[2/21, 2:29 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABANKASA💞 
*2*
By *Reefat yahya*


Bayan sallar magariba iyalan suna zaune suna shan fruits yayan shuairat ne ya fara magana" baba dama a wajen aikinmu ne an bani gida,shine nace tunda baby tayi graduating y not mu koma Abj tare da Ku gaba daya" yayi kyau Allah ya kara budi ya muku albarka " ..yeee xan koma Abj da xama , hapie me" shuairat ta fada da karfi tana murna." Ohh yar nan yaushe zaki girma ne? Mama tana kallon diyar tata " ke de kin Faye takura wllhi, kin sa mata ido sosai ba dama ta sake Sam a gidan nan" hmm malam kai de baka son jin laifinta Ku kuka shagwaba ta ai"  shuairat  ta wani tura baki ta tashi daga inda take ta koma kusa da babanta.." Dama nasan mama tafi son yaya kullum tana hantara ta " murmushi sukayi yayan nata ya jawota kusa dashi yace" yi hkri baby mama na sonki, duk sunfi sonki ma a kaina kuma kinga nima ina sonki koh" kai ta gyada masa tana jin dadi." Dama ina son maka xancen aure, ka girma babana u r 35 now ya kamata ka ajiye family " hakane baba insha Allah xanyi kokari Ku tayani da adua " ba komi Allah ya sanya alheri ya baka mace tagari" ameen " se kuma Ku fara shiri ina so ko jibine mutafi sabida 3days aka bani " Allah ya kaimu " haka Suka cigaba da hira ckn walwala da son junansu. 

******** 
Da safe bayan sunyi kari shuairat ta dau wanka ckn wasu pepalace darkblue n red ta saka yankunne red tayi kyau sosai dayake ita wankan tarwadace se kalar kayan sun mata kyau, tana xaune kenan shukrah ta shigo tare da sallama kayansu iri daya itama tayi kyau sosai ta gaisa da mama sannan Suka shige dakin shuairat." Ke mutuniyar xan tafi Abj' 😳😳 shine har wani dadi kike ji? Bayan zaki tafi ki barni nan hawaye ya cika idon shukrah, " so sorry bestie nah kinsan baxanso rabuwa da ke bah but yaya ne yace xamu koma can tareda su baba da mama kiyi hkri pls" nan Suka rungumi juna shukrah kam se hawaye itama shuairat ta fara nata kukan an rasa mai rarrashin.ya shigo dakin tare da sallama...gurus!ya ja ya tsaya " lafiyanku kuwa? Kun shige daki se kuka kukeyi kamar wadanda aka aikowa sakon mu2wa" yaya shukrah CE bata son intafi in barta kuma nima bana son rabuwa da ita" hmmm lallai rashin duka na damun Ku , if not haka kawai hmmm" yasa kai ya fice yaje yana  sanarwa mama, tana dariya tace " kadan ma ka gani in har shukrah da shuairat kam alamarinsu se Allah" tsaki yaja cike da jin haushinsu ya wuce falon baba.dakyar mama ta lallabasu Suka shirya xuwa makarantar su.tun a bakin gate aka rubuta da many an harufa *FEDERAL POLYTECHNIC MUBI* wato makaranta ta gwannatin tarayya dake can mubi jihar Adamawa,Nigeria. Makarantar ta cika makil da jamaa yanmata da samari, iyayen dalibai ga yara kanana da dai sauransu. An fara gabatar da taron daga karshe anci an sha mutane sun fara komawa gidajensu a yayinda dalibai Suka cigaba da daukan hotuna.shukrah da shuairat suna tsaye a gefen wasu masu daukan hoto, kamar a mafarki se ga saurayin da Suka hadu jiya yana murmushi ya karasa tare da sallama " wato don kinsan xan kiraki shine kika kashe wayarki koh? Ohh har ga Allah ita ta manta dashi kuma dama bata damu da rike waya bah murmushi tayi tare da cewa"no ba haka bane" bayan sun gaisa nan ya gabatar da kansa a matsayin yana son shuairat kuma har ga Allah yana sonta da aure yace sunansa Abubakar Ahmed imam, shuairat tace xatayi tunani a kai daga nan sukayi sallama ya tafi suma Suka koma gida.da dare shuairat ta kasa tabuka komi se kuka takeyi tun mama na rarrashinta har ta gaji ta daina kulata, shukrah ma sun zo tare da innarta sunyi koke kokensu dakyar aka rabasu.haka makota Suka dinga shiga suna musu sallama , baccine ya saceta bata farkaba se da asuba.tayi sallah tare da wanka a daddafe Suka karya daga nan Suka kulle gidan. Ckn mota ma shiru tayi ta jingina jikin mama, baba yana gidan gaba yaya kuma shi yake tuki Suka dau hanyar xuwa Abj......

Safe journey Alh bello maiha n co
[2/21, 2:29 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABANKASA💞
*3*
By *Reefat yahya*

Yamma lis ...Suka shigo birnin tarayya Abj wohoho shuairat tayi kallo kam har ta gaji domin shine karo na farko da ta fara xuwa garin. Anguwan kubuwa Suka nufa a dai-dai wani gida yayi parking, ya sauko rike da makulli ya bude kofar sannan ya dawo yaja motar Suka shiga. Gidan madaidaici mai kyawun gaske flat ne guda 2se karamin bq.flats din kowanne 3bedrum ne, ya bude musu dayan flat din dakuna uku da falo a tsakiya se kitchen a gefe kowane daki da bayi a ciki abun de gwanin shaawa masha Allah.nan ya nuna musu dakunan, master bedrum ne na babansu se kuma dakunan da suke kallon juna  daya na mama daya na shuairat. Kowannensu ya shige dakinsa , yaya kuma ya fita nema musu abunda xasu ci.dakin gwanin kyau gado ne madaidaici se dressing mirror ga kuma wardrobe a gefe se kuma kofar shiga bayi.shuairat ta fada gadon ckn tsananin jin dadi, ta shiga bayin tayi alwala ta fito tayi sallar azahar da laasar .yayantane ya tura kofa tare da sallama ya ajiye mata Leda yana murmushi yace" my bae ki ci abinci ki huta koh wannan shine dakinki hop u lyk it, akwai kaya a wardrobe idan akwai abinda kike bukata ki sanar dani koh" ckn tsananin murna ta tashi ta rungumesa tace "tank u my guy bana bukatar kmai, kaima kaje ka ci abinci ka huta nasan ka gaji " murmushi yayi sannan ya juya ya bar dakin.
 Ta bude ledar fried rice ne da peppe chckn a ckn tek away se kuma hollandia drink mai sanyi , bata yi wasa ba ta hau ci har taji ta koshi sannan ta haye gado ta kwanta tare da yin hamdala.
Wayarta CE ta hau ruri shukrah CE ke kiranta , sun Dade suna hira daga karshe sukayi sallama nan bacci yayi awon gaba da ita.

**********
D next day mama CE ta share falon ko ina fes ta xuba humra a falon ko ina qamshi ke tashi tana son kunna turaren wuta Amma basu da gawayi n abun  basu da electric burner.yayan shuairat ne ya shigo tare da sallama bayan sun gaisa yace" mama baki huta ba kina wahalar da kanki ina baby ne ta barki kina ta shan wahala" karka damu sharace kawai nayi kuma mutuniyar taka bacci ma takeyi" 
" lallai mama shine idan kin tashi se kice muna shagwaba ta, bayan kema baki son ki sata aiki" murmushi kawai mama tayi ya cigaba da cewa 
" yawwa batun girki kuma ku huta koda  na 2 weeks ne xaa dinga kawowa daga gidan shugaban kasa" 
" anya xaayi haka kuwa?
"Karki damu mama ba komai, yanxu bari in fita in sama mana abun kari" daga nan ta ya kai ya fice.
Shuairat tayi wanka tayi kyau sosai ckn kananan kaya Riga da dogon wando tayi parking gashin kanta da farin ribbon dama wandon nata fari neh kuma pencil ne, rigar kuwa 3qtr gown ce white n orange ta saka orange fashion earings tayi kyau sosai.ta tsaya a gaban madubi tana kallon kanta tayi murmushi tace" Ayshat Bello u ar not soo btiful but I knw dat u ar perfect" ta juya ta bude wardrobe din ....
" wooowww! Ya ilahi wannan duka kayan nawa ne? Ya Allah nagode maka , yaya bash I Lov u sooo ...much " tana magana tamkar yana wajen.bayan ta gama shirmenta ta dauko wani karamin gyale ta yafa sannan ta fice xuwa falo.mama da baba suna xaune suna kallon BBC ta gaishesu daya bayan daya sannan ta koma kusa da babanta ta xauna " baba!
"Naam yata "
" baba kaga kayan da yaya ya siyamin kuwa?
" yayanki Dan albarka ne Allah ya kara mishi budi , nima haka na tarar da sababbin kaya a dakin da nake yace min duk nawa ne" haka nan Suka cigaba da yaba halayen basheer har ya dawo ya samesu .sunyi ta xuba godiya sannan Suka ci abincin da ya kawo musu, daga nan ya musu sallama sannan ya tafi aiki.haka Suka yini gidan shiru shuairat tayi kallo har ta gaji  tayi bacci, da rana ma abinci aka kawo musu lafiyayye daga gidan shugabankasa.
Basheer bai dawo ba se bayan magariba shi ya taho musu da abincin dare daga can gidan, bayan ya huta Suka hadu suna hira a falonsa har xuwa tym da xasu kwanta kowannesu ya koma dakinsa.

Haka rayuwarsu ta kasance ckn kwanciyan hankali da rufin asiri kullum ana kawo musu abinci daga gidan shugabankasa , idan kaga shuairat baxaka ganeta ba tayi kyau sosai tayi fresh alamar Hutu ya bayyana a jikinta.yauma kamar kullum tana xaune tana karanta magazine a dakinta , ita de wannan shugaban kasan yana birgeta gashi very young Amma yana da ilimi yana aiki sosai bai wuce 5montz akan mulki bah Amma ko ina ji dashi.yayanta ne yayi sallama a bakin kofa ta bashi ixinin shiga , ya tura kofar ya xauna a kujera a yayinda ita kuwa tana kwance a saman gado." My guy sannu da dawowa". Tnx girl ya kike ya xaman kadaici"
" wllhi ina nan ina fama wannan ma don magazine din nan yana debe min kewa neh".            " ohh dama kina karantawa ne ai ina dasu dayawa a daki nah"
" yaya ka manta I want 2 b a journalist"
" haka ne na tuna,idan result dinku ya fito xan nema miki aiki dashi"
" da gaske? Woww daz y I Lov u, yayana nagode"
Murmushi yayi yana kallonta shi da kansa bai San kalar son da yakewa kanwar tasa bah " ki shirya toh tunda yau weekend xan fita na nuna miki gari " ...yeeehhhh nagode yaya" yana mata dariya ya fita ya bata daman shiryawa.
[2/21, 2:29 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*4*
By *Reefat yahya*

Shuairat ta shirya ckn wasu atampa superwax white background touches of red n yellow adon fulawane a jkn kayan ta daura dankwali tayi kyau sosai , rike dake da karamar purse red color ta fito falo ta same su suna hira nan sukayi sallama Suka tafi.ckn mota yaya bash ne ke ja tana xaune a gefe suna tadi tana kallon gefen titi garin ya burgeta sosai ko ina jamaa ne kowa na ta harkar gabansa tace " my guy yaushe xaka koyamin mota? 
" anytym idan ina free xan dinga koya miki, kuma xan sama miki abin yi bana son xamanki haka nan but se kin huta b4" 
" ok yaya no p" haka Suka kasance ya xaga garin da ita sunyi yawo sosai har yamma Suka koma gida.

********
Haka rayuwarsu ta kasance bayan wata daya result na shuairat ya fito ta fita da second class upper, babu bata lokaci yaya bash ya sama mata aiki a wani gidan jarida  na *JF reporters* gobe xata fara xuwa.murna gun shuairat baa magana babu bata lokaci ta sanarda shukrah itama tayi murna sosai haka nan iyayenta sun sanyawa bash albarka adua sosai Suka dinga masa.
     Da safe ta gama gyare gyaren gidan ko ina tsaf da yake ynxu sun fara girki , kunu sukayi da chips da kwai sai kuma tea saboda baba yana son kunu sosai.bayan sun gama karyawa tayi wanka ta shirya ckn wani lace mai kyau ash n orange, tayi kyau sosai tayi sallama da iyayenta suna mata fatan alheri sannan Suka tafi tare da yayanta.a can maitama office din nasu yake ya sauke ta tare Suka shiga dama tayi interview ta gama komai , a ofishin manager dinsu Suka je bayan sun gaisa yace "  Muawiya pls kaga kanwata bata San kowa ba ka kula da ita don Allah " ba damuwa my man ai tamkar kanwa take a guna" daga nan bash ya tafi ya barta Mr Muawiya ya kirata yaje ya nuna mata kujerar xamanta cos office din a hade yake kowane bangare akwai ofishinsu, misali akwai bangaren fashion magazine, akwai bangaren daily news akwai kuma na weekly reporters wato nan ne bangaren da shuairat take.su 5ne a cikin offis din maza uku mace daya se kuma shuairat. Mr Muawiya ya gabatar da shuairat a matsayin sabuwar maaikaciyar su Sarah tafi jin dadin ganinta sabida dama ita kadai CE mace a cknsu , mr Muawiya ya koma ofis dinsa nan ya bar shuairat Suka gaisa da sauran maaikatan akwai Daniel ..Sadik..Mahmud..sannan  Sarah , ita ma ta shaida musu sunanta " wow! Shuairat wat a nice nem"  " gaskiya ban taba jin irin wannan sunan ba" Mahmud y fada yana murmushi da alama de shine shugabansu nan ya nunawa shuairat aiyukan da xatayi ya bata wasu scripts yace ta dubasu tayi editing. Daga nan kowa ya koma wajen xamansa Suka cigaba da aikin da ya kawo su.tym na sallar azahar yayi suka tashi brk shuairat ta shiga wani madaidaicin dakin da suka tanada don sallah , ta gabatar  da salla daga nan ta fito Suka ci karo da Sarah ta mika mata takeaway tace" ur lunch miss" murmushi shuairat tayi tana mamaki wai dama abinci ma su zasu baka ne? Tamkar Sarah ta San tunanin da take tace mata " kullum oga moawiya shiyake kawo mana lunch he is a nice person" shuairat ta karba tare da yin godiya nan Suka xauna suna ci suna Dan taba hira bayan nan Suka koma bakin aikinsu.haka Suka yini shuairat ta saba dasu duka tamkar sun Dade da sanin juna har yamma Suka tashi yayanta ya dawo ya dauketa Suka wuce gida.
[2/21, 2:29 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*5*
By *Reefat yahya*


Bayan sati daya shuairat ta saba da colleagues nata musamman Mahmud tafi shakuwa dashi.suna xaune a gaban computer suna editing na wani story da aka tura musu , Mr Muawiya ne ya shigo yace " Aishat Bello n Mahmud Adam com 2my office now" yana gama fadin haka ya juya ya koma ofis nasa. Shuairat ta juya Suka hada ido da Mahmud ya sakar mata murmushi yace" c'mon let's go ba wani Abu bane aiki ne zaa tura mu" haka Suka jera xuwa ofishin manager.
 " Mahmud ina son kuje ofishin shugaban kasa Ku masa interview saboda mun samu sakonnin jamaa da dama suna mai son jin tarihin rayuwarsa"
 " but sir ya xaayi mu ga shugabankasa? Shuairat ta tambaya ckn tsananin mamaki
 " daz ur assignment Aishat! Ku xaku nemi hanyar da zaku bi ku gana dashi"
 " sir! Ba kowane Dan jarida bane yake samun ganawa da shugabankasa kasa face Wanda aka gaiyace sa musamman saboda....
  " look Mahmud n Aishat I don't knw u r going 2do dis but nidai ina bukatan details na Mr president kunsan meyasa? Saboda shi sabon shugaba ne Wanda aka bawa rikon kwarya , babu Wanda yasan tarihin rayuwarsa fans namu suna tura mana sakonnin son jin takaitaccen tarihinsa.so tell me, meyasa baxamuyi producing information din bah? N wat do u tink idan har mukayi nasara? Dat minz our company will b among d Best journals in d country "...shiru ya xiyarci dakin sai bugun xuciyoyinsu kake ji kowannensu da tunanin da yake yi.dakyar shuairat ta furta cewa " xamuyi bakin kokarinmu sir"
 " ba kokari nake so ba Aishat biyan bukata nake nema na Baku 5days all d best now u can go pls" ya nuna musu kofa . a hnkli Suka tashi ckn kasala Suka koma ofis nasu, Sarah ce ta lura da yanayin da suke ciki a hnkli ta dawo kusa da shuairat tace " kawa meyake faruwa? ..mtssww manager ne fah wai yana son muyi interviewing Mr president" 😳 huh wannan acting President din? Hmmm lallai u gat job dia Allah ya Baku nasara but is not easy"
 Mahmud kam kasa magana yayi yana ta sake saken hanyar da xasu bi don ganin bukatarsu ta biya.
Haka Suka kasance har lokacin tashinsu yayi yayanta yaxo daukanta nan ta tsaya sallama da Mahmud ya kura mata ido tmkar mai nazarin wani Abu can yace " pls kije ki nema mana mafita kuma ki nemi shawara gun yayanki tunda yana aiki da shi abun xai xo mana da sauki" 
" ok I'll try my best" murmushi ya sakan mata sannan yace " karki manta I.d card naki" " ba damuwa "  " ok a gaida gida" daga nan ta wuce gun mota. 
Ya bita da wani kallon tuhuma ya kura mata idanu " wat! Ta tambaya tana kallonsa .. " baby don't tell me har kin fara soyayya"
" c'mon yaya don't u trust me? Kasan idan soyayya muke xan gaya ma koh"
 " ok I tot" 
" oh is not wat u tink toh"
" mene? F/ship?
"Yayaaa...haa stop it"
" ok ok a gaya min mene?
" yaya I need ur help, muna bukatar taimakonka. My first assignment shine to interview d acting President" 
" wow lallai xaa nuna cute sis a TV kenan?
" hmm..muna Neman hanyar da xaabi mu ganshi kai kana batun xaa nuna ni a TV? Information kawai muke bukata , kuma a newspaper xaa saka ba wai....." Ok nagane don't wory xan Iya bakin kokari xan sama muku hanya kinji? Ki kwanatar da hankalinki my bae "
" ok yaya tank u but gobe xamu fara aikin"
 " no it can't b bcos Baku ckn schedules nasa for d day , so ba lallai bane ku samu ganinsa goben but ku gwada maybe xaku dace"
" ok tanx" haka Suka cigaba da tattaunawa har sun isa gida.

**********************

Sanye take ckn abaya black da adon filawa blue tayi kyau sosai ta rike jaka blue se qamshi ke tashi ko ta ina.Mahmud ne ya iso da motarsa nan ya bude mata kofa ta shiga ya tada mota Suka wuce villa.
Tun a bakin gate securities Suka fara musu wasu tambayoyi duk da cewa sun nuna I.d card dinsu baisa aka barsu sun shiga ba, dakyar wani daga cikinsu ya basu damar shiga.dogon tafiya Suka yi ba komai se kyawawan flowers da kuma masu aiki duk inda ka duba securities ne , can Suka iso dab wani roundabout nan ma an dakatar dasu saida Suka nuna I.d sannan Suka wuce.a takaice de sunyi dogon tafiya kafin Suka fara hango building din ofishin. bayan an bazu izinin shiga wani daki , mamakine xalala a fuskar Mahmud saboda ganin yan jaridu daga kamfanoni daban daban suna xaune daga gani kasan abunda ya kawo su.
Suka sami kujera shi da shuairat Suka xauna se kalle kalle ake a yayinda bodyguards suna kaiwa da komowa.sun share awa 2 ba shugabankasa babu alamarsa , shuairat ta gaji sosai daga idon da xatayi kenan carab Suka hada da yayanta dashi da wasu mutane duk sanye suke ckn bakaken suits dagaa gani kasan securities na Mr president neh, ga wani mutum dogo amma ba can bah da alama de shine shugabankasa domin yanda aka sashi a tsakiya kadai zaka gane ana kula da lafiyarsa.nan take yan jarida Suka tashi kowanne na ribibin xuwa kusa da su ciki kuwa har da Mahmud, shuairat dai ta xauna tana binsu su ido.wani bodyguard ne ya dakatar dasu ta hanyar daga musu hannu sannan yayi magana ckn harshen turanci yace " kuyi hakuri Mr president baxe samu damar ganawa da ku ba don yana da meeting yanxu se nan da awa 2 xe dawo" daga nan Suka juya sukayi gaba a yayinda yan jaridar Suka dinga daukansu hotuna.
[2/21, 2:29 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*6*
By *Reefat yahya*


Haka Suka cigaba da zama har bayan azahar babu Mr president ba labarinsa , yunwa ce ta addabi shuairat tamakr Mahmud yasan me ke damunta ya sa hannu ckn jaka ya fito da chi-exotic ya mika mata tare da cewa" ki karba nasan yunwa kike ji, kuma next tym idan xaki je aiki ki fito da shirin cewa xaki yini a can dou nasan is ur first tym" godiya ta masa ta karba tana sha a hnkli tmkar bata so. Bayan wani Dan lokaci Mr president ya shigo tare da tawagarsa ko ina jamaa ne, babu bata lokaci yan jarida Suka ruga xuwa inda suke.
Wani security ne ya sanar dasu cewa Mr president yana bukatar Hutu baze samu damar ganawa da su bah.
    Jkn rashin kwarin guiwa Mahmud ya kira shuairat wacce take xaune ya sanar da ita halin da ake ciki nan Suka wuce mota ya sauketa a gida..
   Bayan sallar isha tana xaune a falo ita kadai tana kallon CCTV ana yin wani series mai dadi , yaya bash ne ya shigo tare da sallama ta amsa yaxo kusa da ita ya xauna
 " reporter Aisha bello ya akayi " ya fada ckn tsigar tsokana ya sani sarai basu gana da Mr president bah.
Banza tayi masa ta cigaba da kallonta 
" haba cute sis me laifin yaya"
  " look guy am not in d mood , dama ai su shuwagabanni suna da girman kai da Raina talakawa bazasu taba....
  "Calm down hajiya! Mr president bah haka yake bah is just dat u guys ar not lucky bcos 2day....
   " yaya pls don't try to convince ok!
   " am not trying to my dia , I just want u 2understand d situation"
    " hmmm yaya kenan baka son laifin megidanka koh, gaskiya am disappointed ban taba tsammanin haka yake treating na talakawa ba....
   " hey sis! Ina son ki gane cewa Mr president bashi da laifi is just dat yana busy ne"
" ok fine naji" daga nan kowannensu yayi shiru .bash ya tashi ya koma dakinsa ita kuwa ta kira shukrah a waya Suka sha hirarsu.

Karfe 10 na safe ya samesu ne a gidan mr President, yauma irin na jiya ne ko kuma a CE gara jiya tunda sun sami ganinsa duk da cewa basu gana ba.haka Suka yini ko gistawa mr President beyi bah kuma an hanasu shiga har yamma Suka koma gida. A takaice de kwana 4 a Jere suna xuwa basu cimma burinsu bah.
     Suna xaune ckn mota a harabar gidan  shuairat ta juya ta kalli Mahmud tace " kasan Allah! Yau baxan koma ba se na gana da Mr president".  Dariya ne kubcewa Mahmud yace " kada kice haka shuairat"
   " is not funny Mahmud trust me" 
 " ok fine.. I trust u" motocine a kalla xasu kai 11 kyawawa masu tsada Suka jera xasu fita da alama de mr President xashi wani wajene .
  " Mahmud kabi bayansu pls".  " ke lafiyanki kinsan ina zasu je ne?
 " kada ka bata min lokaci pls" ba gardama Mahmud ya juya yana bin convoy na shugabankasa.sun kai 20mins suna tafiya shuairat ta umarci Mahmud yayi over taking ya je kusa da wata farar mota mai bakaken glass da alama shine wanda shugabankasa yake ciki.ckn tsoro Mahmud yace shi baxe Iya bah, shuairat ta cigqba da rokonsa dakyar ya amince yayi over taking yaje dab da motar. Sauran motocin Suka fara horn Mahmud kam ya razana , nan sauran motocin da suke gaba Suka ja birki wannan farar motar itama taja ta tsaya don son ganin wanene ke bin mr President.
[2/21, 2:29 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*7* 
By *Reefat yahya*


Gaba dayan motocin sun xagaya su shuairat da kuma wannan farar motar.securities Suka fito rike da bindigogi babu bata lokaci Suka tunkari motar Mahmud Wanda yayi mutuwar xaune yasan lallai yau kashinsu ya bushe ya juya gun shuairat tana xaune ckn kwanciyar hnkli ta xare I.d card nata tana murmushi tace" idan kunsan wata Baku San wata ba ai" 
Mahmud kam yana ta mmkin halayen yarinyar tana da confidence akan komi bai gama tunani ba ta sa hannu ta bude kofa ta fito rike da I.d card da kuma jotting book nata tana wani shuumin murmushi  "freeze! Wani bakin security katon gaske ya fada da karfi a yayinda ya nuna ta da bindiga , hannayenta ta daga rike da I.d card da jotter tana murmushi.  Securities din suna kallon juna suna mamaki kuma Kansu ya daure don basu taba tunanin cewa mace CE a ckn motar ba.shuairat ta kalli wannan bakin security tace " I min no harm am just a reporter" 
  " hw can I trust u young lady" ta cire I'd card din ta mika masa yasa hannu ya karba a hnkli don su basu yarda da ita bah ganin ta suke tamkar wata Ya'r ta'adda wacce aka turo don kulla wani makirci.ya gana duba I.d card din yace " me kike so?
Babu bata lokaci ta gaya masa bukatarta nan ya juya gun wannan farar motar a hnkli aka sauke glass .mr President yana zaune a baya da jarida a hannunsa ba tare da ya daga kai ya kalli securityn ba ya fara magana" me take bukata"  " she is a reporter sir!
" let her in"
😳urxcellency!
 " yes let her com in here". " but sir we can't trust her"
" Adams dis my command not a request". Ok sorry ur xcellency sir! Nan ya juya gun shuairat ya bata ixinin shiga wannan farar motar bayan ya bude mata kofa.mamakine karara a fuskokin bodyguards din kowannensu da tunanin da yake nan Suka sallami  Mahmud.mr president ya basu umarnin tada motocin don xuwa meeting da zashi.shuairat ta daga kai a hnkli ta sake saukeshi saboda kwarjininsa tayi shiru ta kasa magana 
" young lady ba interview kika zo yi bah? Shiru tayi ta kasa magana dakyar tace " mr President idan bazaka damu ba ina son ka bani tym da zamu sameka a office ni da abokin aiki za....

" kina nufin ke bazaki Iya min tambayoyi ba se abokin aikin ki? Nan ma shiru tayi .yaga dai bata da niyar magana kawai ya umarci p.a dinsa Wanda yake xaune a gidan gaba cewa a rubutawa shuairat notice gobe ta samu ixinin ganin mr President a office. Tayi godiya ta karba sannan aka sauketa a gefen hanya, wani dogon numfashi taja gashi ba waya a hannunta bare ta kira Mahmud kawai ta sami taxi ta wuce office ta karbi kudi gun Sarah ta biya tana shigowa Suka gaisa Sarah tace" ynxun nan Mahmud ya shigo yana gun manager"
" ohh dama yana nan ? Ta tambaya a bukace 
" manager ne ya kira shi yana ta fada wai gobene dateline din aikin da ya Baku" hmm manager baxai gane bane is not easy fah"
" har ynxu basu Baku chance bah? Sarah ta tamabaya tana kallon shuairat
" sarah aikin nan fah akwai wahala"
" yeah I knw , anyway wish u best of luck "
" tanx dear" 
Mahmud ne ya fito daga ofishin mr Muawiya fuskarsa a hade amma suna hada ido da shuairat yaji wani sanyi a ransa." Zo mu gana kanwata" nan yaja hannunta sukayi waje mota Suka shige ya juya suna fuskantar juna" gaskiya u did well"
" tanx" " so ya labari"
" babu fan nikam nace masa gobe zamuje mu same....
" God ! Kin kwabsa girl kinyi wasa da opportunity y?"
" Mahmud mutumin yana da kwarjini sosai wllhi na kasa yin magana a gaban idonsa kuma kasan ni ban taba yiwa wani interview bah"
" haka ne nasan dis ur first tym , but kinsan me? Yanxu xan rubuta miki tambayoyin da zaki masa gobe idan munje ke zakiyi magana" 
" but Mahmud....
" shhhhhh! Ya katse ta tayi shiru sannan yace " idan na baki questions din sai ki kara da naki ok"
"Ok! Nan ya tada mota Suka kama hanyar gida.
[2/21, 2:29 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*8*
By *Reefat yahya*

11:10pm tana kwqnce a saman gadonta bayan ta gama haddace tambayoyin da zata yiwa mr President sai kuma ta fara tunani toh yaransa nawa? Shin ina matarsa? Don gaskiya bata taba jin wani ya ambaci sunan matarsa bah.wayarta ta fitar ta danna layin yaya bash ringing biyu ya daga yace " reporter bakiyi bacci bah?
" yaya I need ur help"
" ok ki bude min kofa gani nan xuwa"
Ckn kankanin lokaci ta fito falo ta bude kofar shiga flat din tana xama kenan ya shigo tare da sallama.
" yaya matan mr President nawa n yaransa nawa?
 " y not gobe ki tambayesa zai gaya miki ai" " no pls yaya ka taimakeni"
 "Ok fine! Mr president bashi da mata a ynxu haka"
" sun rabu kenan?
" ok bari in baki takaitaccen tarihin rayuwarsa....
  Suleiman Mohammed Dan asalin jihar Adamawa ne haifaffen garin mayo-belwa shi Fulani ne gaba da baya, shi kadai ne a gun iyayensa babansa maaikacin banki ne ya tashi a Lagos can yayi karatun primary da secondary sannan yayi first degree a UK ya karanta public administration sannan yayi masters kafin ya dawo ya auro matarsa zainab wacce aka hadasu auren xumunci .sunyi zaman lafiya sosai da ita bayan shekaru 3 Suka haifi ya mace sunanta Aisha ana kiranta umaima daga nan Suka koma Cyprus yayi PhD dinsa a bangaren international relations kafin ya dawo Nigeria ya fara aiki a Lagos, president na wancan lokacin abokin babansa ne shi ya kirasa ya bashi minister of d federation haka ya fara politics bayan shekaru da dama ya rike manyan offices har zuwa tym din president Joshua okafor aka bashi vice president, bayan an sami matsaloli a bangaren mr Joshua senators sukayi meeting aka cireshi aka bawa Suleiman acting president kuma suna son yayi contesting na next election da zaayi.Suleiman is a nice n friendly person b4 mutuwar matarsa , tayi accident da jirgi ta rasu ta bar shi da yara 2 umaima ya'r 18 yrs da sultan 7yrs old.daga nan ya zama shiru shiru kullum baya ckn walwala, kuma baya son shugabancin da aka bashi yana son ajiye aikin a halin da ake ciki wannan shine tarihin rayuwarsa kenan.
Hmmmm.....shuairat ta ja wani dogon numfashi " shekarunsa nawa "
 " he is 45yrs old" " gaskiya yana da jiki mai kyau, bazaka taba cewa yana da ya' har 18yrs bah"
" shikenan koh?
" ehh tank u yaya "
   " je ki kwanta toh" har ya kai bakin kofa ya juya yace "ohh namanta naji labarin yau kun hadu dashi koh? " yaya ...
  ". Yeah kinyi kokari kin kafa tarihi" daga nan ya sa kai ya fita ta tsaya tNa murmushi ita kadai.bayan ta kulle kofa ta koma dakinta ta fara nazarin labarin da yayanta ya bata na mr President. Allah sarki no wonder aka CE yana da girman kai don bai Faye magana ba, tabbas yana ckn matsala Wanda Allah ne kadai xe fitar dashi toh meyasa bai kara aure bah? Oho ta bama kanta amsa haka ta cigaba da sake sake har bacci yayi gaba da ita.

( lols..som people will b wondering wai president 45 yrs old? Anyways don't mind me am just trying to entertain 😊😊😊)
Happyy reading hop kuna jin dadin labarin ....Lov u all😘😘😘😘
[2/21, 2:29 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*9*
By *Reefat yahya*


Da safe ta gama shirinta tayi brkfast ta gama komi tana zaman jiran Mahmud bayan wani lokaci kadan ya kirata a waya ya shaida mata yana kofar gidansu tayi sallama da mama sannan ta fita Suka dau hanyar xuwa villa.
  Ta nunawa wani bodyguard note din da mr President ya bata akan cewa zasu gana dashi yau, firr mutumin ya hanasu shiga haka Suka hakura Suka koma Suka xauna.wasu bodyguards ne Suka fito daga wani bangare sun saka wata yarinya Ya'r kyakkyawa a tsakiya tana tafiya tana waya daga ganinta shuairat ta gane cewa ita CE umaima , a bude mata kofar shiga ofishin baban nata suka wuce ita da bodyguards nata.a ranar ma haka Suka yini ba tare da ganin mr President bah har yamma Suka tashi ckn bacin rai Suka kama hanyar gida. Mahmud ya lura da yanayin da shuairat take ciki na bacin rai don haka ya fara tuannin hanyar da xaibi don ganin ya faranta mata yayi parking a gaban wani supermarket na *cash n carry* ya juya Suka kalli juna yace " sis ki rakani ciki pls"
   " no Mahmud am not in d mood kaje kawai"
  " yi hakuri muje"
  " no just go " haka Mahmud ya hakura ya shiga ya danyi light shopping ya siya mata turare da kuma chocolates sannan ya fito ya ja mota babu Wanda yayi magana bai tsaya ko ina ba sai national stadium.shuairat ta juya tana kallonsa bcos bata taba xuwan stadium din bah murmushi yayi yace " bismillqh " ba musu ta sauka  bayan ya kulle mota yana rike da chocolate a hannu Suka fara trekking har xuwa inda aka tanadi kujerun xama stadium din a cike yake Amma ba makil bah ana kallon wasa ko na ina ne oho! Shuairat dai sai kalle kallenta take nan Suka xauna ya siya musu popcorn da drinks ya mika mata chocolate ta fara ci haka Suka kasance bayan wani lokaci Suka tashi Suka zaga ckn stadium din yana nuna mata ko ina sun dauki hotuna da dama. Daga nan *children's park n zoo* Suka wuce nan ma ya siya musu icecrm Suka dauki hotuna da dabbobi suna tafiya yana bata labaru masu ban dariya har magariba Suka fita ya ajiyeta a gida tare da mika mata ledar cash n carry tayi godiya sosai sannan Suka rabu.

******************
Ta idar da sallar isha tana zaune tana tunanin hanyar da zasu bi su cimma burinsu, wayarta CE ta fara ringing shukrah CE nan ta daga Suka sha hirarsu shukrah tana bata labarin saurayinta Abkr yayi aure .bayan sun gama wayar ne ta ajiye kenan mama da babanta Suka shigo falon hira sosai suke baba ne kawo xancen auren yaya bash yace" 
 Yaron nan bashi da niyar aure ina ganin jibi xan tafi can Adamawa xan nema masa auren shukrah'
  " yeee baba Allah da ka kyauta kuwa"
 " ke dallah rufe mana baki auren dole zaa masa ne malam?
 " haba Fatima kina ganin yaron nan ya girma yana da 30 da doriya zaman me yake yi? 
    " malam ka Dan bashi lokaci man "
 "Ke dai baki son laifin danki"
 " Allah baba shukrah zata dace da yaya" shuairat ta fada ckn marairaicewa
 " rufemin baki, ke da kike zancen yayan naki ke ma kin girma ai aurar dake zaayi" mama ta fada tana kallon shuairat. Bash ne ya shigo tare da sallama ya nemi waje ya xauna " yauwa Dan albarka dama xancen auren ka mukeyi" a hnkli bash ya daga kai Suka hada ido da baban sa." Gani nayi har ynxu baka kawomin wacce kake so bah shine nace mezai hana Ku daidaita da shukrah Ya'r wajen malam Habu"
Shiru yayi shi baya son yayi gardama da iyayensa kuma shi bazai CE yana son shukrah bah kuma bazai CE baya sonta ba hasali ma shi bai taba yin soyayya bah

 ..."kayi shiru baba na"
Muryan mahaifinsa ne ya katse masa tunani 

 " ba komai baba na amince a je a nema min aurenta"

  " masha Allah Allah ya muku albarka"

" ameen " gaba daya Suka amsa.
Shuairat kuwa dadi kamar ta hadiye yayan nata nan kuwa ta rungumesa tana jin dadin amincewar da yayi.
mama ma ta Sanya musu albarka 
Haka Suka cigaba da hira suna shan fruits suna kallon news har xuwa 11pm sannan kowannensu ya koma dakinsa da shirin bacci.
Asuba ta gari 1 family
 


Lov u all my fanx
07030077024 4corrections o advise
😘😘😘
[2/21, 2:29 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*10*
By *Reefat yahya*


Yau shuairat bata da niyyar xuwa wajen aiki bayan tayi sallan asuba ta koma bacci bata  tashi da wuri bah mama taji shiru shine ta leka dakinta tana nan tana baccinta ckn kwanciyar hnkli a hnkli ta fara tashinta dakyar ta bude ido.
Bayan tayi wanka ta shirya tana karyawa mama ta bita da kallo tare da cewa " me ya hanaki tashiwa da wuri"
" uhmm mama ni fah yau baxanje aiki bah"
 " akan wane dalili? Ko wata daya baki yi ba ki fara....
" toh ni mama...ta katseta tana xumbura baki
" kinga malama bani xaki gayawa bah, ki bari yayan naki yaxo se ki gaya masa tunda shi ya sama miki aikin" daga nan mama ta tashi ta bar mata falon shuairat kuwa se kumbure kumbure take .
Ko ya Mahmud ya tashi oho se ynxu ta tuna da cewa wayarta na silent wuff ta koma daki tana daga wayar taga misscalls 15 yayanta , shukrah da kuma Mahmud ta rasa was xata fara nema.
Falo ta koma ta tattara kwaninkan da tayi amfani da su ta wanke tana fitowa taji sallama lallai muryan Mahmud ne. Ta zare mayafi tayi waje, yana nan tsaye a bakin gate ta sakar masa murmushi a yayinda shi kuma ya watsa mata harara tana murmushi tace " tuba nake big bro "
Beyi magana ba ta kama kunne ta marairaice tace 
" sorry naa" wani irin Yarr Mahmud yaji dakyar ya saita kansa yayi gyara murya yace 
" is ok ya wuce Amma gskiya kin bata mana show, kinsan mr President da kansa yace a kira JF Reporters but baki nan na kira wayarki har na gaji baki daga ba, na nemi yaya bash shima yace baki daga ba"
" sorry yayana " nan ta wuce tayi sallama da mama sannan ta dauki handbag dinta da duk wani abunda take bukata.
Yana ckn mota yana jiranta ta bude gidan gaba tare da sallama nan ya tada mota Suka dau hanya.shiru Suka can Mahmud ya katse shirun da cewa

" who knws ma ko ya kira wasu journals olredy"
  " c'mon yaya I said sorry naa"
        " I knw ! Ni ba wai ina blaming naki ne, kawai ina ganin munyi loosing opportunity ne"
 
" kada ka damu insha Allah zasu bamu second chance" a haka Suka cigaba da tattaunawa.

Sun shigo dakin ana ta binsu da ido saboda kowa yaji cewa shugabankasa na son ganawa da su, mutane suna ta gulma ana nunasu shuairat cewa ga yan *jf* din da yake son ganawa da su ko meye dalili oho! 
Wani bodyguard ne shuairat ta masa magana tayi mishi bayanin komai nan yace mata yana xuwa
Bayan kankanin lokaci ya fito ya kira shuairat ya bata ixinin shiga , ta kira Mahmud bayan an duba I.dcard nasu sannan an duba jaka da komi nasu aka basu ixinin shiga.
Bodyguard din yana gaba suna biye dashi a baya wata Ya'r tafiya sukayi ko ina securities ne suke zarya kai tsarin ginin yayi , wata kofa Suka bi sannan ya sada su da wani ofishi kamar falo mai dankareren kyau wani matashi ne yana xaune ya dukufa se faman rubuce rubuce yake ga kuma securities nan birjik , sun sake shiga wani ofishi kafin Suka iso inda mr President yake ganawa da baki.
Dankareren daki ne kamar conference room ga kujeru masu kyau, kai a tsaya baiyana kyaun wajen ma bata lokaci ne, yana zaune a kan kujera hannunsa rike da jaridar daily trust yasha fararen manyan kaya masu uban kyau da tsada idanunsaa sanye da farin gilashi nan shuairat ta kafa shi da ido tana kallonsa guy din ya hadu😜( Allah yasa dai Meenat bata fole ba)
Hannu ya daga nan da nan bodyguards din duk sun fita se yaya bash kadai ya rage yana tsaye a gefen mr President ya wani sunne kai tamkar ma bai taba ganin shuairat ba.
Shuairat ta lura cewa idan zasu yini a wajen mr President baxai taba cewa ko uffan bah, sabanin Mahmud da yake rawar dari sabagen kwarjinin mr President😜👤akyar ta daure tace 
" sir! We ar here 4d interview"
Se da ya kai minti 3 sannan yace 
 " I knw"
[2/21, 2:29 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGAN KASA💞
*11*
By *Reefat yahya*

"Sir!
Ta furta a hnkli ya daga kansa ya kai dubansa gareta a yayinda Suka hada ido tayi saurin sunkuyar da kai tana kallon kasa .
Ya fara magana ckn harshen turanci 
" ke wace irin yarinya ce wacce bata San aikinta bah? Tun dazu na kiraku baki zo ba, dama haka kika saba yi a wajen aiki?

" sorry sir! Ta fada a hnkli tmkar Mara gaskiya.
 " irin kune Baku xuwa aiki idan anzo ba a biya salary ba kuma xaku fara korafi"
  " sorry mr President sir! 
Ya sake kallonta daga sama har kasa ya maida hnklinsa kan jarida.Mahmud ne ya daure yace 
" sory mr President idan Allah ya yarda hakan baxe sake faruwa xamu kiyaye"
Ya share 5mins sannan ya duba hadadden agogon dake makale a hannunsa yace
" well! Na Baku minti 10 "
Shuairat da Mahmud Suka kalli juna tare da xare ido cos sun San cewa 10minz yayi kadan Amma ya Suka iya.
Shuairat ta fara magana
" mr President sir! We will like to know abt u"
 " am Suleiman Mohammed d acting president of federal republic of Nigeria, am from Adamawa state.

Ya cigaba da duba jaridarsa shuairat tayi Jimm...toh shikenan abunda xai Iya gaya musu kenan? Anyways
Ta sake cewa 
" sir! Munji labarin cewa zaka fito Dan takarar shugabankasa nan....
  " no! Bani da burin haka kuma yanxu ma ba da son raayi na ne na zama acting president ba, bana bukatar mulki ko wani shugabanci"
Ya katse shuairat tun bata gama fadar abunda tayi niyan cewa ba.
" mr President shin xamu Iya jin ko yaranka nawa "
Ya daga kai yana kallonta sannan yace
" ina da yara biyu mace da namiji"

" wane lokaci ne  Wanda baxaka taba mantawa dashi ba a tsahon rayuwarka, na farincki ko bakin ciki

Tsitt dakin yayi babu Wanda yayi magana mr President ya ajiye jaridar hannunsa tare da mikewa yace 
" mintuna 10 da na Baku ya kare u can leave pls ina da abun yi"
Shuairat ta gama rubuce rubucenta sannan ta juya tace 
" mungode da lokacin da ka bamu , but mr President wane irin Abu yaranka suka fi so kuma....
" leave now!
Ya fada da karfi har shuairat ta tsorata nan ta tattara takardunta tana rawar jiki bayan Mahmud kuma ya dauko camerarsa sukayi waje yaya bash ya kulle kofa sannan ya dauko ruwan sanyi ya mikawa mr President Wanda take yaji wani ciwon kai na damunsa.
A waje Suka tsaya ta gama har hada takardun Mahmud ya kalleta yace
" kinyi kokari sis Amma kema meyasa zaki yi tambaya akan personal lyf dinsa"

" babu wani personal life kawai de baya son ya tuna wani Abu ne da yake ci masa tuwo a kwarya"
 " wane irin abune haka" murmushi tayi tace 
" mu tafi kawai kada ka damu xakaji komi"
Nan Suka wuce anata kallonsu suna jin dadin samun nasara yau de sun huta da balain mr Muawiya.
Mota Suka shiga direct office nasu yayi parking Suka jera har ciki, ba karamin dadi mr Muawiya yaji ba duk da cewa sun sanar dashi mr President be basu time sosai ba nan Suka fara tataunawa akan yanda xasuyi publishing don samun cigaba a kamfanin nasu shuairat kuwa tayi alkawarin kara musu wasu bayanai daga ckn tarihin rayuwar mr President Wanda ta sani game dashi.
Bayan sunyi sallama da kowa akan gobe zasu fara aikin nan Mahmud ya sauketa a gida sannan ya wuce nashi gidan.

Lov u mah fanz drop yah comments😘😘😘😘
*Dr Reefat Lov*
[2/21, 2:29 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*12*
By *Reefat yahya*


Da misalin karfe 10 na safe sun hallara a office dinsu nan Suka fara editing na interview da sukayi da mr President, shuairat ta kara basu wasu information da basu sani bah nan Suka tura xuwa website nasu da blogs da Facebook da sauran social media bayan sun buga shi a magazine nasu.
Ckn kankanin lokaci Suka fara samun likes da comments ko ta ina , farin ciki a gun mr Muawiya baa misalta shi ckn jin dadi ya musu ordering na snacks da drinks suna celebrating din samun nasara.

Mr President yana xaune a dakin hutawarsa shi kadai bayan ya sallami masu tsaronsa suna daga waje a bakin kofa , yana son kasancewa shi kadai yana bukatar Hutu ya kurawa hotor wata mata ido babu ko keftawa kalaman shuairat ne ke yawo a kwakwalwarsa 
" wane lokaci ne bazaka taba mantawa dashi a rayuwarka, na farin ciki ko bakin ciki"
Ya fashe da kuka tamkar karamin yaro ya rungumi hoton a kirjinsa bai San cewa yana son matar tasa ba sai da ya rasata
Yana tuna irin xaman da sukayi a farkon ranakun aurensu , baya nuna mata kulawa kawai biyayyane yasa ya amince ya aurota. Ya tuna kalamanta na cewa " yaya Suleiman kayi hakuri nasan an hadamu auren nan ba don son raayinka ba, amma duk da hakan bai hanaka xama dani bah baka taba wulakantani ba, shiyasa nake maka adua Allah ya baka wacce zaka so itama ta so ka Ku xauna har abada"
Wiwi ya cigaba da kuka tabbas yayi rashi saboda zainab macece mai hnkli da hakuri tana da kawaici sosai.
Ya tuna ranar da zata tafi lokacin da ya ta sameshi a falonsa zata masa sallama ta so suje airport tare Amma ya nuna mata yana da aiyuka a gabansa , ckn sanyin jiki ta fara magana
" Dadyn umaima ga amanar ya'ya na ka kular min dasu kada ka bari wani ya cutar dasu , kai kuma ina maka fatan alheri kuma Allah ya baka mace ta gari wacce xata rikeka tsakani da Allah"
"Haba zainab don zakiyi tafiya shine kike irin wadannan maganganun? Ya bata amsa ckn sakin fuska
" no ina nufin ka kula dasu kafin na dawo daga tafiyar da zanyi, batun aure kuma nasan ni baka sona shiyasa nake maka aduan Allah ya baka wacce zaka so"
Murmushi yayi sannan yace 
" kedai yau kuma kishin ne ya motsa" ya rakata a bakin mota sukayi sallama tana daga masa hannu har driver ya ja motar Suka wuce airport daga nan kawai sai labarin mutuwarta ya riske shi.kuka sosai ya cigaba da yi tabbas shuairat ta tabo inda yake masa ciwo mutuwar ta dawo masa sabuwa
Ya Dade baiyi kuka irin na ranar bah.
Kalaman shuairat ya sake tunawa a karo na biyu " mr President me yaranka Suka fi so a rayuwarsu?
Ya salam! Anya ya rike amanar da mamansu ta bar masa kuwa? 
Innalillahi wen last ya zauna dasu har yasan matsalarsu, baisan me suke ci ba bare me suke sha kwata-kwata bashi da lokacin zama dasu..lallai bai kyauta musu ba ga rashin uwa ga kuma rashin uba.
Ckn zafin nama ya tashi tsaye kofa ya nufa yana kai hannu aka bude masa duk da kansa na kallon kasa amma hakan be hana bash gane cewa wani Abu na damun uban gidan nasa amma ba halin tambaya.bangaren yaran ya nufa bodyguards Suka Mara masa baya ya iso dab bakin kofa ya daga musu hannu nan Suka tsaya shi kuma ya karasa ciki suna mamakin changin da mai gidan nasu yayi ckn kankanin lokaci.

Ya shigo tare da sallama babu kowa a falon direct dakin baccinsu ya wuce ya kwankwasa kofa
"Waye? Umaima ta fada ckn wani irin muryar da bazaka tantance ba
Yasa kai ya shigo tare da sallama tana xaune a saman gado sultan kuwa yana bacci a kan cinyarta , ya daga kai Suka hada ido idanunta sunyi ja kamar jini xai fita da alama dai itama taci kuka yaji tausayin yaran sosai.
A gefe ya xauna umaima ta kawar da fuskanta gefe ya rasa ta ina zai fara chan yace 
" baby am so...
" dad! Muna lafiya kalau as u can c little ma dakyar yayi bacci yanxu sabida yau birthday din sa ya tuna da mom"
Hawayene ya kara diga a fuskar ta bayan tana kirkiro murmushin karfin hali.
Ya ilahi! Har ya manta yau birthdayn dansa? Me yake damunsa ne ? Tabbas ya cutar dasu Amma ta ina xai fara
" umaima kuyi hakuri nasan...

