda ada ban ganshi ba domin yana ƙarshen gidan, muna shiga ɗakin kamar kitchen haka yake saboda tsabar tarkacen sannan tukwane sai wasu robobi manya manya ga kuma wani abu da akayi shi kamar da icce me ko me gashi nan dai kala kala


  Wani ƙaton baho ta ɗauko ta zuba wani ruwa ta gama haɗe haɗen ta sannan tai min nuni da in yi wanka da ruwa, bokiti na ɗauka na zundumin ruwan sannan na kama hanyar toilet don in watsa, ko da na shiga banɗakin sai ga matar ta biyo ni


 Tsayawa nayi ina kallon matar nan kar dai tace min itace zata min wanka, tsare ta nayi da ido don in san me take shirin yi



  Wani riga ta ɗauko min ƴar ƙarama kamar shimi amma half vest, da wandon sa tace min in saka, ganin na ƙi karɓa ya sa ta fara min faɗa


 Karɓa nayi sannan na juya mata baya, kayan sababbi ne na saka sai da na gama sannan ta juyo,


   Wani botiki ta ɗauko, ta lakuci wani sabulu sannan ta fara gurza min, zafi ne kawai yake ziyartata


  Ko ina na jikina wanda yake waje haka ta dinga bin jikin nawa tana dirza tana ƙara sheƙa min ruwan tare da ƙara saɓar sabulun tana ƙara wanke ni


 Sai da ruwan ya ƙare ta kuma fita ta kuma ƙarowa, ko da ta dawo, sai ta ɗibo ruwa tace min in ɗauraye jikina



 Ruwan na zuba na ɗauraye jiki na sannan ta kuma zaunar da ni akan wata kujera inda ƙasan kujerar




Turiri yake fita yana ratsa ni ta ƙasan sannan jikina kuma tana ta saɓar min shi kai ranar na gurzu sai kace za a canza min fata



   Sai da aka gama tsab sannan na cire rigar jikina da wandon na ɗauro zani na fito, inda tazo ta sakani a cikin wani abu shi ba kwando gashi nan dai


  Turare ne yake ta tashi a cikin sa gabaɗay jikina na ciki in banda kaina da ke waje, gaskiya ranar na sha gashi


  Shi kanshi kai na ba a barshi a baya ba, haka ya sha gyara sai wani ni'imantaccen ƙamshi yake fiddawa



   Kwanan na 7 sati ɗaya kenan ana min wannan gyaran wanda nasan dana gama zan haɗu da ƙanin anty fannah nasan yana ganina zai ruɗe yace saini


   Ga kuma na sha wanda shi wannan da anty fannah muke sha, lkcn da aka gama aka bani izinin kallon mudubi na ɗauka ba ni bace 🤣


  Ɗau haka na yi da baƙin nawa amma ba kamar na da ba, ƙwal haka na koma kai sai kayi zaton daga inji na fito ga wani ƙamshi daya ke tashi a jiki na kamar wacce tayi wanka da ruwan turare sannan ga santsi da laushin duk na haɗa


  Ni kaina daɗin taɓa fatar jikina nake yi balle kuma wani ya taɓa, ita kanta anty fannah sai yaba min take da irin wannan haɗuwar dana ɗauka



  "kin ganki kuwa asmau ai wallahi yanzu idan sabit ya ganki sai ya ruɗe ya dena kula wannan ja ja amalen tasa"


  Zunɓurar baki nayi sannan nace

"ni fa ba don shi nayi wannan gyaran ba fatana Allah ya haɗa ni da mijin da zai so ni kamar ba gobe ba wannan ɗan renin hankalin ba"


   Dariya tayi sannan tace

"hmmmm shima sabit ɗin bari ya afka tarkon nan zaki ga love 😍 har sai kince ya ishe ki" ni sam maganar wani sabit ma bana so balle inyi tunanin zai so ni



  Me ya haɗa ni da shi ai na riga na gama da babin sa, haka muka ci gaba da hira na so ace ta kuma sako zancen ƙanin natan sai naji bata sako ba Allah dai ya sa ba ta manta bane



 Satin mu biyu a maid. muka kama hanyar abj, cike da samun nasara daban daban barin ma ni ƙara kilewa da nayi da kuma gogewa,



   Lfy lau muka sauka agida inda na wuce part ɗin mummy directly don inyi reporting na dawo, nai mamakin yadda ta saki baki tana kallo na kamar bata taɓa ganina ba


 "mummy lfy ko sai kace yau kika fara ganina"

"asmau wannan canji haka sai kace inji kika shiga a maidugurin, kinga yadda kika koma kuwa lallai maa shaa Allah wannan gyara yayi sai dai kawai ace wa sabit ya kawo kuɗi"


 Ɓata rai na nayi sannan nace


 "mummy sabit ɗin daya ce in matar sa ta iya girki sakina zai yi nima ai a hakan take, ina gama haɗa kuɗin da nake so ko matar sa ta iya girki ko bata iya ba dolen sa ya ƙyale ni in tafi"


  "shi yace miki idan matar sa ta iya girkin zai sake kin" shiru nayi don be faɗa min haka ba amma alamu ne suka nuna min


"asmau har yanzu sabit be san irin baiwar da Allah yai miki ba amma daya gano hakan wallahi bazai iya rabuwa da ke ba, ni ma kaina bazan so hakan ba kuma bazan bari ba"

Tsayawa nayi ina kallon ikon Allah naga alamar matar nan ma son kanta ma yayi yawa don haka nasan duk yadda zan fadalta rashin son zama na da sabit baza ta gane ba


  Bana son shi kamar yadda shima yake ikirarin rashin sona da baya yi, miƙewa nayi sannan nace

 "mummy ni na gudu kitchen gwanda inje in ɗaura abincin gidan don kowa yasan na dawo" murmushi kawai tayi sannan ta gyaɗa kanta inda ni kuma na fice









👩🏽‍🍳 *menu of d day*👩🏽‍🍳


*curry rice served egg sauce and banana cocktail*

*curry rice*

```ingredients```

-shinkafa
-curry
-gishiri

*method*

1) ki zuba ruwa a tukunya idan ya tafasa sai ki auno shinkafar ki ki wanke ki zuba ki barta tayi tafasa ɗaya sannan ki sauke ki tace ruwan ki wanke ta

2) ki ƙara zuba ruwa amma ba dayawa ba yadda zata ƙarasa dafa miki shinkafar, idan ruwan ya tafasa sai ki zuba curry da gishiri ki barshi kamar minti ɗaya haka sai ki zuba shinkafar ki ki rage mata wuta a barta ta ƙarasa idan ta dahu sai a sauke







*egg sauce*

```ingrdients```

-egg
-attaruhu
-albasa
-maggi
-sardine


*method*

1) ki jajjaga attaruhu da albasa sannan ki a jiye su

2) ki samu sauce pan ki zuba mai da albasa kaɗan idan man yai zafi sai ki zuba jajjagenki sai ki bari ya tafasa


3) kasancewar ba ruwa don haka bazai ɗau lkcn ba, ki zuba maggi, da sardine (bayan ki dagargaza shi) sai ki juya

3) ki fasa ƙwai a bowl daban sai ki kaɗa, idan miyar ta ɗan ƙara soyuwa sai ki zuba kwan sai a barshi kar a juya amma a rage masa wuta


  4) idan ƙwan ya dahu sai a ɗan juya kaɗan don kar ƙwan ya dagargaje sai a saike



*banana cocktail*

```ingredients```

-banana
-sugar syrup
-milk
-flavour


*method*

1) ki tasafa ruwa kaɗan da sugar idan sugar ta narke sai ki sauke ki juye don ya huce


2) ki zuba madara a cocktail bowl sai ki zuba syrup da flavour ɗin ki sai ki saka a fridge don yayi sanyi, idan an tashi za ci sai a yanyanka ayaba ƙanana a zuba sai aci a take


👩🏽‍🍳 *BON APPETIT*👩🏽‍🍳



  *ASMA'UN SABIT*





 🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)



*Aisha ibrahim maina (mmn mummy) ga page ɗinki nan takanas na ta tashi na hana kaina bacci nayi typing ɗin shi saboda ke, don haka ashaa karatu lfy, ga girki nan a ƙasa da fatan za a ƙawata bbn mummy da shi*


  *my asmy i lobe u cikin kwanon shaaa*😘 🤣🤣🤣🤣


 
*Amrath amrath  & asmau ta hikima grp asmaun sabit na miƙo miki 😘, my asmy ba ke ba ɗayar Allah yasa ta gane kanta*



   P⃗a⃗g⃗e⃗  13🌹




Ɗakin anty fannah na bita inda ta haɗa min turaruka masu kyau sosai, daga nan sai tace min wai zan rakata shopping, kasancewar bana fita yasa ni yin murna sannan na sanar da mummy abinda mummy tace shine

"ki dawo da wuri saboda ɗora abinci" naji daɗin yadda bata hanani fita ba ko tace sai na tambayi ɗan renin hankalin can


   Kuɗina na wajen ta na karɓa kasancewar kuɗin aiki na a wajen ta yake na fito sai ɓangaren anty fannah inda na tarar da ita ta gama shiryawa muka kama hanya



   Shoprite muka nufa don yin siyayyar mu, wurin man shafa wa muka je sannan sai wurin turaruka, sutura, nai mamakin irin kuɗin da anty fannah take kashe wa kamar bata san ciwon su ba



    Rasa me zan siya na yi, sai dana ga alamar muna neman hanyar fita sannan nace wa anty fannah


"ni fa ban siya komai ba kuma ga kuɗina na zo da su" kallo na tayi sannan tai murmushi


"ai duk wannan siyayyar taki ce, jiya isma'il ya bani kuɗi kuma ba abinda zanyi da su don haka sai nace bari kawai in kashe miki su"


  Riƙe baki nayi ina kallon ikon Allah ni na rasa bakin gode mata ma, can dai sai na ɗan buɗe baki sannan nace mata "na gode"


   Yi tayi kamar bata ji ba, muka je counter ta biya sannan aka loda mana kayan mu a boot ɗin motar  muka kama hanya


  Na ɗauka gida zamu wuce sai kawai ganin mu nayi a saloon, muka shiga, ba kowa don haka muna zuwa aka hau yi mana gyaran kai, inda hair dreeser ɗin ta buɗe kaina wanda ya kusan sati uku da wata shegiyar kalba da nayi wa kaina



 Sai da ta tsefe min sannan tai min steaming ɗin sa tunda bana retouching kan nan nawa ya sha gyara dama gani da gashi, don ma bana kula da shi,


 tuni ya sauko har baya na, su ma kansu mutanen shagon sai yaba gashin nawa suke anty fannah ce ta kalle ni sannan tace


"kin ga waɗan nan ma sun yaba balle sabit" haɗe gira ta nayi

"ni wallahi anty fannah indai don sabit kike min wannan gyaran gwanda ma ki daina don ni ba san shi nake yi kuma babu abinda zai haɗa ni da shi"


 "ko kaɗan ba don shi nake yi, asmau buri na ki zama mace yadda ko sabit ya sauwaƙe miki zaki zama me class yadda samun namijin da zai soki bazai yi wuya ba, kinga maza ba abinda suke so kamar mace me gyara, gyara shine mace


   Amma dube ki dubi fuskar ki tukunyar kitchen ɗin ma tafi fuskar ki samun kulawa, haba asmau in ba kya son sabit mu bar zancen shi a gefe akwai wani ƙanina wallahi irinku yake so, ke dai kawai abinda nake so da ke shi, duk abinda na siyo miki kiyi amfani da su har ki goge wannan baƙin naki me dusashewa ya koma baƙi me kyau a lkcn zan sa sabit ya sake ki sannan in haɗa ki da ƙanin nawa wallahi zaki sha gata"



  Ta ƙare zancen ta da murmushi daɗi ne ya cika ni ganin zan samu wanda zai soni, amma ni da sabit haihata haihata, har aka gama mana gyaran kai da kuma pedicure da manicure tana bani duk wasu tips na gyara mace inda ni kuma nake recording a ƙwaƙwalwata



  Sai gab da magariba sannan muka koma gida, don haka kawai sai na ɗora wa gidan jollof na spag ɗuk da de na san sabit baya son



  A zuciyata nace in bazai ci ba matar sa ta dafa masa wani ai tana koyon girki (a ƙaryar ta) anty fannah ce ta tana ni muka gama sannan ta sani yin wanka na shafa sabon man data siyo min tare da turare na kwanta



  Dama haka ƴan gayu suke ko ba miji a kusa da kai sai ka baɗe jikin ka da turare ka nemi lfyr katifa ka kwanta hmmm nima in shaa Allah sai na zama ƴar gayu sai na kwatar wa kaina ƴanci daga wajen sabit sannan sai na auri mijin da zai ji dani murmushi nayi dana tuno da ƙanin anty fannah



  ********************



  Cikin hukuncin Allah nima na fara canza wa, wannan baƙin nawa wanda yake tsokane idon mutane ya fara kyau inda na koma chocolate colour sannan ƙamshi ya fara ratsa ni amma duk da haka sai anty fannah tace be mata ba don haka sai muka fara shirin zuwa maiduguri wai zata ganin gida inda ni kuma zan mata rakiya


   Da ƙyar aka shawo kan mummy ta yadda muje muyi kwana uku, inda anty fannah tace

"taga tafiyar dawowa ba sai lkcn da muke so ba"


  Ban sani ba ashe ta samu sabit sai tayi masa zancen tafiyar tamu buɗar bakin sa sai yace


"in ta tafi wa zai dinga mana girki
Wai yarinyar sam bata san aikin ta bane, bata san biyan ta ake ba zata wani tsiri tafiya to ban yadda ba in kuwa ta sake ta biki wallahi sai na zare a albashinta" ya faɗa a fusace


 "sabit matar ka ce faa kana nufin ba ka hanata bane saboda matar ka ce a a ka hanata ne saboda abincin da take maka anya kasan haqqin aure kuwa"


 Wani banzan kallo ya bita da shi sannan tace

"itace ta ke gaya miki ni mijinta ne, bata gaya miki sharaɗin auren namu bane, wai yarinyar nan me take nufi ne, ni me zanyi da ita Allah ya sauwake min zama da baƙar mace ai ni sai fara kamar yadda nake farin nan"



  Babu yadda anty fannah batai ba akan ya gaya mata yadda asmaun take a wajen sa amma duk kalmar da zata fito daga bakin sa game da asmaun ta ashsha ce da kuma yi wa kansa Allah ya tsare shi da baƙar mace


 "shike nan tunda ka rainata saboda baƙa ce ka bata takarda ta inya so sai ta samu wani ta aura wanda zai so ta"



Nuna mata yayi ko a jikin sa sannan ya ƙara gaba, tsayawa tayi tana ƙare masa kallo lalle ma sabit ɗin nan ashe haka yake,


  Shi ya ɗauka kyan mace a fuska ne kawai be san duk kyan mace in dai bata haɗa abubuwan da ake so na zama cikakkiyar mace hoto ce kawai kuma na wani ɗan lkc ne da an ɗan zauna an zama jiki shike nan sai kyan ya gushe kuma sai a koma zaman gaskiya zaman da ba kwaskwarima ba ƙyalƙyal banza


  Amma shi sam kamar be fahimta ba shike nan mu zuba ido ni da kai sabit zamu ga wa zai zo nan gaba yana ƴar murya, lallai ma sabit ɗin nan ta kuma maimaitawa tana yin gaba abinta



   Shiri muka soma yi na tafiya, ni dai murnata ɗaya zan huta sannan zanje in haɗu da wanda zai soni kamar yadda nake so, sannan in samu kulawa



    Cikin ikon Allah muka kama hanyar maid. ni da anty fannah tafiyar da ta canza min rayuwa, wacce ta fidda ni ƙuncin nan sannan ta saka ni cikin wani hali da babu abinda zance sai godiyar Allah



Muna sauka muka wuce gidan su anty fannah, babban gida ne nayi mamakin irin girman gidan su, sassane daban daban, family house ne wanda yake cike da iyalai daban daban


   Mahaifin anty fannah shine babba a gidan kuma shine me abin hannun gida duk da dai kowa yana da nashi amma nashi ya fi na kowa


  Ɓangaren su ƙato inda mahaifiyar anty fannah ce kawai mata a wajen bbn su, tunda muka sauka nake zare ido inga ko zanga ƙanin natan  da take cewa zata haɗa ni, wayaga azarɓaɓi



   Sauka ta musammam akai min, kasancewar yaren su na kanuri suke yi yasa sam ban ma gane me suke nufi ba amma kuma kamar da ni suke don naga alamar sukan ɗan saci kallo na sannan su ci gaba



  Kunya ce ta kamani, ko anty fannah tana wa mmn bayanin nice wacce za ta haɗa da ƙanin ta Allah ya sa na faɗa a raina cike da kunya




 Sai da suka gama tsab sannan anty fannah ta ja ni zuwa ɗakinta muka ci abinci inda take gaya min cewar zamu koma gidan ƙanwar mmn ta da zama acan za ai mata gyara jiki ne in ina so sai in faɗa sai ai min



  Ganin cewar jikina a haka is ok ya sani cewar bana so nafi son gani na a haka, sam bata tanka ba ko ta musa min sai da muka gama komai sannan muka shirya inda muka kama hanyar gidan kanwar mmn tata



Mun isa gidan ana kiran sallah la'asar gida ne de irin namu na mutan kano, tsarkar gida ne babba sosai sai ɗakuna da suka zagaye gidan sai banɗaki sannan wani tafkeken kitchen



 Kusan rabin tsakar gidan cike yake da shirgi, da tukwane waɗanda duk aka ajiye su, sai uban itatuwa a buhu buhu sai kace ƴar me magani



  Gidan banda ƙamshin turare babu abinda yake yi kamar ma'aikatr sarrafa turaruka, mata ne sun kai kusan 20 kowacce da abinda take yi, daga masu haɗa turare sai masu sassaƙa icce ko dai wani abu.


   Suna ganin shigowar mu su hau yaren su, wanda sam bana ganewa amma daga dukkan alamu murnar ganin anty fannah suke, kayan mu suka karɓa, sannan suka shigar mana da shi wani ɗakin inda muma muka shiga bayan mun gama gaisawa



  Wata mata ce zaune a kan tafkeken carpet ɗin daya malale ɗakin tana ta magana a waya wanda sam ban san me take cewa ba, amma fuskar ta taf da fara'ar ganin mu sannan sai ta dinga ma na nuni da hannu na alamar mu zauna


  Wuri muka samu muka zauna sai da ta gama tsab sannan ta juyo gare mu, inda anty fannah ta ɗan kƙara durƙusawa tare da gaishe ta da yaren su ni ma durƙusawar nayi amma sai nayi gum



  Anty fannah ce take mata bayanin gaishe ta nake, da hannu ta saka ta yafito ni inda ni kuma na tashi na ƙarasa kusa da ita


   Yaran su ta dinga yi tare da ƙare min kallo ido na kai kan anty fannah sai take cewa

"tace kina da kyau" kunya ce ta kamani na sunkuyar da kaina


  Wani ɗan mai ta ɗakko kusa da ita a wata ƙatuwar roba ta kwaɓa min a fuskar ta ba abinda man yake sai ƙamshi


  A hankali ta fara shafa min shi sai daya game fuskar tawa gabaɗayan ta sannan ta soma murza min kamar nayi kuka don zafi amma sai na dake


 Sai da ta gaji don kanta sannan ta dena ta juya tayi wa anty fannah yaren su wanda anty fannah tabi matar da murmushi nuna jin daɗin ta



Wai magunguna ta ɗauko sannan ta kira wata mata inda ta dinga ɗiba tana yi wa matar bayanin yadda za ai amfani da su ni dai ko kalma ɗaya bana fahinta,


  Sai da ta gama sannan anty fannah tace min

"tashi ki bita ita zata miki gyaran jikin" tsayawa nayi na saki baki sai da ta ƙara maimaita min sannan na tashi na bayan mayar


 Wani ɗaki naga mun shiga wanda ada ban ganshi ba domin yana ƙarshen gidan, muna shiga ɗakin kamar kitchen haka yake saboda tsabar tarkacen sannan tukwane sai wasu robobi manya manya ga kuma wani abu da akayi shi kamar da icce me ko me gashi nan dai kala kala


  Wani ƙaton baho ta ɗauko ta zuba wani ruwa ta gama haɗe haɗen ta sannan tai min nuni da in yi wanka da ruwa, bokiti na ɗauka na zundumin ruwan sannan na kama hanyar toilet don in watsa, ko da na shiga banɗakin sai ga matar ta biyo ni


 Tsayawa nayi ina kallon matar nan kar dai tace min itace zata min wanka, tsare ta nayi da ido don in san me take shirin yi



  Wani riga ta ɗauko min ƴar ƙarama kamar shimi amma half vest, da wandon sa tace min in saka, ganin na ƙi karɓa ya sa ta fara min faɗa


 Karɓa nayi sannan na juya mata baya, kayan sababbi ne na saka sai da na gama sannan ta juyo,


   Wani botiki ta ɗauko, ta lakuci wani sabulu sannan ta fara gurza min, zafi ne kawai yake ziyartata


  Ko ina na jikina wanda yake waje haka ta dinga bin jikin nawa tana dirza tana ƙara sheƙa min ruwan tare da ƙara saɓar sabulun tana ƙara wanke ni


 Sai da ruwan ya ƙare ta kuma fita ta kuma ƙarowa, ko da ta dawo, sai ta ɗibo ruwa tace min in ɗauraye jikina



 Ruwan na zuba na ɗauraye jiki na sannan ta kuma zaunar da ni akan wata kujera inda ƙasan kujerar




Turiri yake fita yana ratsa ni ta ƙasan sannan jikina kuma tana ta saɓar min shi kai ranar na gurzu sai kace za a canza min fata



   Sai da aka gama tsab sannan na cire rigar jikina da wandon na ɗauro zani na fito, inda tazo ta sakani a cikin wani abu shi ba kwando gashi nan dai


  Turare ne yake ta tashi a cikin sa gabaɗay jikina na ciki in banda kaina da ke waje, gaskiya ranar na sha gashi


  Shi kanshi kai na ba a barshi a baya ba, haka ya sha gyara sai wani ni'imantaccen ƙamshi yake fiddawa



   Kwanan na 7 sati ɗaya kenan ana min wannan gyaran wanda nasan dana gama zan haɗu da ƙanin anty fannah nasan yana ganina zai ruɗe yace saini


   Ga kuma na sha wanda shi wannan da anty fannah muke sha, lkcn da aka gama aka bani izinin kallon mudubi na ɗauka ba ni bace 🤣


  Ɗau haka na yi da baƙin nawa amma ba kamar na da ba, ƙwal haka na koma kai sai kayi zaton daga inji na fito ga wani ƙamshi daya ke tashi a jiki na kamar wacce tayi wanka da ruwan turare sannan ga santsi da laushin duk na haɗa


  Ni kaina daɗin taɓa fatar jikina nake yi balle kuma wani ya taɓa, ita kanta anty fannah sai yaba min take da irin wannan haɗuwar dana ɗauka



  "kin ganki kuwa asmau ai wallahi yanzu idan sabit ya ganki sai ya ruɗe ya dena kula wannan ja ja amalen tasa"


  Zunɓurar baki nayi sannan nace

"ni fa ba don shi nayi wannan gyaran ba fatana Allah ya haɗa ni da mijin da zai so ni kamar ba gobe ba wannan ɗan renin hankalin ba"


   Dariya tayi sannan tace

"hmmmm shima sabit ɗin bari ya afka tarkon nan zaki ga love 😍 har sai kince ya ishe ki" ni sam maganar wani sabit ma bana so balle inyi tunanin zai so ni



  Me ya haɗa ni da shi ai na riga na gama da babin sa, haka muka ci gaba da hira na so ace ta kuma sako zancen ƙanin natan sai naji bata sako ba Allah dai ya sa ba ta manta bane



 Satin mu biyu a maid. muka kama hanyar abj, cike da samun nasara daban daban barin ma ni ƙara kilewa da nayi da kuma gogewa,



   Lfy lau muka sauka agida inda na wuce part ɗin mummy directly don inyi reporting na dawo, nai mamakin yadda ta saki baki tana kallo na kamar bata taɓa ganina ba


 "mummy lfy ko sai kace yau kika fara ganina"

"asmau wannan canji haka sai kace inji kika shiga a maidugurin, kinga yadda kika koma kuwa lallai maa shaa Allah wannan gyara yayi sai dai kawai ace wa sabit ya kawo kuɗi"


 Ɓata rai na nayi sannan nace


 "mummy sabit ɗin daya ce in matar sa ta iya girki sakina zai yi nima ai a hakan take, ina gama haɗa kuɗin da nake so ko matar sa ta iya girki ko bata iya ba dolen sa ya ƙyale ni in tafi"


  "shi yace miki idan matar sa ta iya girkin zai sake kin" shiru nayi don be faɗa min haka ba amma alamu ne suka nuna min


"asmau har yanzu sabit be san irin baiwar da Allah yai miki ba amma daya gano hakan wallahi bazai iya rabuwa da ke ba, ni ma kaina bazan so hakan ba kuma bazan bari ba"

Tsayawa nayi ina kallon ikon Allah naga alamar matar nan ma son kanta ma yayi yawa don haka nasan duk yadda zan fadalta rashin son zama na da sabit baza ta gane ba


  Bana son shi kamar yadda shima yake ikirarin rashin sona da baya yi, miƙewa nayi sannan nace

 "mummy ni na gudu kitchen gwanda inje in ɗaura abincin gidan don kowa yasan na dawo" murmushi kawai tayi sannan ta gyaɗa kanta inda ni kuma na fice




 👩🏽‍🍳 *menu of d day*👩🏽‍🍳


*curry rice served egg sauce and banana cocktail*

*curry rice*

```ingredients```

-shinkafa
-curry
-gishiri

*method*

1) ki zuba ruwa a tukunya idan ya tafasa sai ki auno shinkafar ki ki wanke ki zuba ki barta tayi tafasa ɗaya sannan ki sauke ki tace ruwan ki wanke ta

2) ki ƙara zuba ruwa amma ba dayawa ba yadda zata ƙarasa dafa miki shinkafar, idan ruwan ya tafasa sai ki zuba curry da gishiri ki barshi kamar minti ɗaya haka sai ki zuba shinkafar ki ki rage mata wuta a barta ta ƙarasa idan ta dahu sai a sauke



*egg sauce*

```ingrdients```

-egg
-attaruhu
-albasa
-maggi
-sardine


*method*

1) ki jajjaga attaruhu da albasa sannan ki a jiye su

2) ki samu sauce pan ki zuba mai da albasa kaɗan idan man yai zafi sai ki zuba jajjagenki sai ki bari ya tafasa


3) kasancewar ba ruwa don haka bazai ɗau lkcn ba, ki zuba maggi, da sardine (bayan ki dagargaza shi) sai ki juya

3) ki fasa ƙwai a bowl daban sai ki kaɗa, idan miyar ta ɗan ƙara soyuwa sai ki zuba kwan sai a barshi kar a juya amma a rage masa wuta


  4) idan ƙwan ya dahu sai a ɗan juya kaɗan don kar ƙwan ya dagargaje sai a saike



*banana cocktail*

```ingredients```

-banana
-sugar syrup
-milk
-flavour


*method*

1) ki tasafa ruwa kaɗan da sugar idan sugar ta narke sai ki sauke ki juye don ya huce


2) ki zuba madara a cocktail bowl sai ki zuba syrup da flavour ɗin ki sai ki saka a fridge don yayi sanyi, idan an tashi za ci sai a yanyanka ayaba ƙanana a zuba sai aci a take


👩🏽‍🍳 *BON APPETIT*👩🏽‍🍳



  *ASMA'UN SABIT*
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)



   P⃗a⃗g⃗e⃗  14🌹




Gyara jikina ya kankama ko dana koma gida ban dena ba sai ma abinda ya ƙaru yanzu na zama ƴar gayu don anty fannah har tsokana ta take yi wai na kile na haɗu saura haɗuwar mu da sabit


  Na kan ɓata rai a ni yanzu na fi ƙarfin sabit sai wanda zai so ni mu gwada soyayya tare wacce zata kasance a tsaftace ba mix ba irin ta sabita ba


  
   Duk wannan abun da nake bamu taɓa haduwa da shi ba tunda ba ɓangaren sa nake zuwa ba tunda badia tayi ɓari Allah ya yaye min wannan bautar


 Sai dai ita badiar wacce ganina da ita na farko bayan na waye sai da ta tsorata da ganina inda ta dake sannan ta fara kushe ni har da cemin


"inde ma don sabit kike yi to ki sa ranki a inuwa don bazaki taɓa birgeshi ba sabit sai ni kaɗai" sam ban raga mata ba nima clna ce mata


  "ai ni mijin da zan aura sabo zai kasance dal a leda ba saura ba" maganar ya ƙona mata rai kuma ƙiri ƙiri ta nuna hakan



  Tana shirin mai da martani ne sai anty fannah don haka sai ta haɗe rai tare da barin wurin tunda basa shiri dama ko da anty fannah ta tambaye ni me ya haɗa mu sai nace mata ba komai


  Don bana son ta ga ko na zaƙu in haɗu da ƙanin ta na fi son ta fara yi min maganar sa da kanta bana son nuna gazawa ta bayan na zama me class 😎


  Rannan da safe na tashi mai na ya ƙare don haka sai naje part ɗin anty fannah na faɗa mata in zata fita zan bata kudi ta siyo min, sai ma tace min inzo bayan azahar sai muje siyayyar tare don itama zatayi


  Da murnata na koma na je na ɗauka girki kafin wannan na gama na bayar aka kai kowanne part nashi sannan na ɗauki na mummy don in kai mata


 Da sallama na shiga falon na ajiye mata, tunda na ɗau gyara na zama kamar wata sabuwar aba a wajen mummy kullum na shiga sai tayi ta bina da kallo kamar bata taɓa gani na ba








Yau ma haka na kai mata har nayi hanyar waje zan fita sai ta kira ni, dawowa nayi na tsaya sai kuma ta rasa abinda zata faɗa min can dai sai tace


"kije kice wa badia ina son ganin ta" rai nane ya ɓaci ba abinda na tsana daya wuce wai inje part ɗin sabit


 Jikina a saɓule haka na fice na kama hanyar, na zo dai dai hanyar da zan shiga part ɗin sabit ne naga anty fannah


"muje ko don na gama shirya wa" ta faɗa min


 "gani nan zuwa mummy ce ta aike ni wurin anty badia" na faɗa murmushi naga ta saki sannam tace min


"maza kije ki dawo kuma ki dinga tafiya da nutsuwa kamar yadda na koya miki" ban kula taba hmmm kaji ta tafiyar da tace min sai a gaban mijina zanyi shi shine take son inyi shi zan shiga part ɗin wannan mara *M* ɗin


  Ƙara sauri nayi ko dana ga na kusa zuwa ƙofar falon sai na saka gudu don inje in dawo da wuri,


  Kiciɓis muka ci da wani dai dai corridor ɗin da zai sada ni da ƙofar falon, ruƙo ni yayi wanda da badan ruƙon ba da tuni nayi ƙasa


  Ko da nayi gaining balance ɗina maimakon ya sake ki sai ya ƙara riƙe ni tare da shaƙar ƙamshin da nake yi



   Can sai ya sassauta min riƙon inda ya kwantar da ni akan hannun sa muka haɗa ido *WAT* sabit ne



   "kina gudu ina zaki je, dubi jikin ki lenge lenge kamar bakya cin abinci da badan na riƙe ki ba da tuni kinyi ƙasa kuma irin masu jikinku basa wahalar karye wa"



  Ya faɗa fuskar sa taf da fara'a har wani kashe min ido yake na salon yaudara, hankaɗe shi nayi wanda yai taga taga zai faɗi sai kuma ya tsaya ƙyam duk da haka ina jikin nasan


 "kar ki kayar da muna preety" ya faɗa


  Haushi ya kuma kama ni, na kuma haɗe raina sai ya sake ni

"ki dinga tafiya a hankali don kar kiyi wa kanki illa" ya faɗa wanda ni ko ta kanshi ban bi ba na shige ciki


*******************


  Sabit tsayawa yayi yana tunanin wacece wannan gaskiya tayi matsalar ta ɗaya baƙa ce kai da fara ce wannan da anyi haɗuwa


 Kasa daurewa yayi sai daya bi bayan ta don yaga ko meye dangantakar su da badiar


  Ima shiga falon ma dinga ƙwala mata kira, sai mula sannan sai gata ta sauko


"bashi na ci miki da kike min wannan kiran"


 "mummy ce tace kije"  na bata ansa


"me zata min" ta tambaya


"wannan kuma imkinje kyaji" na amsa mata tare da juya domin in fice cin karo muka ƙarayi da shi amma wannan karon sam jikin mu be haɗe ba


"asmau" naji badia ta ƙwala min kira, juyo wa nayi ba tare da na tanka mata ba


 "me zaki dafa da daddare"

"tuwon semo miyar egusi" na bata ansa


"bana son tuwo jollof nake so kuma ki kawo da wuri, *SD* me kake son yin dinner da shi" ta tambaye shi


 Be amsa ta ba saboda gabaɗayan hankalin sa baya tattare da shi sai da ta ƙara mai maitawa har da ƙwala masa kira sannan ya amsa inda kunya ta saka shi shigewa kitchen wanda ni kuma na fice na bar musu falon ina jiyo badia tana tambayar sa wai tunanin me yake a zuciyata nace can ta matse muku



    Ina fitowa na ɗanyi nisa daga part ɗin nasu najiyo ana kirana ban tanka ba don nasan sabit ne ƙarasowa yayi ya sha gabana


  "kina ji ina ta kiranki" shan kunu nayi nai masa banza

"naji kince tuwo zaki da daddare ni bazanci tuwo ba kiyi min parpesun naman kai da meat pie" kallon sama da ƙasa nai masa sannan nace


"ai na riga na gama rufe girkin da zanyi yau, in zaka ci abincin da matar ka zata ci wato jollof too in kuwa baza ka ci ba sai ka sata ta girka maka ai ta koyi girki a wajena"


 "ban gane kin rufe karɓar girki ba, ni mijinki nace miki ga abinda zan ci shine zaki wani ce kin rufe karɓar girkin to ni zaki yi wa biyayya ko wa"


 "ni ban san da wani batun aure ba aiki nake yi ake biyana, kamar yadda ka ɗauki auren ka yada shi a kwandon shara haka ni ma na ɗauke shi na saka shi a masai kaga yanzu ba wannan batun ake ba don haka ka ajiye wani batun mijin aiki ne na yau na rufe karbar order in kana son parpesu gobe da safe ka kira kitchen ka faɗa" ina gama faɗa masa na raɓa ta gefen shi na wuce



  Lallai le ma yarinyar nan ni zata ce wa haka, ni da nake a matsayin mijin ta nace ga abinda zan ci shine bazata girka ba sai wasu Ƙarti zata girkawa abinci wallahi da sake ya za ayi wai matata ni baza ta min abinda nake so, wallahi hakurina ya zo ƙarshe dole ne a matsayin ta na matata ta kasance tana ƙarƙashina sannan tana bauta min ne ni kaɗai



  Yana masifa ya kama hanyar part ɗin mummy dole ne duk abinda za a yi ayi a yau amma ban yadda ba ace matata ban da iko da ita


  Har ya shiga ɓangaren mummy yana masifa, tana zaune ta ga shigowar shi ko sallama babu duk a tunanin ta ma ko faɗa sukai da badia ta ɓata masa ransa


  "lfy auta na ganka haka wa ya taɓa min kai," ran shi a ɓace ya zauna kusa da ita sannan yace


 "gaskiya mummy na gaji da wannan abun da ake min wai ace matata ta zama baiwa a gidan nan, kowa zai iya juya ta yadda yake so amma banda ni mijinta gaskiya bazata saɓu ba na gaji lkc yayi da matata zat dawo ƙarƙashin iko na" sam mummy bata fahimci sai tace masa


 "auta wake juya maka badiar taka" mummy ta tambaya, ɓata rai yayi sam baya son ambatan sunan asmau don gani yake yi kamar ajinsa zai zuba amma ganin mummy sam bata ɗauko maganar tashin ba ya sa shi ambatan ta


  "ba badia nake nufi" ya faɗa ƙasa ƙasa, dariya ne ya so ƙwace wa mummy amma sai ta dake lallai tarkon data ɗana ya kama ɗan natan ke nan


  Amma sai ta nuna sam bata gane me yake nufi ba

"auta a gidan nan kana da wata mata ne bayan badia, only ɗin taka" ɓata rai taga yayi sannan ya ƙara sunkuyar da kansa tare da yin ƙasa ƙasa da muryar sa kamar wanda yake jin kunyar furta kalmar sannan yace


"ɗayar matar tawa mana, mummy kar ki ce kin manta ta mana" shiru mummyn ta sake yi kamar me tunani dariya ce take son suɓuce mata amma kuma tafi son sai ya faɗi sunan ta da kanshi


 "in banda abin auta ai da ka faɗa min in ka kuma ganin wata kana son ƙarawa, ai dama na san nan gaba dole ka nemi ƙari tunda baka samu mace ba har yanzu"


 "mummy wai asmaun ce kika manta" ya faɗa a fusace dariya ce ta suɓuce wa mummy

"dama ina son jin sunan ta daga bakin ka yanzu me ya haɗa ku da asmaun kazo kuma kana complain"


"mummy yarinyar nan ko kaɗan bata san matsayin miji ba"  nan ya labarta mata abinda ya haɗa su da asmaun sannan ya ɗaura da cewar


 "gaskiya hakuri kawai nake yi ni matata bata da lkcn da zata kula ni kullum sai dai ta dinga girkawa wasu abinci amma ni sam bata da lkc na gaskiya baza ta saɓu ba nagaji" yai ta mita


  Mummyn sakin baki tayi tana kallon ikon Allah sannan a ranta tana godewa Allah daya dawo da hankalin sabit kan asmau, don kuwa ko ba komai asmau sai tafi badia iya kula da sabit sosai



 Bata da wani buri daya wuce ace ta samu me kular mata da ɗan autan ta sabit, badia ba me son aiki bace don haka gaba kaɗan sabit zai rasa macen da zata kula da shi


 Amma asmau daga ganin ta zata juri wahala kuma zata iya ɗawainiya da wahalar sabit kuma ta asmau sabit zai samu zuria sosai tunda tasan shi da son ƴaƴa


 Amma badia ba lallai bane ta haifawa sabit ƴaƴa dayawa, juyowa tayi ta kalle shi sannan tace

"auta yanzu me kake so"

"ni dai kawai so nake yi dum lkcn da na kira ta tai min wani aiki bana son ta kuma cewa wai zatai aiki wani ko kuma tana wani ya sata aiki nafi son ina bata umarni kawai ta ɗauka"


  Gyaɗa kai mummy tayi sannan ta jinjina maganar sa

"in shaa Allah zan mata faɗa akan ta dinga bin umarnin ka a matsayin ka na mijin ta" daga nan ta shiga lallaɓa shi tare da kwantar masa da hankalin sa akan babu wanda ya isa ya raba shi da *ASMA'UN SABIT* ɗin sa


  Kanshi me ya fasu kamar an masa kyauta sai da ta kwantar masa da hankalin sa sannan yai mata sallama ya kama hanyar sa mummy bin bayan sa tayi da kallo, lallai sabit daga gani ka fara dawowa hanya madaidaiciya ka fara gane cewa ```ba kowacce  ƙwarya me kyau ce take da daɗin shan fura ba```



 ********************



    Ko da muka dawo  kasuwa sai mummy ta kira ni akan tana son ganina sam ban kawo komai ba don haka na shirya na tafi pary ɗin nata


 Ina shiga na zauna sannan ta fara min faɗa akan halin ko in kula da nake nunawa mijina ```wai sabit```😏


  Faɗa ta dinga min wai in dinga kula da buƙatin sa, menene da menene ni jin maganar tata ma nake yi kamar soki burutsu tunda dai ba ɗauka zanyi ba ai ni da sabit sai dai daga nesa amma nai masa nisa sai dai wata ba ni ma'un ba


  Ta gama saki burutsun ta tsap ban tanka mata ba, sai da ta gama sannan ta sallame ni yadda na tashi na kakkaɗe rigata haka zancen nata ya zube daga kunnuwa na sukai ƙasa banji ba balle ince zan aiki da su