" oh dad kar ka damu nasan aikine ya rikeka u almost fgt dat muna existing a duniya ma"
"Umaima pls...
"Dad is ok! Muna Iya Rayuwa ko babu kai, muna cin abinci ana bamu kudi muna shiga motar da muka ga dama me yafi wannan dadi a Rayuwa?
Sam ta hanashi magana a hnkli ya jawota jikinsa ya rungumeta nan ta fashe da kuka , shi ma kukan yake yi Amma Mara sauti.
[2/21, 2:29 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*13*
By *Reefat yahya*

Haka mr President ya kasance an rasa mai rarrashin wani tsakaninsu dakyar ya daure ya share mata hawaye yana bata hakuri akan rashin kulawar da yake musu nan little ya farka yana ganin uban nasa ya rungumesa gwanin tausayi daga nan yace su shirya zasu fita.ya koma bangarensa bayan ya shaidawa bodyguards nasa ayi arranging na garden xaayi birthday, umaima da sultan sunyi kyau sosai se wani nishadi suke mr President ma ya sha manyan kaya mota daya Suka shiga .shopping Suka je yaran sun xabi duk abunda suke so daga nan Suka koma gida sun sake sabon shiri don xuwa birthday. Mr President yayi inviting na vice nashi da wasu yan kalilan Suka xo akayi program sultan ya yanka cake akayi hotuna ga yan jarida daban daban , umaima tayi inviting frenz nata irinsu *Meenat* *Zuby* *khady Mj* *eesha* *teemah* da sauransu su Zuby an turo baki ana selfie😜 
Anci an sha sannan aka watse sultan ya samu gifts sosai.haka Suka kasance ckn farin ciki, ranar truout mr President yana tare da yaran nasa har abinci ma tare Suka ci se dare Suka rabu.
Mr President ya kwanta a gadonsa yana jin wani nishadi rabon da ya ji haka har ya manta, shuairat CE ta fado masa a rai tabbas ita CE sanadiyar daidaitawar su lallai baxe manta da ita ba haka ya kasance har bacci yayi awon gaba da shi.


Shuairat CE tare da yaya bash suna komawa gida bayan sun ajiye baba a airport ze tafi mubi Neman auren shukrah.
Shuairat CE ta katse shirun da cewa
" hmmm wa ya ga my yaya ya zama ango"

" xan buge bakinki wllhi kinsan baba baya nan

" yaya shukrah fa wayayyi CE nasan kana mata kallon Ya'r kauye"
    " mtswww....wayayyi a ina? Yarinya se kunya yaushe zata zauna ta bani lokaci na

" don't worry zata daina"
" mtsww dallah can karki bata min rai"
Wayarsa CE ta hau ruri ya daga yayi magana na minti 3 sannan yace" gani nan xuwa "
Ya juya yana kallon shuairat yace 

" baby kiyi hakuri mr President yana nema na urgent "

" toh yaya ka kaini gida mana first
" no! Kiyi hakuri ki shiga taxi ko kuma mu tafi tare"
Ta xumburaa baki tace 

" ni ka ajiyeni xan samu taxi a nan baxan je gidan ba"
Murmushi yayi sannan ya ajiye ta bayan ya samo mata taxi ta wuce gida shi kuma ya kama hanyar villa.

Bayan kankanin lokaci  ya iso gidan yayi parking yana Sauri ya wuce ofishin mr President yana xaune ya hada girar sama da ta kasa bash ya gabatar da gaisuwansa ko uffan mr President  bai CE masa ba se ya jefa masa wani magazine a gabansa.
Bash ya dau magazine yana dubawa tarihin rayuwar mr President ya gani ..dum! Yaji xuciyarsa ya tsinke dakyar ya daga kai yana jiran umarnin mr President
" ina bukatar ganin yarinyar da take aiki a JF Journals din nan "
 "Ok sir!

"Now! Bana son bata lokaci"
 " angama sir!
Gumi ne ya fara keto masa shuairat y? Sai da ya hanata rubuta labarin nan but bata jin magana.
Motarsa ya ja yana guduwa tmkr xe tashi sama ckn kankanin lokaci yayi parking a kofar gidansu , shuairat tana kwance dama yau bata je aiki bah ya shigo babu ko sallama ya fisgo hannunta " yaya lfy?
" zaki sani ne ba ruwana ba kince baki jin magana ba"
" me nayi?
" ban hanaki publishing din tarihin rayuwar mr President ba? Na gaya miki ki rubuta Iya abunda ya gaya muku da bakinsa gashi ynxu yazo yaga tarihinsa kaf an baza duniya"
Shuairat tayi shiru ta rasa me zata gaya masa
" sorry yaya"
" bani zani cewa sorry bah muje mr President yana son ganinki saura kice ni na gaya miki"

😳😳😳😆😆😆😂😂🤗🤗🤗🤗hmmmm ba ruwana nima saura tace *reefat* ce ta gaya min.kuttt wa zai je cell 😆😆
Lolx.....Ku biyoni Lov u all😘😘😘
[2/21, 2:29 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*14*
By *Reefat yahya*


A gaban mr President shuairat CE tare da yayanta se kuma wasu bodyguards su biyu dakin yayi shiru baka jin komi sai bugun xuciyoyin su, mr President ya daga hannu alamar a barsu nan da nan Suka fita ya rage daga shi dai bash da kuma shuairat mr President ya daga hannu ckn rashin fahimta bash yace 
" mr President sir! Kana bukatar wani Abu ne?

"Leave us! Ya fada kai tsaye nan bash ya juya ya fita yana mamaki saboda yasan ko ina suna tare da mr President ya akayi yau yafi son ya kadaice da shuairat ? Yana fita sauran bodyguards ma suna kallonsa ckn mamaki don sun San cewa akoda yaushe yana tare da shugabankasa a ko ina.
A hnkli mr President ya karewa shuairat kallo ba tare da ta sani bah don fuskarta na kallon kasa bata San me yake faruwa ba. Ya fara magana da cewa
" who ar u?
Se ynxu ta daga kanta a hnkli dakyar ta fara magana
" sunana Aisha bello"

 Sun share minti 10 babu Wanda ya sake cewa komai sannan mr President ya sake cewa
" ina kika samu tarihin rayuwata?

"Ehmm ..ummmm
"Talk to me" ya daka mata tsawa kuka ta fara a hnkli kanta na kallon kasa.ta share minti 5bata CE komai ba, a hnkli ya taka yaxo kusa da ita  suna fuskantar juna har ynxu kuka take.hayaniya Suka ji  daga waje da karfi aka banko kofa, yan jarida ne suna fada da bodyguards a yayinda yan jarida suke kokarin ganin mr President bodyguards kuwa suna hanasu shiga.
    Cak Suka tsaya ganin mr President da shuairat ckn yanayin da suke , bodyguards din kowa ya sunkuyar da kai yan jarida kuwa Suka fara daukan hotuna.ya fito da handkerchief a aljihunsa ya share mata hawaye ba tare da ya furta komai ba sannan ya tashi ya koma kujerarsa ya xauna.
Yaya bash yaje ya umarci shuairat ta tashi ya mayar da ita gida suna tafiya yan jarida sunyi shaa akanta suna tambayar ta me zata fada game da alamarin ko uffan bata CE musu ba dakyar bash ya bude mata hanya Suka fita Suka wuce mota ya ja Suka dau hanyar gida.

Mr President kuwa yana xaune yan jarida Suka sa shi a gaba suna jera masa tambayoyi ko daya bai amsa musu bah, securities Suka zo aka kori yan jaridan dakyar Suka tafi kowa na fadin albarkacin bakinsa.
   A mota ma bata daina kukan ba, bash ya juya yana kallonta yace " sisy me ya saki kuka? Wani Abu ya gaya miki?
Kai ta gyada masa alamar a'ah.
"Toh meyasa kike kuka?
"Ba komi"
"Gashi kina kuka still kina cemin ba komai"
" yaya nace maka ba komi koh"

"Ok fine! Amma kinsan kin jawo wa kanki magana koh?
"How?ta tambaya tana kallonsa
"Yes of course, kinsan halinku na reporters dole zasu zargi wani abu musamman idan kikayi laakari da yanayin da aka tarar daku a ciki n kuma yana share miki hawaye a gaban idon jamaa."
Shiru suka yi kowannensu da tunanin da yake yi.tabbas itama tayi mamakin ganin mr President yana share mata hawaye, kodai ya tuna da matarsa ne? 

Hmmmm....muje xuwa
Drop yah comments 
~dr reefat~ 4u lov u all
😘😘😘😘😘😘😘😘
[2/21, 2:29 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*15*
By *Reefat yahya*

Duk kofofin yada labarai sun hallara a gidan shugabankasa don jin Karin bayani game da labarin hotunan da aka kai musu na mr President tare da matashiyar budurwa kyakkyawa wacce basu San komi game da ita ba.mr president yana xaune a ofishinsa shi da bash ya rike kansa yana tunanin amsar da ze basu game da wannan alamarin, bash ne ya katse masa tunani da cewa 
" mr President me zaa gaya musu? Mutanen nan fa sun hanamu sakewa wai dole se sun gana da kai"
Shiru mr President yayi ya rasa me zai gaya masa can ya nitsa yace
" I rily don't know basheer "
" ok sir! Zanje in musu magana ina zuwa"
Ya fito ya tarar da yan jarida daban daban yace musu 
" kuyi hakuri mr President yana da aiyuka dayawa a gabansa Ku dawo gobe"
Nan ya juya ya tafi ya barsu suna ta guna gunai ya koma ofishin mr President.
Yana nan xaune inda ya barshi kansa na kallon kasa yayi nisa ckn tunani, wayarsa ya hau ruri bash ya daga yace
" mr President senator Sadik ne akan waya"
Ya karbi wayan ya amsa daga dayan bangare senator yace
" mr President meyake faruwa ina jin wasu irin labarun da ban gane Kansu ba"
Ya sunkuyar da kai tare da kulle idonsa yana jin wani iri ya rasa amsar da zai bayar kawai ya kashe wayar.bash ya juya yana kallonsa ya rasa me yake damun mr President ne?
" are u ok sir?
" am fine basheer tank u"
Daga nan ya mike yace
" zan koma ckn gida ina bukatar Hutu"
Bash ya bi bayansa Suka fita bodyguards Suka Mara masa baya ya koma ckn gida dakinsa ya shige a yayinda bodyguards din Suka tsaya a bakin kofa , ya kwanta a saman gadonsa ko takalma bai cire bah ya shiga duniyar tunani shin ina Aisha bello ( shuairat ) ta samo asalin tarihin rayuwarsa?
Meyasa ya share mata hawaye?
Amsoshin da ya kasa samu kenan. An turo kofar dakinsa da karfi babu ko sallama ya juya don ganin mai shigowar umaima ce fuskarta a murtuke ckn bacin rai ta nuna masa iPad nata ckn mamaki mr President yaga hotonsa da shuairat yana share mata hawaye...
" wacece ita?
Umaima ta tambaya tana bin baban nata da ido, ya rasa me zai gaya mata ?
[2/21, 2:37 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*16*
By *Reefat yahya*


Umaima ta fashe da wani irin kuka me ban tausayi ta fara magana tana cewa
" dad wato dama sabida yarinyar nan ne yasa ka daina kulamu?
" no...umaima pls ....
"Pls wat dad! Me zaka fada? Wannan shine amanar da mom ta bar maka kenan? Hw many years da rasuwarta har ka fara son wata?

"Pls umaima let me explain "
"Explain wat dad! Baka da abunda xaka gaya min....fuuu ta juya ta bar masa dakin ya rintse ido yana jin wani irin radadi..
Meyasa abubuwa suke faruwa dashi? Ya Allah
Ya xeyi yayi convincing din umaima? Yana ckn tunani aka kwankwasa kofa bash ne ya shigo ya sanar dashi cewa lallai akwai taron gaggawa ana nemansa ynxu ynxu .dole ya tashi ya watsa ruwa yayi sabon shiri sannan Suka fita don xuwa meeting.


Shuairat CE a office nasu ta zauna ta kurawa hoton da ta gani a internet ido, hoton mr President ya sa handkerchief yana goge mata fuska wani haushi da kunya ne ya lullubeta wato shiyasa yau tunda ta shigo ake binta da ido.ynxu shikenan duk duniya anga wannan hoton?
"No!!! "
Ta fada da karfi Sarah CE ta kura mata ido tace "lafiya shuairat?
"Ba komai "
"Ok oga na son ganin ki"
A hnxarce ta tashi ta shiga ofishin mr Muawiya yana zaune tare da Mahmud yana ganinta ya fara murmusawa , bayan ta xauna ya fara magana
" Aisha n Mahmud ina jin dadin aiki daku sosai, so yau ma ina son zan turaku meeting din da Senate Suka kira ina son samun labarin komai dangane da kiran gaggawa da aka wa mr President"
Dum..dum! Gaban shuairat ya fadi ita da mr President again?
"Shuairat dama kina da alaka da mr President ne? Muryar mr Muawiya ne ya katse mata tunani..
"Emm ...emm no! Ni ban sanshi bah"
" Aisha kada ki boyemin komai, hotunanku ake yadawa a koina kuma idan ban manta ba ke kika bamu takaitaccen tarihin rayuwarsa kuma idan nayi laakari da cewa jahar Ku daya dukkanku yan Adamawa ne sai naga kamar kuna da wata alaka mai karfi a tsakaninku"
Gumi ne ya fara keto mata tabbas ta daure kanta da labarin mr President da ta bayar 
"Tashi Ku tafi"mr Muawiya ya sake mata magana sannan ta tashi Suka fita ita da Mahmud.
A ckn mota ma babu Wanda yace uffan tsakaninsu shi Mahmud haushinta yake ji sabida ya fada sonta kwatsam se ya ga hoton ta da mr President ynxu ya xaiyi idan mr President ne yake nemanta?
Shuairat kuwa tana tunanin haduwarta da mr President da kuma yan jarida Allah ne kadai yasan tambayoyin da zasu jera mata.
      Shin xata amsa tambayoyin ne ko aa? Da ire iren tunanin har Suka kai inda ake meeting din, jamaa a cike makil a harabar wajen ga manya manyan yan jarida ga maaikatan gidajen rediyo da na telbijin da dai sauransu ai kuwa shuairat na fita aka fara nuna ta ana gulma wasu har daukanta hoto suke yi ta gane sarai ana nunata alamar gulmar ta akeyi don haka ckn dabara ta bar wajen ba tare da ta sanarda Mahmud bah.ckn building ta shiga tana dube dube tamkar me Neman wani Abu taxo dab wani lungu xata sa kanta carab aka rike hannunta juyawar da xatayi Suka hada ido da mr President😳😳😳
"Mr pre....
"Shhhhhh! Bai bari ta karasa ya toshe bakinta tare da Jan hannunta da karfi Suka koma da baya...



Hmmmmmmm..

Ku biyoni
~reefat~ Lov u my fans😘😘
[2/21, 2:37 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*17*
By *Reefat yahya*


Sun kurawa juna ido babu ko kiftawa bugun xuciyar shuairat se karuwa yake kasa kasa suka jiyo muryan yan jaridan na tattaunawa dangane da maganan mr President da shuairat daya daga cknsu yace
" dole ya fito ya fadawa duniya me hadinsa da yarinyar domin jamaa sun damemu da sakwanni"
Dayan yace

"Idan bai fito fili ya gaya mana bah tabbas xaa xargeshi  da zargi mafi muni kuma hakan xeyi affecting na gwamnatin sa ko ince kujerarsa"

Shuairat ta kurawa mr President ido ynxu ne ta gane dalilin boyeta da yayi da xata hadu da wadannan yan jarida kuma dole su jera mata tambayoyi.
Ynxu me mafita?
Bayan wani Dan lokaci yan jaridan su wuce nan mr President ya sake mata hannu ba tare da yace mata ko uffan bah ya juya da niyyar tafiya tayi saurin cewa

" mr President sir! Me xakayi dangane da wannnan matsalar ?

"Ba damuwar ki bane"
" damuwata CE mr President"
Ya juya a fusace ya hadata da bango sun kurawa juna ido ya fara magana a hnkli

"Who d hell u tink u are da zaki dinga shiga affairs dina?
"Am nobody! Ta bashi amsa kai tsaye

"Mind ur own business den, ki fita sabgata "
Wal wal hasken camera CE ya haska su gaba daya Suka juya wasu yan jarida ne su biyu suna daukansu hoto ....

"Oh no! Mr President ya furta tare da sake Jan hannun shuairat Suka shiga ta wata kofar da be San ina xasu je bah.duk inda ya leka akwai jamaa ya rasa ya xaiyi nan ya sake mata hannu yana maida numfashi yace

"Look Ayshah! Ki nemi hnyar da xaki bi ki fita ba tare da kin saurari kofofin yada labarai dinnan kinji? Xan nemeki gobe plss "
Ya fada ckn rashin kuxari , bash ne ya karaso yana faman haki da alama ya gaji dayawa

"Mr president Wia have u bin tun dazu ina Neman ...bai karasa ba saboda ganin shuairat da yayi a gefe don da farko bai ganta ba mamaki ne zalla a fuskarsa yana binta da wani irin kallon tuhuma.
    Mr President ne yayi gyaran murya ckn tsarguwa yace

"Ehmm ...bash pls help her n c her out"
Yana gama fadin haka ya juya ya kama hanyar xuwa dakin taron nasu.
Sun kai minti 5 babu Wanda yayi magana

"Wat is going on here little sis" yana mata kallon tuhuma

"Uhmmm...is just...
"Wait baby! Don't tell me dat abunda jamaa ke fada da gaske ne"
ta daga kanta Suka hada ido
" wat do u min?
"Wat Eva dai ,yau ne karo na biyu pls baby kada ya cika uku mind ur way he is not ur type"

"Me kake nufi yaya?
Bai CE mata komi ba ya fara tafiya ta juya tabi bayansa suna tfy suna labewa dakyar ta samu ta fito ta shiga ckn jamaa ba tare da an gane ta bah.Mahmud ta hango yana nan inda ta barshi 
"Mahmud!
"Allah na shuairat ina kika shiga inata nemanki"
Hannu ya mikawa bash Suka gaisa bash yace " ka kula da ita pls"

Daga nan bash ya koma ciki su kuwa Suka wuce mota.a kan hanyarsu ta komawa kowanne yayi shiru da tunani fal a zukatansu

"Shuairat soyayya kukeyi da mr President? Ya jefa mata tambayar da bata San amsar da xata bayar bah

"Ki ban amsa pls"
"Ba abunda ya hadamu Mahmud"
"Hmmm...gara ki fito fili ki bayyanawa jamaa akan batun soyayyarku if not darajarsa da taki zasu xube"

"Kamar yaya darajarmu xata xube?

"Of course! Yau ankira shi meeting baice komi bah dangane da maganar, ynxu mutane sun fara cewa idan har baiyi magana ba dat mins ke farkarsa CE"

"Waat? Farka? Innalillahi wato abinda yaya bash yake nufi kenan da yace mata kada ta bari ya cika uku?

"Shuairat gaskiya xan gaya miki maganan ya girma fiye da ynda kike sammani domin ance zaa Iya sauke mr President akan kujerarsa idan har an tabbatar da zargin da ake yi da gaske ne, don haka gara ki fito ki dayawa duniya gaskiyar alamarin"

"Me kake nufi da gaskiyar alamari Mahmud? Kasan ni ba mazinaciya bace"

"Nasani but jamaan gari fah? Kiyi tunani akai shuairat"
Ya sauketa a gida yayi tafiyarsa ckn bacin rai, shuairat kuwa tunanin maganganun Mahmud take tana Neman mafita.

Hmmmmmm......akwai ~work~
Muje xuwa
Taku a kullum *Reefat*😘😘😘
[2/21, 2:37 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*18*
By *Reefat yahya*


Mr President ya koma gida a gajiye yake likis ga ciwon kai sabida hayaniyar da sukayi da jamaa a meeting nasu ya cire babbar rigarsa ya xauna a kan gado ya buga wani uban tagumi.
    Umaima CE ta shigo tare da sallama ckn sanyin jiki ta xauna kusa da mahaifin nata ta sunkuyar da kai hawaye ne ya fara sauka
"Dad don Allah ka rabu da yarinyar nan kana sauke girma da darjarka too much"
Ta nuna masa sababbin hotunan da aka tura yau , kunya ne ya kama shi don ganin yanayin hotunan sun kurawa juna ido shi da shuairat umaima CE ta katse masa tunani

"Dad pls promise me"
"Don't worry my baby babu abunda yake tsakaninmu kinji? Ki kwantar da hankalinki hakan bazata sake faruwa bah"

"Promise?
"Yes promise" wani murmushn dadi tayi daga nan Suka fara hira sannan ta koma bangarenta ckn wani irin farin ciki.
A hanya Suka hadu da bash yana waya bai lura da ita ba sauran kadan suyi karo ta ja gefe ta bashi hanya ya juya kenan Suka hada ido ya kashe wayar ya sunkuyar da kai alamar girmamawa
Murmushi ta sakar masa tace
"Dama ina son magana da kai"
Mamaki ne a fuskarsa sabida yasanta da shegen girman kai ta gane hakan tace
"Kana mamaki koh? Don't wory wasu yan tMbayoyi ne zan maka"
Nan Suka zauna bayan ta bashi ixinin xama a harabar gidan ne akan wasu kujeru kyawawa.

"Na dade ina ganinka tare da mahaifina kuma nasan kai kana daya daga ckn mutanen da Suka fi kusa da mahaifina, don haka nake son sanin wani Abu dangane dashi da wannan yarinyar"

"Ranki ya dade ni bansan komi game da maganar ba , kawai nasan babu soyayya a tsakaninsu kuma babu wata alaka mai karfi a tsakaninsu"

"Toh kana nufin mahaifina yana bin matan banxa kenan?
"Subhanallah! Ya daga idonsa Suka fada ckn nata 

"Yes! Idan babu soyayya ko wata alaka a tsakaninsu toh me hadinsu?
Ran bash ya baci sosai yace
"Ita wannan yarinyar ba karuwa bace"

"Who knows" umaima ta fada ckn kwanciyar hnkli idanun bash sun canza xuwa ja yace

"Kina xargin mahaifinki da aikata xina?

"Ya zanyi? Duk laifinsa ne shi ya jawowa kansa ana ta zaginsa a gari"nan ta fashe da kuka me ban tausayi tabbas abun akwai daure kai ynxu haka ake zargin Ya'r uwarsa? Kai baxai yiwu bah dole ya dau mataki.
  A hnkli ya fara rarrashin umaima tmkar yace ta kara, bash dama yana da tausayi nan ya fara bata baki bayan ya cire handkerchief ya mika mata ta karba a hnkli tana share hawayen se kuma ta tuna hoton dad nata yana sharewa wata hawaye nan ta sake fashewa da sabon kuka.
       Bash yayi shiru yana kallonta ya rasa me zai gaya mata
"Sorry pls is ok ki daina kuka ni na tsani ganin hawayen mace pls"
ta share hawayrn a hnkli ta daga kanta tana kallonsa shi ita yake kallo
"Tnk u"
"U ar welcom"
Ya fada yana murmushi sunyi shiru can ta tashi tace 
"Zan koma ciki but pls ina bukatar num wayarka"
Babu gardama ya rubuta mata tana murmushi ta daga masa hannu sannan ta koma ckn gida shi kuwa yana mamakin chanjin halin nata.

Bash ya koma gida ya sami labarin cewa baba na nemansa a chan mubi saboda sa ranan aurensa don haka ya nemi ixini daga wajen aikinsa.
Shuairat tana kwance a falo tayi nisa ckn tunani wayarta ya hau ruri shukrah CE

"Kawata ya akayi"
"Uhmm...gani nan dai
"Baba yaxo Neman aure fah...

"Auren wa? Shuairat ta fada tana dariya
"Munafuka dama nasan kin San xe xo amma baki taba gaya min bah"

"Ya ake ciki "
"Oho! Nima bansani bah
"Gulma koh! Ana so ana kaiwa kasuwa kinsan yaya na mai tsada ne yarinya 

"Kya ji dashi munafuka
"Ehh din, nasan ana son yaya na dai ana wani nokewa xamu gani ai"
Haka Suka cigaba da hira har na tsawon wani lokaci.
 Bash yana kwance a falonsa ya kurawa wayarsa ido lambar shukrah CE kullum yana son kiranta Amma ya kasa, ga kwanakin se matsowa yake amma har yau be taba kiranta bah yau dai yayi ta maza ya danna kira yayi ringing har ya kusan katsewa sannan ta daga ckn wani irin murya mai dadin sauraro tayi sallama ya amsa se kuma yayi shiru

"Hello! Wa ke magana don Allah

"Yayanki ne
"Eyya..wanne daga cki
"Yaya bash
Nan taji wani irin kunya ta rufe ido tmkar yana ganinta dakyar tace

" ina yini yaya
"Lfy ya kike ya gida"
"Lfy alhamdulillh ya su mama"
    "Lfynsu lau"
        Nan Suka sake yin shiru chan ya fara magana 
       " kiyi hkri ban taba kiranki ba wllhi aikine ya rikeni"

      "Ba matsala Allah ya taimaka"
  " ameen nagode" nan ma shiru Suka yi bayan minti5 tace
"Hello!
" ina jinki"
" kayi shiru
"Ehh..kema ai shirun kika yi Kiban labari toh
 " ba komi fah
"Ke baki da surutu ba kamar kawarki bah
Haka Suka Dan taba hira sannan sukayi sallama bayan ya sanar da ita gobe xai kama hanya da yardan ubangiji.

😘😘😘
...............muje xuwa
[2/21, 2:37 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*19*
By *Reefat yahya*


Bayan bash ya nemi ixini a ofishin shugabankasa aka bashi kwana3 nan yabi jirgin 12 ya sauka a *yola international airport* daga nan ya shiga motar xuwa mubi.
      Karfe 4:00pm ya sauka daga ckn adaidaita a kofar gidansu daga shi sai akwati, baba yana xaune yana lazimi bash ya shigo tare da sallama bayan sun gaisa yayi salla sannan ya watsa ruwa nan ya shaidawa baba zai je gun shukrah.

 A kofar gidan ya tura a kirata yaron ya dawo ance ya shiga cki, a wani daki aka saukeshi babu komi a ciki sai tabarma da kuma wata ya'r darmuma. 
Kannenta ne Suka shigo da kwanikan abinci bayan sun gaisa Suka bashi waje bayan kankanin lokaci ta shigo tare da sallama wani uban qamshin turare ne ya buga hancinsa habawa ya daga kai Suka hada ido tayi kyau sosai ckn atamfar Sheraton dama tana da Dan jiki dinkin yayi mata kyau sosai.
Bash ya kasa cire idanunsa a kanta ita kuma kunyarsa take ji

" ina yini" ta fada ckn siririyar murya murmushi yayi ya fara kwaikwayon muryarta 
gaba daya Suka fashe da dariya
" na sameku lfy
"Lfy alhamdulillh ya hanya
"Lfy lau
" ka sha ruwa se ka ci abinci nasan ka gaji sosai

Bata jira amsar sa ba ta bude kulolin abincin  rice n stew ne se kuma danwake yasha hadi har da kwai da cabbage se kuma farfesun kayan ciki..
 
"Wanne zaa fara xubawa
"Ni danwake kawai xan ci
"Haba ka isa? 
"Y not" ya fada yana murmushi

" Allah baka isa ba sai ka cinye duka

" haba shukrah kema dai kinsan baxan Iya cinye wannan ba" 

Baya CE komi ba ta diba masa danwaken dama shuairat ta gaya mata yaya bash na balain son danwake, ta ajiye a gabansa sannan ta xuba zobo a ckn Kofi ta tura masa a gefe ya daga kai Suka kalli juna yace

"Sai ki matso muci tare ai"
" a koshe nake"
" no! Ki xo mu ci"
" a'ah naci nawa tun dazu"

Murmushi kawai yYi ya hau ci a hnkli yake kominsa gwanin burgewa shukrah tana satar kallonsa guy din ya hadu😜
Carab ya kamata tana satar kallo ya murmusa yace

" ya dai"
" ba komi"
" ki fadi gaskiya"
Ta rufe fuska ckn jin kunya tace 

"Zan koma ckn gida idan ka gama ka kirani a waya"

" no! Kiyi xamanki ni bana jin kunya ai kece me jin kunyana"

Tana dariya ta kawar da fuska a gefe.
Bayan ya gama cin danwaken yana santi yace

" wannan girkin inna koh? Nasan naki bare kai wannan dadi bah"

"Naji na yarda"ya shanye zobon ma yaji ya koshi yayi hamdala ya juya suna fusksntar juna sosai nan Suka fara magana ta fahimtar juna ya nemi jin raayinta game da auren nasu ita tace duk yadda sukayi ya mata daidai bata da zabi .

Haka Suka kasance har magrib sannan ya mata sallama ya tashi ya tafi kamar karsu rabu sabida dan xaman da sukayi sun fara sabawa da juna.
[2/21, 2:37 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*20*
By *Reefat yahya*


Dakin ya cika makil da jamaa daga ministoci senators members da dai sauransu mr Joshua yana xaune wato vice president kenan ga bodyguards a gefensa ta kowane bangare.
     Idan ka duba wani bangare kuma yan jarida ne birjik ga maaikatan yada labarai dai daban daban ana jiran fitowar mr President , ya fito kuwa ckn manyan kaya yayi kyau sosai fuskarsa ba yabo ba fallasa yana taku ckn kasaita yana wani ji da kai tamkar sarki 😜😜( lols me banbancin)
Ya nemi kujera ya xauna nan wani mutum ya fara magana yana murmushi daga ganinsa yana jin dadin yanayin da yaga mr President a ciki....

"Mr president yau ne karo na karshe da xamu maka wannan tambayar...me hadinka da wannan yarinyar?
Shiru ba amsa ya maimaita maganar sau3 ko uffan mr President bai tanka masa bah
Nan aka fara hayaniya kowa na fadin albarkacin bakinsa..

" muna ganinka mutumin arxiki shiyasa muka baka wannan matsayin Amma ka kunyatar damu ...
Wani dattijo ne ya fadi haka yana rike da speaker.mr president ya runtse ido yana jin wani irin radadi a ckn xuciyarsa dakyar yake furta sunayen Allah.

"Silence" wata siririyar murya ta fada da karfi sanye take ckn wani gown me kyawun gaske black da adon pink tayi rolling da pink veil ta sa lipstick pink Dan kadan tayi kyau sosai.

Wal wal hasken camera kawai kake gani anata daukanta hotuna gaba daya hnklan jamaa ya koma kanta ta karbi speaker ta fara cewa

" ni xan Baku amsar tambayoyinku... *ni da shugabankasa* mun kasance muna son junanmu tun da dadewa, shi ba mutumin banxa bane kamar yadda kuke zargi shi jarumi ne mai mutunci yana da Amana da rikon gaskiya"

Wancan mutumin ya juya yace
" kina nufin soyayya kuke yi da mr President?

" ehh ...soyayya muke"

" toh meyasa yaki ya fada da bakinsa?
" kunyace kasan Fulani ai"

"Kin tabbata"
"Na tabbata hakan ne" ta gyada kai suna kallon juna ita da mutumin shikam beji dadin xuwanta ba yafi so a CE an cire mr President akan mulkinsa.

Yan jarida Suka rubuta duk abubuwan da yake faruwa a yayinda masu gidan talabijin Suka fara haska nasu a wannan lokacin duk duniya ana kallon abunda yake faruwa.
Mr President ya sunkuyar da kai shikam baiso shuairat ta kawo kanta bah toh meyasa ta ceci rayuwarsa daga zargi da ake masa? Duk da cewa yasan abun ya shafe ta tunda tare aka gansu Amma baiyi tunanin cewa xata hada karya haka don.....
" mr President ko xaka bamu Karin bayani kan abunda ta fada?
Shi bai ma San yan jarida sunxo kusa dashi bah

" babu abunda xan fada a kai" ya basu amsa kai tsaye shuairat ta karasa kusa dashi ta xauna tana kirkiro murmushin dole nan kuwa aka fara daukansu hotuna mr President kam mamakin alamarin yake wai yarinya kamar an turo ta.
An gama meeting lfy bayan an wanke mr President daga xargin da ake masa, suna fita yace a nemo masa shuairat a ckn mota Suka xauna su biyu kawai bayan an rufe musu kofar ya juya yana kallonta yace
 
"Meyasa kike shiga min rayuwa ? Na gaya miki ki fita sabga ta"

" am sorry mr President but idan ban fito na kashe maganar ba xaka Iya rasa kujerar ...

" shut upp! N so wat idan na rasa shi? Kinsan kuskuren da kika tafka? Kinsan matsalar da kika jefa kanki a ciki? Kinsan balain da kika jefani ciki? Da kinsani da baki aikata hakan bah...Ayshah kinyi kuskure "

" mr President.....
"Shut up! Ban gama bah" 
Ya tare nimfashinta yana huci kamar wani xaki

" Aysha meyasa kike shiga rayuwata? Meyasa xaki jawomin matsala a Rayuwa? Meyasa ? Meyasa?

Shuairat ta fashe da kuka tana hawaye tsakaninta da Allah mr President ya gitgizata yana nuna wajen window da Dan yatsa yace
" kinsan matsalar da xafi fuskanta ? Me xaki gayawa wadancan nan gaba? Shin har yaushe xaki cigaba da musu karyar? Shin me xan gayawa iyayena? Tell me!
          Ta cigaba da kukanta me ban tausayi yayi shiru kansa ya daga ya kura mata ido dakyar yace
" is ok stop crying"  
Bata sauraresa ba ta cigaba da kukanta ya xuba mata ido kawai se kuma ya sake cewa

"Don Allah ki bar kukan ya isa pls"
Ta sunkuyar da kai kasa 
"Let's talk pls "wayarsa CE ta fara ringing umaimace ba sai angaya masa bah ya daga kara a kunne

" I hate u dad" daga jin muryarta yasan tana kuka ta kashe wayar yayi shiru jikinsa ya mutu gaba daya duniyar ta masa xafi.
Shuairat CE ta lura da halin da yake ciki bayan ta share fuskarta a hnkli tace

"Mr president ar u ok'
"Am fine I just need to go home"

"Umaima koh?
Ckn mamaki yake kallonta ya akayi ta gane cewa umaima CE? n a ina tasan umaima?
Murmushi shuairat tayi don taga yNa mamaki tace

"Ka lallabata kasan karamace "
Daga nan ta bude mota xata fita 

"Ayshah!
Ya kira sunan da wani irin salo ta dakata don jin me zai fada

"I'll c yhu gobe we have alot to talk about"
Daga nan ta fita ba tare tayi magana bah.


*Reefat*CE.....Lov u all😘😘
[2/21, 2:37 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*21*
By *Reefat yahya*

Umaima CE zaune a falonta kuka takeyi tmkar ranta xe fita mr President ya shigo ckn hanzari ya karasa kusa da ita ya kai hannu xe taba ta tayi saurin komawa da baya

"Dad bana son ganinka pls leave"

"Baby am so sorry let me explain pls"

"Explain wat just go"
Babu irin lallarshin duniyan nan da mr President beyi ba Amma firr taki sauraronsa haka ya hakura ya koma bangarensa da damuwa fal a ckn ransa.
    Umaima ta aika a kira mata bash an shaida mata baya gari haka ta yini jugum xuciyarta na tafarfasa tana jin kishin wannan yarinyar da ko sunanta bata rike bah.

***************

Shukrah CE tare da bash suna hira ckn kwanciyar hnkli ya tmbayeta irin kayan da take so a saka mata ckn akwatin lefe , an sanya ranan auren nasu nan da wata1  ya kai mata tsarabar turamen zani 2 da lace da kuma gown se sabuwar wayar Samsung galaxy da turaruka da mai da sabulu masu kyau da sadan gaske.

"Nagode sosai yaya Allah ya kara budi"

"Ameen matata"
Ta sunkuyar da kai ckn jin kunya
"Aw kunyata kike ji? 
"Nifa bana jin kunyarka"

"Toh ki daga ido ki kalleni"
Murmushi tayi ta sunkuyar da kai hmmm masoya.
Haka Suka kasance suna hirarsu irinta masoya daga karshe Suka rabu ya mata sallama domin gobe  xe koma Abj, kamar baxasu rabu bah shukrah har hawaye take 😳😳ahh abun ba sauki an kamu) dakyar ya lallabata ta daina kuka sannan ya koma gida da shirin tafiya.

Tana kwance a falonsu idanunta a lumshe tana tuna kalaman mr President mama CE ta shigo ta xauna a gefenta

"Ya'r baba tashi ki xauna magana zamuyi"

"Ina jinki mama"
"Menene gaskiyan alamarin dangane da magananki da shugabankasa "

"Mama wa ya gaya miki?

"Ina xaune gaban TV na gani da idona kin fito kinyi magana"

"Mama...nifa ba komi tsakaninmu kawai dai..."
Sai kuma tayi shiru ta kasa magana.

"Kawai me? Shuairat kibi a hnkli mutumin nan ba saan aurenki bane mu talakawa masu rufin asiri Muna...

"Pls mama nace miki ba komi tsakaninmu"
Daga nan ta tashi ta koma dakinta ta kwanta ta rasa me ke mata dadi a duniyar ko wane hali mr President yake cki oho! Ko ya zasu kaya da umaima oho! Haka ta kasance har bacci yayi gaba da ita.

A bangaren mr President ma hakan ta kasance ya kwanta yana ta tunane -tunane  wayarsa CE ta hau ruri dum ...xuciyarsa ta buga don ganin kiran mahaifinsa

"Dady nah"
"Boy ya kake "
"Alhamdulillh ya gida ya momsi "

"Gata kusa dani lfyanmu kalau, na bugo ne don tabbatar da news da gani"

"Ohh dady is just...
"Son am happy zanzo next week sai ka nuna min gidan iyayenta idan Ya'r gidan mutunci CE sai a fara maganar aurenku koh"

"Damm...dammm! Kirjinsa ta buga innalillahi ya zaiyi da wannan kwamacalan

"Boy kana ji Nah, am so proud of u, kayi tunani mai kyau ai xamanka haka nan ba dadi "

"Dady....
"Don't worry boy na fahimceka momsi tana gaisheka sai anjima takkia of urslf" garam ya kashe wayar
Mr President ya rintse ido yana maimaita innalillahi lallai rayuwarsa tana ckn matsala Allah ne kadai xai fiddashi.ya rufe ido nan ya hango shuairat yana siffanta ta, doguwa CE siririya bata da hasken fata tana da dogon hanci da karamin baki tana da dogon gashi baki wuluk don ko ta daura dankwali rabin gashin nata a waje yake.tana da kyau dai-dai gorgodo toh amma ya zaayi ya aure ta? Babba da shi ? Yasan zai Iya haifanta don koda ta girmi umaima ma baxe wuce da shekara ko 2 xuwa 3.
To Amma wacece ita? A ina ta samu tarihin rayuwarsa? Shin auren nasu zai yiwu? Ya umaima xata yi idan taji xeyi aure? Kodai ya fito ya karyata labarin?
Shin idan yayi haka ya kyauta? Tambayoyin da ya fara jero wa kansa kenan ya kasa samun amsarsu.

Hmmmmmmmmm muje xuwa *Reefat* CE xata amsa muku wadannan tambayoyin..
Drop ur comments Lov u all😘😘😘

Vote: waye jarumi/jarumarka a ckn wannan littafin umaima" mr President" shuairat" basheer" shukrah"
Wane page yafi burgeki/burgeka....sai naji daga gareku
[2/21, 2:38 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*22*
By *Reefat yahya*


Bash ya shigo falon umaima tare da sallama dawowarsa kenan daga Adamawa ya samu sakon nemansa da take tana kwance tayi nisa ckn tunani ya sake maimaita sallama a karo na biyu ta tashi xaune tana ganin bash ta fashe da kuka.
    Ckn rudewa bash ya karasa kusa da ita 
"Lfy miss umaima?
Ta cigaba da kukan bata saurareshi bah ya rude sosai ya xauna dab da ita yana bata baki dakyar ta tsagaita kukan ta fara magana

"Kai kadai ne ka ragemin a duk fadin garin nan Kaine zan Iya fuskanta in gaya maka duk wata matsalata bani da kowa a ynxu se kai"

"Meke faruwa ? Ina dad naki"
"I hate him bana.

"Shhhh....hannu yasa ya toshe mata baki yana girgiza kai 

"Don't ever say dat pls, mahaifinki duk laifin da ya miki he don't deserve dis"
   "But bana sonmu ni da Kani Nah baya kulamu yafi son budurwarsa"

"No! Yana sonku kece baki fahimcesa bah kuma wancan yarinyar ba abunda yake tsakaninsu she is a reporter"

"Hmmm basheer kenan! Amma de baka kalli news ba koh? Yarinyar da ta fito da bakinta tace sun Dade suna soyayya"

"Waat? No! No! Umaima I tink...shit! Ya buga kujera da karfi take launin idanunsa sun canza
"Basheer ya na ganka wani iri? Any problem?

"Ba komai kaina ke min ciwo"
"Sorry bari na dauko maka magani"

"No! Am ok" xuciyarsa na tafarfasa shin meyasa shuairat xata yi haka?

"Bash ina kaje an cemin kayi tafiya?

"Uhmm..Adamawa naje wllhi"
"Really ! Dama kai Dan jahar su dad ne, no wonder yake sonka"Murmushi yayi yace

"Haka ne!
"Ehh...dad yana sonka sosai"

"Abunda nake so dake shine ki kwantar da hnklinki nasan dad naki yana sonku sosai batun yafi son wata duk be taso bah , nasan akwai wani boyayyen alamari dangane da yarinyar nan Amma xan bincika da kaina xan gano koma menene"

"Ok bash nagode" nan ta kwantar da kanta a kafadarsa tana hawaye wani irin shock da be taba ji bah haka nan yaji wani irin Yarr..a hnkli yasa hannu yana share mata hawayen tana yin ajiyar xuciya 
Mr President da yayi niyyar shigowa gun umaima ya juya a hnkli ya koma bangarensa yana jinjina hnkli irin na bash yaji ya kara son bash har ckn ransa yaron ya burgeshi.

A hnkli umaima ta fara bacci ba tare da ta sani bah bash ya kura mata ido sosai yana kallon kyakyawar fuskarta tabbas loneliness yana addabar ta bata da Wanda xatayi hira dashi don bai taba ganinta da kawaye bah kullum ita kadai take rayuwarta sai kuma kaninta sultan, mahaifinsu is always busy bayi da lokacinsu se masu aiki ne ke kula dasu yaji tausayinta sosai yayi alkawarin zame mata Dan uwa Wanda zai rage mata kadaici.

Ta share awa2 tana bacci bash kuwa yana xaune ya gaji Amma baya son ya tasheta , a hnkli ta bude ido tayi mamakin ganin bash sai kuma ta kalli agogo karfe 4 da minti5 ckn mamaki ta juya

"Basheer u mean tun dazu kana xaune haka?
Murmushi ya sakar mata yace

"I promise to b wit u always"

"Nagode but hw can u" mamakine a fuskarta tana kallonsa nan ya tashi tsaye 

"Am going now, duk tym da kike bukatar gani na am always available "

Bai jira amsarta ba ya fice yana murmushi 
Umaima kam se mmki take yi ynxu haka ya xauna har na tsawon 2hrs ? Allah sarki nan taji wani irin sonsa ya mamaye ta tana murmushi tana tuna fuskarsa dama ta Dade tana Neman Wanda xe kasance tare da ita sai gashi Allah ya kawo mata bash a lokacin da tafi bukatarsa.
Hmmmm.....akwai aiki!!

Bash be tsaya ko ina ba sai gidansu dakin shuairat ya wuce tunda bata falo yayi saa mama ma bata falon maybe tana dakin babansu don tare Suka dawo.
   Tana kwance tana game da wayarta ya shigo tare da sallama

"Hey ango ansha kamshi"

"Uban wa ya turaki ki fito gaban jamaa kice mr President yana nemanki ?

"Yaya me....
"Talk me bana son bata lokaci" ya daka mata tsawa bata taba ganin yayan nata ckn bacin rai haka bah
Ai kuwa ta fashe da kuka

"C ba kuka zakiyi ba koma menene I don't kia just answer me"

"Yaya nifa ba soyayya muke yi bah

"Meyasa zakije ki gayawa duniya hakan?

"Yaya....
"Answer me! Kina da hnkli kuwa? Kinsan kuskurenda kika aikata?

Kuka sosai shuairat take nan ya juya ya bar dakin baya son ganin wani ya sata kuka bare shi da kansa amma ya xama dole ya nuna mata kuskurenta.ya fita ya barta ta cigaba da kukanta babu me bata hakuri .

Ku biyoni ~reefat~
Lov yah...😘😘😘😘
[2/21, 2:38 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*23*
By *Reefat yahya*

D next day shuairat ta gaishe da yaynta yayi bnxa da ita haka ta tashi ta koma dakinta ta kwanta tayi kuka mai isarta sannan ta fara shirin xuwa wajen aiki.
  A can office nasu ma hakan akayi Mahmud yana ganinta ya fara wayar karya ita kuwa ta gane sarai Amma ta share ta xauna ta cigaba da harkokinta.

A can office din mr President kuwa ya kasa tabuka komai kawai so yake ya xauna da shuairat ta amsa masa tambayoyin da yake bukatan ji.bash ya kira ya umarcesa da ya nemo masa shuairat , ya sunkuyar da kai yana tunani kodai da gaske soyayya suke yi? Nan ya tashi ya tafi JF Reporters gun mr Muawiya ya nufa ya sanar dashi sakon mr President nan aka bashi ixinin tafiya da ita, tana xaune tana danne-danne a gaban computer sarai taga wucewarsa Amma bata damu bah yaxo ya tsaya a kanta ya wani bata rai yace

"D president wants to c u"
Ko motsi batayi ba bare ya sa ran xata kulashi daman yasan xaayi haka yasanta idan tayi fushi.

"Miss bello mr President wants an audience"
Ya sake maimaitawa a yayinda yan office din sun juna suna mamakin yan uwan junan da suke Abu tamkar basu taba haduwa bah ganin kallon yayi yawa ne yasa shuairat ta tashi ta rataya Jakarta tare da yiwa su Sarah sallama suna hada ido da Mahmud ya kawar da kansa gefe daga nan ta fice tayi hanyar mota.

A hanya ma babu Wanda yayiwa wani magana a gidan baya ta xauna shi kuwa yana tuki.
          A kofar building din yayi parking bayan ta fito da turare ta kara fesawa tayi hakan ne don batawa yayanta rai ta dau farar hoda ta shafa da kuma lipstick daga nan ta bude kofar ta fito bata jira yayn nata ba tayi aikuwa securities Suka fara gulma ana nunata ana cewa ga budurwar mr President ta xoh.ko a jikinta haka ta karasa duk inda ta wuce ana bata girma direct office da yake ganawa da baki ta wuce.ta tura kofar a bude ta shigo tare da sallama yana xaune yau suit ya saka yayi kyau sosai bazaka CE ya kai shekaru 40 da doriya a duniya bah.ya daga kansa yana kallonta sosai tayi kyau ga kuma qamshin turarenta mai sanyaya xuciya ta nemi kujera ta xauna nan ya tashi daga inda yake ya dawo kusa da ita suna fuskantar juna

"D first lady" ya fada ckn xolaya dum...shuairat taji wani Abu ya tokare mata kirji me hakan yake nufi?ta daga kai Suka hada ido ya sakar mata wani murmushin da ya kashe mata jiki

"My first lady ba gaisuwa ne?
Nan ma shiru kake ji.
"Ok nasan kunya na kike ji pls ki gayamin a ina kika samu tarihin rayuwata?

"Namanta"
Ya mata wani irin kallo ta sunkuyar da kanta saboda baxata jure kallon ba.

"Ok naji! Now ki gaya min meyasa kika CeCe ni ta hnyar cewa mun Dade muna soyayya"

"Nayi hakan ne don bana son ka rasa kujerar ka"
"Idan na rasa mulki na ta ina hakan xai shafeki"

"Ko kadan bazai shafeni bah nayi hakan nan don bana son ka rasa aikinka saboda nice sila"

Yayi shiru yana nazarin maganganunta
"Kai kuma meyasa ka sharemin hawaye wancan lokacin?
Da Sauri ya daga kai yana mamakin tambayar tata

"Kada kiyi tunanin share miki hawayen da nayi yana nufin wai ina sonki ne no! Tausayinki naji shiyasa na share miki"
  Wani shuumin murmushi tayi tace

"Kana nufin kowace mace zaka Iya share mata hawaye kenan?
Ya jefa mata harara dakyar yace

"Ehhh haka ne"
Shiru sukayi ya rasa wace irin yarinya bace Sam bata jin tsoronsa shi da ko manyan mutane suna jin tsoron kallon idonsa su gaya masa magana Amma ita ko bata damu bah. 
Ta sake kallonsa Suka hada ido ta kawar da fuska tana murmushi, bash ne ya shigo ya shaidawa mr President yayi baki suna son ganinsa shuairat ta yi karfin hali tace

"Baka gaya musu muna tare ba ne?
Ba bash ba har mr President yayi mamakin kalaman nata yayi irin ta maza yace

"Sorry bash ka gaya musu ina tare da.... Yayi shiru yana kallonta ta sakar masa murmushi wani irin Yarr..yaji daga tsakiyar kansa yace

"Ina tare da first lady su Dan bani lokaci kadan"
"Ok sir!
Bash ya fada yana kallon shuairat tana wani murmushn mugunta bash ya kai bakin kofa shuairat ta CE 

"Uhmmm ...wait! Ka saukeni a gida, mr President don't wory next tym xamu karasa maganar"
Cak! Bash ya tsaya wani irin haushinta yake ji lallai yarinyar nan ta na wuce gona da iri Amma xaiyi maganinta nan shuairat ta tashi ta rataya Jakarta tayi ficewarta bash yabi bayanta mr President kam ya tsaya galala yana kallon ikon Allah daga nan ya wuce dakin da bakin suke jiransa.


.....muje xuwa😘😘😘😘😀akwai drama kenan!
*reefat*
[2/21, 2:38 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*24*
By *Reefat yahya*

Gidan baya ta sake shiga ta xauna ya shigo ya tada motar suna tafiya yana kallonta ta ckn mirror ta juyar da kai gefe se wani shan qamshi take

"Wai angaya miki ni driver enki ne"
Ko uffan bata CE masa bah

"Ina miki magana hajiya"
Nan ma shiru tayi yaja wani wawan birki ya tsaya a gefen titi

"Se ki fita ki nemi taxi ya kaiki gida don ni ba drivernki bane"

"Eyya ...da tun farko ka gayamin ai xan sanar da mr President kaga kuwa akwai mototci da dama sai wacce na xaba , Amma ynxu din ma is not late let mi just call him ya turo min wata motar "
Ta cire waya tana faman danne danne a dole wai tana Neman layin mr President
Yaja motar Suka cigaba da tafiya yana harararta wani guntun murmushi ne ya bayyana a fuskarta.

"Look baby nifa yayanki ne dole kiyi respecting dina "
Bata CE masa komi bah tana danna wayarta da alama chatting take tana faman murmusawa , yana kallonta yana jin haushin abunda take masa wato sunyi nisa da soyayya haka har xata Iya xartar da hukunci ba tare da mr President yayi gardama bah toh a ina Suka hadu? Yaushe Suka fara soyayya? Yana mamakin wannan alamarin har Suka kai gida babu wani kalman da ya fito daga bakin shuairat.

*********  A can bangaren mr President kuwa baki yayi daga kasar waje suna tattaunawa dangane da harkokin siyasa har sun gama xasu masauki sannan daya daga cknsu ya juya yana tayasa murnar samun santaleliyar budurwa a matsayin matar da xai aura.

"Yaushe ne zamu sha biki mr President"
Mutumin ya fada ckn harshen turanci ga kuma yan news a xagaye dasu

"Nan ba da dadewa bah da yardar Allah"
Ya bada amsa kai tsaye se kuma yana mamakin ya akayi maganar ta fito daga bakinsa.

************
Haka Rayuwa ta kasance shuairat da yayanta sun share mako 2 basa magana duk abunda yake faruwa iyayensu basu sani bah don basu ga alamar hakan bah, shirye shiryen bikin bash da shukrah akeyi babu kama hannun yaro ynxu ya rage sati2 ayi bikin. Ya gama hada lefe akwati set daya da kaya kala 45 a ciki , lefe kam yayi kyau sai San barka mama da baba sai shirin bikin suke shuairat kam ko a jikinta kawai ta dinka anko nasu na kawayen amarya kuma ita ta zabi kalar kujerun da xaa xuba a falon amarya, suma sun canza nasu kujerun an sake wa gidan sabon fenti yayi kyau sosai ynxu kam se shirin xuwa mubi don gabatar da bikin.
        Tana kwance a daki tana karanta novel din "behind our Lov" na miemie bee😘
Novel din ya burgeta sosai hnklinta ya tafi ga karatun dama a watsap ne aka tura a grp din *gidan gyara*😊teemah ashaka CE ta tura musu...wayarta ya fara ringing bakuwar lamba CE ta ja tsaki ckn jin haushin katse ta aka yi

"Hello! Ta amsa kamar bata so

"First lady ina son ganinki ynxu"
Yana fadin haka ya katse wayar toh waye shi? Oh mr President kenan? Tasan dai shi kadai yake kiranta da wannan sunan toh a ina ya samu num ta ? Hmmm shine wai ina son ganinki ynxu wato ma har wani gadara yake mata...mtsswww se shegen girman kai 😏
Bata motsa ba ta cigaba da karatunta ckn kwanciyar hnkli kofar dakinta aka bude bash ne ya shigo tare da sallama tayi banxa dashi tmkar bata San ya shigo bah

"Baby magana xamuyi but muje mr President na son ganinki first "

"Bani da lokacin magana da kowa"

"Look am serious about it pls" ya fada yana kallonta ta daga kai Suka hada ido tayi saurin dauke kanta nan kuwa ta soma kuka a hnkli, ya taka ya xo kusa da ita ya jawota jikinsa ya fara magana a hnkli

"Am sorry pls nasan nayi laifi baby kiyi hakuri kin ji koh my baby"
Ta cigaba da kukan da take Mara sauti

"Sorry yaya bai kyauta miki bah but am sorry now plss....
Ta tura baki ckn shagwaba tace 

"Ba kaine bah wai kana fushi dani baka tsaya ka saurari me xan gaya maka bah

"Naji is ok now ynxu nagane ba laifinki bane sorry koh

"Uhmm"
"Toh tashi ki shirya idan mun dawo sai muyi maganar koh"
Haka dai ya lallabata sannan ya koma falo yana jiran fitowarta.

Wani dankareren lace ta saka green da touches din wyt n golden ta saka yan kunne cika wuya golden masu uban kyau ta fesa turare masha Allah tayi kyau sosai.
      A gaban madubi ta tsaya tana kallon kanta ba karya ta hadu Iya haduwa..ynxu kwalliyan nan tayi shi ne don mr President?
No! ta bawa kanta amsa kawai tayishi ne don kar a Reina ta kuma a matsayinta na budurwar mr President she have to look unique always.light make up tayi a gurguje sannan ta fito falo yayanta ya sakan mata murmushi yace 

"Wow! My sisy is looking cute"
"Tnx" ta fada daga nan Suka dau hanya ...


😘😘😘tnx 4ur support my fans Lov u all
*Reefat ce*
[2/21, 2:38 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*25*
By *Reefat yahya*


Mr President yana xaune a filin hutawarsa yayi shiru daga gani yayi nisa ckn  tunani ta karasa tare da sallama baima San ta iso bah xama tayi a gefensa qamshin turarenta ne yasa ya juya don ganin ko wayene ido ya kura mata babu ko keftawa
Wani kunya ne ya lullubeta ta sunkuyar da kai dakyar ya saita kansa sannan yayi gyaran murya ya fara magana

" first lady ko xan Iya sanin dalilin da yasa kikayi wannan kwalliyar kodai kin kamu da son tsohon neh😉"
Ya fada yana kallonta ta daga idonta Suka fada ckn nasa lallai mutumin nan

"Ko kadan Aisha bello bazata auri tsoho ba kuma tana da saurayi mai sabon jini me xatayi da tsoho ?
 Yayi murmushn yake yace 

" wa ya sani Abu a hudu kuma waya San inda rana xata fado"

" mr President kenan ai kowa yasan cewa a yaMma rana take faduwa "

" shikenan...ynxu na nemeki ne saboda kisan halin da ake ciki
Kin rabani da ya'ta ynxu haka tana fushi dani kuma kin hadani da iyayena kinsa mahaifina yace lallai xai xo nema min aurenki "

😳😳😳ta xare ido ckn tsananin firgita shima kallonta yake 

"Yes! First lady, kina tsammanin cewa maganan xe wuce haka kawai ne? Dama saida na gaya miki kin tafka kuskure gashi ynxu outcome din kenan, kuma duk duniya an baza kunne ana jiran ranar aurena da ke"

Me shuairat xatayi in ba kuka ba😆😆😆 mr President yayi shiru yana kallonta tun tanayi a hnkli har ta fara da karfi wani security ne ya leka don jin muryar ta yana son ganin ko lfy daga ganin mr President a gefe yayi saurin komawa bakin aikinsa.
Mr President ya tashi ya koma kusa da ita har suna jin hushin juna.

Ya kai hannu xe share mata kwallan da ya bata mata fuska tayi saurin kawar da fuskan gefe yana murmushi yace

"Toh ai laifinki ne my first lady, kefa kika fito kika gayawa duniya cewa mun Dade muna soyayya koh?
Harara ta galla masa tace

"Kai de kace kaga Ya'r budurwa kana so shine ka gayawa dad naka amma ka daina labewa da wani magana daban"
Dariya sosai ta basa yace

"So? Toh ai ni bansan wannan Kalmar bah kuma ban taba yinsa ba a rayuwata , xancen aure kuwa tunda na rasa matata ban taba tunanin sako auro wata bah don haka ki kwantar da hnklinki ni bansan wani Abu wai shi so bah"
Tana kallonsa ckn mamaki sannan tace

"Y not ka gayawa dad naka gaskian lamarin"

"Ban taba masa gardama kuma baxan fara a kanki bah amma idan xaki Iya fuskantarsa ki gaya masa da zan fi kowa jin dadin hakan"

"Me xan gaya masa?
"Oho!duk abunda kike so"
Sunyi shiru kowanne da tunanin da yake can ya daga kai yace

"Kije kiyi tunani a kai ko ki fito ki fadi gaskiya ko kuma ki yarda da auren kaddara da xai fado kanki nan ba da jimawa bah"

Yana kawo nan a xancensa ya tashi ya tsaya ya mata wani irin kallon da ta kasa gane maanar sannan ya koma ckn gida ya barta tana xaune ta shiga duniyar tunani...
Me abin yi????????

Hmmmm muje xuwa dai,
Lov u all😘😘😘😘
[2/21, 2:38 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*26*
By *Reefat yahya*


 Bash ne ya katse mata tunani 
"Sis ya naganki haka?
Kuka ta fashe masa ya jawota jikinsa 
"C'mon let's go home  ki share hawayenki pls ga securities suna ganinmu tashi mu tafi "
Nan ya Suka tashi bayan ya share mata hawaye tana gaba yana biye da ita a baya Suka fada mota ta tadata Suka hau hanya, bayan sunyi tafiya mai nisa yayi parking a gefen titi 

"Now tell me me yasa kike kuka?
Nan ta kwace labarin komi tun daga farkon haduwarta da mr President har xuwa hirarsu na karshe ta shaida masa yayi shiru yana naxarin maganganun can ya nitsa yace

"Sisy kinyi Abu mai kyau da kika kare mutuncinki da na mr President but ynxu problem din shine mahaifinsa..dama iyayensa sun jima suna mishi maganan aure baya sauraransu kinga ynxu dole hnklinsu ya kwanta n 2b frank I tink mr President likes u a lot cos tunda nake dashi ban taba ganin ya xauna yana hira da wani har da dariya ba sai ke, idan kinga yana magana da wani dai toh bai wuce maganar siyasa ba se kuma yaransa su kadai yake sakewa fuska"

"And so wat yaya! Kana nufin na auri tsoho kenan? 

"Baby ina son ki gane cewa aure mukaddari ne daga ubangiji kuma matar mutum kabarinsa n mr President mtumin kirki ne bashi da matsala ta kowane bangare, kuma idan kika amince da auren nan tmkar jihadi ne don kin rufawa musulmi Dan uwanki asiri.idan har baki auresa ba xaa fara jita jita kuma xai xama wata magana mai girma"

"But yaya...
"Baby kiyi adua Allah ya xaba miki mafi alheri kawai daz final kuka da duk wani bacin rai ba naki bane"

Daga nan ya tada mota Suka koma gida.
Bash yana kwance a dakinsa yana lissafin yadda aurensa xe kasance wayarsa CE ta fara ringing umaima ya gani akan screen yana murmushi ya daga
" hey best friend ina ka shiga ne?
"Friend ina nan aikine ya min yawa"

"Kullum aiki baka hutawa ne?
Murmushi yayi yace

"Hutu ai se manya irinku"

"Hmmm.xolaya koh"

"No! Daz d fact"

"Naji toh yaushe xaka xo mu fita "

"Yaushe kike so?
"Ko ynxu ma am ready"

"Kiyi hakuri xuwa gobe kinji my dear"
Ta lumshe ido tana jin wani farin ciki tace

"Shikenan ina jira Allah ya kaimu"

"Ameen bye"
Tare Suka ajiye waya umaima ta rungumi tabbas ta fada tarkon son bash Allah ne kadai yasan adadin son da take masa😳😳hmmmm...umaima kin shiga tarko amma kash!!! Ance rashin sani yafi dare duhu bata San cewa saura kiris👌🁢ash ya angwance bah



***********
Mr President kuwa yana xaune a falonsa yana tunanin hnyar da xaibi ya sasanta da umaima yrinyar Sam taki bashi fuska bash ne ya fado masa a rai tabbas shi kadai zai Iya shawo kan matsalan.
se kuma shuairat ta fado masa a rai yana murmushi shi kadai yarinyar akwai shagwaba kam maybe ita kadai iyayenta Suka Haifa da alama dai Ya'r gata CE ko su waye iyayen nata oho!

Se ynxu ya tuna baima San gidan nasu bah, idan dady yaxo yace su je tare fah? 
Lallai dole ya nemo gidansu Amma wannan duk aikin bash ne..ya zaiyi da umaima bayan ya auri shuairat ? Ya zaman nasu xe kasance? 
Shuairat xata amince da auren ne ko aa?
Idan tace aa'a me zai gayawa dadynsa ? Me mutane xasu dauke shi? 



Ku biyoni don jin amsar tambayoyin😘😘😘😘
~reefat~
[2/21, 2:38 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*27*
By *Reefat yahya*


Mr President yana xaune a ofishinsa bayan sun gama ganawa da vice dinsa akwai xasuyi tafiya xuwa China don kula da harkar kasuwanci tsakanin najeriya da china .
     Bash ne ya shigo masa da wasu files ya ajiye xe fita
" a moment pls"
Bash ya juya ya dawo a tsaya a gabansa mr President ya nuna masa kujera ya xauna wato alamarin da ya bashi mamaki kenan saboda tunda suke mr President bai taba masa hakan bah.

"Basheer wani taimako nake so ka min"

"Ina jinka mr President"
"Wato lura kusancinka da yata yayi karfi har nake ganin cewa xata Iya aikata duk abunda ka umarceta, basheer ina so ka bawa yata hakuri akan maganata da Aysha bello pls"

"Don't worry mr President xan mata magana insha Allah "

"Nagode" bash ya tashi har ya kai bakin kofa mr President yace

"N I want to know about Aysha bello"

"Ok sir! Ya bashi amsa sannan yasa kai fice.

A falonsu ya sameta da masu aiki suna mata gyaran farce tana waya, ya shigo tare da sallama 
Fuskarta ne ya fadada da murmushi nan kuwa ta kashe wayar 

"Aboki se yau"
"Yes my kawa" ya maida mata martani sannan ya samu kujera da yake kallon nata ya xauna nan ta sallami masu aikin bayan ta umarcesu da su kawo kayan motsa baki.

"Ya'r gatan dad ya kike"

"Lfy ya aiki"
"Alhamdulillh ya hutawa"

"Ya kadaici dai koh"
Sun Dan taba hira bash yace 

"Kawa me yake damun dad naki ne kwanan nan duka naga yana ramewa"

"Oho! Maybe ya bata da budurwarsa"

"No! It can't b ki dai bincika ki gano matsalar he is ur dad after all"
Tayi shiru tana naxarin maganganun nasa kenan dad dinsu ya rame saboda tana fushi da shi? Dama haka ya damu da ita? Lallai bata kyauta masa bah, kamar yadda take fama da kadaici shima hakan yake fama amma meyasa tayi haka?
Hawayene Suka gangaro a fuskarta nan ta sunkuyar da kai kasa ta fara magana

"Laifina ne na daina kulashi ya bani hakuri har ya gaji ban saurareshi bah"
Nan kuwa ta fara kuka tamkar ranta xe fita

"Me kika masa umaima?

"Akan maganar wannan yarinyar "

"Haba umaima a ina kika taba jin anyi fushi da iyaye? Shin baki ganin irin biyayyar da dad dinku yake nunawa iyayensa ne? Meyasa baxakiyi koyi da halayensa ba?
Ta cigaba da kukanta ba kakkautawa bash kuma ya cigaba da magana

"Tabbas kinyi kuskure Amma is not late kije gun mahaifinki ki nemi gafararsa idan har baki son fadawa ga halaka ". Nan ya kwace labarin komi dangane da alakar shuairat da mr President ya gaya mata cki kuwa har batun aurensu jikinta ya mutu sosai ynxu ne ta gane cewa dad bashi da laifi ko kadan.
 Bash ya mata nasiha me ratsa jiki sannan ya tashi ya tafi.

Mr President yana xaune ya buga uban tagumi a hnkli aka tura kofar umaima CE ta shigo tamkar barauniya.sum sum ta karasa kusa dashi

"Dad....
Se kuma hawaye sun taru a idanunta .
Hannu ya bude mata ta fada jikinsa tana kuka yana rarrashinta dakyar ta daina kuka tace

"Dad am sorry ka yafe min sharrin shaidan ne"

"Is ok baby, idan har kin fahimceni dai shikenan "

"Dad I understand ba laifinka bane kuma itama taimakonka tayi "

"Am happy dat u know  ynxu me kuke bukata cos gobe ko jibi xan tafi China"

"Bana bukatar komi dad Allah ya tsare ka ya dawo da kai lfy"

"Ameen my baby"
Haka Suka kasance suna hira ckn farin ciki da jin dadi ya kalli fuskarta yace

"Baby kodai an samo min suruki ne"

"Laa...dad babu fah"

"Are u sure? Wat of basheer?

"Dad! Ta fada tana dariya bash da yake bakin kofa yayi murmushi sannan ya juya ya bar wajen.



😘😘😘😘to u my fans
[2/21, 2:38 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*28*
By *Reefat yahya*


Karfe 5dai dai bash yayi parking a kofar gidansu na mubi yaran anguwan ne Suka tayasu shigar da kaya ckn gida.
   Mama da baba Suka fito ana musu maraba da xuwa tuni shuairat kuwa ta kama hanyar gidan mutuniyar tata ckn xumudi ta shigo tare da sallama.
Inna tana tankade gari shukrah kuwa tana shara aikuwa sun kankame juna ckn jin dadi bayan sun gaisa da inna dakin shukrah Suka shige tare da sauke labule 
( ni kuma nace baxaa barni a baya bah ..lolx)
" kai bestie kin ga hasken da kikayi kuwa? Se shining kawai kike yi"

  "Ya'r rainin wayo na kaiki ne, ke amarya ce fah ansha gyaran jiki ana ta shinning"
" ya gida ya hanya ya su mama"
  "Lfynsu lau ya shirye2"
Shukrah ta harareta ckn tsigar wasa tace
   "Wane shirye shirye"
"Oh! Wa yaga su bestie amarya"
   "Kya ji dashi ya'r nema"
   "Oho dai! Ana so ana kaiwa kasuwa , yawwa baki ban labarin haduwarku da yaya bah kince masa I love u ko ya?

" munafuka ai shuairat kina fama wallhi"
  "Lolx muna fama dai"
Haka Suka kasance suna hirar yaushe gamo shukrah ta kawo mata dambun xogale ta ci tayi hamdala har magarib sannan ta tashi ta kama hNyar gida shukrah tana mata rakiya shuairat ta juya ta kalleta tana murmushi tace

"Anti shukrah ki koma se munxo xance to nyt" shukrah ta kai mata duka suna dariya Suka rabu.

Hakan ko akayi bayan sallar isha bash ya shirya ckn kananan kaya se qamshin turare ke tashi a jikinsa yayi sallama ya tafi shuairat ta yi masa tsiya har ta gaji yana dariya ya tafi.
     Bayan kwana biyu aka kai lefe jamaa na ta yabawa nan aka fara shirye2n biki ba kama hannun yaro su shuairat kirjin biki itace kan gaba a kowane bangare. babbar kawa kuma kanwar ango, sun shirya xasuyi kauyawa day da walima se kuma kamu night"


********** 
A can birnin tarayya kuwa mr President ya tafi China don gudanar da harkokinsa
  Umaima kuwa gidan ya mata fadi gashi ta nemi layin bash baya shiga kuma ta tambaya ance mata yayi tafiya sultan ne abokin hirarta se kuma watsap da Facebook, gashi makarantar su ana hutu .
  Tana kwance a falonsu yau taji shaawar shiga watsap dinta ta bude kenan mssgs Suka fara shigowa anyi adding dinta a wani grp din *Gidan gyara* mata ne xalla a GRP din, batasan wacece admin din bah kawai ta ynke shawarar yin magana a grp din ta rubuta "salam" ta tura bayan minti2 Meenat da esha Suka amsa mata😊 "wslm"
"Pls wacece tayi adding dina a wannan grp din? Bayan wani Dan lokaci mssg ya shigo from *Reefat* tace "nice nayi add din ki" Mmn Ummul ta tura novel din *tana tare da ni"* kamar da wasa umaima ta fara karanta novel din se kuma taji grp din ya burge tah anata hira a grp din so lively haka, tun tana sharewa har ta fara contributing ta Dan saba da yan grp din har magariba tayi sannan kowacce ta tashi don yin sallah.

    Bayan umaima ta idar da sallah ta sake daukan phn din ta shiga grp taga anyi posting din wasu pre-wedin pix kala2 batayi download bah ta cigaba da karanta novel din *yar Riko* da aka tura, chan an sake tura wasu pix din se a kasan aka rubuta 

"Matan gidan nan u r invited auren yaya nah  gobe kamu night"
Cmnts aka fara aikowa 
"Wow couples din sunyi kyau"
Su Rabi Oga da su momi Ummi da zaheeda da sauransu duk sunce xasu je auren.
Haka nan umaima taji tana shaawar bude hotunAn tayi download daya yana buduwa
😳😳😳 dam....dam....xuciyarta ta buga guess wat?
Hoton shukrah CE da basheer sunyi kyau sosai nan take wani jiri ya fara diban umaima
😳toh fah....hmmmm"
Wani xaxxabi ne ya rufeta haka ta kwanta akan sallaya idanunta na fitar da wasu xaxxafan hawaye

 😥😥eyya umaima nah...

Lols Ku biyoni

*Reefat*ce😘😘😘😘😘
[2/21, 2:38 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*29*
By *Reefat yahya*


Karfe 7 katon multipurpose hall din Adamawa state university mubi, ta cika makil da jamaa ga yan mata samari manyan mata da dai sauransu can na hango amarya tare da kawayenta dai Kelli suke ansha kyau.
Decoration din hall din ma abin kallo ne anyi decorating da purple n silver se fulawas masu kyau abun dai se Wanda ya gani.
       Kawayen amarya na sanye da purple head da material ash colour n silver wyl amarya kuwa ta saka purple material da silver n ash colour head tie sunyi kyau sosai an fara program sannN ango ya shigo da tawagarsa ckn fararen kaya masu kyau sai shinning suke. 
Anfara gabatar da taro su shuairat anyi rawa har an gaJi ga abinci da drinks kala kala anci ansha an xuba kudi kamar ba gobe su Rabi Oga tun daga Jada aka tashi aka je auren😜 ga su nan dai matan gidan gyara birjik anyi ta kashe pix xaa canza dp.nima dakyar nasamu nayi pix 2 da amarya da kuma shuairat...
Bayan angama taro aka watse kowa ya kama hanyar gida.


A can Abj kuwa umaima aka kwantar a asibiti in banda kuka ba abunda take a waya aka hadata da mr President tmbayar duniyan nan ya mata Amma Sam tace xaxxabi ne ke damunta...( Kutt...Ashe dama she is in love wit yaya bash eyya poor umaima😥😥....lolx😜)
Bayan an bata magunguna aka sallameta Suka koma gida tare da masu kula da lfyarta, yan uwan mamanta se kira sukeyi suna mata sannu haka nan iyayen mr President ma sun kirata sun gaishe ta.

****†

D next day da yamma su shuairat Suka hada walima na mata xalla anyi nasiha sosai akan hakkin aure shukrah ko har kuka se da tayi shuairat na tsokanRta
BayN wani lokaci Suka raba Qur'an da handfan da kuma memo daga nan aka raba abinci sannan akayi adua aka watse.

Ran jumaa aka daura auren shukrah Abubakar da Basheer Bello maiha daurin auren ya samu jamaa sosai.da dare aka kai amarya gidan mijinta.
D next day akayi fansar amarya da ango sannan da dare aka sallami kawaye shikenan jamaa kowa ya watse.
         
    Shuairat CE tare da aminiyar tata tana bata yan shawarwari ynda xata xauna da mijin nata bash ne ya shigo tare da sallama shuairat CE ta amsa ya kalleta yace

"Ke me kike jira baki tafi gida bah"

   "Ho...yaya korata xakayi yau"

"Ehh mana ba dole bah
"Hmmm...lallai gashi nikuma se nayi 1week kafin....

"1me? Tabdi ba dai a nan gidan bah, idan kinji haushi kema ki shirya a daura muku ke da wancan tsohon"

"Yaya....tsoho fa kace! Se na gaya masa kuwa"
Yana dariya yace
"Yi hakri ur Excellency kada a dakatar da salary nah na 1month"
Haka dai Suka cigaba da tadinsu ckn xolayar juna shukrah de bata sa musu baki bah daga karshe shuairat ta musu sallama Yayan nata ya ajiyeta a gida shukrah kuwa se hawaye take 😏ni Reefat nace ki gama kukan munafurcin ki bada kai bori ya hau


Ku biyoni ku sha labari😜

*Reefat* CE .....love u alll😘😘😘😘😘
Hop kuna manage da hausar tawa😜
[2/21, 2:38 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*30*
By *Reefat yahya*


Bayan sati daya da auren shukrah da bash Suka dugunxuma xuwa Abj shukrah tayi kukan rabuwa da iyaye da yan uwanta sosai.
Baba da mama flight Suka bi sannan bash shukrah da shuairat kuwa Suka bi hanyar mota.

Da yamma Suka iso garin shukrah ma tana kalle-kalle har Suka shiga gidan nasu bangaren yaya bash ta wuce sannan shuairat kuwa ta shige bangarensu.bayan sunyi wanka sun huta shukrah ta share bangaren tas ko'ina se Kelli yake ta kunna turaren wuta nan take qamshin ya gauraye gidan bash kuwa yana sauke baccin gajiya , shuairat CE ta shigo musu da abinci tare Suka ci nasu bayan ta ajiyewa bash nasa.

Bayan sallar magrib gaba daya Suka hallara a falonsu mama ana hira har da shukrah ta sake sosai a gidan bata daukesu a matsayin surukai ba, wayar bash ne ya fara ringing "umaima ! Ya gani a rubuce kwata2 ya manta da ita se kuma yaga be kyauta ba saboda be taba kiranta bah kuma bai gaya mata xaiyi aure bah.
Yayi picking tare da sallama ckn sanyin muryarta ta amsa tare da cewa 
"Ina son ganinka yanxu" 
Tana gama fadin haka ta kashe wayar.ya kurawa wayar ido sannan ya tashi yace
"Baba ana nema na a gidan mr President "
A dawo lfy Suka CE masa daga nan ya fice



Tana xaune a falonta ita kadai sultan yayi bacci ta shigar dashi daki tana xaune ta buga uban tagumi ya shigo tare da sallama sanye yake ckn kananan kaya yana ta qamshi se shinning yake, suna hada ido ta fashe da kuka ai kuwa ya rikice ya xo kusa da ita ya xauna ya marairaice yace
"Umaima am sorry nasan ban kyauta bah na tafi ba tare da sallama ba"
Ta daga idanunta suna kallon juna se kuma ta sake sunkuyar da kai ta cigaba da kukanta har ckn ransa yana jin kukan Amma ya xaiyi? Ya lallabata amma taki dainawa.

"Umaima I said soryy naa kiyi hkri pls bana son jin kukan nan naki don Allah"
"Bash! Farkon haduwarmu da kai u promised dat xaka kula dani xaka xame min kadangar da xan jingina a kai ashe ba haka bane?
Bash har xaka iya aure baxaka sanar dani ba?
Damm...gabansa ya fadi, toh ya akayi tasan yayi aure?

"Kana mamakin ya akayi na sami labarin aurenka koh? Ba abin mamaki bane amma gskiya banji dadin hakan bah

"Am sorry umaima"

"Sorry 4wat? Sorry dat kayi aure ko sorry dat ka tafi baka sanar dani bah? O sory dat ka kasa cika alkawarin da ka dauka?

Carab! Suka hada ido, hawaye na diga tace 

"Y basheer? U knw dat I kia a lot meyasa zaka min haka? But....

Kuka ne yaci karfinta ta kasa karasar da maganan da take a hnkli ya jawota jikinsa😳🙊.....
Gam ta kamkameshi tana kuka me ban tausayi.
     Dakyar ya rarrasheta ta sagaita kukan 

"Kiyi hakuri umaima auren ya xomin unexpected ne iyaye na Suka hadani da yarinyar wllhi ba wai...
Se kuma yayi shiru toh wai meyasa yake kokarin kare kansa ne?.

Shiru sukayi na Dan wani lokaci a hnkli ya daga kansa ga mamakinsa umaima har ta fara bacci haka Suka xauna har sunkai 1hr a xaune sannan ya xame jikinsa a hnkli ya kwantar da ita a saman kujerar 3str sannan ya fita ya shige motarsa ya kama hanyar gida.
    A hanya ma yana tuki yana tuna kalaman umaima da kuma halin da ta shiga toh meya bata mata rai? Kuma yaga alamar damuwa a tattare da ita ko meyake damunta ne
Oho! Nima nace oho!


😘😘😘lov u alll
[2/21, 2:38 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*31*
By *Reefat yahya*


Shukrah ta gama shirin kwanciyarta ta hau gado ta kwanta bash ne ya shigo dakin tare da sallama ta amsa cki-cki a dole fushi take ya karasa kan gadon inda take kwance yana murmushi yace
" my wife fushi kike dani"

Ko uffan bata CE masa ta kirkiro wani guntun murmushi

"Am sorry kiyi hakuri "
"Uhmm..ba komai"

"Sure"
"Uhmm"

"Toh ki danyi murmushi mana"
Hakan kuwa ta sake masa murmushi yana dariya yace

"Daz my wife, tashi mu ci abinci toh"

"Na koshi"
"Pls mana " ya marairece hmmm bash akwai iya salo..lolx
Nan ta tashi ta xauna nama ne da exotic mai sanyi ya CE shi xai shiga wanka ta fara ci daga nan ya wuce dakinsa ya watsa ruwa tare da sa kayan baccinsa ya dawo ya sameta a inda ya barta.
Yana lallabata tana ci tana yauki😆😆  kamar bata so har Suka gama Suka kora da juice nasu se kuma Suka dawo falo ya kunna musu wani series film *walking death* suna kallo.

Shuairat kuwa 11pmta tashi daga bacci dama tun suna hira ita ta shige daki ta kwanta . falo ta nufa don yunwa take ji sai kuwa tayi saa foil pepa ta gani tana budewa taga nama a ciki nan ta hau ci se da ya isheta ta sha ruwa sannan ta koma dakinta xama tayi a carpet saboda bata jin bacci ta rasa me zatayi sai ta kunna data dinta watsap ta shiga mssgs Suka fara shigowa new number ta gani an tura mata hi"
Ta shiga ta ga num na online
"Helo!
Babu bata lokaci aka mata rply da 
"Hw u"
"Fine alhamdulillh n u"

"Same"
"Eyya waye ne"
"New friend dinki ne princess maimah daga grp din gidan gyara "

"Aw Ayya am Ayshah"

"Nice meeting u"
"U too "
"Will like 2b ur kawa idan baxaki damu bah"

"Aww..really ! Naji dadi sosai u r welcm"

"Tnx ya gida yasu mum n ya yayanki da amaryarsa "

"Lfynsu lau..amma nayi fushi bakizo auren bruh bah"

"Eyya sory wllhi bana Adamawa ne daz y"

"Ok wane gari kike"

"Ina kd"
"Wow..daz gud"

"Ki ban labari toh" shuairat tayi murmushi tana jin dadin chat nasu da alama dai princess bata da girman kai sai tayi rply

"Me ya hana princess bacci ko dai tunanin prince ne😜

"😃😃laaahh...wa ya gaya miki? Nayi bacci fah ynxu na farka shiyasa"

"Aww...just like me wllhi"

"Baxaki ban labari ba koh"

"Toh princess wane irin labari kike so"

"Ur love story"

"Lolx...wllhi ban taba yin soyayya bah "

"Ar u serious Ayshah? Nima haka wllhi"

"Meyasa toh"

"Babu fah kawai ban taba bah kuma Wanda nake so din yayi aure"

"Allah sarki😥 naki tausayin ki sorry"

"😊😊tnx"
"Amma ya akayi kika bari yayi aure ko kun bata ne?

"😊is a long story"

"Ok hard luck"

"Tnx" haka Suka cigaba da hira har 1 sannan Suka rabu kowacce ta kwanta .

Asuba ta gari first lady👍🏼👍🏼


Love u all😘😘😘
[2/21, 2:38 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*32*
By *Reefat yahya*


Da safe shukrah ta hada lafiyayyen brkfast ta ajiyewa maigidan nata ta chaba ado ckn atamfa ya'r holland tayi kyau sosai bangaren su mama ta je ta gaishesu suna falo sabida baba kullum se ya kalli news na safe ta ajiye musu brkfast sannan ta shige dakin shuairat bacci takeyi ckn kwanciyar hnkli shukrah ta kai mata duka nan kuwa ta bude ido tare da Jan tsaki ta koma baccinta wani dukan ta sake kai mata a baya aikuwa taja bargo ta gyara kwanciya

"Ke baxakije aiki bane"
Firgigit ta tashi xaune kwata2 ta manta yau xata koma bakin aikinta ban gida ta fada tayi wanka bayan ta fito shukrah bata nan ta shirya kanta ckn material tYi kyau sosai ta fito falo bayan sun gaisa da iyayen nata ta wuce bangaren shukrah.

 Suna kari da mijinta ckn so da kulawa ta shigo tare da sallama ta gaida su sannan ta nemi wajen xama abinci ta deba iya cin ta tana ci suna hira bayN sun gama tare Suka fita da Yayan nata ya ajiyeta a wajen aikinsu.


************
Mr President tare da tawagarsa Suka sauko daga ckn jirgi ga jamaa nan birjik ana ta daukansu hotuna daga nan Suka shiga motocin da aka tanada musu Suka dau hanyar villa.
     Bayan ya huta ya bada umarnin cewa bazai ga kowa ba se xuwa gobe saboda yana bukatar Hutu. Ckn gida ya wuce bangaren yaransa bodyguards na binsa a baya ga bash kuma a gefe ya iso dab da falon sauran sun tsaya amma banda bash , tare Suka shiga katafaren falon tare da sallama umaima tana kwance tana chat sultan kuma yana buga game . suna ganin mahaifin nasu Suka ruga a guje Suka shige jikinsa ya rungumesu gam gam gwanin tausayi yaran daga gani ansan cewa kadaici da maraici na addabarsu sun kai minti2 a rungume da juna sannan Suka sake shi yana murmushi yace

"My sultan ya kake"

"Lfy dad I miss u"

"I miss u more my sultan ya jikin sisy"

"Dad bansan meya sameta ba kullum se tayi kuka"
Mr President ya juya yana kallonta ta sunkuyar da kai bash ma ita yake kallo.a hnkli ya rike hannunta ya fara magana

"My baby me yake damunki"

"Ba komai dad"

"No tell me pls"
Sai kawai ta fashe da kuka nan ya jawota jikinsa ya fara rarrashinta dakyar ta bar kukan Suka xauna a kujera daya ya fara jansu da labari suna kwance a jikinsa.
Duk sanda umaima ta daga kai sai sun hada ido da bash , mr President ya kira iyayensa a waya ya hadasu sun Dade suna hira grandpa ya shaida musu yana nan tafe nan ba da dadewa bah haka Suka Dade a falon yana ta basu labarin China sosai ya cire mata radadin da take ji ya rage mata damuwanta , bash kuwa hnklinsa yayi nisa yana son ya gano matsalar umaima Amma ya kasa tuna komai.
Bayan tsawon lokaci mr President ya musu sallama ya tafi bash kuwa ya xauna yace magana xaiyi da umaima.
  
"Umaima ki gaya min me yake damunki"

"Babu"

"Umaima look at me"
Ta daga kanta idanunta Suka fada ckn nasa tayi saurin kawar da nata 

"Umaima dama baki daukeni a bakin komai ba daz y kike boyemin damuwarki"

"Ba haka bane bash"

"No! Nagane matsayi na tnx"

Yana gama fadin haka ya tashi ya fara tafiya se kuma ta fara kuka cak! Ya tsaya ya juya yana kallonta haka nan sultan ma ita yake kallo "ya ilahi me yake damun yarinyar nan ne"
Ya taka yaxo ya sunguna a gabanta yace 

"4Allah's sake umaima ya kike so a miki? Ki fadi matsalarki kin kasa fada kullum se kuka"

Tayi shiru batace komai bah
" pls ki daure ki gaya wa dad dinki tunda ni baxaki iya gayamin bah, kuma ki rage yawan tunani kar ya jawo miki prblm pls"

"Nagode" ta furta a hnkli daga nan bash ya tashi ya tafi tabi bayansa da kallo Allah Sarki bash baisan ma tana yi bah ita kanta takanyi mamakin irin son da takewa bash Wanda bata San yaushe ta fara shi bah haka nan bata San ranar dainawa bah.
Ita dai tayi imanin cewa tana sonshi Amma ko xata mutu ne baxata taba furta mishi bah, kuma bata tunanin cewa xata so wani mahaluki a duniya bayan basheer bah.maybe ita ma auren xumunci xaa mata cos ita kam basheer kawai take so a rayuwarta.

Allah Sarki umaima😥😥


Muje xuwa love u all 😘😘😘
[2/21, 2:38 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*33*
By *Reefat yahya*


Shuairat tana xaune a ofishinsu bodyguards Suka shigo Suka sanar da ita cewa mr President na bukatar ganinta ba tare da bata lokaci ba Suka fice tare.

     Yana xaune a dakin hutawarsa ta shigo tare da sallama ya amsa ba tare da kalleta bah yana rike da wani Dan karamin cup black coffee ne a ciki yana sha a hnkli , waje ta samu ta xauna shiru sukayi babu Wanda yayi magana har tsawon minti 10 shuairat CE ta gaji da xaman nasu tace

"Mr president ka aika a kirani ina aiki n u din say anytin"

"My first lady yaushe xaki koyi gaisuwa ne? Ko baki iya respecting magabatanki"

Wani irin kunya ne ya lullubeta amma bata son ya gane hakan tayi gyaran murya tmkar Mara gaskiya tace

"Emm...uhmmm sorry about dat actually...

"Is ok! Neva mind , anyway na kira ne saboda ina son sanin hukuncin da kika yanke ko kuma in CE shawarar da kikayi batun maganar da mukayi som few weeks ago"

Ya tare numfashimta tare da kura mata ido

"Mr president I don't knw wat to say about it"

"Look Ayshah lokaci yana tafiya ya kamata ki fito fili ki gaya min cos my dad is on his way soon kuma xancen auren ne xe kawo shi"

Shiru sukayi kowanne da tunanin da yake yi ckn sanyin murya shuairat tace
"Mr president idan nace baxan aure ka bah wat will b d outcome"
Murmushi yayi yana girgiza kai yace

"Funny girl! Me a ciki ? Kawqi ki fito ki gayawa yan jarida da sauran jamaa cewa karya kikayi tun da can ba abunda yake tsakanin mu kinyi hakan ne....
" mr President ya xakayi da ...

Hannu ya daga mata yace
"Don't worry about me, kawai ki fito ki gaya musu gaskiyan idan xaa cireni akan mulkin ma fine I don't kia n xanyi tunani akan abunda xan sanar wa mahaifina so kada ki sa damuwa a ranki"

Ta rintse ido ya ilahi wannan wace irin jaraba CE? Shin ya xatayi? Ta amince da auren ko kuwa ? Toh idan ta fito ta fadi gskiya tabbas jamaa xasu mata kallon mutuniyar banxa daga ita har mr President yanxu me abun yi? Muryan mr President ne ya katse mata tunani

"Ayshah u don't have to worry about me"

"About u? Mr President dis is about us ya shafeni ka gane koh?
Murmushi yayi yace 

"Nasan ma kina son auren kina wani nokewa pls feel free Ayshah"
Ta daga idanunta Suka fada ckn nasa ta murguda masa baki tare da cewa

"Meyasa xan so auren tsoho ? Kawai de kai kafi bukatar auren ba ni bah"
Tana gama fadin haka ta juya tabar masa falon yana murmushi shi kadai.

A waje Suka ci karo da umaima kallon kallo Suka tsaya yi daga karshe shuairat tasa kai xata wuce umaima ta fisge hannunta da karfi
"Ina xaki je munafukar karuwa kawai kin xo kin like wa mahaifina daga ganin arxiki koh"

Wani shuumin murmushi shuairat ta sakar mata tare da cewa 
"Karuwancin ma iyawa ne wata idan tayi ta samu kudi wata idan tace xatayi duka xata sha"

Hannu umaima ta daga da niyyar Marin shuairat cas ta cafke hannun tana murmushi ta nunata da yatsa
" yarinya kinyi kadan wannan fuskar ba kowane mahaluki bane xe iya taba shi ba kingane koh, n don't 4get saura kankanin lokaci na xame miki uwa "

"Har abada Baxaki taba xama matsayin uwa a gareni bah" 
Nan kuwa umaima ta fara hawayen jin an ambaci sunan uwa ta tuna da mahaifiyarta shuairat ta sake mata hannu ta juya xata tafi umaima ta sake Jan gyalenta da karfi ta juya suna fuskantar juna tace

"Ke umaima kike ko wa ki shiga taitayinki ni ba Saar yinki bane da mahaifinki nake dealing ba da ke ba , so ki kiyaye"
Bash ne ya hangosu ckn Sauri yaxo ya shiga tsakaninsu umaima ta fashe da kuka dai2 nan mr President ya fito don ganin meke faruwa shuairat ta juya ta kakkabe gyalen ta fara tafiya sai kuma ta juya ckn gadara tace

"Mr president I tink ya'r ka bata da tarbiya yana da kyau ka sanar da ita cewa aurenmu yana nan xuwa bada dadewa bah xan dawo gidan nan da xama she shul learn how to respect me "

Mr President da bash baki Suka bude suna kallon shuairat wacce ta wuce direct gun mota aka bude mata ta shiga umaima kuwa ta fashe da sabon kukan bakin ciki dad nata ya juya xai mata magana ta daga masa hannu alamar cewa bata bukatar jin komi daga garesa , wani dogon numfashi yaja sun hada ido da bash ya masa nuni da ido akan yaje ya mata magana hakan kuwa akayi umaima ta koma bangarenta bash yabi ta baya.






😘😘😘lov u all
[2/21, 2:38 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*34*
By *Reefat yahya*


Ta xauna dirshan a kasa wani irin bakin ciki take ji bash ne ya shigo yana mata murmushi ta kawar da fuskarta gefe handkerchief ya fara mika mata ta karba ta share hawayen sannan ya tashi ya bude fridge ya dauko mata ruwa mai sanyi nan ma batayi gardama ba ta karbi goran ta shanye tana sauke numfashi a hnkli nan kuwa taji hnklinta ya kwanta

"Umaima kiyi hakuri I know hw u feel"

"Hakurin me xanyi basheer? Nasan laifi na ne ni nafara nemanta da fada but...
Kuka ta fara yi bash ya cije lebe yana tunani halinsu iri daya da shuairat se saurin hawaye ga Neman magana koda yake mata ma dukkansu suna son kuka

"Bash baxan jure ganin dad da wata bah a matsayin matar da xai aura, it always reminds me of my mom"

"But umaima ya xakiyi? Allah ne ya kaddara hakan y not kiyi hakuri ki xuba musu ido"

"But na kasa bash! I can't baxan jure ganinsu bah wai ma dad har soyayya yake da wannan yarinyar?

"Umaima...
"No bash! Kasan me yake bata min rai? Tun ynxu fah idan ta fadi Abu dad baya tsallakewa idan sunyi aure fah?

"Umaima don't worry kiyi hakuri komi xai daidaita , nide ki rage yawan fushin da kike yi pls kuma ki daina disrespecting din dad naki pls"

"Ok "
"Pls promise me dat baxaki kara fushi da dad bah"

"Ok I promise"
"_gud girl daz y I like u"

Murmushi take ita kadai tasan abunda take ji, haka bash ya xauna yana debe mata kewa daga karshe ya mata sallama ya tafi.waya ta cire ta kira wata yar mamanta bayan sun gaisa take shaida mata cewa dad nasu xeyi aure haka anty kadi ta bata hakuri akan cewa ta kwantar da hnklinta dama dole wata ran xeyi aure ko ba ynxu ba.


***********

Shuairat CE tare da shukrah suna xaune suna hira a falon shukrah ya shigo tare da sallama shukrah ta karbe jakan hannunsa shuairat ma ta masa sannu da dawowa yace

"Baby I don't like wat u did today"

"Yaya ba laifina bane"
"I know but da kin kyaleta kawai"

"Haba yaya ya xaayi...
"Baby kada ki manta aure xakiyi ki koma a gidan bai dace Ku fara samun matsala tun ynxu bah"

"Yaya kasan baxan taba barinta ta mare ni ba koh"

"Yes na sani kuma ki rage nuna gadara da iko a gaban mr President he deserve som respect , duk da bansan limit na soyayyarku bah"
Shiru sukayi suna kallon kallo shukrah CE ta fito daga ckn daki tana kallon halin da suke ciki tace

"Lfy? Meke faruwa?
"Ba komai bash ya bata amsa sannan ya tashi tayi shigewarsa daki ya barsu ta juya gun shuairat tace

"Bestie menene?

"Ki tamabayi mijinki "
Nan itama ta fice ta koma bangarensu dakinta ta shiga ta fada gado ta rike kanta
"Ya Allah Kaine gata na ka xabamin mafi alheri tsakanina da mr President " ta lumshe idonta nan ta fara tuna fuskar mr President farine Sol dogo mai matsakaicin jiki yana da saje da dimple gashin kansa baki mai laushi yana da shanyanyun idanu farare gashi nan so cool bai iya fada bah baya son hayaniya duk abunda tayi se ido kawai yake xuba mata baxai furta komai bah
"He is too young 4his age"
ta furta a hnkli se kuma tayi murmushi .

Hmmmmm *Reefat* tace 
"Shuairat ar u in love??? 
Hmmmm muje xuwa


😘😘😘😘
[2/21, 2:38 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*35*
By *Reefat yahya*


Alh Mohammed mahaifin mr President ne yake saukowa daga benen jirgi ga nan jamaa da dama ciki kuwa harda mr President ga yan jarida birjik se daukansa hotuna suke mr President ya karasa ya rungumi mahaifin nasa ckn farin ciki ya rike shi a kafada suna dariya Suka wuce filin motocin da aka tanada musu convoy na motocin Suka dau hanyar xuwa gidan mr President.

       "Daddy nah I miss u so..much"

"I missed u too my boy"
Suna dariya bash ma yaso yin dariya Amma ya danne sarai mr President ya gane hakan se ya juya gun mahaifin nasa yace

"Daddy kaga wai kirani boy shine yake basu dariya"
Mahaifin nasa ya juya yana murmushi ya kalli bangaren da bash yake a gaban mota yace

"Yes! He is my boy cos shi kadai Allah ya bani kuma har ynxu ganin karamin yaro nake masa"
Murmushi sukayi haka Suka kasance har Suka karasa gida.
Umaima da sultan Suka fito da gudu Suka fada jikin kakan nasu yana dariyar jin dadi ya rungumesu sosai yaran na basa tausayi musamman idan ya tuna irin shakuwarsu da mahaifiyar tasu bayan sun shige katafaren falon mr President nan masu aiki Suka cika dinning da abinci kala2 ga yan xuwa barka da xuwa nan birjik bayan jamaa sun da tsagaita ne Suka wuce dinning table don cin abinci.
Mr President yana xaune kusa da mahaifinsa umaima kuwa tana gefen bangarensa na hagu sultan ne gefenta anyi serving dinsu kowa ya fara cin nasa, Alh Mohammed ne ya fara magana 

"Son am so happy batun auren nan naka ka farantamin rai sosai"
Mr President ya fara tari daga nan ya dau ruwa yana kurba a hnkli sun hada ido da umaima ta kawar da fuska gefe.ya cigaba da cewa

"Dama naxo ne xancen auren naku , gobe xanje mu gana da iyayenta mu sa rana"

"Daddy y not...
"Boy bana son musu pls"

"Ok daddy Allah ya tabbatar da alkairi "

"Yawwa haka nake son ji.ynxu in banda abinka shkru nawa da rasuwar matarka amma ka kasa samun wata ko don yaran nan naka baka tunanin suna bukatar wacce xata debe musu kewa da rashin mahaifiyarsu?

Se ynxu umaima ta sa baki
"Granny mu bamu da matsala idan sultan ne kuwa yana da nannies masu kula dashi ba sai ya auro wata ya kawo bah"

"Oho! Ynxu nagane me  yake hanaka aure wato wannn ja'irar ya'r taka ce bata son kayi aure koh? Toh karya kike umaima aure kam dole sai yayi kuma nan ba da dadewa bah"

"Daddy pls..
"Rufemin baki, baka da abunda xaka gaya min.Amma ka bani mamaki wallahi "

"Daddy plsss...
Fuu..umaima ta tashi ta bar falon ta tafi bangarenta Alh Mohammed ya juya yana kallon Dan nasa yace 

"Boy! Irin tarbiyar yaranka kenan? Gaskiya nayi mamakin ganin haka a ckn gidanka son.kai kadai Allah ya bamu mun dauka son duniya mun dora a kanka amma hakan bai hanamu baka tarbiya mai kyau bah but y?

"Daddy am sorry wllhi umaima bata jin magana na ban....

"Quiet! Boy...kai ka haifeta ko ita ta haifo ka? Which one? Tell me!

"Daddy am sorry"
Mr President ya marairaice tmkar xeyi kuka nan kuwa mahaifin nasa yaji tausayinsa yasan sarai Suleiman be iya fada bah he is too cool shiyasa umaima take yin abunda ta ga dama can yace

"Ok son! Gobe insha Allah xan gana da mahaifin yarinyar xaa saka ranar aurenku nan ba da jimawa bah, aurenka na fari ni na xaba maka matar da ka aure n dis tym ka kawo wacce kake so dole xan jajirce don ganin na cika maka burinka.Allah ya bada xaman lfy insha Allah wannan yarinyar xata xame mana alkairi xata kawo farinciki a rayuwarka believe me son"
Yana magana yana kallonsa bayan ya gama ya tashi yayi shigewarsa dakin da ya saba sauka duk lokacin da ya kawo musu xiyara.sultan yabi bayan kakan nasa  aka bar mr President shi kadai a xaune yasa abinci a gaba yana tuna kalaman mahaifinsa "shin da gaske Aysha xata kawo farinciki a rayuwarsa? How? Meyasa daddy ya fadi haka? 

Hmmmmm..... Ya xata kaya tsakaninsu?
Muje xuwa

😘😘😘
[2/21, 2:38 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*36*
By *Reefat yahya*


Mr President ne xaune a falonsa yayi nisa ckn tunani bash ya shigo tare da sallama

"Mr president sir!
Firgigit ya motsa a hnkli yace

"Ehmm...basheer pls ina son ka kai daddy na gidansu Ayshah Bello"
Jim bash ya tsaya yayi shiru se kuma yace 
"Ok sir!
Daga nan yayi waje wayarsa ya fitar yayi dialing din numbar mama ckn kankanin lokaci ta daga tare da sallama

"Mama ya gajiya"
"Lfy ya aiki"
"Alhamdulillh, dama mahaifin mr President ne zaizo Neman auren baby ynxu haka xamu taho tare shine nace bari na sanar daku"

"Tohh! Ikon Allah , dama shuairat ta daidaita da shugabankasa shine bata gaya mana bah?

"Mama kada ki sa damuwa a ranki kawai ki sanar da baba gamu nan xuwa yanxu"
Ya katse wayar a dai2 nan daddy ya fito yasha many an kaya se uban qamshi ke tashi bash ya fara soshe 2 kamar Mara gaskiya daga nan aka bude musu mota Suka dau hanyar kubuwa xuwa gidansu shuairat. Bash ya turawa matarsa text akan ta tanadi kayan motsa baki danginsu snacks da fruits se kuma lemuka masu sanyi ya sanar da ita gasu nan a hanya yana tare da manyan baki.