 Komawa nayi hidimar gabana na tattara lamarin sa na watsa a kwandon shara, tsakanina da shi ya kira kitchen ya faɗi abinda yake so in faɗa masa


 Wani sabon salo daya ɗauko shine kullum in an gaya masa menu na gidan sai ya canza kuma abu me wahala yake ɗauko wa sam bana jin komai haka zan dafa masa


 Sai kuma ya canza salo wai innai girki in dinga kai masa nan ma nace bansan zance ba sai da mummy tai min magana sannan na fara kaiwa part ɗin nasaa


  Amma bana tashi kawai sai inna ga matar sa na nan ta yadda ba yadda za ai yai min magana ko ya kawo min wani renin sense


 Amma duk da haka ban tsira ba, idan na kai masa yai ta sani aiki kenan yi kaza gyara kaza, zuba min abinci kwashe kaza


 Haka dai amma ban taɓa tunanin sakar masa fuska ba don dana shiga ɓangaren nasa idan na cukune fuskar nan tawa har na fito be isa ya ga sakin fuskar tawa ba balle yace ze kawo min wani wargi


 Har yanzu be isa in kula shi be kai matsayin da zan tanka masa ba, duk da dai idan na shiga ɓangaren nasun yai ta surutu kenan ko kuma yai ta tambayar


  Da me dame nayi abincin wai saboda badia ta koya, in na daddage na tsuke wannan fuskar tawa sai dai yayi tambayar sa ya gama amma ƙala bazan ce masa ba



   Sai dai in ya gaji ko badia tai masa magana sannan zai dena amma gobe bazai daddara sai ya sake, sam wannan abun da yake yi be sani tanka masa balle inji ina sha'awar mu'amala da shi ni asmau sai namiji wanda ya san darajar mace ba muna maza ba
[4/26, 11:44 PM] Oum Haidar: *******************

Na ci gaba da kula da tattalin kaina ina yi wa ƙanin anty fannah tanadi,


  Watan azimi ne ya kama don haka anty fannah in ta zo kitchen tun safe bata barin shi sai mun gama abincin iftar, in itace da girki muna gama wa sai ta tafi in kuwa ba ita baca sai mu sha ruwan mu tare


   A lkcn na gano ashe macece me ibada sosai karatun qur'anin nan da azkar baya wuce ta safe da yamma, ganin haka ya sa nima na fara mata maganar akan ta koya min in ƙara sani sosai akan addini na tunda de Allah be sa na je islamiyya ba sosai ba



   Karatu sosai muka fara da anty fannah ba ɓangaren da bama taɓowa, wasu karatun inji kunya wasu kuma ba komai, kamar karatun ɓangardn tsarki 🙈


  Ba a karatun ilimin addini  ba har da na ilimin aure, wallahi wani lkcn idan tana wani maganar sai inji kamar in nutse a ƙasa saboda tsabar kunya amma ita ko a jikin ta kamar ba itace take faɗa ba, lallai sai a lkcn nasan cewar ni babbar jahila ce wacce ba abinda ta iya sai girki



  Lallai girki ba shine kaɗai abinda zai jawo hankalin miji zuwa ga matar sa ba har yaji bazai iya rayuwa sai da ita akwai dabaru dayawa ko in kissa



   Kamar su kissar iya magana ```wata bata da wani salo na iya yi miji magana yadda take yi wa ƙawarta haka take yi wa aikinta shi ma miji haka, ba wani ɗan laƙwasa harshe ko yango ko kararraiya```


Sai kissar iya zance
```wasu matan sam basu iya tauna magana kafin su faɗe ta ba haka suke suyi ta zuba kamar ƴaƴan kanya marasa daɗi``` inji mmn farency 😜


 Sai kissar iya kwalliya,kissar tafiya, yanga, rangwaɗa, shagwaɓa da kuma last but not d list wacce muke ganin kamar tafi kowacce itace iya kwanciyar aure, ```ƴammata ku gafarce, amma maganar gaskiya ce, duk macen da ta iya waɗannan kissosin sai dai wani ba mijinta ba```


   da kuma sauran su duk waɗannan abubuwan idan muka riƙe su gam sannan muka haɗa da roƙon Allah day in day out in shaa Allah sai dai muji anayi rigimar aure a maƙota ba dai gidajen mu _Allah ka bamu dacewa da ƙarshe me kyau_



    Ilimi sosai take koya min kuma nake naɗewa ina ɗauka ina haddace wa burina kawai Allah ya kaimu lkcn da zan kashe wannan auren nawa na bautaswa inyi auren soyayya 😍




👩🏽‍🍳 *menu of d day*👩🏽‍🍳


*tuwon semovita miyar egusi and kunun tsamiya*


   *tuwon semo*

```ingredients```

-semo
-flour
-butter

*ki zuba ruwa a tukunya sai ki rufe, idan ya tafasa sai ki zuba wani ruwan daban a bowl sai a dinga zuba semo ɗin ana juyawa har yayi kauri


 2) daga nan sai a ɗauki talge a talga tafasash shen ruwan, idan an talga sai a saya murfin sannan a rage masa wuta talgen ya dahu a hankali


3) idan talgen ya dahu sai ki haɗa  flour da semo, kamar flour ya fi semon yawa sai  a tuƙa bayan yayi ta sai a saka butter a ƙara tuƙawa sannan a rufe a rage wuta ya turara idan ya turaru sai a kwashe a leda


*miyar egusi*

```ingredients```

-kayan miya
-man ja
-egusi
-egg
-alayyahu
-maggi
-nama
-crayfish
-kifi


Method

1) ki saka naman ki a tukunya ki zuba maggi, albasa da tafarnuwa sannan ki rufe, idan tafasa sai ki zuba kayan miyar ki ki barshi ya dahu


 2) a wata tukunyar daban kuma sai ki zuba man jan da zakiyi miyar da shi idan yayi zafi, sai ki wanke kifinki ki zuba a mai ki soya sannan idan ya soyu sa a tsane

3) daga gefe kuma sai ki kwaɓa egusi ɗin ki da ruwa sai ki zuba a man jan sannan sai ki rage masa wuta yai ta dahuwa a hankali, idan ruwan ya ɗan tsotse sai ki fasa kwan ki ki kaɗa shi sannan sai ki zuba shi akan egusin ki bar shi ya ɗan dahu sannan ki juya idan kina son egusin ki ya dundunƙule kar ki juya shi sosai


4) sai ki juye egusin a miyar sannan ki zuba crayfish, ki ƙara maggi da albasa sannan ki rufe, in ruwan yai kaɗan sai ki ƙara ruwan


5) idan miyar ta yi dai dai sai ki zuba alayyahun ki wanda kika yanka kika wanke sai ki zuba kifin ki ki rage wutar sannan ki rufe


Minti ɗaya sai ki sauke


*kunun tsamiya*


*ingredients*

- ƙulun kunu
-tsamiya
-lemun tsami
-sugar


```method```

1) ki zuba ruwa sannan ki saka tsamiyar ki, idan ruwan ya tafasa sai ki tace sannan ki ƙara mayar da ruwan don ya ƙara tafasa


2) ki zuba ƙullin kunun sannan idan yayi kauri sai ki ɗan ƙara masa ruwa daga nan sai ki zuba a cikin ruwan zafi ki rage, idan yayi kauri sai a sauke


3) sai ki kuma ɗiban  ƙullin ki sakar masa ruwa sannan ki ɗauraye kunun sannan ki ɗan matsa lemun tsami sannan ki juye a flask



👩🏽‍🍳 *BON APPETIT*👩🏽‍🍳




*ASMA'UN SABIT*
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)



   P⃗a⃗g⃗e⃗  15🌹




  Yin karatu a wajen malama ta anty fannah ya sani ƙara wayewa da yanayin zamantakewa ta ɗan adam, kasancewar garden ɗin gidan a bayan part ɗin su ga sanyi ga iska ya sa kusan kullum a can muke karatu



   Idan nagama aiki sai in je part ɗin su sai mu koma garden ɗin mu zauna muyi ta karatun mu ko tai ta min fatawowi da dai sauran su


  Har akai sallah lfy muna karatun mu kuma na ɗau alwashin ko bayan sallah zan ci gaba da biɗar ilimina don ilimi shine hasken rayuwa, in babu shi mutum zai kasance kamar a duhu yake Allah dai yasa mu wanye ƙalau kuma ya bamu ilimi me amfani da mu da ƴaƴan mu amin summa amin



 Rannan muna garden ɗin sai ga isma'il ya zo

"ina ta neman ki a ciki ashe kina nan" ya ƙaraso yana faɗawa anty fannah, gaishe shi nayi sannan nayi niyyar tashi don in bar su su shana



  Hana ni yayi tace shima aiki ne ya kawo shi in zauna muyi karatun mu, komawa nayi na zauna muka ci gaba, kasancewar doguwar riga ce ƙirar dubai a jikina me belt wacce ta saka belt ɗin na ɗaure jikina da shi sai ɗan kwalinta da nayi rolling kaina da shi


  Ya sa sam ban sake ba ni da na saba yawo a cikin hijab kamar bukka 🤣, karatun mu muka ci gaba amma sam a nutse nake



  Sallamar gogan na badia na ji a bayana inda duk muna amsa ni kuma na haɗe raina don bana son wannan shishshige min daya ke yi



  Ƙarasowa yayi ya zauna dai dai kusa da ni har jikin mu yana ɗan gogar juna wanda hakan ne ya sa ni kuma na ɗan kuma matsawa ko ya sake amma bada ni ba, basarwa yayi kamar be san me yi ba sannan yace


"ku ashe anan kuka  yini kuna shan iska me daɗi shine sam ba a san a gayyaci mutum ba ko" ya ƙarashe zancen sa da sigar tambaya yana kallo na



  Iskar data kwaso shi ma ban shaƙa ba balle in tanka masa littafi na na ɗauko na rufe fuska ta da shi kamar ina karatu


 Anty fannah ce ta tanka masa

"yo ai ba a damu da ba, balle a san a ina muke yini" na san martani ta mai da masa murmushi yayi sannan yace


"ai matsalar taku ce ba kwa fara'a ga shegiyar shariya ko an muku magana kun san da ku ake amma sai ku share mutum kuyi kamar baku jiba"


"wannan shine cikar mace me aji" inji anty fannah


Su ka ci gaba da maidawa juna martani wannan ya faɗa wannan ya mayar dana ga abin nasu ba na ƙare bane sai kawai na miƙe na sannan nace


"anty fannah naga alamar kin samu abokin hira bari ni in wuce maci gaba da karatun nan gaba" ina gama faɗar haka nai gaba abina




  Nayi nisa naji yana ƙwala min kira ban tanka masa ba haka zalika ban tsaya ba, sai kuwa gashi ya sha gaba na

"baki ji ina kiran ki bane wai asmau me yasa kike da taurin kai ne"


"ai ban ɗauka da ni kake ba, na ɗauka badia kake son kira ka manta kace asmau" murmushi yayi wanda yai masa kyau kamar kar ya dena


"ashe kice abin naki kishi ne, to in banda abinki ai badia alba sa ar ki bace, yarinya kyakkyawa son kowa ƙin wanda ya rasa fara me kyan ɗaukar hankali"



  Haushi ne da takaici suka cika ni tsayawa kulashin da nayi gashi nan ya ɗige da yaɓa min magana



   Raɓa wa nayi ta gefen sa na wuce

"sai kace gurin ta ni kuma ka ƙyale ni Allah zai kawi min wanda zai soni ba don abinda nake da shi ba"



   Wannan kalmar tai mutuƙar ɓata masa wanda har ya sa shi shan gaba na tare da damkar hannun da ƙarfi wanda hakan ya sani wani radaɗi a hannun daga dukkan alamu matse mun hannun yayi


"saboda baki da hankali da auren nawa a kanki kike maganar samun wani, to wallahi karki ga ina ɗaga miki ƙafa ina nan a sabit ɗin da kika sanni in kika sake na kuma jin wannan kalmar daga bakin ki sai ki yaba wa aya zaƙin ta"



   Wulli yayi da ni inda na faɗi ƙasa har da gurje gwiwar ƙafa ta, kuka na saki dama me hali yana fasa halin sa ne na faɗa, kuma wallahi abinda kake nema a wajen nawa baza ka samu ba sai dai wata



   Kuma neman rabuwa da kai ban ma fara ba sai lkcn da na tara iya kuɗin da nake so zaka san cewar shayi ruwan na faɗa a raina tare da miƙewa ina karkaɗe kayan jikina mugu kawai


 ********************


   Tun daga lkcn na shiga wasn ɓuya da shi don duk abinda na san zai haɗa ni da sabit bana ma tunkarar sa shima a nashi ɓangaren naga alamun haka


  Don yawan kiran da ya ke min da yanzu ya daina sam kamar ma be fara ba,



  rannan da rana na gama lunch na kaiwa mummy na tarar da ita tana ta mita, zama nayi sannan nace

"mummy lfy kuwa"


"ina fa lfy ni da wannan har iskar kishiyar taki wai tayi tafiya amma sai da ta sauka sannan mijinta ya sani, shi ma da yake be san ciwon kansa ba ko a jikin sa" dariya ce ta so kubce min amma sai na dake


 Kaɗan ya gani be gama ganin komai ba ba dai zalinci ya riƙe ba ai ba abinda ya soma gani ma,

"mummy garin ƙaƙa akai haka" na tambaye ta da alamar damuwa a fuska ta


"ai da yake kin san ta riga ta shanye shi tas baya ganin laifin ta, kome tayi sai yace ai duk abinda take yi tana sane, be san mace ba a sakar mata, kai wannan yaron wai sai yaushe ze farka ne ya fahinci abinda nake nuna masa" ta faɗa tana dafe kanta alamar abun yana damun ta


" ke ma hadda ke sam baki san amfanin mace ga mijinta ba, kin saki mijinki wata sai juya miki shi take sam kin kasa jawo hankalin sa zuwa gare ki, gashi dai kinje kin sha gyara amma sam bashi da amfani tunda duk da gyaran naki kin kasa jawo hankalin mijinki gare ki, kullum sai dai a ganki a ɓangaren wannan yaro (isma'il) kina bibiyar fannah amma ke mijinki ko a jikin ki



   Haka kika ga fannah ta nayi wa nata mijin, wallahi har da laifin" faɗa ta shiga min tare da ƙarawa wai duk laifi na ne na kasa shishshigewa sabit balle har in samu fada a wajen sa ya jani jikin sa har ya banbance tsakanina da badia


Kallon baiwar Allah nan kawai na tsaya yi lallai so sone amma son kai ya fi, wato ma lefi nane, ni bata san ko a ƙafa a ɗaura min wannan koɗaɗɗan ɗan natan ba sai na yanke na gudu balle har a kai ga faranta masa ko shishshige masa Allah ya kyauta min Allah ya tsare ni



Sai da ta gama faɗan ta sannan ta sallemi tare da ja min kunne akan in fara jawo hankalin sabit zuwa gare ni,


  Binta kawai nayi da to amma kuma nace hmmm wayaga wallahi badai ni asmaun ba sai dai wata ai ni da sabit hayhata hayhata



   Na koma ɗakina ina tunanin abinda mummy take son nayi wa sabit wato da yake abin son kai ne, ni da nake mace nice za a ce inja hankalin sa me makon amatsayin sa na namiji ace ya fara ɗaukar action ni kuma a matsayina na mace a bani damar duba wa ko zan iya manage da shi amma sam abin ba haka yake ba nice ma zan cusa kaina lallai mummyn nan har yanzu baki san wace asmau ba



  Da yamma ina cikin yin dinner na kusa kammalawa ma sai naji call na intercom ɗin kitchen ɗin yana ringing kasancewar ba kowa ya sani zuwa ɗauka,


"hello" naji ance ko bacci nake yi nasan muryar ɗan renin hankalin nan amma sai na nuna ban sani ba


"hello waye" na amsa

"mijinki ne" na ji ya bada da amsa, murmushin mugunta nayi sannan na mai da masa martani bayan na maƙe muryata na shake ta sannan na gyara ta


"kana nan ƙalau ya gidan da komai da komai wallahi ina kewar ka sosai"  ina jin ɗan murmushin daya saki sannan yace min

"da gaske"

"zan maka ƙarya ne kasan ni kasan zuciyata kasan banda wani sai ka, lkc kawai muke jira ya kasance mu kasance waje ɗaya har abada"


 Daɗine ya lulluɓe shi kamar me, ni kuwa da yake nasan abinda nake shukawa ya sani ƙara sakin baki sai faɗa masa kalaman soyayya nake yi shi kuma yana biye min sai can dana ga ya shiga sosai sai nace masa


"ya maidugurin kuwa, Allah dai ya san ƴam matan can basa kalle min kai dan sunga bana kusa da kai" shiru yayi na ɗan wani lkc yai jim


"ABDUL baka jina ne" na kuma maimaitawa


"uban waye abdul" na ji ya faɗa, sai da na ɗauke phone ɗin daga kunne na na ƙyalƙyala dariya ta sannan na mai da ta na kuma cewa

"ba abdul ɗina bane na maiduguri ba, don Allah waye ya kira ni sannan yace min matar sa" wani ƙasurgumin zagi da luluƙo ya antayo min ni da abdul ɗin ya sani cire phone ɗin daga kunne na na kuma ƙyaƙyacewa da dariya



 "Abinda kike yi Kenan dama da auren ki to yau Allah ya tona miki asiri kuma wallahi zaki san baki da wayo" sai da ya gama bala'in sa sannan ya kashe wayar



 Dariya na ci gaba da yi gobe ma ka kuma kirana, ni abin ma dariga ya bani wai mijin ki ne, ko ta ina ya zama mijin nawan mijin suna dai girki na na cigaba da yi ina yi ina maimaita conversation ɗin mu ina dariya ni kaɗai lallai yau na kunna sabit



   ********************


   Takaicine ya ishi sabit har ya rasa yadda zai yi, tun yana kwance ya tashi ya zauna ya kuma kwanciya amma duk da haka ya rasa mafita, ya ze yi da wannan ƴar iskar yarinyar


 Wai da auren shi akanta amma take kula wani ƙato, har da cewa lkc kawai take jira su kasance tare, kenan da take nufin kashe auren da gaske take



   Gaskiya da sake ya za ayi ma in bar ta ta tafi, lallai ma dole ne in samu mafita, mummy ce kawai ta faɗo masa a rai, lallai mummy ce kawai zata iya kawo ƙarshen wannan lamarin



  Miƙewa yayi ya nufi ɓangaren mummy sam be nuna mata komai ba kawai sai yace mata


"mummy kinga badia bata nan part ɗin nawa ba mace don haka me zai hana ki saka waccen yarinyar ta koma tunda akwai spare ɗaki a ƙasa sai ta zauna anan"


  Daɗi ne sosai ya kama mummy har tana jin daɗi ita a tunanin ta asmau ce ta ɗau shawarar ta ta fara aikin da ta saka ta


 "to shike nan auta ai dama tun farko kai kaso hakan kana da mata har biyu amma ki ɗige a guda gudar ma mara quality" ɓata ransa yayi shi sam har yanzu be ga aibin badia ba da mummy kullum take cikin kushe ta



  Ko ma dai menene yanzu ba lkcn maganar badia a bane yanzu ta ƴar iskar yarinyar can ake yi



   Mummy shawara ta ci gaba da bashi akan yadda zai kula da asmau da kuma yadda asmaun zatai masa rana da kuma yadda zata kula shi fiye da badiar


 Jinta kawai yake yi amma yanzu ba lkcn wannan bane yanzu burin sa kawai yaga asmau a part ɗinsa ya koya mata hankali



 ******************


  Sai da na gama dinner tsab sannan na zuba aka raba aka kai wa kowa nashi sannan na ɗauki na mummy domin kai mata


  Ina shiga part ɗin ta tana zaune tana kallo nai sallama na jiye mata na tashi zan fita kenan sai ta kira ni


"asmau idan kin gama abinda kike yi ki tattara kayanki a yau ki koma part ɗin mijin ki da zama zaman naki a BQ ya ƙare, su ma ragowar ƴan uwan nakin na gaya musu daga yau koya ya dinga girkin sa kin dena mijin ki yace ki koma"



  Tsayawa nayi na saki baki kamar wata wawiya ina kallon ta me wannan yake nufi kenan in koma ɓangaren sabit wulaƙanci ke nan sunfari sunfari zan dinga kwasa gaskiya da sake bazan iya ba


 "mummy amma me yasa zan koma kin............" bata bari na ƙarasa ba ta hau yi min faɗa kamar zata ari baki, wai dama ni shegen taurin kai gare ni,


   Wata macen ce mijinta ya gayyace ta ta koma ɓangaren ta a matsayin matar sa kamar yadda kowacce mace take da matsayi amma ta ƙi kina nufin kin ta zama kenan a matsayin cook ai dama wataran dolr ne ya nemi ki koma ki karɓi girki



   Faɗa ta dinga min daga nan kuma ta hau faɗa min wai yadda mallaki zuciyar sabit cikin ruwan sanyi, sannan da yadda zan dinga masa biyayya tare da yin duk abinda ya sani



  Duk wani faɗan ta ya ƙare ne akan yadda zan farantawa ɗan ta sabit sam bata damu da halin da zan shiga ba ƙiri ƙiri na nuna mata bana ƙaunar komawa amma hakana sam be gamsar da ita ba itadai in koma in farantawa ɗanta





 Miƙewa nayi jikina a sanyaye na kama hanyar fita, sai naji mummy tana kiran me aikin ta wai ta raka ni ta taya ni haɗa kayana sannan ta raka ni ɗakina

"ai ba a bar amarya ta tare ita kaɗai ba ba ɗan rakiya"


  Wannan kalmar ta amarya tafi komai ƙona min rai lallai ma waya ga amarya


  Tas matar nan tasa na haɗe kayana na kwashe su ta taimaka min kwasar su sai part ɗin sabit abin haushi ma yana zaune a falon yana kallo



 Wani takaici ne ya ziyarce ni danaga mun shigo ya wani taso har da karɓar jakar hannuna na tare da yi mana welcome, ita kuma babar har wani washe baki take tana cewa


 "ga amarya nan na kawo maka ita Allah ya bada zaman lfy ya kawo ƙazantar ɗaki" nuna mana ɗakin yayi


 "ga ɗakin ta can sai ta shiga da kayan natan" tare muka shi da babar ni ko ƙala bance masa sai da taga na shiga na ajiye kayan nawa sannan tai min sai da safe ta fice


  Kayana na fara gyarawa inda duk na jera su a kwabar da nagani a ɗakin sannan sai kayan kwalliyata waɗanda na jera su a kan dreesing mirrow



 Sai dana ga na gama gyaran sannan na shiga toilet nai wanka na ɗauro alwala, sallah na gabatar ta ishsha sannan na kwanta



   Ina cikin addua naji an buɗe ƙofar ɗakin, gabana ne ya yanke ya faɗi, ko da dai fitilar ɗakin a kashe take amma ai nasan sabit ne


   Da sauri na miƙe na nemi wani zani da ke kusa da don in ɗaura, ban kai ga ɗauka ba naga hasken pitilar ɗakin ta kauraye ɗakin ya ɗau haske



  Ga wata ƴar mitsitsiyar rigar bacci da ke jiki na, saurin lalubar zanin nayi sannan ɓata rai tare da ce masa

"me ya kawo ka"


"zuwa nayi in karɓi haƙƙin ta ko ta ƙarfi ko ta tsiya na ga alamar innai sanya sai a kai wa wani abanza a wofi" gaba na ne ya yanke ya faɗi amma sai na dake don kar yaga ma tsorata ya rena min wayo


  
   Matsowa ya fara yi kusa dani gabana yana ƙara faɗuwa

"abinda kike burin kaiwa abdul ne nake son ruguza wa, tunda yanzu halak ɗina ne me zai hana in mori kayana tun kafin a kai wa wani banza, gwanda in karɓi kayana da hujja" fara matsawa nayi baya kashe fitilar yayi sai ɗakin ya ɗau duhu wanda hakan yasa na kasa gane a ina yake,



  Haƙuri na fara bashi na don Allah ya ƙyale ni wallahi wasa nake masa, jinshi nayi kusa da ni wannan ya ƙara firgita ni


  Ganin bashi da niyyar ƙyale ni yasa ni ma na fara kokawa da shi wallahi bazan bari yayi abinda yaga dama dani ba ai nia ina da ƙarfi



********************

   Wayyo Allah sabit ya cuce ya raba ni da budurcina ba lallami ba daɗin baki ba komai sai azaba da nuna ƙarfi in short zan iya cewa raping ɗina ma yayi


 Kuma abun takaici yana gamawa yayi wulli da ni sannan ya fice bayan rashin mutuncin da ɗiban albarka daya min, ina kwance nai rigingine ina ta kuka ba abinda nake ji sai tsabar raɗaɗi


Wayyo ni asmau wannan wace irin rayuwa ce mijina ya same ni budurwa sannan yai min wannan aika aikar amma sam a lamarin sa ba tausayawa wayyo sai yaushe wai zan samu me sona ne na gaskiya gashi abinda nake ta tattalin sa ina alfahari da shi yanzu babu kuma a wulaƙance ya ba wani daraja ko nuna mutunci ko wani abu gaskiya sabit ya gama cutata har abada








👩🏽‍🍳 *menu of d day* 👩🏽‍🍳


 *fatan doya, meat balls and mixed fruit juice*

*fatan doya*

 ```ingredients```


-doya
-wake
-attaruhu
-albasa
-kifi
-salt
-sugar
-mai



*method*

1) ki zuba mai a tukunya da albasa idan yayi zafi sai ki zuba jajjagen ki na attaruhu da albasa

2) idan ya sayu sai ki zuba ruwa da maggi da salt daga nan sai ki bar shi ya tafasa idan ya tafasa sai ki wanke waken ki ki zuba sannan ki rufe ki barshi ya dahu


3) ki fere doyar ki sannan, sai kin tabbatar da waken ya dahu sannan sai ki zuba doyar ki zuba sugar ki ƙara albasa sannan ki dagargaza soyayyan kifi a ciki ki rufe har dahu idan ya ɗauko dahuwa a rage masa wuta


*Meat balls*

```ingredients```


-nama
-kwai
-garin bushashen burodi
-maggi
-albasa
-attaruhu
-mai


*method*

1) ki dafa naman ki da albasa maggi, tafarnuwa idan ya dahu sai ki sauke sannan sai ki daka


2) bayan ya daku sai ki fasa masa kwai ɗaya sannan sai ki zuba daddakekken attaruhu da albasa da maggi in yana buƙata ki zuba garin burodi ki ɗaure shi sannan sai ki fara dunƙule wa kamar ƙwallo


3) ki fasa ƙwai a bowl daban sannan ki kaɗa shi, ki ɗora mai a wuta idan yayi zafi sai a ɗauko ƙwallon naman nan a saka shi a cikin garin burodi a jujjuya sannan a tsoma shi a kwai daga nan sai kasko a soya idan yayi brown sai a sauke



 *fruit salad*


```ingredients```

Seasonal fruits


*method*

1) a samu duk fruit ɗin da kike son amfani da shi amma wanda yake bozo ki wanke ki fere sannan a yanka shi sannan a markaɗa sai a tace a zuba sugar a saka a ƙanƙara a sha



  👩🏽‍🍳  *BON APPETIT*👩🏽‍🍳


  *ASMA'UN SABIT*
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)




   *A sakamakon ramadan dake matsowa sannan gashi ina fatan kammala littafin kafin lkcn in shaa Allah, nake so in cire menu ɗin da nake kawo wa sannan in ƙaɗa yawan read more, in shaa Allah kafin ramadan na kammala, sannan in shaa Allah zaku dinga samu 2pages each day saboda ao sauri a gama*



```masu comment ina gani ina jin daɗi da masu miƙo min addua Allah ya amsa mana baki ɗaya ya kuma biya mana buƙatun mu gabaɗaya```





*ALLAHUMMA BALLIGNA RAMADAN BIL IMAN*




   P⃗a⃗g⃗e⃗  16🌹









Ina kwance kamar wata matattaciya can dai dana ga ba sarki sai Allah sai na miƙe na shiga toilet na samu na ɗan gyara jikina na fito na kwanta


  Bacci ne yake son kwashe ni amma kuma sam bana jin ɗadin yanayin da nake ciki kyanta ace ina da pain killer dana shaa



    To cikin ikon Allah a hankali bacci ya soma kwasata kamar a mafarki naji ana yaye min mayafin dana rufa da shi bude idona nayi a hankali


 Kasancewar da duhu a ɗakin yasa na kasa gane wane amma kuma kamar ƙamshin turaren sabit yake


  Gabana ne ya ƙara faɗuwa kar dai sabit ne ya kuma dawo wa


"sabit don Allah kaji tsoron Allah ka ƙyale ni wallahi bana jin daɗi"


"da kina tsoron Allahn zaki dinga mu'amala da wani gardi da aure na akan ki, ai na faɗa maki sai kin gane kurenki"


   "wallahi wasa nake maka"


 "ni sa an wasan ki ne, kinsan a matsayin baiwa na ɗauke ki amma kike wasa da ubangidan ki, to ki sani baki da wani matsayi har yanzu a wajena daya wuce na baiwata wacce na siya don haka duk yadda naso yi da ke haka zanyi baki da wani zaɓi, ko an gaya miki ana wasa da ni ne, hankalina kike son jawowa gare ki ko, to albishinki kin samu amma sai kin rena kanki"

 
   Fuzge zanin jikin nawa yayi yai wulli da shi sannan ya hankaɗa ni, azabar da nake ji da ce ta kuma ƙaruwa inda na saki wani kuka me ciwo amma sai yace


"ki buɗe bakin ki kiyi da hujja ba me ceton ki"


   Banni da ƙarfin yin kokawa da shi don haka sai kawai na zuba wa sarautar Allah ido na miƙa wuya in ma kashe ni zaiyi a daren yau shike nan na ma huta



      Be ce min ƙala ba sannan be bi ta kaina ba yana gamawa ya fice hannuna ma kasa ɗagawa nayi balle in motsa ban da kuka ba abinda nake yi ga raɗaɗi da azaba kamar ana yankani da reza



  Kafin meye wannan zazzaɓi ya rufe ni ruf zanin gadon na ɗan jawo na rufe jikina da shi ina ta karkarwa a haka har wani wahallalen bacci yai gaba da ni




     Ina cikin bacci naji an sheƙa min ruwan sanyi akai na, da sauri na farka na buɗe ido na ɗan halak ɗin ne yana tsaye fuskar sa a murtuke yana ta kallona


"bana son ƙazanta, ina da rules don haka dole u have to abide by it, har ƙarfe 06:30am amma baki tashi ba balle kiyi wanka in ina da buƙata da safen nan are u expecting me in doshe ki a haka kina wannan yanayi oyaa maza go and wash up kizo ina jiranki a ɗakina"



   Gabana ne ya kuma faɗuwa wayyo Allah yau da wane bunsuru Allah ya haɗa ni, me nayi haka da sabit yake min wannan wulaƙancin na tashi zan miƙe naji jiri na ɗauka na ga jikina nawa da zazzaɓi sosai ga kuma azaba wallahi duk abinda za a yi ayau bazan kuma barin wannan mara imanin ƙara kusantata ba



     A hankali na miƙe ina tafiya a sanɗa sanɗa har naje na buɗe ƙofar parlon na mu na kama hanyar part ɗin isma'il gurin anty fannah gwanda in gudu daya kashe yanzu a halin da nake ciki in ya kuma kusantata ai sai dai wata ba ni ba


 ********************



   Yana ta window ɗin ɗakin sa ya hango ta tana nufar part ɗin isma'il tsab ya san wajen fannah zata, wani haushin ta ya ƙara ƙule shi lallai ma yarinyar nan nufin ta bata daddara ba ke nan



  Lallai wannan tabbas ne sai ya ƙara hukuntata tunda ta zama wacce bata da sirri sai ya sa gane shayi ruwa ne, ko da yake gwanda ma taje wajen fannar don ita fannar ta gano cewar asmaun yanzu ba budurwa bace ko ta faɗawa ɗan iskan yaron nan da ya liƙe mata



  Lallai ma kowane wannan abdul ɗin lallai ma ya rena shi matar sa wai ace wani ɗan iska yana shirin raba su ko be kula ta ba be sata a cikin lissafin sa ba ai matar sa ce mallakar sa don haka dole ta yi haƙuri da shi


 Amma ƴar iskar yarinyar nan wai har da wani cewa lkc suke jira su kasance tare, lallai ma asmaun nan, shi bama wannan ba wani irin abu ne a tattare da yarinyar wanda sam ko kaɗan badia batta da shi



  Shi a rayuwar su da badia sai su shafe sati ba abinda ya shiga tsakanin su amma ita kuma sau biyu a dare ɗaya kuma duk da haka jin shi yake yi kamar a wuni anayi



  Lallai wannan yarinyar daban take, ita iya girki gyara da komai da komai matsalar ta ɗaya baƙa ce, duk da dai ta sha gyara amma shi har yanzu bashi da ra'ayin baƙar mace


  Daga dukkan alamu sha'awace take jan shi zuwa yarinyar nan daya kau da ita zan yi disposing yarinyar fatan shi ma kafin badia ta dawo ya kau da duk wata sha'awar sa akan ta kije ki huta maa haɗu da daddare ya faɗa yana rufe window tare da faɗawa toilet don yin wanka



 *******************


  A ƙofar part ɗin fannah ta fara knocking ta ɗan jima kafin anty fannah ta zo ta buɗe ƙofar cike da mamakin wa ye yake mata wannan knocking ɗin da sassafe



   Ganin asmau a cikin halinda take ya saka ta yi salati sannan ta ruƙo hannun asmaun wanda yai zafi rau da shi


"me ya same ki" ta faɗa ta ƙoƙarin zaunar da ita akan kujera, cikin kuka asmaun ta amsa

"sabit ne ya........." anty fannah bata bari ta ƙarasa ba ta toshe mata baki


"mara tarbiyya ce ke fallasa abinda ya wakana tsakanin ta da mijinta, amma me ya sa har ya kai ga haka, ince dai gardama kikai masa don nasan ki da taurin kai barin in haɗa miki ruwan wanka ki gasa jikin ki" ta faɗa tana shige ɗakin ta don haɗa ruwa



  Ajiyar zuciya asmaun tayi tare da ɗan kwanciya a kan sofa ɗin tana ɗan maida numfashi kaɗan kaɗan

 Fannah bata daɗe ba sai gata ta dawo,

"tashi muje na haɗa miki ruwan ki samu kiyi wanka ko kya ji daɗin jikin ki"  miƙewa nayi ina tafiya da ƙyar tana bina abaya tana kallon yadda nake tafiya sai tace


 "wai garin ƙaƙa akai haka asmau kokawa kukayi yai miki haka, waya faɗa miki anawa namiji musu ne a gado ai kawai daya doso ki ko kibi yarima ku sha kiɗa ko ki sakar masa linzami yayi yadda yake so


   Gaskiya baki kyauta ba shima sabit ɗin har da shi wannan abu sai kace be san yadda abin yake ba, kar ki kuma yi masa gardama ki zubawa sarautar Allah ido wallahi ko ba daɗe ko ba jima sai sabit ya durƙusa miki ai ba ƙaramin haɗi kika sha a garin mu ba


  Laƙani ne wanda duk ya kuskura ya fara ɗanɗana wa to shikenan shi kuma da haƙura da mace sai dai wani ba shi ba"


 

  Allah ma ya sauwaƙe min wai ni da sabit har abada mutumin da ko a ƙafa aka daura min sai na tsinke na gudu balle wai ace na zauna amatsayin matar sa



  Muka ƙarasa toilet ɗin ta cika bath da ruwan zafi sai wani ƙamshi yake tashi na misk


"Maza shiga ki gasa jikin ki kuma ki tabbatar kin daɗe sosai a ruwan don ya ratsa ki sosai amma kafin ki shiga ki fara yin wanka don kar dauɗar ƙafar ki ta ɓata ruwa" tana gama faɗa ta fita


  Wanka na soma yi, sai yanzu ma naji yadda na fulani na suke ashe suma sun sha massage dai zafi suke min


  A hankali na wanke jikin nawa sannan na shiga bath ɗin, zama na keda wuya wani raɗaɗi da azaba daya shige ni ban san lkcn da ƙwalla ƙara ba sannan na miƙe da sauri



 Muryar anty fannah naji


"kar ki sake ki fito yana miki zafin haka zaki shiga a hakan ne zaki warke in baki gasa kanki ba baza ki taɓa warke wa ba kuma sabit ba zai daina kawo miki ziyara ba kema kin sani haka kawai ki lalace a banza maza ki shiga ki gyara kanki in ba haka ba in shigo in miki da kaina"




Ƙara shiga nayi ina kuka kamar ana tsaga min wurin haka nake ji, dama haka mata suke ji ko kuma ni kaɗaice don na haɗu da mara tausayi
\

 Wallahi sabit zai gane bashida wayo ni da part ɗin sa hayhata hayhata, sai da ruwan ya ɗan fara sararawa sannan na fara jin daɗin jikina



  Na daɗe sosai a toilet ɗin sannan na fito inda na tarar da anty fannah ta haɗa min tea me kauri sai pepper soup



  Na zauna na karya sannan na sha magani daga nan sai bacci,



 *******************


 Abin ya ba fannah mamaki yadda sabit yai wa asma'u aika aikar nan amma sam be bi ta kanta ba gaskiya be kyauta ba duk abinda asmaun tai masa tai ai sai ya ɗauka duk a cikin yarinta ne



  Ɗaukar wayar ta tayi ta kira shi ringing ɗaya ya ɗauka, yana ɗaga wayar yace


"yayata ina patient ɗin taki take" wannan maganar ta bawa fannah haushi


"ka damu da ita ne da ka damu da ita da ba kai da kanka zakai jinyar ba"


 "wallahi babu yadda banyi da ita ba akan ta bari in gasa ta amma ta ƙi wai kunya take ji ita wurinki zata zo shine nace to ta tafi nasan zata sha gyara fiye da nawa"


 "au ai na ɗauka ƙyale ta kayi tayi ta kanta tunda kai ka gama biyan buƙatunka"


"haba yayata ni na isa ƙanwar taki ai ƴar baiwa ce, ni na isa in wulaƙanta ƴar baiwa kawai dai a kular min da ita zuwa dare inna dawo zan zo in ɗauke ta" ya faɗa cike da nishaɗi


"a a ba sai ma kazo ba tana farkawa anji ma zan makda ita ɗakin ta saboda ayi shirin tarar ango, amma don Allah sabit a dinga saurara mata"


 "ba komai yayata yadda kika ce ɗin hakan za ayi" sukai sallama


  Sabit wani daɗi ne yaka ƙara shigar zuciyar sa ganin yadda asmaun zata dawo da kanta ba tare da yaje ya bada kansa ba don shi yanzu zuwa ma wai ya dawo da asmau wani tashin hankali ne a wajen sa in shaa Allah kafin badia ta dawo duk wani daya ji a game da ita ya kau amma kuma anya zai iya 🤔 shine abinda yake tambayar kansa



  Ba komai ko bazai iya ba sai kawai ya mai da ita standby duk lkcn da badiar tayi balaguro ga standby ɗin sa always available murmushin mugunta yayi daya tuno da gurasar da zai tarar yau inya koma gida


  Lallai kam ya yadda da aka ce ko wacce mace da baiwar da akayi mata wata Allah ya bata kyau wata kuma Allah ya bata wani abun to amma ita asmaun matsalar sa da ita shine baƙin ta duk da dai ya ragu yanzu ta koma chocolate amma shi gaskiya har yanzu taste ɗin sa na farar mace be canza ba


*******************



Sai bayan azahar sannan ta farka ras taji ta kamar ba abinda ya faru da ita, abinci taci sannan anty fannah ta kuma bata wani papper soup ta shaa sqm bashi da daɗi ga wani uban gari a cikil amma haka ta sha


   Bayan ta gama kuma anty fannah ta kuma kawo mata nono da wani garin magani a ciki