Baba da mama suna xaune a falo mamakin alamarin sukeyi domin basu taba tunanin cewa mr President xe auri ya'rsu bah suna nan xaune suka ji dirar motoci a kofar gidan bash ne ya sauka da sunan zeyi sallama don a basu ixinin shiga ya tura kofar gidan a hnkli yasa kai a ciki (basu San cewa gidansu bane lol) bayan kankanin lokaci  ya fito ya shaidawa daddy ya fito nan Suka shiga har falon baba yana xaune shi kadai daga nan bash ya bar musu falon...
Bayan sun gaisa nan Suka fara hira tamkar sun Dade da sanin juna daddy ya shaidawa baba kan cewa shi Dan jahar Adamawa ne haka nan shima ya gaya masa shi Dan Adamawa ne sosai sunyi hira harda dariya tamkar sun saba da juna tun asali 
Shukrah CE ta shigo tare da sallama ckn ntswa ta gabatar da kayan motsa baki bayan sun gaisa ta sa kai ta fice ta koma bangarenta bayan wani Dan lokaci mama ta fito Suka gaisa da daddy sannan ta koma ckn daki daga nan daddy ya gabatar da bukatarsa na Neman auren shuairat baba yayi shiru can kuma yace

"Alh da zaka bani lokaci zan...

"Haba Alh bello ai anzama daya, kuma yaran nan suna son juna tunda sun fito fili sun bayyana hakan.kuma shi yaron matarsa ta Dade da rasuwa munyi iya bakin kokarinmu ya kara aure amma Sam yaki, don haka ina rokonka ka taimaka ka bamu ya'rka tunda de sun daidaita suna kaunar juna"

"Alh Muhammad bawai zan hanaku bane, kasan shaanin yara"

"Haba Alh..Suleiman fah ba yaro mana shekarunsa 40 da doriya na tabbata xai rike ya'rka bisa gaskiya da amana , nidai burina ka amince mu sanya musu albarka kuma in son samu ne a daura auren nan da sati 2 masu xuwa"

"Ahhh..abun ma da wuri haka ne?

"Ehh mana..burina shine ka amince batun wani shiri koma menene bai taso bah ba se ansiya mata komai ba ni xanyi kayan daki da duk wani abunda zaa bukata na auren"

"Haba Alh Muhammad bazaayi haka bah"

"Alh bello bazaka gane farinciki da nake ciki bah, Suleiman shi kadai Allah ya bani a duniya burina shine naga ya tara min jikoki dayawa se kuma Allah ya kaddara matarsa ta haifi yara2 ta bar duniya.don haka nake son ayi wannan auren da wuri ko Allah zaisa da rabo a ciki"
Baba yayi shiru yana naxarin kalaman daddy

"Kayi shiru Alh bello, kada ka manta yanxu mun xama yan uwan juna fah " ya fada yana dariya baba yace

"Shikenan Allah ya tabbatar da alheri ya basu zuria ta gari masu albarka"

"Ameen yanzu naji magana! Nagode sosai ALh bello Allah yabar xumunci ya saka da alheri" nan ya xare bundir na yan dubu sabbi fil har bandur 3 ya ajiye a gaban baba

"Me wannan Alh Muhammad? Kaga abunda bana so kenan, ni ban nemi koda sisi ba daga gareku don Allah ka maida shi kuma auren nasu idan yazo bana son almubazzaranci a kimanta komi a yishi  dai2 gwargwado nasan kuna da kudi amma ni bana son hakan"

"Alh Bello jahar mu daya da kai kasan al-adunmu na Adamawa idan anzo Neman aure da goro ake xuwa , nikuma ban siyeshi ba saboda ina marmarin xuwa don haka wannan kudin goron Neman aurene ba komai bah"

"Nasan da hakan Amma na yafe"

"Aa'a bazamuyi haka da kai bah alada CE dole sai anyi , batun almubazzaranci kuma insha Allah bazaayi bah na maka alkawarin hakan"

Baba ya xare bandir daya ya maida sauran yace

"Allah yayi albarka ya sanya alheri nagode"

"Sauran kudin fah Alh"

"No! Wannan ma yayi yawa kawai bana son gardama ne"

"Toh nagode sosai Alh bello se a fara shirin daurin aure nagode sosai"
Nan sukayi musabaha baba ya rakashi har bakin mota sukayi sallama driver ya ja a yayinda bash yake zaune a gefe Suka dau hanyar gidan mr President.


Hmmmmmm.muje xuwa
[2/21, 2:39 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*37*
By *Reefat yahya*


Shuairat tana xaune a ofishinsu ta buga uban tagumi wayarta CE ta hau ruri numban mama ta gani ckn mamaki ta daga sabida mama bata taba kiranta ba muddin tana wajen aiki
"Hello mamana"
"Baby kizo gida yanxu"
"Lfy dai koh?
"Kizo ina jiranki"
Ta kashe wayar tayi jugum se kuma ta tashi ta fara harhada takardunta bayan ta gama tayiwa Sarah sallama akan cewa ana nemanta a gida carab Suka hada ido da Mahmud yayi sauri kauda fuskarsa gefe taku biyu tayi ta karasa inda yake

"Mahmud ina son yin magana da kai"

"Sorry am busy"

"I knw but maganar is very important"
Ba gardama ya tashi Suka fita waje

"Mahmud wane laifi nayi to deserve dis?

"Bangane bah ! Wani Abu ne ya faru?

"Mahmud pls ka gaya min me namaka plss...

"Shuairat baki min komai bah"yana gama fadin haka ya juya ya koma ciki ya barta nan tsaye tsaki taja ckn jin haushin kanta wato ma har wani rigima yake mata mtswww... 
Nan ta tare taxi ta kama hanyar gida.

Mama CE zaune a dakinta tayi shiru tana tunannin kalaman aminiyarta Hajiya mairo
"Amina ki godewa Allah da irin kyautar da ya baki ki kwantar da hankalinki , ai wannan shine arxiki na binka kana gudunsa idan ba haka ba waye xaiki amincewa da auren shugabankasa? Kawai ki nusar da shuairat ki gyarata sosai ki koya mata dabarun xama da miji ba wani batun ya tsufah ki manta da zancen shekaru ki tashi tsaye ki nemawa ya'rki hanyar da xatabi ta zauna da mijinta lfy wannan shine abunda ya dace kiyi tagumi ko tunani ba naki bane"....shuairat CE ta katse mata tunani ta shigo tare da sallama ta fada jikinta tana juyi

"Oh mama! Kin tsoratani I tot wani Abu ne ya sameki tank God u ar fine"
Murmushi mama tayi tace
"Lfy ta kalau na kiraki ne ina son muyi magana"

"Go ahead ina jinki"
"Dazun nan mahaifin shugabankasa ya bar nan, ya zo Neman aurenki"
Dumm...xuciyarta ta buga nan ta tashi xaune 

"Waat? Neman aurena? Me baba yace masa?
"Me zai fada kuwa an saka ranan auren nan da...

"No! Mama it can't b nikam baxan auri tsoho bah"

"Aww really? Bazaki auri tsoho ba kika fito gaban dubban jamaa kika bayyana cewa kuna soyayya? Kiyi amfani da hankalinki shuairat ke fa kika amince masa ya turo iyayensa me kika maida mu?

"Haba..mama kinfa San komai akan alamarin nan na gaya miki yanda abun ya faru kuma wllhi bamu taba wani xancen soyayya dashi bah ..ni ..ni"
Se kuma ta fara kuka
Mama ta tabe baki tace 
"Kanki ake ji yarinya da can wani ne ya turaki kika CE kuna kaunar junanku? Ko a wancan lokacin baki San shi tsoho bane se yanxu? Bazaki maidamu mutanen banza bah bari kiji gara ma ki saita kanki kisan abunda kikeyi"
Nan mama ta tashi ta bar mata dakin shuairat ta nemi hawayen ta rasa😆😆 da can ta dauka mama xata rarrasheta ne aikuwa ta tashi ta nufi bangaren shukrah a falo ta sameta tana buga game
"Yadai mutuniyar"

"Mtswww...wato kina xaune ckn kwanciyar hnkli baki damu da halin da nake ciki ba koh"

"Me ya faru bestie" shukrah ta fada a yayinda take ajiye wayar hannunta ta gyara xama
Shuairat ta tura baki tace
"Kina ji wai daddyn mr President yaxo neman aure nah"

"😳😳kai ...dama shine yaxo gun baba dazun nan?

"Mstsww...ke ana serious kina wani mtsww

"Yi hakuri bestie dama kina soyayya da mr President ne baki taba gaya min bah"

"Allah na! Shukrah! Haba try to understand mana haaa da muna son juna xan damune ?😏😏

"Okkk...calmdown n tell me meyake faruwa"
Nan shuairat ta kwashe labarin kaf ta gaya mata murmushi shukrah tayi tace 
"Trust me kuna son junanku just dat Baku fahimci hakan bane but wit tym...

"Hey hang it girl! Ar u kidding me? Ya zan fara soyayya da tsoho ne ..yurk! U know I can't "

"Babe baki gane ....
"Pls bestie stop it! Shi tsoho ne bai San me ake cewa love bah n shima ya gaya min bai taba yi bah"

"Tsoho? Ya kai 80 ne?
"Ahh..haba he is 40+"

"Hmmm bestie he is still young u can handle it, waima lemmi ask u salman khan na Indian film shekarunsa nawa?
"40+"

"Wat of sharukh khan? 
"40+"
"Akshay kumar fah?
"🙄🙄🙄 shima haka"
"Me zasu nunawa mr President? Kyau? Ilimi ko arziki? Hey girl wake up! Mata nawa suke neman mutanen da basu kai mr President bah? About 1000+ n duk fadin duniya babu macen da zata ki auren mr President but y bestie? Kiyi aiki da brain naki pls ke da kanki kika CE he is so cool..meyafi hakan toh namiji kyakkyawa ga ilimi ga hankali ga tausayi ga arixizi ga ga ...komai ya tara me laifinsa? N tell me ke din kintaba son wani namiji? Maza nawa Suka so ki Amma baki sauraresu bah kinga kenan Allah ne ya hadaku shi bai taba soyayya ba kema haka kiyi tunani akai shuairat u can do it u can handle it after all u ar a lady ni kaina ke kika koyamin wasu abubuwa da dama y not kiyi amfani da su? Ki zauna da kyau kiyi tunani"
Daga nan shukrah ta tashi ta shige kitchen ta bar shuairat da dogon tunani akan kalamanta...



Hmmmmm
[2/21, 2:39 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*38* 
By *Reefat yahya*


Mr President tare da daddy da sultan suna cin abincin dare a dinning table na bangaren mr President umaima kuwa taki xuwa a dole wai tana fushi daddy ne ya fara magana

"Boy u ar lucky wallhi surukinka mutumin kirki after ol Dan Adamawa ne"

"😳 ..uhmmm ehh dad namanta ne ban gaya maka cewa shi Dan Adamawa ne ba "
Lallai shi da bai taba xuwa gidan surukan nasa bah ina zai San halayensu...

"Boy kana ji nah"
"Ehh..ina jinka daddy"
" idan na koma zanyi magana da momsin ka batun hada lefe xatayi magana da sakeena ya'r wanta wacce take business na kaya zaa hada komai a kawo daga nan sai a kai gidan nasu koh"

"Ok daddy nagode but da nace kudi zan bata ta siya da kanta"

"No! Mu zamu siya komai kuma babanta yace baya son almubazzaranci saboda haka komai dai2 gwargwado zaayi"

"Ok daddy nagode Allah ya kara tsawon rai "
"Ameen! Auren naku nan da 3weeks ne"
😳😳wani tari ne yaxo masa wani bugun xuciya yaji...damm

"Boy ar u ok!
"Ehm..umm.am ok daddy am am fine"
Gub...gub haka xuciyarsa ya cigaba da bugawa innalillahi kawai yake maimaitawa can yaji muryan daddynsa na cewa 
"Sultan tashi muje muyi hiranmu koh kasan gobe jirgin 7 zanbi insha Allah"
Daga nan Suka tafi aka barshi shi kadai nan ya fada duniyar tunani ....yanxu da gaske aure zaiyi? Ya zasu kaya da umaima? Ya zaman nasu zai kasance? Shuairat zata zauna lafiya ta rike masa sultan ? Anya xai iya kallonta a matsayin mata? Wace irin rayuwa zasu yi? Hmmm lallai yana da babban aiki a gabansa...haka dai ya cigaba da tunane tunanensa..



****************
Shuairat CE xaune a gaban dressing mirror tayi jugum tana tunani wai ynxu da gaske aure zatayi? Mr President xata aura? Ze iya bata romantic lyf da ta Dade tana mafarkin samu? Zai iya kallonta a matsayin matarsa? Zata iya zama da umaima da sultan? Ya rayuwarta zai kasance? Ya.....
Bude kofar dakin da akayi ne ya dawo da ita daga kogin tunanin da take mama CE rike da waya a hannunta ta mika mata 

"Hajiya mairo xata miki magana"

"Ok" nan ta sa hannu ta karba ta kara a kunne tare da sallama
"Ina yini anti"
"Lfy my baby ya kike ya aiki"

"Lfy alhamdulillh"
"Baby nah magana xamuyi ta fahimtar juna"

"Ok anti ina jinki"

"Mama ta gaya min halin da kike ciki Amma ina son ki kwantar da hankalinki ki gane cewa aure nufi ne na Allah kuma matar mutum kabarinsa ki daure ki amince da zabin da Allah ya miki alkairi ne insha Allah, ki sake ranki ki cigaba da activities dinki kinji?

"Ok anti nagode"

"Ki kwantar da hankalinki munyi magana da yayanki zai sama miki ticket ki bi flight gobe kixo Kano gida kinji"

"Ok anti tnxx"

"Yawwa my baby takkia sai na ganki koh"

"Ok anti bye"daga nan ta mikawa mama wayar ta kashe ta juya suna fuskantar juna mama tace

"Ki shirya kayanki gobe jirgin safe zaki bi ki tafi Kano "

"Ok mama "
"Batun events kuma walimah kadai ya wadatar ko kuwa akwai program da zaki yi"

"Walima is ok "
"Toh shikenan ki fara shirya kayanki yanxu"
"Ok toh" daga nan mama ta bar dakin shuairat ta hada kayanata kala10 a travelling bag bayan ta gama se ta shiga watsap mssgs Suka shigo dama ta kwana2 bata shiga bah. Mssg din princess maimah ta gani

"Hi dear fren ya kike
"Fyn " ta mata reply tana online dat tym se ta tura
"Wia have u bin shiru 2days"

"Ina nan just busy ya gida n evrtin"

"Fine alhamdulillh kawai gt a little prblm wit dad ne"

"😳ur dad? Haba y?

Nan ta gaya mata abunda ya hadasu shuairat tace

"Haba kawa ba kyau fushi da iyaye"

"Ok tanx xan kiyaye next tym" 
murmushi princess tayi a dayan bangaren a xuciya tace she is just like her bro.haka Suka cigaba da chat nasu har na tsawon lokaci sannan sukayi sallama.



Ku biyoni....😘😘😘😘😘
[2/21, 2:39 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*39*
By *Reefat yahya*


A airport mr President yayi sallama da mahaifinsa yana rike da hannun sultan suna dagawa daddy hannu har sun juya xasu tafi daddy ya sake dawowa gun mr President yace 

"Boy is gud kaje ka gaida surukinka"

"Ok daddy xan samu lokaci"

"No! Son xanso ace yau xaka je"

"Ok insha Allah zanje"
"Ok gud na tafi sai munyi waya"

"Safe trip a gaisheda momsi"

"Ok zata ji" daga nan mr President ya ja hannun sultan Suka shiga mota Suka kama hanyar gida.
     Da yamma misalin karfe 4:30 mr President yasha manyan kaya se qamshin turare ke tashi an jera motoci bash na gidan gaba tare da driver a yayinda mr President ke xaune a gidan baya hannunsa rike da magazine yana karantawa , a kofar gidansu shuairat akayi parking na motocin dama can baba ya San da xuwan surukin nasa batare da bata lokaciba Suka shiga ckn gidan bodyguards Suka tsaya a waje bash na gaba mr President na biye dashi.baba na xaune a falo Suka shigo tare da sallama bayan sun gaisa an jerawa mr President kayan marmari iri2 Amma ko ruwa bai iya ya sha bah saboda kunyan baba yake ji, basuyi wani dogon hira bah shiru Suka yi tamkar babu kowa a falon chan baba ya daure yace

"Duk da naji cewa kana kaunar ya'ta amma don Allah ina rokonka ka riketa bisa gaskiya da amana bana son wani Abu ya sameta"

"Insha Allah baba na dau alkawarin kula da ita babu abunda zai taba ta "

"Nagode! Allah ya Baku zaman lafiya da zuria mai albarka"

"Ameen" mr President ya amsa ckn jin kunya daga nan mama ta fito Suka gaisa ta koma ciki ta barsu, haka nan sukayi sallama mr President ya tafi sannan bash ya shigo da bandir din kudade ya ajiyewa baba shi kuma se fada yakeyi wai akan me bash xe karbi kudin bai sauraresa ba yayi ficewarsa saboda ana jiransa a waje xasu koma gidan mr President.


*******************
Shuairat CE zaune a dakin da aka sauketa a can Kano ta ajiye kazar da ta sha hadin magunguna a gaba ta rasa ya xata fara cinsa gashi ta taba ta jishi ba dadi anti mairo CE ta shigo tare da sallama 

"Lalala..baby har yanxu baki cinye bah? Gaskiya xamu bata dake"
ta tura baki tare da yatsina fuska tace

"Allah anti ba dadi bazan iya ci bah"

"Baby ki daure haka ki ci if not xamu bata oya ..now "
Haka tasa shuairat a gaba dole ta cinyeshi tass tana maida numfashi dakyar.bayan ta huta kadan mai gyaran jiki ta fara tata aikin haka Suka yini ranar gaba daya se gyarata ake yi har dare bata huta bah wani hadin tsimi aka bata dole ta shanye. 
     Misalin 9:00pm ta watsa ruwa tayi shirin bacci kenan ta kwanta a gado dama dakin ita kadai CE a ciki ta bude data mssgs na watsapp dinta Suka fara shigowa se kuma wayar ta fara ringing sabuwar num ne kuma special har ya kusan tsinkewa sannan ya daga ta kara a kunne tare da sallama

"Hey reporter ina kika je ? Wato baki xaman gida koh?

"Pls who is on d line?
"Baki ban amsa bah"

"Mr president?
"Baki xaman gida ina kike xuwa?

"Mr president ko kamanta cewa am a reporter so I have....

"Luk Ayshah daga yau nayi banning duk fitanki har xuwa ranar daurin auren"

"Aww..da gaske? 
"Tambaya kike? Dont u have som respect?

"Umm..am sorry"
Shiru sukayi dukkansu biyu kowannensu ya rasa abun fada daga karshe ya kashe wayar.daga can bangarensa tunani yake meyasa ma ya kirata? Kuma idan tana fita ma meyasa zai damu? Daya bangaren xuciyarsa yace of coz matata tace dole na damu, no! I don't have too" shiii...ya sunkuyar da kai yana tunani ya kasa samun amsa ko daya.shuairat ma haka abun ya kasance mata ta kurawa wayar ido tana tunani daga karshe ta share maganar kawai ta shiga watsapp dinta Suka fara chatting da princess maimah da kuma shukrah.


Ku biyoni....
Love u all 😘😘😘
[2/21, 2:39 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*40*
BY *Reefat yahya*


Bayan sati daya aka kawo lefen shuairat mata biyu ne kacal Suka xo anyi musu kyakkyawar tarba an karbesu ckn mutunci akwati set 2 ne cike makil da kaya masu kyau Wanda bazan iya siffantasu ba sai dai masu karatu su kimanta da kansu😜 daga karshe sukayi sallama Suka tafi bayan an cikasu da snacks da drinks kala2.shukrah kam se santin kayan take xubawa aikuwa tayi snapping ta tura a instagram da watsapp cewa ga kayan lefen aminiyarta amma bata bayyana cewa mr President ne xai aureta. Shuairat ma ta yaba da kayan sunyi kyau ba karya , shirye shiryen biki ake Amma mr President ya hana duk wasu programs da zaayi ciki kuwa har fansan amarya yace bayaso sabida yasan yan gulma zasu cika wajen shuairat CE zatayi walima shikenan.


****************

"Umaima lfynki kuwa? Yarinya kin dau karan tsana kika dora akan mahaifinki bayan kinsan Allah ne ya hallata masa auren kin isa ki hana ne?

"Wllhi anti khady wannan cin amana ne yanxu shekaru nawa ne da rasuwar mom amma har ya manta da ita? Se kuma ta cigaba da kukanta anti khady ta sake baki tana kallonta sannan ta cigaba da cewa

"Nidai baxan goyi bayanki ba umaima wannan ai rashin gaskiya CE , Allah ya halasta masa auren mata 4 ke kice baki so yayi auren? So kike ya kare rayuwarsa haka?

"Anti kinga yarinyar karamace fah wllhi tun bata shigo ba ya daina kulamu kuma...

"Ki bude kunnuwanki kiji abunda zan gaya miki, ki tashi ki koma ki bawa mahaifinki hakuri ki rungumi kaddara ki xauna lafiya da matarsa Allah ne ya kaddara baki isa ki hana bah "

"Gaskiya nikam baxan iya bah, ynxu dama duk son da yakewa mom ya...

"Dakata umaima bari kiji labarin da baki taba ji bah, dad da mom dinku auren xumunci aka hadasu dad naku ba shi ya nemi auren mom naku bah biyayyace ta sa ya amince ya aurota har Suka xauna tsawon xaman da sukayi.dad dinku bai taba yin soyayya a rayuwarsa bah kuma....

"Wait..an..anti kina nufin duk xaman da sukayi babu soyayya a tsakaninsu?

"Bansani ba umaima Allah shine masani nidai nasan dad mutumin kirki ne yana da kara sosai har gobe baraa sami yaro mai biyayya irinsa bah a duk fadin danginmu"
Shiru umaima tayi tana tunani kanta ya kulle kwakwalwarta ya to she anti kady CE ta dafata a kafada tace

"Kiyi hakuri ya'ta nasan kina taya mom naki kishi but koda ace tana raye itama bata da ikon hana wannan auren kiyi hakuri ki shirya ki koma gun mahifinki"

"Zan koma amma ba yanxu bah, sai bayan bikin nasu "

"Shikenan xan kira dad na fada masa kada ya tada hankalinsa gun nemanki "

"Ok anti nagode"
Haka ta cigaba da xubda hawaye tana jin wani radadi a ckn xuciyarta.


*********
Shuairat CE a gaban dressing mirror tana kallon kanta tabbas ta canza ba kadan bah fatar jikinta se sheki yake ga gashin kanta da ya sha gyara se kuma dadaddan qamshin da yake tashi a jikinta murmushi tayi a yayinda ta cigaba da kallon fuskarta tana admiring din kanta lallai mr President yayi dace😀😀tunaninsa ne ya fado mata a rai fuskarsa ta hango , kyakkyawan karshene ita kanta tasan da hakan kuma yana da karamin ruwa idan bakasan shrkarunsa xaka CE Dan shekara 32 ne ta lumshe ido tana tuna farkon haduwarsu yana magana so cool yana da class sosai kuma yana da tausayi musamman idan ta tuna ranar da ya share mata hawaye lokacin da take kuka, shin zata iya soyayya dashi? Anya kuwa? Hmmmm ko kadan bata taba mafarkin cewa taxa auri babban mutum kamarsa bah sai kuma rayuwarta na baya ya fara dawo mata a kwakwalwa.....


Muje xuwa....
*Reefat*
[2/21, 2:39 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*41*
By *Reefat yahya*


*wacece shuairat*???

Alh Bello mamman hafaffen garin maiha ne na jahar Adamawa su hudu ne a gun iyayensu Ahmadu Salihu bello da kuma zainabu a can garin maiha aka haifesu duka amma shi bello ya koma garin mubi da xama gun wan mahaifinsa a can yayi primary da secondary sannan ya wuce jamia ta bayero Kano a can ya karanta bangaren education, bayan ya gama ya dawo gida a Yola yayi bautar kasa a wannan lokacin ne ya hadu da Fatima ya'r layinsu mahaifinta ne limamin unguwarsu a can karamar hukumar maiha ta jihar Adamawa.
          Bayan ya gama bautar kasa akayi aurensu da Fatima shi kuma ya samu aikin koyarwa a makarantar secondary na technical school a can mubi.Bello da Fatima suna son juna sosai kullum suna cike da begen juma haka Suka xauna ckn rufin asiri , sun share sama da shekara 6 Allah bai basu haihuwa bah amma duk da haka bello bai taba nuna damuwarsa bah, Fatima tayi2 ya kara aure yaki sauraranta har ta gaji don kanta ta daina kawo masa xancen.kwatsam Allah ya bata ciki sunyi murna sosai hKa Suka kasance ckn farin ciki har Allah yasa ckn ya cika wata9 da yan kwanaki Fatima ta haifi kyakkyawan danta fari tas babu inda ya bar fuskarta cki kuwa har hasken fata saboda Fatima fara CE sosai, ranar suna yaro yaci suna Basheer.

Haka Suka cigaba da rainonsa har ya girma yayi wayo aka sashi makarantar firamari har ya gama Allah be kara basu wani rabon bah , basheer ya gama primary ya shiga secondary har ya kai ss1 sannan Allah ya bawa Fatima wani ckn batun murna kam baa magana basheer duk yafi xumudi akan cikin kullum hirarsa be wuce xancen a haifa masa kanwa ya'r kyakkyawa.
Bayan wata9 ciff Fatima ta haifi kyakkyawar ya'rta wacce tayi kama da bello tamkar anyi kaki an tofar yarinyar baka CE Amma ba sosai bah tana da Dan hasken fatA , haka aka saka mata suna Aisha ana kiranta shuairat.
   Shuairat ta tashi ckn gata gaba da baya koina sonta ake musamman yayanta basheer baya barin kowa ya taba ta, a wannan lokacin Alh bello yana koyarwa a jamiar federal university of technology Yola. Daga kan shuairat haihuwa ta tsaya musu cak da wannan lokacin ko bari Fatima bata sake yi bah, haka Suka rungumi yara biyun da da Allah ya basu.bash ya gama secondary dakyar ya yarda ya tafi jamia wai shi baya son ya tafi ya bar kanwarsa dakyar aka lallabashi ya tafi jamiar  Ahmadu bello zaria bayan ya kammala ya dawo yayi bautar kasa sai kuma aka daukesa aiki da state security service , shekaru sun gabata Alh bello yayi retire ya koma gida yana hutawa se kuma dansa ya samu canjin aiki xuwa fadar shugabankasa a wannan lokacin ne shuairat take Jin karshe a federal polytechnic dake can mubi har ta samu ta kammala inda ta karanta bangaren mass communication...
Wannan kenan shine takaitaccen tarihin rayuwarta.

A hnkli ta ja wani gauron numfashi kamar a mafarki take ganin duk abubuwan da suke faruwa a rayuwarta "ikon Allah kenan"
ta furta a hankali ynxu matsalarta shine ya xata fara nunawa mr President so? Anya zai kulata kuwa? Wane irin zama zatayi da umaima? Tabbas tana da aiki a gaba idan batayi da gaske ba xata fuskanci matsala a gidan wayarta ta hau ruri sunan shukrah ta gani nan ta daga
"Matar Yayan"
"Amarya bakya laifi ko kin kashe Dan masu gida"

"Lallai sai dai idan baa kashe din bah , ya kike ya gidan"
"Lfy lau yaushe zaki dawo"

"Umm..kinyi missing dina ne "
"Bani kadai ba harda angon mah"

"Bangane bah"
"Ehh..mana wai dama baki gaya mishi zakiyi tafiya bane?

"Y? Meyasa xan gaya masa?
"Hmm...dazu ya tura bodyguards wai yana son ganinki"

"Uhmm..yayi kyau"
"Munafuka kina so kina nokewa"
"Ehh..sai akayi yaya"

"Nidai ki dawo da wuri kan a buga mana news paper cewa mr President yana Kano"
"Wannan kuma maysalrku "

"Uhmmm..in tayi tsami ma ji"
"Babu abunda zakuji"

"Se anjima toh "
"Ok bye sai na kira "
"Ok takkia"
Tare Suka katse wayar shuairat tayi jugum tana tunani lfy mr President yake Neman ganinta?
Oho! 


Nima nace oho! Ku biyoni
[2/21, 2:39 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*42*
By *Reefat yahya*


A bangaren mr President kuwa yana xaune a dakinsa yayi shiru yana tunani anya zasu zauna lfy da yarinyar nan? Ta fiye takama da nuna isa, ysushe sukayi  waya amma taki ta sanar dashi cewa tayi tafiya?.mtsww meyasa ya nemi ganinta ma? Lols Reefat tace cos u miss her preety face"  wayarsa ya cire yana son kiranta sau 2 yana dialing sai kuma ya fasa a karo na ukun ne yayi ta maza ya kira har ya kusan katsewa sannan ta daya ckn sanyin murya tace

"Ur excellency"
Haka kurum yaji dadin sunan da tayi adressin nasa da shi wani murmushi ne ya subuce a fuskarsa
"My stubborn first lady! Ya kike"

Murmushi tayi da jin sunan stubborn ta gane abunda yake nufi

"Am sorry ur excellency nayi tafiya ba tare da na sanar maka ba"

"Is ok! Zaki iya yin duk abinda kike so as of now b4 ki shigo gidana"

"Don't worry a gidanka ma abunda naga dama zanyi cos am d first lady"
maganar ya sashi dariya sosai yace

"Well..we shall c! Anyway dama ina son ganinki ne saboda ina son sanin programs naki da kuma amount da kike bukata"

"Ur excellency ka kwantar da hankalinka bana bukatar komi iyayena xasu min idan ma akwai bukatar hakan"

"Nasan da haka but is my duty ..anyway zan tura miki 2mil kiyi shopping idan akwai bai isa ba let me know"

"😳2wat? No! No! Me zanyi da 2milion? Walima CE zanyi fah n olredy iyayena sun riga sun tanada komi na walimar so no need pls"

"Bana son jayayya sai anjima"
Nan ya katse waya shuairat ta kurawa wayar ido tana nanatawa 2mil ? Hmmm lallai ma ai wannan almubazzaranci ne.mr president kuwa ya tsinci kansa ckn wani farin ciki haka kawai yana murmushi yana lumshe ido daga nan ya kira bash ya shaida masa yana bukatar account number din shuairat.


***********\\
Jirgin yamma Suka bi sai gasu nan a Abj shuairat ta kara haske fatar jikinta ta murje tayi kyau sosai duk Wanda ya daga ido ya kalleta dole ya kara kallonta a karo na biyu. Bash ne yazo daukansu ita da anti mairo da diyarta Sadiya wacce take saar shuairat daga nan Suka kama hanyar gida .
        Gidansu a cike yake makil da jamaa babu masaka tsinke saboda saura 4days daurin auren shuairat , bangaren shukrah ta shiga a yayinda haj mairo ta wuce gun aminiyar tata ga danginsu nan birjik mutanen Adamawa kyawawa dasu falon shukrah a cike makil da jamaa ta sa kai tare da sallama shewa Suka fara yi wata ya'r kawun shuairat me suna Ummi ta tashi Suka rungumi juna da shuairat se ihu suke sai ga shukrah ma ta fito ta Ruga a guje Suka rungumi juna ta kalli shuairat tayi wani guntun dariya tace

"Gaskiya ne mata a gidan Dr Suleiman Muhammad first ladyn Nigeria da kanta, kasar ta kusa ta dawo hannunmu sai yanda muka juya ta"
Aikuwa sauran yan matan Suka fara shewa
"Aiyuriri ...mata a gidan shugabankasa Allah ya bar mana ke"
Dakyar shuairat ta samu ta shige dakin yayanta ita da shukrah da Ummi da kuma Sadiya.shukrah ta kawo musu lafiyayyen abinci ita da Sadiya Suka ci sukayi nak sannan aka baje a gado aka fara xuba shukrah tace

"Bestie kawaye nawa kika zaba"

"Ummi da Sadiya da maimuna ya'r anti luba sai kuma Hafsat mubi"

"Ok! Dama mr President ne ya turo yayanki yazo ya tambaya kuma tym din layinki baya shiga""

"Ok na kashe wayar ne tym da zamu tashi"

" mr President fah yana ji dake yarinya ! Kinga kalan zirga -zirgan da yan gidansa suke?

"Allah ko"
"Ehh ..mana wllhi ki rike tsohon nan da kyau don na lura yana sonki sosai"
Gaba daya Suka kwace da dariya Ummi tace
"Wa ya gaya muku shi tsoho ne? He is just 40 somtin ne fah "
Sadiya tace

"Gaskiya kam! Kimanta da zancen wani tsoho ki fito ki nuna masa so zalla Ku zauna lfy ya fiye miki wllhi, kuma kinga yana da wata shu'umar ya' mai shgen girman kai kada ki kuskura ki bari ta rainaki wllhi"
Shuairat tayi murmushi tace

"_ina nake da lokacin ta"
Mama CE tayi sallama a bakin kofar dakin shuairat ta ruga a guje ta bude ta fada a jikinta tana dariya

"Mama na I miss u"
"Ba wani u miss me bayan kinzo kinyi zamanki a nan baki nemi gani na bah"

"Wllhi Bahaka bane! Naga mutane sunyi yawa ne"
Daga nan tabi bayan Maman nata sukayi ckn gida.


Love u my fans😘😘
[2/21, 2:39 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*43*
By *Reefat yahya*


Karfe 4pm harabar city garden ya cika makil da manyan motoci kala2 idan ka duba can ciki bangaren da akayi decoration kuwa xaka bude baki ne galala tsantsan haduwar filin nikam xan iya cewa tunda nake ban taba ganin hadadden decoration irin haka ba😜😜😜 dama ansan city garden waje ne mai kyau kuma babu hayaniya se kukan tsuntsaye ga kuma flowers masu kyaun gaske anyi arranging kujeru kowane table kujeru hudu na zagaye dashi an rufesu da kyalle masu kyau colors daban2 wato multi color kenan haka nan bangaren da amarya zata zauna tare da kawayenta ma multi color ne abun de sai Wanda ya gani.
   Idan ka duba kujerun sun cika da jamaa dangin mr President yan uwan marigayiya matarsa zainab dangin Maman shuairat da kuma dangin babanta ko ina dai manyan mata ne ansha ado na kece raini ga yan Adamawa kyawawa sun kara haska wajen both dangin ango da na amarya duka fulanin Adamawa ne idan kaga mummuna dai yan ganyan sodi ne😜😜 a dayan bangaren kuwa invited guest ne ga matan ~gidan gyara~ ~Nisaul jannah~ ~professional writters~ ~Hausa novel grp~ ~dangin juna~ ~qasaitattun mata~ da dai sauransu.idan ka duba wani bangaren kuwa *adda bena*CE da *m jabo* *pherty* *Maman shakur* *khaleesat haidar* *miemie bee* *Ummi Aysha* da sauran online writers nima a can na xauna ina watsa rubutu na. Yan gidan TV radio da news papers duk sun hallara ana daukan live a kowane tashar TV idan ka kunna xaa hasko maka walimar Aysha (shuairat) bello matar mr President😊, nayi rubutu har na gaji sai na taba miemie nace "amarya baxata zo bane" ta watsa min harara tace "tsiyata dake kenan rashin hakuri"😏 daga nan naja bakina nayi shuru wani dadaddan qamshi ne ya buga hanci na ina daga kai na hango shuairat tare da tawagarta😱😱😱
Mutuwar xaune nayi *halamcy* CE ta saka hannu ta tare min baki na Wanda saura kiris ya fada kasa...hmmm kawai na ajiye Biro na nace baxan iya siffanta irin wannan kyawun bah sai Ku jira *afrah* idan ta gama da jumaiya se ta siffanta muku kyaun da shuairat tayi.😊😊😊Amarya da kawayenta Suka sauna a filin da aka tanada musu nan kuwa yan jarida Suka fara daukansu hoto wal...wal hasken kamera kawai nake gani sai kuma aka bude taro da adua nan malama Maryam ta fara gabatar da waazi akan hakkin aure da rayuwar aure a musulunci.haka aka cigaba da taron masu video recording nayi masu daukan hoto nayi ga yan jarida iri2 ga  reportrs din tambari magazine ga JF ma sun tura Mahmud Wanda kansa  me kallon kasa yana jin wani radadi har ckn ransa .Karfe 6pm aka raba souvenirs iri2 har da kayan makeups a ciki abinci kuwa dama table by table aka raba daga nan akayi adua sannan kowa ya fara shirin komawa gida a yayinda wasu sukaje daukan pix tare da amarya dakyar ta samu hanya wannan ma don bodyguards ne.



😘😘😘
[2/21, 2:39 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*44*
By *Reefat yahya*

Yau aka daura auren Ayshat bello maiha tare da Alh Suleiman Muhammad mayo ( PhD) akan sadaki naira 100k jamaa da dama Suka halarci daurin auren manyan kusocin gwamnati tare da manyan sarakuna ta kasashe daban-daban ga mutane dai talaka da masu arziki , yan jarida suna nan birjik an daura aure lfy aka watse daga nan villa Suka wuce akayi hadadden reception kowa ya ci ya sha sannan aka watse ango de furkarsa na dauke da murmushi .

A can bangaren amarya kuwa ta sha kwalliya ckn wata hadaddiyar shadda masu kyau da tsada ga gwalagwalai carkaf a kunne da wuyarta tayi kyau tmkar a saceta a gudu tana zaune a bangaren shukrah tare da kawayenta.ta buga wani uban tagumi shukrah CE ta shugo tare da sallama 
"Amarya bakya laifi ko kin kashe sultan lolz"

"Hmmm...lallai mah rufa min asiri kan a jiki"
"Tashi muje an tura camera man yazo ana ta daukar hotuna"

"Kuje Ku dauka nikam na gaji"

"Haba ranki shi Dade, kinsan gobe war haka fah ganinki sai da ticket ki tashi muje muyi last card pls"

"Mttsww...me wani na cewa last card sai kace mutuwa zanyi"
Su Ummi suna mata dariya haka Suka fita akayi ta daukan hotuna da yan uwa da abokan arziki.

Tun Karfe 5 shuairat ta shiga wanka tare da anti mairo har magrib suna ckn bayi shiru kawai kake ji na so zuwa in gano me ya sukeyi acan Amma ba dama haka na hakura na zuba ido.by 7 Suka fito amarya sai qamshi take tmkar anyi barin turare dakin mama Suka wuce ta saka wasu atamfa ya'r super mai uban kyau da tsada batayi wani makeup bah dakin babanta aka kaita ya mata nasiha sosai tAna kuka Suka koma dakin mama a can aka kawo mata dafaffiyar kaza ta sha hadi sosai dole ta cinyeshi Tass sabida anti mairo ta sata a gaba, mama CE ta shigo haj mairo tace 
"Mutuniyar idan akwai abunda zaki gaya mata kiyi sauri cos ance by 8 zamu wuce da ita gidan mijin nata"

Mama ta sunkuyar da kai tace "ba komi duk abunda ya dace ki sanar da ita " daga nan ta tashi ta tafi haj mairo ta kara fesheta da turare sannan Suka wuce bangaren yayanta baya nan Mr president ya kirashi haka suka zauna ckn shiri by8 Suka ji tsayuwar motoci . duk yanda shuairat taso ganin mamanta don suyi sallama abun ya gagara firr mama taki fitowa haka Suka hakura yan raka amarya Suka shirya Suka fito shuairat kam se kuka take anti mairo na bata hakuri daga nan akayi mota da ita.
Motocine masu kyau se sheki sukeyi gasu nan birjik sai Wanda ka zaba daga nan Suka dau hanyar villa.
Bayan sun iso gidan aka wuce wani dankareren building upstairs ne mai kyau gaskiya bazan bata lokacina ina zayyana muku tsaruwar ginin bah kawai de kunsan gdn shugabankasa kam😀😀karshen kyawu kenan. Yan rakiyar amarya sun zaga building din ko ina suna ta yabawa , an nuna musu dakunan daga nan anti mairo ta sallami kowa ya rage daga ita sai kawayen amarya da wata yar mama se kuma kanwar baban su shuairat. Dangin ango sun shigo wasu mata kyawawa su 6 Suka shigo musu maraba tare da ajiye musu abinci mai rai da lfy sannan Suka tafi. Kawayenta daki daban aka ware musu ita amaryar kuwa da anti mairo zata kwana, bayan sunyi shirin kwanciya Karfe 11pm anti mairo ta ajiye shuairat ta fara mata nasiha..

"Baby kiyi hkri bansan ko kina son mijinki koma yaya ne ki daure ki fara sonshi ki koyawa kanki yanda zaki so shi , haka nan shima ki koya masa sonki ki dasa sonki a ckn zuciyarsa Ku zauna lfy.yi nayi bari na bari kuyi hkri da juna wannan shine zaman aure, bauta ne ya kawoki ba wani Abu ba aljannarki kika zo nema kiyi kokari ki kasance mai faranta ran mijinki.ki zauna lfy da kowa ki mutunta kowa nashi ki daraja iyayensa ki girmamasu ki kula da dukiyarsa da ya'yansa, fada da umaima ba naki bane ki kame girmanki kada raini ya shiga tsakaninku...haka dai anti mairo ta cigaba da mata nasiha masu ratsa jiki daga karshe Suka kwanta.


😍😍😍lov u all
[2/21, 2:39 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*45*
By *Reefat yahya*


Da misalin Karfe 9 na safe masu aiki sun gama gyara komai na gidan sai qamshin air freshener ke tashi an jera abinci kala-kala a dinning table.building din dakuna 4 a sama da babban falo a tsakiya da dinning table mai kujeru6 sai kuma dakuna 3 a kasa da kitchen da kuma dinning mai kujeru 10 ga wani tangamemen  falo da kujeru duma2 har set 4 kai kayan more rayuwa dai an narkasu a wanga falon.
  Shuairat tayi wanka tayi ado ckn wani uban leshi Wanda zai kai 100k golden n lemon green da milk color ta saka yan kunnen gold mai tsadan gaske tayi kyau sosai tana tsaye a gaban dressing mirror tana kallon kanta yanda ta chanza tayi kyau sosai,  anti mairo ta shigo dakin itama ckn uban kwalliyarta tana murmushi tace
"Wow my baby is looking gorgeous kinyi kyau sosai I wish Mr president zai ganki yanzun nan"

"Tnx anti" ta fada tana murmushi anti mairo ta rike hannunta Suka bar dakin sai kuma ga sauran yan uwan nata sun fito kowacce ckn ado na alfarma tare da kawayenta anti mairo na gaba tana rike da hannun shuairat Suka fito sai zuba gaisuwa ake musu wani Dan building Suka nufa me karen kyau .
   Sun shigo tare da sallama wani makeken falo ne a cike makil da jamaa mata zalla gasu nan birjik kowacce tasha ado tana ji da kanta ckn faraa aka karbesu daga nan aka fara gaisuwa.

Bayan kowa ya nitsu anti mairo ta fara magana
"Ga ya'rmu nan mun kawo muku sai Ku riketa da amana idan tayi abunda ba dai2 bah a nusar da ita ko kuma a sanar damu saboda karama ce , Allah ya basu zaman lfy da zuria dayyiba"

Gaba daya falon aka amsa da ameen .sai ynxu na lura da wata dattijuwa mai kyaun gaske kamarsu daya da Mr president tunda aka shigo da shuairat se murmushi take a hnkli ta fara magana

"Insha Allahu zamu riketa hannu2 Allah ya basu zaman lfy da ya'ya nagari"
"Ameen" aka sake amsawa daga nan aka kai shuairat kusa da wannan matar Suka gaisa ta rike hannun shuairat cike da so tace  "ya'ta Allah ya miki albarka kiyi hkri nasan zaku zauna lfy insha Allah "

Bayan wani lokaci kowacce tana Dan tufa albarkacin bakinta tare da musu fatan alheri daga nan aka fara daukansu hotuna sai kuma kyaututtukan da shuairat ta samu na ban mamaki wato turamen zani ne da lesuna sai kuma kdade mai dumbin yawa kai sunga abun arzki kam daga karshe Suka koma bangaren ta.kowa yana yabawa dangin Mr president da irin karamcin su.

Wani bodyguard ne ya shigo ya sanar dasu cewa Mr president na son ganin shuairat tayi shiru bata CE komai bah anti mairo CE ta jawota xuwa daki ta kara fesa mata turarurruka iri2 sannan ta kara powder da lipstick tace mata
"Saura kije kina wani nokewa , feel free mijinki ne"
 Murmushi kawai shuairat tayi tana mamaki halaye irin na anti mairo daga nan ta sauka zuwa kasa inda bodyguard din yake jiranta daga nan Suka wuce ckn mota ya kaita bangaren Mr president.
Sau daya ta taba zuwa amma yau taga komai ya canza mata an sake fenti da furniture's da komi a bakin kofa bodyguard din ya tsaya ta karasa.
Bata sameshi a falon farko bah don haka ta wuce personal falonsa ta shigo tare da sallama yana zaune ckn manyan kaya yayi kyau sosai ko don ta kwana2 bata ganshi bane oho ya amsa ba tare da ya daga fuskarsa bah yana danna waya da alama wani yake son kira ta nemi waje ta zauna suna fuskantar juna. Shiru sukayi sai kuma ta tuna cewa ynxu itace kasa dashi nan kuwa a hnkli ta furta

"Ina kwana ur xcelency"
Wani kayataccen murmushi ya sakar mata duk da cewa baya kallonta sannan ya amsa ckn wani salon ji da kai

"My first lady kin tashi lfy"
"Lfy alhamdulillh"
"Hw was ur nite ya bakunta"

"Lfy kalau"
"Daz grt, dama na kiraki ne ina son jin nawa zaa sallami frenz naki"
Shiru kake ji ta rasa me zata gaya masa yaji shirun yayi yawa don haka ya daga ido 😳😳😳 masha Allah haka ya furta a ckn zuciyarsa dama yarinyar nan haka take da kyau? Wow..she luks soo...btiful" carab Suka hada ido a dai dai lokacinda shuairat ta daga kanta , kowannensu yayi saurin dauke kai zuciyoyinsu ne ke harbawa.Mr president ya daure yace

"Kinyi shiru"
"Uhmm...gskiya nima bansani bah just give dem...

"No first lady! I hate dat word "bansani bah" ki gayamin pls"
Nan ma tayi shiru sai kuma ta tashi ya bita da ido har ta kai bakin kofa yace 
"Ina zakije kuma muna magana"

"Uhm...zanje gun anti mairo ne"

"Zakije ki tambayeta nawa ya dace ?
Murmushi yayi yana tunani shi kadai cewa lallai akwai yaranta a tattare da ita
"Ok dawo ki zauna tunda baki sani bah lemmi tink on my own" ba gardama ta koma ta zauna yana danna waya can ya kara a kunne yace 
"Ka tura sakon da na baka jiya ? 
Ok yes ka hada duka ka basu a ckn gida "
Daga nan ya kashe wayar ya maida kallonsa gareta sun kurawa juna ido can shuairat ta kauda fuskarta yana Murmushi sannan ya fara magana

"Aysha ynxu idan aka baki mukamin first lady haka zaki dinga yi?
Ta daga kai ckn rashin fahimta yace 

"Yes! Wat I min is dai komi sai kin tambaya ? Bazakiyi on ur own bah?
Ta zumbura baki tace 

"Ni...ni nace a bani first lady ne dama"
A hnkli ya taka xuwa gabanta ya sunguna idanunsa a kanta suna fuskntar juna shuairat ta sunkuyar da kai tana wasa da warwaronta yasa hannu ya daga habarta Suka kurawa juna ido yace 

" ke matata CE dole zaki koyi yanda zaki gudanar da wasu harkokin on ur own , u have to fight Aysha"
Bash ne tare da wani bodyguard Suka shigo tare da sallama ganin halin da Suka tarar da ogan nasu a ciki ne yasa Suka bar wajen shuairat kuwa kunyane  ya kamata haka nan Mr president ma nan da nan ya tashi ya koma kujerar da yake da ya zauna ya dannawa bash kira a waya Suka shigo Suka sanar dashi cewa yayi baki daga England nan ya tashi Suka fita tare shuairat kuwa bodyguard Suka rakata ta koma bangaren ta.



😍😍😍👍🏼😘lov u all
[2/21, 2:39 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*46*
By *Reefat yahya*


Ta shigo bangarenta kawayenta suna mata tsiya Hafsat tace 
"Ohhh shuairat an kasa hakuri a jira mu koma mana"
Ummi tayi dariya tace 

"Gane min hanya dai da ana nokewa wai tsoho zaa aura ba zancen love gashi nan tun baaje ko ina bah an fara lumewa"
Suka fashe da dariya Suka shewa anti mairo ta shigo tana dariya tace 

"Rabu dasu baby nah love kam kowa ma yana yi sai Wanda bai samu bah , Ku kuwa Ku tashi Ku tattara mu bar musu gida ynxun nan"

Suna dariya se kuma Suka hau godiya abun arzikin da Mr president ya aiko musu kowacce an bata kaya lace super da kuma Holland se kudi 120k shuairat kam mamaki ne karara a fuskarta sai kuma ta share zancen haka nan su haj mairo ma an basu kudade Masu yawa daga nan ta sake Jan kunnen shuairat akan zaman da zatayi a gidan tare da koya mata wasu dabarun sarrafa miji Wanda ba sai na fada bah😜 nan sukayi sallama shuairat ta fara hawaye haj mairo tace kul..karki bata kwalliyanki daga nan motoci Suka kwace su sai gida aka bar amarya daga ita sai halayenta sai kuma masu aiki.
Sama ta haura sai ynxu ta samu damar karyawa tea ta hada sannan ta Debi chips kadan da kwai ta zauna ta cinye tas sannan ta dawo falo ta kunna TV MBC ta kama tana kallon film din "triple X" yan uwan Mr president ne Suka shigo sun Dan taba hira daga nan Suka shaida mata cewa yau zasu wuce Adamawa wasu kuma Kano wasu kd da kuma Lagos, cin-cin doughnut da cake ta diba musu da turarurruka masu yawa ta basu suna godiya Suka tafi. Haka masu aikin Suka shigo Suka gabatar da Kansu nan ma ta kawo  musu abubuwa iri2 suna yaba mata Suka koma bakin aikinsu. 

A can bangaren Mr president kuwa wasu turawa ne Suka zo tayashi murnan auren da yayi maza 3 da mata 2 dukkansu manyan mutane ne masu fada a ji a can kasar England daga fadar sarauniya Suka zo don haka Suka nemi ganin amaryar tasa Mr president ya daga waya bayan ya Dan fita daga dakin da aka sauke bakin nasa layin shuairat ya kira ringing 2 ta daga 
"Hello ur xcelency"
Wani yarr...yaji a jikinsa dakyar ya saita kansa yace

"Ki shirya baki nayi kuma turawa ne suna son ganinki"

"Eyya...Mr president y not su bari xuwa dare Allah na gaji ynxu bacci zanyi"
Tayi maganan ne ckn wani salon shagwaba murmushi yayi shi kadai yasan ma'anar yace 

"Ok sorry ki huta zuwa daren sai ki shirya koh"

"Ok tnk u my dear"
Nan ta kashe wayar ya tsaya Jim...tmkar mai tuna wani Abu sai kuma ya nanata kalamanta na karshe "tnk u my dear" nan ya sake yin murmushi haka nan tun jiya yake jin kansa ckn wani nishadi daga nan ya koma gun bakin nasa ya basu hakuri cewa amaryar tasa tana tare da baki sai zuwa dare zasu gan ta haka Suka cigaba da hirarsu.
Bash da john suna zaune a waje John ya juya ya kalli bash yace 
"Aboki Mr president fah ya fada tarkon son yarinyar nan ba kadan bah"

"Me ka gani john?