 "wai anty duk wannan abun da nake sha na menene" na tambaya don wallahi inda irin maganin matan da naji ana faɗa ne wai don ya ƙarawa mace taste bazan sha ba taste ɗin dana wofi sabit ɗin zan wa taste Allqh ya sauwaƙe mi



  "Maganine maza ki shanye" ta amsa min


 "maganin menene ba dai maganin matan nan bane ba kooo" na tambaye ta fuskata a ɓace, kallon yadda na ɓata rai tayi sai ta ƙyalƙyale da dariya wanda ni kuma hakan ya sani kyakkyaɓe fuskar kamar zanyi kuka


"wallahi anti indai shine bazan sha ba mutumin nan so yake yi ya kashe ni kina gani fa abinda yai min amma wai ki ƙara ɗura min abinda zai sa shi ya kuma kusantata wallahi ban yadda ba ni da shi hayhata hayhata" hawaye ne shar shar shar suka dinga shatata a fuska ta


 "to kuma meye na kukan ce miki nayi shine, maganine fa da zai sa ki warke da wuri, kuma kika sha wannan maganin idan sabit ya kusance ki sau ɗaya bazai kuma ba saboda lalata mace yake yi" ta faɗa fuskar ta ba alamar wasa


 Ɗauka nayi na kwankwaɗe tas har da lashe cup ɗin sannan na sha ruwa


Rigima ce sabuwa ta faru tsakanin mu da anty fannah lkcn da ta nemi in koma ɗakina


  Kuka na saka nace mata wallahi bazan koma ba, kashe ni zeni yi, tsayawa tayi tana kallo na ina kuka,


 "me kenan kike nufi da bazaki koma ɗakin ki ba, a nan zaki zauna in kai nawa mijin ina"


 "ni de gaskiya anti bazan koma wallahi kashe ni zeyi yace sai na gane kurena, wallahi bazan koma ba"


  Zama tayi kusa da ni tare da riƙe min hannuna tana lallashi na sai da na ɗan tsagaita kukan nawa sannan tace min


 "haba asmau sai da  nace miki in baki koma wajen sabit ba bazai taɓa ƙyale ki ba, wannan maganin da kika sha shine zai kore miki sabit, yanzu in baki koma ba wallahi sai kin rena kanki gwanda salin alin ki koma tunda ɗumi ɗumin maganin ai miki aiki kafin ya salance"



   Jikina ne yayi sanyi wato sai dai na koma sannan sabit zai ƙyale ni, gabaɗaya ni fuskar sabit ma bana son gani ballr wani abu ya shiga tsakanin mu amma wai yanzu ana cewa in koma ni ma'u naga ta kaina



   Da wayon ta da dabara ta sakani a gaba muka koma, bata bar part ɗin namun ba sai da mukai girki tare muka gyara sannan tasa ni yin wanka na shirya cikin wani english wears masu jikin zebra


  Rigar armless ce amma tana da tsayi don har ƙasa ta kaimin sai dai ta ɗame ni sosai, ni wallahi duk kunya ma nake ji wai sabit ya zo ya ganni a haka ai sai ya ɗauka ko dan shi nayi



   06 :00pm dai dai ya shigo lkcn muna zaune a falo muna hira, kallo ɗaya ya min ya ɗauke kansa sannan ya koma kan antƴ fannah yace mata


"ashe kuna nan na ɗauka a wajen ki zan same ku"

"ko ɗaya tun ɗazu muka dawo gashi har munyi girki mun gyara ko'ina ma"


 "lallai komai yayi kyau bari inje in wanka sai in sauko koo" ya faɗa yana shige don hawa sama


"tashi ki bishi mana" inji anty fannah ɓata fuska ta nayi kamar ba zani ba, sai da naga ta haɗe girar sama data ƙasa sannan na tashi



   Saman na hau da sanɗa sai kace me shirin shiga ɗaki yin sata, a hankali na buɗe ƙofar ɗakin nasa wacce ƴar iskar ƙofar ta yi ƙara ƙiiiiiiiiiiiiiii



   Yana tsaye a gaban fridge ɗin sa daga gani ruwa yake sha juyowa yayi fuskar nan tashi ba annuri

"me ya kawo ki ɗak..........." ban bari ma ya ƙarasa ba na juya tare da doka masa ƙofar ɗakin don yasan baya gabana



    Ina sauko wa na tarar da anty fannah bata falon don haka saina jera mishi Abincin shi, sannan na wuce ɗakina don naji an fara kiran sallah magariba



  Ban fito falon ba sai 09 :30pm lkcn na san ya gama cin abinci na zo na kwashe kayan, yana falon a zaune yana kallo ben ce masa ba shima haka,


Sai da na gama komai sannan na koma ɗakin, lalubar mukullun ɗakin nayi na rufe ƙofa sannan na nemi jeans na saka tare da wata doguwar riga ƙirar morocco irin masu nauyin nan na maka ta sannan nai addua ana kwantaa



    Ina cikin bacci naji kamar ana yanka min kayan jikina, farkawa nayi inda mukai ido huɗu da sabit da kuma scissors ⚔ a  hannun sa


  A firgice na miƙe inda yaga ya doso ni da scissors kamar wanda zai chaka min, hankalina a tashe na ce masa


 "don Allah bari incire kayan"


 Tsaywa nayi wanda ni kuma jiki na ɓark na cire kayan nawa ina cewa kayi ka gama daga yau dai an bar wajen


********************



   Duk yadda nake tunanin sabit zai ƙyale ni ba haka na gani ba sai ma wani ƙara liƙe min yake yi kamar chewing gum abinda ya fi ƙona min rak da shi shine wulaƙancin da yakr min kamar ba ƴar adam ba



  Kullum cikin moriyata yake ba dare ba rana amma sam kamar wanda ya samu jaka haka yake ba lallami ba komai da sai dai tsabar gadara da nuna isa



 Sam bana jin daɗin zama da sabit don har yanzu na kasa sabawa da shi kullum cikin fargaba nake dana ganshi sai gabana ya faɗi


   Rannan ya dawo da yamma lkcn ina kitchen ina girki sam banji shigowar shi ba kawai sai fitowa nayi kawai na ganshi gabana ne yai mugun faɗuwa ban san lkcn dana saki plate ɗin da ke hannuna ya faɗi ƙasa ba tare da furta kalmar


*innalillahi wa inna ilaihi raji'un* wannan kalmar ce ta katse masa kallo ya juyo gare ni


"dodo kika gani ko me, da zaki dinga gani na kina jin tsoro kamar wani aljani ko meye" tasowa yayi ya taho inda nake wacce ni kuma nake ta komawa baya har na haɗu da garun kitchen ɗin



  Ƙafarsa ya saka ya take min tawa ƙafar wanda zafin hakan ya sani sakin ƙara, ba ankara ba naji lips ɗin sa a nawa yana tsotsa kamar wanda yake da niyyar cire mins



  Hawaye ne kawai yake bin fuska ta, don azaba hankaɗa ni yayi ƙasa inda na kwanta ruf da yaga min kayan jikina ya somayi kamar wani taɓɓaɓe



  Kuka na dinga masa ina roƙar sa akan ya ƙyale ni ko ma dai me zai min ya min a mutunce amma mutumin nan kamar kunne sa a toshe yake



  Haka ya wulaƙanta ni kamar wata karuwa mara class,  ɗurkusawa nayi a ƙasan kitchen ɗin ina ta kuka, ba abinda ya fi ƙona min rai kamar wannan wulaƙancin da sabit yake min



  Tashi nayi na jawo skirt ɗina wanda yai fata fata na ɗan samu na kara shi a jikina sannan na wuce ɗakina ina wanka ina hawaye



  Kai wallahi wannan wulaƙanci ya fara isata gaskiya dole ne ayi wacce za a ayi amma a gaskiya na gaji



  Mijin da ke aure na ya mai da ni baiwar sa kamar siyata yayi kamar banni da wata ƙima ko daraja a wajen sa, gaskiya na zo ƙarshe dole ne asan abinda za a yi ina wanka ina ƙara jadda hakan
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)




 🤲🏻 *ALLAHUMMA BALIGNA RAMADAN BIL IMAN*🤲🏻




   P⃗a⃗g⃗e⃗  17🌹






 Sai dana gama wanka na tsab na fito ɗakina na ɗauki jakata na fara haɗa kayana ina hawaye yau dole ne in barwa sabit gidan nan



   Ban dan ko nawa ne kuɗi na a wajen mummy ba amma dole yau zan bar gidan nan ko da kuwa tace baza ta bani kuɗina ba na tafi inje gidan abincin hjy munnira ina mata aiki inna samu kuɗin in koma garin mu amma gaskiya wulaƙanci yayi yawa sosai na faɗa ina hawaye



   Ƙarar buɗe ƙofar ɗakin nawa naji ko ban kalli ƙofar ba nasan cewar sabit ne don kuwa ƙamshi turaren sa kawai nake ji sam ban kalli inda yake ba na ci gaba da abinda nakeyi


"ke meye wannan kike yin haka nan"


"tafiya zan yi ai ko aure ma sai da ra'ayi ake zama to na bincika har ƙasan zuciyata banni da ra'ayin zama da kai bana ƙaunar ban taɓa son ka ba kamar yadda kake ikirarin hakan to meye dalilin da zai sa mu ci gaba da zama bayan bama ƙaunar juna"



  Ina magana hawaye na zuba daga ido na sakin baki yayi yana kallona daga dukkan alamu be ɗauka zan masa haka ba


 "da izinin wa zaki fita ko ita fannar da zakije wajen ta barin ki zama zatayi"


"ban ma tafi ba kenan in dai a waken anty fannah zan zauna, garin mu zan tafi aure tsakanina da kai babu shi ka bani takarda ta an gama show ɗin daga yanzu"


 "daɗin abindai sakin a hannuna yake kuma bazan sake ki ba har sai lkcn da na ga dama, wai ke asmau me kike so ne meye bana baki saboda tsabar rashin godiyar Allah da rashin gode masa shine zaki tafi ko ki tafin mu gani in hakan ne zai sani ƙara miki matsayin"



    Ficewa yayi daga ɗakin ni kuma naci gaba da haɗa kayana, sai da na gama haɗa komai na sannan na ɗauko jaka ta na fito


  Ko kaɗan banji wani abu ba wai zqn bar gidan duk da dai bam san wace irin rayuwa zanyi a azoren ba amma ni  a ganina gwanda in tafi da wannan cin zarafin da sabit yake min



   A garƙame na tarar da ƙofar fita daga falon, an rufe da mukulli daga waje jijjiga ƙofar nq fara yi tare da dukan ta ko ta buɗe duk da dai nasan a banza nake amma kuma ance baka fidda rai da tsammani



   Sai da na gaji da dukan ƙofar sannan na sulale ƙasa na zauna ina kuka na, alamar buɗe ƙofar naji nasan sabit ne zai shigo muciya na shiga kitchen na ɗauko da niyyar yana buɗewa in muƙa masa sannan in tsere


   Anty fannah ce ta shigo ganina da muciya a hannu ya sata ɓata rai tare da ƙwacewa ta yar sannan ta ja hannuna zuwa ɗakin na

"me ye haka sai kace wata matar ƙauye, kamar wacce bata da ilimi ina karatun da nake koya miki kar dai kice ba ɗauka kike ba kawai zuba ta nake yi kamar ƴaƴan kanya"



  Bayan ta sabit ne ya shigo, faɗa ta shiga min wai sabit ya kai mata ƙarata akan ina mishi rashin kunya, sakin baki nayi ina kallon mutumin nan wanda yake ta danne danne sa a wayar sa kamar baya wurin


   "Wallahi anty ba haka bane ƙar........" ban ƙarasa ba naji ta toshe min baki


"kar ma ki ƙaryata mijinki da ido na na gani kin ɗauko muciya zaki doke masa kai, in banda shima sabit ɗin me haƙurine wane namijin ne zai yadda da irin wannan cin kashin"



   Fashe mata nayi da kuka ina rants rantse na wanda sam kamar ma bata yadda ba don bata nuna alamar yadda ba


 Sabit da ke gefe wanda tunda aka fara bece komai ba sai yanzu


"anty ni fa bana kawo ki bane don kiyi mata faɗa ba kawai so nake yi ki ja mata kunne akan abinda take yi be dace ba"


   "yi haƙuri sabit zan mata faɗa tashi ka tafiyar ka uzurinka" miƙewa yayi tare da zira hannu a aljihu sa sannan ya fice, bin bayan shi nayi da harara



    "au ko a gaban nawa bazaki bari yi masa rashin kunyar ba, haba asmau wallahi duk abinda kike yi Allah dai  yana kallon ki" ƙara fashe mata nayi da kuka nan na hau labarta mata duk zaman da muke yi da shi bata katse ni ba sannan sam bata nuna alamar tausayawa ba ko wani abu


 Sai da nagama tsab sannan tace min in share hawaye na, tas na goge fuskata ta, na nutsa sannan ta kalle ni tace min


 "Asma'u shawara ɗaya zan baki ko ki ƙi ko ki sa amma ɗaya ce ba ƙari, duk wannan abun da kika ga sabit yana yi har yanzu be san meye so bane kawai dai yana bin sahun ƙyal ƙyal banza ne


  In kina son sanin ainihin waye sabit me sabit yake so kamata yayi ki zauna ki karance shi ki karanci aban da yake so kafin ki fara judging ɗin sa


  Har ga Allah ina sonki da sabit kuma duk wani abunda nasan zai ƙara ku
kusanta da shi shi nake miki amma na lura sam ke ba haka kike so ba kin fison tafiya ko" ta tambaya da alamar tambaya


 Gyaɗa mata kai nayi alamar ni na fison tafiyar

 "to shike nan duk yadda kike so hakan za ai miki yanzu abinda da so da ke shine ki kwantar da hankali sosai akan sabit duk abinda yake so kiyi masa sai a lkcn da ya saba da ke da duk wani abu naki sai ki tsiri rama abinda yai miki tas ki rama kar ki yadda kice zaki raga masa daga lkcn idan yaga abin ya mishi yawa sai kiga ya sake ki salin alin ko ya kika ce"



  Tsayawa nayi ina tunani shin anya kuwa wannan mafita ce ko kuma wani sabon salon ƙara jawo sabit gare ni ne, ganin ban amsa ba ya sa ta miƙewa


"to bari in tafi tunda na baki shawara amma naga kamar bata miki ba"

  Hannun ta na kamo sannan nace mata

"ba haka bane kawai dai ni bana son abinda zai sake haɗa ni ne da shi"


"to shike nan duk abinda yai miki ya tashi a banza kenan, ai in baki koyi rama abinda ɗa namiji yai miki ba daga farko to ko kin ƙara auren ma ƙila abinda zaki tarar kenan amma kin ga inkin saba ba abinda zai zame miki sabo"



   Shiru nayi ina tunani to wai ramuwar dole ce na faɗa a zuciyata ni fa sam abinda ya danganci sabit nr bana so


 "kinga in shawara ta bata yi ba na yi gaba sai kine mi me baki shawara nan gaba" ganin cewar in ta tafi shikenan a ina zan samu wanda zai haɗa ni da wanda yake son irin na


  Don haka dai na riƙe mata hannu tare da cewa

"na haƙura amma wallahi saboda ke" shafamin gefen fuska ta tayi sannan tace


 "yauwa ƴar albarka" zama tayi ta dinga bani saƙwanni ta yadda zan kama sabit jinta kawai nake yi amma abu guda banjin zan iya amma kasancewar bana son tace na ƙi jin maganar ta yasa kawai sai gyaɗa mata kai nake yi kamar ina ji ta gama zancen ta sannan tai min sallama ta fice nice har da rakata bakin ƙofa sannan mukai sallama


 ********************


 Tun daga lckn na koma bana yi wa sabit musu duk abinda yake so ina mishi amma fa babu batun sakin jiki kadaran de kadahan



   Rannan da safe yana zaune akan dining table yana break fast sai ga call, yadda naga naga ya ɓata fuskar sa sai na ɗauka ko wani wanda yake damun sa ne amma ga mamaki na sai naji yace


"only ya dubai" ban san me tace masa nadai ji ya amsa mata da



"only ki yi zamanki ku gama siyayyar ku a nitse ni sam ba a takure nake ba am taking really good care of myself don haka kar ki damu"


  Shiru yayi inda ta ci gaba da mai masa da martani

"only ba komai ko wata ɗaya zaku ƙara is ok by mee, ni yanzu am really busy at d office inna fita tun safe karfe 06 : 00am  bana dawowa sai 12 :00 na dare don haka am really busy gwanda kawai ki nutsu kiyi shopping ɗinki"


  Wayaga zuƙi ta malle ina kitchen ina iya jiyo sa yana ta zankaɗawa matar sa gidoga 🤣 wai office tun safe sai yamma mutumin da sai kusan 09 :00am yake fita kuma duk inda  06 :00 tayi na yamma ya dawo amma shine yake shararowa matar sa wannan sharhi kai gaskiya wasu mazan ma sai a slow da lamarin su



  Ina jin sa ya gama lallashin ta akan kar ta dawo ko ta gama shopping ɗin ta zauna ta huta, har da wani cewa ko kin gama ki zauna ki huta a can, wato ga banza ka samu ko to wallahi sai na san yadda na samu number badiar na saka ta ta dawo don in samu in huta



  Sai da suka gama wayar sannan ya ajiye wayar ya ƙarasa cin abincin sa, ya na gama wa ya kirani inzo in kwashe kayan



   Sama ya hau inda ni kuma na fara kwashe kayan, har na zo wuce ta ta kusa tv set ɗin falon sai na hango wayar tasan tana chargy da sauri na na je na ajiye kayan sannan na zo na ɗauka na rubutawa badiar text


```only nayi missing ɗinki dana ce miki ki zauna wallahi am joking pls ki yi sauri ki dawo as soon as possible i miss u a lot```


  Nai mata sending ina shirin deleting naji foot steps ɗin sa don haka sai kawai na kashe wayar na mayar na ajiye rigima ba uban wanda ta kashe barin ma rigimata da sabit mun saba




Yana saukowa ya ɗauki wayar ya fice, farin ciki ne ya rufe nk Allah dai yasa message ɗin ya shiga


  Be daɗe da fita ba sai gashi ya dawo a fusace daga ganin sa nai kitchen a gujr na ɗauko muciya, gadan gadan ya nufo ni fuskar nan tasa a murtike kamar an masa mutuwa


 "wallahi idan ka ƙaraso kusa da ni sai na muƙa maka ita" tsayawa yayi ya kallo muciyar da ke hannun sannan sai ya ja burki


"uban wa yace ki taɓa min wayata balle har ki min text"


"meye text" na tamyaba cike da renin sense

"baki ma san meye text ba, da kika ɗauka kikai wa badia text wai ina missing ɗin ta ta dawo zaki ce baki san text ba"


 "ni tunda nake ban taɓa riƙe waya ba tayaya za a yi in san yadda ake yin text" na kuma bashi amsa


"to ni da waye a gidan da har akai wa badia text amma baki gani ba bayan anan na ajiye wayar na hau sama kuma lkcn da na hau sama akai mata text ɗin"


 "oho ni dai ban sani ba don ba taɓa riƙe wayar nayi ba balle in iya wani abu wai shi text" duk wannan maganar da muke yi muciyata na ɗage daya matso kusa da ni in muƙa masa


  Kallo na ya tsaya yana yi tabbas da badan muciyar nan ba da tuni ya fara muguntar tasa, amma babu halin hakan tunda yanzu am armed 🤺



    Ƙwafa yayi sannan yace

"zaki gane kuren ki" a zuciyara nace oho dai nasan ta inda zaka rama kuma am already immune to it, na riga na saba yanzu bana jin komai wani lkcn ma sai nishaɗi 🙈


   Juyawa yayi ya fice inda na bi bayan sa da gwalo sam ban san zai waigo ba sai gashi mun yi ido huɗu da shi ina masa, shan kunu nayi na ƙara ɗaga muciyata ƙwafa ya kuma yi


"wallahi sai kin rena kanki" ya faɗa yana ficewa, ina jin shi yana waya da badia inda yake cewa


 "yanzu only kin riga kin yi booking ba za ku iya canceling flight ɗin ba ki ƙara hutawa" ban san me tace masa ba na dai ji yana ce mata ok safe jorney



  Ranar wuni nai ina murna badia zata dawo in huta da jarabar wannan jarababben nata ta dawo can suje su ƙarata ni ma in samu in sakata in wala



   Ina gama abinda nake yi na shiga part ɗin anty fannah na bata lbr ina ta dariya ita ma dariyar ta taya ni sai da muka gama sannan tace


 " bari in baki wani haɗi ki shaa, idan kika shaa badia tana dawo wa idan ya kwana a ɗakin zai manta da ke saboda salanta mace yake"


  Da murnata na ce mata tooo nice har da taya ta haɗa shi da zuma a ke sha sai tsimi wanda ta haɗa tace nata ne shi sam ban sha shi ba haka kurum ina neman hanyar gujewa sabit me zai kaini shan wani tsimi *ƙila ma na mmn fareeda ne sunan shi maƙale mata*





Da yamma kuma ta haɗa min wani shayi mara daɗi wai in shanye na tambaya ta ko na menene haɗe rai tayi tace min

"kin taɓa jin ance shayi yana maganin mata barin ma baƙi kawai ki sha" ɗaga takashin kofin nayi nayi ɗaɗɗake shi sam ba daɗi


  Sai farfesu da ta haɗa mana muka sha shima sam ba wani daɗi gare shi ba, anty fannah a wannan lkcn ta iya girki amma wani lkcn in tai maka girki sai dai kawai aci da haƙuri barin ma ace pepper soup ne sam baya daɗi wani spice take sakawa me gari gari wai haka ake yi a garin su ni sam baya min daɗi


 Tare mukai dinner da ita anan part ɗin nata kasancewar shima isma'il ɗin ana part ɗin ta yake


   Sai yamma lis sannan na tafi da guzurin abinci na, ina shiga toilet na faɗa nai wanka na ɗauro alwalar sallah magariba



   Yau gogan be dawo da wuri don har akai magariba sam banji ɗuriyar saba, sai can kusan tara sannan naji shigowar sa



  Ban bi ta kansa ba don komai na buƙata na tanadar masa, bashi ga shigo ɗakin nawa ba sai ƙarfe  10 :30 na dare gashi ya hanani bacci indai br shigo ba haka na zauna ina ta gyangyaɗi



   Ranar munyi wani abu wai shi till dawn 🤣 daɗin abun i was enjoying myself all along 💃🏼💃🏼💃🏼


  A ɗakin ya ƙarasa baccin sa bayan ya tasa ƙeya ta toilet munyi wanka tare, Allah sabit ɗin nan yana son ɓata min tarbiyya ta



   Wajen ƙarfe shida ya fita ɗauko badia kamar sallah haka nake jin kaina, ko da ya fita sai daya karta min warning ɗin kar badia ta sake ta dawo ban gama girki ba sannan yace min


"idan kika sake naji wani abu daga gare ki zaki ga yadda zan miki" yana ficewa nai tsalle tare da cewa


*FREEEEDOM* 💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼


 ********************



    Yana tafe a mota yana tunani abinda asmau tai masa sam be ji daɗi ba, wannan ƴar iskar yarinyar sam ban gama mission ɗina akan ta ba ta ruguza min budget ɗina yanzu in badia ta dawo tayaya za ayi in samu sake wa da ita


  Ga wani shegen  abu a tattare da ita da sam mutum baya gajiya da ita, wani abun da ke birgeshi da ita shine duk da taurin kanta amma yakan juyata son ranshi


  Kamar kissing sam badia bata son kissing sai tace wai ƙazantar hakan take gani, ita kuwa wannan sarkin taurin kan yaga har ta fara responding sannan wanka tare



   Wannan no go area ne a wajen badia wankan ma a ɗakin shi sam bata yi balle yayi joining ɗin ta sai ta tafi ɗakin ta ta saka key a toilet sannan take wanka


 Amma asmau tuni ta saba da wanka da shi duk da dai kullum kamar bata so amma shi hakan sam be dame shi ba


  Sai kuma bacci tare wannan ma haram ne ga badia yana son yaga yana kwance matar shi a jikin sa amma sam badia bata so wai bata son ya farka ya ganta ba makeup


  Amma ita wannan sam makeup ɗin be dame ta ba ita dai tayi wanka ta saka turaren ta me shegen tayar masa da hankali


Gaskiya tsakanin su akwai banbanci sosai amma matsalar asmau ɗaya ce baƙa ce shi sam har yanzu bashi da taste akan baƙar mace balle har ace zata haifa masa baƙaƙen ƴaƴa subhanalli ai da anyi yaƙi da shi ina shi ina baƙaƙen ƴaƴa


 Ai dole ne ma ya ɗau mataki akan asmau don kar ta haihu shi sai yanzu ma ya kawo maganar cikin ashe zata iya samun ciki gaskiya dole ne ya ɗau precaution akan asmau haka kurum kar ta haɗa shi da baƙaƙen ƴaƴa ta cuce shi ya rasa yadda zai yi da su



  Da wannan tunanin ya ƙarasa airport ɗin inda ya tarar jirgin nasu haɗ ya sauka, sam ba kamar da ba yadda idan badia ta dawo yake rawar ƙafa yanzu kawai sai yaji wani iri amma sai ya dake yai mata welcome kamar yadda yake mata adaa sannan suka kama hanyar gida 🚕
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)




 🤲🏻 *ALLAHUMMA BALIGNA RAMADAN BIL IMAN*🤲🏻




   P⃗a⃗g⃗e⃗  18🌹










Kafin ma su ƙaraso na gama komai na gyara gidan tsab, banji tsayuwar motar su ba kasancewar parking lot ɗin yana can wajen gidan



 Sallamar su kawai naji inda na tafi da gudu naje na rungume badia tare da cewa

"anty badia sannu da zuwa wallahi nayi bala'in murnar dawo warki" abin mamaki ya bata inda take ta ƙoƙari yakice ni daga jikin ta


 Bayan ta ɓanɓareni sai ta kai duban ta ga sabit

" *SD* yarinyar nan lfyr ta ƙalau kuwa" be kai ga amsa mata ba na ƙara ruƙunƙume ta


 "wallahi anty badia ba komai kawai dai nai murnar dawowar kine" ina kallon sabit yana ta doka min harara sai na share shi


 "yanzu tunda kin dawo sai ki karɓi duty ɗin kula da mijinki in huta da........." ban kai da ƙarasawa ba naji sabit ya toshe min baki tare da hankaɗa ni cikin falon


"wuce ki ba mutane wuri da shegen surutun ki faɗi ba a tambaye ki ba"


" *SD* wane duty ne kuma asmaun take magana na kula da kai"


 Ɓata rai yayi sannan yace

"wa yake bani abinci in ba ita ba, ya yake kula da gidan duk ai itace take yi, muje only na san kin gaji ne da wannan tafiyar da kika"



    Jan hannunta yayi suka shige ni kuma na tsaya ina kallon wannan wawiyar tunda kika ji nace duty ai sai ki harbo jirgin



   Sai da suka jima sosai a sama sannan suka sauko kowanne su yai wanka ya canza kaya a zuciyata nace tabbas me wuri ya zo me tabarma dole ya naɗe


   Yanayin fuskar sabit sam be nuna wani alamar farin ciki ba ko wani abu,



 ba kadaran kadahan dai kamar ba wani abun da ya shiga tsakanin su ko me yasa sam ba haka yake yi ba in ya kwana a ɗakina da fara'ar sa da nishaɗin sa yake fitowa


   Ko ma dai menene su suka sani sunfi kusa can ta matse musu ni dai na samu freedom


  Ranar da wuri na gama dinner naje na jera musu bayan sun gama na kwashi, wanka naje nayi na samu na kwanta, nai juyi sosai akan gadon kamar ranar na fara kwanciya akan gado



   Wani lafiyayyan bacci ne yayi awan gaba da ni, ina cikin mafarkina me daɗi kawai naji an ɗaka min duka


"bana ce miki kar ki kwanta banzo ba, maza wuce kije kiyi brush ki sake wanka kizo ina jiranki"


  " Kai mafarki nake yi koo" na faɗa, ranƙwashi naji a tsakiyar kaina


"wannan ma a mafarkin kika ji shi"

  Kallon shi nayi sannan nace


"wallahi ko ka fitar min daga ɗaki ko in maka ihi ai yanzu matar ka ta dawo"


"Allah ya baki sa ar ihun baza ta jiba don na ɗura mata maganin bacci, wai zaki tashi ki gyara jikin ki ko musu zaki zauna kina min"


 Banni da bakin magana haka na miƙe na shige toilet ina cikin wankan ne ma sai gashi tare muka yi kamar yadda yake so sannan ya nannaɗo ni a towel na fito kamar yadda nake gani a littafi

  


  ƙwiiiii wasa nake yi da ƙafa ta na tako ko ta kaina ma be biba, a ɗakin ya kwana, nai mamakin da ko a jikin sa haka ya kwantar da ni a jikin sa har yayi bacci


 Ko cikin baccin idan nai birgima na koma ƙarshen gadon sai ya jawo ni jikin sa mun cigaba da baccin mu,


  Da asubar fari ya bar ɗakin a zuciyata nace an dai ji kunya


 
  ********************


   Tun daga lkcn ya tsiri min shigar dare amma ba kullum ba kwana bibbiyu zaku ga ya shigo ya kwana in kwana biyu kuma ya zagayo ko ƙeyar sa bana gani


 A yanzu ma fara sabawa da sabit sosai, amma duk wannan abun da ake yi badia bata da masaniya


  Rannan tafiya ta kama shi, ƙiri ƙiri na dinga nuna masa ina murnar tafiyar sa, ranar da zai tafi da daddare ya shigo ɗakina


  Muna kwance sai yace min

"naga alamar murnan tafiyar nan tawa kike ji ko, bakya ganin zakiyi kewa ta"


 "ko kaɗan" na amsa masa, mintsini kawai naji wanda ya saka ni zabura


  "ni ma ba zan yi missing ɗinki ba da daddare ne kawai zanyi kewar ki amma zan kira badia musha hirar mu"


 Ban tanka ba don nasan halin muguntar sa sai ya ƙara min wani salon muguntar tasan


  Kashegari da safe sai gashi da sabuwar wayar sa ya kawo min sqm badia bata ji daɗi ba wai meye na sai min waya


  Ina jin shi yana ta lallaɓe ta akan wai ko idan suna son abinci kafin in dawo sai in haɗa musu,


  Yana zaune a falo kafin lkcn tafiyar sa yayi, ita kuma gimbiyar tana kan cinyar sa sai wani shagwaɓa take zuba masa wai zatai kewar sa, shi kuma sai wani biye mata yake yi sai kace gaske


  Ada idan badia tai masa wannan shagwaɓar tata jin sa yake yi kamar ba yashi a duniyar nan, amma yanzi sai ganinta yake yi wani banbarakwai ba kyan gani akan cinyar sa, kyan cinyar sa asmau amma ita matsalar ta shegen taurin kai ne da ita



  Ni kunya ce ma ta sake su ta kama ni, lallai ma namiji sai a gaishe shi jiya yana ɗakina anan ya kwana amma da safe yana wajen ɗayar har da wani zaiyi missing ɗin ta


  Wallahi na dawo daga rakiyar sabit tabbas me fuska biyu ne, ɗakina na shige sam ban ma san lkcn daya tafi ba



  Yana tafiya naje part ɗin anty fannah na nuna mata ita ta nunnuna min yadda ake operating ɗin ta ranar wuni nayi acan sai da daddare dana ci na ƙoshi sannan na tafi inda na tarar da bala'in badia wai na barta da yunwa kallo bata ishe ni ɗakina kawai ma wuce inda tabi ni da zagi




  Da daddare da wuri na kwanta ban daɗe da kwanciya ba sai naji wayar na ringing, ɗaukar ta nayi number sabit kawai nagani


 Sai da ta kusa tsinkewa sannan na ɗaga


"hello" nace masa

"baki iya sallama ba sai hello" sallamar nayi masa sannan ya amsa


 "me kike yi"

"ba komai na dai kwanta ne bacci zanyi"  na bashi amsa


 "ke baki san mijinki yayi tafiya ba ki kira shi ki tambayi ya ya sauka ba ko"


 "yi haƙuri ya ka sauka, yau wuni nayi ina koyon wayar nan shiyasa shap na manta da kai"


"meeeyeee kika manta dani saboda wata ƴar iskar waya lallai ma ke ɗin nan wai fannah bata koya miki yadda ake kula da miji bane"



 Masifar sa daya saba ya hauyi shiru nai masa ya gaji dayi ya kashe wayar sa

  Nima ajiye tawa nayi sannan na kuma kwanciya, can sai ya kuma kira, ohhhhh yanzu kuma menene ina ɗauka naji yace


"ke baki san mijinki ya yi fushi ya ajiye wayar sa ba ki kira shi ki bashi haƙuri ba" shiru nayi don sam ban san me zance ba


"asmau" naji ya ambaci sunana da harufa masu sanyi har cikin zuciyata sai da naji su


 "na'am ai ban san fushin kayi ba kayi haƙuri"


"sai dana roƙa, to punishment ɗinki shine ki bani labari kawai" shiru nayi to ni labarin me ma zan bawa sabit ni sam bamu saba hira ba balle in ce ga lbrn da zan bashi


 "baki jini bane"

"naji ai na rasa ko name zan baka ne"


"bani lbrin akai na" toofaaa ba gwanda yace in bashi lbr a kan garin da ban taɓa zuwa ba nayo sharhin daya zo min akaina amma labari akan kan sa me na sani



  Shirun daya ji yayi yawa ne ya sa shicewar

"to gaya min abu goma da bakya son nake yi" ban wani ɓata lkc ba na fara lissafo su



"na ɗaya kana da wulaƙanci, na biyu ga mugunta,........ Haka na dinga lissafo masa halayen sa da bana soo har ya dakatar ni sannan yace


"naji yanzu ki gaya min me kike so a dangane da ni" to faaa anzo wajen


Hmmmmmmmmmmmmmmm kawai na dinga yi ashe ya ƙulu, masifar tasa dai ya hauyi, nidai nawa jine sai da yayi ya gama sannan ya kashe wayar nima sai na kashe wayar gabaɗaya na kwanta, tunda lkcn be kuma kirana ba har ya dawo gida



********************



Rannan da sassafe ya shirya inda Allah ya taimake sa na san da fitar sa da wuri don haka sai na haɗa masa breakfast da wuri



  Ina kitchen ina wanke wanke badia ta kira ni wai sabit ya manta da agogon sa in kai masa agogon part ɗin mummy don kuwa a lkcn be ci ace ya tafi ba



Karɓa nayi sannan na kama hanyar part ɗin a daidai ƙofar shiga naji kamar ana magana ana ambatan sunana sai na tsaya don inji meye ake ta ambaton sunana


 "kai kuwa sabit ai na ɗauka son yarinyar nan kake yi, to me zai hana ka bari ta haihu ɗin" inji mummy


 "gaskiya mummy bana son haihuwa da asmau haka kurum ta haifa min baƙaƙen ƴaƴa inyi da su, ni dai kawai ina zaki san dabarar da zaki dinga yi mata har ta dinga shan ƙwayar kullum to gaskiya zan so hakan"



   Duk da dai mummy taga rashin dacewar hakan amma kuma bata iya yiwa ƴaƴan ta musu, sam bata so ba amma kuma sabit be san a a ba


  "to shi kenan amma baka tunanin ya kamata ka bari ko ɗaya ne ta gwada kafin a hanata"


"mummy akwai probability na asmau zata haifi baƙin ɗa kuma abinda bana soo kenan inda ace dukkan chances ɗin na fararen ƴaƴa me da zan fi kowa murna amma baƙin ƴaƴa inyi yaya da su"


  Duk yadda mummy ta so hana abin amma sam sabit ya ƙi yadda ba yadda ta iya haka ta karɓa tare da yiasa alƙawari kullum asmau zata dinga shaaa



 Sulale wa nayi na zauna a ƙasa gabaɗaya duk wani service nawa ya ɗauke, shin wai baƙi lefi ne da mijina baya son kalar nan


  Na ɗauka Allah ne ya hallicce mu kuma yake son ganin mu a haka, kallon skin ɗina yayi wanda yake a chocolate colour, wanda a kowane lkc yake glowing


  Kusan sai dai in ban fita amma sai an ta yaba kyau na amma wannan kyaun nawa sam baya burgr mijina, shi kawai baƙin nawa yake gani



 Sam be damu da abinda yake cikin zuciyata ba, jin takun sa ya sani miƙewa a tare muka buɗe ƙofar falon



   Sam ban nuna masa wani abu ba inda na miƙa masa agogon nasan sannan na shige don gaida mummy



  Tana zaune da sachet ɗin maganin a hannun ta tana kallo, tana ganina sai ta ɗan firgita amma kuma sai ta ɗake


  Zama nayi sam sai na nuna mata ma ni ban san me ake ciki ba, gaisawa mukayi sannan na miƙe zan fita


 "asmauk naji ta kira  ni, komawa nayi na zauna sannan nace

"na'am mummy kina son wani abun ne"


"sam ko ɗaya maganine dai na samo miki,  naga ƴar uwar ki har yanzu bata haihu ba shiyasa nace bari na samo miki magani ke sai ki dinga sha ko a dace"


  Murmushi ne sosai a fuskar ta da badan naji komai ba da abinda zai sa ince ƙarya ne, tashi nayi na shiga kitchen na ɗebo ruwa na kawo



   Guda ɗaya ta bani na haɗiya da in haihu da sabit ɗan ya hanani barin sa gwanda ban haihu da shi in yaso in lkcn tafiya ta yayi babu abinda zai hanani tafiya



  Hawaye ne taf ido na wanda a hankali suka dinga gangarowa duk wannan abunda nake wa sabit be sa shi ya fara so na ba to sai yaushe, shin wai baƙi laifi ne


   Ya Allah ka dube ni ka saka min cutar wa nan da nake fuskanta ba tare da wani hakkin na ba, ganin ina kuka ya sa mummy tambayar menene


"ba komai mummy kawai da ina farin ciki ne yadda kike nuna min soo" sanyi jikin ta yayi ta jawo ni ta rungume ni sannan tace


 "wani lkcn ni kaina nakan yi judging abinda nake yi amma i cant help it, wataran idan kika haihu zaki fahimci halin da nake shiga in terms of deciding wat mah kids want"


 Sam ban fahimci abinda take nufi ba amma na san cewar ita uwa wacce bata saba kwaɓar ƴaƴanta ba balle ta nuna musu sun yi ba dai dai ba, wannan shine weekness ɗin ta



  Her weekness is her boys kuma ban taɓa jin haushin ta ba saboda kowa a duniyar nan yana weekness ɗina sa


  Amma wannan karon gaskiya ta kaini bango sam na daina ganin mutumci ta at least in ɗan ta ya tashi yin abu wanda tasan be dace ba ai sai ta kwaɓe su ko amma sam ba haka take ba



   Tashi nayi na kama hanyar part ɗin mu ina shiga ɗakina kawai nayi, na kwanta kuka ne ya ƙwace min lallai maraici be yi ba


 Inda ace iyayena suna nan a raye da ko hakan zata same ni zai kasance ya zo min da sauki, amma yanzu bani da wanda zan tunkara


  Don ko idan na faɗa wa anty fannah hana ni shan maganin zata yi tace sai na yadda na yi cikin ni kuma kamar yadda baya son haihuwa da ni, nima haka na tsani haɗa jini na da shi, wani wahalallen bacci ne yayi gaba da ni



   Sai la'asar na tashi gabaɗaya bana jin daɗim jikina da kyar ma nayi dinner, ko da na gama ma sam banci ba shayi na haɗa na sha sannan na kwanta sai bacci


Ina cikin bacci naji mutum yana tashina tare da balbale ni faɗan nayi bacci ban jira shi ba


  Kaina ciwo kawai ya ɗauka sakamakom tashin nan da yayi min, toilet na shiga nayi wanka kamar yadda na saba in yazo nayi bacci nayi brush sannan na fito



  Yana matsowa kusa da ni da ƙamshin turaren nan nasa ya doki hanci na sai naji amai yana taso min, danne zuciyata mayi amma a gaskiya na ina cutuwa


   Yana shirin ɗaga ni wani yunƙuri da nayi sai amai ya fito gabaɗaya na wanke masa fuska da shi, sai da na amaye duk abinda ke cikina sannan na iya maida numfashi


  A gaskiya turaren nan ya cutar da ni dani dayawa, ido na a rufe banyi aune sai jin saukar mari nayi, na kuma jin wani a ɗayan gefe


  Dafe fuskar tawa nayi na buɗe idon nawa, nan naci karo da fuskar sa wanke tas da amai na, duk da zafin marin nan da nake ji amma hakan be hanani murmusa wa Allah ya kara ya faɗa a raina



   Ɗaga ni yayi ya shige toilet inda ya watsa ruwa yana fitowa ran shi a ɓace yace

"ki kwashe bedshit ɗin nan ki wanke min su tas idan na dawo da asuba na tarar da su ba a wanke ba a bushe ba zaki gane kuren ki"


   Ficewa yayi daga ɗakin ni kuma na miƙe tare da kwashe kayan shinfiɗar na nufi toilet don wanke su, to me ya saka ni aman nan, ni ko kaɗan banci wani abun a zo a gani ba balle ince ko shi ya ɓata min ciki



   Ina wankin ina tunani na, ko da na gama sai na fita waje na shanya su sannan na samu na tsarkake jikina ni ko ya gama ma oho masa, ban damu ba zani na na shinfiɗa sannan na kwanta

  Asuba ta gari 😴😴😴😴😴😴🤤🤤🤤🤤🤤🤤
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)




 🤲🏻 *ALLAHUMMA BALIGNA RAMADAN BIL IMAN*🤲🏻




   P⃗a⃗g⃗e⃗  19🌹





 Da asubar fari ya zo lallai mutumin ya iya doka sammako tashi na yayi sannan ya karta min warning kar ya sake ya dawo daga masallaci ban gyara ɗakin ba


  Wanka na fara yi sannan na ɗauko shayata na gyara ɗakin, sannan nayi sallah asuba, na idar ina lazimi ne ya shigo ɗakin nawa lkcn garin ya fara wayewa


 Ƙamshin turaren sa ya fara dukan hanci ma wanda hakan ya sa zuciyata ƙara tashi, da gudu na ruga toilet na fara amai, har banɗakin ya biyo ni


"wane irin iskanci ne yake saki wannan aman"

"wallahi ban sani ba ni bama abinda na ci" na faɗa a marairaice



   Matsowa yayi kusa da ni ya damƙi gashi kaina sannan ya ɗago min fuskata wani azaba naji ya ziyarci kaina fuskar nan tasa a tamke sam ba fara'a


"yaushe rabon ki da menstruation" ya tambaye


 Shiru nayi don wallahi ni na manta ba calculating nake yi ba, indai yazo min shikenan in bai zo ba matsalarsa, ƙara jamin gashin nawan yayi wanda hakan ya sani sakin wani ƙara


 "wallahi ban sani ba bana lissafi" 


 Sakin kan nawa yayi sannan yace

"ki yi brush ki fito ina jiran ki" brush nayi sannan na fito daga toilet yana kwance akan gadon, alamar inzo in kwanta kusa da shi yayi min sannan yace min


 "kika sake kika ƙara min amai wallahi sai na zane ki"


"wallahi warin turaren ka ne bana jin daɗin sa shi yake sani aman"


 "Wannan matsalar kice don baki isa in dena saka turare ba saboda ke"


   Ƙarasawa nai kusa da shi na kwanta ina mai ɗauke numfashi na, Allah dai cikin ikon sa dai banyi aman ba amma kuma na wahala



     Bayan ya fita ne naje toilet na kwarara shi kamar ba gobe kai wannan amai sai kace me, kodai ciki gare ni 😱 ni mau naga ta kaina. Ciki a wannan marrar gaskiya dole ne in faɗawa anty fannah don ta san abinyi



 ********************


  Sabit yana fita daga ɗakin asmau ɓangaren mummy ya nufa, fuskar nan tasa kamar an aiko masa da labari mafi muni


  Tana zaune tana lazimi ya shiga ɗakin, sai da ta idar sannan ta juyo ganin yanayin fuskar sa tasan ba lfy


"auta lfy me ya faru"

"mummy ina jin fa yarinyar nan ciki gareta kuma wallahi bana so"

"wake nan kake nufi kardai asmau"


"to in banda abin mummy cikin wa zan ƙi inba nata ba gaskiya i cant stand being a father to her black kids" ya faɗa bayan ya firzar da wata iska daga bakin sa



"sabit baka ganin ya kamata kayi murna da farin ciki ganin cewar an daɗe ana neman haihuwar amma sam badia bata haihun ba ɓarin ma da take yi kwana biyu shiru"


 "mummy badia zata haihu tunda ta taɓa amma ni gaskiya banason baƙaƙen yara, itama a matsayinta na matata ina manage ne da ita sannan kuma ace nazo na haɗu da ƴaƴa baƙaƙe gaskiya bazan iya ba bana sooo"



    Tsayawa mummy tayi sam tama rasa abinda yake mata daɗi, wai sai yaushe sabit zai hankali ne ya fahimci halin matansa sam ita bata ga alamar badia tana son haihuwa ba, asmaun kuma da zata iya haifa masa ko nawa ne batare da ta gaji ba shi wai baya son kalar ta, hmmmm wannan abun yanzu gaskiya ya fara isar ta


   "To yanzu me kake son ayi"


 "mummy ai ba akan ta aka fara cikin da ba a so ba kawai sai a zubar da shi sannan sai in ɗauki ƙwaƙƙwaran mataki akan ta"


  "kana nufin zaka zubar wa da asmau cikin da ke jikin ta, haba sabit me yarinyar nan tai maka haka dat u soo much hate her"


 "mummy sam baki fahince ni ba bana son baƙin ƴaƴa, farare nake so kamar ni, ki duba cikin gidan nam kowanne ɗan sa fari ne haka kurum akai na sai a fara haifar baƙaƙe kawai ƴaƴa na su zama bare a cikin dangi gaskiya banyi wa ƴaƴana wannan planning ɗin ba ina son su saje a cikin dangi"


  "to gaskiya ba da ni ba, duk yadda kaga zaka iya kayi tayi amma ni na riga na dawo daga rakiyar ka kullum am trying my possible best inga na nuna maka amfanin da darajar yarinyar nan amma kullum sai ƙara botsarewa kake yi to wallahi kaje kayi duk abinda zakayi amma banda ni aciki"


 Tana gama faɗar hakan ta miƙe tayi ficewar ta tare da barin sa a falon, sam be tsammaci hakan daga wajen mummyn nasa ba ita me goya masa baya akan komai da yayi amma wai yau itace ta zaɓi wata akan sa,


  Lallai dole ko menene sai ya zubar da wannan cikin na asmau don bazai yadda ya haifi baƙaƙen ƴaƴa ba, wayar shi ya ɗauko sannan ya kira wani abokin sa likita ne, sun jima basu haɗu ba


  Abokin nasan ya kasance me shegen neman matan tsiya wannan ɗabiar tasan ce ya sa suka ɓata da sabit ɗin har suka raba hanya, yasan tabbas indai yana neman mata to bazai hana sanin yadda ake zubar da ciki ba


  Ringing ɗaya abokin ya ɗauka tare da cewa

"manya ashe za a neme mu"basar wa sabit ɗin sannan ya fara gaishe shi


Bayan doguwar gaisuwa da tambayar juna iyali sai sabit yace masa

"aboki na har yanzu ana halin ne ko an daina"


"wallahi sabit tunda matata ta haifi ƴa mace na sallama, sai dai ɗan abinda ba' a rasa ba amma bana ɗaukar yara sai waɗanda suka jiƙu a abin kaga ban farka ba balle a farke min tawa" ya ƙarashe zancen nasa cikin shaƙiyanci


 "ashe dai ba a dena ba" inji sabit


"yo me za a fasa mutuwa ko hisabi muna dai fatan denawa kafin mu tsufa, don kar a tsufa kuma ana bin ƴaƴan ciki"


"Allah ya shirya ka wato kai abin ma wasa ka maida shi ko to Allah ya baka sa a kar ka shiryu ɗin" inji sabi


"kai fa ɗan iska ne ya ina neman shiryuwa amma kana min wani fatan, wai ma meye na nemana nasan dai ba halin da nake ciki kake son jiba"


  Shiru sabit ɗin yayi don shi sam be ma san ta inda zai fara ba, can dai da ta matse shi sai yace


 "wallahi abortion nake son ayi wa wata ban sani ba ko kana yi"

"ɗan iska kace kaima kayi joining grp ɗin namu ya akai haka ta faru bakwa using protection ne"


"wane grp ɗin naku Allah ya kikaye ni, kai in kasan inda za ai min kawai ka faɗa min bana son long story" ya faɗa a fusace don yanzu haƙurin sa ya fara ƙarewa


"sorry bro abin bai kai nan ba kawai ka shigo asibitin mu ana yi ni ma da kaina zan mata kar
 ka samu damuwa"


"kai ka isa wallahi baza ka taɓa min matata ba, in kuna da macen da zatai aikin ka haɗa ni da ita in kuwa babu in nemi wani"


  "haba bros kawai ka taho, amma me yasa kake son zubar wa da matar ka ciki"


"ai ba exams nake ɗauka ba balle ka tambaye ni kowane question sannan in amsa wannan personal matter ɗina ne, ko kana so in dinga bayyana sirrin gidana gare ka" inji sabit


"sorry bros kawai kuzo in shaa Allah kafin nan na tanadar da komai ready har dr. ɗin"


 "ok see u, zan shigo da daddare"


  Sallama sukai sannan sabit ya koma part ɗin sa, yai wanka ya fice ko abinci ma be tsaya ci don yarinyar haushin ta yake ji sosai wai tayi ciki to garin ƙaƙa hakan ta faru lallai yayi sanya dayawa


  Jiya jiyan nan yakai wa mummy pills akan ta dinga bata amma wai a yau wai a tashi da ciki, kai wallahi da sake bazan iya ganin baƙaƙe a matsayin ƴaƴana ba


 ********************


  Sai gab da la'asar sannan ya dawo, ina kitchen ya same ni ina wanke wanke


"idan anyi sallah la'asar zamu je a sibiti a duba ki wannan aman naki ban gane shi ba"


  To kawai nace na cigaba da aiki na, sai da na gama sannan, nai wanka na ɗauro alwala na gabatar da sallah la'asr


  Sannan na je falo na shi yana zaune

"na gama" na faɗa

"muje waje ki jirani gani nan zuwa"

Wajen na fita be wani daɗe ba sai gashi, motar muka shiga muka kama hanyar asibitin hankali na a kwance nasan dai me za a ce ciki gare ni shine dai be san ina da shi ba



  Muna ƙarasawa asibitin ya kira wani abokin sa a waya sai kuwa gashi kamar daman mu yake yi, gefe sabit ɗin ya ja shi suka fara ƙus ƙus ban san me suke cewaba daga ƙarshe dai naji abokin yana cewa


"haba bros ai nai mata bayani baka da matsala"


  Sai da suka gama gulmar su sannan suka ƙaraso, shi yayi mana jagora har wani ɗaki in da muka tarar da wata likita tana zaune akan wata kujera


  File aka buɗe mana sannan ta fara mana ƴan tambayoyi ina bada amsa iya sani na,

  Sai da ta gama rubuce rubucen ta sannan tace min in kwanta a kan ɗan gadon da ke ɗakin, kwanciya nayi sannan ta ɗaga min rigar da ke jiki na


   Wani abu ta matsa min akan cikin nawa wanda yake a shafe kamar ba komai a cikin sa sannan ta kunna ƴaɗ computer da ke kusa da gadon ta ɗauko wani abu tana goga shi a kan cikin nawa tana kallon cikin computer


  Sai da ta gama sannan ta bani tissue wai in goge, in sauko, hakan kuwa nai, ƴan rubuce rubucen ta ta kuma yi a file ɗin nata sannan tace


"positive ya nuna cikine amma kama son ayi proceding da allurar"


"abinda ya kawo mu kenan"

"ok bari in rubuta mata sai kuje ku siya sai nurse tai mata ai bazai bada wani matsala ba 6weeks kawai yake"


  "ok mun gode" sam ban fahimci me take nufi ba na ɗauka tana nufin cikin bazai bani matsala ba don haka sai muka karɓi



    Allura ce guda ɗaya muka siya sannan muka je nurses room akai min, allurar shegiyar zafi gare ta ga sagar da ƙafa, ko da muka fito sai muka kuma haɗuwa da wannan abokin nasa inda ya ce mana ba wani matsala in muna son zama mu zauna in kuma zamu tafi in matsala ta faru sai mu dawo


  Sabit shine ya matsa mu tafi kawai don akwai abinda zai yi a office ɗin sa, sallamar mu aka yi muka kama hanyar gida


A ƙofar gida ya ajiye ni, ina shiga ɓangaren anty fannah na nufa tana ganina sai tace min

"naje wajen ku aka ba a san inda kike ba wannan ƴar iskar kishiyar" murmushi nayi yadda anty fannah ta tsani badia ni ban tsane ta ba


 "ni albishir ma na zo miki da shi amma kuma kin fara kawo zancen badia" barin abinda take yi tayi sannan ta ƙaraso wajena


"ciki gare ki don ashine kaɗai albishir ɗin da za ki min inji daɗi" murmushi nayi sannan na shafa ciki nace

"wata ɗaya" ina faɗa mata ina murna, rungume ni tayi tana murna nima ina yi, sai da muka gama murnar mu sannan tace min


 "asibiti kuka je aka tabbatar" gyaɗa mata kai nayi sannan nace mata


"har allura ma akai min me shegen zafi"

"allura kuma ta mecece" ta tambaya fuskar ta da alamar mamaki


"oho ni ban sani ba, don da muka shiga office ɗin su suke ta abun su banda ni"



   "ƙila ko na ƙarawa babyn ƙarfi ne" inji ta muka ci gaba da hirar mu, har anty fannah tana bani shawarar kar in sake in bari badia ta san da cikin sai dai kawai ta ganshi



   Hira tai hira muna ta yi can sai naji mara ta ta fara mintsini na, na share, abu wasa wasa tun ina basarwa har na kasa na faɗawa anty fannah ga abinda nake ji faa


 "ikon Allah tace ba yanzu kuka je asibiti ba akace muku lfy har da baku magani ba"


  Gyaɗa kaina nayi bayan na cije leɓan ƙasa saboda azaba, wani murɗawa da cikin nawa yayi sai kawai naji wani na fita daga jikina kamar fitsari


"anty fannah fitsari nake yi" nace mata

"fitsarin lfy tashi mu gani"


 Ina miƙewa ta leƙa inda na zauna wani irin ƙara ta saki sannan ta kama hannun


"asmau zo muje a sibiti kar cikin nan ya zube" jikina ne ya fara rawa ina miƙewa jinin ya cigaba da zuba yana bin ƙafa ta



    Har mun kama hanyar fita sai taga ina zubar da jini don haka dole ta raka ni toilet ɗin ta na gyara jikina sannan muka kama hanyar jikina sai rawa yake yi kardai ɓari nayi



  Asibitin da suke zuwa ta kaini inda nan da nan aka shigar da ni labour room, ciki ya riga ya gama lalace wa, dƙn haka suka taimaka ya ƙarasa fita sannan suka dinga min tambayoyi akan yadda abin ya faru



  Tsab nai musu bayani abinda ya faru anan nurse ɗin ta gane allurar abortion akai min, kuma cikin ya fita sam ba wani matsa, magani kawai aka bani sannan ta ce mu fita tunda dai komai is normal



    Anty fannah ce ta bita office inda tai mata bayanin abinda ya faru da ni da kuma asarar cikin ya zube gabaɗaya bashi



   Da kuka anty fannah ta fito daga office


"asmau dama sabit allurar zubar da cikin nan ya sa akai miki" ta faɗa tana kuka


  Dakewa nayi don bana son taga weakness ɗina


"anty kaɗɗara tace kuma shima babyn Allah dama yayi ba me taka ƙasa bane, don haka babu komai Allah yana kallo kuma zai saka min" kuka ne yaci ƙarfi lallai yau na tabbatar da tsanar da sabit yake min ba kaɗan bace



  Sai da muka gama kukan mu sannan muka kama hanyar gida bayan mun sai magani


 ********************


   Sam sabit ya manta ma da wata sai asmau balle har ya tuna da cewar zata ɓari at any moment, hidimar sa kawai yake yi


  A yunwace ya ƙarasa gidan yai mamakin da ya shiga ya kan dinning table ɗin ba komai, badia ya kira sannan ya tambayeta me ya faru yau abai girki bane ko mee


"wallahi ban sani ba ni tunda ta fita da yamma ban kuma ganin ta ba" gabansa ne ya faɗi kai dai ace ta san abinda yai mata kuma ta gudu kai ina zata gudu ai har yanzu batta da wannan wayon ƙila tana ɓangaren fannah


  Miƙewa yayi ya kama hanyar burin shi yaga asmau acan in bai ganta ba yanzu tayaya za ayi ya fara rayuwa ba ita, ƴar iskar yarinyar duk da dai ba kalar sa bace amma kuma Allah ya bata wani baiwa da duk wanda ya fara sanin ta bazai iya rabuwa da ita



  Gudu gudu sauri sauri a haka ya ƙarasa part ɗin fannah, itama a kulle yake bata nan, hankalin sane ya tashi, isma'il ya kira bayan ya ɗauka ne yake tambayar sa fannah


  Inda isma'il yake cewa ta cemin suna asibiti ita da matar ka, wani ajiyar zuciya yayi wanda shi kansa bai san zai iya ba Allah ya taimake shi
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)




 🤲🏻 *ALLAHUMMA BALIGNA RAMADAN BIL IMAN*🤲🏻




   P⃗a⃗g⃗e⃗ 20 🌹




 Basu suka dawo ba sai kusan 08 :00pm sannan muka dawo, directly part ɗin anty fannah muka wuce sallah kawai nayi sannan na kwanta sai bacci ya kwashe ni



    Sabit yana ɓangaren sa amma ya kasa zaune ya kasa tsaye tunanin sa kar asmau ta faɗawa fannah yai mata allura gaban shi sai faɗuwa yake yi


  Sai kusan 09 :00 sannan ya miƙe, badia da ke kusa da shi ta tambaye shi

"sabit ina zaka a daren nan"

"zanje in duba yarinyar nan ne dare yayi a maimakon ta zo ta kwanta" inji sabit


"to meye na damuwa da ita in ta gaji ai dole ne ta samu wurin kwanciya ko, amma ka wani tada hankalin ka sai kace wata matar ka"


  Wani kallon banza ya bita da shi sannan ya fice, ɓangaren fannah ya dosa, yana shiga ya tarar da fannahr tana kallo


  Sallama sukai shida badia suka shiga, kallo ɗaya fannah tai musu ta kau da kanta gabaɗaya ta dawo daga rakiyar sabit ɗin balle wannan ƴar iskar matar tasa


 
 "fannah don Allah ina asmau take naga har yanzu bata dawo ta kwanta ba" bata kalli inda suke ba ɗakin da asmaun take kawai ta nuna masa da hannu


 "amma ta riga tayi bacci don haka zaku iya tafiya da safe in ta tashi ta koma" tsayawa yayi yana kallon fannah kai gaskiya da sake bazai taɓa iya barin asmau ta kwana a wani wajen ba sai da ɗakin ta


  "bari inje in taso ta" ya faɗa yana yin hanyar ɗakin, miƙewa ta bi ta sha gaban sa


"baka isa ka tashe ta ba ai matar ka ce indai har ka matsu ta koma ɗakin natan sai dai ka ɗauke ta in kuwa ba haka ba sai da safen"


   Nannaɗe hannun rigar sa yayi yana shirin shiga ɗakin, sai badia ta tare shi

" *SD* kar kace min kana son shiga ka ɗauki yarinyar nan da kanka, ka barta mana da safen ta dawo da kanta"


  Kallon ta be yi ba ya shige, masifa ta fara yi tana cewa wallahi indai har ka sake ka ɗauke ta wallahi zaka sani don ni kuwa ban yadda in yi sharing miji da wata ƴar aiki ba



   Kinkimar asmau yayi yai mata ɗaukar jarirai sannan ya kama hanyar fita da badia a bayan sa tana ta balbala masa bala'i inda shi kuma ko ta kanta be bi ba



   Anty fannah ta murmusa dama abinda take som sani kenan da sabit shin anya yana son asmau kuwa ko a a amma ita a ganinta yana son asmaun amma kuma me yasa yake mata haka



   Kuma duk wani shawarar da yakamata ya bawa asmaun amma duk da haka sabit ɗin ya kasa sallamawa wannan abun da ɗaure kai yake


   Sabit har cikin ɗakin ta ya kai ta badia na biye da shi, 

"to tunda ka kawo ta sai ka ajiye ta muje ko" ta faɗa masa kamar wani ɗan yaro, abin nan yai masa ciwo yadda take nuna halin ko in kula da asmaun duk kuwa da yadda asmaun take kular mata da gida



  Wani banxan kallo ya bita da shi wanda ya sata jan bakin ta tai shiru, yana son rungume asmau kafin ya fita amma kuma badia ta ƙi barin ɗakin


  Haka ya haƙura ya fice bayan ya gyara mata kwanciyar ta sannan ya tafi ɗakin sa badia ce ta shigo tana wani rangwaɗa tsab ya fahinci me take so amma sai ya basar daga baya ma data ishe shi sai ya kore ta ya rufe ɗakin sa




   Tinanin asmau ne kawai ya faɗo masa arai yana jin yarinyar sosai a ransa amma gaskiya bazai taɓa barin ta ta haifa masa ƴaƴa ba



  Sai da ya tabbatar da badia tayi bacci sannan ya kama hanyar ɗakin asmaun tana ta baccin ta kamar yadda ya kwantar da ita


  Kusa da ita ya kwanta sannan ya janyo ta jikin sa ya dinga shafa mata bayanta har bacci shima ya kwashe shi



********************


  Na riga shi farkawa ganin yadda yake kwance yana ta sharar baccin sa ya sani zame jikina a hankali na shiga banɗaki tare da ɗauro alwala



 Ina fitowa na tarar ashe har ya fice, sallah nayi sannan na kuma kwanciya don kuwa ji nake yi kamar bacci be ishe ni ba



   Bacci ne ya kwashe ni, cikin baccin nawa naji muryar badia tana min magana


"sai yaushe zaki tashi ki haɗa mana breakfast gashi lkcn office zai ƙule" miƙe wa nayi sannan ta kalle


 "matsayin mu ɗaya a wajen sabit kamar yadda kike tunƙahon mijinki yake haka yake tinƙaho da ni a matsayin matar sa don haka kowacce tata ta fish she ta daga yau na daina bauta wa ko wa kowane ɗan iskan yayi aikin sa an gama wannan wasan"


  Sakin baki tayi tana kallo na lallai ma yarinyar nam,
 Sabit ta ƙwala wa kira wai yazo ya yi magana


  Shigowa yayi shima kamar gaske bayan ya haɗe girar sama data ƙasa


"me yake faruwa ne a ana anga ana ta ƙwala min kira"


" *SD* yarinyar nan taƙi tashi tai mana breakfast nai mata magana tana gayamin maganar banza"

   Juyowa yayi ya kalle ni wacce ni kuma idon yake ƙyam akan sa inga irin matakin da zai ɗauka


 "ke sai yaushe zaki ki haɗa mana breakfast ne"


 "bani da lfy ko kana don ingaya maka abinda yake damuna ne" shiru yayi sannan sai ya juya ga badia sannan yace mata



 " Muje mu ƙyale ta tunda tace bata jin daɗi inta warke ta koma duty" ya faɗa yana tura ta don su fita


  " a a ku dawo in faɗa muku abinda ke damuna mana ya kuka fita ai kamata yayi kiji ki san me ya same ni" na bita da wannan ina ganin ta juyo shi kuma ya hankaɗa ta tare da riƙe mata hannu yana janta


  Ai na dawo daga rakiyar sabit zai sqn ya zubar min da ciki wallahi sai ya gwammaci kiɗa da karatu, wallahi sai ya san asmau ya taɓa bari dai in fita mu haɗu da anty fannah nasan zata bani shawara


  Guduwar ma dana ce zan yi na fasa wallahi sai na zauna a gidan nan na haifawa sabit baƙaƙen ƴaƴa sannan hankali zai kwanta in ban haifa masa baƙaƙe ba ban rama wulaƙancin da yai min ba



  Wallahi sai ya gane bashi da wayo da asmau yake to nima yanzu lkcn da juya kaina yayi na daina ɗaukar order daga wajen wani nima daga yanzu na zama ogar kaina



 ********************


   Sai da na tabbatar sun fita sannan na tafi ɓangaren anty fannah, tana zaune ta zuba uban tagumi kamar an aiko mata da mala'ikan mutuwa, na shiga da fara'a ta


  Tana kallona tace

"lallai yaro be san ciwon kansa ba wai har kin wats tsake kin koma duty"


 "wane duty ba abinda nai musu ai yanzu ciwon ido zan zame musu a gidan nan kuma wallahi sabit abinda baya so shine baƙaƙen ƴaƴa ko wallahi anty fannah sai na haifa masa sai na cika wa sabit gida da baƙaƙen ƴaƴan daya baya so" tsayawa tayi tana kallo na


 "asmau da niyyata in saka daddy ya ƙwatar miki ƴancin ki, yasa sabit ya sallame ki ke ma kije ki ne mi wanda yake sonki kk aura"


"haba anty fannah ai da kin cuce ni, sabit shi nake son ya kasan uban baƙaƙen ƴaƴana, ko yana so ko baya so wallahi sai na nuna masa shi ƙaramin ƙwaro ne a wajena, abinda ba abinda ban sani ba nashi, wallahi anty fannah cikin sakan ƙalilan zan iga juya sabit, kawai dai yana da taurin kai da tsatstsauran ra'ayi, amma wallahi na ɗau ɗamarar sai na nuna masa banbanci aya da tsakuwa, sai na nuna masa cewar wasu matan ma suna suka tara, wani ƙyalƙyal banza na mace ba lallai ta zama me quality ba"


   Tsayawa kawai tayi tana kallona na bata mamaki sosai, yama za a yi in tafi in ƙyale sabit a haka ai ya ci galaba ta wannan yaƙi ne ya soma wallahi sai naga ƙarshen yaƙin nan sai na haifa wa sabit ƴaƴa baƙaƙe mu ga yadda zeyi kuma wallahi ni da sabit ya raina sai na zame masa ciwon ido


  "anty fannah kayan gyara nake so" har yanzu bata daina mamaki na ba don haka sai ta jawo ni ta zaunar dani tare da cewa


 "asmau ko dai ɓarin nam ne ya juyar miki da ƙwaƙwalwa, naga duk kin rikice kin zama wata ba asmaun da na sani ba"


"wallahi anty fannah nice hankali kawai nayi, kuma nasan ciwon kaina wanda yayi sanadiyyar rasa baby na innace na barshi haka ai banyi ba wallahi sai na ƙun sa masa abinda har abada bazai taɓa mantawa ba amma sai da taimakon ki sai na haifa masa baƙaƙen ƴaƴa iya son raina, goma ma zan haifa masa ko sha biyar"



  Tabbas asmau ta zauce inji fannah, zaman dirshen nayi a gaban ta ina ta lissafo mata irin plan ɗin dana ɗauka zan aiwatar akan sabit da matar sa wallahi sai sun san shayi ruwa ne


  Tun tana basarwa har tazo ta fara bani tips na mallakar miji a hannun na ada in tana faɗa min yana shiga ne ta kunnen hagu yana fita ta kunnen dama


  Amma yanzu tsab nake haddace wa ai yanzu za a fara wasan ada ba komai akayi ba, amma yanzu wasan zai fara


  Sai yamma na kama hanyar part ɗin mu abinci na naje na dafa lafiyayye na zuba a cooler na ajiye, na shiga ɗaki na ɗau wanka na sai da na turare jikina da turare na daƙƙo wata fitted gown da mukai da anty fannah na saka



   Falo na fito ashe ita uwar gidan ta dawo ma abanji dawowar ta ba, cooler dana ajiye akan dinning table ta buɗe ɗan wake ta ci karo da shi da mai da yaji sai kunun tsamiya


  Wani shegen kallo ta bini da shi

"bana cin wannan ki sake ɗaura min wani"

"ai ba naki bane nawa ne, ai na dena yi wa kowa girki duk wanda ya ji yunwa ya shiga kitchen muga in zai iya"


  Hannu ta ɗaga zata kwaɗa min mari a dai dai lkcn sabit ya shigo


 "ke badia me ya haɗa ku zaki mare ta"


" *SD* wannan yarinyar wai me take taƙama da shi ne, gaskiya na fara gajiya da zama da ita ya kamata a sallame ta"


 Juyowa yayi zai min faɗan da yasa wani ƙayataccen murmushi na sakar masa tare da kaɗa masa ido cikin kissa



 Tuni ya maida wuƙar tasan sannan yai gyaran murya


"me tayi miki ne da zaki dake ta, bana son hayaniya"


"ni dai kawai na gaji da ganinta" in da inda ya fara ya rasa kalma ɗaya ma da zai ce sai wani kame kame yake



  Dining na nufa n zauna na fara cin abinci na ina jinta tama jarabar wai ban kai wannan matsayin ba tana ƙara yi wa sabit maganar ya kore ni ko ita ta barmana gidan


  Lallaɓa ta yayi ya hau sama inda ni kuma na zauna ina ta cin abincina, nai mamakin da ya gama kintsawa ya sauko ya ci ɗanwaken


   Ita kuma badia tana nan kan bakan ta bazata ci ɗan wake ba sai dai in dafa mata wani abun, iskar da ta ɗauko ta ma ban kalla ba balle ita sabit ɗin ma nai mamaki dana ga sam be ce komai ba
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)




 🤲🏻 *ALLAHUMMA BALIGNA RAMADAN BIL IMAN*🤲🏻




   P⃗a⃗g⃗e⃗  21🌹







 Tun daga lkcn na zame musu ciwon ido sai haƙuri sai abinda na ga dama nake yi a falon sam sabit sai yayi wani sanyi ashe abun nashi ma iskanci ne