"Haba ...kana ganin yanda muka samesu dazun"

"Hmmm...next tym zamu hana kowa zuwa bangaren Mr president sai da izininsa cos yanzu yana da iyali bai dace ana shiga anyhw bah"

"Yes haka zamu yi"
Daga nan sukayi shiru shi kansa bash yana mamakin kalan soyayyar kanwar tasa da Mr president hmmm...mata kenan zasu maida tsoho yaro.

Shuairat kuwa tana zaune a falo har bacci yayi awon gaba da ita se bayan azahar ta farka tayi sallah sannan ta fada wanka, wani material pitch color ta saka dinkin buba da zani ta saka danyar gwal mai kyau ta fesa turare se qamshi ke tashi. Dinning ta wuce masu aiki suna tsaye a gefe aka zuba mata rice n chicken ta fara ci a hnkli tmkar bata so sai wani yauki take. wata mata ta shigo tare da wani Dan yaro nan kuwa ta gane sultan ne nan ta sake fuska tana faraa sun karasa falon ta musu tayin abinci matar ta jawo kujera ta zauna shuairat ta rike hannun yaron tace 

"Boy zo mu ci tare" ba musu sultan ya karasa gunta ta daurashi a kafa nan ta fara bashi a baki suna ci suna hira masu aiki kam se yaba halayenta suke nan da nan anty khady ma taji son shuairat ya shige ta don ba haka tayi tsammanin ganinta bah ta dauka shuairat irin matan nan ne masu girman kai da wulakanta mutane.sunyi hira sosai bayan anty khady ta damka mata amanar sultan nan kuwa ta karba ckn jin dadi Suka rabu akan anti kadi xata koma yau.

Haka shuairat ta kasance tare da sultan tana biye masa duk abunda yake so shi zatayi sunyi game sunyi kallo sunyi karatu haka Suka kasance har lokacin sallan la'asar nan ma tare sukayi sallar shuairat ta masa wanka ta canza masa kaya sannan Suka tafi bangaren momsi( Maman Mr president )

Love u alll😘😘
[2/21, 2:39 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*47*
By *Reefat yahya*


Sun shigo falon tana tare da wasu mata su 2 nan shuairat ta gaishe su sannan ta zauna a gefe momsi kuwa wani irin dadi taji don anty khady ta shaida mata komai fuskarta dauke da murmushi ta fara Jan shuairat da hira tana tambayarta ko ta taba zuwan mayo belwa can Adamawa haka dai Suka cigaba da hira shuairat ta sake kadan suna hira sultan kuwa yana makale da ita, aka kawo musu fruits da drinks dakyar shuairat ta dau apple kwaya1 tana ci wannan ma saida momsi ta bata rai ne ta nuna mata cewa ta dauka  nan gidan su ne ta daina jin kunya ta sake jikinta nan ne shuairat take tmbayar ina umaima aikuwa momsi ta zayyana mata daga biri har wutsiya sannan ta Dora da nasiha kan cewa tayi hkri da halayen da zata fuskanta gun umaimA haka dai Suka cigaba da hira har magrib sannan ta koma bangaren ta tare da sultan , bayan sunyi magrib da isha ta dibawa sultan abinci yaci ya koshi ta kunna masa cartoon yana kallo har yayi bacci nan ta daukesa ta kaisa dakin barcinta daga nan ta fada wanka.tana fitowa ta tsara wani uban kwalliya sannan ta fito da wani hadaddiyar dinner gown silver da duwatsu a jiki sai shinning suke ta sanya rigar mai dogon hannu pencil hand ya dame hannunta haka nan rigar dai-dai da jikinta ta saka wasu English diamond mai uban kyau ta daura wani red net daurin step har 6 tayi kyau sosai ta saka takalmin Vinci red color ta rike clutch purse din shima red ga red lipstick tayi kyau sosai woow....ta fesa turaren laylatul sahr da musk- almudhakkr se kuma far away , bleu feeling, diable bleue, to nyt , mekako Miami, Cuba , touch me da kuma esabella Curie.☺☺☺ turare 10...hmmmm qamshi kam baa magana ita kanta tasan ta hadu sosai.wayar intercom na dakin ne ya fara ruri ta daga wata mai aiki CE take sanar da ita cewa Mr president ya turo mota yana bukatar ganinta nan ta ajiye wayar ta kurawa fyskarta ido a ckn mirror tace 

"Wow...yarinya kinyi kyau but hakan ya dace ta fita ne ko ta yafa gyale? Ahhh....turawa ne bata son su mata kallon bakauyiya don haka red net din ta dauko wani ta yafa sannan ta daurashi ta baya tayi kyau sosai😘😘😘😘.
A hnkli take takawa har ta fito falon ba kowa duk masu aikin sun koma bangaren su sai masu gadi a waje ta Tarar da bodyguard din 😳😳😳gaba daya Suka zuba mata ido dakyar ya saita kansa ya bude mata gidan baya ta shige daga nan ya ja motar .

Bangaren saukan baki sukayi parking ya bude mata kofa ta fito tana takun kasaita ta hadu da yayanta yana fitowa murmushi ta sakar masa sannan ta wuce ya tsaya galala yana kallonta har ta bace masa da gani yana tsaye yana mamaki shi kadai. Suna zaune a dinning area da alama ita ake jira Mr president ne yake fuskantar kofa tana shigowa ya kasa dauke idonsa a kanta tmkar a mafarki haka ya ganta kurrr ya ajiye ido ya kasa motsi tana murmushi ta karasa kusa dashi ta mika masa hannu nan ya tashi yana rike da hannunta gaba dayawa turawan sun shagala da kallonta basu taba ganin bakin fata kyakkyawa irin shuairat bah.Mr President ne ya katse musu tunani ta hanyar cewa

"Pls meet my wife mrs Suleiman"
Murmushi shuairat ta sakan musu sannan tace 

"Hello everyone" tare da mikawa matan hannu sun gaisa ckn faraa sannan Mr president ya jawo kujera kusa da nasa nan ta zauna tare da cewa 

"Tnk u Darling"
Ckn wani tsiga tana fari da ido Mr president kam se kallonta yake tmkar wata sabuwar hallita nan shuairat ta fara musu barka da xuwa tare da basu hakurin rashin xuwanta akan lokaci, haka nan ta sace zukatansu hira sosai sukeyi ckn harshen turanci Mr president in banda murmushi babu abunda yake shuairat ta bashi mamaki sosai nan da nan Suka fito da wayoyinsu aka fara daukan selfie an dauketa tare da Mr president ma sunyi kyau sosai nan aka fara turawa a instagram da Facebook ana taya Mr president murna. Daga karshe Suka gabatar da kyaututtukansu diamonds golds da dalolin amurka shuairat de tasha kyaututtuka da dama har wajen 12 sannan kowannensu ya koma masaukin sa shuairat ta tashi zata tafi Mr president ya rike hannunta sai kuma ya rungumeta gam a jiki, mutuwar tsaye tayi ta kasa motsawa Sun share minti 3 ckn wannan hali dai2 nan john ya shigo don kulle kofa aikuwa a 360 yabar bangaren ya tsaya a waje ya rike kai yana maida numfashi . Mr president ya motsa bakinsa a hnkli yace

"Allah ya miki albarka nagode sosai ki fitar dani kunya tnx much Allah ya biyaki"

"Amee..men" dakyar ta amsa daga nan ya sake ta yace 

"Muje ki kwanta dare yayi"
Nan ya rike hannunta Suka fita gidan shiru sai securities ke kaiwa da komowa sunata kallon Mr president hannunsa tsarke ckn na matarsa suna taku a hnkli farinwata da hasken fitillun gidan sun haska koina , haka Suka cigaba da tafiya har xuwa bangaren shuairat aka bude musu kofa a tuaninta nan zai dakata da rakiyar se kuma taga ya biyota har dakin bacci ya bude kofar ga mamakinsa sultan ya gani kwance yana sharar baccinsa ya juya Suka hada ido tayi murmushi nan ya sake mata hannu ya koma kusa da sultan ya shafa kansa tare da tofa masa aduoi daga nan ya tashi yace

"Nagode sosai gud nite"

"Nite" ta fada a hnkli daga nan ya sa kai ya tafi tare da rufe musu kofar yana tafiya yana murmushi shi kadai yasan abunda yake ji.


😘😘😘😘ku biyoni kusha labari
*Reefat* ce
[2/21, 2:39 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*48*
By *Reefat yahya*


Shuairat ta gama shirin kwanciya tsaf tayi aduoin bacci ta kwanta sai kuma abubuwan da Suka faru tsakaninta da Mr president ne yake yawo a kwakwalwarta haka nan ta tsinci kanta ckn wani farin ciki he is so calm bashi da matsala tabbas idan haka yake toh lallai zasu zauna lfy.haka dai ta cigaba da sake sakenta har bacci yayi awon gaba da ita.
   A bangaren Mr president ma hakan ta kasance Sam ..ya kasa yin bacci fuskar shuairat yake gani idan ya rufe idanunsa dama matarsa wayayyiya ce? Daman haka take da kyau? She is so cute n presentable.tabbas yayi dace kuma yaji dadin ganin sultan a dakinta da alama tana son yara kuma xata rike masa sultan da amana , haka nan ta faranta masa rai haka ya cigaba da sake sake har bacci ya daukesa ba tare da ya sani bah.


   Asuban fari shuairat ta tashi tayi wanka tare da daura alwala tayi nafilfilun ta sannan tayi sallar asuba tayi lazimi bayan ta gama tayi adua ta shafa sannan ta koma bakin gado ta zauna a hnkli ta fara shafa kan sultan bayan wani Dan lookaci ya bude ido a hnkli tace 

"Boy tashi kayi sallah koh"
Ckn muryan bacci yace

"Um um anty nikam ki bari ba ynxu bah"

"Haba my boy jiya fa cemin kayi kana son ka shiga aljannah ka tuna?
Kai ya gyada mata tayi murmushi tace 

"Good! Duk Wanda baya sallah akan lokaci bazai shiga aljannah bah, oya get up"
Nan kuwa sultan ya tashi ya shige toilet yayi alwala ya fito ta shinfida masa sallaya ya tada sallah tana zaune tana kula da yanda yake sallar a natse lallai ko ya iya batayi mmki bah sabida a hiran da sukayi ya gaya mata akwai malamin da yake xuwa har gida yana karantar dashi.bayan ya idar da sallah nan ya koma gado ya kwanta shuairat tace 

"Boy ba gaisuwa ne?
Murmushi yayi yace 

"Morning anty!
Ta shafa kansa tace 

"Morning my boy! Ynxu se mu dau Qur'an mu karanta koh"

"Anty bacci nake ji kuma kinsan anjima zanje skul "

"I knw my boy! But pls mu karanta koda 5pages ne se mu koma bacci koh

"No! 5pages yayi yawa"

"Ok 3pages koh"
Dakyar ta lallabashi ya karanta pages 2 na suratul baqarah sannan ya kwanta , ita kuma ta cigaba da karatu har 6:30 sannan ta wuce falo nan ta hadu da masu aiki suna xuba gaisuwa ta bukaci su kawo mata kayan makarantar sultan babu bata lkci kuwa aka kawo duk abunda zai bukata ta bada umarnin a shirya masa kayan kari sannan ta koma daki.
Karfe 7am masu aikin sultan Suka nemi izinin ganin sultan saboda xaa mishi wanka ya tafi skul, shuairat ta hana.ita kanta ta masa wanka ta shirya sa ckn kayan makaranta ya fito fes dashi ta fesa masa turare itama ta sha wanka tayi ado ckn atamfar super masu kyau ta ajiye dankwali ga gashin kanta ya kwanta a kafada tayi kyau sosai tana rike da hannun sultan Suka fito falo masu aikin Suka kura musu ido tabbas sunyi kyau sosai.
         Dinning area Suka wuce a nan ta zuba masa abinci yaci sosai tana xuba mishi hira ckn raha tana biye wa duk shirmensa har ya gama aka kai jaka da lunchbox nasa a mota.an bude motar ana jiran fitowarsa shuairat ta rike hannunsa tace 

"Muje ka gaida dady koh"
Ba musu Suka wuce bangaren Mr president masu aikin Suka xuba musu ido ckn shaawar ganin sabon chanjin rayuwa da sultan ya samu.a hnkli ta tura kofar dakin da take tunanin dakin barcinsa ne sabida basu tarar dashi a falo bah, ta shigo tare da sallama yana zaune da Qur'an a hannunsa bayan ya rufe qur'anin ya amsa sallamar nan Suka hada ido shuairat tayi saurin dauke kanta

"Good morning ur Excellency"

"Morning hw was ur nite dafatan kun tashi lfy mom sultan"
Wani kayataccen murmushn jin dadi tayi saboda sunan da ya kirata dashi

" lfy alhamdulillh dady sultan hop kaima haka"
"Alhamdulillh"

"Dady good morning"
Sultan ya furta bayan ya karasa kusa da mahaifin nasa

"Morning my boy "
"Laa..dady kaga anty ma boy take kirana fah

Murmushin jin dadi yayi yana kallon shuairat wacce kanta ke kallon kasa

"Dady kaga yau na karanta Qur'an har 2pages ni da anty

"Wow...am so happy my boy kip it up koh Allah ya muku albarka da kai da antyn naka "
"Ameen dady"
Shuairat ce ta katse hiran nasu ta hanyar cewa

"My boy kamanta mota na jiranka kar kayi latti let's go"
Ya tashi tsaye yace

"Bye dad na tafi"
"Ok takkia ayi karatu banda wasa koh"

"Ok dad zanyi cos anty tace idan ina karatu sosai zata siyamin yacht kuma zan shiga aljannah"
Dariya sosai Mr president yayi yana kallon shuairat gwanin birgewa yace 
"Ok a dawo lfy"
Daga nan Suka fita Suka bar dakin ya bisu da kallon shaawa shi ganin shuairat yake tmkar ita ta haifi sultan nan da nan wani farin ciki ya ziyarci xuciyarsa ya manta da duk wani bakin ckn da yake cki a da tabbas maganar dadynsa gaskiya ne da yace masa shuairat zata zame musu alkairi a rayuwa zata kawo musu farin ciki , gashi tun baaje ko ina bah ya tsinci kansa ckn farin cki Mara misali.


Ku biyoni love u my fans masu turamin mssg ta private tnx alot I love u all😘😘😘
[2/21, 2:39 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*49*
By *Reefat yahya*


Shuairat ta raka sultan a bakin mota suna dagawa juna hannu har ya bace mata da gani sannan ta wuce bangaren momsi a falo ta sameta tana xaune da carbi a hannu ta karasa tare da sallama sun gaisa ckn girmamawa ta amsa tana mai faraa daga nan ta bukaci shuairat ta jira daddy ya fito su gaisa bayan yan mintuna Alh Mohammed ya shigo falon fuskarsa dauke da murmushi Suka gaisa da shuairat daga nan ta musu sallama ta koma bangarenta daki ta shige ta haye gado tayi kwanciyarta wayarta ce ta hau ruri layin anti mairo ta gani nan ta daga 

"Ina kwana anty"
"Amarsu ta ango an tashi lfy ya gida ya kadaici"

"Alhamdulillh anty dafatan kuna lfy"

"Lfy me kikeyi haka"
"Wllhi ynxu na dawo daga rakiyar sultan ya tafi skul shine nace bari na samu bacci kadan"

"Kaji min yarinya da shirme..sultan kika aura ko ubansa? Bazaki je ki duba lfyar mijinki bah se dansa?

"Anti naje mun gaisa fah dazu"

"Haba baby..ynxu duk abubuwan da na gaya miki sun tashi a banza kenan? Mijinki ne bazaki je ki kula dashi bah ki tabbatar yaci abinci yayi shirin office sannan ki mike a gado wai bacci zakiyi ? Anya zaki sinana abun kirki kenan..

"Eyya fah anty..
Ta fada ckn shagwaba

"Eyya me? Ki tashi maza ynxun nan kije ki kula da mijinki ki tabbatar ya shirya ya fita office kan ki dawo kiyi baccin..aikin me zakiyi girki ko shara? Eyye..
Haka dai anti mairo ta dinga balbale shuairat da balai ba shiri ta tashi bayan sunyi sallama ta sake fesa turare ta kara makeup kamar yanda Antin ta umarceta ta tsaya a gaban dressing mirror ita kunyan masu aikin gidan take ji , ya zaayi ta dinga shiga tana fita a bangaren Mr president ? Ya ilahi ya zatayi?
      Haka ta daure ta fito bayan ta yafa veil nata se uban kamshi ke tashi ta fito tana taku dai2 har ta fito nan bodyguards Suka bude mata mota duk da cewa ba wani nisa bane Amma abunka da manya haka aka ajiyeta a bangaren Mr president ta fito bayan an bude mata kofa ana xuba gaisuwa tana amsawa ckn sakin fuska nan Suka gaisa da yayanta shima se kallonta yake daga nan ta wuce ciki .baya falonsa don haka dakin bacci ta wuce direct ta kwankwasa tare da sallama ta tura kofar carab Suka hada ido yana tsaye ya gama shiryawa yana rike da turare a hnkli ta karasa tare da karban turaren a hNnunsa ba tare da tayi magana ba shi kuma ya bita da ido ta fesa masa koina ckn kasaita da wani irin salo, Mr president de ya xuba mata ido kawai bai CE ko uffan bah bayan ta gama ta ajiye ta sake daukan wani haka ta fesa masa turare har kala5 a hnkli ta daga kanta Suka hada ido ckn jin kunya tace

"Sorry ur exceelency na barka kai kadai "

Murmushi ya sakar mata daga nan ta juya ta dauko hulan da ta gani a kan gado ta saka masa a kai sai kuma tace 

"Muje kaci abinci koh"
Falo Suka fito a Jere har dinning area ga abinci nan kala2 a Jere ba abinda babu ta tambayeshi abunda yake bukata yam freets ne da sausage rolls yaci sannan ya dora da coffee .ita kam bata wani sake sosai ba kunyarsa take ji chips da sauce din kwai take ci a hnkli tmkar bata so yana kurba coffee yana kallonta tana da natsuwa sosai tana yin komai ckn tsari babu rawar kai, samm...bai taba tunanin cewa haka halinta yake bah yana ganintane a matsayin futsararriya wacce zata...

"Mr president yaushe umaima xata dawo"
Muryar shuairat CE ya katse masa tunani har ga Allah shi ya manta da xancen wata umaima 

"Ohh..umaima! I rily don't knw gskiya cos mun kwana2 bamuyi communicating bah"

"Haba dadyn sultan.. Me yasa?

"Mom sultan ni na haifi umaima at least I deserved som respect amma ta raina ni batajin magana ta ko kadan"

"C'mon dad sultan she is a kid lallabata zakayi ka...

"Aysha! Let's not talk abt dis ok!

"Ok sir! Am sorry kayi hakuri na shiga affairs din familynka koh...sorry"
  Nan ta ajiye fork din hannunta ta tashi idanunta sun cika da kwallah tayi hanyar kofa ba shiri mr president yabi bayanta baiyi wata2 bah ya jawota ta fada jikinsa nan ta fara kuka a hnkli ya rungumeta yana shafa bayanta alamar rarrashi sai ajiyar xuciya take a hnkli ya furta 

"Am sorry mom sultan I din min 2hurt u..
  Ta cigaba da kukanta bata saurareshi bah haka Suka kasance ya sake cewa 

"Pls mana Aysha wadu munyal( yi hakuri ..da yarensu😜) am sorry ok..
Ta dan sagaita kukan yana murmushi yNa shafa kanta dankwalinta ne ya zame zai fadi Mr president yayi saurin rikewa ..wow...kitsonta ne ya bayyana kanana masu kyau ga gashin ya bazu a baya da kafadanta ya kurawa gashin ido nan ta daga kanta da yake kwance a kirjinsa Suka kurawa juna ido , ita ta fara dauke nata shi kuwa murmushi yayi 

"Ya'r shagwabar baba da mama ..am sorry koh"
Kai ta sunkuya ckn jin kunya sannan ta xumbura baki tana magana ckn shagwaba tayi rau-rau da ido tace

"Ba Kaine kamin tsawa bah"
Ya rike mata hannu yana murmushi yace 

"Am sorry my first lady nayi laifi a yafe min ok!
Bash ne ya tura kofar tare da sallama carab Suka hada ido da shuairat yayi saurin sunkuyar da kai ya gabatar da gaisuwarsa sannan ya shaidawa Mr president cewa daddy na bukatar ganinsu da shuairat nan Suka amsa da cewa suna nan tafe , daga nan bash ya juya ya bar falon.
   Shuairat ta sunkuyar da kai ckn jin kunya tace 

"Nikam bazan kara xuwa side dinka bah kullum securities suyi ta kallona zasu ce bani da kunya"
Yana murza yatsunta a hnkli yana murmushi yace 

"Toh me ne? Ba matata bace?
Ta gyara dankwalinta Suka fito ajere bodyguards Suka diban gaisuwa gun  Mr president yana amsawa ckn sakin fuska da faraar da basu taba ganinsa dashi bah...

Ku biyoni😘😘😘
[2/21, 2:39 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*50*
By *Reefat yahya*


An kawo mota a gaban Mr president ya daga musu hannu alamar cewa da kafa zasu taka haka ko akayi suna tfya suna hira sama sama da shuairat ita kanta tana mamakin halayen Mr president da tana ganin tmkar idan sunyi aure zai wulakanta ta Amma sai taga sabanin hakan.
  John ya bude baki yana kallonsu bash ya juya ya dafe kafadarsa yace
  "Me haka john"
  "Bash am rily happy 4mr president, ban taba ganin irin wannan murmushn a fuskarsa ba tun bayan rasuwar matarsa sai yau.lallai yana bala'in son wannan yarinyar"

Murmushn jin dadine ya bayyana a fuskar bash duk da cewa har yau in banda Mr president da daddynsa babu Wanda yasan cewa shuairat kanwarsa ce , ya juya yace
     "Gaskiya naga alama suna son juna sosai , ni har kunyar shiga side din Mr president nake ji cos dazu ma na samesu suna soyewa"

  "Hmmm..ai ni naga love jiya da dare, ina ganin Mr president ya tsufa Ashe de ya kware .kaga wani warm hug da ya bawa matarsa jiya? Na shiga basu ganni ba sai na fito ai @ 380...
Me bash zaiyi in ba dariya bah haka Suka cigaba da yaba irin kulawan da Mr president ke bawa amaryar tasa.

A falo Suka tarar da daddy da momsi Mr president ya wuce gun momsi tana zaune a 3seater nan yayi kwanciyarsa ya kwantar da kansa akan cinyarta tana dariya tace 

"Hoo...boy baka San ka girma bane"
Shuairat kuwa mamkine ya bayyana a fuskarta wai dama haka Mr president yake xuba shagwaba a gun iyayensa? Muryan daddy ne ya katse ta 

"Com hre boy! Rabu da momsi ai dama nagaya mata ni nafi sonka dawo nan ka kwanta"
Gaba daya Suka yi dariya shuairat kuwa kunyansu take ji ba gardama Mr president ya tashi ya koma kusa da mahaifinsa ya jingina kansa a jikin daddy .momsi tace

"Taho nan ya'ta wannan mijin naki bashi da kunya haka daddynsa ke biye masa suyi ta xuba shirme"
Kan shuairat na kallon kasa kawai jin momsi tayi kusa da ita tana daga kanta Suka hada ido momsi ta cigaba da cewa 

"Ba kunya tsakanin mu ki daukeni tamkar mamanki kinji koh"
Kai ta gyada Mr president yace 
"Momsi ita wannan ta fini shagwaba fah"
   "Ba dole tayi bah! Ita karamar yarinya ce kai kuma fah?
Daddy yayi carab yace
  
"Shima karamin yaro ne a guna har yau ganin yaro nake masa"
Haka dai Suka cigaba da hirarsu ckn nishadi gwanin birgewa daga nan aka Dora da nasiha akan su xauna lfy haka nan momsi ma tayi tata nasihar mai ratsa jiki gaba daya jikinsu yayi sanyi kowannensu da tunanin da yakeyi a ckn xuci Mr president yana tunanin anya zai iya tunkarar shuairat a matsayin su raya sunnah har ya samowa iyayensa farin ckn da suke nema? Hmmm ...akwai aiki kenan.daga nan daddy ya sanar dasu cewa jirgin yamma zasu bi su koma Lagos yau.shuairat bata ji dadin hakan bah cos momsi na debe mata kewa, haka Suka kasance sannan Mr president yayi sallama da cewa zashi office. Daga nan itama ta koma bangarenta tayi lfyar gado nan bacci yayi gaba da ita.


******************
Bayan kwana2 da komawar su momsi da daddy zaman kadaici ya isheta sabida Mr president yana nan busy ckn kwana biyun basu hadu bah , sultan ne ke Dan rage mata kadaicin idan ya tafi skul kuwa shikenan zatayi bacci idan ta gaji tayi kallo tayi karatun Qur'an shikenan.
    Yauma tana zaune misalin 2:30pm sultan se 5yake dawowa don yana xuwan islamiyya , ta rasa me zatayi sai ta bude watsap dinta rabon da ta shiga tun kafin aurenta yakai 1week kenan.aikuwa shukrah da princess meemah suna online nan Suka fara chatting shukrah na zolayarta wai amarci ya boyeta kurum ta daina hawa online, haka nan princess meemah tace tayi missing nata har laasar sannan ta ajiye wayar ta tashi don gabatar da sallah.

Haka rayuwa ta kasance har shuairat ta fara sabawa da al-amuran gidan shugabankasa , yau ta share 2weeks kenan a gidan kuma basa haduwa da Mr president idan taje sai ace yana meeting har 11 na dare zatayi ta jiransa bazata samu ganinsa bah sai dai ya tura text yana tambayar lfyarsu itada Sultan.
   Da yamma tana xaune a falo ana sefe mata kai tana chatting da shukrah bodyguards ne Suka fara shigo da kaya bata damu bah, wata kofa aka bude Wanda tun xuwarta gidan bata taba ganin an bude part din ba sai yau...umaima CE ta shigo tare da sallama masu aiki suna mata maraba ko kallo basu isheta bah shuairat kuwa ko daga kanta batayi bah hakan ba karamin batawa umaima rai yayi bah.ckn gadara ta karasa kusa da shuairat tace 

"Ke me kike ji dashi da baraki bude baki ki gaisheni bah"
Ko uffan shuairat bata tanka bah ta cigaba da danna wayarta masu aikin duk sun rakube a gefe saboda sanin halayen umaima 

"Ba da ke nake magana bah ...
Shuairat tayi wani kayataccen murmushi tace

"Aw...dota! Welcome back kije ki huta daga baya ma tattauna koh"

"Dota! Umaima ta maimaita sunan "dankari ..Amma yarinyar nan ta raina mata wayo" ta nuna ta da yatsa

"Am not ur dota n I'll Neva b...mtssww matsiyaciya kawai"
Daga nan ta juya tayi shigewarta daki shuairat tana murmushi tace

"Drama queen is back zaa sha kallo kenan" 
Bayan an gama sefe mata kan ta haura sama ta wuce daki, wanka ta fara yi bayan ta fito ta caba ado ckn wata gown black mai stones da adon fulawa golden n Orange tayi parking gashin kanta ta kwantar da jelar a gefen kafada nan tayi rolling da Dan karamin Orange veil tayi kyau sosai ta fesa turare sannan ta tsaya a gaban mirror tana murmushi tace 

"Welcome back umaima sai kin raina kanki is time for d show"
Ta fito rike da wayarta a hNnu tana takawa a hnkli ta fito harabar gidan bodyguards Suka bude mota direct bangaren Mr president Suka nufa bayan anyi parking ta fito tayi shigewarta, dakin baccinsa ta shiga tasan war haka baya nan ta haye gadon tayi kwanciyarta.
     Umaima ta shigo falon mahaifin nata tazo ta bashi hkri baya nan sai ta wuce dakin barci shuairat ta baje a gado tana chatting suna hada ido shuairat ta sakar mata murmushi umaima ta ja wani dogon tsaki juyawar da zatayi saura kiris suyi karo da Mr president.



Hmmmmmm muje xuwa
[2/21, 2:39 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*51*
By *Reefat yahya*


Rawar jiki umaima ta fara yi sabida ynxu tana shakkar dad nata baya sake mata nan ta fara in ina..
"Amm..am soryy dad..bansan baka"
Bai bari ta karasa bah ya sa kai a gefenta ya shige dakin shuairat kuwa tana ganin haka ta tashi tayi hugging nasa tare da ajiye masa Peck a kumatu ckn kissa tace

"Oh..my swt hrt I rily missed u"

Murmushi ya sakar mata shima yayi missing nata don sun kwana 2 basu hadu bah umaima ta gagara tsayuwa wani kululun bakin ciki ne ya tokare mata wai dad nata ya manta da mum nasu har zai iya soyayya da wata irin haka? Lallai maza mayaudara neh hawaye ne ya cika idanunta fal ya fara gangaro wa a fuskarta nan ta juya ta bar dakin da guduwa ta fito a bakin kofa Suka ci karo da bash tana ganinsa ta kara fashewa da kuka ba sai ya tambaya bah yasan matsalarta  hannunta ya rike Suka wuce bangaren ta.
   Shuairat kuwa tana ganin burinta ya cika ta zame jikinta daga na Mr president  ckn jin kunya shi kuwa murmushn jin dadi yake yace

"Mom sultan 2days..ya kike ya boy naki"

"Lfy alhamdulillh ya aiki"

"Lfy kalau alhamdulillh hop kina tayani da adua..
"Uhmm..ta fada sai kuma ta tura baki ckn zolaya tace 

"Ni da sultan muna fushi da kai"
Ya langabe kai kamar karamin yaro yace

"Eyya..
Am sorry ku yafe min ba laifina bane kinsan kasar tamu ce sai adua" 

Murmushi tayi tace 
"Haka ne ..Allah ubangiji ya taimaka ya bada saa..

"Ameen...my first lady nagode"

"Ka gaji koh..bari na hada maka ruwan zafi sai kaji dadin hutawa"
Daga nan ta wuce toilet nasa😳😳ita kam bata taba ganin haduwa irin haka bah, bayin ya tsaru  sosai ta tsaya tana yan dube-duben ta dakyar ta gano heater din ta hada masa ruwan xafi sai kuma ta hada da turarukan wanka nan ruwan ya fara bada wani irin qamshi mai dadin gaske ta tara shi a Jacuzzi sannan ta fito ta sanar dashi nan ya fada bayin .



Tnx all
[2/21, 2:39 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*52*
By *Reefat yahya*

Sorry pals page 51 is not up2 d oda pages kuyi hkri somtin came up ina sauri ne daz y.


Mr president ya fito daga wanka shuairat bata ckn dakin Amma ta ajiye masa kayan da zai saka bayan ta feshe su da turaruka masu uban qamshi, ya gama shiryawa ya fito falo tana zaune a kujera tana danna wayarta motsin da taji ne yasa ta juyawa Suka hada ido ta sakar masa wani qayataccen murmushi ya maida mata martani nan ta tashi tayi serving dinsa wani lafiyayen jolof rice da hanta da kuma kayan lambu ta xauna a gefe yana ci a hnkli tana satar kallonsa. Mr president yana da kyau sosai komi nasa yana burgeta shuairat ar u inlov? No...it can't b wanann tsohon yasan love ne? Kawai he is nice to me daz all...
"My lady ar u ok"

Muryar mr President ne ya katse ta
"Yeah..am fine"
  Ya bita da kallon tuhuma yace
   "Are u sure?

     "Am sure mr President.. Trust me"

  "Ok tunda haka kika fada but gaskiya ban yarda ba.
         "Ba komai fah"
"  Allah yasa"
 Haka Suka kasance har mr President ya gama cin abincinsa sannan Suka koma falo .
 kusa dashi ta xauna a kujerar 2seater yana mamakin irin shige masa da takeyi duk da yasan dama suna zama tare Amma yau yaga changes a tattare da ita ko meyasa oho!  News suke kallo shiru ya ziyarci falon kowa da tunanin da yake yi.


Umaima kuwa suna shiga falonta ta sake fashewa da sabon kuka tayi regretting dawowarta Amma skul nasu anyi resuming babu yanda da iya dole ta dawo ta cigaba da xuwa, bash kam tsayawa yayi yana kallonta ya rasa me zai gaya mata ta daina kukan da take yi.tayi kuka mai isarta sannan tayi shiru hanky ya mika mata ta share hawayen sannan tayi ajiyar xuciya yace
 "Wia have u bin umaima"

"Um..um..naje gun sistan mom dina 

"Kin sallami dad naki lokacin da kikayi tafiyar?
Shiru ba amsa ya cigaba da kallonta 

"Talk to me umaima"
"A'a ban gaya masa bah"

  "Umaima baki jin magana , tunda hakane ba ruwana dake daga yau kada ki sake nema na"
 Yana gama fadin haka ya juya yayi ficewarsa . ta shiga uku nan kuwa ta sake fashewa da wani sabon kuka mai ban tausayi amma kash! Babu mai rarrashin ta.
  Da yamma sultan ya dawo yaji labarin dawowar yar uwar tasa yayi murna sosai , dakinta ya wuce tana kwance a gado tayi shiru idanunta duk sun kumbura ta rasa me ke mata dadi a duniyar gaba daya sultan ne ya fada jikinta har ta wani tsorata sabida bata San da shigowarsa ba..

"My boy I missed u so much"
Ta kankamesa a jiki nan kuwa wani sabon hawaye ya fara fitowa sultan ya saketa yana share mata hawayen yace

"Muje ki gayawa anty nah me ya saki kuka kinji "
 Ta bisa da kallon mamaki 

"Sultan wace antyn taka?

   "Lahh...baki San dad ya kawo mana wata anty kyakkyawa tana sona sosai tana kula dani a dakinta ma nake kwana ynxu tana ...

   "Kai sultan waccan ba antynka bace kaji , kada ka sake xuwa kusa da ita koh..
   
"Um..um nikam ina sonta , don tana kula dani sosai har wanka ita take min tana koyamin karatun Qur'an tana taimakamin da assignment dina kuma tana...

  "Stop it! Will u? Nace maka ba antynka bace , kuma ba wai sonka take bah munafurci ne ka dawo nan mu dinga kwana tare kaji"

 "Bana so..nikam da anty nah zan kwana" 
Ya fara kuka ya gudu ya bar dakin umaima ma kukan take yi tana nanata ..innalillahi shikenan shuairat ta mallake kowa a gidan har da kanin nata.ta kai minti 20 tana kwance tana kuka garam aka bude kofar dakin..😳😳🙊mr president ne tare da sultan daga ganin fuskarsa zaka San cewa ransa a bace yake baiyi wata2 ya wanka mata mari ji kake tasss....aikuwa umaima ta sake wani irin razananniyar kara shuairat tNa kwance a falo dama tana jin karan ta fito da wuri nan Suka ci karo da ladi mai aiki jikinta sai rawa yake

 "Haj..Hajiya ki taimaka ki ceci umaima ..mr..
Bata karasa ba shuairat ta sauko a guje ta wuce part din umaima tana shigowa ganin mr President tayi ya sake kaiwa umaima wani Marin da saida ta ga taurari ckn Sauri ta karasa ta shiga tsakaninsu ran mr President sai tafarfasa yake umaima na kuka mai tsoma rai shuairat ta juya tana fuskantar ta tasa hannu zata rike ta umaima tayi saurin komawa ta baya ckn daga murya tace
"Don't dare touch me ...munafuka Allah ya isa sai...

Mr President ne ya sake yunkurin xuwa wajenta shuairat tayi saurin rike masa hannu tana kallonsa tace
  "Pls...pls ur excellency ka rabu da ita she is just a kid ok"

Ransa a bace idanunsa sun kada sunyi ja..shuairat ta rike hannunsa tana ja a hnkli Suka bar dakin masu aiki suna waje sun rakube sai rawar Dari suke tunda Suka zo gidan basu taba ganin mr President ckn bacin rai irin haka ba ko me umaima tayi oho! Shuairat ce ta umarcesu da su kula da sultan da umaima daga nan ita kuwa dakinta Suka wuce da mr President suna shigar dakin ta tura kofa sai me😳? Hawaye ta gani a idanun mr President ya sunkuyar da kai kasa batayi wani tunani ba ta jawosa a jiknta ta rungumesa gam...tana shafa bayansa a hnkli shima hannu yasa ya kankameta😍😍😍

Ku biyoni...are dey in lov??🤔🤔
[2/21, 2:40 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*53* 
By *Reefat yahya*


Sun kai 10mins ckn wannan hali sannan shuairat ta zame jikinta a bakin gado Suka xauna mr President yace

"Na mareta wit my own hands"

"Is ok mr President"
"Aysha I rily love umaima but bata respecting dina she is taking d advantage of d love I have 4her , tana yawan bata min rai kullum dannewa nake yi but now she pushes me to d wall"

   "I know but kayi hakuri ka yafe mata koma menene she is still young ai"
   "She is not young Aysha! Daddy da kansa yace ban bawa yarana tarbiya mai kyau ba, kuma Allah yasan nayi iya bakin kokari na but umaima is rily stubborn"
 A hnkli ta sarke hannunta ckn nasa tace
    "I knw dat but a hnkli zaka lallaba ta ba sai ka hada da duka bah, kuma adua zaka mata kaji koh my man"
Kai ya gyada mata sai kuma ta tashi ta debo pineapple drink me sanyi a firji ta xuba a cup ta dawo ta mika masa ba gardama ya karba ya kurba sau 3 sannan ya ajiye cup din a kasa yana kallonta yace

  "Nagode Allah ya miki albarka tnx a lot ..am..

"Shhhh....yatsa ta dora a bakinsa tana murmushi tace
"Is my duty as ur wife, ina alfahari da kai kana da matukar girma da daraja a ido na I can do anything for u.kuma ina jin dadin aduar da kake min nima nagode sosai"

  Shi kam yana mamakin hali irin na shuairat tana da tunani da kaifin basira sosai abun mamakin ma shine, bata nemi sanin laifin umaima ba kawai ta hau bada hakuri duk da irin kiyayyar da umaiman ke nuna mata Amma bata taba nuna damuwarta bah hakan ba karamin dadi yake ji ba ta wani bangaren kuma idan yayi la'akari da kulawar da take bawa sultan yakan jinjina mata tabbas yayi dace da mace ta gari.
( mata mu kula pls..mu rike ya'yan mazajen mu da xuciya daya muyi koyi da kyawawan halaye irin na shuairat banda hassada da kyashi , hakan zai sa mijinki ya girmamaki kuma ya kara sonki..Allah yasa mu dace Ameen)

"Mr president tunanin me kake ?
"Uhmm..ba komai nagode zan koma side dina ina Dan wani aiki ne"

"Ok muje na ma rakiya"
   "No..don't worry kiyi xamanki ki huta "
  "A'a muje zan tayaka hira idan kana aikin"
Ba musu Suka fito tare suna tfy har xuwa bangaren sa.
    Umaima kuwa family doctorn su ne yaxo ya dubata ya bata magunguna nan kuwa zazzabi ya rufeta.
Kowace safiya shuairat tana xuwa tana duba jikinta duk da cewa umaima bata kulata Amma bata fasa xuwa bah haka nan sultan ita ta cigaba da kulawa dashi tana kuma kulawa da mijinta ba laifi ynxu ta saba da mr President sun fara shakuwa Amma ba wai can bah.

***********
Haka rayuwa ta kasance yau da gobe sai Allah ynxu shuairat ta share wata3 a gidan mr President kullum sai tayi waya da mama da babanta su Suka hanata xuwa , umaima kuwa babu abunda yake hadasu kowa na sabgar gabansa sultan kam ya gama shakuwa da ita kullum basa rabuwa idan yana gida dai suna tare a can bangaren mr President. Haka nan suna waya da momsi da daddy mah kullum, rayuwar gidan de gwanin shaawa masu aikin ma suna yaba halayen shuairat bata da girman kai ko kadan.matan ministoci da sauran abokan mr President duk sun saba da ita suna yawan kawo mata ziyara saboda faraarta.
       Yau weekend babu aiki tun karfe7 shuairat tayi ado na gani na fada sultan ya koma bacci don haka ta fito ta wuce bangaren mr President , bedroom ta shiga yana zaune da carbi a hnnunsa a gefe ta xauna ta sunkuyar da kai kasa ya juya yana kallonta Murmushi ne ya subuce masa yasan akwai maganar da take son fada Amma ta kasa

"My lady ya dai"
"Ina kwana dad sultan"
   "Lfy ya kuka tashi"
"Lfy alhamdulillh"
Sai kuma tayi shiru ta rasa me zata fada
  "Fadi bukatar ki my lady"
Kai ta daga Suka hada ido yana murmushi yace
   "Kina mamaki ne? Just tell me mene ne..
  "Umm..ehmm..dama..
"Mom sultan go 2d point ok"
Ya fada a yayinda ya tallabo habarta ta runtse ido a hnkli tace

  "Gida nake son xuwa gun mama"
"Mama's gal! Kin manta baba yace sai nan da 1 yr zaki fita?
  Rau rau tayi xata fara kuka yana murmushi yana kallonta yace
   "Oh no! Shagwaba again, gara ma ki Adana hawayenki cos babu inda zaki"
Hawayen da suke makale Suka fara gangarowa mr President ya zare  ido yace
   "Ohh...yi hakuri ba sai kinyi kuka bah tashi ki shirya muje koh don't cry pls"
Nan kuwa murna fal har ckn ranta taji dadi kawai ta rungumesa tare ta yi masa peck a kumatu tace
  "Tnk u so much mr President nagode"
Daga nan ta tashi zata ruga a guje yayi saurin riketa yace 
  "Ke lafiyanki? AHakan zaki fita securities suna kallonki? Idan kinyi ma sai mu fasa xuwa sai ...
Bai karasa ba ta rungumesa ta baya ckn salon shagwaba ta fara magana
  "Eyya fah...yi hkri toh na daina tsallen a hnkli xan tafi kaji"
Shiru yayi yana jin wani irin yanayin da ya kasa tantance ko menene dakyar ya furta 
"Ok jeki ki shirya tare zamu je" nan ta bude kofa tana tfya tana murmushi ita kadai har ta fice daga bangaren nasa.


😘😘😘😘lov u all
[2/21, 2:40 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*54*
By *Reefat yahya*


Mr president yabi bayanta da ido yana murmushi tare da girgiza kai shuairat tana da shirme wllhi tana Abu kamar karamar yarinya.
   Shuairat kuwa wani wankan ta sake yi tasha ado ckn wasu leshi maroon n golden da touches din milk color ta saka yan kunnen gwal tayi kyau sosai.
   Karfe 8 ta gama shirinta tsaf haka nan ta shirya sultan ma ckn kananan kaya yayi kyau sosai sai qamshin turare ke tashi daga nan Suka wuce bangaren mr president a can sukayi kari ckn jin dadi suna ci suna Dan taba hira.

Karfe 10 na safe motoci sukayi parking a kofar  gidan Alh bello maiha shuairat ta fito ckn xumudi ta fada gidan tare da sallama falon mama ta wuce suna zaune suna hirarsu ta fada jkn mama tana dariya farin cki ne bayyane a fuskar iyayen nata baba yace
 "Ahh...ya'r baba wato kinfi son mamanki koh"
 Nan ta tashi ta koma kusa da mahaifin nata tana dariya tace 

"Ba haka bane fah..baba nayi kewarku sosai"
Daga nan Suka gaisa bash ne ya shigo yana hararinta yace

   "Bansan yaushe zakiyi hnkli bah , dama kinzo da mr president shine kika baro shi a waje"

"Lalala..baby dama tare kuke shine kikayi zamanki baki sanar damu bah

  "Toh baba nikam ba na manta bane"
 Ta fada tana xumbura baki daga nan mama ta tashi ta koma ckn daki aka shigo da mr president dama sultan kam yana xaune a falon , ckn girmamawa Suka gaisa da surukin nasa sun Dan taba hira sama2 sannan yayi sallama ya tafi.shuairat kam ta haye gadon mamanta ta mike tana jin wani dadi, sultan kuwa ya sake sosai yana xubawa baba hira  mama ta kawo masa abinci yaci sannan ta koma daki gun ya'rtata suna hira tana tambayarta zamanta kewar tasu , shukrah ta shigo Suka baje sunata surutu mama ta koma falo tabar musu dakin.shukrah ta gyara zama tace

   "Mutuniyar kinga kyawun da kika kara kuwa? Sai wani shinnin kike ko dai..ta kanne mata ido daya shuairat ta buge kafadarta tace

  "Munafuka! Toh ba abunda kike nufin bane
  "Hmmm..wa yasani Abu a duhu..maybe rabo ya zauna naga sai wani kyau da haske kikayi"

"Shukrah kenan..baki da dama wllhi, don kina da ciki shine kike zaton kowa ma haka ne?

  "Hee...wa yagaya miki ciki ne dani?
  "Ahaf..tun yaushe naji labarin a gun Yaya"
    "Hmmm..zai dawo ya sameni ai tunda Allah yayi shi da shegen suru2"
Shuairat ta fashe da dariya tana tsokanarta shukrah tace 
  "Ke dinma na baki nan da wata daya..naga wani kalan soyayyan da kuke har rakaki anguwa yake hmmmm"
  "Oho dai..ki fama dashi "

"Baby me sirrin ne, naga alama fah mr president ya fada kuma naji labarin xuba love da kukeyi a gaban kowa ma Baku jin kunya"
    "Ikon Allah..shiko Yaya dan sa ido ya koma! Lallai zan gayawa mr president "
"Keee..rufamin asiri wasa nake miki"
Haka Suka kasance suna yiwa juna shakiyanci .
   Yinin ranar curr..tare sukayi ckn farin cki da walwala har xuwa 7pm sannan aka zo daukan su shuairat ta koma gida.

Karfe9 ta gama shirin baccinta tsaf xata kwanta sai kuma ta tuna tabar wayarta can falon mr president kuma tana son shiga watsap dole ta tashi ta Dora hijabi kan kayan baccinta ta nufi bangaren mr president.
Yana xaune a falo yana shan coffee idanunsa nakan TV yana kallon news, ta shigo tare da sallama can cki ya amsa ba tare da ya juya ya kalleta bah.wayar na gefensa akan kujera batayi masa magana ba taxo wucewa zata dauka ckn rashin saa tayi tuntube da kafar mr president tayi luuu...ta fada jikinsa jagwab Suka kurawa juna ido , turo kofar akayi tare da sallama umaima CE ta shigo suna hada ido da shuairat ta saki wani shuumin murmushi nan kuwa ta Dora bakinta kan bakin mr president ba shiri ta fara kissing nasa tamkar xata cinye shi.
Mutuwar tsaye umaima tayi ta fara jin haushin kanta tayi regretting xuwan da tayi ckn axama ta juya tabar falon shuairat na ganin haka ta cire bakinta mr president kam saura kadan ya suma..tunda yake a rayuwarsa bai taba shiga irin yanayin da yake cki a hlin yanxu bah, shuairat kuwa wani irin kunyarsa take ji ta kasa tashi daga jikinsa kuma ta gagara hada ido dashi.sun share minti 10 ckn wannan halin sannan ta tashi tmkar Mara gaskiya ta fara tafiya a hnkli rike hannunta mr president yayi sannan ya damka mata wayarta a hannu daga nan ta juya tayi tafiyarta.
      Bacci ya gagaresu mr president shuairat da kuma umaima kowanne da kalar tunanin da yake dakyar bacci ya sace su.
Asuba tagari ....


😘😘😘
[2/21, 2:40 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*55*
By *Reefat yahya*


Haka rayuwa ta kasance shuairat ta share shekara daya a gidan mr president zaman nasu ba laifi tana bashi kulawa irin Wanda baa rasa bah, sultan kam ya manta da cewa shi maraya ne cos shuairat ta maye masa gurbin uwa tana basa kulawa fiye da komai.shukrah ta haifi danta namiji mai kama da ubansa sak aka rada masa suna Bello ana kiransa waleed. Ynxu kam duk fadin Nigeria babu inda baa San fuskar shuairat bah tana yawan xuwa gidan marayu tana tallafa musu haka nan ta bada shawara aka bude makarantun islamiyya da dama ga kuma masallatai, bangaren asibitoci ma sun bada gudunmawa.

Shuairat ta kara cika tayi kyau sosai alamar Hutu ya bayyana a jikinta ta kara haske sai sheki take yi, shuairat ce a kitchen tana bada umarnin girkin da zaayi yau surukan nata xasu kawo musu ziyara itama ta taba xuwa sau daya. Karfe 4 Suka shigo gidan ckn murna ta tare momsi direct dinning Suka wuce nan Suka gaisa ta xuba mata abinci ta tura a gabanta

"Hoo...shuairat daga xuwan mutum ki tura masa abinci a gaba "
 Murmushi tayi tace 
  "A'ah momsi kamata ki fara da abinci kafin ki huta koh"
  Ba gardama  fara cin daga nan shuairat ta tashi taje gun daddy Suka gaisa.
   Da dare suna xaune a babban falo a bangaren shuairat ita da momsi da sultan da kuma umaima suna ta hirarsu umaima bata sa baki bah don ta lura da shakuwar dake tsknin momsi da shuairat. Sultan ne ya juya gun shuairat yace 
"Anty muje mu kwanta bacci nake ji"
Carab momsi tace
  "Kaji min yaro! Dama kullum da ita kake kwana ne"

"Ehh..mana granny baki sani bah dakinmu daya da anty nah , ita take kula dani tana sona sosai"
Zare ido momsi tayi tana kallon shuairat har umaima tayi mamakin jin hakan shuairat kuwa ta sunkuyar ya kai kasa ckn jin kunya ta gane kallon da momsi take mata..Muryar momsice ta katse ta tana kiran ladi mai aiki ba bata lokaci taxo ta rintsina ckn girmamawa

 "Ki raka sultan dakin baccinsa"
Dakyar sultan ya amince saida shuairat ta lallabasa tace masa tana nan xuwa.wayar hannu momsi ta fitar ta kara a kunne
  "Ka sameni a falon matarka"
Daga nan ta kashe wayar ta juya tacewa umaima ki bamu waje xamuyi magana, nan ta tashi ta koma bangarenta.ckn kankanin lokaci mr president ya shigo falon tare da sallama ya nemi waje kusa da ita ya xauna nan ta fara magana

"Ina son jin meke faruwa a gidan nan"
Ckn rashin fahimta mr president ya daga ido ya kalleta
    "Momsi wani Abu aka gaya miki ne? Nidai nasan ba komai muna xaman lfy da ita kodai tace na mata wani abun?