  Tuni na ajiye girkin sai abinda naga dama nake dafawa wank lkcn badia taci wani lkcn kuma tace ita bata so kuma wallahi ruwa bana bata balle in ɗaura mata wani abu



  Tuni na ƙwatar wa ƴanci sam yanzu sabit baya min abun da yake min ada kamar ma shakka ta yake yi ko ince tsoron badia tasan akwai abinda yake shiga tsakanin mu yake oho mishi



   Lallaɓawa kuwa sai dai in be shigo ɗakina ba yai ta lallaɓa ni yana min wani daɗin bakin wai in kwantar da hankalina zai sanar da badia cewar ya mai da ni matar sa official



  Hmmm kawai nake bin sa da shi besan ni da nawa ƙudurin a raina ba, abu kaɗan idan tayi sai in fara "ke kin san meke faruwa a gidan nan in ƙafa ta ɗauke kuwa, kina can kin saki baki kina bacci kamar mushe" 🤣🤣🤣🤣🤣



  A lkcn zaku ga rawar ƙafar sabit nan da nan sai ya janye ta yai ɗaki da ita sam bazai bari mu ƙarasa faɗan ba, da gayya nake tsokanar faɗa, ko shi ma gogan yana zaune yana kallo sai inzo in canja channel ɗin kuma in ajiye remote ɗin inyi gaba sam bazai taɓa ce min ko mai



  Duk wata hanyar dana san zan bi in takalo sabit faɗa muyi don in tona masa asirin shiga ɗakina da yake yi nayi amma sam ba nasara



  Daga ƙarshe na tattarar na watsar na ci gaba target ɗina na neman ciki ido rufe abu kamar me ba ciki ba alamar sa, har wurin anty fannah naje ta bani maganin da take sha amma shiru, lallai ma kodai sabit yana yin wani abu ne a nashi ɓangaren sam ban sani ba amma ciki de ina nan ko ba daɗe ko ba jima sai nayi shi



  
********************



   Wani project ne aka tura sabit lagos zai je yayi na shekara uku, sam ban so ba saboda ba lallai bane ya tafi da mu ba tunda ina lagos ina abuja ai ba wani nisa bane kuma ba lallai ne mummy ta barshi ya tafi da mu ba amma gaskiya ni ina son bin sa don haka ko daya dawo ɗakina da daddare ranar na kai shi makka da madina a ƙafa da haɗine na karɓo na musammam a wajen anty fannah na sha



  Muna kwance yana min wasa da gashi na sai nace masa


"sabit kai da wa zaku koma lagos ɗin"


"kina son zuwa ne, kinga yarinyar nan ƴaɗ ƙaramar ki da ke amma baki son rabuwa da mijinki ko, shike nan zan wa mummy magana sai mu koma tare kin ga sai muci karen mu babu babbaka tunda badia baza ta ba"


"cewa zaka yi ka daina bin dare de kana lalube" mintsini ya mannara min au lalube ma nake yi



  Wasa mukai da sabit sosai kafin mu kwanta bacci,



  Ko da lkcn tafiyar yayi badia taji da ni za a wai don in dinga yi masa girki sai hankalinta ya tashi, itama sai taje



  Sam sabit be so badia tace zata ba amma babu yadda ya iya har wani nuna jin daɗin sa yayi wai zamuje tare hmmm ni dai kallo shine nawa



   Shirye shiryen komawar mu lagos ya kankama inda sabit ne ya karɓo wa badia transfer na wajen aiki, sannan muka kama hanyae birnin yanki



  Mun sauka lagos lfy gidan flat ne me 4bedroom a apapa kowccen mu ta ɗau ɗaya inda sabit ya ɗau master bedroom ɗin



   Zaman mu lfy sam bana shiga sabgar su haka suna basa shiga tawa girki ne inna yi in badia na da ra'ayi taci in bata da ra'ayi kuma sai ta siyo nata ba wanda yake shigar sabgae wani tsakani na da ita



  Rannan da daddare sai sabit yace badia ta shirya su fita, ina kallom su aka ci kwalliya har tana cewa


" *SD* dinner zaka kaini restuarant" sam be tanka mata ba suka fice, ni kaɗai ma ci dinner ta ranar kuma sam abin ma be dame ni ba saboda ni akwai zaman da nake yi kuma wallahi ko baɗe ko ba jima sai na cimma buri na



  Kusan awan su guda a waje sai gasu sun dawo, fuskar sabit kamar wacce aka aiko wa da mala'ikan mutuwa tai jajawur kamar bashi ba



  Inda ita kuma badia ita ma tata fuskar sharkaf da hawaye



 "wallahi bazata saɓu ba lallai ma badiar nan wallahi bazan yadda ba"


 "don Allah sabit kayi haƙuri wallahi bada son raina banr naga jikina ne yake attracting ɗinka zuwa gare ni kuma idan haihu nayi loosing shape ba lallai ne ka so ni ba shiya sa na cire mahaifar" 😱😱😱


 Wai kunne na ne yajiye min ko kuma mafarki nake yi


"wannan ma maganar banza ce kice min wai kin cire mahaifar ki akan wani banzan excuse naki, ni da naƙe expecting ƴaƴa na daga gare ki amma shime kika cire mahaifar ki"



  Faɗa ya shiga yi sosai ni dai dana ga abin nasu ba na ƙare bane sai na ahige ɗakina amma gaskiya badia tayi kuskuren cire mahaifa



  Wallahi akan wani ƙato bazan cire mahaifata ba, har kusan 11 :30 na dard suna bala'i akan cire mahaifar


  Ni dai bacci na nayi na ƙyale su, ko da na tashi da safe ma atmosphere ɗin gidan ba daɗi tunda dai masu gidan suna faɗa



  Haka dai akai ta zama ba daɗi don ɗan zuwa ɗakina ma sam ya daina ni ma ta shafe ni, duk ya bi ya tsangwami kansa



  Allah ya ƙara shine kawai abinda yake fita daga bakina, da ka barmin cikina da tuni na haife shi amma gashi yanzu inda ya kai kansa Allah ya ƙara ai yanzu bashi da wani mafita sai dai ta haihuwa da ni



********************


Sabit yana zaune duk abin duniya ya ishe shi, yanzu ya zaiyi shi fara neman matar ma da zai aura ta haifa masa fararen ƴaƴa shine aiki


  Yawancin matan yanzu ba farara bane farin kanti ne, kuma baya son kawo fara kamar badia ya ƙara ƙarawa kansa aiki, inda ace zai samu fara kamar asmau wallahi da ba abinda zai dame shi amma yanzu ga shi nan ya zama shi ba ga tsunstu ba baga tarko ba



  Har yanzu bashi da ra'ayin haihuwa da asmau kai sam ma bazai taɓa yadda ya haihu da itaba, shiyasa ya bata turaren da take amfani da shi


  Daga china ya taho da shi muddin mutun zai juri saka shi to har abada bazai taɓa bari asmau ta haihu da shi ba, turare ne kamar kowanne amma ƙamshin same illa ne, ƙamshin sa yana lalata ƙwan haihuwa



  Buɗewar ƙofa yaji yasan ba me shigo masa ɗaki sai badia don haka sai ya haɗe rai sannan yace


"me ya kawo ki" ko kallon inda take be yi ba


" *SD* na zo ne muyi magana, wallahi ban cire mahaifa ta ba har sai da san zamu samu solution"

  Jin kalmar solution ɗinne ya sashi juyowa tare da tsare ta da idon sa


  Ganin ya kalle ta ya sa ta ƙaraso qa har da riƙe masa hannun sa

" *SD* me zai hana mu samo surrogate mother, wacce zata haife mana ƴaƴan mu da ƙwai na da sperm ɗin ka kaga shike nan, ni ban yi loosing shape ɗina ba, kuma ga ƴaƴan mu"



  Zame hannun sa yayi daga nata


"kina nufin mu nemi wata arniya ta renar mana ɗa a cikin ta sannan ta haifa mana shi sam baza ayi haka da ni ba"


 "ba arniya ba, ga asmau ai an ɗaura muku aure ba sai muyi amfani da ita ba, ba hankali gareta ba sam ba ganewa zatai ba"


 Shiru yayi yana tunani tabbas wannan shine hanyar sa kawai ta samun fararen  yaran da yake so wato kenan ƙaddarar sa ce sai asmau ta haifa masa ƴaƴan sa kenan ko


 "to kije kiyi mata maganaa inta yadda shi kenan in kuma bata yadda ba wallahi sai na ƙara auren wacce zata haifa min ƴaƴa"


"zama ta yadda" ta faɗa da murnar ta tana miƙewa



   Ina kwance a ɗaki ima ta shiɗin kwanciya sai badia ta shigo nai mamakin ganin ta amma kuma sai na dake tunda take bata taɓa shigo min ɗaki ba nasan akwai abinda ya kawo ta



  stool na bata ta zauna, sannan sai tace min

"asmaj kamar yadda kika sani na cire mahaifa ta saboda wallahi ni bana son haihuwa, amma kuma sabit yana so don haka sai muka yanke hukunci sabit zamu dasa miki cikin a jikin ki in ya so sai ki haife mana shi"


  "ban gane ba " nace mata


 "za a saka miki ƙwai na da sperm ɗin sabit a cikin ki sai ki haife mana"


  "kina gani sabit zai yadda da hakan" na tambaye ta

"ƙwarai kuwa da sabit muka tattauna shi yace ma in miki maganar" takaicine yazo min har maƙogwaro na wani abu ya tokare min wato sabit jini nane baya so ko wai sai yaushe zan samu ƴanci ne sai yaushe zan samu cikar buri na



  Kallon ta nayi cike da tsana sannan nace mata

"kije ki gaya masa ciki na bazai ɗauki renon sa ba don haka yaje ya samu wacce zai biya kuyi abunku amma wallahi ni asmau bazan yadda ayi wannan abun da ni ba"



   Kuka na fashe da shi na takaici lallai sabit ashe abin nashi har ya kai haka wallahi bazan renar masa ɗa ba


Kukan da taga ina yi ne ya sata miƙewa sannan ta fice, kwanciya nayi akan gado na fashe da kuka


 Wannan wulaƙancin da me yayi kama, wai me nayi wa sabit ne haka daya tsani sooooo much shin baƙi laifi ne ko kuma haɗa mun da Allah yayi sam be ɗau wannan a matsayin ƙaddara ba



  Wallahi baza ta saɓu ba yacce matar sa ta cire mahaifar ta ya kasance baza ta ƙara haihuwa ba dole ne ya haƙura nima gashi tunda nai ɓarin nan ban kuma samun ciki ba ko menene dalilin oho


 Takaicin sabit ranar hanani bacci yayi kwana nai ina kuka dana gaji da kukan sai na miƙe na ɗauro alwala ina kuka ina faɗawa Allah matsololina duk da yasan a halin da nake ciki amma kuma ina sake gaya masa ya kawo min ɗauki



  Anan kan sallayar bacci ya kwashe ni da asuba na farka sakayau haka naji ni, da wuri na haɗa breakfast ɗina sannan na zauna ina cin abinci na kasa ci nayi



  Maganar badia ce ta faɗo min a raina, wai in zama wacce zan reni cikin su, lallai ma sun rena ni


  Amma kuma wani ɓangare na zuciyata na son yi, ko ba komai zan dai ɗauki cikin da ba a son in ɗauka


  Miƙewa nayi kawai na yi na kama hanyar ɗakin sabit hankalina Akwance, suna zaune shida badia sun yi jugum jugum abin duniya ya ishe su


  "na yadda zan ɗau cikin ku amma ina da sharaɗi" kallo suka juyo wa sukai gare ni


"meye sharaɗin naki" suka haɗa baki


  Kallo na bisu da shi sannan nace

 "sai an biya ni ladan ɗaukar cikin"


"faɗi ko nawa kike so ni zan biya" inji sabit, tsayawa nayi na ƙare masa kallo sannan nace

 "250k kuma cash nake soo"


  Badia ce ta miƙe ta fita daga ɗakin bata daɗe ba sai gata da kuɗi


"gashi nan 300k ne na ƙara miki 50k" karɓa nayi ina murmushi sannan nace


"kun biya sai a saka lkcn dashen" murna sosai ya kama su badia har da rungume sabit


    Fita nayi daga ɗakin naje na adana kuɗina akwai ranar da zakuyi amfani, nace a raina



 Fara shirye shiryen dashen cikin muke yi abin mamaki shine na nemi turare na ko sama ko ƙasa


  Babu neman da banyi ba amma babu har sabit na faɗawa sai yace min zai sai min sabo


  Gaskiya nai missing wannan turaren zan so ace be ɓata ba haka nai ta neman har na haƙura


  Ranar laraba muka shirya muka je asibitin akai mana test da komai da komai, komai ya kasance normal kawai lkcn dashe aka saka sati biyu



   *****************


    Ranar da kawo za ai dashen da kuɗi na na fita 200k a tattare da ni, sai da muka gama komai na shiga ɗakin dashen sannan nace wa dr. ɗin wacce ta kasance macece kuma bayarabiya


 "nawa aka biya ki kuɗin dashen nan" kallo na tayi kamar batai magana ba, kuɗin da ke jikina na fito mata dashi kallon su kawai tayi sai ta washe baki tare da cewa


"30k"

Ɗari biyu na ɗauko gabaɗaya sannan  na bata na ce mata

"kiyi aikin ki da kyau" kallo na tayi sannan tai murmushi tare da soke kuɗin sannan aka fara dashen fatana dai Allah ya bada sa a



   Lafiya aka gama sai da nayi awa ɗaya bayan dashen sannan tace min in miƙe, kuma aka kafa min sharaɗin kar in kwanta da kowane namiji sai an tabbatar da cikin



  Badia ce me cewa ai dr. kar ki damu bata da miji, tunda muka koma gida sabit yake nan nan da ni,


   Komai na tashi zanyi sai a hana ni, har Allah ya kai mu 2 weeks inda muka koma asibitin aka tabbatar da cikina



  Murna kamar me a wajen sabit da badia, kallon su kawai nake yi dafe cikin nawa nayi sannan nace Allah ya kawo min kai duniya lfy
🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)




 🤲🏻 *ALLAHUMMA BALIGNA RAMADAN BIL IMAN*🤲🏻




   P⃗a⃗g⃗e⃗  22🌹








 Cikin ikon Allah na ci gaba da renon cikin mu 🤣🤣, Kulawa sosai nake samu daga wajen sabit inda badia ke ƙorafi wai ya fiya shiga harka ta, sam banni da wata matsala kuma duk abinda nake so nake yi



   Tun cikin yana ƙarami sabit ya fara cika mana gida da siyayya tun ba a san me zan haifa ba amma ɗaki guda haka ya ware yake kashe kuɗin domin isowar ɗan so



   Allah sarki lkcn da nai ɓari ko mace ko namiji, duk banga wannan ba amma yanzu ko aiki nake yi yai ta faɗa kenan wai sam bana son hutu ko ya isheni da sam ban damu da cikin da ke jikin na ba


  Wani lkcn abin nashi ma wallahi har haushi yake bani, daga baya ne ma ya nemo mana me aiki wai don in dinga hutawa



  Amma sam bana son wani hutu domin ni na riga na saba da shige da fice na tun ma kafin in samu ciki balle kuma yanzu



  Jina nake yi kamar cikin ba a jikina yake ba sam bawani matsala ko laulayi haka nake ɗaukar sa salin alin karatun fatara



   Sai da cikin ya zauna sannan sabit ya kira mummy yace mata badia nada ciki, mummy tai murna sosai sannan tai fatan Allah ya inganta



  Bayan kwana biyu sai ga mummy nai murnar ganin ta sosai har da saƙo na daga anty fannah Allah sarki anty fannah nayi kewar ki sosai



  Mummy tai ta faɗa wai badia mahaifar ta bata da ƙwari kuma gashi ta kuma samun ciki amma ta ƙi zama ta kula da kanta



  ba wanda ya tanka sai dai lallashi da suke ta bata wai zasu kula da cikin, ni dai ina gefe ina kallon ikon Allah wannan rayuwa wato akwai abin mamaki sosai



  Kwanan mummy biyar sannan ta kama hanyar gida, kamar nayi kuka ranar da ta tafi, don kuwa yanzu zan koma rayuwa ni kaɗai


   A hankali cikin ya ci gaba da girma har lkcn da zai zo duniya yayi


 Rannan da yamma sai ga mmn badia tazo gidan ita da wata mata, ɗakin badia suka sauka sam ban sam me ya kawo su ba amma kuma bini bini a bini da ido



  ranar wata talata da safe na tashi da nakuda, tun ina yi ni kaɗai har dai dana ga abin bana ƙare bane na fita, ina fita naci karo da wannan matar zata shigo ɗakina


 "kar dai naƙuda kike yi ƴannan" gyaɗa mata kai nayi don bazan iya magana ba sabida ciwon da ke damuna



 Sabit ta kira shima ya fito jiki si ɓari yake yi yaji ina labour, asibiti muka je, inda aka shigar da ni labour room Awa uku cur na ɗauka sannan Allah ya sauke ni lfy, ajiyar zuciya na saki dana ji Allah ya raba ni da wannan cikin lfy



    Ɗagowa nayi na kalli yaron.........  Fari tas da shi kana ganin shi kaga sabit


  Miƙo min shi nurse ɗin tayi na karɓi kayana na tsaya ina kallon sa, godiya nai wa Allah daya sani ina da rabon ganin jini na



  Sai da nurse ɗin gama gyara ni sannan ta karɓi babyn don gyara shi, shima, ko da aka gama shirya shi zata fita da shi na kira ta na karɓi abuna



  Ƙare masa kallo nayi kamar sabit yayi kaki ya yar addua nayi masa sosai, na so ace yaron kamata ya ɗauko


  Ko kuma ace baƙi ne amma ba komai duk abinda Allah yaso haka zan karɓa, kuma ina fatan ya zama me jin ƙan iyaye


   Ɗa na yana hannuna na fito daga labour room, da sauri suka ƙaraso tare da karɓar sa mmn badia ce ta fara karɓar sa


 "namiji ne ko mace" ta tambaye ni kalmar tai bala'in ƙona min rai ba Allah ya raya ba komai amma wai ita burin ta namiji ne ko mace


 sabit ne ya karɓi shi shima daga gani maganar tai masa ciwo, karɓar sa kawai yayi ya wuce ɗakin da aka bamu na hutu


  Addua ya dinga masa, ina amsa wa da amin, duk wannan abun da muke ita uwar ɗan bata sani ba don sammako tayi ta tafi kwatano wai ta tafi siyo kayan da zata saka da suna



  Sai da ya gama masa addua sannan mmn badia ta kuma karɓar sa ta buɗe masa diaper inda ta gano namiji ne



  Nan da nan murna kamar me, har wani ƙara ruƙunƙume shi take yi, mijinta ta kira ta shaida masa badia ta haihu,


  Shima yai mata murna sannan yace a bawa badiar, nan ta hau ƙarya wai badiar bacci take yi

  Mummy sabit ya kira yace mata badia ta haihu ita ma mummyn tai murna sannan tace a bawa badiar tai mata barka shima duk ɗaya yace tana bacci



  Haka suka dinga kiraye kirayen waya suna shaidawa badia ta haihu, ni dai kallo ne nawa


  Zuwa can baby ya fara mutsu mutsun yunwa, dabino sabit ya tauna ya lasa masa a bakin sa sannan aka bishi da zam zam



    Wajen azahar aka sallame daga asibitin muka kama hanyar gida, wai don renin hankali babu wanda yake ta kaina ni dana haihun sai ta baby,


  Ɗakina na shige na samu na watsa ruwan zafi a jikin sannan na fito kitchen na ɗaura indomie na ci na ƙoshi sannan na wuce ɗaki na na kwanta



   Wajen ƙarfe 06:00 na yamma sai ga mummy, ina kitchen ina dafa shayi
 Sai ga mummy, da sauri naje na tare ta

"mummy ashe kina tafe" tsayawa tayi tana kallona


"ya naga kamar ma kece me jegon duk kin wani ɗashe"

  Ta faɗa tana kai hannun ta kan fuska ta, murmushi na saki sannan naja hannun ta zuwa ɗakin badia

"zo muje kiga jikan naki"


  Bina tayi, da sallama na shiga, suna zaune a bakin gado shi kuma babyn yana cikin gadon sa na jarirai yana ta baccin sa



A razane suke da suka ga mummy, sai suka fara kame kame


 "hjy fatima yaushe kika ƙaraso, muje falo mu zauna yaron yana bacci" inji mmn badia


  "ni da nazo ganin baby sai ace min yana bacci, ina ita mejegon"


Tsuru tsuru sukai, nidai tunda naga na haɗa su sai nai ficewa ta na barsu


  Ɗakin nawa naji an turo ƙofar, ashe mummy ce ta shigo, sai da ta ƙaraso da sannan na bata wurin zama


 "har yanzu sabit ɗin basu dawo bane ko dai wani abun ne ya samu badiar"


  Ni dai ban tanka mata ba saboda sam ban san ma ina ta dosa ba,


 "ni wallahi duk a gajiye nake, nace musu su shirya gobee mu koma abuja ai suna acen dama dalilin zuwa na kenan"


  Ni dam ban tanka mata ba don kuwa a gaskiya na fara kewar ɗana, don haka sai nai mata shiru,


  Mara ta naji ta fara murɗa min, mitsss sai yanzu na tuna sam ban ma sha magani ba, miƙewa nayi don in ɗauko magani sai naji mummy tana cewa


"asmau lfy naga kina tafiya kamar kece kika haihun, gashi kuma duk kin ɓata zanin jikin ki"


Juyawa nayi don inga inda na ɓata ban ɗago ba sai ganin mata nayi kusa da ni


"asmau ke kika haihu ko badia"

 Tsare ta nayi da idona wanda a yanzu suka ciko da hawaye, ɗago min fuskar tawa tayi


"asmau ke kika haihu, ba badia ba" gyaɗa kaina nayi hawaye yana zuba a ido na


 "haba biri yayi kama da mutum" inji mummy takaici ne ya kamata sai ta kama hanyar fita



  Ban san me tace musu ba sai gata da babyn,

"ungo shi bashi nono ya sha ki gama in gyara ki, wallahi idan sabit ya dawo yau sai yaga ɓacin raina wanna wane irin zalinci ne"



  Karɓar babyn nawa nayi na rungume shi sannan na zauna na fara bashi nono kamar dama yunwa yake ji haka ya karɓa ya fara tsotsa



 Muryar badia muka ji a bakin ƙofa tana masifa


"ban gane ɗan ta bane yaushe ya zama ɗanta don kawai ta rene shi a cikin ta sai ace ɗan ta wallahi bazai sha nonon ta ba, na riga na gama booking nurse ɗin da zata dinga kular min da yaro" ta faɗa tana shigowa a fusace da zummar karɓar mummy



Mummy ce tace

"wallahi kika sake kika katse masa wallahi tallahi sai na saɓa miki"


"mummy ya za ayi jini na ya sha nonon ta"


"ya akai ya zama jininki"


  Nan badia ta kwashe komai ta faɗa wa mummy, bata gama ba mummy ta fashe da kuka, adai dai lkcn sabit ya shigo



 Ingiza badia yayi ya kora daga ɗakin, mummy kuwa kuka ta dingayi,ba irin lallashin da sabit be mata ba amma taƙi shiru


 Shima sai ya fashe mata da kuka

"anya sabit kana tuna ranar da Allah zai kama ka kuwa akan haqqin yarinyar nan, tunda Allah ya haɗa ku kake zalintar ta, anya kana da tausayi kuwa"


  "mummy don Allah kiyi haƙuri wallahi sai da ta amince muka biya ta sannan akai mata dashen"


 "wannan yarinyar me ta sani, da har zaku ce wani kun biya ta yanzu ɗan na wane na wacce tai dakon cikin ne ko na ƴar lelen taka ne"


 "mummy ƙwan badia ne"

"mummy ba nawa bane" na bata amsa

"amma ni alfarma ɗaya nake so a barni in kula da shi in dinga bashi nono in yaso idan na yaye shi sai badia ta karɓi abinta"


   Kallona mummy tayi sannan tace

"asmau ke yarinya ce har yanzu baki san ciwon kanki ba nan gaba zaki zo kiyi dana sani"


"mummy duk yadda Allah ya tsara bawa rayuwarsa haka zai yi ta" na bata amsa
 Nai ta mata daɗin baki akan maganar don bana son a jata da tsaho, ta yi mugun jinjina min sannan daga ƙarshe ta saka aka kira badiar sannan ta kuma kafa sharaɗin ni zan kula da babyn



 Sam badia bata damu ba, shima sabit ɗin sai ya nuna ya fi son hakan,


  Mummy itace ta dinga kula dani, ko da lkcn suna yayi a can wani hotel sukai sunan su, daga ni har mummy ba wanda ya je



  Amma ita da sabit da babyn sun sha hotuna kamar ba gobe, wallahi duk wannan abin da ake yi ko kaɗan a jikina be taɓa damuna ba sdon nasan akwai ranar ƙin dillance


yaro ya ci sunan bbm badia amma anace masa annur mummy tai faɗa sosai wai ai sunan daddy ya kamata a saka amma sam ba ai mara kara ba


  Kaji mummy wani ɗigimi




********************

*BAYAN SHEKARA ƊAYA*





 kamannin annur da sabit ya gama fitowa, sosai ga wayau kuma Sam baya yadda da badia, shegiyar ƙyuya gare shi kamar


  Daga ni sai ni, ko sabit in dai ba fita yaga zai yi da shi ba sam baya yadda ya ɗauke shi


  Sam badia bata damu ba, ita dai kawai burin ta taga an masa wanka an masa kwalliya tai ta ɗaukar shi a hoto ta na ɗora shi a dp, facebook da instag.


  Shima haka sabit ɗin yake sai dai in ban masa wanka ya ɗau gyara ba, nan zaku ga da sabit ɗin da badiar duk suna rige rigen ɗaukar a pic


Sam wai nuna so ko jan yaron a jiki badia bata san wannan ba, ko tashi yayi da safe ya tafi ɗakin ta sai dak kawai kaji tana ƙwala min kiran in zo in dauke shi in masa wanka



  Sam bata yadda ta ɗauke shi sai an masa wanka, wai ko yayi pupu ko fitsari sai dai kaji tana kirana inzo in cire masa



  Wani rashin *M* ɗin ma sai in yayi pupu a ƙasa kamar ta dake shi haka take, akwai randa mukai faɗa da ita akan shi,



   Ya shiga ɗakin ta ba diaper a jikin sa, sai yai mata pupu a kan gado, kawai zagin shi naji tana yi


  Da gudu na tafi ɗakin ta ɗaga hannu zata dake shi, da sauri naje na tare masa,


"haba anty yaro ne"
Harara ta bini da shi sannan tace

"ni ƙazanta ta yara ce bana so, zo ki kwashe kashin nan kije kiyi masa wanka"


  Tabbas ba ta san ciwon sa bane don wallahi da ta san ciwon sa da uwa tana cikin cin abincin ta ɗan ta zai yi pupu ta saki abinci ta wanke masa sannan ta zo ta ƙarasa




  Ita dai bangaren kayan sawa, kayan wasa, anan fa to kusan Rabin albashinta yaron take kashe mawa,



   Sai dai jawo shi ajiki ne dai batayi


    Ana haka wani zazzabi ya kama shi aiko sai ya kasance ni kaɗai yake yarda in dauke shi, hatta da sabit baya yarda da shi




 Anan ne wani sabon rashin mutunci ya tasowa badia inda tace ita Sam atafau ayaye yaro abata ɗanta, saboda gaskiya ita bata yadda ba tana uwar yaro amma sam be shaƙu da ita ba



  A zuciyata nace me kike masa da zai sa shakuwa da ke, don kayan wasan da kike sai masa sani yayi shi yaro


  Tuburewa nayi nace sam be isa yaye ba sai ya ƙara watanni, abi kamar wasa har sabit ya saka baki shima sai ya goyi bayan badia wai shima baya jin daɗin yadda annur ɗin yake masa



  Ban musa ba ganin bana son sa'insa akan shi ya sa na miƙa mata shi nasan ko kukan sa na dare ya sata dole ta dawo min da shi



  Ai kuwa tana karɓar sa daya tsanyare da wani kukan ko a jikinta ni kuwa wannan kukan jin sa nayi kamar ana yankan sa har cikin zuciyata naji



  Ɗakina na shike ina jin sa yana cewa ```maaa``` da yake haka yake cemin don bakin sa ba wani buɗewa yayi ba



   Aiko ko awa daya batayi da daukan shi ba naji ana ƙwallamin kira a ruɗe na fito inda naga yaro shame shame ahannun sabit kamar marar rai


   Ruwa ne a hannun badia tana shirin sheƙa masa na karɓa a hankali na yayyafa masa yana farfaɗowa ya fara ```maaa```  ```maaa```



"na'am baby na" na amsa masa ɗagowa yayi ya kalle ni, duk da dai jikin sa ba ƙwari amma a hakan ya ɗago ya taho wajena da saurin sa ya rungume ni



   Sosai na matse ɗana a jikina sai ajiyar zuciya yake saki, wanda hakan ya sa zuciyata ta karye naji hawaye ya cika min ido na



 Bani ba hatta sabit sai da jikinshi yayi sanyi ni ko hawaye suke sulalo min ganin yadda yaron cikin ɗan lokaci kadan ya fita hayyacin shi amma da ganina yawani lafe ajikina harda ƙara rungumeni


  Bacci ne ya kwashe shi a kafaɗa ta ina ɗan jijjigashi ko da yai baccin sai na sauke musu shi


 "zo ki ɗauke shi" inji sabit


"ya ci gaba da zama a wajen ki har sai ya saba da badiar sai ya koma, ke kuma dia ya kamata ki dinga samun time kina spending da shi mana don ya saba da ke kooo" ya faɗa da sigar lallashi


"ok shike nan zan duba"


  Wuce wa nai da shi ɗakina muka kwanta, kallon shi nayi sannan nace

"annur ɗana ina alfahari da kai, kuma wallahi da kai sai na nuna wa duniya cewa ni asmau ƴar halak ce"



  ********************


  Tun daga lkcn badia take shigowa ɗakina wai don annur ya fara sabawa da ita, amma ko ta shigo tana manne da wayar ta tana chatting shi kuma daya ganta to ahike nan ya liƙe min kenan har sai ta fita



  Sam wannan method ɗin be yi ba haka naji tana faɗawa sabit, sai suka tsiri fita da shi yawo, kunsan yaro da son yawo, wannan ne ma sa ya ke ɗan yadda ta ɗauke shi in dai har ya ganta da mayafi ko hijab amma da ta zauna shikenan sai ya fara ```maaam``` yana kuka



*******************
[5/4, 7:14 PM] ‪+234 806 925 8300‬: 🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)




 🤲🏻 *ALLAHUMMA BALIGNA RAMADAN BIL IMAN*🤲🏻




   P⃗a⃗g⃗e⃗  23

 


  Bayan kwana biyu sai ga mummy nai murnar ganin ta sosai har da saƙo na daga anty fannah Allah sarki anty fannah nayi kewar ki sosai



  Mummy tai ta faɗa wai badia mahaifar ta bata da ƙwari kuma gashi ta kuma samun ciki amma ta ƙi zama ta kula da kanta



  ba wanda ya tanka sai dai lallashi da suke ta bata wai zasu kula da cikin, ni dai ina gefe ina kallon ikon Allah wannan rayuwa wato akwai abin mamaki sosai



  Kwanan mummy biyar sannan ta kama hanyar gida, kamar nayi kuka ranar da ta tafi, don kuwa yanzu zan koma rayuwa ni kaɗai


   A hankali cikin ya ci gaba da girma har lkcn da zai zo duniya yayi


 Rannan da yamma sai ga mmn badia tazo gidan ita da wata mata, ɗakin badia suka sauka sam ban sam me ya kawo su ba amma kuma bini bini a bini da ido



  ranar wata talata da safe na tashi da nakuda, tun ina yi ni kaɗai har dai dana ga abin bana ƙare bane na fita, ina fita naci karo da wannan matar zata shigo ɗakina


 "kar dai naƙuda kike yi ƴannan" gyaɗa mata kai nayi don bazan iya magana ba sabida ciwon da ke damuna



 Sabit ta kira shima ya fito jiki si ɓari yake yi yaji ina labour, asibiti muka je, inda aka shigar da ni labour room Awa uku cur na ɗauka sannan Allah ya sauke ni lfy, ajiyar zuciya na saki dana ji Allah ya raba ni da wannan cikin lfy



    Ɗagowa nayi na kalli yaron.........  Fari tas da shi kana ganin shi kaga sabit


  Miƙo min shi nurse ɗin tayi na karɓi kayana na tsaya ina kallon sa, godiya nai wa Allah daya sani ina da rabon ganin jini na



  Sai da nurse ɗin gama gyara ni sannan ta karɓi babyn don gyara shi, shima, ko da aka gama shirya shi zata fita da shi na kira ta na karɓi abuna



  Ƙare masa kallo nayi kamar sabit yayi kaki ya yar addua nayi masa sosai, na so ace yaron kamata ya ɗauko


  Ko kuma ace baƙi ne amma ba komai duk abinda Allah yaso haka zan karɓa, kuma ina fatan ya zama me jin ƙan iyaye


   Ɗa na yana hannuna na fito daga labour room, da sauri suka ƙaraso tare da karɓar sa mmn badia ce ta fara karɓar sa


 "namiji ne ko mace" ta tambaye ni kalmar tai bala'in ƙona min rai ba Allah ya raya ba komai amma wai ita burin ta namiji ne ko mace


 sabit ne ya karɓi shi shima daga gani maganar tai masa ciwo, karɓar sa kawai yayi ya wuce ɗakin da aka bamu na hutu


  Addua ya dinga masa, ina amsa wa da amin, duk wannan abun da muke ita uwar ɗan bata sani ba don sammako tayi ta tafi kwatano wai ta tafi siyo kayan da zata saka da suna



  Sai da ya gama masa addua sannan mmn badia ta kuma karɓar sa ta buɗe masa diaper inda ta gano namiji ne



  Nan da nan murna kamar me, har wani ƙara ruƙunƙume shi take yi, mijinta ta kira ta shaida masa badia ta haihu,


  Shima yai mata murna sannan yace a bawa badiar, nan ta hau ƙarya wai badiar bacci take yi

  Mummy sabit ya kira yace mata badia ta haihu ita ma mummyn tai murna sannan tace a bawa badiar tai mata barka shima duk ɗaya yace tana bacci



  Haka suka dinga kiraye kirayen waya suna shaidawa badia ta haihu, ni dai kallo ne nawa


  Zuwa can baby ya fara mutsu mutsun yunwa, dabino sabit ya tauna ya lasa masa a bakin sa sannan aka bishi da zam zam



    Wajen azahar aka sallame daga asibitin muka kama hanyar gida, wai don renin hankali babu wanda yake ta kaina ni dana haihun sai ta baby,


  Ɗakina na shige na samu na watsa ruwan zafi a jikin sannan na fito kitchen na ɗaura indomie na ci na ƙoshi sannan na wuce ɗaki na na kwanta



   Wajen ƙarfe 06:00 na yamma sai ga mummy, ina kitchen ina dafa shayi
 Sai ga mummy, da sauri naje na tare ta

"mummy ashe kina tafe" tsayawa tayi tana kallona


"ya naga kamar ma kece me jegon duk kin wani ɗashe"

  Ta faɗa tana kai hannun ta kan fuska ta, murmushi na saki sannan naja hannun ta zuwa ɗakin badia

"zo muje kiga jikan naki"


  Bina tayi, da sallama na shiga, suna zaune a bakin gado shi kuma babyn yana cikin gadon sa na jarirai yana ta baccin sa



A razane suke da suka ga mummy, sai suka fara kame kame


 "hjy fatima yaushe kika ƙaraso, muje falo mu zauna yaron yana bacci" inji mmn badia


  "ni da nazo ganin baby sai ace min yana bacci, ina ita mejegon"


Tsuru tsuru sukai, nidai tunda naga na haɗa su sai nai ficewa ta na barsu


  Ɗakin nawa naji an turo ƙofar, ashe mummy ce ta shigo, sai da ta ƙaraso da sannan na bata wurin zama


 "har yanzu sabit ɗin basu dawo bane ko dai wani abun ne ya samu badiar"


  Ni dai ban tanka mata ba saboda sam ban san ma ina ta dosa ba,


 "ni wallahi duk a gajiye nake, nace musu su shirya gobee mu koma abuja ai suna acen dama dalilin zuwa na kenan"


  Ni dam ban tanka mata ba don kuwa a gaskiya na fara kewar ɗana, don haka sai nai mata shiru,


  Mara ta naji ta fara murɗa min, mitsss sai yanzu na tuna sam ban ma sha magani ba, miƙewa nayi don in ɗauko magani sai naji mummy tana cewa


"asmau lfy naga kina tafiya kamar kece kika haihun, gashi kuma duk kin ɓata zanin jikin ki"


Juyawa nayi don inga inda na ɓata ban ɗago ba sai ganin mata nayi kusa da ni


"asmau ke kika haihu ko badia"

 Tsare ta nayi da idona wanda a yanzu suka ciko da hawaye, ɗago min fuskar tawa tayi


"asmau ke kika haihu, ba badia ba" gyaɗa kaina nayi hawaye yana zuba a ido na


 "haba biri yayi kama da mutum" inji mummy takaici ne ya kamata sai ta kama hanyar fita



  Ban san me tace musu ba sai gata da babyn,

"ungo shi bashi nono ya sha ki gama in gyara ki, wallahi idan sabit ya dawo yau sai yaga ɓacin raina wanna wane irin zalinci ne"



  Karɓar babyn nawa nayi na rungume shi sannan na zauna na fara bashi nono kamar dama yunwa yake ji haka ya karɓa ya fara tsotsa



 Muryar badia muka ji a bakin ƙofa tana masifa


"ban gane ɗan ta bane yaushe ya zama ɗanta don kawai ta rene shi a cikin ta sai ace ɗan ta wallahi bazai sha nonon ta ba, na riga na gama booking nurse ɗin da zata dinga kular min da yaro" ta faɗa tana shigowa a fusace da zummar karɓar mummy



Mummy ce tace

"wallahi kika sake kika katse masa wallahi tallahi sai na saɓa miki"


"mummy ya za ayi jini na ya sha nonon ta"


"ya akai ya zama jininki"


  Nan badia ta kwashe komai ta faɗa wa mummy, bata gama ba mummy ta fashe da kuka, adai dai lkcn sabit ya shigo



 Ingiza badia yayi ya kora daga ɗakin, mummy kuwa kuka ta dingayi,ba irin lallashin da sabit be mata ba amma taƙi shiru


 Shima sai ya fashe mata da kuka

"anya sabit kana tuna ranar da Allah zai kama ka kuwa akan haqqin yarinyar nan, tunda Allah ya haɗa ku kake zalintar ta, anya kana da tausayi kuwa"


  "mummy don Allah kiyi haƙuri wallahi sai da ta amince muka biya ta sannan akai mata dashen"


 "wannan yarinyar me ta sani, da har zaku ce wani kun biya ta yanzu ɗan na wane na wacce tai dakon cikin ne ko na ƴar lelen taka ne"


 "mummy ƙwan badia ne"

"mummy ba nawa bane" na bata amsa

"amma ni alfarma ɗaya nake so a barni in kula da shi in dinga bashi nono in yaso idan na yaye shi sai badia ta karɓi abinta"


   Kallona mummy tayi sannan tace

"asmau ke yarinya ce har yanzu baki san ciwon kanki ba nan gaba zaki zo kiyi dana sani"


"mummy duk yadda Allah ya tsara bawa rayuwarsa haka zai yi ta" na bata amsa
 Nai ta mata daɗin baki akan maganar don bana son a jata da tsaho, ta yi mugun jinjina min sannan daga ƙarshe ta saka aka kira badiar sannan ta kuma kafa sharaɗin ni zan kula da babyn



 Sam badia bata damu ba, shima sabit ɗin sai ya nuna ya fi son hakan,


  Mummy itace ta dinga kula dani, ko da lkcn suna yayi a can wani hotel sukai sunan su, daga ni har mummy ba wanda ya je



  Amma ita da sabit da babyn sun sha hotuna kamar ba gobe, wallahi duk wannan abin da ake yi ko kaɗan a jikina be taɓa damuna ba sdon nasan akwai ranar ƙin dillance


yaro ya ci sunan bbm badia amma anace masa annur mummy tai faɗa sosai wai ai sunan daddy ya kamata a saka amma sam ba ai mara kara ba


  Kaji mummy wani ɗigimi




********************

*BAYAN SHEKARA ƊAYA*





 kamannin annur da sabit ya gama fitowa, sosai ga wayau kuma Sam baya yadda da badia, shegiyar ƙyuya gare shi kamar


  Daga ni sai ni, ko sabit in dai ba fita yaga zai yi da shi ba sam baya yadda ya ɗauke shi


  Sam badia bata damu ba, ita dai kawai burin ta taga an masa wanka an masa kwalliya tai ta ɗaukar shi a hoto ta na ɗora shi a dp, facebook da instag.


  Shima haka sabit ɗin yake sai dai in ban masa wanka ya ɗau gyara ba, nan zaku ga da sabit ɗin da badiar duk suna rige rigen ɗaukar a pic


Sam wai nuna so ko jan yaron a jiki badia bata san wannan ba, ko tashi yayi da safe ya tafi ɗakin ta sai dak kawai kaji tana ƙwala min kiran in zo in dauke shi in masa wanka



  Sam bata yadda ta ɗauke shi sai an masa wanka, wai ko yayi pupu ko fitsari sai dai kaji tana kirana inzo in cire masa



  Wani rashin *M* ɗin ma sai in yayi pupu a ƙasa kamar ta dake shi haka take, akwai randa mukai faɗa da ita akan shi,



   Ya shiga ɗakin ta ba diaper a jikin sa, sai yai mata pupu a kan gado, kawai zagin shi naji tana yi


  Da gudu na tafi ɗakin ta ɗaga hannu zata dake shi, da sauri naje na tare masa,


"haba anty yaro ne"
Harara ta bini da shi sannan tace

"ni ƙazanta ta yara ce bana so, zo ki kwashe kashin nan kije kiyi masa wanka"


  Tabbas ba ta san ciwon sa bane don wallahi da ta san ciwon sa da uwa tana cikin cin abincin ta ɗan ta zai yi pupu ta saki abinci ta wanke masa sannan ta zo ta ƙarasa




  Ita dai bangaren kayan sawa, kayan wasa, anan fa to kusan Rabin albashinta yaron take kashe mawa,



   Sai dai jawo shi ajiki ne dai batayi


    Ana haka wani zazzabi ya kama shi aiko sai ya kasance ni kaɗai yake yarda in dauke shi, hatta da sabit baya yarda da shi




 Anan ne wani sabon rashin mutunci ya tasowa badia inda tace ita Sam atafau ayaye yaro abata ɗanta, saboda gaskiya ita bata yadda ba tana uwar yaro amma sam be shaƙu da ita ba



  A zuciyata nace me kike masa da zai sa shakuwa da ke, don kayan wasan da kike sai masa sani yayi shi yaro


  Tuburewa nayi nace sam be isa yaye ba sai ya ƙara watanni, abi kamar wasa har sabit ya saka baki shima sai ya goyi bayan badia wai shima baya jin daɗin yadda annur ɗin yake masa



  Ban musa ba ganin bana son sa'insa akan shi ya sa na miƙa mata shi nasan ko kukan sa na dare ya sata dole ta dawo min da shi



  Ai kuwa tana karɓar sa daya tsanyare da wani kukan ko a jikinta ni kuwa wannan kukan jin sa nayi kamar ana yankan sa har cikin zuciyata naji



  Ɗakina na shike ina jin sa yana cewa ```maaa``` da yake haka yake cemin don bakin sa ba wani buɗewa yayi ba



   Aiko ko awa daya batayi da daukan shi ba naji ana ƙwallamin kira a ruɗe na fito inda naga yaro shame shame ahannun sabit kamar marar rai


   Ruwa ne a hannun badia tana shirin sheƙa masa na karɓa a hankali na yayyafa masa yana farfaɗowa ya fara ```maaa```  ```maaa```



"na'am baby na" na amsa masa ɗagowa yayi ya kalle ni, duk da dai jikin sa ba ƙwari amma a hakan ya ɗago ya taho wajena da saurin sa ya rungume ni



   Sosai na matse ɗana a jikina sai ajiyar zuciya yake saki, wanda hakan ya sa zuciyata ta karye naji hawaye ya cika min ido na



 Bani ba hatta sabit sai da jikinshi yayi sanyi ni ko hawaye suke sulalo min ganin yadda yaron cikin ɗan lokaci kadan ya fita hayyacin shi amma da ganina yawani lafe ajikina harda ƙara rungumeni


  Bacci ne ya kwashe shi a kafaɗa ta ina ɗan jijjigashi ko da yai baccin sai na sauke musu shi


 "zo ki ɗauke shi" inji sabit


"ya ci gaba da zama a wajen ki har sai ya saba da badiar sai ya koma, ke kuma dia ya kamata ki dinga samun time kina spending da shi mana don ya saba da ke kooo" ya faɗa da sigar lallashi


"ok shike nan zan duba"


  Wuce wa nai da shi ɗakina muka kwanta, kallon shi nayi sannan nace

"annur ɗana ina alfahari da kai, kuma wallahi da kai sai na nuna wa duniya cewa ni asmau ƴar halak ce"



  ********************


  Tun daga lkcn badia take shigowa ɗakina wai don annur ya fara sabawa da ita, amma ko ta shigo tana manne da wayar ta tana chatting shi kuma daya ganta to ahike nan ya liƙe min kenan har sai ta fita



  Sam wannan method ɗin be yi ba haka naji tana faɗawa sabit, sai suka tsiri fita da shi yawo, kunsan yaro da son yawo, wannan ne ma sa ya ke ɗan yadda ta ɗauke shi in dai har ya ganta da mayafi ko hijab amma da ta zauna shikenan sai ya fara ```maaam``` yana kuka



*******************
[5/4, 7:27 PM] ‪+234 703 450 4161‬: 🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)




*HIKIMA WRITERS ASSO.*




   P⃗a⃗g⃗e⃗ 24 🌹





 Renon ciki na nake yi hankali na a kwance ga ɗana a kusa dani, sam su sabit basu tafi da shi ba nima na so hakan



  Duk wani siyayya mummy tayi haihuwar kawai muke jira, amma saɓanin saɓanin cikin annur wannan cikin girma gare shi sosai da sosai


  Har anty fannah tana cewa ko dai ƴan biyu ne, ko da muka je scanning twins ɗin ne kuwa


  Muna dawo wa anty fannah ta faɗawa mummy, bashiri mummy ta kwashi anty suka tafi kasuwa aka sake sabuwar siyayya



   Cikina yana da wata 8mths sabit suka dawo shida badia, sam duk wannan abunda ake yi badia bata san da cikin ba



   Tun da suka zo bamu haɗu da sabit ba, dana ji alamar zai shigo sai in gudu ɗaki duk wannan abun Allah bai taɓa haɗa mu da shi ba



 Kwanan su uku da dawo wa ya badia ta zo da kanta lkcn ina ɗaki ina bacci ta ɗauke annur, ita kanta badiar bata san da cikin ba


   Ko da na tashi, sai ban ganshi ba, sai na tambayi mummy yana ina sai mummy tace min ai badia ce ta ɗauke shi


  Ba badiar ba hatta mummyn ta bani haushi yadda har ta bar badia ɗaukar sa bayan tasan ƙyuya gare shi



 "mummy bari inje in ɗauko shi kin san halin annur idan ya tashi be ganni ba"


"to shike nan ni sai da na hanata sai tace wai sabit ne yace ta ɗauke shi"


 Ficewa nayi daga part ɗin na doshi part ɗin sabit da tsohon ciki na, a hankali nake tafiya don kuwa cikin yai girma dayawa fiye dana annur


 Tun kafin in ƙarasa ciki nake jin kukan yaron nan yana kira na, sai na ƙara ɗaga ƙafa, da sallamat na shiga tana zaune akan kujera tana kallo shi kuma yana zaune a ƙasa a kusa da ƙafar ta yana kuka



  Sallamata ce ta sata juyowa, ai kuwa ta ci karo da ƙaton cikina, wani ashar ta daddage ta ɗura sannan ta ƙaraso inda na ke kamar wacce zata dake ni


"uban waye ya miki cikin nan"

  Kallon ta na tsaya ina yi yadda take huci kamar zaki, sai nishi take yi kamar wacce take shirin yin dambe


 "tambayar ki nayi uban waye yayi miki cikin nan" ban kula ta ba saboda tsayawa ma kula ta ɓata lkc ne ai ta san zaman aure nake yi


  Wuce ta nayi na ƙarasa kusa da annur zan ɗauko shi, ji nayi ta jawo ni sai saukar mari naji a fuskar ta, kammm bata ajiye ba nima na kai mata bama ɗaya nayi mata biyu


  Sannan nace mata

 "kina san ki san wanda yai ciki tooo mijina ne, kafin wannan ma na taɓa ɓari, kafin in haifi annur banza kawai wacce bata san inda yake mata ciwo ba"


   Ban ankara ba kawai sai jin matar nan ta hau ni da kokawa tana ihu tana kuruwar

"ƙarya kike yi me sabit zai yi da ke" faɗa sosai mukai da ita


 Kasancewar cikin da ke jikina yai min nauyi ya sata samun galaba akai na hai ta kaini ƙasa ta shaƙe ni tare da cewa


"wallahi duk macen da tace zata haihu da sabit sai na kashe ki na kashe abinda ke cikin naki inga abinda za ai min tunda ba wani gata gare ki"



  Duka ni kuma na dinga mata inda tana ta ƙoƙarin haye min ruwan ciki Allah ya jeho anty fannah, da saurin ta ta zo ta hankaɗe badiar daga kaina



 Tafiya tayi taje ta daki bango wanda har sai da kanta yai ciwo amma sam bata daddara ba kafin anty fannah ta ɗago ni tuni ta yo kaina



 Wannan karon da ƙarfi anty fannah ta hankaɗa ta sai kuwa ta faɗa kan annur inajin yaro na ya ƙwalla wata irin ƙara, hankali na ne ya tashi na miƙe da ƙyar na yi wajen sa amma anty fannah ta hanani ta janye ni muka bar part ɗin


  Hankalina sam ba a jikina yake ba naso in san me ya samu yaro na amma anty fannah ta hanani



  Part ɗin mummy muka nufa anty fannah tana bata lbrin yadda ta ganmu ni kuma ina ce mata annur fa yaji ciwo


"ai dole sabit ya san wannan rashin hankalim da matar sa tayi" inji mummy


  "Baki ciwo ba ko" girgiza kaina nayi,

"amma mummy annur kamar ya ji ciwo faaa"

"ina ruwanki da wani annur duk kin bi kin ɗaga hankalin ki akan yaro bayan uwar sa ba sanki take ba"


 Kuka na saka musu ni kaɗai na san abinda yake damuna akan irin abinda sabit yake min gaskiya na kai matuƙar ƙarshe a haƙuri



   Ganin ina kuka yasa mummy tace min in daina sanna in shiga ɗaki na in kwanta in huta tunda ba abinda ya same ni ita kuma badiar bari sabit ɗin ya dawo za ta ja masa kunne ya faɗawa matar sa ta fita hanya ta



   Anty fannah ce ta taimaka min duk da bana jin komai har ɗakin nawa, ban daina de kuka ba, abin ya min ciwo, anty fannah ce ta zauna kusa da ni tana bani haƙuri


 "wallahi anty fannah haƙuri na ya ƙare na zo ƙarshe wallahi sai na nuna wa duniya wacece mahaifiyar annur"


 "ban gane ba"


Nan da nan na hau mata bayanin yadda aka samu annur, sai da naga tas sannan ta hau ni da faɗa wai nayi wauta ai duk inda muka je bani da gaskiya, tunda ga yadda aka haife shi har kuɗi na karɓa


  Kuka na dinga mata ni dai a gaskiya ɗana nake so a hannuna, kukan da nake mata ne ya sa jikin ta yin sanyi, kuka wiwi haka na dinga mata



"yanzu asmau ya kike son in miki"


"ni wallahi in ba barin gidan nan nayi ba wallahi zan iya mutuwa don na gaji da matsalar gidan nan" kuka na dinga mata



   Kasancewar tana sanyi ya sa ita ma ta saki kuka, muka haɗa kai muka dinga kukan,


"don Allah anty fannah ki taimaka min"


  Kuka ne ya kuma ƙwace mata, mu kai me isar mu muka lallashi sannan ta hau ni da nasiha, ita dama anty fannah haka take sam bata da zafi bata taɓa ce min rama ba



 "asmau wannan matsalar ke kika jefa kanki a ciki don haka ki cire annur a ranki ki mai da hankalin ki akan wannan Allah ya raba lfy"


 "anty annur ɗana ne don me zaki ce in ƙyale shi"


 "ba wai nace ki ƙyale shi har abada ba, amma 4 now ki ƙyale shi"


 "wallahi anty na gaji da zaman gidan nan, don Allah ko wani gurin ne ki kai ni in huta in samu in sauka lfy kafin in haihu"


"in banda abin asmau ina kika taɓa jin gidan miji yai zafi, komai aka yi miki haƙuri zakiyi, kuma in shaa Allah wataran zai zama tarihi, dukkan me haƙuri wataran dole ya ga amfanin hakurin"


  Kuka na dinga yi tana bani haƙuri tare da cewa ita ba inda zani kawai in zauna in shaa Allah akwai ranar ƙin dillanci, amma don Allah sai yaushe ne zan ga wannan lkcn Lallashi na ta dinga yi tun ina kuka har na zo na haƙura amma wallahi daga yanzu bazan kuma ɗaukar cin kashin shi ba



  Sai da ta tabbatar na haƙura na kwanta sannan ta tafi, kuka na kuma fashewa shike nan ni ke nan a haka zan ƙare banni da wanda zai kare min ya Allah ka kawo min ɗauki, bacci ne ya kwashe ni




 ********************



 Sabit yana wajen abokan sa yaji call ɗin badia tana kuka wai ya zo yaga asmau da fannah sun haɗa su ita da annur sun musu duka


  A guje ya garzayo ya zo ya tarar da su cikin jini, shi ma kanshi annur ɗin ya kuje a goshin sa




 Ita kuma ta ciwo a ƙafar ta yana ta jini, tana ganin shi ta fashe masa da kuka


"sabit kaga abinda asmau tai min, wai don kawai na ganta da ciki na tambayeta na waye shi ne tace nata ne wai zuwa tayi ta kashe mu ni da annur tunda yanzu ta kusa haihuwa bata son ƴaƴan ta su samu ɗan uba"


  Sam sabit be fahimci abinda badia take cewa ba shidai kawai kallon annur yake wanda yake kwance a yashe goshi na ta jini


  Ɗaukar shi yayi ya shiga da shi toilet ya wanke masa sannan ya fito da shi ya gyara masa ciwon ya saka masa plaster sannan ya ajiye shi


 Itama badiar first aid box ɗin ya ɗauko ya gyara mata ciwon nata wanda daga gani wuƙa ce ta yanke da ita


  Takaici ne ya hana sabit magana, yana gama gyara su ya shirya su sai da ya tabbatar sun kimtsu sannan ya fito daga part ɗin nasan directly part ɗin mummy ya taho a fusace





 Ina kwance kawai naji an janyo ni daga kan gadon na faɗo ƙasa sannan ya shaƙe min wuya tare da miƙar da ni sama sannan sauke min yatsun sa guda biyar a kan fuska ta



  Tuni na watstsake na ware ina kallon sa

"sabida baki da mutunci har ki shiga part ɗina ki yi mata ta illa sannan ki cutar min da ɗa........


  Be gama ba sai ga mummy ta shigo


"wallahi ko ka sake ta ko in ɓata maka rai"




 Wancakar da ni yayi ya fice in da mummy ta ɗago ni sannan tace min

" kiyi haƙuri komai me wucewa ne"

  Wucewa wallahi an gama da ni haƙuri na ya ƙare anzo wani abu wai shi d end


  Miƙewa nayi na wuce part ɗin anty fannah ina mata kukan ta bani aron kuɗi zan tafi ni na gaji da wannan bala'i


 Ta so ta lallashe ni amma da ta ga yadda na rufe ido na sai tace min,

"to yanzu in kika tafi ina zaki"


"wallahi ko ina ne ni dai in tafi kuma wallahi bazan bar musu ɗana ba wallahi da abina zan tafi kuma wallahi ko ki taimaka min ko kuma in tafi ko banni da ko ƙwandala"


  Jawo ni tayi sannan ta zaunar da ni kusa da ita,

"kwantar da hankalin ki akwai gidan da zan kaiki ki zauna wallahi sai sabit ya gane kuren sa sannan zan dawo da ke"


 Wani sanyi naji ya ratsa min zuciya, sannan nace mata

"to yaushe zamu"


"haba so kike a gano ni na fita da ke, ai ke kaɗai zaki fita da annur akan zaki kaishi asibiti nima idan na fita sai ku haɗu, gidan yayana ne shi da matar sa sai kiyi zaman ki a can har sai yadda hali yayi"


  Daɗi naji kamar me na kama hanyar part ɗin mummy na fara haɗa kayana



 Duk wannan abun da ake yi mummy bata sani ba, sai dana gama haɗa kayan tas sannan na ɗauko su na kawo su part ɗin anty fannah



  Itace ta sato min annur sannan muka kama hanyar barin gidan, ƴar tafiya mukai kaɗan sannan muka iso gidan da zamu,



 Amaryace ashe na ɗauka ma babba ce kasancewar dare ne yasa san anty fannah bata daɗe ba ta kama hanyar gida


  Ɗaki guda aka bani wanka nai wa ɗana sai alkcn naga cieon goshin nasa

"Allah ya saka maka annur"


  Sallah kawai nayi na kwanta sai bacci


  *******************


  Sai sha ɗaya na dare sannan sabit ya dawo gida yana can yana ta fafutukar yadda zai  wa asmau rashin mutunci so yake yi tana haihuwa ya kwashe abinda ta haifa ya kai gidan marayu wallahi bazai zauna da baƙaƙen ƴaƴa ba



  Yana shigo wa gidan directly ɗakin annur ya shiga yai mamakin daya ga baya nan don haka sai ya ɗauka ko yana tare da badiar ne


  Sai da yayi wanka ya gama komai sannan ya shiga ganin shi kafin ya kwanta, badia tana ta sharar baccin ta amma sam be ga annur a kusa da ita ba



  "badia badia ina annur yake"

Cikin magagin bacci tace

"yana ɗakin sa da wuri yai bacci na kwantar dashi"

 "ban gane ba yanzu daga ɗakin yake sam baya nan"


Miƙewa tayi itama tare da yin hanyar waje domin taje ɗakin annur ɗin amma wayam kamar sabit ɗin ya faɗa



Nan da nan hankalin su ya fara tashi, kafin me wannan tuni gidan ya ɗauka asmau ta ɗauke annur ta gudu


  Mummy sabit hankalin su ya fi tashi, fara neman su akai abin takaici ma shine sam ba a san lkcn da ta tafi da su ba


  Sabit kamar yai hauka, kasa zama yayi inda ya shuri motar sa ya fice neman annur don ita asmaun sam baya ta tata duk inda taje ai dole wataran ta neme shi ko don abinda take ɗauke da shi


 nema aka dinga yi har tsakar dare sannan mummy ta kira sabit ya dawo gida


  Da kuka ya dawo mata

"wallahi mummy sai yarinyar nan ta gane bata da wayo, wallahi sai na haɗa ta ƴan sanda ta sace min ɗa na ta gudu"


  Kamar zararre haka ya dinga magana lallai sabit ya shiga tashin hankali, ko da mummy ta nemi ya kwanta ƙin kwanciya yayi a haka ya kwana yana ta trying number ta


  Da asussuba ya miƙe ya nufi part ɗin sa yana zuwa ya tarar badia itama ta shirya


"wallahi sabit sai mun shiga kotu da yarinyar nan sai ta gaya min menene dalilin ta na sace min ɗa"


  Tanka ta be yi ba saboda yanzu haushin ta yake ji duk ita ce ta jawo sam bata san ciwon yaron ba wai har kana gidan amma a sace yaro sam bata sani ba



  Kaya kawai ya canza yana ji tana waya tana faɗa wa mmn ta asmau ta sace annur, takaici ne ya ishe shi yadda yake ta jinta tana ta zage zagen sai kace bamagujiya


  Yana canza kaya ya fito zai fita

"sabit ina zaka na ga ka shirya wallahi ko asmau ta dawo min da ɗana sai munyi sharia da ita akan sace min ɗa da tayi sai kotu ta raba su wallahi sai na saka an mana katangar ƙarfe tsakanin mu da ita, duk babu muna fiki sai kai ko kunya baka ji ƴar cikin ka kake kwanciya da ita saboda ka zama sallamamme wallahi kaji kunya"


  Har ya fice sai ya dawo, wani kyakkyawan mari ya kwaɗa mata sannan ya juya yai ficewar sa, yana jinta tana zagin sa ta uwa ta uba amma sam ba ta ita yake shi dai kawai burin sa ya ga ɗan sa



  Ɓangaren mummy ya shiga ya saka mata kuka, lallashin sa ta farayi sannan ta sanar da shi ai ta aika a gano musu ko asmau taje garin su


  Kuka ya dinga mata wiwi

" mummy wallahi asmau ta cuceni ta raba ni da farin ciki na annur shine komai nawa shine farin cikina ya zanyi idan banganshi ba don Allah mummy ki taimaka min, don Allah mumy ki cece ni ki dawo min da ɗana"


  Tausayi ɗan nata ya bata, gaskiya asmau bata kyauta ba duk da dai duk abinda sabit yayi mata ai bai kamata tayi masa haka ba



  Sallamar hjy munnira suka ji, da sauri mummy ta tashi ta tare ta sabit wanda yake zaune yai shaɓe shaɓe da hawaye ya rarrafa yaje wajen su


"don Allah ina ɗana yake" ya tambaya


Mummy ce ta daka masa harara gabaɗaya sabit ya susuce

"wallahi hjy har garin su aka je bata je, babu wanda kuka san ta sani a garin nan, wallahi tunda kika kirani jiya wallahi hankalina yake a tashe na rasa kwanciyar hankali yarinyar nan a dalilina aka san ta kuma ace ta ɗauki ɗan masu gida ta gudu da shi wallahi tun jiya jiki na yake ɓari"


  "wallahi hjy na san bata wajen ki, asmau ce tayi wauta sosai" inji mummy


 kuka sosai sabit ya saki kamar wani ƙaramin yari, kunya ce ta rufe mummy kamar ta nutse ƙasa sam be ji kunyar hjy munnira ba, kun san tsakanin ɗa da uwa tun tana masa faɗa akan kukan


  Har ya karyar mata da zuciya, ita ma sai  ga hawaye, hjy munnira sai ta saki baki tana bawa uwa da ɗa haƙuri



   Suna cikin wannan halin ne sai ga ƴen uwan badia nan sun shigo
[5/4, 7:27 PM] ‪+234 703 450 4161‬: 🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)




*HIKIMA WRITERS ASSO.*




   P⃗a⃗g⃗e⃗ 25 🌹








 Da masifar su suka shigo

"wallahi sai an fito mana da ɗan mu" yayar badia ce hauwa a gaba tana masifa tana ƙarawa


  A zaune suka ga mummy da sabit sun zuba uban tagumi suna sharɓe kuka

 "badia wallahi baki sa ar miji ba, ace namiji da kuka ke kuma kiyi me" wannan maganar ta ƙonawa mummy rai sai ta tanka


 Aikuwa nan da nan aka hau zage zage, mmn badia ce me cewa


"wallahi sai mun kai yarinyar nan kotu sai alƙali yai mata munmunan hukunci, wallahi sai tayi zaman gidan yari, ku ma baku tsira ba wallahi sai an ƙwatar wa badia ƴancin ta a gidan nan kun mai da ita baiwar ku"


   Faɗa sosai shi dai sabit yana zaune ya kasa taɓuka komai yana jin yadda ƴan uwan badiar suke ci masa mutumci duk da dai yana ganin laifin su amma asmau ta fi kowa ƙona masa rai


  Cikin hukuncin Allah sai ga muktar wan sabit shi ya shigo yai musu jan wuya sannan suka haƙura suka tafi akan su jira kiranye daga court

"kuma wallahi idan court ta karɓar mana ɗan wallahi ya bar gidan nan ke nan har abada tunda dai baku iya kula da shi ba har kukai sake wata yar aiki ta sace shi wallahi annur ya bar hannun ku har abada"
 Injimn badia ta faɗa tana yin waje



  Sabit kara fashe wa yayi da kuka

"don Allah mummy ina zanga asmau wallahi yanzu bazan mata komai ba don Allah ta dawo min da ɗana wallahi na yafe mata wallahi na daina yi mata duk abinda nake mata, wallahi ina son annur sosai wallahi bazan iya rabuwa da shi ba"


  "kai sabit wane irin mutum ne kai kamar ba namiji ba ka zauna sai kuka kake tayi, ita kuma mummyn tace me" inji muktar

 "don Allah muktar kar ka bari a ƙwace min annur wallahi ina son ɗana" ya faɗa yana me riƙe ƙafar muktar ɗin


 "wai mummy me yasa yarinyar nan ta ɗauke annur ɗin ne, ko faɗa suka yi, in banda abinta ai ko faɗa kuka yi ba kya ɗauki ɗan da ba naki ba" muktar ya tambaya


  Sam mummy sai ta kasa cewa komai don bata ma san ta ina zata fara ba, sabit ma shiru yayi


******************


 Fannah tana ɗakin ta suna waya da asmaun tana faɗa mata yadda gidan ya rikice, sam ko a jikin ta asmau bata ji komai ba, ita burin ta ma Allah ya sauke ta lfy wallahi ƙarawa gaba zatayi da ƴaƴan ta taje ta nemi dangin uwarta


 Saboda tasan ko baɗe ko ba jima anty fannah zata iya tona mata asirin inda take



   Sai da ta kuma jawa fannah kunne akan kar ta sake ta faɗi inda take sannan sukai sallama


  Tun ana ɓoyewa daddy har yazo magana taje wajen sa, ranar mummy ta sha faɗa sosai kamar ba gobe daddyn yai mata yai wa sabit wanda a yanzu yake kwance saboda zazzaɓi da ya rufe shi


  Takanas daddy ya saka mutane suka kama hanyar garin su asmai don ganin ko ta je amma ba same ta ba


  Tas ya tara mutan gidan akan su faɗi ko akwai wanda yasan inda asmau take, amma duk ba wanda yasan inda take


"har ke fannah don naji ance kullum kuna tare" jikinta ne ya fara rawa don ita fannah Allah yayi ta surutu amma sam bata da zafi sanyi gareta da kuma sanyin hali



 Amma da ta tuno irin cin kashin da sabit ɗin ya ɗinga yi wa asmaun sai ta dake tace

"nima ban sani ba"

"to duk lkcn da ta kira ki ki ce mata ta neme ni koma menene wallahi sai na ƙwatar wa yarinyar nan ƴancin ta tunda dai na lura kamar zaman haƙuri take yi da ku, in ba haka ba tayaya za ayi ace ta ɗauki ɗan da ba nata ba ta gudu an rasa ta ko sama ko ƙasa"



 Ya juyo ga mummy

"anya fatima ke uwa ce kuwa tayaya za ayi ace wai a gidan ɗan ki ana samun matsala amma sam baki sani ba, wane irin abu ne wannan, kince ke ƴaƴan ki baza suyi nesa da ke ba amma kuma sam ba kya kwaɓar su

  To wallahi ku sani duk wanda na same shi da laifi a guduwar yarinyar nan sai nayi mugun saɓa masa, kuma ku shirya jibi monday zamu fara shiga court don iyayen badia sun kai ƙara an aiko mana da sammaci sai ku shirya"


  Sabit da ke zaune kamar mutum mutumi sai ya ƙara narke wa ɗan zazzaɓin da ke jikin sa nan da nan ya kuma hauhawa, shi sam be ma san ya zai yi ba



  Miƙewa yayi don ya tashi dole duk yadda za ayi ayau sai ya nemo inda asmau take don kuwa wallahi bazai yiwu ace ya yi rashin ɗan sa ba


 Don kuwa ya san indai suka shiga court ɗin nan da badia sannan suka ci case ɗin dole ne ace ya bata ɗan in kuwa ya bata shi ya zaiyi da rayuwarsa





 Miƙewar nan da zai yi sai jiri ya kwashe shi ya faɗi ƙasa a sume, a guje akayi kansa inda mummy kuma ta fashe da kuka



  Ruwa aka kawo aka yayyafa masa nan da nan ya farfaɗo jikin sa kamar garwashi saboda zafi


 Yana farfaɗowa kuka ya saki ya riƙe hannun mahaifin sa

"daddy don Allah kar ka bari su raba ni da ɗana, ƙila shi kaɗai ne ɗan da zan so a duniyar nan don Allah daddy a nemo min asmau ta bani ɗana a maidawa badia ɗan ta saboda ta barshi a gidan nan"


   Ko wa a wurin sai da hankalin sa ya tashi, isma'il ne ran shi ya ɓaci ya fara magana


"wallahi yarinyar nan idan na sake na ganta Allah ko su badia basu kai ta kotu ba ni sai na sa an hora ta wane irin abune wannan"


  Lefi suka dinga ɗaurawa asmaun bayan sam basu san gaskiya suna ta ƙoƙarin cusa wa daddy magana saboda ya ji haushin yarinyar, da fannah ta ga haka sai kawai tace


 "nasan inda asmau take"


  Gabaɗaya kowa ya waigo gareta har da daddyn

"tana ina, suka haɗa baki"


  Nan da nan fannah ta kwashe inda asmau take ta faɗa musu amma sam bata faɗi dalilin zuwan asmau gidan ba


  Sabit shine a gaba ya fice domin tafiya, daddy ne ya tsai da shi

 "kai baka da lfy yi zaman ka nida isma'il da ita fannah zamu je mu dawo da ita" inji daddy



 "ka kira badia a waya su zo nan za a kashe maganar kafin aje court a kashe maganar a gida"


  Amsawa sabit yayi ya ɗauko wayar sa yana neman number badia wacce tunda abin ya faru ta koma gidan su


  Bayan ya samu badia ya faɗa mata ne ya zauna  amma ba don ransa ba ya so ace yaje wallahi da sai asmau ta gane bata da wayo



Ina kwance sai jin muryar anty fannah nayi a kaina

"ki fito da daddy muke"


  Rasa abinda zanyi nayi na ɗauka na ja mata kunne ashe sam bata ji

"asmau ki tashi mana na ce miki da daddy muke"


Miƙewa nayi jiki na a sanyaye, na fito na same shi yana zaune a falon gidan da isma'il da kuma wan anty fannah


  Ina fitowa na gaishe su, daddy da fara'ar sa yace min

"me yaji munzo mai da ke ɗakinki maza ɗauko kayanki mu tafi"


  Bazan iya masa musu ba na shiga ɗakin, anty fannah ce ta ɗauko min annur inda ni kuma na kwaso kayana muka fito


  A mota ba wanda yace min komai sai ma ɗana dana karɓa daga hannun anty fannah na rungume shi duk da ƙaton cikin da ke jikina





 Da sallama muka shiga babban falon gidan wanda yake cike da mutanen gidan harda mutan gidan su badia


  Tana ganina ta yo kaina da zagi wai in bata ɗan ta


  Daddy ne ya dakatar da ita inda yace duk a zauna a tattauna me yasa na ɗauke annur ɗin


 Sai dana zauna sannan daddy ya buƙaci ai masa bayanin abin da ke faruwa, sabit ne ya wangale baki yai masa bayanin, yadda aka samu annur


  Ba daddy ba hatta ƴan uwan sabit sai da suka jinjina maganar nan, daddy kuwa faɗa ya dinga yi yana ƙarawa sai da yai wa sabit wanki babban bargo sannan daga baya yace

"sabit wai duk bokon ne ya saka haka ko menene, dashe ka sa akayi wa matar ka saboda ɗayar matar taka ta cire mahaifar ta"



    Rufe ido daddy yayi ya zage tas shi da badia bayan ya gama sannan kuma ya ɗaura da nasiha akan abinda muka aikata gabaɗayan mu haramun ne


  Ko da kuwa dukan su matan ka ne bw hallata a ɗauki ƙwan ɗaya a saka wa ɗayar ba haram ne wannan


  Duk wani abu daya danganci dashw na ciki indai akwai mutun na uku daya shigo cikin abun ko da kuwa ko wane kusanci ne tsakanin su to ya haramta


  Faɗa sosai daddy yayi musu duk sai suka rasa bakin magana


 "ai asmau tana gaskiya ɗa ɗan ta ne babu wata badia, tai wahalar ɗaukar ciki ta sha naƙuda yanzu kuzo kuce wani ɗan badia tayaya akayi ɗan ya zama nata, to ku sani wallahi daga yanzu na gama case ɗin nan asmau ki ɗauki ɗan ki zan ga wanda zai kuma kawo maganar annur anan, kai in banda ma kai sha sha sha namijin kawai ka ɗauki ƙwan matar ka ka dasawa wata idan ɗan ya girma kace masa wacce ce uwar sa, wacce ta ɗau cikin sa ko wacce yake da jinin ta"


  Dukkan su jikin su ne yayi sanyi in banda badia wacce tace

"wallahi sai kotu ta ƙwatar min ɗana" ta faɗa tana kuka


"ai dole ne ɗa jinin ki ne duk inda aka je akai gwajin jini jinin ki za agani don haka ban ga dalilin da zai sa ace don mace bata da mahaifa ba ace kuma sam bazata
 mallaki ɗan kanta ba" inji maman su





 Gyara zama daddy ya yi ya fahimtar da mmn badia sharia akan duk wacce ta ɗau cikin ɗan adam ta kawo shi duniya itace mahaifiyar sa amma sam matar nan bata yadda fuuuuu haka ta ja badia suka fice


   Sabit wanda jikin sa yai sanyi ya ƙaraso kusa da ni zai ɗau annur daka masa harara nayi na miƙe tare da daukar ɗana na fice



   Babu wanda ya bashi gaskiya kowa sai rashin gaskiya yai ta bashi,


   Ɗakin na da ke part ɗin mummy nan na koma na kwanta, sabit ne dai ya kuna shigowa,


 " Na fahimci har yanzu taurin kan ki na nan, kina gani idan munje court gobe zasu baki annur ni ne dai uban annur kuma nace baza ki renar min ɗa ba"


  "kai ma ai bamu fara da kai ba, idan an gama case ɗin annur a court ɗin dole ne ka bani takarda ta don kuwa na gama aure da kai"


 "zan ga wanda ya isa ya sani sakin ki" ya faɗa a fusace

"wannan kuma in munje court ɗin na gabatar wa da alƙali buƙatata idan ya saka ka sake ni kace kai baka yadda ba"


  Haushi ne ya kama shi sosai ya fice daga ɗakin ko ganin annur ɗin ma be yi, nima na bi ƙofar da mukulli sannan na kwanta sai da safe Allah ya kaimu court ɗin inga in za abata ɗan bayan bata san komai nashi ba





 *******************


 Kashegari da wuri na tashi na shirya ɗana don zuwa court duk da dai yanzu sam hankalina ba a kwance yake ba ga ciki amma hakan be hanani gyara fuskata ba


  Mummy ce ta shigo wai daddy na kirana

  Hijab ɗina na ɗauka na same shi a falo yana zaune, har ƙasa na durƙusa na gaishe shi ya amsa min sannan ya kuma kwantar min da hankali na


 "nayi wa lawyer na magana shine zai kare ki koda kuwa jinin badia ne wannan yaron. Amtsayinki na wacce kika ɗau ɗawainiyar yaron nan sharia ta baki naki ne ko ina suka je ke kika haife shi ɗanki ne"


  Hankali na ya kuma kwanciya, anty fannah ce ta shigo itama taci laffayar ta,


"daddy nima dani za aje, don kuwa nima shaida ce, kuma ina kamun ƙafa idan an gama case ɗinnan ni zan karɓe shi ko asmau" gyaɗa mata kai kawai nayi amma wallahi bazan iya bawa kowa ɗana ba


 "to ai shike nan wannan ɗan ƙaramin case ne nasan ayau za a gama shi ma idan kun shirya sai ku fito"


  Mummy har gabana ta zo nasiha tai min sosai wallahi har jikina yai sanyi, akan kar in sake in bari a ja shariar da tsaho don mafi akasari idan ana faɗa akan ƴaƴa to wallahi su take shafa


  Gabana ne ya faɗi na ƙara matse abina a jikina in shaa Allah yau za a gama case ɗin tunda dai ƙiri ƙiri ga yadda abin yake



********************


 Badia ce da mmn ta sai lawyern da suka ɗauko a zaune duk abin duniya ya ishe su,

"gaskiya hjy kamar yadda na faɗa miki duk inda aka je indak ƙasar nan ne baza a taɓa badia ɗan nan ba tun da dai a ƙundin tsarin mulki na ƙasar nan wacce ta kawo ɗa duniya itace uwa"


  Kuka badia ta saki

" wallahi ƙwai na ne fa, ya za ayi in ɗau ƙwai na in bawa wata ƴar iska ita in banda rashin godiyar Allah ma gawani ɗan iskan ciki nan a jikin amma kuma bata godewa Allah ba sai ƙwaya ɗayan nan shine zata ce sai ta raba ni da shi, mummy don Allah ya zamu yi wallahi zan iya rasa rai na idan aka ƙwace min annur"


 "yi shiru yi shiru inji mummy yanzu kai barister ya kake ganin za ayi"



  Shiru yayi can sai ya e

"to akwai mafita amma sai in me gidan ya yadda da hakan" nan da nan ya tsara musu yadda za ayi


  Ba musu suka yadda nan da nan badia ta kira waya lagos ta faɗa wa dr. ɗin nan da tayi dashe akan ta bar asibitin na ɗan wani lkc kuma ta kashe wayar ta



 Shi ma sabit ta kiɗa shi ta faɗa masa shawarar da barister ya yanke, nan da nan ba tare da wani shawara ba yace ya yadda duk yadda suke so hakan za ayi


 ********************



          *COURT*


  Sai da aka gabatar da case 4 sannan aka kira su, inda magatarda ya gabatar da case ɗin su, aka kirawo badia da asmau kowacce ta gabatar da kanta


 Alƙali ya nemi badia tai bayanin abinda ya faru

"asmau kishiyata ce, kusan a tare Allah ya azirta mu da samun ciki, amma ta riga ni haihuwa inda ita ɗanta be zo da rai ba, ni kuma nawa yazo da shi, kuma shine wannan na hannun natan


  To kasancewar ban da ruwan nono sai mijin mu yace asmau ta dinga bawa ɗana nono, shine yanzu ta ɗauke min shi ta gudu da shi wai nata ne"



  Sakin baki kawai su anty fannah sukai suna kallon ikon Allah, sai da alƙalin ya gama rubuce rubucen sa sannan ya tambayi asmau ita kuma ta faɗi me ya faru


  Nan da nan na zayyano duk yadda akayi na samu cikin annur, kowa a court ɗin sai ya ɗau salati aka fara ƴan ƙananan surutai


 Sai da alƙalin ya doka ƴar gudumar sa sannan akai shiru,


"ina me gidan nakun"alƙali ya tambaya


  Nan da nan aka taso ƙeyar sabit ya fito, alƙalin ya tambayi cikin mu wake faɗar gaskiya, mutumin nan be ji kunyar Allah ba sai buɗar bakin sa yace


 " badia ce take faɗar gaskiya"


Hmmm sabit in bakai haka ba ai baka cika ɗan halak ba

 "to malama asmau kinji abinda mijinku yace ko ke kina da taki shaidar"

Gyaɗa kaina nayi sannan ya bani damar faɗar menene nan nace masa dr. ɗin da tayi min dashen kasancewar bata nan ya sa aka ɗaga ƙarar har sai dr. ɗin tazo da kanta



  Daga nan sati biyu akan mu zo da dr. ɗin, aka sallame mu bayan alƙalin ya ja min kunne akan kar ya sake naji na bar gidan balle in tafi da ɗan




 *******************


 Tun a mota daddy yake faɗa akan abinda sabit yayi, yana komawa gida ya faɗawa mummy ita ma sam bata ji daɗin hakan ba


  Daddy ya tambaye ni number dr.  ɗin don a kira ta a faɗa mata abinda alƙalin yace


  Tooo nan fa ake yi don gabaɗaya ban san komai na dr.  ba ni ko sunan asibitin ban sani ba, don inda akai min dashen daban inda kuma muke zuwa nan ma daban ne


  Babu yadda zasu yi dole ne aka nemo sabit don ya faɗi a ina za a samu, abin takaici wai sai sabit yace shi ma be sani ba wai badia ce ta san ta


  Haka daddy ya zaunar da sabit yai mai masa nasiha, tunda ya ga faɗan ma sam baya shiga, amma ƙiri ƙiri sabit yace shi be san zance ba



  Daddy ya rasa yadda zai yi da sha'anin mu, don yasan ko ana ha maza ha mata badia baza ta taɓa faɗar address ɗin dr. ɗin ba balle ayi contacting ɗin ta


  Zaunar dani yayi yai ta min nasiha, sannan yace min in Allah yayi annur zan rayu a matsayin ɗana too in kuwa Allah yayi kotu zata bawa badia to a matsayi na na uwar sa ba abinda zai so daga gareni face in kasance ina masa addu amma shi sam baya son ai ta ja'inja akan yaron don kar abin yai affecting ɗin sa


  Tabbas maganar daddy haka ne amma kuma in shaa Allah addua zan dage da ita kan Allah ya bayyana mana da dr ɗin nan

[5/8, 12:54 AM] ‪+234 803 638 7172‬: 🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)




*HIKIMA WRITERS ASSO.*




   P⃗a⃗g⃗e⃗  27🌹





 Ina kwance sai anty fannah,


"lallai me jego kice kina hanya amma shine ba a kira ni ina can na saki baki ina ta bacci"


 Murmushi kawai nai mata, ƙarasowa kusa da babies ɗin tayi tana ƙoƙarin ɗaukar ɗaya


"lallai maa shaa Allah kalar mu kalar da sabit baya so zan ga yadda zai yi yanzu da Allah ya haɗa shi da kalar mu"


  Murmushi na kuma yi

"wallahi nima anty tunanin da dinga yi kenan"


  Tattaunawa muka dinga yi da ita akan irin reaction ɗin da sabit zai ɗauka idan ya ji labarin ƴaƴan baƙaƙe ne biyu ma ba guda ɗaya ba



   Sai gab da asuba sannan bacci ya kwashe ni bayan na sha tea me kauri da anty fannah ta haɗa min


  Ban san lkcn da anty fannah ta kira mummy ba nidai kawai naji muryar ta ne a kaina tana cewa


"maa shaa Allah fannah kin yaran nan wallahi gaba ɗayan su kama suke yi sabit"


 "haka ne kuwa
 mummy amma inda za ai rikici da shi idan yaga kalar su"



 "hmmm fannah sabit ɗin daa kika sani na yanzu ba me tsirface tsirface ba na yanzu yayi laushi, jiya dana koma gida ake bani labari har get ta bishi tana zagin sa tare da ci masa mutunci,


  Hmmm wannan ƴar iskar yarinyar da badan daddyn ku yace inya sake ta sai ya sashi ya saki asmau ba wallahi da tuni ya manta ya rabu da ita


 Wallahi yanzu zancen da nake gaya miki tun daya fita tun jiyan har yanzu be dawo ba, a hanya ma ina ta trying ɗin shi in faɗa masa haihuwa amma wayar shi a kashe"


  Tausayi ya bani wallahi sosai, kai gaskiya banji daɗi koman lalacewar sabit uban ƴaƴana ne kuma bazan so wani abun ya same shi ba


 Tunda indai akwai wani ya same shi sai dai ƴan uwan sa su koka amma kuma ƴaƴan har abada a rayuwar su haka zasu kasance suna masu rashin uba


  Tashi nayi na gaishe ta da fara'ar ta amsa min da


"sannun asmau abinda bamu taɓa samu ba kika kawo mana ƴaƴa mata, tunda aka faɗamin na faɗawa daddyn ku yake murna don ma yana da meeting ne da wasu turawa amma ana tashi zaki gan shi, suma ƴan uwan naku nasan yanzu zaki gansu"


  Bata rufe bakin ta ba kuwa sai ga sallama

Dukkan mutan gidan ne suka shigo, dole ne ya sank fitowa parlour saboda yawan su

 

  Sai hayaniya ake tayi tare da murnar samun mace a dangi, barin ma mummy ta ɗauki babbar ta goye ta baya duk wanda zai ganta sai dai ya ganta a bayan ta sai dai ƙaramar ce ake ta passing passing da ita


 "mummy don Allah muga ta bayan ki" inji kishiyar anty fannah

"wannan da kuke ganin ta takwara ta ce shiya sa bana son a jagwalgwala min ita" mummy ta faɗa


 Ana haka mazan ma suka ƙaraso amma banda sabit ko ba komai ai zan ji daɗi idan na ganshi ko amma sam be zo ba


 Duk wanda ya zo gidan nan murnar samun ƴa mace yake a dangin nan, don kuwa har zuwa yanzu mummy bata da jika mace sai maza sai waɗan nan baƙaƙen dana haifa


 Abinda ya min daɗi da ƴan uwan sabit da matan su shine babu wanda ya luɗa da cewar yaran.ba farare bane sam ba wanda ya kawo wannan


  Kawai yaba kyan yaran suke yi, suna ƙara musu adduar Allah ya raya su cikin addinin islama


  Ana cikin hakan ne daddy ya zo, kasancewar parlour ɗin a cike yake yasa sam bamu ji sallamar sa ba duk an saki baki ana ta hira akan jariran da Allah ya hana kowa a dangin ya ba sabit



  Sai da daddy ya daka tsawa sannan aka san ya shigo


"haba tun ɗazu na shigo a miƙo min yaran in gansu amma kun saki baki sai zuba kuke yi kamar ƴaƴan kanya, dan Allah a miƙo min da baƙi nake a waje


 Na kasa zaman meeting ɗin ma sai ce musu nake yi ba a taɓa haihuwar mace a gidana ba sau yau kuma Allah ya bamu guda biyu"


  Sai da kowa ya dara da maganar daddy, is'mail da muktar ne suka fita da babies ɗin sai a lkcn mummy ta sauko babbar



   Sunfi awa guda sannan suka dawo inda daddy yace


"lallai yaran nan daga gani da albarka suka zo, mutanen nan suna ganin su sukai mana signing contract ɗin da mukai kusan wata biyu ana ta fama akan ta, lallai in gama suna suna da rabo in shaa Allah, ko ba"


   Mummy ce tace

"Allah daga zuwan su har ka fara nuna banbanci tsakani na  da su" 

 "yoo ke ba tsohon hannu bace, kinci kuɗin kinci kuɗin har kin gaji sukuwa ai kinga sababbi ne"


   Raha suka dinga yi tsakanin su inda wasu suke goyan bayan mummyn wasu kuma suna goyan bayan twins


  Ni dai ina gefe murmushi kawai nake yi ina jin daɗin yadda suke nuna kulawa ga abinda na haifa



  Sai da suka gama sannan ya tasa ƙeyar mazan suka fice inda aka bar gidan daga matan sai ƴaƴan su



Mummy ce ta sa anty fannah ta kaini asibiti ko akwai wani problem, muka je suka duba ni tas ba komai, sai dai magani da suka bani muka dawo gida



   Gidan ƙin kyau yayi sai da kowa ya bar gidan da daddare sannan gidan ya dawo hayyacin sa


  Mummy ce kawai bata tafi ba, wai ita ta dawo kenan sai bayan suna


  Muna zaune a falo wajen ƙarfe 10 :30na dare muna ɗan taɓa hira kafin mu kwanta sai nace wa mummy


 "har yanzu ba a san inda sabit yake ba" juyowa tayi ta kalle ni, dagani ita ma abin na damun ta

"wallahi asmau tun rana nake ta trying mumber sa amma sam a kashe take wallahi kawai ƙarfin hali nake amma hankalina ba a kwance yake ba"



  Hankali na ne ya tashi ya za a yi ace ba gan shi ba kuma ba wanda ya damu,


"mummy yanzu baza a duba a sani ko lafiyar shi ƙalau ba" na tambaya


 "wannan daddyn ku ne kawai zai iya kuma nasan inna faɗa masa bazai yi ba saboda har yanzu haushin sabit ɗin yake ji akan abinda ya miki"


   Kuka na saka mata nidai mummy don Allah ki sa a nemo shi, shekaran jiya ya fita ba a san inda yake ba amma ba wanda ya neme shi yanzu in wani abun ya same shi fa me zance wa ƴaƴana, wallahi duk lalacewar sabit na fi son ganin shi kusa da mu saboda ƴaƴana mummy dƙn Allah ki taimaka kiyi wa daddy magana"


  Shiru tayi daga dukkan alamu bata son yin kuka ne yasa ta ƙin yin maganar, wayata ta ɗauko tayi dialing number daddy sai da ta fara ringing sannan ta bani



  ringing ɗaya ya ɗauka tare da sallamar sa daga gani bashi da number ta

"daddy asmau ce"

"asmau kina nan lfy ko, ko akwai abinda kuke so ne"


  Kuka na saka masa sannan nace

"daddy ba aga sabit ba don Allah ka sa a nemo shi don Allah daddy"


  Shiru yayi kamar be ji ba sai da na sake bashi haƙuri na ɗauka ko be haƙura ba ne sannan yace


 "asmau lallai ke ƴar halak ce kuma wallahi baza ki taɓa taɓewa ba, ki kwantar da hankalin ki mijinki nanan ƙalau yana lagos ne, wajen aikin sa can ya koma amma in shaa Allah zan koro miki shi"


 Kunyar sa naji nai murmushi sannan nace

"ni fa daddy ba ni nake son ganin sa ba, kawai dai ya zƙ yaga babies ɗin ne"


 "ato abu ne sauƙi kawai zan sa a aika masa hotunan su kinga shike nan ya huta da zuwa kooo"


  "a a daddy don Allah ya dai zo" dariya yayi irin tasu ta manya sannan yace


"shike nan in shaa Allah zan sa a gaya masa"


 Mukai sallama sannan na sanar wa da mummy abinda ya faru, ta nuna jin daɗin ta sosai itama tai ta sa min albarka kamar ba gobe



 ********************



  Sabit yana kwance a kan kujerar gidan sa na lagos duk abin duniya ya gama isar sa, sam ya rasa farkn ciki, yana matuƙar kewar asmau daba dan daddy ya kafa masa doka akan zuwa wajen ta ba da tuni ya san yadda zai yi ya taho da ita lagos


  Tabbas asmau tana da taurin kai amma kuma zuciyar ta tana da sanyi, shiyasa duk abinda yake mata yasan bata riƙo



  Gashi yanzu wallahk yadda yake kewar to ko kaɗan baya kewar badia, wacce sam baya ma son ganin ta, burin shi kawai asmaun sa wacce yanzu aka kafa masa takunkumin ganin ta


  Knocking yaji ana yi, agogon bangon parlour ya kalla 11 :20na dare, waye wannan da daren nan yake min knocking



 Kamar bazai buɗe ba sai kuma ya tashi yaje bakin ƙofa yayi shahada ya buɗe


 Wani yaron daddyn sa bola inda ya faɗa masa wai daddyn yace ya kunna wayar sa matar sa ta haihu


 Ai ko sallamar yaron ma baiyi ba ya tafi ciki a guje shi sai a lkcn ma ya tuna da batun wayar sa tun da ya kashe ta lkcn da ya baro abuje



   Watsappa ya shiga don yasan ta nan zai ga pics ɗin babyn, aikuwa messages ne sukai ta shigowa kamar ruwan sama


 Message ɗin ƴan uwan sa kawai ya shiga dubawa, nan ya ci karo da wasu jarirai kyawawa an turo masa


 Duk da dai yaran ba farare bane amma kuma sun masa kyau sosai ashe shima baƙi yana da nashi kyan


 Duk da dai ƴaƴan shi baƙaƙe ne amma ya ga kyan ababan sa sosai kamar ba nasa ba, kamar su ɗaya da annur


  Miƙewa yayi ya fara haɗa kayan sa dalilin ganin asmau ya kama shi yanzu inyaje gidan ba wanda zaice masa don me


 In shaa Allah sai ya samu ya shawo kan asmau kafin a ƙara yi masa get da it don ba ƙaramin wahaltuwa yayi da rashin ta ba barin ma waɗannan ƴan kyawawan ƴaƴan nashin da ta kawo masa duniya


  Sai yanzu yai dana sanin zubar mata da ciki da yayi, inda yasan cewar idan asmau ta haifo masa ƴaƴan sa ko da zasu kasance baƙaƙe amma za suyi kyau ai da tun farko be dinga wannan abin da yake ba


 A gaskiya ya cuci asmau a rayuwa, sam shi sai yanzu yake jin kunyar kansa ma, yarinyar nan ba abinda tai masa kawai ya kafa mata ƙahon zuƙa



  Hawayene su ka sauko daga idon sa da ya tuna irin abubuwan da dinga yi mata, lallai yayi nadama kuma yana fatan ita ma ta yafe masa



  Da asuba ya kama hanyar abuja a jirgi inda yayi sa'ar samun flight na ƙarfe 06 :00 na safe, suna sauka diretly gidan da asmaun take ya wuce


 Gidan da yake ganin sa kamar na wani shugaban ƙasa saboda tsabar takunkumi da daddy ya saka masa



  *******************


 Ina kwance ina bacci kawai naji mutum ya kwanta kusa da ni ko ban kalle shi ba nasan sabit ne don nasan duk duniyar nan babu wanda ya isa ya rungume ni sai shi


   Da sauri na miƙe tare da haɗe raina

"lfy" na faɗa raina a ɓace, ai na waye yanzu ya za a yi in barshi ya same ni a banza bayan sam be san daraja ta ba


 "my asmy godiya zan miki akan wannan kyauta da kika kawo min duniya Allah ne kaɗai zai biyaki"


  Baki na taɓe sannan nace

"baka ganin baƙaƙe ne"

"au haba ban lura ba ni kawai kyan ƴaƴana nake gani"


"au ƴaƴan ka ma, ƴaƴan da ka so in zubar su sune yanzu kake kira da naka"


  "wai har yanzu ba a yafe min bane"


 "sabit ai tuban dole kayi tuban muzuru da kaga na dawo gareka shi ke nan sai a koma gidan jiya"


"ke kuma baza ki min fatan shiryuwa ba"


  "wannan kai ta shafa ko da kai ko babu kai zan iya rayuwata"


  Duk yadda ya so ya ga na sakar masa jikina sam yaga hakan be samu ba, da ƙwarin gwiwar sa ya shigo ɗakin amma ganin yadda na dage ban yadda da tuban sa ba ya sa jikin sa yin sanyi




 Ƙarasawa yayi ya ɗauki ɗaya wacce itace ƙaramar addua ya hau yi mata ina ganin shi yana ƴar ƙwallar sa ko me ya tuno oho


  Ganin zai karya min zuciya ya sani miƙewa na fice na bar masa ɗakin parlour na koma na zauna kusa da mummy


 Sam bata tanka min ba, ya daɗe sosai sai gashi ya fito

"mummy ni zan wuce gida in ɗan huta, akwai abinda kuke buƙata ne"


 Lallai ma sabit ɗin nan dama ba dan mu kazo ba don kazo kaga badia kazo kenan har da wani zaije gida kenan nan daji ne


 Harara mummy ta bishi da shi inda ni kuma na miƙe na bar wajen, sam be fahimci manufar mu ba ya ɗauka daga mummyn har ni fushin muke da shi


  Sim sim sim yasa kai ya fice shi sam ya ma rasa tudun dafawa wannan shine abinda ake cema rana zafi inuwa ƙuna




 Ko da ya koma gidan nan har gidan asmau yafi ni'ima don badia tana ganin sa ta hau shi da zagi da cin mutunci, sam be kula ta ba


 Ɗakin sa kawai ya wuce yana shiga ya rufe ƙofar da key kamar ya sani yana juyawa zai shiga toilet yaji bugu kamar za a ɓalla ƙofar


 Share ta yayi ya shiga toilet, hmmm lallai badia har yanzu batai hankali ba wai ita har yanzu burin ta sai ya bada sperm ɗin sa sun ka nemo wacce za a sake mata dashen ta haihu ita lallai sai taga ƙwanta a duniya ta nuna wa asmau


 Ƙin yadda dan da baiyi ba ne yasa kwanaki sukai fada ta bishi har waje tana ci masa mutuncin sa


 In banda ma daddy wallahi da tuni badia ta manta da rayuwa da wani sabit don wallahi in ya tashi katse auren da ke tsakanin su ko duka ba tare ya rage ko igiya ɗaya ba don ya




 : "wallahi sabit ka buɗe ƙofar nan ka ɗura min sperm ɗin ka a robar nan in kai asibiti a ɗura wa wacce za tai mana ɗaukar cikin, don baka isa ba kace wai bazan ga ƙwai na a duniya ba, wallahi ba za ta saɓu ba"


  Surutai tai tayi wanda suka saka sabit ɗin yin nadama sosai gaskiya ada ya bi son zuciyar sa sosai na cewae shi bazai auri baƙar mace ba balle ya haifi baƙin ɗa amma yanzu in shaa Allah ko ƴaƴa zai dinga haifa kamar baƙaƙen tukunya zai so kayan sa kuma ya basu tarbiyya


  Balle baƙin asmau ba me muni bane irin wanda yake da tsadan nan ne wanda bature yake cewa chocolate


 Barin ma yanzu da haihu ɗin nan tai wani fresh da ita duk sai ya jishi ya matsu ya jishi a jikin ta tana sarrafa shi kamar yadda take masa idan suna shiri



  Wani irin yarrrr yaji a jikin sa lallai akace wani kaya sai amale, asmau tayi wa badia nisa nesa sosai wanda duk abinda badiar zata yi ba lalle ne ta kamo ƙafar asmaun ba



 Kai lallai wallahi dole ne ma in dawo da matata wallahi duk abinda za a yi sai na dawo da matata


  Yana fitowa daga toilet ya tsiri haɗa kayansa shima gidan zai koma da zama duk yadda za ayi da shi wallahi sai dai ayi amma sam bazai iya rayuwa babu asmau ba



  ********************



  Ina zaune a ɗakina takaici ya ishe ni wai sai yaushe sabit zai fahimci shi wani jigo ne a rayuwa ta da bazan iya cigaba da ita ba face da shi a kusa dani kusan kullum banni da buri daya wuce inga na mallaki mijina a hannuna yai treating ɗina kamar yadda ake wa kowacce mace amma ni sam har yanzu ba samu ba


  Ina cikin tunani na naji muryar mummy tana magana


 " lfy kai kuma meye haka sai kace me shirin hijara"


"ai mummy duk inda asmau take da yarana ni ma ina nan, zuwa nayi gida ai na kwaso kayana ni ma ayi jegon dani"


 Murmushi nayi amma kuma sai na haɗe raina don kar ya shigo ya ganni ya raina ni


  Na ɗauka zai shigo ɗakin ko ince naso ya shigo ɗakin amma har na gaji da gyaran fuskar da zan sauke shi da ita na saki fuskata ba shi babu dalilin sa





 Sam be shigo ɗakin ba ina jin shi a parlour yata ta zuba cikin mata, kuna duk wacce ta zo sai ya shigo ɗakin ya ɗauke su don kai wa yan barka


 Kuma shigowa goma fita goma sak ya min magana, ƙala bana ce masa amma baya gajiya


  Haka aka dinga yi da shi ina jin anty fannah tana mai tsiya


"ni na taɓa ganin jego har da namiji"

"kin san ai autar mata ce ta haihu duk abinda take dole ne ai mata, ko da dai bazata yaba ba"



  Murmushi kawai nake yi ina cikin ɗaki na


  Har azore garin mu mummy ta aika da mota akan idan da masu zuwa suna



 ƴan garin mu da yake ba hankali haka suka ciko motar wata akan wata ƴaƴan su da jikokin su, har da me tsohon ciki


Ɗadin abun ma acan gidan mummy akai sunan can muka je saboda kar a ɓata min gida, inda ƴaƴana suka ci sunan

*FATIMA & FATIMA*

  sunan mummy da kuma suna mahaifiyata, ɗaya muna ce mata nur ɗayar kuma hoorain amma hoor in short


  Hoor da noor sun shaa kaya sosai da kyautuka da kuma hotuna


 Tunda aka fara sunan nan har aka gama sabit yana maƙele da ni kamar jaka, duk wani hoton da za ayi tare da shi yana riƙe da baby ɗaya


 Wallah tun abin na bani dariya har ya zo ya faɗa bani haushi don kuwa tuni mutan garin mu suka fara magana


"shi mijin mau haka yake abin nasa sam ba kunya"


  Ga dukkan kayan da na saka sai shima ya saka, ko kaɗan bansan ya akayi akai mana kaya iri ɗaya ba, ko da yake nasan aikin waye


 Na anty fannah ne don kuwa itace akan komai na kayan da zan saka ranar suna,


 Mun sha pics sosai da mu da ƴan biyun mu da annur


 Suna yai suna haka akai suna aka tashi lfy a daren muka koma gidan mu don gidan mummy babu masaka tsinke

  Fatana dai Allah yasa mijina ya shiryu kenan har a bada
[5/8, 12:55 AM] ‪+234 803 638 7172‬: 🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)





*ALLAHUMMA BALIGNA RAMADAN BIL IMAN* 🤲🏻🤲🏻





*HIKIMA WRITERS ASSO.*




   P⃗a⃗g⃗e⃗  28🌹






 Satin twins 2, sabit ya tattara yanasa yanasa ya koma lagos duk wannan zaman da yayi ko kaɗan baya samun daman ta, wai ko sakin fuska ko kaɗan


  Idan yana parlour to ina ɗaki, sam ba abinda yake haɗa mu, amma ta ɓangaren yara kuwa kusan shi yake renon su


 Don ko cikin dare sai kawai in ganshi a cikin ɗakin nawan ya zo ganin su sam na ƙi sakar masa fuska, sai dai kawai ya ta abinsa shi kaɗai ni dai ido ne nawa



  Ko ran da zai tafi ya shigo ɗakin nawa inbawa hoor nono

"me jego mu office yayi kira faa, in shaa Allah yau zan koma bakin aiki na"


 Kamar yadda fuskar nan tawa take haka na bar ta sannan na bishi da
" Allah ya kiyaye hanya"


  "babu wani kalmar i will miss u ko love u" ƙara shan kunu nayi wanda hakam ya sashi cewa

"ayi haƙuri naga alamar har yanzu ba a sakkowa ba ni me lefi ne don haka bazan yi fishi ba zan jir har sai lkcn da Allah ya sa kka sakko dan kanki kika fahimcin irin son nake miki........


  Ɗago ido na nayi na kalle shi dana ji ya furta kalmar sooo ɗin nan


"kina mamaki ne wallahi asmau i really doo love u, u r d only one i doo love"


  Wai love kaji kuma zance, kamar da gaske, hmm sabit kenan u love abinda kake love de amma badai ni asmaun ba kuma wallahi abinda kake love ɗin is d last thing da zan baka


  Surutan sa ya ƙaraci yi daga ƙarshe daya ga ba reply ya miƙe ya fice jikin sa ba ƙwari, a daidai bakin ƙofa ne na ce masa

 "Allah ya kiyaye hanya"


 Dawowa yayi fuskar shi ɗauke da murmushi, ɗan kiss ya sakar min a lips wanda ban bar shi ya daɗe ba na ɗauke fuska ta tare da ƙara shan kunu


  "sorry na kasa haƙuri ne" ya faɗa, hannun shi ya kai kan fuskar hoor wacce ta daddage sai tsotsar mama take tayi


  "my lil princess a sha a ƙoshi a rage wa daddy" ya faɗa da murmushi a fuskar sa, ban tanka mishi ba sai daya gama wasa da ita sannan ya juya ya fice


  Ina jiyo shi shida annur a falo suna hira shi da annur a falo yana ta masa gwarancin sa shi kuma yana ta biye masa


  Sai da ya shafe kusan rabin awa sannan yai sallama da su mummy wacce tunda akai haihuwa bata tafi ba


*******************


   Har kusan yamma ina ta sa ran inji mummy tace sabit ya sauka ko wani abun amma na ji shiru wannan ne ya sakani fitowa parlour ɗin suna zaune ita da baaba suna hira


  Baaba tana yiwa twins wankan yamma

 "me jego an fito ne" inji baaba


 "wallahi zaman ɗakin ba daɗi"

 Na nemi waje na zauna kusa da mummyn

"mummy  ya matafiya sun sauka ƙalau"

Tsayawa tayi tana tunani can sai tace

"ke yanzu tunda suka sauka baki kira kin tambaye su sun sauka ƙalau ba, haba asmau ya ina ganin hankalin ki ace mutane sun taho daga kano amma har su koma baki kira ba"

"mummy bafa su ba ai na kira waɗancen"

Na bata amsa, wallahi sam bana son ina damun kaina da lamarin sabit amma bazan ignoring ɗin shi ba


  Ko da dai ace bazan masa directly ba nayi masa indirectly

 "waɗannan matafiya ne kuma suka kuma tafiya bayan ƴan uwanki"


 Murmushi nayi tare da sunkuyar da kaina ƙasa

Baaba ce ta ɗago ni sai naji tayi dariya tace

"lallai mmn annur wato kunya ake ji, hjy ai me gidan ta take tambaya"

  Murmushi mummy tayi sannan tace

"ƙyale ta baaba tsab na fahimci abinda take nufi, yo ni ina ruwana da wani mijinki ba ke ya kamata ki kira shi kiji ya ya sauka ba"


Muryar anty fannah naji a bayana tana cewa

"lallai kam mummy ke dai ai kina gama naki tunda yanzu yayi aure ai haƙƙin kula shi ya koma kan matar sa"


  "kai anty fannah don Allah yanzu har da ke ake wannan abin, don Allah kira shi muji ko ya sauka lfy"

 "wallahi bazan kira ba inkin matsu ki kira shi" inji anty fannah

 Kallon mummy nayi wacce kafin ma ince wani abun tace

 "kar ma ki ɓata bakin ki, kije ki nemi mijinki inkuwa ba haka ba wallahi babu me kira miki shi"


  Tsayawa nayi ina kallon bayin Allah nan yanzu so suke yi in zubar da ajin nawa in kira shi

"malama dalla can tashi kije ki kira shi ana so ana kasuwa Allah ya haɗa shi da matan lagos masu shegen naci"inji anty fannah


  Da gudu na na miƙe nayi cikin ɗaki yanzu ace sabit zak ƙara aure ai ƙaramin hauka zanyi

  Kasa kiran shi nayi don haka sai nayi masa text