"Boy kenan.. Ka bani mamaki wllhi, ynxu da girman ka da ilimnka amma ka kasa sauke hakkin aure dake rataye a kanka?

"Momsi wane irin hakki? Wllhi muna xaman lfy da ita gata nan ki tmbayeta koh my lady na taba bata miki raine?
  Sunkuyar da kai shuairat ta kara yi momsi ta ja tsaki sannan tace
     "Ynxu irin xaman da kukeyi kenan? Tsawon shekara 1 da auren naku Amma ....
Ta kasa karasa maganar sabida nauyin Kalmar sai kuma tace

  "Kasan idan Alh yaji wannan maganar ranku xai baci ba kadan bah, garama Ku daidaita tskaninku Ku wuce Kuban waje sakarkaru kawai"

   "Kiyi hkri momsi Allah ya huci xuciyarki"
Shuairat ce ta furta a hnkli mr president kuwa kansa a kulle yake ya kasa gane me take nufi haka nan shima ya bada hkri sannan ya mata saida safe ya koma bangarensa, itama ta tashi tace
   "Ni zan Kwanta maza ki shirya kibi mijinki ynxun nan"

"Mu kwana lfy momsi"
Daki ta wuce ta fada wanka bayan ta fito ta shirya ckn kayan baccinta ta fesa turaruka daban2 sannan ta wuce bangaren mr president wani irin kunya take ji gani take tmkar bodyguards din duka ita suke kallo.a hnkli ta turo kofar dakin tare da sallama yana xaune ya buga uban tagumi yana ganinta ya tashi a hnxarce ya karasa ya jawota tare Suka xauna a gadon yace
  "Pls Aysha wane laifi na miki zaki hadani da momsi na Wanda bazaki iya gaya min bah..kinsan tunda muke bata taba fushi dani bah amma yau naga alamar hakan a fuskarta"
     "Am sorry mr president wllhi ni...
"Just tel me Aysha me na miki"
Nan ta fashe da kuka tana cewa 
   "Ni..ni baka min komai bah kuma babu abunda na gaya mata"
Ya fara rarrashinta yace
  "Ok naji ...ba laifinki bane , toh gaya min me ya faru"
   "Umm...ba sultan bane ya gaya mata cewa kullum tare muke kwana "
  "Ok..nagane, kinga ynxu sultan is 8yrs old tana ganin ya girma bai dace kuna kwana tare ba koh?
  "Ah'ah..tana nufin cewa  uhmm..uhmm"
Shiru tayi ckn jin kunya ta rufe ido tana murmushi dogon numfashi ya ja sai ynxu ya gane me momsi take nufi da cewa ya kasa sauke hKkin aure ...hmmm anya zai iya????

Masu karatu ya kuke gani hakan zata faru kuwa??

Hmmmm...muje xuwa
Love u oll😘😘😘
[2/21, 2:40 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*56*
By *Reefat yahya*


Shiru sukayi dukkansu biyu daga karshe shuairat ta tashi zata fita yace
  "Ina zaki ?
   "Uhmm..falo zan koma can xan kwanta"
Wani irin kallo ya watsa mata ba shiri ta dawo ta xauna
     "So kike ki tonamin asiri ko me? ..as from today ki tattara kayanki ki dawo nan da xama"
Ckn Sauri ta kura masa ido ya kada kai yace
    " yes! Ki dawo nan mu xauna tare kinga babu wanda xaiyi magana koh, oya ki hau gado ki kwanta ba sai kinje falo bah"
Ba musu ta cire hijabinta ta hau saman gadon ta kwanta a gefe tayi aduointa ta shafa sannan ta rufe ido tana son bacci Amma ta gagara she is not comfortable. 
Mr president kuwa ya tashi ya fada bayi ys watsa ruwa sannan ya fito ya saka kayan baccinsa ya fesa turare sannan ya kwanta a gfenta bata rufe da bargo ba ya kura mata ido na yan dakika sannan ya dauke kai.baccine yayi awon gaba dasu can tsakiyar dare ta mirgina ta koma kusa dashi ta kankame shi gam wutar dakin a kashe yake, ckn bacci mr president yaji alamar mutum a jikinsa a hnkli ya bude ido ya kunne side lamp tana baccinta ckn kwanciyar hnkli ya kura mata ido tana sauke numfashi a hnkli tayi masa kyau sosai ya juya zai kashe wutar ta Dan motsa nan ya koma ya kwanta a hnkli shima ya kara rungumarta.
    Da asuba ita ta fara tashi a hnkli ta zame jikinta daga nasa ta fada bayi zama tayi a ckn bahon wanka tana lumshe ido tana tuna halin da ta farka ta gansu a cki, tana mamaki ya akayi hakan ya faru? Dakyar ta daure tayi wanka  tare da yin alwala ta fito har ynxu baccin yake ta tsaya Jimm...hannu tasa a gefen fuskarsa tana shafawa a hnkli take ya bude ido tace
   "Morning... Tym din sallah yayi"

Daga nan ta tada sallah tayi nafilfilu sannan tayi sallan asuba ta xauna tana Jan carbi ya fito ya gabatar da sallah haka Suka kasance har rana ta fito shuairat ce ta nade sallayar ta xauna a gefe tace
    "Ina kwana"
"Lfy ya kike"
  "Lfy alhamdulillh"
Da tashi ta kama hanyar fita dakin 
     "Ina zaki ?
  "Nayi wanka Xan je dauko kaya a...
   "Dawo ki xauna xaa kawo miki"
Ba musu ta koma kan gado ta xauna tana wasa da yan yatsunta.
Falo ya nufa bayan yan mintoci ya dawo ya shige bayin da alama wanka zaiyi.motsi take ji a falon ta fito don ganin waye ne ga mamakinta akwatunan ta aka jera da sauran kayayyakin da ta mallaka a dakinta , wani dakine da yake kusa da na mr president a can Suka shigar  da kayan sai kuma mata masu aiki Suka shigo Suka gaisheta sannan Suka shige dakin take Suka ajiye komai inda ya dace Suka gyara dakin se qamshi ke tashi daga aka hada musu abinci a dinning.
  Tsarin dakin ya birgeta kwalliya ta fara yi bayan ta gama ta saka wasu material masu kyau daga nan ta yafa veil ta wuce bangaren da momsi take Suka gaisa se kuma daddy shima ya fito ta ritsina ta gaida shi.sultan ya fado mata a rai a hanya Suka ci karo dashi yana ganinta a guje ya fada jikinta yana cewa 
   "Anty ina kika je nida jummai muka kwana jiya" ( jummai ya'r aiki CE)
Tana shafa kansa tace
  "Sorry boy muje kayi brkfast koh"
Daga nan Suka wuce bangaren mr president don karya kumallo.


Bayan kwana4 su daddy sukayi sallama akan cewa zasu koma , momsi kuwa ta ajiye mr president da shuairat tayi musu nasiha sosai akan zaman ta kewar aure daga nan Suka fara shirin komawa.



Love u all....😘😘
[2/21, 2:40 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*57*
By *Reefat yahya*


Shuairat tana zaune a falo tana danna wayarta da alama chatin takeyi mr president yana office ynzu saura masa 1yr regime dinsu ya kare cos an fara shirye-shiryen zabe na gaba ana son ya fito Dan takara shikuwa baya so yace mulkin ya ishesa haka.
         Umaima CE ta shigo ckn gadara da nuna isa ta zauna a daya daga ckn kujerun ta kalli shuairat da wani irin kallon raini sai kuma ta fashe da dariya, shuairat bata juya ta kalleta bah ta cigaba da chatting dinta
  "Ke munafuka bakiji shigowata bane bazaki gaisheni bah"
 Nan ma bata kulata ba kawai shuairat taji wani wawan mari a fuskarta dankari ko iyayenta basu taba wanka mata mari irin wannan bah..ba tare da dogon tunani bah ta daga hannu ta rama dai-dai nan mr president ya shigo falon 
   "Subhanallah Aysha meke faruwa"
Nan umaima ta rike kunci ta fashe da kuka sannan ta fada jikin mahaifin nata tana rusa uban kuka mr president yabi shuairat da wani irin kallon tuhuma ransa ya baci kwarai da gaske shuairat ta kawar da fuska gefe..
  "Aysha wannan shine amanar da na danka miki? Dama zaman da kukeyi kenan idan bana gida ko nayi tafiya...

  "Dad wllhi kullum se ta mareni ta kuma zagi iyayena , ba hali inyi magana cos babu Wanda xe yarda...dad don Allah ka bata hakuri idan wani laifin na mata kuma don Allah ta daina zagin mom ....
Ta karasa maganar ckn kuka ran mr president ya kara baci sai tafarfasa xuciyarsa ke yi shuairat tace
  "Mr president.....
Hannu ya daga mata alamar baya son jin komi daga gareta daki Suka wuce yana rike da hannun umaima se kukan munafurci take yi.ran shuairat ya baci tayi mamakin rashin adalci da aka nuna mata ido da ido, dakinta ta wuce ta fada kan gado tana rusa kukan bakin ciki.
Yinin ranar tayishi ne a dakinta abinci ma bata fito ta ci bah mr president kuwa ya lallaba umaima ta koma bangarenta tana jin dadin abunda ya faru ko a banza ta shiga tsakaninsu Ashe dai dad yana sonta.
Mr president ya dawo da dare yana cin abinci ya jira fitowar shuairat Amma shiru babu labarin ta ladi ya kira yace a kira shuairat ta fito taci abinci nan ladi ta shaida masa cewa bata ci abincin rana bah kai ya gyada ya koma dakinsa zama yayi akan gado ya fara tunani tabbas baiyi adalci bah kamata ace ya tsaya yayi bincike Amma Sam ya rufe ido ya nuna yafi son ya'rsa hakan babu adalci Sam.a hnkli ya taka xuwa gaban hotonsa da Maman umaima yana shafa hoton yace
 "Zainab ki gafarceni Tabbas na zauna lfy dake Amma ban taba jin sonki a xuciyata kamar yanda na fara jin son Aysha bah, na yarda da maganarki idan abubuwan da kika fada min a baya hakane toh lallai na fada tarkon so...ckn kankanin lokaci namanta dake ya daina yawan tunawa dake ya daina xubar da hawaye a kan rashin ki...am sorry"

Hawayene Suka fara gangarowa yana lumshe ido yana tunanin cewa dama haka so yake? Tunda yake a rayuwarsa bai taba shiga yanayi irin na ynxu bah..lallai yayi nisa ckn tarkon so yana son Aysha bazai iya rabuwa da ita bah.nan ya juya ya fito direct dakinta ya nufa ya tura kofar a hnkli tana kwance ckn wasu kananan kaya skinny jins da red top gashin kanta a ya rufe mata fuska...wow😍 mr president ya tsaya tamkar statue shi bai taba ganin kyawunta irin na yau bah, bata San ya shigo bah ta juya kenan Suka hada ido tayi saurin kawar da kanta gefe a hnkli ya taka xuwa kan gadon ya xaune a gefenta

  "Look Aysha! Am sorry ..nasan banyi adalci bah I shul have...
   "Me laifin ka ? Don ka nuna ka goyi bayan ya'rka? No..ko kadan I din blame u, am just...
Bata karasa ya rungumeta gam a jiki hawaye na malala a fuskarsa wani ajiyan xuciya tayi itama kuka Mara sauti takeyi
  "Am so sorry my lady..pls kada kiyi fushi dani , muje kici abinci koh"
Ya sassauta rungumar ya daga kansa yana kallonta a hnkli yasa hannu yana share mata hawayen da suke fitowa ya sake cewa 
 "Am sorry pls...
"Is ok! Nima ka yafemin kuma...

  "SHhhhh...bakiyi laifi bah ki kwantar da hnklinki now let's go n eat"
Ba gardama ta tashi hannunsu sarke da juna Suka fito falo bata damu da kayan da suke jikinta ba don tasan cewa babu Wanda zai shigo a wannan lokacin.a dinning area Suka xauna kan kujerun table din suna fuskantar juna ya xuba mata abinci ya tura a gabanta ta fara ci a hnkli tabbas taji yunwa ba kadan bah, suna ci suna kallon juna a haka har Suka gama sannan Suka koma daki sun fara shirin bacci.

Muje xuwa.......



😘😘😘😘
[2/21, 2:40 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*58*
By *Reefat yahya*


Haka rayuwa ta kasance kullum shuairat da mr president suna Dada shakuwa da juna akwai kyakkyawar fahimta a tsakaninsu kuma suna girmama juna sosai babu raini a ciki mr president ya siyawa mahaifin shuairat wani dankareren gida a can maitama gidan ya hadu sai San Barka shuairat tare da iyayenta sunje hajji sun dawo tana kwance a dakin mr president ta gaji sosai sabida yan xuwa mata Barka da dawowa, wanka tayi da towel a jikinta haka ta kwanta bacci yayi awon gaba da ita.
Karfe 10 mr president ya shigo dakin ya tsaya ya kura mata ido babu ko keftawa tayi kyau sosai gashin kanta ya baje akan gadon don ta wanke kan nata batayi parking bah.a hnkli ya daga ta zan gyara mata kwanciya 😳😳 towel nata ne ya kunce kurr...ya kurawa jikin nata ido🙊hmmmm...wani irin yanayi ne ya ziyarci xuciyarsa chak! Ya tsaya ya kasa motsawa ita kuwa baccin takeyi ckn kwanciyar hnkli ya dau tsawon minti5 a ckn wannan hali dakyar ya daga kafansa ya fara tfy sannan ya kwantar da ita ta juya akan gadon towel din ya kunce gaba daya 🙈🙈🙈ckn hnxari mr president ya fada toilet yana rufe ido tmkar Mara gskiya dakyar ya saita kansa.
     Ya share 30mins ba tare da yayi wanka ba kurum ya xauna xuciyarsa na dukan 3-3 haka ya daure ya watsa ruwa ya fito har ynxu tana nan inda take ya kawar da fuska gefe sannan ya jawo bargo ya rufa mata jikin, ya gama shirinsa na bacci tsaf ya koma kan rest chair yayi kwanciyarsa  ya kulle ido Amma me? Hoton shuairat kawai yake gani.

     12:15am ta bude ido a hnkli ganin haske a dakin yasa ta juya tana kallon koina mr president ta hango saman kujera yana bacci ckn kwanciyar hnkli sai ta fara tuna yanda akayi ta dawo kan gadon cire bargon tayi 😳ganin babu kaya a jikita nan ta kwala ihu take mr president ya farka 
   "Lfy...my lady meya faru"
 A hnkli ya karasa kusa da ita tace
  "Don't touch me pls"
"Meya faru?
Tayi shiru ta rasa me xata ce masa kawai ta fashe da kukan shagwaba take ya rikice ya xauna kusa da ita ya jawota jikinsa har ynxu bargon ne ta rufa dashi
   "Tell me my lady! Mafarki kika yi?
  "Um..um "
"Toh meya sameki?
"Ba Kaine bah...ka ciremin kaya na ka barni haka ...
Dariyane ya subuce masa lallai ma wannan yarinyar 
  "Nifa ban cire miki kaya bah haka na tarar dake kwance "
"Allah ban yarda bah" ta tura baki tana magana
  "Shikenan tunda karya xan miki"
Ya kawar da kai gefe hannu ta sa ta jawo kumatunsa tana murmushi tace

  "Bance karya kake bah my man wasa nake ma"
Bai kulata ba yana kallon gefen har ynxu
  "Eyya..ur excellency fushi kake dani! Am sorry toh"
Nan ta rungumesa ta baya gashi babu kaya a jikinta wani irin shock ne mr president yakeji a jikinsa ya kasa daurewa nan ya juya ya hada bakinsa da nata .....🙈🙈🙈

Hmmmmmm....muje xuwa
[2/21, 2:40 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*59*
By *Reefat yahya*

~love zone~ I knw many will love dis page irinsu anti waine😜😜


10mins kiss sukayi dakyar Suka rabu da juna kowannensu yana maida numfashi kunyane ya hana shuairat daga kanta a hnkli ta juya tayi kwanciyarta tare da rufawa da bargo daga sama har kasa ta shige bargon lub...murmushi yakeyi ya yaye bargon dai-dai fuskarta ta kulle ido nan ya kwanta a gefe ya jawo kanta ya dora a saman kirjinsa yana shafa gashin kanta wani irin nishadin da bai taba samu a rayuwarsa haka ya tsinci kansa a ciki wai dama wannan shine so? Tabbas idan hakane babu abunda yafi dadi a duniya irin ka samu wacce kake so Ku kasance tare har abada..rayuwarsa a baya ya fara tunawa da irin zaman da sukayi da zainab, Allah Sarki zaman mutunci da girmama juna sukayi Amma babu so a ciki ko kadan..Allah yajikanta yasa
  "Ur xcelency are u ok!
"Uhmm..am fine "
       "Sure?
"Yeah am sure, kawai tunanin rayuwa nakeyi"
     "Uhmm..ka tuna da Maman umaima ne?
Baice komai ba ya rintse ido tmkar mai jin bacci Amma Sam baccin ya ki xuwa shuairat ta kura masa ido tana kallon kyakkyawar fuskar tasa ya bude idanun nasa Suka fada ckn nata tayi murmushi ta cire idon ya daga mata gira yace
   " kallon bai isheki bani"
Ckn jin kunya ta cusa kanta a kirjinsa tana murmushi.

1:40am suna nan kwance basuyi bacci bah shuairat ta lura da halin da mr president yake ciki a hnkli ta tashi baiyi magana da bargon a jikinta ta fita dakinta taje bayan 10minz ta dawo sanye da kayan bacci tana rike da wani littafi a hannunta yana kallonta ta dawo tayi kwanciyarta a saman kirjin nasa nan ta bude littafin "d little mermaid" haka aka rubuta batace komai ba ta fara karanta masa story buk din yana sauraronta yana jin wani irin nishadi , haka Suka kasance har 2:15 taji saukan numfashi a hnkli ta daga kanta ya fara bacci ckn kwanciyar hnkli ya kara kyau sosai nan ta kura masa ido tana kallonsa tanajin wani shauki a tattare da ita tabbas kaunar mr president ya mamaye mata xuciya ba komai bane ya janyo hakan in banda kulawar da yake bata sai kuma kyautawa iyaye da danginta yana matukar girmamasu yana karramasu ....haka ta kasance se 3 bacci ya saceta.


Tana zaune a falo ta harde kafa daya kan daya tasha kwalliya tamkar sabuwar amarya sultan ne ya shigo ya fada jikinsa yana cewa 
  "Mami kinga anty umaima ta ki ta kaini shopping koh" 
"Me kake son siya a shopping my boy"
  "Story books nake so kuma ina son chocolates da ice cream"
Zuwaira itace sabuwar mai aikin shuairat ita take kula da duk wasu hidimomin ta.shuairat ta bada umarni a kira bodyguards 5 suxo su raka sultan shopping , babu bata lokaci Suka shigo nan ta dauko kudi masu yawa ta mikawa zuwaira tace sukai sultan shopping su kula dashi sosai daga nan Suka sa kai Suka fita.
    TNa nan xaune mr president ya shigo tare da sallama nan ta tashi ta rungumesa tana murmushi tace
 "Wlcm back my man! Nayi kewarka sosai"

 "Really?
"Yeah...Sosai fah ba kadan bah"
Suna dariya nan taja hannunsa daki ta nufa dashi ta hada masa ruwan wanka tare da ajiye masa kayan da zai saka bayan ta fesa kayan da turare me kamshi.bayan minti10 ya fito daga wankan ya zauna a Gavan mirror shuairat ta karasa hannunta rike da karamin towel nan ta fara goge masa ruwan jikin nasa mr president de se binta da ido yakeyi yana ganin sabon salon kulawar , bayan nan ta shafa masa mai yana xaune ko  Kwakkwaran motsi bayayi..a takaice dai shuairat ce ta taimaka masa har ya gama duk wani shirin da zaiyi sannan Suka fito falo ta xuba masa abinci yana ci tana basa labarin gida.

  10:30 pm suna kwance akan rug carpet a ckn dakin mr president yana rike da newspaper yana karanta musu a yayinda shuairat tayi filo da kirjinsa suna duba jaridar tare daga karshe ya ajiyeshi a gefe ya juya yana kallon shuairat yace
  "Oya...gist me"
Tayi fari da ido tace
  "Gist kuma? Wane iri?
"Kowanne...maybe about ur love story"
Shiru ta masa ta rasa me zata fada
   "Ina jinki"
"Uhmm...nifa ban taba yin soyayya da kowa bah"
  "Uhhhh..uhhh fadi gaskiya man my lady"
  "Serious"
"Aww...sai a kaina koh?
"Ni nayi soyayya da kaine?
   "Oho!...tsohon da kike cewa bazaki aureshi ba dai shi kike so kuma dashi zakiyi soyayya insha Allah"

"Waya gaya maka cewa ina son ka , kuma waya ce ma zanyi soyayya da kai?
 "Idan baki soni bah wa zaki so? Kuma da waye zakiyi soyayya idan ba da mijinki bah?
 Shiru sukayi suna kallon juna yace 

"Trust me Aysha! Muna kaunar junanmu kawai we didn't realized it ne shiyasa, I can admit it now..I have feelings for u n am ready for it ryt now.
Aysha zan iya sadaukar da komai akanki cki kuwa harda mulki da kuma rayuwata, matukar zaki soni ki xauna dani I can give up anytin..pls let's start a new life."
Shuairat kam shiru tayi ta kura masa ido tmkar taga sabuwar halitta ya cigaba da cewa 
  
"Tunda nake a rayuwata bansan menene so bah, bansan ya ake yinshi bah.so daya tak! Na sani a duniya shine son da nake yiwa iyayena sai kuma lokacin da na samu ya'ya apart from dis bansan feelings for somtin else ba"
Ya ja wani dogon numfashi ya juya yana kallon fuskarta nan ya tallabo habarta yace

"Aysha! I want to b wit u har xuwa ranar da xan koma ga mahalicci na , pls accept me stay wit me n show me ur love n kia"
A hnkli shuairat takai fuskarta dai2 nasa hancinsu yana gogan juna idanunsu na kallon juna lebensu na taba juna ta xira harshenta ckn nasa ta fara tsotse bakin ba tantama ya fara maida mata da martani gaba daya ya rikice har ya fara fita daga hayyacinsa shuairat shu'umace haka ta cigaba da kissing nasa sai kuma ta tura yatsa ckn kunnensa tana masa tafiyan tsusa aikuwa lbri ya fara canzawa da ganin haka na ajiye pen dina na koma daga falo ina maida numfashi....


Hmmmmmm
Ku biyoni...

*Reefat* ce
[2/21, 2:40 PM] Reefat: 💞NI DA SHUAGABAN KASA💞
*60*
By *Reefat yahya*


Wata duniya daban Suka fada..dakyar shuairat ta xame jikinta ta koma gefe ta kwanta idanunta a rufe mr president kam ko kwakwaran motsi ya kasa yi sun share 10mins a haka sannan ya jawota jikinsa a hnkli ya rada mata
" let's  sleep"
Haka ya rungumeta gam a jikinsa akan rug carpet din Suka kwanta ranan har bacci yayi gaba dasu.

Da safe bayan sungama brkfst mr president ya tafi office tana xaune a falo wayarta ya fara ringing anti mairo ce , ta daga ta kara a kunne

"My only anty"
"Ke ki kira wadannan securities naku su bani ixinin shigowa tun daxu muna bakin gate kamar masu shigan aljannah se wulakanta mu ake"

Dariyane ya kubce mata sannan tace 
"Sorry anty gani nan fitowa"
Daga nan ta xaro mayafi tayi waje ana gaisheta tana amsawa direct wajen adana motocin da take fita dasu ta wuce nan kuwa aka bude mata ta shiga ta shaida musu inda xasu je wato babban gate na shiga gidan.
      Anty mairo tare da shukrah ta hangosu suna tsaye ta fito da faraa ta karasa ta rungumesu sannan Suka dugunzuma xuwa mota basu tsaya ko ina ba sai can bangaren ta har ckn bedroom Suka shige , shuairat tana rike da waleed dan shukrah tana masa wasa.masu aiki Suka jera musu abinci da fruits da drinks kala2* bayan sun gaisa anty mairo tace
  "Baby naga gidan da mr president ya ginawa iyayenki gskiya gidan ya hadu Allah ya kara budi ya Baku xaman lfy, gdkiya mijinki mutumin kirki ne ki kara godewa ubangiji da ya hadaku"

Murmushi take tana jin dadin kalaman anti mairo, shukrah ta harareta tace 
"Munafuka da kince baki son tsoho fah, gashi ynxu kin fada tarkon sonsa"
  "Kai shukrah ..ni nace miki ina sonsa ne?
  "Ahaf..ga xahiri ! Daga yabonsa kawai kin hau murmushi babu gaira ba dalili..yarinya kibar munafurci idanunki ma sun bayyana karara kin dulmiya ckn kogin sonsa"
Gaba daya Suka fashe ta dariya anti mairo tace

  "Yawwa..nikam ba wannan bah, wai ina lbrin haihuwa ne har ynxu shiru"
Shuairat ta sunkuyar da kai kasa tana wasa da hannun waleed
   "Ah toh..gara dai kimata magana anti don gskiya ina xargin cewa dakyar in akwai abunda ya shiga tsakaninsu" 
Shukrah ta fada tana hararar shuairat aikuwa anti mairo kamar jira take ta hau masifa
    "Anya lfynki kuwa bby? Kinsan nauyin dake kanki kuwa? Ko angaya miki aure wasa ne...toh wllhi ki kiyayeni idan ba hakaba xan saba miki "
  "Kiyi hkri anti Amma..
"Amma me? Rufemin baki wawiyar yarinya kawai, dame ya rage ki? Toh bari kiji wllhi samun nmji irinsu mr president sai antona a wannan xamanin namu.wani ma yana da kudin kina gani baxaki samu ba bare iyayenki, Amma bawan Allhn nan yanata hidima da danginki kaff babu Wanda ya bari, nidai ki farka daga baccin da kike kuma kiji tsoron Allah.
    "Anti shima fa bai taba nemana bah" ta fada tana tura baki 
Sallallami ne anti mairo ta fara yi sannan tace
   "So kike yace miki ki zo mu sadu? 
Shukrah da shuairat sun fashe da dariya sosai maganar ya basu dariya
  "Aww..dariya na baki koh? Ki cigaba da rashin hnklin naki..wai ke ba na mace bane? Baki San yanda zaki ja raayin namji bah"
Haka dai anti mairo ta cire kunya ta wayar da kan shuairat sosai ta koya mata wasu abubuwa da dama , sun yini tare har yamma sannan Suka kira bash ya ajiyesu a gida.mr president bai shigo ba sai 11pm dakinsa ya wuce yayi wanka ya fito ya ci abinci har ya gama baiji motsinta bah dakinta ya shiga tare da sallama tana kwance a gado ckn wasu shu'uman kayan bacci , a hnkli ya karasa ya xauna kusa da ita ckn yanda da Jan hnkli tace
  "Wlcm my man"
"Tnx my lady lfy yau baki xauna falo ba "
 "Sorry kaji ni shiru koh..kaina kemin ciwo shine na dawo na kwanta"
Hannu yakai ya taba kan "eyya..sory gashi kai din baiyi wani zafi bah"
     "Ehh..nasha magani ai"
  "Ok..sorry"
"Tnx"
"Baraa tayani hira bane ko ciwon kan xe rabamu"
Tayi fari da ido tace
"Babu mai rabamu sai Allah"
 "Hakane? "Ehh..ko kana shakka ne"
Murmushi ya sakar mata sannan ya gyara kwanciyarsa ya jawota a jiki ta kwantar da kanta a hnkli ta fara magana
"Mr president am so..sory nasan kana da juriya har ka xauna tsawon 1yr + baka taba Neman hakkinka ba duk da nasan cewa kana bukatar hakan, don Allah ka yafemin duk laifinda na aikata am sorry from....

  "Shhhhh....Aysha ke nake so ba jikin ki bah, kuma na yafe miki. Idan har kina tare dani bana bukatar komai ok!
Ta daga kanta Suka hada ido yana murmushi yace 
  "Yes! Am ok..don't worry about me"
Wani tausayinsa ne ya kamata ta rungumeshi sosai tace
  "I love u so much...Allah yabar min kai har abada , kuma daga yau ni taka ce sai yanda kayi dani am all urs"
Kankameta yayi a jikinsa yana jin wani irin shauki nan Suka fara kissing din juna daga nan kuma Suka fada wata duniyar..ya rabata da kayan jikinta sannan yasa hannu a switch ya kashe wuta, wani salon romance ne shuairat tayi amfani dashi ta birkita kwakwalwar mr president tmkar bai taba sanin wata mace a duniya bah gaba daya ya fita hayyacinsa sai sambatu yake ..........



Hmmm muje xuwa
[2/21, 2:40 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*61*
By *Reefat yahya*


Mr president ma ba tayan baya bane gun Iya sarrafa mace hmmm...wadan nan masoyan sun Lula sararin samaniya😜😜 sun Dade suna romancing juna kafin ya shigeta gaba daya basa ckn hayyacinsu, shuairat taji jiki kam ba laifi suna ta Abu daya har 3 kafin Suka sagaita nan kuwa ya kankameta a jikinsa sosai sai hawaye yakeyi duk da xafin da take ji bai hanata jin tausayin mijin nata bah a hnkli itama ta rungumesa bayan hnklinsa ya dawo jikinsa cak! Ya dagata xuwa toilet shi da kansa ya mata wanka sannan ya hada mata ruwan xafi yace ta xauna a ciki babu gardama ta xauna duk da radadin da takeji hakan nan ta hakura ta cigaba da xama a ckn shikuwa ya koma dakin ya cire bedsheet da Suka bata ya bude wardrobe ya fitar da wani ya shinfida sannan ya dawo ya sameta tana wankan tsarki daga nan ya dauketa ya shinfideta a gado ya rufa mata bargo sannan ya dawo yayi wanka . nafila yake yana kuka yana godewa ubangiji da irin ni'imomin da ya basa a rayuwa , shuairat kuwa tuni bacci yayi gaba da ita.
Da asuba ya tasheta ya taimaka mata tayi sallah sannan ta koma bacci.

11am ta bude ido ganin anti mairo tayi a gafen gado tana jera kwanukan abinci ckn mamaki ta tashi
  "Anti ..
"Ah..Ya'r albrka har kin tashi ne, muje kiyi wanka kixo kici abinci koh"
Ba gardama ta tashi dakyar take Iya tfya anti mairo CE ta taimaka mata tayi wanka sannan ta hada mata ruwan xafi Wanda aka tafasa shi da magarya da bagaruwa tace ta xauna a cki, haka ta xauna kamar xatayi kuka bayan ta gama ta fito ta shirya ckn doguwar Riga lipgloss da powder kawai ta shafa sannan ta xauna cin abinci.farfesun kifi ne yasha hadi da kuma soyayyar dankalin Hausa sai kuma soyayyen kwai, tana ci mr president ya kira wayarta ta daga yana tmbayarta ya jiki.
Haka yinin ranar gaba daya anti mairo ce ke kula da ita, ko falo bata je bah mr president kuwa bayan kowane awa 1 sai ya kira yana aiki amma hnklinsa na gun shuairat. Kwana 2 anti mairo tayi tana jinyarta ta warke sumul kamar ba ita ba, daga nan ta shirya ta koma bayan tasha kyaututtuka gun mr president.

 10:30pm tana kwance tana chatting a watsap ita da princess maimah tana korafin son ganin pix nata haka nan itama dukkansu basu taba saka pix nasu a dp ba sai na cartoons ko na couples shuairat tace nikam nafi son muhadu face-face ne"
 "Allah koh..tohh ynxu haka ina Abj kefa?
  "Uhmm...nima haka toh yaushe zaki zo gidan mu"
   "A..ah ke zaki fara xuwa gidan mu"
  "Naki wayon"
"Toh shikenan na yarda zanxo  jibi, xan kiraki"
  "Ok toh..ina jira"
"Let's sleep bacci nake ji"
"Ok nyt" daga nan shuairat ta kashe data dinta cos shukrah bata online. Wayarta ya fara ringing mr president ne bata daga bah ta tashi ta fada wanka bayan ta fito ta shirya ckn kayan baccinta masu daukan hnkli ta fesa turaruka da humra ta jefa chewing gum din orbit a bakinta sai qamshi yake sannan ta rike hijabinta ta nufi hnyar xuwa dakin oga..
   Yana kwance ya kurawa ceiling ido baiji shigowarta ba ta jefar da hijabin a gefe ta fada a jikinsa wani dogon numfashi yaja sannan ya sauke idanunsa a kanta
  "Ohh my lady kin tsoaratani"
  "Haba..babba dakai"
"Ehh.mana banji shigowarki bah"
  "Soryy..but tunanin me kake yi"
"Tunaninki nake" ya fada yana kallonta ta juya ido sannan ta xagaya hannayenta a bayN wuyansa tace
  "Toh..ba gani bah"
"Yeah..am hpy to c u" ya hada lebensa da nata ya fara kissing a hnkli tun tana nokewa har ta fara maida martani haka Suka cigaba sai kuma ya fara shafa duk ilahirin jikinta a hnkli yake wasa da kirjinta nan ya turata ta fada kan gado ya susuce ganin yana Neman wuce gona da iri yasa shuairat ta fara kuka Amma ina..kamar kara tunxurasa take dakyar ta bude baki tace
  "Plss...kasan ban gama warkewa ba fah..
A wahalce yace
  "I knw baby ..don't wory a hnkli xanyi pls"
"No..."
Daga nan ta turashi gefe ta tashi ta xauna tana rawr jiki ya runtse ido ckn bacin rai ya juya yana kallonta kawar da kai gefe tayi ya tashi zai fita a hnkli tace
  "Am sorry..
Tsaki yaja yayi ficewarsa xuwa falo ta rike kai innalillahi! Badai fushi yayi bah, Allah ka yafe ni"
Ckn axama tabi bayansa yana xaune da gorar ruwa a hnnunsa ya kurba sannan ya ajiye a hnkli ta karasa ta sunguna a gabansa
    "Am sorry swt hrt ka yafemin pls"
"Tashi ki koma daki"
"Don Allah kayi hkri pls..
Kawar da fuskarsa gefe yayi nan ta tashi ta xauna a saman cinyoyinsa ta rungumesa tana kuka tana cewa 
   "Pls dad sultan ka yafemin kasan mala'iku xasu tsine min kuma ubangiji ma yana fushi dani pls am sorry"
  Yana shafa kanta yace
"Baby baki jin magana ..toh na yafemiki shikenan?
"Da gaske?..tank u so..much😘
Ta manna masa peck a kumatu kai yarinyar nan xata haukatashi bakinta takai dai2* kunnensa tana yawo da harshenta ckn kunnen ..hmmm sauran kadan mr president ya suma baiyi wata2* ba ya dagata sai bedroom dinsa.acan Suka Lula duniyar masoya yaukam bata ji xafi sosai bah ita kanta tayi sambatun bare oga kam🤔hmmm..se a slow sau3 yayi sannan Suka kwanta manne da juna har bacci ya sace su.

10am mr president yana xaune a conference room suna meeting sai faman murmushi yake yana lumshe ido shi kadai yana tuna Daren jiya tabbas shuairat daban ce a ckn mata tana da abubuwa da dama Wanda ....
    "Mr president sir! 
Firgit ..ya juya yaga an xuba mishi ido wani senator ne yace
 "Are u ok sir?
"Sure..am ok! Yeah...
Yana girgiza kai tmkar Mara gskiya sannan yayi gyaran murya yace
"So! Wat am I saying"
Gaba daya Suka juya suna kallon juna dakyar dayansu yace
  "Sir! We are discussing about your trip to China"
 "Waat? No..no.no pls...maybe mr Joshua will represent me"
 
"But sir! Its very important n u....
"I said am not going daz final" ya fada ckn daka tsawa daga nan ya tashi 
Yana hushi sannan ya bar dakin taron kowa yana mamakin wannan al'amarin bash ne ya shigo a matsayin p.an sa ya basu hakuri kan cewa zai shawo kan al'amrin nan Suka sanar dashi lallai ya gaggauta yin hakan saboda muhimmancin tafiyar kuma gobe ne ya kamata su tafi don meeting na duniya gaba dayane zaayi a can kan tattalin arxiki don hada kasuwanci da kasar China.


Ku biyoni😘😘😘
[2/21, 2:40 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*62*
By *Reefat yahya*


Dakinsa ya wuce kai tsaye ya xauna kan rest chair ya cire hularsa ya ajiye a gefe ..sam bazai Iya yin nisa da shuairat ba koda na dare 1 tlkless of sati 1 no...yana runtse ido wani daci yake ji acan ckn makwakwaronsa .
   Shuairat tana kwance a dakinta tana danna laptop wani file take saving na gidan marayu list din da aka turo mata jiya shine take shigarwa ..wayarta CE ta hau ruri yaya bash ne ta daga tare da sallama
  "Baby ki fito falo ina jiranki"
Xumbur ta tashi ta saka hijabinta a hnkli take tfy har ta fito falon yana tsaye
   "Zauna mana yaya"
"No..am ok! Dama magana nake so muyi"
  "Ina jinka"
"Mr president ya shigo ne?
   "Bangane bah...ba ya tafi office ba yacemin yana da meeting"
"Wato bby ina rokonki pls kisan hanyar da xaki bi ki tabbatar ya amince da wannan tafiyar"
     "Wace tfy kuma?
"Ana nemansu a China ne n is very important shi kuma yace bazashi bah"
   "Hmmm..mr president akwai rigima, don't wory I'll talk to him"
   "Ynxu fah...pls ana meeting ne ya fita kuma dole suji daga garesa don asan shirin da xaayi na tafiyar"
   "Ok..go n continue ynxu xaku ganshi insha Allah"
Murmushi yayi yace
  "I trust mah sisy ..ina jiranki plss"
   "Worry not my guy"
Daga nan ta wuce xuwa dakin mr president bash kuma ya juya ya tafi.ta shigo yana nan xaune shuairat Ya'r duniya tana ganinsa ta sakar masa Murmushi ta karasa ta xauna a kan cinyarsa tace
   "Wane bako mukayi da tsakiyar rana haka, mr president yaukuma lfy dai ka shigo da wuri haka"
Harara ya jefa mata sannan yace 
    "Wato ma nikadai na damu dake koh...ina can na kasa tabka komai sai tunaninki nake amma ke kina nan hnkli kwance "
Ta langabe kai tace
   "Eyya...Bahaka bane fah! Nima nayi missing dinka sosai" sai kuma ta hau kissing nasa saida ta tabbatar yazo hannu sannan ta sake shi tace
  
"Now..gayamin, me yasa ka dawo da wuri haka bayan kacemin kunada meeting?
Ya bata fuska sannan yace
   "Wai tfy xamuyi xuwa China 4 1week"
  "Allah sarki..Allah ya taimaka ya bada sa'ar abunda aka je nema"
"Haba..Aysha meyasa baki damu dani bane pls"
"My man..kaima kasan ina sonka kuma baxan so rabuwa da kai koda na min1 ne but ya xama dole ka kula da aikinka hkkin miliyoyin jamaa ne rataye a wuyarka kaga dole ka sauke hakkin ko?

Yayi shiru yana sauraron kalamanta tabbas abunda ta fada gskiyane muryarta ce ya katse masa tunani
"Ni taka CE har abada babu mai rabamu sai Allah, don haka ina son ka maida hnkli kan aikinka Allah ne ya baka shugabanci ba yinka bane so u have to tank him n handle everything ok"
Kai ya gyada mata nan ya rumgumeta sosai idanunsa a rufe yana rada mata a kunne
 " tank u so much Ayshata Allah ya barmin ke tabbas ke macce ta kwarai nagode Allah ya miki albarka ya baki gidan aljannah nagode"
Murmushin jin dadi ne bayyane a fuskarta ta Dan sassauta rungumar tace
  "Tashi kaje ana jiranka"
Yana murmushi ya tashi har ya kai bakin kofa sai kuma ya dawo ya manna mata peck a goshi yace
"Lov u"
"Lov u too" daga nan ya fita yana murmushi yana godewa Allah da ya hadashi da mace ta gari.
      A can conference room sun fara surutun rashin ganin mr president kwatsam! Ya shigo fuskarsa dauke da murmushi sunata mamakin wannan al-amrin haka aka cigaba da meeting daga karshe aka zabi wadanda xasu raka mr president a yayinda mr Joshua kuwa xai xauna ya kula da harkokon kasar.
Ba karamin murna bash yayi ba da ganin mr president lallai kanwarsa tana ja😜😜.

Bayan sallar isha ta gama shirya kayan da mr president xeyi tfy dasu tana kwance a dakin ya fito daga wanka bayan ya gama shirinsa tsaf yana kallonta yana murmushi yace
  "Baby I have somtin 4u"
"Aw..da gaske?
"Ehh.. Nan ya rike hannunta Suka fito falo wata Ya'r karamar kofa Suka bi ta bayan gidan Suka bullo suna tfy can sukaje garage inda yake ajiye motoci nan yaje kusa da wata katuwar mota an rufeshi da wani bakin kyalle a hnkli mr president yace ta rufe idonta bayan ya irga 3 ta bude guess wat😳😳h..........mmmmmmmmmmm....nikam saida na fadi a kasa shuairat ta bude ido a hnkli wata arniyar lemo CE fara Sol...yeah lemozin da kuke ji ko kuma kuna gani 😃😃 motar da take da komai a ciki ga  kyau da tsada idan xaa kirga masu shi a duniya ma kalilan mutane ne basu da yawa☺☺.shuairat kam shiru tayi ta kasa cewa komai , daga nan ya sake nuna mata wata hadaddiyar Ferrari baka wuluk yana murmushi yace 
"Dis my gift 4u na mallaka miki su duniya da lahiraa"
Hawayene Suka gangaro a kumatunta yayi saurin riketa yace
 
"No..pls bana son kuka"
Daga nan ya dagata cak! Suka koma ckn gida a dakinsa ya ajiyeta yace

"Cloz ur eyes again"
Ta rufe idonta alamar takardu taji a hannunta ta bude ido yana murmushi yace

"Ki duba ki gani"
Takardun filayene guda 5 😳😳 daya a mubi, yola, Lagos,2 a Abj .habawa ta rungumesa tana hawayen farin cki

"Tnk u soo..much Alllah ya biyaka nagode sosai"
Ita kam ta rasa wane irin godiya zatayi tace 

"Bani da abunda xan biyaka dashi bansan da wane baki ko kalamai xan gode maka bah..nagode nagode I Lov u so much" 
Ta kara shige jikinsa yana murmushi yace

"Bana bukatar komai ..fatana ki soni ki zauna dani ki haifamin yara masu kama dake"
Ckn jin kunya tace

"Ina sonka kuma har abada baxan barka komin tsanani komin wuya insha Allah, yara kuma Allah ya kawo masu albarka"
"Ameen"


Nima reefat nace
 ameeeennnn.......
Ku biyoni😘😘
[2/21, 2:40 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*63*
By *Reefat yahya*


Sun dade suna rungume da juna sannan shuairat ta sakesa ta juya ta koma dakinta wani sabon wanka ta sake yi ta fito ta shafa mai ta gama shirinta ckn wata doguwar vest Iya cinya ko ina qamshin turare ne me tashi a jikinta ta dauko wayarta tana duba tym new mssg tagani tana budewa 😱😱😱 tsayuwa ya gagareta dakyar ta xauna ta kurawa wayar ido..alert ne daga bankin first bank kudi kimanin 500mil😜😜 tunda take a rayuwrta bata taba shiga irin yanayin da take cki bah gaba daya ta rikice nan kuwa ta tashi ta koma dakinsa yana kwance ya gama shirin bacci ta shigo ckn sanyin jiki hannu ya nuna mata alamar ta taho gunsa ta fada jknsa sai kuma ta fara kuka hnklinsa ya tashi ya fara rarrashinta dakyar ta daina kukan ta gaya masa batun alert da ta gani dariya sosai ya dinga yi yace
"Ki kwantar da hnklin ki dama akwai allowances na first lady shine na hada da kyautar da nayi niyya na bayar aka tura miki a account"
Godiya sosai tayi sannan Suka kwanta bacci a wannan Daren shuairat ta faranta  masa sosai gaba daya tana Neman haukatashi da kalan soyayyarta ta kware sosai haka nan itama ta kasance ckn farin ciki.


Karfe 6:30am suna airport a ckn mota suke dakyar mr president ya banbareta a jikinsa shima yaji wani iri tmkar ya fasa tfyar ya cigaba da kwantar mata da hnkli sannan ya fita ya barta ckn motar taku 2 yayi ya sake dawowa ckn mota ya rungumeta gam a jiki yayi pecking nata a goshi yace

"I Lov u Aysha ki kular min da kanki da kuma ya'yana da dukiyata"
 Daga nan ya juya ya tafi wani sabon kukane ya kubce mata driver ya shigo ya tada mota Suka dau hanyar gida.
A ckn jirgi sai faduwan gaba yakeyi idan ya tuna halinda ya bar shuairat a cki Allah sarki shuairat yarinya me hnkli haka dai mr president ya cigaba da tuna kyakkyawar fuskar matar tasa .
Shuairat kuwa yinin ranan sukuku tayi shi bata ckn walwala ko abinci ta kasa ci wayartace ta hau ruri princess maimah ce dakyar ta daga

"Kawata ya kke"
"Lfy princess ya gida"
"Lfy alhamdulillh dama ina son xuwa gidanku ne"

"Allah..gskiya naji dadi sosai "
  "Kibani address dinki"
  "Uhhmm..ynxu haka dai bana gidan mu naje villa ne"

😳"😃 really...kina ckn gidan ynxu haka?
  "Ehh...
"Wane side?
"Ke dai idan kinxo bakin gate ki kirani"
"Ok toh"...

1hr leta..phn din shuairat ya fara ringing princess CE
"Kina ina"
"Na shigo ina ckn gidan"
"Ok kice a nuna miki bangaren mr president xan jiraki a bakin kofa"
Shuairat ta fito tana tsaye umaima taxo tayi  shigewarta shuairat ta tabe baki tace kya jida shi"
Umaima CE ta sake fitowa wayarta ta xare tana danne2* can ta kara a kunne dai2* lokacin phn din shuairat ya fara ringing
"Hello princ...
Ckn mamaki da raxana Suka juya suna kallon juna
Wayar hannun umaima CE ta fadi a kasa ji kake kasssss.....
Screen yayi hali...





Hmmmmmm ...muje xuwa
[2/21, 2:40 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*64*
BY *Reefat yahya*


Sun dade suna kallon kallo sannan shuairat ta wuce ckn gida falo ta nufa ta xauna tana sauke numfashi har ynxu tana mamakn wannan al-amari wai umaima CE princess da suke chat a watsap...umaima ta shigo ckn mutuwr jiki ta xauna sunyi shiru can umaima ta daga kanta a hnkli tace
   "Ynxu dama ke kanwar bash CE?
Murmushi shuairat tayi ta gyada kai alamar ehh..shiru Suka sake yi umaima kam mamakine karara a fuskarta sai kuma ta tuna irin abubuwan da takewa shuairat a matsayin matar mahaifinta nan taji wanni kunya ya kamata anya burinta na son auren bash xe cika? Ita kam bata San ta ina xata fara bah ta juya Suka hada ido shuairat kam se murmushi take umaima tana son bada hkri Amma girman kai ya hanata don haka ta tashi ta koma bangarenta.
    Shukrah ce tazo mata ta Dan debe mata kewar rashin mjin nata a kusa haka Suka kasance tare da sultan shi kuma yaxo yana wasa da waleed don sultan akwai son yara shukrah ta kalli mutuniyar tata tayi Murmushi tace
"Ikon Allah ...an fada tarkon so hmmm!

  "Nifa bana son gulma azo gidanka ana sa maka eyes"
Shuairat ta fada tana murguda baki
Shukrah ta kwashe da dariyan mugunta tana mai cewa

"Allah sarki wata tayi missing din mijinta...hmmm ko 1 day baiyi ba fah baby"

   "Wai ke kwantar min da hnkli kika zo yi ko me?

"Oho..nidai ina son kiyi accepting cewa u r inlov daz ol"

   "Ok fine shukrah.. Shuairat is inlov wit her gorgeous Darling husband, Alh Suleiman Mohammed shikenan!
Habawa me shukrah xatayi inba dry ba tayi mai isarta sannan Suka cigaba da yiwa juna shakiyanci.
    Haka Suka kasance har dare suna xaune shukrah tana sanyawa waleed kaya saboda suna shirin komawa bash yana kan hanyar xuwa maidasu gida. Umaima ta shigo tare da sallama shuairat CE kawai ta amsa shukrah kam ko kallo bata isheta bah ..Sam! Ta tsani yarinyar umaima ta lura da rashin amsa sallamar da tayi ta tabe baki ta nemi kujera ta xauna can ta juya gun shuairat tace
  "Amm...mom sultan nace bah..

Shuairat ta juya tana kallonta tana mmkin sabon sunan da ta kirata dashi *mom sultan* sabanin *ke* da ta saba 
"Nace kunyi waya da dad ne layinsa baya shiga"

    "Wllhi bamuyi bah..even me am worried Allah yasa dai lfy"
    "Ameen...maybe yana busy ne"
Shuairat tace 

"Ga matar bro dina Ku gaisa..
Shukrah ga umaima"

"Sannu koh..
"Yawwa ..kema sannunki"
Shukrah ta fada a takaice tana mai yatsina fuska umaima tabi ta da kallon mmki gaba daya shukrah ta canza don tana da pix din aurensu , tayi kiba ta kara hske tayi kyau sosai sai kace matar wani minister lallai bash ya Iya kiwo Amma ta rasa meyasa shukrah ke daure mata fuska haka ko meyasa oho! Ta tashi tayiwa shuairat saida safe abunda bata taba yi ba duk Iya tsawon xamansu a gidan a bakin kofa Suka cikaro da bash saura kadan su buge juna yayi saurin komawa da baya ta sunkuyar da kai kasa tana murmushi
 "Sorry...
Kamar hadin baki suka  furta Kalmar tare murmushi Suka sakarwa juna dai2* nan shukrah ta hangosu wani kululun bkn ciki ne takeji tmkar ta shake wuyan umaima😳🙊shukrah akwai xafin kishi nan ta tashi ta karasa wajensu tace

  "Bbn waleed tun dazu ina jiranka shine kazo ka tsaya bayan kasan munyi missing diinka sosai nida waleed"
Tana magana ckn wani salon makirci umaima kam xuba mata ido tayi tana kallon ikon Allah 

  "Ok sorry gani nan xuwa koh" ya fada kai tsaye shukrah ta juya tana hararin umaima ita kuma tayi wani guntun murmushi kamar cewa zanyi maganinki tayi saurin cewa

"Ohh..namanta zamuyi magana ynxu pls idan baxaka damu bah ka roki matarka ta bamu aron 10min pls"

"Sure..ba komai muje waje kiyi maganar"
Suka sakarwa juna harara shukrah ta koma ckn falo umaima kuwa tabi bayan bash Suka fita waje .
    Shukrah ta koma kan sofa wani irin radadi take ji sai huci take kamar zakanya tace 

   "Hmmm...yarinyar nan xata ci ubanta wllhi xata San dani takeyi, hmmmmm..."
Abun yaso bawa shuairat dariya ta danne tace

   "Wacce...
"Mtswww...wacece kuwa idan ba umaima ne ko me take da suna..