```ka sauka lafiya```


  Be fi minti biyu da text ɗin ya shiga ba sai ga call ɗin sa ina ɗauka yace

"baby na kina nan ƙalau"

"ba babyn ka bace asmau ce" na faɗa cike da takaici

"oh ai na ɗauka baby ta ce to ya kike mmn twins"

  Wani ƙululun baƙin ciki ya zo ya tokare min a maƙogwarona da ƙyar na haɗiyi miyan da ke baki na sannan nace masa


"ka kira babyn taka kuyi hirar kawai sai anjima"


  Da sauri sa ya dakatar da ni

"haba my husna ai kece babyn tawa daga ke ba wata, wallahi tun da na sauka nake son kiran ki amma bana sƙn takura miki ban ɗauka zaki damu ba don baki jini ba"


"ba damuwa nayi ba dama mummy ce tace bata sani ba ko ka sauka, shine nace bari in kira ka inji"


 Murmushi yayi don tuni ya ranfo jirgin natan yana sauka yayi wa mummy waya akan ya sauka ƙalau amma shine wai take masa wannan gidogar


"kai amma wannan mummyn ta kyauta wannan ya nuna an damu da nine ko, kai amma naji da daɗin da wannan mummyn ta nuna damuwar ta gare ni"


  Shiru nai masa inda shi kuma yai ta tambayar yara ina bashi amsa a taƙaice, mun ɗan jima muna waya daga bisani kuma mukai sallama


  Shike nan tun daga lkcn sabit ya tsiri kirana safe rana dare kamar baya jin kuɗin wayar sa wani lkcn idan ƴan jujun suna kaina yana kira sai in haɗa shi da annur yai tayi masa gwarancin sa wani lkcn kuma in ɗauka


  Sam baya gajiya da gaya min ni kaɗai ce a zuciyar sa nakan rasa gane gaskiya ne ko ƙaryar sa ce, itama badiar haka yake mata ko a a

 In dai aka ce kana auren me mata sai Allah


  Rannan ya kira ni a waya da yamma

"baby na kiyi min addua akwai wani course da zanje turkey inyi na wata biyar in shaa Allah nan da wata ɗaya ne tafiyar, kuma ke zaki  min rakiya sai mu tafi tare da su annur ko"

 Daɗi ne ya lulluɓe ni don wannan ne ya nuna ana yi da ni, ranar mun sha hira kamar baza mu gama ba har sai da wayata tai zafi sannan muka kashe


  Kamar da gaske na fara sakin masa jikina, saboda tafiyar da yace za ai dani ko ba komai zan nuna wa duniya da ni miji yake yayi



  Na so ace a lkcn ya kuma min maganar tafiyar amma sai naji shiru har gashi watan ya kusan cika sai na ɗauka ko ga fasa tafiiyar ne don haka nima sam sai ban ƙara yi masa zancen ba don kar yace abin ya dame ni ne, tunda dai haɗ yanzu bama ƴar hakan da shi


  Kullum ya kira a waya shine yake hirar ni kuma ina sauraro ko bada amsa amma sam bana taɓa kawo mana topic


  *******************



  Mummy sai da mukai sati huɗu sannan ta tafi gida wai ai yanzu zamu iya kula da su, amma sai ta ƙara kawomin ƴar aiki amma wannan karan ƙarama ce


  Rannan da yamma muna zaune a falo muna hira da anty fannah sai ga badia, wallahi dana ganta sai da gabana ya faɗi


  Rabo na da ita tun a court da aka raba mu, da sallamar ta ta shigo kamar gaske, me aiki na aika ta kawo mata abin sakawa a bakin ta


 "a a barshi ba zama zanyi ba, dama nazo ne in miki sallama don kuwa gobe zan tafi lagos daga nan zan yi wa sabit rakiya zuwa istanbul don akwai course ɗin da zaiyi na wata biyar acan"


  Ji nayi kamar an ɗauki guduma an doka min a kaina, sam sai na kasa gane inda zancen ta ya dosa na kasa gane maganar ma da zan mata ko baƙa zan mata ko me daɗi zan mata


  Lallai sabit ɗin nan  na gaishe shi wato bazai taɓa dena abinda yake min ba ko


"kin san daa nace ya tafi da ke da farko har ya yadda amma daga baya sai yace shi baya son gayyar ƴaƴa haka kurum kije da ƴaƴa ki hana shi sakewa shi yasa nace to shike nan bari kawai in bi shin"



 Kalaman ta ƙara ƙona min rai suke suna kuma tabbatar min da sabit ba zai taɓa canza wa ba,


 Zata buɗe baki ta ƙara wani maganar anty fannah ta katse ta

"wannan tsakanin ki ne ke da mijin naki sai kuje can ku ƙarata amma mu ba abinda ya dame mu ko kinga wani abu daya shafi sabit a nan in ba ƴaƴan sa ba, don Allah ki tashi ki tafi in ba fitina kike nema ba"


"toooo daga zuwa abin arziƙi sai ya zama na tsiya, to shi ke nan bari in tafi amma a sani duk abinda mace zata yi wallahi baza ta kamo ƙafa ta don kuwa ance farar mace alkyabbar mata, duk wani jiji da kai da mace zata yi ta tuna cewar sai naga dama zan bar ta ta sake da miji





 Anty fannah ce ta miƙe suka fara cacar baki da badiar inda daga ƙarshe sai baaba ce ta raba su domin ni ina zaune kamar gunki ba motsi


 Wallahi sabit ya gama bani mamaki wallahi na gama dawowa daga rakiyar sabit har abada, da ƙyar na iya riƙe kukana har badiar ta fice sannan na saki abina


  Janye ni anty fannah tayi zuwa cikin ɗaki inda sai da ta lallashe ni sannan ta tambayeni menene na kukan


  Tsap na kwashe yadda mukai da sabit na faɗa mata itama sam bata ji daɗi ba kuma ta jinjina da lamarin amma sai ta ce min ki kira shi kiji ya mw ya faru


   "wallahi anty bazan kira shi ba bazan kuma yadda da maganr sabit ba, ya cutar da ni na yafe masa ya kuma wallahi wannan karon bani bashi ai ba zuciyar dutse gare ni balle yace bazan ji abinda yake min ba"


 Haƙuri dai anty fannah ta dinga bani kamar kullum ni kuma na riga na gama kulle shafin sabit a rayuwa ta sai dai wani ba shi ba


  Nunawa anty fannah nayi naji faɗan natan don haka sai ta tafi, tana fita na ɗauki wayata na tura masa da text kamar haka


 ```naji ashe da badia zaku tafi turkey tooo Allah ya kaiku lfy ya ƙara danƙon soyayyar ku amma wallahi ka sani ka sake naga ƙafar a gidana wallahi kaji na rantse maka sai na kira daddy ya raba mu```


  Ina gama rubuta saƙon na kashe wayata, haba sabit daaa kenan zakai min ba tare da na ɗau mataki akan ka ba amma ba yanzu ba da kan mage ya waye


  *******************


  Sabit yana zaune a gidan sa yana ta haɗa kayan sa zai taho kano sallama da asmaun sa sam wannan tafiyar da badan ta zame masa dole ba da ba inda za shi


  Tunda ya kira daddy ya faɗa masa maganar tafiyar yace masa da asmau za shi daddy ya soke tafiyar da ita yace ana sanyi ga yara basu yi ƙwari ba gwanda kawai ya tafi da badia in yaso ita asmaun sai ya kaita hajj yake jin wani iri a jikin sa


 Sam ya kasa yi wa asmaun bayani a waya yafi son idan yaje can sai yayi mata bayani face to face ya san zata saurare shi kuma zata fahimta




 Ƴar ƙara yaji daga wayar sa alamar message ya shigo, sam be damu yasan ko waye ya turo ba ya fison idan ya gama komai sai ya duba


Sai daya gama komai sannan ya ɗauko wayar da don ya duba sakon da aka turo masa


 Yai mamakin daya ci karo da saƙon asmau, hankalin shi ya tashi sosai ya rasa abinda ke masa daɗi ya akayi asmau ta san da batun tafiyar sa da badia


 Yasan muumy sam bazata taɓa faɗa mata balle kuma daddy, inbanda su biyun nan babu wanda ya sani sai badia


 Badia tabbas badia ce ta faɗa mata rasa abinda zai yi don takaici


 Ɗaukar wayar ta yayi ya fara trying a kashe ya jita, shit ya faɗa sannan yai jifa da wayar sa wai sai yaushe zasu samu zaman lfy da asmau ne


  Ya daɗe ya na tanadin lkcn da zasu haɗu da asmau amma yanzu duk wannan budget ɗin nasa ya ruguje, mtsss, gashi ƙarshen satin nan zasu tafi


  wallahi shi ya sa da daddy yace asmau baza ta je ba yace bazai tafi da kowa ba, daddyn ne ya matsa masa sai ya tafi da badia, yanzu gashi nan ga abinda aka jawo masa ya rasa abinda ke masa daɗi wannan wace irin rayuwa ce ace kullum ka rasa farin cikin da iyalan ka da komai


 Sam baya ganin laifin asmau shi ne ya fara ɗora ta akan wannan hanyar ita kuma da ta tashi sai ta doke shi,


  Lkcn da yake iskanci sam be taɓa hanata haƙƙin ta na aure amma ita da ta tashi ramawa nata ya fi ci masa tuwo a ƙwarya ta hana shi kanta ta hanashi ganin ƴaƴan sa


  Kai wannan da me yayi kama


Zai ci gaba da trying ɗin wayar ta har ya samu ta shiga, don ya kamata ace lkc ya yayi da zasu daina involving mutane cikin maganar sha'anin auren su



  Ya kamata idan ka girma ka san ka girma ƴaƴa uku tsakanin su, gaskiya lkcn da zasu zauna su magance matsalar sune yanzu ba lkcn da zai dinga ya maɗiɗi da duk wani ɗan saɓanin da suka samu bane



  Wayar shi ya ɗauka yai mata reply kamar

```baby na don Allah idan kin kunna wayar ki ki kirani wallahi zan miki bayanin komai, na so ace na zo kano nai miki bayani ni da ke amma ganin text ɗin ki ya dakatar da ni don Allah call me```



Kwanciya yayi kawai akan gado yana me fatan Allah yasa idan taga message ɗin shi ta kira shi



Tun sabit ya jiran call ɗin asmau har ya sare, har badia ta zo, inda ranar da ta sauka ma sai da akai abunda aka saba don tana sauka ta fara masa maganar dashe wanda shi kuma ya taka burki wanda
 hakan ya kai su ga faɗa


Har ranar da zasu tashi ba asmau ba labarin ta abin ya dame shi sosai bazai iya tafiya ba ba tare da yaji muryar ta ba



  Ɗaukar wayar sa yayi ya kira anty fannah tas ya kwashe mata abinda ya faru ya faɗa mata sannan ya roƙe ta akan don Allah ta sa asmaun ta kunna wayar ta ko sallama ne suyi tunda ta hana shi zuwa gidan


  Anty fannah ta tausaya masa sosai sam bata san haka abin yane ba kuma sam bata san cewar asmaun ta aikata hakan ba


  Haƙuri ta bashi tare da yi masa alƙawarin zatai wa asmaun magana



 Suna gamawa ta miƙe da ɗan cikin ta wanda a yanzu ya fara nuna wa tayi hanyar part ɗin asmaun,


  Tana zaune tana bawa annur abinci sukuma twins ɗin suna baccin su da sallamar ta tashiga


"anty fannah yanzu nace bari in gama bawa annur abinci yaje wajen ki don in samu in bacci wallahi ya hanani da rigimar sa"


 "ba dole yayi rigima yaro yaushe rabon da yayi magana da bbn sa" shiru nayi don bana ma son ayi min maganar sabit ko kaɗan


 "yanzu asmau duk faɗan da nai miki rannan ashe baki jiba, sai da kika kira sabit kika ƙara tayar masa da hankalin, yanzu asmau dama an taɓa rayuwa a haka,


  Kin ganni wallahi a gidan mu sam bamu san wai namiji yai maka laifi ba kace zaka rama, duk abinda namiji yai maka indai har ya dawo ya tuba wallahi sai ka yafe masa ku zauna lfy


 Yau namiji yai miki kin yafe gobe ya miki kin kuma yafe wa wallahi jibi kunyar ɓata miki zai yi,


  Amma idan kina yi namiji haka asmau kina ƙara ɓata masa rai kina ƙara nisan ta kanki ne da shi, lkcn da zaki zo ki so shiryawa sai kiga shi kuma ya riga yai miki nisa


  Don me yasa duk abinda sabit yake miki ban taɓa cewa ki rama ba, saboda nasan kowane *AURE BAUTA* ne


  Kuma duk matar da tace wallahi ba za tai  haƙuri da jarabawar da Allah ya jarabce ta da shi a rayuwar auren ta ba to wallahi tallahi tai kuka da kanta


 Kin taɓa jin inda akace wannan abin ibada ne kuna ya kasance ka same shi kasatan ba wani wahala ko wani abu


 Wallahi ki nutsu, ke me kishiya, ma d more kike nisanta kanki da mijinki d more shima yake ƙara nisanta kanki da shi duk kuwa da son da ya ke miki za a wayi gari wataran yaji da ke da babu duk ɗaya


Duk matar da tai sacrificing farin cikin ta ga mijin ta wallahi ko ba daɗe ko ba jima sai ya dawo wajen ta, ko kin taɓa jin inda akace haƙurin wacce be mata rana ba sai dai a ce rashin haƙurin haƙurin wacce ya cutar ta


  Kiyi haƙuri ki ja mijin ki a jikin ki, in shaa Allah wataran sai labari wataran ke zaki girbi abinda kika shuka walau khairan au sharran"


 Tun da ta fara nake kuka nasan tsab anty fannah macece me haƙuri sosai da  mai da komai ba komai ba shiyasa tunda muke da ita ban taɓa jin tace wani abu akan isma'il ba


  Amma ni yanzu wai ace duk abinda sabita ya min in share in mai da komai ba komai ba to wai sai yaushe ne duk waɗannan abubuwan zasu zo ƙarshe


 Ko da yake ance aure ibada ce kuma aure bautar Allah, muna fatan a wannan bautar Allah yasa mu kasance muna yin ta iyakacin iyawar mu


"in shaa Allah anty zan kira shi komai ya wuce"

"indai har da gaske kinji abinda na faɗa miki ɗauki wayar ki kira shi, kuma ki bashi haƙurin tayar masa da hankalin da kikayi"


  Wayar na ɗauka na kunna sannan nayi dialing number sa, ringing ɗaya ta ya katse wayar daga dukkan alamu shi ya kashe kallon ta nayi alamar ta gani ko


 Murmushi tayi sannan tace

"ki bari zai kira ki nasan yana wani abun ne"

"nasan ba wani abun da yake yi yana tare da badia ne suna ta shirye shiryen tafiya mtsss"


Kallona tayi sannan ta saki murmushi

"asmau manya duk kishin ne haka, ana so ana kaiwa kasuwa daaa kina kishin nasan kika bar mata shi, wa ya gaya miki ana bar wa kishiya miji, barin ma ita da suke tare kullum,


 Wallahi asmau ki shiga hankalin ki da wannan wautar taki ta nuna halin ko in kula da sabit, yaro kina ganin shi sabon jini son kowa ƙin wanda ya rasa amma kina miss using damar ki


 Yarinya idan yaje ya haɗu da ƴammatan lagos masu shegen naci, maƙale mata kya faɗawa ƴan garun ku"

  Ta ƙarashe zancen ta da dariya

  Kyakyaɓe mata fuska nayi kamar wacce zatai kuka a dai dai lkcn call ɗin sa ya shigo, kallo na tayi sannan tace

"tashi ki shiga ɗaki ku sha hirar ku zan ci gaba da kula da yaran sauran kar ki bashi haƙuri sauran kar ki kwantar masa da hankali wallahi ya kuma kawo min ƙarar ki sai dai ki nemi wata ba ni ba"


  Miƙewa nayi jiki na asanyaye nayi hanyar ɗaki tare da ɗaukar wayar sannan na kara ta a kunne na tare da cewa


"hello daddyn annur ya lagos"
[5/8, 12:56 AM] ‪+234 803 638 7172‬: 🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠


      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)





*ALLAHUMMA BALIGNA RAMADAN BIL IMAN* 🤲🏻🤲🏻





*HIKIMA WRITERS ASSO.*




   P⃗a⃗g⃗e⃗  29🌹







 "hiii baby na wallahi na wahala kwana biyu ban jiki ba don Allah my asmy duk abinda zan miki nan gaba kar ki ƙara kashe min waya, a hukun tani ko ta wane hali ne amma don Allah banda hana ni jin muryar ki kinji"

  A ɗan shagwaɓe na amsa ƙasa ƙasa

"fannah ta matsa miki ki kira ni koo, shike nan kar ki takura kanki duk lkcn da kika sauko zan jira"


  Ya faɗa tausayi ya bani sai nace masa

"ni ba haka bame anty fannah ce tace idan ka haɗu ka matan lagos masu maƙewa namiji zan sani ne"


   Murmushi yayi sosai wanda hakan ya ƙara sani ƙuluwa

"haka tace"

"hmmmm" na amsa a takaice

"shike nan rabu da ita in ma zan samo ƴan matan lagos zan samo wacce zata dinga baki arona"


  Kuka na saka masa

"wallahi sai dai ka zaɓa ko ni ko ita wallahi bazan kuma zama da wata ba, bayan ga badia kuma ka kuma kawƙ wata wallahi sai na haɗa ka da daddy"


   Daɗi ne ya rufe sabit, wanda sam be san ina zai saka kansa ba

"haba baby na daga gani har yanzu baki yadda ba dana ce miki daga ke an zo d end, in shaa Allah ba wata macen da zata kuma ɗaukar hankalina sai ke my asmy, i really love u sooo much"



  Hira mukai tayi yana faɗa min kalamai masu ɗumi wasu in mayar masa wasu kuma sai dai inji amma ba bakin mayar wa


   Kun kusan awa guda muna waya sannan mukai sallama inda yake gayamin is tooo late daya zo kano


 Nuna masa nai ba komai zan ta bin shi da adduar Allah ya kaishi lfy ya kuma dawo da shi lfy sannan mukai sallama





 ********************


 Tun daga lkcn duk wani motsin sa sai ya gaya min sosai muke communicating da shi duk wani motsin sa ko tusa yayi wacce ta canza wari sai ya gayamin ƙarewa kenan


 Munyi wata irin shaƙuwa wacce bazan iya fasalta ta ba, ban dai san alaƙar da ke tsakanin shi da badia ba amma ina ji a jikina ko ita bata isa tace sun fi kusa ba




 Yara na sun ƙara girma sunyi ɓula ɓula da su kamar kaji kiwon gidan gona


 Sam basu damu da shan nono ba ko cikin dare sai dai su sha feeder su don wani lkc ma sai na danne su nayi musu dole sannan suke sha


  Itama anty fannah cikin ta na nan ya ƙara girma sosai ya fito haihuwa ko yau ko gobe duk wani siyayya da za ayi na haihuwa munyi shi mun gama jiran ta kawai muke yi



 A kwana a tashi ba wuya wajen Allah, har sun gama course ɗin nasu suna ta shirye shiryen dawowa a lkcn ni kuma duk wani gyara nayi shi


 Duk wani abunda nasan anace masa mai da tsohuwa yarinya ya daɗe da tsima a jikina buri na kawai mijina ya dawo in nuna masa banbancin da ke tsakanina da badia


  Ranar wata alhamis ana sauran kwana biyar sabit ya dawo anty fannah ta tashi da naƙuda inda Allah ya sauke lfy ta samu baby girl ɗin ta itama

  Murna a wajen ta kamar ba gode, haka muka haɗu aka cika gidan ana ta murna, kashegari da sassafe ta kama hanyar maid. na so in bita amma sai sabit yace in bari sai ya dawo


  Ko da na faɗawa mummy sai tace inyi haƙuri Allah ya dawo da shi ɗin, ban damu ba saboda nasan yana dawowa zai saka ni a gaba mu je maid




 Ana gobe zasu dawo da yamma ina zaune na kunna data muna chatting da anty fannah sai naga sabit ya aiko min da messages


 Buɗewa nayi me zan gani

Pics ɗinsu ne kala kala shi da badia wasu ba laifi don an yaɗa su amma wasu sam be dace ba


  Kala kala sun kusan 20pieces haka aka turomin su wallahi wasu sam ba kyan gani ma, takaicene ya rufe ni


 Nasani sarai ba sabit bane ya turo badia ce amma don me ze bata wayar sa har ta shiga ta duba mana sirrin mu


 Duk abinda zasu yi bazan hana su ba amma don me zata turo min wallahi sai ta gane bata da wayo,


  Haɗa kayana na fara yi maiduguri ma zan tafi,


   Isma'il na kira nace yai mana booking flight ni da baaba da kuma yara zamu suna, sai dana gama komai sannan na tattara kayana naje gidan mummy na sauke mata annur sannan na kama hanyar maid.



   Sai da na sauka sannan na kunna wayata, ina kunna wa naci karo da text ɗin sabit yana min faɗan wai bana jin magana bayan yace min ƙar in tafi sai ya zo


 Forwarding pics ɗin ta aka turo min nai masa, bayan nayi copy and paste yadda zai gane daga phone ɗin sa aka turo min



  Ƙanin anty fannah ne ya zo ɗaukar mu, ko dana sauka sam ban nuna mata ba itama sam bata kawo komai ba


 Masauki guda akai mana inda aka sauke mu ɗakin da anty fannah take, kusan kwana mukai muna hira kasancewar bata san ba da san ran sabit na taho ba ya sa sam bata kawo min wani zancen yi min faɗa ba


 Kuma ina ta sa ran sabit zai kira ni yai min wani bayanin yadda akai pics ɗin suna zo wayata sai naji shiru


 Tun ina sa ran call ɗin sa har na haƙura, a haka na kwanta cike da takaicin rashin kirana da sabit be yi ba


********************


 Da wurwuri muka tashi saboda ana ta shirye shiryen gobe suna duk wani gyara mun sha shi barin ma ni da biyu nake gyaran nawa


  Kitson bare bari akain min wanda yake zuwa gaban nan sanna a tifke shi ya koma gefe bayan wanka da turare da nake ta sha


 Duk wani gyara na tarar suna mun sha shi kawai jiran zuwan sunan muke yi, in ka ganni zaka ɗauka banni da wani damuwa amma can ƙasan zuciyata tana tunanin yanzu sabit yana nigeria faa


Amma sam be neme ni ba wallahi ni ma bazan neme shi ba, har la'asar muna ta hidimar mu duk da dai ni ba abinda nake yi ina kusa da anty fannah dai dai da yaran wallahi sai su wuni ban gansu ba suna can cikin gidan wajen mmn anty fannah itace take kular min da su



 Ina zaune kawai naji sallama kamar muryar sabit, ina ɗagowa mukai ido huɗu da shi


 Kunya ce ta kama ni na kaaa tashi daga inda nake,

"jibi ƴar ƙauyen nan dama haka karɓar baƙo" inji anty fannah


 "ƙyale ta anty ni me laifi ne a wajen ta shiyasa na tako da ƙafata in bata haƙuri"


"au baki daina faɗa da mijiba, dama shine dalilin daya sa kika taho lallai ma asmau ashe bakyaji magana dama" inji anty fannah


 "don Allah ki ƙyale ta wallahi am at fault kuma na karɓi laifi na kuma nazo bada haƙuri ne"


  Ƙarasowa yayi kusa da ni ya tsugunna inda ni kuma kai na yake ƙasa

"baby na ayi min afuwa"


Faɗawa jikinsa nayi wallahi babu ƙarya nayi missing ɗin shi sosai

 Wata kyakkyawar runguma naji ya min wanda ya sauke ajiyar zuciya tare da fara shinshina min wuya na wanda ya tsumu da ƙamshi


"anty wannan ƙanwar taki ta sha gyara sai kace wata amarya" ya faɗa muryar sa a shaƙe


 "sabit ko dai in muku gadin ƙofa ne don naga daga dukkan lamu anan zaka bada tsarabar taka"


 "wallahi da kuwa kin kyauta" ya faɗa

  Wallahi duk a tunani na wasa suke sai naga ta ɗauko mukullin ɗakin ta miƙo masa

" ka saka key ni kuma zan zauna daga can ɗakin ina kallo ɗakin don kar a katae muku hadda"


"anty wasa fa yake yi" na faɗa


"waye yake wasan" naji sun haɗa baki sabit hadda zare ido


 Shiru nayi, ban tabbatar da maganar su ba sai dana ga anty fannah ta fice shi kuma ya mai da ƙofa har da key sannan na tabbatar da rashin kunyar sabit


 Tsere muka fara yi da shi a ɗakin

"wallahi ni kunya nake ji"

Yana bina yana dariya

"in banda abinki ko min yi wani abu ko bamuyi ba ai duk ɗaya ne ba gwanda munyin ba in yaso baza mu musa ba"


   "wallahi ban yadda ba wayo zakai min" na faɗa ina zame wa a lkcn da ya kai hannu zai cafko ni


  Taku ɗaya yayi ya cafekeni ya ɗaga ni sama inda ni kuma ina ta wuntsile wuntsile ne na ina ce bana so bana so

 Sauke ni yayi dai dai fuskar sa yace min

"baby na bakya so na"

  Yadda naga ya nutsu ya sani ni ma shiga taitayi na

"ina sanka mana" na faɗa ina shigar da kaina jikin sa

"to me zai hana a barni in nuna miki yadda nai missing ɗinki"


   Ban tanka masa ba hakan ya bashi dama fara kwance min tsarabar da ya taho min da ita 😜😜😜😜



 *******************



  Lallai gaskiya sabit yai wani abu wai shi missing ɗina, don haka ya dinga min kuka, yana roƙona kar in sake in kuma cewa zan rabu da shi


 Wallahi sosai ya bani tausayi, inda nima daga ƙarshe na tausaya wa kaina don kuwa tas sai dana biya bashi ba sassauci



   Sai da mukai wanka sannan ya buɗe ƙofar inda yace min in kira anty fannah yunwa yake ji, tooo fa anan ake yin ta wallahi bazan iya fita


 Babu yadda be yi da ni ba amma naƙi wallahi kunya nake ji, sai daya gaji da tsokanata sannan ya ɗauki wayar sa ya kira ta wanda bata daɗe ba sai gata ta shigo


"haka da wuri na ɗauka sai kun yi awa uku haka"


"wannan ƙanwar taki itace ta hana mu sake wa da yaya ma ta yadda" nintsini na mannara masa, zabura yayi kamar da gaske

"kinga har da mintsini na a gaban ki"


  Harara ta doka min wacce ya sani ƙaɗa shigewa jikin sabit shi kuma jin daɗin hakan ne ya sashi ƙara rungume ni


 "sai wani shishshige mishi kike yi sam baki iya saukar baƙi ba ko ruwa balle abinci amma kin iya shishshige masa"


 "kai anty wallahi ba haka bane"

"ke kika sani bari inje in kawo maka abinci in kuma kafin in dawo kun kuma komawa sai a tabbatar an rufe ƙofar don kar inga abinda ya fi ƙarfin idon"


 Ta fita tana dariya, ƙara jawo yayi jikin sa ya fara wasa da kitson da ke kaina yana faɗa min yadda yai kewa ta sauraren shi kawai nake yi ina ƙara tausaya masa lallai tabbas yayi kewar tawan


  Har ta kawo abincin ta zauna yana ci muna ɗan taɓa hira har ya gama sai da ya gama sannan ya miƙe suka shiga ciki domin gaisawa da mutan gidan lallai ma aka ce namiji ba kunya



  Ba shi ya tashi barin gidan ba sai kusan ƙarfe goma, inda anty fannah tace min in bishi sam ban so hakan ba amma sai dabta matsa min na bishi inda na bar yaran a nan gidan su wajen baaba


  Hotel muka je muka kama, wanka kawai mukai sannan muka kwanta wanda duk wata maganar sabit bata wuce ta kewa ta da yayi ba,


 Kashegari da sassafe ya kama hanyar abuja, inda ni kuma ya mai dani gida, da faɗa muka rabu da shi saboda badia ce ta kiɗa shi tana masa magana har ya tashi ya kama hanya ba shiri


  Baza ka taɓa canza wa ba sabit na faɗa a raina



  Kasancewar ina jin haushin sa yasa sam ban samu damar kiran sa ba balle inji ya ya sauka


  Sai wajen ƙarfe goman dare duk hankali na yana kan sabit ko ya ya sauka wallahi tunda ya tafi, hankalina yake akan sa na so ace in sa ya ya sauka amma sam banna son kiɗan shi saboda nasan suna tare da badia kuma sam bana son kiran shi idan suna tare kamar yadda bana son ta kira shi idan muna tare da shi



  Wayar anty fannah ce tayi ringing yadda naga ta kalli wayar tai murmushi yasa na san isma'il ne ɗauka tayi da sallamar ta suka gai sa


  Sai naji tace gata nan, nan da na gabana ya faɗi me ya faru,

Innalillahi wa inna ilaihi raji'un kawai naji tace me ya same shi


 Tuni na gama tsurewa Allah Allah nake yi ta gama waya ta faɗa min menene, Allah ya sa ba wani abun ne ya samu sabit ɗin ba


  Sai da taga ma sannan ta kalle ni tace min asmau sabit ne yai accident a  abuja yanzu yana asibiti be ma san wanda yake kansa ba


  Wani irin kuka ne ya ƙwace min sabit ɗin nawa ya Allah kar ka kashe min sabit ɗina ya Allah ka dube ni marainiyar ka kar ka raba ni da mijina ya Allah ka dube ni ba don halina ba ina faɗa ina kuka ina haɗa kayana


 "anty wallahi tafiya zanyi wallahi wajen sabit zanje inga halin da yake ciki"

🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦

        *A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
                   
              🍷🍽🥛


  👩🏽‍🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽‍🍳




  🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠





 🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚




      
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)







*ALLAHUMMA BALIGNA RAMADAN BIL IMAN* 🤲🏻🤲🏻





*HIKIMA WRITERS ASSO.*




   P⃗a⃗g⃗e⃗  30🌹






 Sai kashegari da sassafe sannan muka kama hanyar a jirgi,


  Muna sauka directly asibitin muka wuce inda na tarar da tashin hankali wanda ban taɓa gani ba


 Sabit ne a nannaɗa kamar me, baka ganin komai nashi sai idon sa wanda yake a rufe sai kuma bakinsa sannan hancin sa wanda yake ɗauke da oxygen


 Mummy ce a zaune akan sallaya tana addua, jikin ta ne na faɗa ina kuka, rungume ni tayi ita ma muka cigaba


  Sallamar daddy muka ji, wanda hakan ya sa muka sake sakin wani sabon kukan

 "nasiha ya zauna yai ta mama akan mu gode wa Allah tunda ba wani abun bane, karaya ya samu a cinyar sa ta dama sai kuma ƙafar sa ta hagu


 Sannan hannun sa na dama ya samu karaya, na hagun kuma ya samu gocewar ƙashi da kuma tsage war sa" kuka na kuma saki sosai


 Lallai bawa ba a bakin komai yake ba


 "daddy kansa fa da a ka nannaɗe" na tambaya don ni sam ban yadda da naɗin kan na ba


  "Ba komai ɗan bigewa yayi a kan"


  Na ɗauka zasu gaya min abinda ya same shi sai naji sun yi shiru ni ma haka, ƙarasawa nayi kusa da shi na kira sunan shi


 Amma sam be amsa ba kamar ma bacci yake yi ko a sume yake oho,

"mummy bacci yake yi ne"

Ajiyar zuciya tayi ba tare da tace komai itama kamar bata sani ba,

Likitoti dai sunce zai farka, zuwa yamma,

"Allah ya kaimu shine kawai abinda nake cewa"


  Zuwa goma ƴan gidan an cika asibitin ana ta kuma jaje


 Daga ganin su ba wanda ya san me ya same shi, don cewa sukai kawai kiran su akayi aka ce yayi accident, to me ya haɗa su da badia


 Tabbas ko ba a faɗa ba nasan badia tana bayan wannan hatsarin nashi amma kuma Allah ne masani


 Har zuwa yamma ba abinda ake bashi sai kunu, inda ake feeding ɗin shi ta hanci sam be ma san inda kansa yaba


 Sai ledar ruwa da yake ta shaa,

  Bayan magariba aka kuma cika ɗakin lkcn duk sun dawo daga wajen aiki, kusan anan suka ci dinner ana yi ana jajan tawa juna, isma'il ne yace


 "shin mummy wai badia bata san sabit yai accident bane ni sam ban ganta ba"


 Taɓe baki tayi taƙi cewa komai, ragowar ne suka dinga tankawa ni dai ban ce komai ba saboda kar ince wani abun ace kishi ne amma ni kaina naji haushi


 Sai goman dare sannan aka tashi tafiya mummy ce ta kalle ni

"asmau kije gida ki huta kinga tunda kuka dawo twins suke gida sam basu gan ki ba, gwanda ki tafi, don ma nace a kai su can gidan mu ba naku ba, kije ki zauna acen har muga yadda hali zaiyi"


 Kuka na saka mata

"wallahi mummy ba inda zani, jinyar mijina zanyi, mummy don Allah ki barni in zauna anan"


  Na ɗauka zasu goya min baya sai naga kowannesu yana cewa in tafi in huta na dinga zuwa da safen tunda ba komai ake masa mummy ma ta isa



 Kuka sosai na dinga yi, inda a lkcn daddy ya shigo yaga halin da muke ciki sosai ya musu magana akan su barni, gwanda in zauna ana hankali na zai fi kwanciya akan ina gida


  Naji daɗin yadda daddy yayi supporting ɗina lallai shi kaɗai ne yasan halin da zan shiga idan na koma gida a wannan halin



Sallama sukai suka tafi, inda ni da mummy muka zauna, yadda aka tsara shine zan dinga zuwa gida sau uku ina bawa yara nono kullum ko a dinga kawo sun suna sha


 Na yadda da wannan tsarin amma sam bazan yadda inyi nisa da mijina ba


Haka muka kwana lfy vba wani abu sam sabit ko motsi ba ya yi, sai dai in ya daɗe da kwanciya likitocin su zo su juya shi su gyara masa kwanciya wanda sam ko motsi baya yi idan an taɓa shi kamar wani matacce


  Zuciyata tana karye wa idan naga wannan halin da mijina ya ke ciki wai wannan sheine sabit ɗin dana sani kai ɗan adam ya shiga uku



*******************



Tin muna sa ran farfaɗowar sa har abin ya fara bamu tsoro, likitocim ne suka bada shawarar za a kuma ɗauko wani likitan ƙwaƙwalwa ya duba ko akwai matsala a ƙwaƙwalwar ta sa wacce ta hana shi farfaɗowa


   Likitan dr. jamal daga lagos ya zo, dole da accomodation ɗin shi da komai nashi su daddy ne suka ɗauka


  Sai da ya zo sannan aka kuma yi wa sabit general check up inda aka gano ,akwai matsala a kansa hmmm wata sabuwa inji ƴan caca



   Dole tasa akai emergency operation na kansa inda akai masa fixing matsalar

Awan su shida a cikin theater inda daga baya aka gangaro shi aka fito da shi kamar matacce,


  Babu wanda bai yi kuka ba lkcn da muka ganshi kamar ba rai a tattare da shi,


 Awa 48 aka bamu akace in bai tashi ba dole a kuma wani, addua ce kawai tamu yanzu da kuma fatan ya miƙe, kusan bana daɗewa sai na kalli agogo ina yi ina lissafin awowin kamar basa gudu



 Anty fannah ma ranar da akai masa theater ta dawo lkcn kwanasu goma sha ɗaya, itama tana ganin sa kuka kawai ta saki sabida gaba ɗaya sabit ya canza kamaninsa na da sun canza ya wani kunbura kamar ana hura shi



  Har dare ta kai sannan ta tafi akan itama zata koma ɗakin mummy ta ci gaba da jegon ta saboda ta dinga saka ido akan yaran namu


 Sosai mukai mata godiya ni da mummy don kuwa ragowar ba wanda ya kawo wannan abun a ransa


  ********************


Yau kusan kwanan mu goma a asibitin amma sam ba badia balle wani wani nata tun abin baya damuna har ya fara damuna nai wa mummy maganar


  Kuka kawai ta fashe min da shi

"asmau kin san kuwa badia itace silar wannan abun da ya samu sabit, wallahi har duniya ga naɗe bazan taɓa yafe wa ƴar iskar yarinyar nan ba wallahi ta cutar min da ɗa ba kaɗan ba"


 Jikina ne yayi sanyi yadda naga mummy na kuka lallai na koka da lamarin badia amma sam ban ɗauka za a ce mijin ta na wannan halin ba amma ta kasa zuwa ko wani nata ya zo ya duba shi



  Hira mukai da ita sosai inda ta dinga bani irin rayuwar da sukai da badia a turkey yadda suka dinga faɗa, akan ita lallai sai sun sake yin dashen don taga ƙwan ta a duniya



 Ooooh ni asmau na ɗauka badia ta bar wannan maganar ashe ba a barta ba, ashe har yanzu badia batai hankali ba


 Yanzu gashi nan abinda ta jawo wa mijin ta kuma sam ko a jikin ta abin be dame ta ba, shin dama akwai mutane masu irin wannan halin a duniya



 Wallahi ko da kuwa za a ce sabit yankan naman jikina yake yi saboda tsabar ƙiyayya na ganshi cikin wannan halin wallahi sai ba zqn bar shi ba sai na kula da shi in yaso idan ya farfaɗo sai mu ɗora daga inda muka tsaya




 Hira muka dinga yi da ita har kusan 12 :30am na dare inda nishin sabit ya tayar da mu daga wajen hirar tamu


   Nishi kawai yake yi na alamar zafi ko azaba, dr. na kira inda ya zo ya duba shi sai yayi murmushi yace aiki yayi kyau


 
   Wata allura ya kuma yi masa a cikin ruwan da aka saka masa sannan ya fice, wallahi a ranar haka ya kwana yana wannan gunji wanda kuma ni da mummy muka kwana muna masa addua tare da kuka shaɓe shaɓe


  Sai gab da asuba sannan yai shiru alamar bacci, sai a lkcn nima na ɗan rintsa inda mummy ta ɗauro alwala ta tayaɗ da sallah


  Tun daga lkcn kullum da daddare sai sabit ya mana wannan gunjin indak aka ce sha biyu tayi na dare ya fara kenan sai a suba


 Kuma duk wannan abin da yake yk sam be farka ba balle ya zauna


  Rannan da yamma wajen ƙarfe huɗu na yamma, lkcn watan mu guda da sati biyu muna zaune sai ga badia da bbn ta


 Nai mamakin ganin ta, sosai muka gaisa da mahaifin natan inda ya bada haƙurin wai wallahi baya gari ne sai daya dawo sannan ya samu lbr


  Sam badia bata ji kunya ba ta ƙaraso kusa da gadon da sabit yake kai, kallo. Shi tayi sannan ta taɓe baki

"Allah ya sauwaƙe" bbn ta ne ya hauta da zagi da faɗa, wallahi wani haushi da ya ziyarci zuciyata kama in maƙe ta


 "hjy fatima gatan su haɗu ita da ƴar uwar tata suyi jinyar mijin su ke kuma ki koma gida ki huta, ai ba haƙkin bane jin yar saba"


  Ƙiri ƙiri mummy tace bata yadda ba in badiara zatai jinyar ta zauna mu haɗu mu uku amma ita sam baza ta bar ɗan ta ba


 Ganin hakan ne yasa itama badiar tace

"daddy kawai ka barsu su dinga kwana ni na dinga wuni, don Wallahi ni ban ma san ta yadda zan fara kwanan asibiti ba"


 Harara ya bita da shi sannan sukai sallama akan zata dinga zuwa da safe tana wuni mu kuma mu dinga kwana sai mu dinga shiftinga kamar gaske



   Sam badia bata nuna tausaya ga sabit ba sai ma dai kamar wani da take yi kamar da gayya







 Badia aka fara zuwa jinya amma sam ba abinda take yi wuni take tana chatting ko kuma idan ta zo sai ta ajiye jakar ta ta fice


  Ba zamu kuma gani ta ba sai dare, dats in ta zo ma kenan, wannan abun ya fara bawa mummy haushi rannan da ta zo mummyn tai mata tas ta ce kuma idan ta kuma takowa sai ta saka an mata duka, tun daga lkcn ta daina zuwa


 *******************


  Sai da sabit yai wata biyu sannan aka cire masa naɗin gaskiya yanzu ya samu sauƙi sosai, yanzu fara koyan tafiya kawai ya rage mana



 amma kuma wani abun mamaki ga sabit shine sam baya magana


  Baya wani abu ko na farin ciki ko baƙin ciki, baya umm baya umm umm, haka yake kamar wani mutum mutumi


 Kuma wani abu da yake yi shine, kawai yana zaune sai ya saki pupu ko fitsari, ran da muka fara ganin wannan abun ni da mummy mun yi wani abu wai shi kuka


 Ko da daddy ya zo aka faɗa masa shima abin ya bashi mamaki, dama tun kafin lkcn ya na complain ɗin rashin maganar sabit ɗin


 Dole ta sa aka sake yi masa check up, mu dai ba a faɗa mana ko menene ba daddy de yace mana dole sai an fita da sabit waje an duba masa kan sa,


 Sam ban kawo komai ba, muka ci gaba da jinyar sa inda yanzu ƴan uwan sa maza suke koya masa tafiya


  Rannan sai ga badia da mmn ta sun zo, tunda sabit ya kwanta a asibiti in banda bbn badia da yake zuwa a kai akai ba wanda muke gani nata


  A tsats tsaye muka gaisa don mummy ko kallon inda suke ma bata yi ba



 "sannu sabit ashe kuma haukace wa akayi, Allah ma ya taimake ka kana da wata matar ta kula da kai amma wallahi ƴata ba kalar wahala bace don haka wallahi baza ta wahalta maka ba"


 Mummy ce ta miƙe ranta a ɓace ta matso har kusa da mmn badiar kamar zata dake ta

"duk rashin mutuncin da kuke yi ban taɓa tanka muku ba amma ki rasa abinda zaki ce wa wanda ya rufa wa ƴar ki asiri sai haukace wa, ai in ya haukace ya shafi ƴar ki tun za ace mijin ta ya haukace"


  Wani banzan kallo ta bi mummy da shi sannan tace

"au ance fa ku ba a faɗa muku maganar haukan sa ba, ai ya samu matsala ne a ƙwaƙwalwar sa" ta faɗa da fara'ar ta


 "wannan abun da yake yi ai duk samun taɓin haukan ne, baki gani, in ba mahaukaci ba wanene be san komai ba sai dai komai ayi masa, haba ki duba mana"


"maama ni fa wallahi bazan iya zama da mahaukaci ba haka kurum a dinga ce min matar mahaukaci" inji badia


"barsu a wallahi dole ne ma a sakar min ƴa da ƙuruciyar ta baza ta ƙare a jinyar mahaukaci ba, wallahi ko a samu me sakar ta a cikin ku, ko in kai court a ƙwatar mata ƴancin ta yana lafiyayye ne ya ke mijin aure amma yanzu ya zama sai dai yai depending akan wani to wallahi ba dai badia ta ba" inji mmn badia


 Gaba ki ɗaya service ɗin kaina ne ya ɗauke na rasa abinda ke damu na haba biri yayi kama da mutum ashe matsala ya samu a ƙwaƙwalwar sa


 Tausayi ya kuma bani kallon inda yake nayi yana kwance idon shi a buɗe yana kallon sama, baya umm baya umm umm,


 Wasu hawaye naji suna zubar min na tausaya masa Allah sarki sabit Allah ya tashi kafaɗar ka


 "wallahi ba ɗa bare jika bazan zauna a matar mahaukaci ba, Allah na gode maka ma annur ɗin ba ɗana bane Allah na gode maka banni da ɗa da shi balle ace min ko don ɗana in zauna"


 Kallon inda nake tayi

"kema wallahi ki kama gaban ki tun da jajayen sahun ki kar ki zauna ki yi jinyar sa a banza ya haukace bashi da wani amfani yanzu" mari kawai taji na sauka mata shi a fuskar ta wanda ni kaina ban san lkcn da na yi hakan ba


  Ɗaga hannun ta tayi zata mare ni wanda kafin ta sauke shi a kan fuskata, na kuma ƙara mata wani sannan na rufe ta da duka


  Mmn ta ce ta hau duka na wanda sam bana ji buri na sai nayi wa badia illar da ita sai an kwantar da ita don ta san cewa tsautsayi yana kan kowa


 Sai da mummy taga abin namu da gaske ne sannan ta kira nurses suka raba mu


 Zage zage suka dinga tare da kiran sabit mahaukaci miskini mara amfani wannan kalmar itace take ƙara ƙona min rai na


  Sai da suka fita sannan na fashe da kuka naje na faɗa kan sabit ɗin wanda duk abinda ake yi yana nan kwance sam be ma san anayi ba


 Kuka nayi wanda itama mummy iɓa jin nata, haka muka zauna muna ta abinmu babu me lallashin  wani, har mukai muka haƙura kowacce ta lallashi kanta sam wannan abun ba abin kuka bane


"asmau kema kar ki zauna anan ki ɓata lkcn tunda kinga yadda Allah yayi da shi"


"mummy wallahi ko sabit ya fi haka bazan iya rabuwa da shi ba, balle sam ban yadda da maganar badia ba, kusan yawancin maganar ta ƙarya ce ƙalilan yake gaskiya"


 Mummy ba babu yadda batai da ni ba amma sam naƙi yadda dana ga ta matsa min sai na fashe mata da kuka

"mummy ya za ayi in iya fuskantar ƴaƴana ince na bar mahaifin su ne kawai saboda kawai wata jarabawa ta same shi, wallahi mummy yanzu ne ma nake son zama da sabit fiye da daa, wallahi bazan taɓa barin shi ba wai don wani ya same shi ba"


  Kuka sosai mummy tana gode min tana ƙarawa, muna cikin wannan halin ne daddy ya shigo ya ganmu


  "to menene kuma ku da bakwa rabo da kuka"


 Nan mummy ta kwashe tas abinda mmn badia ta faɗa mana ta faɗa, jikin shi yayi sanyi sai ya samu wuri ya zauna sannan ya kalle yace


 "sam asmau mijin ki be haukace ba, jijiyace ta toshe jijiyar da ke comtrolling tunanin ɗan adam, duk da dai wannan rare case ne ba a cika samun sa ba cikin mutane saboda jijiyar tana can cikin kan mutum amma ba wani abu bane, da an masa aiki an masa flushin ɗinta zai dawo dai dai in shaa Allah"


 Wani ajiyar zuciya muka saki ni da mummy inda daddy yai mana bayanin cewar suna ta processing yadda za afita shi inda za ai masa aikin a china



 Sosai daddy ya kwantar mana da hankalin mu inda yace zai dinga sa ɗaya daga cikin maza su dinga kwana ana shifting saboda yanzu ya riga ya warke


 Gwanda ace da namiji abin sai ya fi sauƙi, tun daga lkcn ƴan uwansa maza suka fara



 Zuwa suna taya mu jinya, kwana ɗai ɗai suke yi in wannan yazo ya kwana gobe wani ne zai zo,



  Mun sai da muka ƙara wata ɗaya a haka kafin a gano lkcn da sabit yake yin pupu ko fitsari, tunda aka dai daici lkc sai ya kasance da lkcn yayi za akai shi toilet kuma cikin hukunci Allah yayi ɗin


 Sam bana ƙyanƙyamin aiki kashin sa ko wani abun, haka ma mummy, ni dai kawai amai ne yake yawan taso min


 Rannan da safe bayan ya gama cin abinci sai ya ɓata bedsheet ɗin da fitsari sam mantawa nayi ban saka shi ba


 Tare da mummy muka kwashe kayan inda amai kwai yake ta taso min, bamu gama ba nayi toilet a guje na dinga sheka amai kamar zan amayar da kayan cikina



  Sai da nagama sannan na fito, sannu kawai mummy tayi min sannan tace in je gida in huta zata ƙarasa


 Karɓar kayan naje nayi inda naga ta kauda kayan daga kusa da ni

"asmau kin ma yi ƙoƙari wallahi bazan taɓa judging ɗin ki ba, amma wallahi bazan taɓa zama inga kina takura ba saboda jinyar sabit, jinya sam bata da daɗi kna da zaɓin da kike so ko ki zauna da shi ko ki tafi, amma ya za ayi ina kallon yadda kike kuma ince ki cigaba wallahi asmau na yafe ki koma gida ki kula da yaran ni kuma zan kula da shi har Allah ya bashi lfy"


 "wallahi mummy ba a takure nake ba, kawai dai haka kurun sai inji zuciya ta na ta tashi, ko me naci sai ya dawo"


 Kallo na tayi

"yaushe rabon da kiyi period ɗin ki"


 Tsayawa nayi ina tunani, kai 😱😱 kar dai ace ciki gare ni, murmushi na gani a fuskar


"dama yace yaje maiduguri ranar daya dawo ashe rabo ne ya kai shi, kai amma naji daɗi" ta faɗa tana rungume ni


 Cikin nawa na kuma shafawa wanda sai yanzu na fahimci ɗan motsin da nakan ji akai akai a cikin nawa


  Wajen sabit ɗin ta jani, yana zaune akan kujerar sa, hannun shi ta ɗauka ta kai kan cikina


 "sabit kaga ajiyar ka kayi sauri ka warke kafin ya zo duniya"


 Kamar ba shi ake ba sam be kalle mu balle ya tanka, wannan abun ya kuma bani tausayi da lamarin sabit kai Allah ka bawa wannan bawan naka lfy


Ko da daddy ya zo sai da mummy ta faɗa masa sosai ya nuna murna da wannan labari, shine ma yace wa mummy muje muji yadda babyn yake



  Lami lfy haka aka gano babyn mu ƴar wata huɗu da ƴan sakita, wannan ya fi komai farin ciki, inda daddy ya kafa dokar dole in daina kula da sabit nima in zauna in kula da kaina


  Sam ƙin yadda nayi, inda daga ƙarshe aka bar maganar akan zan dinga zaman asibitin amma kuma bazan kuma wani aiki ba saboda nima mara lafiya ce



 Sosai nake kula da cikin jikina har lkcn da sabit ya iya tafiya, yana iya tafiya yanzu sosai ba tare da taimakon komai ba, amma matsalar itace yana ɗingishi


  Badia sun zo ita da bbn ta inda ya kawo ta ta bada haƙuri daddy ya so ace an bawa badia takardar ta amma sam sai bbn ta ya ƙi, yace a bari a ga in kai masa aiki da za ai masa a waje yadda hali zai yi


 Wannan ne yasa har yanzu badia take a matsayin matar sabit amma sam bata zuwa ko bbn ta ya matsa mata zata zo amma maganar da zat dinga yaɓa wa sai kace dama bata zo ba


  Lkcn da muka tashi tafiya china yayi a lkcn cikina yana da wata bakwai ya ɗan fito amma ba sosai ba, ba  kamar na twins ba



Da ni da mummy, isma'il sai anty fannah mukai tafiyar domin neman lfyr sabit,


  Ranar da muke je a ranar akai admitting ɗin mu a asibitin na ƙwaƙwalwa a wani ɗan ƙaramin gari da ke garin yangshuo a birnin Guangxi na garin china




 Sam garin bashida wani girma sosai sannan a zagaye yake da duwatse sai  tafkeken kogi dake gefen gari


  Hanya ɗaya ce wacce zaka shiga garin kuma ka fita ta shi inda a mota zaka sai dai ko in a jirgin ruwa ne shine zaka shigo ta kogi



   Shi kanshi asibitin ba wani babba bana amma kuma duk faɗin china yana ɗaya daga asibitocin ƙwaƙwalwa da ake ji da shi


  Kwanan mu uku aka shiga da sabit theater inda sai da suka sake masa sabon general check up anan suka gano ɗorin da akai masa a ƙafar sa sam be yiwu ba don haka sai an sake ɓalla ƙafar sannan asake masa sabon ɗauri



 Gyaran ƙafar ne yasa aka ɗaga aikin a alkcn da aka saka don dole sai an ɗauko orthopedic dr. sannan ayi masa aikin rana ɗaya



  Sati biyu babban likitan na ƙashi ya bamu kafin yazo, wanda ranar da ya zo a ranar aka shiga da shi theater


 Tun ƙarfe 10 :30na dare suka shiga operation ɗin inda za afara masa na ƙafar dana nan ayi masa na ƙwaƙwalwar


  Wannan jar danjar da ke kunne a ɗakin theater room itace nake ta kallo wacce in tana a kunne hakan yana nuna operation ɗin ake yi


 Fatana da burina sabit ya samu sauƙi, awan likitan ƙashin uku cur sannan ya fito, in da yai mana bayanin an gama komai amma sai da akayi masa ciko da ƙarfe a ƙafar tasan


 Inda zai dinga zuwa ana duba after every six months kafin ƙafar ta dawo dai dai a cire masa

 Sam banji daɗin wannan labarin ba duk da dai na godewa Allah amma nafi son jin sakamakon operation ɗin ƙwaƙwalwar


 Ƙara kwantae nama da hankali yayi akan kar mu damu, wanda zai masa na ƙwaƙwalwar ƙwararre ne,

 

  Riƙe hannun likitan nayi

"pls can i watch da operation" na tambaye shi


Gyaɗa kansa yayi sannan yasa wata nurse ta rakani, sai da na canza kaya zuwa kaya irin nasu na likitoci sannan na shiga nima amma daga gefe nake inda zan dinga kallon komai da komai


   Wani irin ɗan iskan operation akai masa wanda ba 'ai masa allurar bacci ba idon sa biyu


  Sai da aka fara masa aski sannan aka yanke fatar kansa sannan aka buɗe ƙoƙon kan nasa da wani abu kamar ana drilling grrrrrrrrrr haka kawai kake ji yana yi



  Sun daɗe suna abun su nidai ina gefe ina kallo a wata na'ura yadda suke abin nasu, ashe haka ƙwaƙwalwar mutum take


 Tsab suka dinga abin a hankali a hankali, shi kan shi dr. ba directly yake abin ba, ta microscope kake ganin komai na cikin ƙwanyar kan nasan, yana yi ana goge masa gumi sannan ana miƙo masa duk wani abu da yake buƙata



  Sai da ake je wajen da jijiyar ta toshe sannan  sannan naga ya buɗe ya saka wani abu kamar ɗan zare ya soka cikin wata jijiya haka



   Tsab abin ya shige  ya kuma ɓata ɓat a cikin jijiyar, wani ɗan abu kamar allura suka saka a gurin da wannan abun ya shige sannan suka kunna


   Ba wani ƙara da abin yake yi sai dai jijiyar ce take ta girgiza kamar ana jijjigata


 Sun yi hakan kusan na minti ɗaya sannan suka dakata, wani likita ne yaje gaban sabit yai masa magana


 Abin mamaki sai ya amsa, kaiii


 Ya tambaye shi sunan sa, tsab ya bada amsa, ɗagowa sukai suka kalle ni alamar gaskiya ya faɗa na ce yes


 Suka dinga masa tambayoyi akan rayuwar sa yana basu amsa dai dai kuma duk amsar da ya basi sai sun tambaye ni na gyaɗa kai


 A haka suka ci gaba da masa aikin ƙwakwalwar ana yi masa suna masa tambayoyin har aka gama



   Sai da aka gama tsab sannan akai masa allura waccw ta saka shi bacci dole sannan suka rufe masa kan nasan shike nan aka gangaro da shi



 Kuka na dinga yi na murna kamar me, har sujjadar shukuriyya sai da nayi na godewa Allah daya bashi lfy


 Kwana huɗu aka bashi akan zai yi bacci kafin na sai su tashe shi, in dai be tashi ba in kuwa ya tashi shike nan



********************


Ranar da sabit zai farfaɗo ranar daddy da badia suka ƙaraso bata tanka min ba nima bance mata komai ba amma sosai ta nuna mamakin ganina da tayi da tsohon ciki haihuwa ko yau ko gobe


 Ina kallon ta har ƙasa ta durkusa ta gaida mummy, nace ai yanzu mummy tana da mutunci tunda dai kunji labarin haukacin ɗan ta ya warke


  Tashi nayi na basu wuri don naji tana son ayi hira da ita, ɗakin da sabit yake kwance na shiga na zauna kusa da shi


 Ɗan kwantar da kaina nayi kusa da shi, ban san lkcn da bacci ya kwashe ni ba, ina cikin baccin naji kamar ana taɓa min kai na


 Buɗe ido na nayi sabit ne amma idon sa a rufe yake sai bakin sa daya furta wata kalma wadda sai da na ƙarasa kusa da shi sannan naji inda naji yana cewa

"only" kut mar lallai ma sabit ɗin nan kana farfaɗowa badia ka tuna ba ni ba ko


 Haushi ya kamani kamar in make shi ficewa nayi daga ɗakin zuciyata a kufule


  Mummy suna zaune da badia na same su kallon ta nayi a wulaƙance sannan nace


"ya farfaɗo yana neman ki" dukkan su juyowa sukai suka kalle ni

"niiii" inji mummy, girgiza kansa nayi sannan nace

"only naji yana kira" da saurin ta badia ta miƙe

"Allah sarki *SD* na ko da ka farfaɗo ni ka fara nema aka ce true love never fades" tashi tayi cike da yanga ta shige ciki ta bar mummy da mamaki ni kuma da takaici


"wallahi mummy bazan kuma ɗaukar wulaƙancin sabit ba"

 Kasa magana mummy tayi

"hmmm banni dai ya kasa nema na ya kasa neman kowa sai wannan ƴar iskar wallahi bari ya dawo hayyacin sa sai dai ya zaɓa ko ni ko ita"


  Haɗa kai mukai ni da mummy muna ta jajan tawa juna,


 Buɗewar ƙofar ɗakince ta samu juyawa mukai duban mu ga ƙofar, badia ta fito ranta a ɓacd ko kallon inda muke bata yi ta fice fuuuuuu kamar wacce aka zaga


 Binta mukai da kallo sannan muka miƙe muka shiga ɗakin, inda muka tarar da sabit a zaune

"only " naji ya kuma cewa yana kallona, harara na doka masa, wacce ta sashi murmushi

"mummy kinga only baby ta tana harara ta ko bayan bani da lfy"


 Kallon sa tayi taid murmushin jin daɗi sannan tace

"wannan tsakanin ku kunfi kusa, ni dai duba lfyr ka nazo yi tunda na ga ka watsatsake barin in kama hanyar in tafi apartment ɗin mu in huta, Allah ya ƙara sauƙi"


 Gaba ɗayan mu muka haɗa baki muka ce amin, tana gamawa ta fice ta bar mana ɗakin,


"zo nan mu only" kallon sa kawai nayi na ɗauke kaina, lallai ma sabit ɗin nan gwanjon sunan da yake kiran matar sa zai laƙa min saboda ya mai da ni second hand



  Matsamin yayi sosai wai in ban matso ba zai taho da kansa, ganin ƙaton bandage ɗin dake ƙafar sa ya sani matsawa kusa da shi


 Hannuna ya riƙe, ya kalle ni cikin idona sannan yace

"asmau ban taɓa son kowacce mace ba kamar yadda nake sonki don Allah will u be my only wife 4 ever"


  Girgiza kaina nayi

"ni dai wallahi bana son only ɗin nan gwanjon sunan badia ne" na faɗa fuskata kamar zanyi kuka


"kin riga kin gama da ni a duniyar nan kin min abinda bazan taɓa iya mantawa da ke ba da kuma soyayyar ki gare ni don haka duk abinda kike son a dinga kiran ki da shi hakan za a yi, yanzu gaya min wane suna kike sooo"


 *ASMA'UN SABIT*
shine kawai abinda na iya faɗa,

In shaa Allah in Allah ya yarda ni da asmaun sabit har abada



    Sosai mutumin nan yana kwance yake nuna min soyayya sunfari sunfari kamara ba patient ba, wani abun ma in yayi sai ya bani kunya ko kuma mamaki wallahi sabit ya ɓaci sam baya jin kunyar kansa


 Yana kwance a gadon asibitin nan amma maganar da ke bakin sa tafi ƙarfin sa, sam mummy bata wani daɗe wa inta shigo ɗakin da ta shigo ta ganmu sai ta fice ta bar mu mu sakata mu walawar mu


   Tun randa ta shigo ta ganni a kanannade a jikin ɗanta lips ɗina a nashi, a hankali ta mai da ƙofar ɗakin ta rufe wallahi na ganta sabit ne de sam be san ta shigo kasancewar ya juyawa ƙofar baya


 Tun daga lkcn bata kuma zuwa asibitin ba, ni kuwa kunyar ta sosak nake ji amma da yake ita uwar zamani ce sai bata nuna min komai ba


  Satin sabit biyu da operation na haihu inda na sauka lfy na samu ƴa ta kyakkyawa itama baƙa kamar twins,



 Murna awajen sabit kamar me sam be nuna wani abun akan kalar ta ba sai ma huɗuba da yayi mata da sunana

"Allah ya raya min ke asmaul husna ta" shine abinda yake cewa



  Watan mu biyu sabit ya warke ras kamar bashi ba ga ƴata itama tayi wayo sosai, sai alkcn muka dawo nigeria cike da murna da farin ciki



 Nai mamakin dana ga a gidan mummy zamu zauna ashe isma'il ne ya koma can gidan namu shi da iyalan sa mu kuma zamu ci gab da zama anan kafin sabit ya gama nashi



   Rayuwa muka shinfiɗa ni da sabit ɗina da kuma ƴaƴan mu waɗanda babu yadda mummy batai ba sabit ya bata ɗaya amma ƙiri ƙiri yaƙi sai dak suje can suyi wasa ko da rana amma in dare yayi ko sunyi bacci sai ya ɗauko su sun dawo part ɗin mu



 Babu wanda yasan sabit ya saki badia sai da daddy yace yaje ya dawo da ita inda anan ne ya ke shaidawa cewar shi ya sake ta ko kaɗan daddy be so hakan ba mummy kuwa har addua sai da tayi masa saboda nuna murnar ta




  *BAYAN SHEKARA GOMA*


  Rayuwa babu yadda bata juyawa ,muna zaune lfy da mijina inda a yanzu ina da ƴaƴa takwas shida daga cikin su mata ne kuma baƙaƙe sai ɗan autana me sunan daddy wanda yake kamar annur fari tas kamar sabit


 Na ɗauka irin sabit zai rawar ƙafa dan haife shi amma sai naga saɓanin hakan


"kai yanzu yayin baƙaƙe akeyi" ya faɗa lkcn da ya ɗau baby irfan, harara na doka masa

"ina ka koma kenan" na tambaye shi

 Murmushi yayi ya ajiye irfan ya matso kusa da ni tare da rungume ni sosai sannan yace


"kalar asmaun sabit ce dole ne in sota


I really love u my asmaun sabit" ya faɗa yana haɗe lips ɗinsa da nawa



 *TAMMAT BI HAMDULILLAH*


*Godiya sosai ga dukkan masoyan wannan littafin anan na kawo ƙarshen sa Allah ya sada mu da alkharinsa*


*ayi ramadan lfy Allah ya bamu alkhairin da ke cikin ta sannan ya raba mu da sharrin da cikin ta*


 *pls kusa my cutie walid a  adduar ku mura 🤧🤧 ta danƙe min shi*


  Sai mun haɗu a next Littafina


*RABONA CE* wanda in shaa Allah bayan sallah amma kafin lkcn


*I LOVE Y'ALL*😘😘😘

  Bis salam nice a kullum


```mmn walid and walida ce```

 Mrs Aliyu 🤝🏻


Download Auren Bauta Littafi Na Daya Complete