"Me tamiki best"
Da gangan shuairat tayi tmbayar shukrah sai karkada kafa take tace

"Dallah..karki rainan wayo, xaki CE baki lura da take taken bane..kina gani tana kashewa yayanku murya tana wani yanga...mtswww xata gane batada wayo..hmmm mijina take so koh? Tahmmm...xanyi maganinta"

"Chill..bestie kibi a hnkli kinga...

  "Ke dakata malama! Nabi a hnkli? Lallai ma baby hmm...toh ba dai ni bah wllhi babu wata shegiyar da xata shiga tsakanina da mijina"

"Ah'ah shukrah abun bai kai hakaba Allah ya huci xuciyarki"

"Yakai harma ya wuce ..ahaf aikin banza Allah ya huci xuciyata? Daga baya kenan wai anyi sadaka da karuwa...mtsww"
😂😂😂😂

Shuairat kam taja bakinta tayi shiru daga nan ta dau sultan ta kaishi daki ta dawo remote ta dauka ta kunna TV tashar CCTV ta kama ta koma kan sofa ta gyara kwanciya shukrah kuwa tana cika tana batsewa.
     Wani jirgi aka nuna ya fadi dayan bangaren jirgin duk ya kone ana fitoda gawarwaki shuairat ta gyara xama tana xare ido innalillahi take nanatawa sai kuma repotern ya fara magana ckn yaren China ana fassarawa da turanci

*yau da yamma ne akayi hadarin jirgin sama a kusa da garin Beijing ta kasar China an samu I'd card din matattun da kuma lambar jirgin Wanda ya nuna cewa jirgin ya fitone daga kasar Nigeria , bayan munyi bincike da hukumar kula da jiragen sama ta kasar Nigeria anshaida mana cewa jirgin yana dauke da jamaa da dama cki kuwa har da shugabankasa kasar.....* kunnuwanta basu karasa jin Kalmar karshe bah ta sake wata irin razananniyar kara ji kake timm! Ta fadi kasa bata ko motsi shukrah ta rude ta tashi tana taba jikinta Amma inaa...dai2* nan bash tare da umaima Suka shigo ckn tashin hnkli bash yana tmbayar lfy..shukrah se kuka take tana cewa
  " mr president ne Allah yayi masa rasuwa ynxu muka...

Wani gigitaccen mari umaima ta ajiye mata idanunta sun rikide xuwa kalar ja tace
  "Karya kike munafuka..karyane mahaifina bai mutu bah...

Tohfah...yau akeyinta 😱😱😱😭😭😭😭 masu karatu shin da gaske mr president ya rasu?
Ana surviving hatsarin jirgi kuwa?
Shin ya shuairat xata yi kodai itama mutuwar tayi?
Ya rayuwar umaima xata kasance?

Ku biyoni...mai fatan nishadantar daku
*Reefat CE* hop u enjoying d story....dis is just d beginning
4 comments o correction ~07030077024~
Bana editing so don't wory abt typing errors😘😘😘
[2/21, 2:40 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*65*
By *Reefat yahya*


A hnkli ta bude idonta tana bin dakin da kallo sai kuma ta tuna abunda ya faru hawaye ne ya fara gangarowa a gefen fuskar ta bash ne ya shigo tare da momsi suna mata sannu suna hada ido da momsi shuairat ta fashe da kuka nan Suka fara bata hakuri

"Momsi da gaske ne mr president ya rasu?
  "Shhh...mr president yana nan ki kwantar da hnkli"
Ta xare ido ckn tsananin mamaki 

"Hw comz"
"Ikon Allah kenan..ya'ta, Allah ya kaddara da sauran numfashinsa a doron kasa..ynxu haka mun sami lbrin cewa su 2 Suka rage a ckn jirgin suna can asibiti a Beijing"

"Alhamdulillh..
Ta furta a hnkli tare da ajiyar xuciya tana kokarin tashi xaune sai ynxu ma ta lura da drip da aka saka mata 

  "Ina sultan da umaima"

"Suna nan ki kwantar da hmklinki ga abinci nan ki ci"
Momsi ta deba mata abinci dan kadan taci tace ya isheta sai ynxu ta daga ido ta kalli agogon dake makale a dakin 8am lallai ta Dade a kwance nan ta koma tayi kwanciyar ta bada dadewa ba akayi sallama Muryar mamanta CE nan ta juya Suka hada ido mamace tare da shukrah Suka shigo tana ganin haka ta fara kuka dakyar aka rarrasheta daddy ne ya sake shigowa

"Ah..ta farka ne..alhamdulillh ya jikin de Aysha"
"Da sauki"
"Masha Allah..kici abinci ki kwantar da hnklinki mijinki yana nan a raye ynxu haka xamu tafi nida yayanki kinji koh"
Kai ta gyada masa daga nan sukayi sallama shi da bash akan xasu tafi China  don ganin halin da mr president yake ciki.
  Haka jamaa Suka dinga xuwa jaje gidan kullum cike yake makil da jama'a mr Joshua kuwa kullum sai ya shigo ya duba lfyar yaran tare da shuairat. Umaima ta rame kullum ckn tunani take tana yiwa mahaifinta adua haka nan shuairat ma ta warke se yawan tunani shiyasa momsi take matukar bata kulawa ta musamman.bash tare da daddy sun share 2 weeks kafin Suka dawo akan cewa yana samun sauki Amma shuairat kam Sam hnklinta bai kwanta bah don haka ta dage cewa xataje ta kula dashi babu yanda Suka Iya dole daddy ya amince aka mata visa ta faran shirin tafiya..bash yace tare zasu tafi firr taki yarda tace ya xauna ya kula da yara hakan kuwa akayi daddy da momsi sun shirya sun koma Lagos  sultan kuwa gidan mama aka turashi can xai cigaba da xama umaima kuwa bash yace a gidansa xata xauna ba don tana so ba dole ta amince da haka.
Shuairat ta tattara motocinsu da nata da na mr president ta aika gidansu tare da duk wani Abu mai muhimmanci ta tura can daga nan taje sukayi sallama da iyayenta baba ya mata nasiha sosai daga nan ta koma gidan babu dadi sam .

Jirgin 7 Suka bi ita da bodyguard din da xai rakata bayan ta xauna ta fara jera aduoi kam😀😀 don ynxu ta tsani jirginma kwata2* .bayan sun sauka taxi Suka shiga xuwa doushin hospital ga yan China nan birjik kowa na shaanin gabansa babu mai kula harkar wani har dakin aka nuna musu Suka shiga yana kwance ckn coma ko motsi baya yi ga na'urori daban2* a manne ajikinsa shuairat tana ganin haka ta fara kuka bodyguard din yana bata hkri daga karshe ya mata sallama ya tafi ta kura masa ido yana kwance tmkar matacce haka ta cigaba da xubda hawaye babu mai bata hkri har ta gaji don kanta ta daina.toilet ta shiga tayi alwala ta fito da abun sallar ta nan ta biya duk sallolin dake kanta tana idarwa ta koma kusa dashi ta xauna tare da kura masa ido.gashi dai babu rauni sosai a jikin nasa Amma baya motsi lallai ikon Allah kenan, Allah mai yin yanda yaso da bayinsa.wata nurse CE ta shigo nan ta wuce ta dudduba na'uororin ba tare da tayuwa shuairat magana ba , allura ta saka ckn ledar drip din sannan ta juya ta fara yarensu murmushi shuairat tayi sannan ta nuna mata bata jin yaren yarinyar ta fita bayan mintuna kadan ta dawo tare da wani saurayi.
Murmushi yayi sannan ya fara magana da turanci
"Sunana baek San chu..ni ma'aikacin wannan asibiti ne, mr president yayi loosing memory dinsa..
😳😳innalillahi nan hawaye ya wanke mata fuska .
Yace
  "Kiyi hkri ki kwantar da hnklinki xan warke very soon ana bashi kulawa ta musamman, kuma Chinese president ya aika a wuce dashi Hong Kong gobe..he is lucky to survive a plane crash"

Daga nan yacigaba da bata hkri da kalamai masu kwantar da hnkli Daga karshe Suka tafi Suka barta ita kadai.daddy ya kirata sun Dade suna hira nan ta sanar dashi komai ya bata momsi Suka gaisa tana gamawa wayar bash ya shigo nan ma sun Dade suna magana har umaima ma ta karba Suka gaisa tana tmbyn jikin mahaifin nata. 
      Haka shuairat ta kasnce ckn xaman kadaici ko yunwa bata ji dakyar bacci ya saceta.da safe tayi sallah ta watsa ruwa sai ynxu ta fara jin yunwa ba bata lokaci ta xari kudin ta fita wajen harabar asibitin , babbar asibiti ne na kudi ga kyau tana tafiya tana yan dube2* har bakin gate bata ga alaman shago bah , ta fita waje ne ta hango stores a tsallaken titi daga nan ta wuce ta shiga wani super market mai kyawun gaske drinks da snacks ta dauka sai kuma grapes n apple ta biya kudin ta koma ckn asibitin dakyar ta gane dakin.bayan ta gama ci tana xaune baek San ya shigo tare da wasu mutane ckn bakaken suit yana murmushi ya fara magana da turanci

" dafatan ki tashi lfy"

"Lfy kalau "
"Ga wadannan daga fadar shugabankasa aka turosu sunxo da private jet xaku tafi tare xuwa babban asibiti acan hong Kong "

Shuairat ta gyara akwatin ta daga nan aka kawo wani gadon tura marasa lfy nan aka dora mr president akai Suka wuce xuwa wata katuwar mota mai kyau sai Suka wuce filin da aka ajiye private jet din don xuwa hong Kong....


Muje xuwa Lov u all
[2/21, 2:41 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*66*
By *Reefat yahya*


A fadar shugaban kasar China akayi musu kyakkyawan tarba nan aka basu masauki mai kyau ckn kankanin lokaci aka shigar da mr president ckn wani daki dama can likitoci suna xaman jiransa nan take Suka fara aiwatar da aikinsu, shuairat kuwa an kaita wani bangare mai kyawun gaske babu bata lokaci ta fada wanka tana fitowa ta xauna gaban madubi tana kallon kanta ..tabbas ta rame sai Dan hasken da ta karayi tana nan xaune ta buga uban tagumi wayartace ta hau ruri tana dubawa taga layin umaima ta daga 
 "Hello princess ya kke"
    "Lfy anti ya jikin dad"
"Alhamdulillh da sauki"
 "Allah ya bashi lfy"
    "Ameen..hop kina lfy koh"
     "Uhmm lfy alhamdulillh"
Daga nan sukayi shiru hawaye ne ya cika idanun umaima tabbas tayi nadamar tsanar da ta nunawa shuairat a da can baya 
   "Hello princess yadai"
   "Lfy ba komai"
"Ok toh..takkia koh ynxu muka sauka a hong Kong bari na huta xan kira anjima"
  "Ok bye"

Daga nan Suka kashe wayar tare shuairat tana mmkin sauyin umaima ko don rashin lfyn dad dintane oho..nan ta shafa mai ta fesa turare, doguwar Riga ta saka mai kyau daga nan ta fita falo ta kunna TV tana kallo ammaa Sam hnklinta baya wajen ta kurawa TV ido amma tunaninta yana gun mr president.. Allah sarki kamar yasan abunda xe faru dashi yaki amincewa da tafiyar ita ta tilasta mishi , daren da zasu rabu ta fara tunawa..dare ne me kunce da so da kulawa Wanda baxata taba mantawa dashi ba har karshen rayuwarta..hawaye ne Suka diga a fuskarta ba tare da ta sani bah

"Excuse me!
Wata murya taji yasa ta waigo wata yar budurwa ta gani kyakkyawa bazata wuce 25yrs bah dakyar shuairat tace
  "Yes! How may I help u"
Yarinyar ta mika mata hannu tana murmushi

"Gum jankim n u"
"Shuairat"
"Shu..??
    "Shu..ai..rat"
"Wow nice name shu..-ai...-rat..." 
Ta sake maimaita sunan nan ta xauna ta shaida mata cewa ita likita CE a america tayi karatu an daukota ne don kulawa da mr president a nan hong Kong take aiki a can babban asibitinsu.
    Shuairat taji dadin xama da jankim sabida yarinyar akwai raha da fara'a tana da saurin sabo ckn kankanin lokaci shuairat ta sake da ita sosai suna hira ta Dan ji saukin damuwar da take ciki.


**********
Umaima tana xaune tayi jugum tana tuanin duniya da abunda ke cknta rayuwarta na baya ta fara tunawa har xuwa rasuwar mom da kuma auren dad da shuairat da irin cin mutuncin da ta dinga yiwa shuairat.. Allah sarki yarinyar akwai hkri ko kadan bata taba nuna damuwa ba duk irin rashin kunyar da take gwada mata, ga irin kulawa da take ba sultan ga sanin darajar Dan Adam ga fara'a ga yawan taimako ga kuma saukin kai..shuairat bata dau duniya a bakin komai bah ..Sam abun  duniya baya rufe mata ido, hmm ita umaima ga girman kan tsiya ga kallon banza da kaskanci ynxu duk ina suke? Dad da take ji da kanta don ta kasance yarsa ma ina yake yau? Yana kwance rai a hannun Allah ko zai tashi ko baxai tashi ba wallahu Ahlam ..duniya kenan wata ran naka wata ran kuma na wasu shiyasa ake son mutum ya dinga hangen nesa ya tuna gobe.. Hawaye ne Suka wanke mata fuska tana mai jin haushin rayuwar da tayi a can baya.girman kai ya hanata samun kawaye haka nan ma samari , gani take tmkar tafi karfin kowa..Ashe ba haka abun yake bah, lallai ko ynxu ne ta karanci menene duniya tabbas duk...........garam!!!!! Banko kofar dakin da akayi ne ya dawo da ita daga dogon tunanin da take shukrah CE ta watsa mata kallon tsana ckn daga murya tace

    "Munafuka! Kukan me kike yi? Kinzo kin share gindi kin xauna wato gaki ya'r gwal koh? Toh bazata sabu bah..maxa ki tashi kixo ki min wanke2* don ni ba ya'r aikin gidanku bane shegiya ba kina son mijina bah...hmmm mu xuba nida ke"

Umaima ta sunkuyar da kai kasa ta fara kuka Mara sauti..wannan wace irin rayuwace? Yau ita CE zatayi wanke2* ? Yau ita akewa gorin gida? Allah sarki duniya juyi..dad ta tuna nan ta kara fashewa da kuka Allah ya bashi lfy.shukrah ta fara tafa hannu
  "Iyye..lallai ya'r gwal kenan.. Wanke2*n yake saki kukA? Ah..lallai kina da aiki babba don kuwa ynxu muka fara wllhi, ba kin bi mijina kika zo min gida kince zaki xauna bah? Toh sai ki koyi xama dani Dan wllhi sai na koya miki  hnkli xaki gane borno gabas yake"
Daga nan shukrah ta juya tabar dakin , umaima ta tashi tabi bayanta kitchen Suka nufa..kwanukane tirim a ckn sink ga nan wasu ma a kasa daga nan ta fita tana dariyar mugunta umaima kuwa kuka takeyi tmkar ranta xe fita.
  Bash ya shigo falon ba kowa amma ya ji motsi a kitchen kai tsaye yaa wuce tana xaune ta hada kai da guiwa tana kuka ckn hnzri ya karasa

😳😳" innalillahi! Umaima meya faru kike kuka"
Batayi magana ba ta cigaba da kukan taba daya hnklinsa ya tashi ya fara rarrashinta dakyar ta sagaita kukan ta daga jajayen idanunta

  " don Allah yaya bash ka taimaka ka kaini gun anti shuairat ina son ganin dad pls"
  "Is ok ..ki gayamin me ya faru? Wani Abu shukrah ta miki?
Shiru tayi bata CE komi ba ta sake fashewa da kuka tace

  "Nikam don Allah ka kaini ko ina baxan xauna a wannan gidan ba"
    "Ok kiyi hkri koh..muje xan kaiki gun mama na xaki xauna dasu ? Kinga sultan ma yana can nasan kinyi kewarsa daz y"
Kai ta gyada masa alamar ta amince nan ya rike hannunta Suka tashi tsaye a dai2* bakin kofa Suka ci karo da shukrah tana shiga..😳😳😱😱ta xare ido ckn takaici tace

  "Me zan gani haka? Wanke wanken da na saki kenan? Shine zaki kira mijina a waya..sannan har da rike masa hannu? 
Aikuwa shukrah ta daga hannu xata kaiwa umaima mari bash yayi saurin rike hannun ya fara magana
   "Haba shukrah behave urslf mana.. Meyasa kike yin Abu as if u ar not matured"
  "Which kind matured..wllhi bazan yarda ba ai wannan cin fuska ne"
  "Naji..is ok toh kiyi hkri ni na rike mata hannu n am sorry ok! Batun wanke2* kuma kiyi hkri bata saba ba kinga amanarta aka bani n I have to takkia of her "

  "Haba baban waleed ynxu aiki ma ban isa in sata tayi ba sabida an baka amanar ta? Allah is not fair"
Shukrah ta fara xubar da hawaye bash ya sake hannun umaima ya jawo shukrah a jiki yace
   "Am sorry pls ki daina kukan nan kinsan bana so..n bawai na hanata bane wllhi am sure bata iya bah "
     "Kai dai kace min sonta kake shiyasa dama ka kawo ta nan gida saboda Ku dinga ci min face toh wllhi baxan yarda bah"
Ya juya gun umaima yace
  
" kije dakin ki ina xuwa" daga nan ya ja shukrah Suka bar kitchen wani kishine ya turnuke umaima nan ta koma daki ta cigaba da kukanta tasan lallai ta rasa bash har abada idan ta tuna yanda yake lallaba shukrah sai ta ji wani tsananin kishinsa..hmmm anya burinta ze cika?








Muje xuwa😘😘
[2/21, 2:41 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*67*
By *Reefat yahya*


A daki bash yake bawa shukrah baki
"Haba my love ki Dan rage kishin nan mana ai zata raina ki..kuma ni ban ce miki ina sonta ba meyasa zaki damu kanki she is just lyk a 6ter to me pls kidaina wannan haukan"
   "Ohh..hauka kace koh? Toh shikenan zaka ga haukan wllhi xanyi maganinta..zancen so kuma ai naga kwayar idonta sonka ne zalla a ciki, wllhi bazan barta bah"
Dariya sosai bash yayi sannan yace
 
  "Hohh..shukrah! Dama haka kike da kishin tsiya?
Ta tura baki ckn shagwaba tace
  "Dariya kake min koh..wllhi ni nasan tana sonka kuma kaima kana sonta kawai boyewa kake"
  "Ok naji tana sona ..amma trust me ba komai tsakanimu kinji? Ki kwantar da hnklinki , aiki kuma idan kina janta a jiki ita da kanta xataji shaawar koya ba sai kin nuna mata karfi bah pls my love kiyi respecting din kanki ok"
Kai ta gyada masa haka nan ya lallaba abarsa sai gashi ta sakko abunka da mata da miji har ya mantar da ita xancen wata umaima ckn salon soyayyarsa nan Suka lula sararin samaniya duniyar masoya😜😜.
   Umaima tun tana sa ran xuwansa har ta fidda rai tayi kuka mai isarta lallai namiji munafuki ne ynxu ya shanyata yana can tare da matarsa yana bata kulawa hmmm ke kuma a suwa? Hakane bata dawani matsayi a gunsa haka ta kwanta a gado ckn rashin kwarin guiwa.
Bayan 1hr ya shigo dakin tare da sallama ckn shigar kananan kaya yayi kyau sosai ga sajenasa kwance luf-luff se qamshin turare ke tashi a jikinsa yayi kyau sosai umaima ta kura mishi ido babu ko keftawa har ya karasa kan kujera ya xauna fuskarsa dauke da murmushi yace
  "Em..sorry sis kinji ni shiru koh"
  "Ah..ah ba komai "
Ta furta a hnkli se yaji tausayinta ya kamashi tabbas yasan kadaici na addabarta a rayuwa bata da abokin hira se TV ko waya don bai taba ganinta da kawaye bah toh saurayi fah?ya daga kansa Suka hada ido har ynxu kallonsa take ckn tsananin kunya ta dauke kanta

  "Yadai ko nayi kama da wani ne?
"Wani? Kamar waye kenan?
   "Oho..maybe mr right"
 "Hmmm..kai kasan wannan"
" ohh..ke baki sani ba kenan, yawwa gskiya fa umaima baki taba hadani da bro-inlaw na bah ko rowarsa ake mana"
Haushin maganganun take ji wato shi bata taba burgeshi bah koh..Allah sarki baisan tana yi bah , nan kwalla ya cika mata ido

  "Umaima lfy..ko tambayan da na miki ne? Am sorry pls"
"No..is ok ba komai"
"Akwai mana..gashi kina Neman xub da hawaye ko kun rabu ne shiyasa kika tunashi kina son yin kuka"
   Ckn haushi tace
  "Ya mutu"
😝😝😝😝bash yaso yin dariya amma ya gimtse don daga ganin yadda tayi maganr yasan karyace don haka yaja bakinsa yayi shiru.haka Suka xauna har tsawon minti10 babu Wanda ya sake cewa komai don haka bash ya tashi yabar mata dakin ta fada gado ta cigaba da kukan rashin masoyin nata.haka rayuwa ta kasance ba laifi ynxu shukrah na amsa gaisuwarta kuma ta daina takura mata , waleed ya fara sabawa da umaima haka nan sultan ma yana xuwa su yini idan babu makaranta.umaima kuwa tana xuwan tasu makarantar amma har yau bata da kawaye ko abokai, mr Joshua kuwa shi yake kula da al'amuran kasar..Rayuwa kenan.


****************
Shuairat ta share wata 2 da xuwa hong Kong ynxu wata3 kenan da kwanciyar mr president rashin lfy amma har yau bai farfado bah..wani lokaci shuairat gani take tmkar ya rasu kawai boye musu akeyi bayan likitoci kuwa sun bata tabbacin cewa zai warke don haka ta dage da adu'a ba dare ba rana tana yawan karanta masa Qur'an a saitin kunne haka nan tana tofa masa wasu ayoyin, nafilar dare kuma ba'a magana .daddy da momsi kafarsu2 suna xuwa haka nan bash ma yaje sau1 umaima kam duk nacinta daddy ya hana sabida cewa yayi idan taje hnklinta zai tashi.
   Shuairat tana xaune apple ne a hannunta tana taunawa a hnkli mr president yana kwance a gadon marasa lfy na'urori ne iri2* makale a jikinsa ga kuma ledojin ruwa. Jankim CE ta shigo tana murmushi ta fara magana da turanci
 
  "Maman bby gskiya babyn nan namu mayen apple ne..kusan kullum shine abincin ki fah"
    "Jankim sarkin xolaya..wani bby kike nufi"
   Ta karasa kusa da mr president ta fara dudduba na'urorin tana gyarawa tace
   "Shu..ai..zaki cemin baki San cikine da ke bah"
    "Watt??😳😳da gaske?
   "Ehh..tun farkon haduwarmu na lura kina da ciki"
Mamakine ko murna ko bakin ciki wanne xatayi? Jankim ta bude Jakarta ta dauko kayan aikinta tace

 "Muje na gwada ki"
Ba musu Suka wuce dakin da aka tanada don likitoci babu abunda babu a ciki nan da nan ta gama test din ya nuna musu result shuairat tana dauke da juna 2 na tsawon wata 3 ciff sai kuma ta kwanta akayi scanning sun duba komi.murna ne fal ckn ranta sai kuma hawayen tunawa da halin da uban yake ciki sai kuma ta tuna cewa rabonta da period tun a najeriya daga nan suka fita sun sayi magunguna da abubuwan kara lfy har nafila shuairat tayi ta godewa Allah sannan ta roki Allah ya bawa mr president lfy .
Haka ta cigaba da rainon ckn, jankim CE ke debe mata kewa first lady ma ta dawo daga tafiyar da tayi ta jajantawa shuairat haka nan manyan mutane na yawan xuwa duba mr president wasu abokanan aiki ne wasu kuma shuwagabannin kasace daban2* ga tarin duniya da suke xuwa dashi kudade kam ba'a magana shuairat tana turawa a account don bata bukatar komai Chinese president yana matukar kulawa dasu.
   Ynxu ckn nata ya shiga wata4 ta kara cika tayi kyau sosai gwanin sha'awa tayi haske kamar me...ta shigo dakin tare da sallama kamar yanda ta saba duk tasan cewa babu me amsawa ta nemi kujera kusa dashi ta xauna ta kura masa ido
    "Masoyin yaushe zaka tashi ne we rily missed u nida little... Pls get well soon Allah ya baka lfy"
Hawayen idonta take sharewa sai me??? Alamar ya motsa ta gani tayi waje da ido ta kara masawa 
   
"My man...mafarki nake ne ko da gaske😳😳
Nan ma ya Dan motsa yatsa ckn hnzri ta gudu kiran jankim..tare Suka shigo nan ta kira likitoci ta sanar dasu ckn kankanin lkc Suka taru a dakin tabbas ya farka ynxu yana jin komai kuma memorynsa is ok a kowane lokaci zai tuna da rayuwarsa na baya don haka ake bukatan shuairat ta dinga zama kusa dashi don ya tuna komai, yana jin komai amma ba lallai bane ya fara magana ynxu .ranar shuairat ta kwana da farin ciki nafilfilu ta dinga yi bata samu bacci sai da safe sannan ta koma bacci.
Haka ta kasance ckn kula da mijin nata kullum tana bashi lbri kala2* na najeriya tare da nuna masa hotuna ..har ynxu motsi kawai yakeyi idanunsa ma a kafe suke sai daga baya ya fara ita kefta su.daddy ya xo ya dubashi yaji dadi sosai haka ya xubawa shuairat albarka nan ta nemi alfarma a gina musu gida a can najeriya kan su dawo, daddy ya shaida mata mr president yana da gidaje da dama sai dai a gyara hakan kuwa akayi yana komawa aka turawa bash kudi ya bada kwangilar sake gidan Nas dake garki babu bata lokaci aka fara aiki.

*****
Bayan wata2 Alhamdulillh mr president yaji sauki sosai har ya fara takawa tamkar karamin yaro haka ake koya masa tfy shuairat kuwa cknta ya Dan fito ta zama abunda shaawa duk Wanda ya kalleta dole ya maida ido ita take koya masa tfyar ya tuna komai na rayuwarsa na baya amma har ynxu baya son yin magana shiru kawai sai dai murmushi.
   Yau suna xaune a masaukinsu ta ajiye masa magunguna a gaba ya hada fuska da alama baya son sha nan shuairat ta juya masa baya alamar tayi fushi ba shiri taji ya rungumeta ta baya 
 "Am sorry swt hrt"
Ya mata rada a kunne ckn mamaki ta juya suna fuskantar juna
 "Mr..mr president dama kana magana? Na dauka ka samu problem fah"
Murmushi ya mata sannan ya jawota a jiki ya kankameta sosai har bata iya motsi mai kyau hawaye ne ya fara diga yana kuka ya fara magana a hnkli
  "Nagode!! Nagode!! Nagode!! Nana Aysha ke ya'r aljannah CE insha Allah..Allah ya miki albarka ya baki duk abunda kike bukata duniya da lahira..ya baki ya'ya masu albarka bazan manta dake ba har karshen Rayuwata ..bazan tozartaki ba..ya Allah ka bani ikon rike wannan baiwa taka..ya Allah ka yafe mata dukkan zunubanta..ya Allah ka bata gida a aljannah ka biya mata bukatunta ameen...I love u Aysha"
Ya kara kankameta shuairat ma kukan farin ciki take ya Dan raba jikinsa da nata yana kallonta yace

 "Swt hrt ke kuwa kukan me kike yi"
   "My man..dole nayi kukan farin ciki saboda Abu 3"
  "Menene wanna?
"Na farko ka warke Wanda har na cire tsammanin sake xama kusa da kai kamar ynxu na dauka na rasaka har abada kaga kuwa farin ciki ya zama dole"
  "Hakane rahamar ubangiji kenan baya karewa ..uhmm na 2"
 
"Na 2 kuma adu'oin da ka jera tabbas duk macen da ta samu irin wannan aduar a bakin mijinta toh lallai tayi dace a duniya babu kamarta..kaga Allah yana amsa aduar miji ga matansa kaga dole nayi murnan samun wannan Alhamdulillh ko ynxu nabar duniya nayi dace"
  "Uhmm...Ayshata kenan.. Allah ya miki albarka, idan har ta hanyar kyautatawa miji ake shiga aljannah toh na daga kafata..Allah ya baki jannatul firdaus..tabbas kin cika alkawarin da kika dauka na cewa komin tsanani komin wuya komin dadi kina tare dani bazaki barni ba har abada,
[2/21, 2:41 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*68* 
By *Reefat yahya*


Mr president ya cigaba da cewa 
  "Tabbas da ace duk matan duniya halayensu irin naki ne da lallai zaman lfy xata dore a kowane gida ..Allah ya miki albarka Allah ya barmin ke har a gidan aljannah"
Ya kara kankameta yana me kuka shuairat ta kwantar da kanta a kirjinsa tana jin bugun xuciyarsa , a hnkli ta daga kai tace
  "Mr president kawo kunnenka "
Ba musu ya kai kunnensa dai2* saitin bakinta a hnkli ta furta
   "Am pregnant"
😳😳😳😭😭😭 ya xare ido sai kuma ya fara hawaye ya rungumeta gam a jiki yana kuka tamkar karamin yaro
  "Haba my man..me abin kuka a ciki ? Kai da zakayi farin cki "
    "Kuka ya xama dole Ayshata..bansan wane irin farin cki nake bah tabbas babu abun bautawa da gaskiya sai Allah kuma Muhammad manxonsa ne..Allahu Akbar! Allah mai ikon komai da kowa..yau ni Suleiman matata tana dauke da ciki? Allah nagode maka ..dama da rabon xan sake ganin jinina a doron kasa ..Allahu Akbar"
Haka mr president ya cigaba da sambatu Dakyar shuairat ta lallaba shi ya daina kuka har ya bata tausayi..eyya mr president😜.daga nan ya tashi ya wuce bayi ya daura alwala ya fito ya fara nafila yana godiyarsa ga ubangijin talikai, shuairat ta kwanta a gefe tana kallonsa tana jinjina masa sabida ya kasance daga ckn bayi masu nuna godiyarsu ga ubangijin da ya haliccesu..bacci ne yayi awon gaba da ita a yayinda mr president kuwa yacigaba da nuna godiyarsa ga ubangiji.


************
Shukrah tana xaune a falo sai hura hanci take tana cika tana batsewa bash ya fito daga dakin bacci ya kalleta sau1 ya kawar da kai gefe yana mmkin wasu halaye irin nata ..
  "Wllhi ina kan bakata, idan har bazaayi tafiyan nan dani bah toh sai dai kaima ka hkura don bazan yarda da wannan salon yaudaran bah..uhmm inaji ina gani ka dauko wata can ka tafi da ita turai da sunan zakuje duba jikin mahaifinta salon kuje kuyi soyayya a can koh..toh ban amince bah'"
 Sai ynxu ya juya ya kalleta sosai ya girgiza kai yace
  "Wai dama haka halinki yake ne shukrah? Kodak kin fara bin xugin kawaye ne? 4Allah's sake shukrah ina matsayin mijinki mu haifi waleed amma ace har yau baki yarda dani bah? Yaushe zaki daina zargi na ne..bayan kinsan cewa aure da zargi babu kyau"

  "Kaga malam..ni ba jahila bace da zaka min wa'azi ehen, bazaka fake kana min dadin baki bah kawai ka fito fili ka gayamin aurenta zakayi ba sai ka tsaya yin wani kame2* bah"
  "Allah sarki..yau kuma ni nake kame2* shukrah! Lemmi ask u..idan ina son umaima wai tsoronki zanji? Ko kina tunanin cewa idan ina son aurenta wannan haukan taki xata hanani yin abunda nayi niyya?"
        "Koma menene..tafiya ce baxa ayi bah "
Ran bash ya baci sosai gskiya shukrah ta canza amma dole ya ja mata birki ( mata a kiyaye..wannan kishin hauka ne kuma hakan yake kara tunxura miji har yayi aurenda be shirya yi bah Allah yasa mu dace ameen).
Ya tashi kai tsaye dakin umaima ya wuce fuu..shukrah tabi bayansa, umaima tana kwance bash ya shigo tare da sallama ta gyara zaman ta kenan shukrah ta shigo kamar wata zakanya😝😝😝(Wa ya gamin anti rabi ana kishi😜)
Bash yayi banza da ita yace
  "Umaima hop kin gama shiryawa cos jirgin 8pm zamu bi"
  "Na gama but yaya I tot tare zamu tafi dasu sultan da gran mah"
 "No..I change my mind mu 2 kawai zamu tafi su kuma jirgin 7am na safe zasu bi , zamu jira su @ Beijing"
      "Ok..Allah ya kaimu"
Basuyi aune ba sai ganin shukrah sukayi ta makure umaima a jikin gado tana huci ta fara magana
   "Shegiya munafuka..wllhi mijina yafi karfinki kije can....
Bata karasa ba taji saukan mari Tass! A fuskarta ba shiri ta sake umaima ta juya tana kallonsa tmkar a mafarki wai yau bash ne ya daga hannunsa ya mareta? Hawaye ne Suka cika mata ido a hnkli Suka fara sauka 
  "Shine ka mareni? Ak..kan ..akan wannan yarinyar? Baban waleed?
   Ya runtse ido ckn jin zafin abunda ya aikata.shukrah ta juya tabar dakin shi kuwa ya jingina da bango kansa na kallon kasa, umaima kam tayi Kim..tmkar gunki ta rasa me xatayi tabi bayan shukrah ko kuwa ta tsaya gun bash? Shiru ya ziyarci dakin a hnkli ta karasa kusa dashi

  "Yaya bash kayi hkri laifina ne da nazo gidanka..na hanaku kwanciyar hnkli am sorry"
Hannu ya daga mata ya juya yace
  "Ki shirya ynxu xamu bar gidan nan"
Daga nan dakinsa ya wuce ya shiga bayi ya watsa ruwa gaba daya ransa a bace yake , ckn kankanin lkci ya gama shirinsa ya dauko wani Dan karamin jaka dakin shukrah ya shiga tana kwance rub da ciki tana kuka Mara sauti waleed kuwa yana gefe sai sharar baccinsa yake ckn kwanciyar hnkli.
           Ya karasa kusa da ita yace
"Am sorry..nayi kuskure ki yafe min ni zan tafi kiyi hkri"
Daga nan ya ajiye mata rafar yan 1k ya juya ya fara tafiya har ya kai bakin kofa ya tsaya cak! Yace
   "Ki gyara kwanciyar ki Allah yana fushi da masu irin wannan kwanciyar"
Daga nan ya tura kofa yayi ficewarsa shukrah ta cigaba da kukan da take.umaima ta fito da jakar kayanta ta sanya a mota bash ya ja Suka wuce gidan iyayensa don yin sallama dasu.

**********
       Shuairat ta caba ado tana xaune a gaban mirror mr president ya fito daga wanka bayan ta taimaka masa ya kimtsa Suka fito falo sai kallonta yake ya lura cewa tana ckn nishadi yau ya juya yace
  "Nana Aysha !
"Sir! ta amsa tana murmushi, saida yayi dariya sannan yace
  "Sir! Kuma? ..anyway na lura dake yau tun safe kike ckn nishadi ko meyasa?
    "Hmmm..ba komai fah haka nan nake jin kaina ckn annashuwa "
"Kin tabbata?
Kai ta gyada tace
   "Na tabbata sir!
"Hmm..ke din ne somtymz u r amazing, kuma am sure u ar hiding somtin baki son gaya min koma menene dai nasan gud news ne"
Murmushi kawai tayi bata CE masa komai ba tana duba agogon hannunta , bayan 30min aka kwankwasa kofa shuairat ta mike a hnxarce ta bude kofan tare Suka hada baki wurin cewa 
  *surprise*!!!
😳mr president ya tashi ckn tsananin mamaki yana binsu da ido..ko a mafarki bai taba tunanin ganinsu a wannan lokaci bah..
Bash, umaima, sultan, momsi, daddy da kuma baban shuairat.. Wow wani farin cki ne ya lullubesu wen last Suka hadu irin haka...



Muje xuwa😘😘😘
[2/21, 2:41 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*69*
By *Reefat yahya*


Gaba dayansu Suka dugunxuma ckn falon mr president kuwa murna ne har ya rasa ina zaisa kansa ya kankame daddy kamar xai shige jknsa momsi tana dariya, sultan kuwa da gudu ya fada jkn shuairat yana cewa 
" I rily miss u mom Nah"
"Miss u mor my son"
Mr president ya raba jkinsa da na daddy ya jawo sultan ckn sauri yana cewa
  "Boy kayi a hnkli kada ka ji wa kaninka ciwo"
"Wane kanin dad?
Ba sultan kadai bah ..duk wadanda suke ckn falon sun maida kallonsu ga mr president shi kuwa ko a jikinsa ya cigaba da cewa
  "Sultan mom tana dauke da ckn kaninka very soon zata haifa mana baby koh"
  "Wow...da gaske dad? Am so happy nima na huta da gorin frenz dina a skul "
Daga nan sultan ya koma gun shuairat ya sake kankameta ckn hanzari mr president ya sake rabasu shuairat kam kunya yasa ta bar falon ya shige bedroom.
    Momsi da daddy kuwa wani farin cki ne ya lullubesu umaima ma haka , daga nan Suka zauna aka gaisa har ynxu shuairat bata fito bah momsi tana hararar mr president tace
   "Kaga rashin kunyarka yasa ka korarar min ya' ko gaisawa bamuyi bah..anyway Allah ya raba lfy ya Baku zuri'a dayyibah"
   "Ameen momsi nagode"
  "Hooo..dad ko kunya babu"
Umaima CE ta fadi hakan gaba daya Suka sa dariya bash kam sai faman murmushi yake haka nan baba shikuwa yana son ganin ya'rtasa.momsi CE ta tashi ta nufi dakin a hnkli ta tura kofar shuairat tana xaune tayi jugum momsi ta rike mata hannu suna fuskantar juna tana murmushi tace
"Allah ya miki albarka ya'ta nagode sosai da irin kulawar da kike bawa dana Allah yasaka miki da gidan aljannah ya sauke ki lfy ya albarkaci abunda zaki Haifa"
Sunkuyar da kai tayi ckn tsananin jin nauyinta momsi ta cigaba da cewa
  "Tabbas kin zame mana alheri a Rayuwa ..kin dawo da farin ckn mu , kin cancanci yabo a garemu mun gode Allah ya saka.tashi muje ki gaisa da mahaifinki nasan yana bukatar ganinki"
Ba musu ta tashi Suka fice xuwa falo.

Ckn jin kunya ta gaisa da baba da kuma daddy sai kuma bash  , umaima kuwa Sam ta tashi ta koma kusa da shuairat. Haka Suka kasance daga nan Suka xauna akan dinning table lafiyayyen abinci masu aikin gidan Suka shirya musu, daga Chinese dishes da Nigerian duk babu abunda babu suna ci suna hira babu batun kunya abun dai gwanin burgewa.baban shuairat yake Dan jin kunya daddy ya lura da hakan yace
  "Alhaji bello gara ma ka cire kunyan nan ka ajiyeta a gefe kaga surukin naka babu alamar kunya a tattare dashi"
Gaba daya Suka fashe da dariya mr president ya Dan Sosa kai..har ga Allah shi yamanta da cewa a gaban baba ya fadi xancen cikin. Bayan sun kammala cin abincin aka nuna musu masauki Chinese president yaxo Suka gaisa da iyayen nasu sannan ya tafi , mr president tare da iyayensa Suka ware suna hira haka nan shuairat ma dakin baban ta Suka xauna ita da bash da kuma sultan suna ta hiran yaushe gamo.

D next day Suka shirya gaba daya daddy momsi baba shuairat bash umaima sultan da gum jankim yawon bude ido Suka fita, sun zaga garin sosai gskiya hong Kong ya hadu har yamma Suka koma gida bayan sun tsaya sunci abinci a wani restaurant.
  Washe gari Suka sake fita , haka dai Suka kasance har tsawon 5days kullum suna tare.shuairat sai nan2* ake da ita duk motsin da tayi mr president ko momsi ko daddy zasu tmbayeta wani Abu take ji ne? Itakam har kunya take ji irin yanda Suka dau son duniya Suka doramata ita da ckn nata gashi ynxu ckn ya bayyana cos yana 7mnth ne.bayan kwana 2 Suka fara shirye2* komawa 9ja duk nacin momsi na son tafiya da shuairat firr...mr president yaki yarda yace musu zasu ga likita kafin su koma Nigeria, babu yadda Suka Iya dole ta hakura nan Suka cigaba da shirinsu.
      Misalin 8pm umaima tana kwance a dakin shuairat tana chat a waya shuairat ta shigo ta zauna a gefe tana fuskantar ta tace
   "Baby ya maganan aure ne kinga ynxu kin girma fa ya kamata ace kin fito da Wanda kike so"
Shiru umaima tayi a yayinda xuciyarta ya fara bugawa can ta kirkiro murmushi tace
   "Anti Nah dad ne yace ki min maganan aure?
  "Ah'aa wllhi nice dai naga ya dace cos zaki shiga final year naki a uni daz y"
  "Ok ki bari idan Allah yasa kin sauka lfy after den sai muyi maganar"
    "Toh Allah ubangiji ya nuna mana.. Amma ni ban taba ji ko ganin wani saurayi yazo wajenki bah"
"Oh..antyyy...wllhi har kinsa naji kunya"
Daga nan ta tashi ta gudu tana murmushi ganin shuairat na Neman tona mata asiri. A bakin kofa ta tsaya tana maida numfashi, bash ne ya shigo Sam hnklinta baya ckn jikinta tunanin maganganun shuairat takeyi ynxu ya xata yi? Pamm! Bash ya tafa hannayensa a saitin fuskarta ckn tsoro ta bude baki xatayi ihu yasa hannu ya toshe bakin nata yana dariya sannan yace
   "Matsoraciya kawai"
Daga nan ya cire hannun nasa ita kuwa taja dogon numfashi
  "Haa..yaya kaban tsoro wllhi na razana ba kadan bah"
"Ajebo kawai..babu abunda kika iya sai shagwaba wllhi mijinki zai sha fama dake"
Umaima ta rage sautin muryarta tayi magana ciki2* tace 
  "Kaine zaka sha faman ai cos kaine mijina"
 "Wat? Me kike cewa"
"UHmm
.ni nayi magana da kai ne?
Ta fada ckn tsigar shagwaba yana dariya yace
  "Hmmm a cigaba da boye2* dai wata ran dole a amayar"
 "Wat? Hw do u min?
Ta tambaya ckn tsarguwa 
"Oho..nima nayi magana dake ne?
Harara ta watsa masa sannan ta wuce falo ta xauna yana dariya yabi bayanta shima xaman yayi kusa da ita.

"Yawwa..yaya bash nifa bazan koma gidanka bah"
 "Ina zaki koma ?
"Gidan baba xan koma b4 su dad su koma"
 "Matsoraciya shukrah ce ta hanaki koh"
"Hmm..wannan matar taka se a hnkli"
"Ba dole bah..ta gane kina son mijinta ai dole tayi kishi"

😳😳waat?..mijin wa? Ni din?
Ta jera masa tambayoyin ckn mamaki da firgita wani murmushi ya sakar mata sannan ya tashi Sam ya dawo kusa da ita har suna jin hucin juna ya kura mata ido yace 
"C'mon baby sis..stop pretending ya isa haka ki daina wahalar da xuciyar taki kowa yasan cewa ni kike so stp hiding n b strait fowod"
Xuciyar umaima sai dukan 3-3 yake bash ya cigaba da cewa
"Umaima na Dade da sanin cewa kina sona kawai kunyace ya hana ki gayamin.tun bayan dawowata daga Adamawa kika kirani na sameki a gidanku kina kuka kina maijin haushin cewa nayi aure ban gaya miki bah, tun a wannan lokacin na fuskanci sona kike.duk rashin lafiyar da kikayi bayan aurena ina sane da hakan kuma dad ma ya gane lagonki shiyasa yake turani miki magana a duk lokacin da kikayi fushi dashi, n naga chat naki da shuairat a yayinda kike gaya mata cewa kina son wani amma kin kasa tunkararsa har yayi aure. Ranar da kuka samu misunderstanding da shukrah har na lallabata xuwa daki nace ki koma dakinki ki jirani bayan na dade kafin na je dakinki nan ma na hango kishina xalla a kwayar idanunki har na tambayeki hiran samarinki kika cemin saurayinki ya mutu kin tuna? kuma dazu maganan da kikayi cewa nine mijinki duk naji abunda kika fada , so umaima pls ki daina wahalar da xuciyarki ki fito ki bata abunda take nema"

Yana gama fadin haka ya tashi ya kashe mata ido daya sannan ya juya yayi tafiyarsa.mutuwar xaune umaima tayi tana mamakin faruwar al-amarin dakyar ta tashi ta koma dakinta ta hada kayanta don jirgin safe xasu bi.

*****da safe mr president da shuairat Suka rakasu xuwa airport har jirginsu ya daga sannan Suka juya don komawa gida.
A ckn jirgi kuwa umaima Sam taki hada ido da bash don wani Sabin kunyarsa take ji haka Suka kasance har lokaci da jirginsu ya sauka a Lagos.umaima tace xata kwana 2 kan ta koma Abj haka bash da sultan da kuma baba Suka wuce Abj gidan baba direct Suka sauka.bayan kwana2 umaima ta koma Abj a gidansu shuairat ta yada Zango ta sanarwa mama cewa tare zasu zauna ita kuwa taji dadi sosai dama zaman kadaici ya isheta don ma sultan yana nan kenan.

*********
Shuairat kuwa jankim CE ke kulawa da ita duk awon ciki da komai ita take mata tana shan magunguna masu inganci don karawa bbyn lfy.honey moon Suka shirya xuwa jankim tana xolayarsu wai honey moon da tsohon ciki, har airport ta rakasu jirginsu ya daga xuwa *Akita Japan* wani hadadden city ne a can Japan jankim CE ta xaba musu garin *akita* saboda tsarin yanayin garin akwai dadin xama don kuwa duk arean tsakanin Korea China da Japan babu garin da yakai akita kyawun weather.
Bayan sun sauka taxi ne ya kaisu can gefen gari a *akita snow fall* wow..kankara ne ke xuba kotaina wani hotel mai kyawun gaske Suka kama daga nan wanka Suka shiga tare ..tafasashen ruwan zafi Suka Tara a jacuzzi shuairat na ganin haka ta xare ido tace
  "Haba😳 my man ynxu kana nufin ckn ruwan nan xamu shiga?
Ya jawota jikinsa yace
"Don't worry my lady ..kinga nan snow fall ne bqzaki ji xafin ruwan bah"
"Ah'ah nikam gskiya baxan shiga bah"
"Plsss..haba ke baki jin sanyi ne? Nida nake son ki haihu a nan kiyi wankan jego kinga bazaki ji radadin wanka da ruwan xafi bah"
   "Mm..dama wa yace zanyi wanka da ruwan xafi"
Ckn dabara ya tura bakinsa ckn nata ya fara kissing dinta cak ya dagata sai ckn jacuzzi....
Ummmm a hnkli na ja kofar bayin nayi waje.

Ku biyoni😘😘😘😘
[2/21, 2:41 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*70*
By *Reefat yahya*


Wata sabuwar rayuwar soyayya da kulawa mr president da shuairat Suka shimfida a *akita* bata daga komai hatta wanka shi yake mata kullum suna fita trekking saboda yana da kyau mace mai ciki ta dinga motsa jikinta kwanciya ba naki bane..a wannan lokacin ne shuairat ta kara tabbatar da irin son da mr president ke mata shikuwa gani yake tmkar  baxe Iya biyanta karamcin da ta nuna masa, kullum suna manne da juna basu rabuwa wata irin shakuwa da so mai karfi ya kullu tsakaninsu.cikin ya shiga wata 9 su momsi Suka damesu da kira kan cewa yaushe zasu dawo mr president yace suna nan tafe momsi ta umarcesa da ya dinga karanta yasin kafa1 ya tofa a ruwa ya bata tana sha kullum saboda Neman haihuwa ckn sauki da iznin Allah.hakan kuwa akayi kullum mr president sai ya tofe suratul yasin 1 ya bata tasha. *Doughbunji hospital akita Japan* can sukaje aka shaida musu cewa haihuwan na nan bada jimawa, habawa mr president ya fara shopping ne kamar ba gobe babu abunda be siyo bah.

10days leta... Gobene suke shirin komawa Nigeria by 11pm suna xaune a falo shuairat tayi filo da cinyar mr president suna kallon news ana election a can Nigeria shuairat ta daga kanta tana kallon mr president tace
 "My man da ace kana nan akayi wannan zaben babu makawa na tabbata talakawa xasu xabeka"
Murmushi yayi yace
  "Wllhi nikam dadi naji don dama ni ba son politics nake bah..wancan karon ma daddy ne da frenz dinsa Suka dage har na samu shiga but now I have u I have everything"
Ya manna mata peck a goshi tana murmushi ta gyara kwanciyarta batasan lokacin da bacci yayi awon gaba da ita bah.
      1hr leta ...ckn bacci taji ciwon Mara a hnkli ta bude ido mr president yana bacci a xaune har ynxu tana kan jikinsa hannu tasa ta shafa sajen fuskarsa dake kwance luf-luf a hnkli shima ya bude idon
  "My man dauko min magunguna na marata ke min ciwo"
😳ckn hanxari ya dagata yace
  "Hospital xamu je am sure haihuwace my lady"
Ta tura baki tace
  "Ah'ah nikam ba ynxu bah..kawai fah ciwon Mara CE da kuma ciwon baya" 
Bai jira komai bah ya daga ta cak dama doguwar rigace a jikinta don haka yayi waje da ita tana tmbayar ina ze kaita bai kulata bah ckn sa'a kuwa a harabar asibitin ya hango wani mutum yayi parking motarsa yana fitowa wani Dan bature neh da harshen turanci Ya roki mutumin akan cewa ya taimaka ya kaisu asibiti matarsace take nakuda babu gardama mutumin ya bude musu gidan baya Suka shiga yana kallonsu ckn yanayin tausayi yana yiwa shuairat sannu.a wannan lokacin ne ciwo yace salamu alaikum Ashe da can wqsa ne aikuwa kuka ta fara masa ta kankameshi sosai gaba daya ya rikice haka nan baturen ma yana tuki yana juyawa yana mata sannu gudu yake da motar tamkar xasu tashi sama *doughbunji* hosptl Suka nufa ckn Sauri aka karbesu dakin haihuwa aka wuce da ita mr president ya nemi kujera ya xauna sai adua yake jerawa yana rokon Allah ya sauketa lfy.
45mins leta...wata nurse ta fito fuskarta dauke da murmushi ta hango mr president xaune ya buga uban tagumi tace
  "Congratulations sir! Ur wife gave birth to a baby boy"
😳😀take fuskarka ya fadada da murmushi a hnkli ya furta
"Alhamdulillh.. Allah nagode maka da wannan kyauta"
Daga nan dakin Suka wuce an gyarasu ita da jaririn duka idanun mr president sun cika da kwallah ya wuce gun shuairat tana kallonsa sai murmushi take ya kankameta sosai a jikinsa yace
   "Thank u so much my lady Allah yabar min ke "
Ya manna mata peck sannan ya wuce ya dauki yaron ya kura mishi ido suna kama sak babu abunda ya rabasu har hasken fata nan ya masa huduba sannan ya bude bakinsa ya tofa masa adu'oi da kuma sauran gabobin jikinsa haka nan ya dafe goshinsa ya karanta wata adu'a sai kuma ya shafa kansa yace
  "Allah ya maka albarka yasa ka gama da duniya lfy Allah ya albarkaci rayuwarka ya tsareka da sharrin mutum da aljan ya doraka a tafarkin addinin Islam ameen "
Ya mikawa shuairat yana mata murmushi yace 
    " karbeshi ki masa adu'a Allah yana karban aduar iyaye ga ya'yansu ki sanya masa albarka"
Ckn jin kunya shuairat ta karbeshi tana kallonsa tana murmushi a ckn xuciya tayi tata adu'ar da ko ni *Reefat* bansamu naji me ta fada bah sai ta shafa kansa ta mikawa mr president yana dariya yace
  "Aw..adu'ar sirri ne? Ba damuwa naga alama kunyarsa kike ji nidai kar kunya yasa a cutarmin da da' "
Murmushi kawai tayi ta kawar da fuska gefe hmmmm...real Fulani kenan *pulaku*☺☺☺☺👍🏼👍🏼 daga nan mr president yayi waya akan cewa a turo masa private jet dinsa sai kuma ya kwantar da yaron gefen mamansa yace 

  "Ki kula dashi ina xuwa baxan Dade bah..saura kunya yasa ki barshi ya fado kasa"
Dariya sosai sukayi gaba daya, mr president yasa kai ya fice a nan ne ta samu ta karewa yaron kallo
Sak!! Yana kama da uban kamar an tsaga kara. Wata nurse CE ta shigo rike da wani tray da wani Dan container tana mata sannu da harshen turanci ta samu kujera ta xauna nan ta mika mata wani babban mug cup shuairat ta karba tana binta da ido wani karamin flask ta daga ta siyaya mata wani hadadden tea mai kauri sai qamshi ke tashi ga kuma Tiririn da yake nan ta umarci shuairat ta shanye ckn zare ido take kallonta aikuwa matar ta hada rai nan da nan tasa a baki a hnkli ta fara sha sai kuma taji dadinsa don haka ta cigaba da kurba matar ta ajiye containern da tazo dashi ga mmkin shuairat abun gasa nama ne da jajayen gawayi a kasa nan matar ta fara gashin tanayi tana juyawa har yayi dai2* yanda take so ta xuba a plate ta turawa shuairat. Gaskiya  naman ya gasu woww....kan ta Ankara ta cinye fiye da rabi tayi nak! Ta mikawa matar plate tana godiya daga nan ta bata wasu magunguna tasha sannan ta fara bata shawarwari dangane da ydda xata kula da kanta.

1hr leta shuairat ta fara bacci bayan tafiyar wannan nurse din..mr president ne ya shigo tare da sallama ya tsaya a kanta tana bacci ckn kwanciyar hnkli jankim CE ta shigo tana murmushi ta dauki yaron tana masa dry mr president baya son tashinta don haka y dagata kamar wata karamar yarinya jankim tabi bayansa da jaririn. Wani lungu sukabi Suka haura xuwa lift, last floor sukaje shuairat ta lafe a jikinsa ta cigaba da barcin.bayan sun iso last floor din can harabar wajen Suka nufa haba sai kawai na hango bash tare da wasu mutane 3 ckn bakaken suit ga private jet nan mai Karen kyau a gefensu suna xuwa kowa ya shiga ,har jankim tana yaba kyawun jirgin ya hadu sosai ga manya2* Leda seats masu kyau.tana rungume da jaririn bayan kowa ya shirya pilot ya tada jirgi Suka tashi don dawowa kasarmu mai albarka
*Nigeria*
🛩🛩🛩🛩🛩
Ni *Ree* nace musu safe trip perfect couples😘😘😘😘😘



Ku biyoni.........
[2/21, 2:41 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*71*
By *Reefat yahya*


Duk yanda Mr president yaso a wuce da Shuairat xuwa gidansa bai samu bh momsi taki amincewa tace lallai a wuce da ita gidan iyayenta babu yanda ya Iya dole ya hakura . gidan cike yake makil da jama'a  cki kuwa har momsi da daddy, Shuairat kam dakin mama ta wuce bayan ta gaisa da surukan nata  .momsi kuwa murna fal ckn ranta tana rike da jaririn anata musu barka.
         Kwanciya tayi bayan kankanin  lokaci anti mairo ta hada Mata ruwan wanka  bayan ta gama ta sake zama ckn ruwan zafi Wanda aka tafasa da bagaruwa da  magarya kamar zatayi kuka  dole haka ta xauna acki .bayan ta fito aka kawo mata kunu da kuma tuwon semovita da miyar kuka ta xauna ta.cInyeshi Tass..sannan tabi lfyar gado bacci mai nauyi ya dauketa.

Da dare tana xaune bayan an wanke nonon ta fara bawa yaron yana tsotsa umaima ce ta shigo tare da sallama a gefenta ta xauna tana me sunkuyr da kai kasa ,Shuairat ta lura da ita tace 
" umaima lfy akwai wata matsala ne?
  "Umm..dama anti nazo ne domin na baki hkri kan abubuwanda suka faru a baya/, don Allah ki yafemin kiyi hkri"
   "Dama don wannan ne? Ki kwantar da hnklinki ni ban taba  rikeki a xuci bah"

"Nagode anti insha Allah daga yau ki daukeni a matsayin Ya'r da kika haifa ,ni kuma ina son ki xamo uwa a gareni"

"Nagode umaima insha Allah nayi alkawarin rikeku tskani da Allah ..Allah ya bani ikon cika alkawarin"
"Ameen"
Daga nan suka cigaba da hira sallama suka ji shukrah ce ta shigo sai wani yatsina take Shuairat dai tayi mamakin hakan Amma bata nuna bah..gaisuwa kawai sukyi bbu wata hirar arxiki tayi mata barka bayan yan mintuna tace xata tafi daga nan tasa kai tayi tafiyarta ko uffan bai hadata da umaima bah.
     Bayan tafiyarta Shuairat tayi Jim..tana tunanin wannan sabon sauyin umaima ce tace mata 
  "Mom Shuairat kada kiyi mamakin ganinta ckn wannan yanyin ni nasan meyasa ta miki haka"
Daga nan ta labrta wa Shuairat irin xaman da tayi a gidan da kuma abubuwan da suka faru lokacin da take gidan bash.dariya sosai Shuairat tayi sannan tace
 
"In banda shukrah da kishin hauka ni me nawa a cki idan ma kuna soyayya da yaya?
  " oho..maybe gani takeyi tamkar dake ake hada baki ana cutar da ita "
 
"Allah dai ya kyauta irin wannan ai ba kyau cos zatone n kuma zato kuma kowa yasan xunubine koda ya xamto gaskiya"
 "Hakane..Allah de ya shirya"
"Ameen"
Jankim ce ta shigo a gajiye ta fda gado tana maida numfashi murmushi Shuairat ta fara mata magana da turanci

"Ina kika shiga tunda muka zo ban kara ganinki bah"

  " bari kawai..nagaji sosai , muna tare da sultan "

"Lallai kinsha surutu kuwa"

"Ni ina son yaron sosai...Shuairat mutanen garinku suna da kirki "

"Da gaske?
" ehh...suna da karamci naji dadin xuwa kasarku"
  "Nagode jankim"
Daga nan ta fito da magunguna ta bata tasha suka cigaba da hira karar wayar Shuairat ce ta katse su Mr president ne ya Kira.
Ckn natsuwa ta Daga 

"Hi swt hrt"
"Don't swt hrt me...bayan kin manta dani "
Ya fda ckn tsigar wasa tana dariya tace

"Bahaka bane kayi hakuri wllhi baccin gajiya ne"

"Toh na yarda ya kike ya little dasu sultan"
"Lfyan mu kalau ya ka koma gida"

"Alhamdllh but nima ban Dade da shigowa gidan bah cos muna tare da jama'a a gidanku dasu daddy da baba"

"OK ya gidan toh"
"My lady u need to c d house.. Gaskiya gidan yayi tubarakallah..bash yayi kokari sosai Allah yasaka masa"

"Ameen..but kana ta yabashi gyara fa kawai yasa akayi"
  "Yh I know..but samun Wanda xai kula maka lamura ma ai abun farin cki ne ,Amma gidan ba dadi "

"Haba meyasa?
" hmm..kinsani ai! Bcos baki kusa dani daz y, gaskiya na shaku dake sosai I'm realy missing u wllhi"

"Eyya my man sorrie...kayi hakuri ka daure just d matter of few days ne I miss u more"
Haka suka cigaba da soyewarsu ta waya jankim de ta xuba ido kawai tunda batajin me suke fada.
    Umaima kuwa tana adu'a a ckn xuci itama Allah yasa bash ya sota.



Ku buyoni..Lov u all
*wannan page din naki ne kawaalliya romon jaba @ nanastically😘😘*
Lov u my fans n tanx 4yah support also my tanx goes to *nazeer Adam* of ~voice of ohr~
Tnx to all....
[2/21, 2:41 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*76*
BY *Reefat yahya*


1wik sukayi a garin mubi mr president yaji dadin zama a garin yanayin weather dinsu ya burge shi sosai don haka ya nemi siyan fili a garin daga nan Suka wuce yola Airport Suka wuce nan Suka hau flight xuwa birnin tarayya.
        A gajiye shuairat ta fada gado saboda hanyar mubi xuwa yola da dan tazara tsakaninsu, bayan ta huta kadan ta fada wanka ta fito kenan mr president ya shigo rike da salman yana murmushi yace
   "Ke kuwa haka akeyi...daga dawowa se ki gudu dakinki kin bar min daddy na da yunwa "
Dariya takeyi tace

   "Wannan Dan lukutin daddyn naka ya gama tsoseni yana ramar dani"
Ckn wasa ya harareta yace
  "Wato daddyn nawa ne Dan lukuti koh...shikenan bari na kira daddyn Lagos sai na sanar dashi abunda kika fada"

   "Lahh..rufamin asiri nikam ba ruwana wllhi"
Daga nan ta karbe yaron ta xauna a gefen gadi dama towel ne a jikinta nan ta bude ckn style ta fara bashi nonon yana sha mr president ya xauna a gefe ya tallabo kumatu yana kallonsu yana murmushn jin dadi..shikam de yayi sa'a a duniya babu abunda ya rage bai mallaka bah daga ya'ya har dukiya ga kwanciyar hnkli da koshin lafiya ga kuma mace ta gari wacce ta wadata shi da komai a hnkli ya furta 
"Alhamdulillh"
Shuairat ta juya Suka hada ido tace

   "Lfy my man? ...naga kam zauna kayi shiru"
Ya taka ya dawo kusa da ita ya xauna yana murmushi yace
   "Ina godewa ubangiji ne da ni'imomin da ya bani a rayuwa ..tabbas babu abunda narasa a nan duniya shiyasa nake godewa Allah da ya bani komai na rayuwa cki kuwa harda ke"
Ya karasa maganar yana shafa kumatunta wani dadi ne ya xiyarci xuciyar shuairat mr president ya lumshe ido sannan ya cigaba da cewa 
   "Ina alfahari dake akoda yaushe ..ina sonki har raina kuma baxan daina sonki ba har karshen rayuwata sabida ke kika dawo da farinciki a Rayuwa...da bansan me so bah, amma a kanki na fara soyayya nasan dadinta kuma a kanki na fara sanin menene shakuwa.shuairat ke abun alfahari na ne ..ina sonki sosai, kin soni kin zauna dani kin kular min da ya'ya na baki taba hantararsu bah kin jawosu a jiki kin maye gurmin mahaifiyarsu kin kula dani a lokacin da nake bukatar hakan baki gujeni bah kin xauna dani kin......

"Shhhhhh....haba ya isa haka pls"
Shuairat ta sanya Dan yatsa ta rufe masa baki 
Wani guntun kwallah ne ya fito a idonsa yana murmushi yace

  "Allow me ..kin cancanci yabo a gareni kinyi min halaccin da ba kowace mace bace xata iya yiwa mijinta"

"Nayi hakane saboda Allah da zuciya daya nayi ba don...
  "I knw Ayshata..but u deserv it daz y...I rily Lov u Aysha"
  "I lov u too"
Peck ya manna mata a goshi tana murmushi ta kwantar da salman a gado yana mata dariya tana kaunar yaron fiye da komai a duniya Amma kunyar mutane yasa take kawar da kai tana nuna masa halin ko in kula..hannu taji a saman kirjinta ckn tsananin kunya ta juya tace 

  "Haba swt hrt salman yana kallonka fah"
  "Ah-ah yasha rabonsa saura ni "
Ba kunya kuwa ya fara tsotse na fulaninta shuairat kam kulle ido tayi wai tana kunyan salman🙄🙄🙄.yayi romancing dinta daga karshe ya dagata cak Suka fada bayi tare sukayi wankan sunayi suna wasanninsu irin ta masoya.

Bayan 5days ta gama ware gajiya ta shirya taje yini a gidansu ta kai musu tsarabar Adamawa da na Lagos sultan kuwa tamkar ya shige jikinta haka ma umaima yaran suna son shuairat ynxu jinta suke kamar ita ta haifesu.har yamma ta kira driver ya kaita gidan yayan ta, ta shigo da sallama a falon kida ke tashi kamar ana party a gidan carab! Suka hada ido da yarinyar shuairat ta nunata da yatsa

" kee...me kikeyi a nan gidan"
Yarinyar ta fara xaxxare ido...

🤔🤔🤔🤔 ina Suka taba haduwa???

Muje xuwa..Lov u all😘😘
[2/21, 2:41 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*77*
By *Reefat yahya*


Shuairat da fatee sun tsaya suna kallon -kallo shukrah ce ta sakko daga bene tana ganin shuairat ta hada face tace

   "Lfy sahiba na ganku cirko-cirko"
"Uhm..emm..ba komai bakuwa kika yi daz ol"
   "Dole ki ce bakuwa ai munafuka gara ma ki tattara kibar gidan nan cos yaya ba....

Shukrah ta dagawa shuairat hannu tace
  "Um um...malama dakata! Nan ba gidan mr president bane bare azo ana bada order..nan gidana nane baxaki shigo har gida ki ci mutuncin bakuwata "

  "Aw..haka kika CE? Shikenan a bar maganar Amma duk abunda ya biyo baya ki kuka da kanki"
Daga nan shuairat ta juya ckn bacin rai tabar gidan Allah yasa dama driver na jiranta a waje daga nan ya ja mota Suka koma gidan iyayenta, dakinta ta wuce ta fada gado ckn tsananin damuwa umaima ta shigo rike da salman ta zauna a gefe
  "Lfy mom ya na ganki wani iri haka"
  "Him..shukrah tana ckn hadari wllhi"
  😳 me ya faru"

"Fatee lion na tarar a gidanta"
   "Mom sultan wacece fatee lion kuma"
"Hmm..ynxu ne nagane meyasa shukrah ta canza min ta tsaneni ta daina kulani nasan duk hudubar fatee ce"

  "Mom sultan kin ajiyeni a duhu"
"Umaima Allah ya rabamu da sharrin fatee cos yarinya ce mai hadarin gaske..ta kasance tana bin manyan mata masu kudi tana yin lesbianism dasu kuma tana asirce mazajensu ta rabasu sannan ta kwashe kudadensu tayi gaba, fatee bata taba yin aure bah kuma batada sha'awar hakan tafi son harka da mata a dalilinta mata dayawa Suka rabu da mazajensu she is a dangerous gal Allah"
Umaima ta nitsa tace

"Toh mom ina kika Santa kuma me takeyi a gidan yaya bash"
 " a wani grp din watsap ne aka taba tura pix dinta dama tana grp din ta nemi wata daga ckn yan grp din da lalata yarinyar CE ta tona asirinta aka cireta daga grp tare da tura pix nata , kuma mun taba haduwa da ita a sahad stores ta cemin tana son yaya bash bata taba jin wani namiji ya burgeta ba sai shi..kuma tayi ikirarin aurensa kinga dole hankalina ya tashi "

Wani dogon numfashi umaima taja sannan tace
   "Hw comz tazo gidan ?
  "I rily donno...but ina zargin cewa a watsap Suka hadu da shukrah don shukrah ta fiya shiga grps sosai"
( mata a kiyaye masu shigan groups da basu sani bah muyi hnkli kada mu shiga inda yafi karfin mu ..ynxu watsap yayi kaurin suna ya zama hanyoyin yada jita-jita yada gulma da hotunan batsa , kungiyoyin cult , lesbians da sauransu don haka a kiyaye a kula asan grp din da zaayi joining Allah ya tsaremu baki daya ameen..wasu sun shiga watsap ne da wata manufar ta daban Allah ya tsaremu da sharrinsu)

Haka dai shuairat ta cigaba da bawa umaima labarin fatee har magriba tayi Suka gabatar da sallah tare da shirin komawa don umaima da sultan duk tare xasu tafi.

******shukrah kuwa ta juya gun fatee tace 

"Dama kun taba haduwa ne?
Fari da ido tayi ckn kissa tace
    "Laa..nifa yau na fara ganinta tamin kyau ne shiyasa na tsaya kallonta ita kuwa ko meyasa take son na bar gidan oho"
Guntun tsaki shukrah taja tace

  "Rabu da munafuka haka take sai ta dinga commanding mutane tmkar ita ta haifesu wannan ma an sauke girman shugabancin da har ynxu mijintane shugabankasa kam bansan wane kallon banza zata yiwa mutane bah"

  "Ohh...shuairat CE? Gaskiya tana da kyau akwai alamar Hutu a tattare da ita"
  "Hmmm ba tana cin arxiki bah"
  "Shiyasa nace miki ki daina sakewa mijin nan naki don zai rainaki wllhi matukar kina yawan bashi girma ze dinga nuna miki iko da gadara"

"Toh ni ya zanyi sahibah...
   "Yawwa ki bude kunne da kyau ki saurareni...da farko duk wata tarba na Barka da dawowa ba naki bane, idan ya shigo ki daure fuska ki bari shi ya fara miki magana kuma ki daina yawan sake masa fuska don kar ya raunaki.matukar baki sake masa wllhi zeji tsoronki sosai, zancen girki kullum2* ba naki bane  yana da kudi meyasa bazai kawo miki masu aiki bah? Ita kanwar tashi ba ke kanki cewa kikayi ko tsinke bata dagawa a gidan bah?"

Shukrah tayi shiru tana nazarin kalaman fatee🤔🤔🤔
"Kuma haka ne fah...wllhi duk abubuwan da kika fada gskiyane"

  "Ahtoh...ki zauna kekam kina ta shan wahala kullum gaki nan a kitchen kamar wata mai aikin salary, wllhi kika sake kina aiki kullum ynxu zaki rame ki sabe kiyi losing shape ya auro sabuwar budurwa su zauna tare"

   "Dankari...wllhi bai isa bah...cabdi ni da kishiya? Hmmmm...lallai zaa yita kuwa"
Dariyar mugunta fatee tayi tana xancen xuci tace

  "Kidahuma bagidajiya kawai...xaki gane kurenki ai sai na auri mijin naki muga karshen tsiya"
A fili kuwa murmushi tayi tacewa shukrah 

  "Yawwa..ina fatan kinyi amfani da pils na hana daukan ciki da na kawo miki koh?
  "Haba tun yaushe na shanye gaba daya mah"
Dariyar mugunta fatee tayi tace
  "Ba sauki "
"Ah..kina ganin waleed kawai na Haifa Amma har na fara tsufa gashi nan da shegen jaraba "
Suka fashe da dariya har da tafawa ( hmm..Allah ya shirya).
Bayan sallar isha bash ya shigo tare da sallama suna xaune fatee ce ta amsa shukrah kam hankalinta na kan TV bash ya danyi Jim..sannan yace 
 "Shukrah tafiya ki sameni a daki"

"Me kake son gayamin ai wannan Ya'r uwata ce koma menene kam fada kawai"
Murmushi mai ciwo yayi sannan yace

"OK dama tafiyace ta kama ni
ynxu jirgin 10  xamu bi xuwa chicago"

"Aw..toh yayi kyau a dawo lfy"
Daga nan ta cigaba da kallonta ran bash ya baci sosai haka nan ya juya ya dauki jakarsa yabar gidan xuwa gidan iyayensa don waleed ma yana can..kuma duk shirin fatee CE ta CE shukrah ta mayar da waleed gun iyayen bash don ragewa kanta dawainiya.
       Karfe 11 Suka kwanta bacci shukrah ta gama shirinta Sab...dama irin wannan Damar take jira ,ta tashi daga dakin da aka mata masauki ta xuba wasu kwayoyin magani a ckn exotic mai sanyi dakin shukrah ta wuce kai tsaye ta tura kofar shukrah tana danna wayarta da alama chat takeyi 

 "Sahiba bakiyi bacci bah"
   "Mtsww wllhi na kasa baccin kuma wani tsoro ne ya shigeni "
"Haba dai..ko zaki zo mu kwana tare"
  "Bazan takuraki bah"
"Aa ba komai wllhi"
"Toh nagode ..ga juice fah"
   "No..kisha kayanki am ok"
"Kyamata kike yi? Ok sorry "
"Haba sahiba wace irin kyama kuwa"
Nan shukrah ta tashi ta karbi cup din fatee tana murmushn samun nasara aikuwa ta shanye gaba daya ta ajiye kofin...fatee ta kwanta a gefe dama wata Ya'r vest CE a jikinta.bayan 5mins shukrah taji gaba daya jikinta ya mutu ga kuma muguwar sha'awar da ta taso mata se maida numfashi take 
  "Lfy maman waleed"
"Uhmm..wllhi bana jin dadin jikna ne"
  "Kodai kin fara missing din maigidan ne"
  "Wllhi kuwa"
"Ok bari na taimaka miki"
"Taimako? Hw?
Bata Ankara ba taji bakin fatee ckn nata tana mata wani kalan kiss da koh bash bai taba mata irinsa bah..sai kuma ta fara shafa na fulaninta tana murzasu hankalin shukrah ya gushe nan itama ta fara maida martani haka dai Suka kasance har after 12 daga nan kuma fatee ta tura yatsanta a gaban shukrah ta fara wasa dashi har kururuwa shukrah take fatee shu'uma CE sosai...


(Hmm Allah ya tsaremu)
Muje xuwa
[2/21, 2:41 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*78*
By *Reefat yahya*

Da safe shukrah ce ta fara tashi ganin kanta babu kaya a jikinta yasa ta fara tuna abunda ya faru...nan kwakwalwarta ya tuna mata abubuwan da Suka faru a daren jiya, wani wawan mari ta sakarwa fatee ba shiri ta farka tare da tallabo kumatu wani Marin shukrah ta sake ajiye mata tare da cewa
  "Azzaluma! Munafuka! Mayaudariya! Dama halinki kenan?...Allah ya isa tsakanina dake bazan yafe miki bah, kuma ynxu zaki tashi ki barmin gida macuciya...tirrr da hali irin naki"

Tana me xubda hawaye ta fada bayi wanka tayi tare da daura alwala sannan ta fito fatee bata dakin haka tayi sallah tana istigfari tana kuka tare da yin Allah wadai da hali irin na fatee.
  Fatee kuwa dariyar mugunta tayi tare da cewa

  "Yarinya ai kuka ynxu kika fara ...mu xuba nida ke kuma wannan marin se na dau fansa akai"
Daga nan taja akwatinta tabar gidan mai gadi yana mamakin fitan safiya irin haka.
Bayan kwana3 bash ya dawo daga tafiyarsa bai samu wani tarban kirki ba don kuwa har ynxu tana amfani da hudubar fatee ..sai wani hada rai take.

******shuairat CE zaune a falonta daga gefe kuma salman ne yana kwance ckn gadaje irin na kananan yara umaima ta shigo tare da sallama a gajiye ta fada kan kujera
 "Yadai ..yan matan final year"
  
"Hmmm..mom wllhi na gaji sosai, exam din yau de se adua"
  "Allah ya bada sa'a"

"Ameen...don Allah mom sultan ki tayani da adua"
   "Don't worry u'll pass insha Allah ..ki kwantar da hankalinki baki da matsala"
 "Nagode"
Waya ta kira masu aiki Suka shigo mata da abinci bayan ta gama ci shuairat tana murmushi tace 

"Albishirinki"
"Goro"...
   "Fari ko ja?
"Ummm...se wanda kika xaba amma xan baki fari Sol"
 "Yawwa..gobe insha Allah dad xe bude textile industry a kano ki shirya flight din....

"Yeaaa...umaima bata bari ta karasa ma ta fada jikin shuairat ta rungumeta tana dariya"
  "Nidai kada ki karyamin mata da shirmen nan naki"

Mr president ne yayi wannan furucin a yayinda yake shigowa nan kuwa yayi sallama ya koma kusa da shuairat ya xauna umaima ta xare jikinta tana murmushi tace

  "Congrats dad"
"Tank u ya exam"
"Alhamdulillh"
  "Allah ya taimaka ya bada sa'a kuma Allah yasa a gama lafiya"
  "Ameen dad nagode"

"Ina fatan de baki da examz gobe "
  "Ehh..har jibi ma bani dashi"
Dariya sukayi shuairat tace 

  "Ina ruwan umaima sarkin son yawo"
Umaima tana dariya tace
   "Allah ina matukar son kano ne"
Dad ya juya yana murmushi yace
  "Kodai a can surukin nawa yake"
Shuairat tayi saurin cewa

  "Who knows ..nifa ban taba ganin wani yazo wajenta fah"
"Kyaleta..na bata nan da 1month ta fito da miji don tana gama final examz nata na next semester da 1week zan aurar da ita"

Umaima ta shagwabe fuska tace
  "Haba dad..kamar ka gaji dani"
  "Toh umaima zaman me zakimin? So kike na ajiyeki nayi ta kallo?..ynxu idan wani ya shigo ya ganki tare da Aysha ma ai se a rasa wacece matata a tsakaninku"

Shuairat me xatayi inba dariya bah..umaima kuwa tamkar xatayi kuka nan ta tashi tana tafiya dad yace mata
  "Mark my words girl..am not joking"
Shuairat ta juya tana kallonsa tace 

  "Da gaske kake?
"Yeah...am serious wllhi, matukar lokacin da na bata ya wuce bata gabatar da kowa bah ni zan zaba mata duk wanda naga dama"

  "Haba swt hrt ya xakayi haka"
  "Don't worry..u will c Allah ya nuna mana lokacin"
  "Ameen...
Nan ya jawota a jikinsa yana cewa 

  "Com here!..kin ajiyeni ko wlcm kiss baki min ba kun cikani da surutu"
Wani passionate kiss ya fara mata dakyar ta kwace kanta tana cewa 
  "Haba falo muke fah..baka tunanin wani ya shigo"
Murmushi yayi yace 
 "Babu mai shigowa don kuwa na basu rules na gidan babu wanda zai shiga last floor matukar ba ke kika nemesu bah"
Bai jira amsarta ba ya cigaba da kissing nata salman ne ya farka yana Neman abincinsa ba shiri Suka sake juna mr president ya shafa kai tare da cewa

  "Gaskiya daddy na kana yawan shiga hakki na fah"
Dariya shuairat take masa sannan ta dauki salman tana basa nono mr president kuwa ya xauna a gefe yana masa wasa yaron se dariya yake 
Shuairat tace 

"Kana sa shi dariya idan ya kware ba ruwana"
    "Da ruwanki"
Suna hira suna dariya.

  A can ckn daki kuwa umaima ta kwanta tayi shiru tunanin kalaman mahaifin nata take ..tasan halinsa idan ya fadi magana baya canzawa , hankalinta ya tashi tabbas akwai matsala ita tasan duk duniya babu wanda take so sama da bash amma har yau bai furta yana sonta bah shin ya xatayi?
Zuwa xatayi ta zayyana masa halin da take ciki ko kuwa mahaifin nata xata fadawa? Haka ta kasance ckn rudani dakyar ta tashi ta shirya kayanta misalin 4pm jirginsu ya daga xuwa kano tana faman Neman bash a airport Amma Sam bata ganshi bah.
        Bayan sallar isha suna zaune a falonsu dama mr president yana da gida a garin kano don haka can Suka sauka falo 2 ne a gidan da dakuna 6 se kitchen da dinning area daga waje kuma bangaren baki ne. Xaune suke a dayan falon shuairat tana kallon news umaima ta xauna shiru ta buga uban tagumi sultan kuwa yana wasa da salman , kamar daga sama Suka jiyo sallamar bash ya shigo tare da waleed nan kuwa sultan ya ruga a guje yayi hugging dinsa 
  "Oyoyo uncle Nah..
"My boy ya kke "
 "Lfy uncle nayi kewarka sosai kuma nagode da ka kawomin kani Nah"
Nan sultan ya rike hannun waleed Suka koma gun salman Suka cigaba da masa wasa. Bash ya xauna Suka gaisa da shuairat tna kallonsa tace

"Ina maman waleed na dauka tare xaku zo"
  "Nop...na barta a gida"
"Y?...haba my yaya "
"Bazaki gane bane baby..dama ina son muyi wata magana amma se mun koma ABJ"

"Hop de lafiya"
"Umm..kedai ki bari mu koma"
  "Toh..Allah ya kaimu"
"Ameen "ya amsa a gajarce yana satan kallon umaima wacce tayi nisa ckn tunani yayi Dan kasa da Murya yace

  "Ita waccan meyake damunta"
Murmushi shuairat tayi sannan tace
  "Ita da dad ne as usual"
Daga nan bash ya tashi ba tare da ya kalli bangaren umaima ba ya sallami shuairat yayi ficewarsa.


Hmmm...wace irin magana bash xeyi da shuairat kodai batun umaima ne????🤔🤔🤔🤔

Muje xuwa.....
[2/21, 2:41 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*79*
BY *Reefat yahya*


10pm mr president ya shigo ya sanarda umaima ta hadawa bash tea ta kai masa yana dayan falon xuciyarta na harbawa dole ta tashi ta hada sai kuma ta xumbula dogon hijab ta nufi falon ta shigo tare da sallama firgigit ya amsa dama yayi nisa ckn tunani suna hada ido tayi saurin dauke kanta nan ta ajiye masa cup din ta juya xata tafi ya kira sunanta a hnkli
 "Umaima!
Cak...ta tsaya ba tare da ta juya bah ya sake cewa 

  "Dawo ki xauna"
Ba musu ta dawo ta xauna a kujerar da yake kallon nasa 
    "Umaima meyake damunki"
  "Kaima meyake damun ka?
Murmushi yayi wanda ya Kara fito da kyawunsa yace
"Ni nace miki wani Abu yana damuna ne?
   "Toh.. Ni na gaya maka nawa ne?

"Umaima fuskarki ta nuna kina ckn matsala tell me"
     "Kaima ai fuskar taka ce ta nuna hakan"
Shiru yayi daga bisani yace 
"Bansan yaushe kika fara boyemin matsalolinki bah..da can baya har nemana kike idan kina ckn matsala Amma ynxu ki canzamin I donno y"

"Hmmm...naga babu amfanin hakan ne shiyasa"
"Haba umaima...don na kasa furta miki Kalmar so?
😳😳😳😳 ta daga kanta Suka hada ido tayi saurin sauke nata daga ta mike zumbur ta bar masa falon.tagumi bash yayi..shidai yasan yana matukar kaunar umaima tun ba yau bah Amma Sam ...ya kasa gaya mata hakan don gani yake tamkar tafi karfinsa bata dace dashi bah, mahaifinta babban mutum ne mai arziki shiyasa yake ganin kamar soyayyan nasu baxata yiwu bah..duk da cewa ya gane irin tsananin son da take masa Amma shi bazai iya tunkarar mr president da wannan zancen bah.

Umaima tana kwance bacci ya kaurace mata sai tunanin kyakkyawar fuskar bash take gani ..tana sonsa kamar ta hadiyeshi Amma tayi alkawarin danne wannan son matukar bai fito ya furta cewa yana sonta bah ta gwammace sonsa ya zamo ajalinta akan ta bude baki ta gaya masa duk da yagane halin da take ciki.
   A bangaren bash ma hakan ta kasance sai faman sake2* yake ga uwa uba canjin da ya fuskanta a gun shukrah. ..kwata2* ta daina kulasa abinci ma sau1 take a rana ga kuma bukatarsa Sam ta daina amincewa dashi..abun duniya ya masa yawa dakyar bacci barawo ya saci wadannan masoyan biyu.


Taro yai taro jamaa ne makil duk inda ka duba ga kuma yan Chinese yawanci sune ma'aikatan katafaren kamfanin mai suna 
*AS4 textile industry* bayan an kaddamar da bude sabon kamfanin aka raba abinci da sauran abubuwa daga karshe aka rufe taro da adua ga yan jarida nan birjik sai daukan rahoto suke..ckn kamfanin Suka shiga tare da iyalansa da sauran abokan arxiki daddy ma ya halarci taron yana rike da salman duk yawon da suke story building ne mai kyawun gaske ga ofishin maaikata nan birjik abun de ya hadu.
Har bayan azahar Suka dugunxuma xuwa gida dama da masu aiki Suka zo don haka bayan sunyi sallah Suka baje a dinning, daddy shuairat mr president umaima sultan bash waleed se kuma salman take hannun kakansa suna cin abinci suna barkwanci gwanin sha'awa daddy yayi gyaran murya ya fara magana

"Dama zancen umaima ne boy, akwai wani abokina yace yana nemawa dansa aurenta shine nace sai nazo zamuyi maganar"
😳😳😳😳 umaima ta zare ido tace 
  "Haba daddy...

"Ke rufemin baki shashasha kawai..kina ajin karshe a jami'a me ya rage miki?
Mr president ne yace

 "Yi hakuri daddy daman nima na gaya mata idan ta gama da 1week zan aurar da ita kuma...

  "Gafara can...dama ba kai kake biye mata bah, idan ba kam dage bama da zan bari tayi karatun jami'an ne?...toh nidai na gama magana aure de dole tayi ko taki ko taso"

  "Sorry daddy Nah..ba ina goyon bayanta bane but na bata damane ta fito da wanda take so sai ayi auren"

"Bana son shiririta ita wannan ka taba ganin wani yazo wajenta ne? Ba ta dauki girman kan tsiya ta dorawa kanta bah..gani take tmkar tafi karfin kowa "

Sai ynxu shuairat tasa baki tace
"Allah ya huci xuciyarka daddy insha Allah xaayi auren nan ba da dadewa bah"
Sai ynxu yayi murmushi ckn jin dadi yace

"Yawwa Ya'r albarka ynxu naji magana..kinga mijin naki da ya'rtaki duk mashirmata ne rabu dasu "

Murmushi shuairat tayi ta kashewa mr president ido sannan tace
  "Don't worry daddy kam kwantar da hankalinka "

"Tank u my Dota...am now counting on u"
  "Trust me daddy"
Daga nan Suka fara hirarsu mr president kam yasha jinin jikinsa bash kuwa sai Satan kallon umaima take ita kuwa ta cika tayi famm..murmushi yayi ya mata gwalo batare da kowa ya gani bah yace

"Gaskiya gara a aurar da ita da wuri daddy..don kuwa ta fara tsufa"

  "Yawwa ganemin hanya dai basheeru..mu a zamaninmu mace tana 13-14 zaa aurar da ita Amma ynxu yahudu ya bata muku rayuwa kuna nan kuna biyewa bokon banza"

Umaima dama kiris take jira nan ta fara kuka ta tashi tabar dinning daki ta wuce shuairat ta harari yayan nata tace

"Se kaje ka lallabata ai..kasan halinta sarai Amma kake tsokanarta"
Daddy yace

  "Rabu da wannan shagwababbiyar "
Dama abunda bash yake so kenan..don haka ya tashi yabi bayanta mr president kuwa ya cigaba da cin abincinsa sultan kuwa sun koma falo da waleed. daddy ya juya yana kallon Dan nasa yace

"Boy wai fushi kayi "
Shiru bai amsa bah daddy ya shafa kansa yace
  "C'mon..smile my boy, kam tsufa ai fushi ba naka bane "
Ya hada rai yace

"Toh..daddy ba Kaine kake min fada akan laifin da ba nawa ba"

😳😳😝😝😝shuairat bata San lokacin da dariya ya kubce mata bah tace 
"Oh...dad sultan yaranka suyi shagwaba kaima kayi?

"Daddy ka jita koh..
"Yi hakuri boy din daddy duk laifina ne OK"
Haka daddy ya cigaba da lallaba mr president tamkar wani karamin yaro shuairat kuwa sai tsokanarsa take tana mamakin irin son da daddy yakewa dannasa Sam baya so yaga bacin ransa ko kadan.

Umaima kuwa ta fada gado tana rusa kuka ..ita ba kalaman bash ne damuwarta ba aa xancen hadata da wani da daddy yayi ne ya daga mata hankali ..shikenan ta rasa bash har abada! Ya shigo ya tsaya yana kallonta bata ji shigowarsa bah ya nemi kujera ya xauna a hnkli ya furta 

"Tashi ki xauna magana xamuyi"
Ta juya jajayen idanunta tace

"Baka da abunda zaka gaya min kawai ka fita ka barmin daki "
"Look umaima am sorry bansan kalamai na zasu bata miki rai haka bah...am sorry pls"

..hmmm lallai ma wato ba zuwa yayi yace yana sonta ba kawai yaxo bata hakuri akan silly maganar da yayi dazu? Bash y? Meyasa yake wahalar da xuciyRta?...umaima CE ke wannan tunanin hawaye wani na bin wani ta nuna masa kofa ckn tsawa tace

"Out of my sight ..now!
"Sorry...
   "I said...out...nowww!
Ta karasa ckn daga murya nan ya juya ya fita ckn bacin rai ita kuwa ta kara fashewa da wani sabon kuka 
"Shikenan na rasashi har abada"

  "Baki rasashi bah matukar ina Raye...babu abunda zaki nema a duniya ki rasashi umaima"
😳😳😳 ta juya don tabbatar da abunda kunnuwanta Suka jiye mata ...carab! Suka hada ido....


Muje xuwa...
[2/21, 2:41 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*80*
By *Reefat yahya*

*dis page is dedicated to Rabeah majeed😊 tnx 4ur kia*
N ~2all fanz of nida shugabankasa ina sonku sosai..mr president ma yana sonku. Jameelah feekah n co, tnx to u all~


Umaima tana daga kanta Suka hada ido da shuairat tayi saurin sunkuyar da kai shuairat ta karasa tare da rungumarta tana rarrashinta umaima kuwa sai hawaye ke fita a idonta tana kuka ..wani irin radadi take ji a ckn xuciyarta 
"Umaima am sorry..I donno hw u feel abt dis but am very sory"
Ta share hawayen da yake xuba tace

 "Mom pls..ki taimakamin ina sonsa bazan iya rayuwa idan babu shi bah"
  "Zaki rayu insha Allah..ki kwantar da hankalinki burin ki zai cika ckn kankanin lokaci"
 
"Kina nufin zaki taimakeni"
"Matukar hakan zai sanyaya ranki umaima I can do dat 4u"
Nan umaima ta kankameta ta cigaba da kuka tana cewa 

  "Tnx so much...I Lov u mom sultan"
"Shhhh...ya isa haka bana son ki sake cewa komai, kiyi shiru da bakinki ki xuba ido..yaya zaixo ya durkusa a gabanki ya furta miki kalmar so harma ya nemi ixinin aurenki I promise"
Haka shuairat ta cigaba da bawa umaima hakuri dakyar ta daina kuka daga nan Suka tashi don gabatar da sallan la'asar.

D next day Suka koma ABJ daddy ya wuce Lagos umaima bata kara saka bash a ido bah duk tabi ta damu.
   Da dare shuairat tana xaune a falo aka sanar da ita xuwan yayan nata nan ta bada ixinin shigowa dama ita kadai CE a falon ya shigo tare da sallama ta amsa Suka gaisa ya fara magana
"Baby magana zamuyi ta fahimtar juna pls..kada ki boyemin komai ok"
  "Ok my yaya..go ahead"
"Baby.. Kin xauna da shukrah sama da 10yrs kinfi kowa sanin halayenta shin wai dama kinsan bata da halaye na gari shine kika bada shawara na aureta?

Tambayar yaxo mata a bazata..ita ta dauka zancen umaima zasuyi...muryarsa ne ya dawo da ita daga tunanin

"Answer me..."
"Umm..emmm yaya u knw wat"
   "C...baby don't dare lie to me ki fadamin gaskiya"
"Calm down pls yaya...meya faru tsakaninka shukrah just tellmi"
"Babu abunda bai faru bah..shukrah ta canzamin gaba daya, she is now a monster"

"Subhanallah..yaya y u saying dis...
Idanun bash sun kada sunyi jaa dakyar yace
 "Bazan boye miki u r my 6* n she is ur friend.. Baby nayi nadamar auren shukrah"

"Innalillahi...abunda shuairat take nanatawa kenan dakyar ta daure tace
"Yaya am very sory abt dat...but kowa yasan shukrah is a good person maybe zugin kawaye ne "
Tsaki yaja Sam babu mafita don haka xumbur ya mike ya mata sai da safe yayi tafiyarsa , shuairat ta kasa motsawa daga inda take lallai shukrah na ckn matsala dole ta nemi hanyar da zata bi ta daidaita tsakanin su. Dare yayi sosai tana nan xaune a falon gaba daya ta rasa me ke mata dadi, mr president ne ya shigo ya sameta da taimakonsa ta rage yawan tunanin da take sukayi shirin kwanciya.

***bayan 2weeks umaima ta gama jarabawar first semester dinsu saura semester daya ta gama makarantar Hutu na musamman mr president ya shirya musu dama sultan suna Hutu , tafiyar kasar China ya shirya musu xasu kaiwa Chinese president xiyara a hong kong daga can zasu je Singapore da kuma Korea ..murna tamkar suyi yaya nan kuwa ya kira bash ya sanar dashi cewa tare zasuyi tafiyar don haka ya shirya shi da iyalinsa duk zasu tafi.
    Ckn tsananin farin cki ya wuce gida yasan dole zasu shirya da shukrah a Daren yau matukar taji wannan kyakkyawan albishir don kuwa zaman nasu har ynxu babu wani sauyi tana gallaza masa son ranta...bash yana da hakuri sosai samun irinsa a wannan xamanin se a tona, bai taba gayawa wani sirrin zaman nasu bah face shuairat itama bai sanar da ita komai bah...ya shigo falonsu babu kowa daki ya wuce kofar a bude take  yasa kai xe shiga kenan Amma abunda kunnuwansa sukaji yasa yayi Saurin komawa da baya ya labe a gefe yana sauke numfashi... Shukrah tana magana ne a waya tana kuka tace 

"Anti wllhi jinin yaki tsayawa kuma Dr ya gayamin cewa pills na tsarin iyali da nayi amfani dasu su Suka jawomin wannan matsalar"

Tayi shiru da alama tana sauraron me ake gaya mata daga dayan bangaren sai kuma tace
"Ni ba wannan bane matsalata..cewa yayi dakyar idan zan sake haihuwa saboda mahaifar ta lalace"

"Innalillahi wa innailaihi raji'un..abunda bash yake nanatawa kenan.hawayene ya fara gangarowa bisa kuncinsa ya runtse ido, shukrah ta cigaba da cewa

"Idan yaji wannan maganar nasan sakina xaiyi..kuma wllhi iyayena ma zasuyi fushi dani, pls anti ki taimaka min yau ya zanyi? ..wayyo Allah na wllhi sharrin shaidan ne da kuma fa....
Bata karasa ba taji takun mutum a bayanta ckn hanzari ta juya Suka hada ido ya bita da wani mugun kallon da bata ganin irinsa bah😳😳😳😳
Wani gumi take hadawa ga fuska chabe2* da hawaye ba shiri ta sake wayar hannunta ckn raxana.......
...
...nima na ajiye tawa wayar

Hmmm ya bash zaiyi da ita?
Sakinta zai yi ?
Wane mataki zai dauka?
Ku biyoni...Lov u all😘😘
[2/21, 2:41 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*81*
By *Reefat yahya*


Hawayene yake gangarowa a fuskar bash ya durkusa a gaban shukrah yana kuka yace

  "Shukrah me na tsaremiki a Rayuwa ...wace irin tsana kike min da har yasa bakison hada jini dani..wane irin laifi na aikata da nayi deserving irin wannan punishment din tell me plsss..."
Ya karasa maganar yana kuka me ban tausayi shukrah ta xauna dabas a gabansa ta cigaba da kukanta tace
  "Yaya don Allah ka yafemin nasan na aikata laifuka da dama a gareka amm...

Bai bari ta karasa ba ya dauketa da wani wawan mari xuciyarsa se tafarfasa take nan ya tashi yabar dakin..shukrah ta cigaba da rusa kuka ta nadamar abubuwan da ta aikata masa itakam fatee ta cuceta kuma laifinta ne daga haduwa da mutum a watsap se ta biye  mata ta rusa farincikin gidanta..kuka sosai takeyi tana jawa fatee Allah ya isa ( ni Reefat nace ..ohh dama ke bakida tunani ne kawai daga haduwar watsap...mtsww🙄🙄🙄 duk masu biyewa kawayen banza haka zasu kare ..Allah ya tsare mu da sharrin mugayen mutane)
Bash yana fita ya shige motar sa ya hada kai da guiwa yana kuka tamkar karamin yaro , ya share minti 30 yana kuka sannan ya fara kiran sunayen ubangiji ya dan samu sauki a ckn xuciyarsa daga nan yaja motar be tsaya koina ba sai gidan mahaifinsa.ya fito ckn sanyin jiki ya karasa ckn gidan waleed ne ya rugo da gudu ya fada jikinsa yana cewa 

"Oyoyo Abba Nah "
Murmushn karfin hali yayi nan kuma ya tuna da zancen shukrah ya jawo yaron ya kankameshi sosai a jiki nan hawaye ya malale fuskarsa , mama CE ta fito daga daki tana Neman waleed turus...taja ta tsaya bata taba ganin dan nata ckn wannan halin bah .tayi gyaran murya tace 

"Waleed kaje daki ka jirani ina xuwa"
  "Yawwa mama..zaki bani sweet koh"
"Ehh..je ka xauna banda kiriniya gani nan xuwa ynxu xan kawo maka sweet har da chocolate"

Yaron ya hau tsalle nan ya sake uban nasa ya ruga aguje xuwa dakin mama , bash ya xauna kasan carpet yayi shiru ya kasa furta komai.mama kuwa ta juya xuwa dakin mijinta ta kirasa tare Suka fito bayan sun zauna baba yace
"Ni bazan nemi jin matsalar ka bah..koma menene kayi kokari ka kasance mai juriya da jajircewa, shi zaman duniya iyawa ne kuma mai hakuri shi zai dafa dutse har yasha romonsa..Dana! Na dade da gane cewa kana ckn matsala tun ba yau bah na lura da ramar da kakeyi nasan kana ckn damuwa kwarai da gaske kuma naji dadi da ka iya rike sirrin aurenka alhamdulillh ..hakan na nuna cewa ko bayan raina xaka iya rikemin iyalina"
Ya dan ja dogon numfashi sannan ya cigaba da cewa 

  "Nasan damuwar tsakaninka da matarka ce sabida baka rasa komai na rayuwa bah..don haka ina mai baka shawara ka cigaba da Hakuri wata ran zaizo karshe koma menene matsalar kayi kokari ka shawo kanta"

Bash yayi shiru ya jingina da kujera yana nazarin kalamn mahaifin nasa sannan ya share hawaye Muryar mama yaji tana cewa
"In banda shashanci matarka CE zata sa ka kuka kamar wani karamin yaro? Ai nasan dama zaa rina don ni kaina shukrah ta fara nunamin rashin kunya bare kai...dama Allah yayi ka shiru2* ba dole ta hau kanka ta xauna bah..tirrr! Allah wadai da mijin da zai xubda hawayensa saboda mace"

  "Haba Fatima..ke da xaki bashi hakuri ki gyara tsakaninsu Amma kuma kina...
"Ah-ah Alhaji..abun ne da ban haushi wllhi, dubi yanda yaron nan yake zubar da hawaye tamkar wanda ya rasa iyayensa..toh wllhi bazan lamince hakan bah, don kawai ina zuba ido bana magana? Wllhi hakuri na ya kare dole na dau mataki akanta"

Baba yayi murmushi yace 
   "Kai mataa..halinku da tunaninku duk iri daya wllhi..toh in banda abinki Fatima kinsan me ya shiga tsakaninsu ne da har kike ikirarin daukan mataki?"

"Koma menene ai nasan ba karamin Abu bane zai sashi kuka irin haka"
   "Wannan duk ba matsalar ki bace ..kuma babu ruwanki da maganar"
"Ya zakace babu ruwana a cki..dana ne fah?
"Sannu masu da' .."
Bash kam haushin kansa yakeji meyasa zai dagawa iyayensa hankali? Nan yayi gyaran murya yace

"Baba ..mama..Ku gafarceni maganar bata kai haka bah..ni aure nake son karawa ina Neman amincewar Ku"
    "Dakyau yarona..Allah ya maka albarka , haka ake son namiji ya kasance mai xuciya ba wai ka xauna da mace daya tana wulakanta ka bah..haba ga mata nan birjik. ...gaskiya naji dadin wannan zancen"
Mama CE tayi wannan furucin ckn jin dadi ta juya tana kallon mijin nata ya watsa mata harara yace

"Yanzu ke idan nace zan kara aure zaki amincene ?
 "Aure? Hmmm..Alhaji kenan! Ya kake magana kamar karamin yaro"
Maganar taso bashi dariya ya gimtse yace

"Toh ni ban amince da auren bah..matukar kika dage kuwa nima auren zan kara"
Yana gama fadin haka ya juya yabar falon mama ta bisa da ido ta tabe baki tace

"Kaji dashi..masifaffe kawai"
Nan ta maida hankali gun bash tace
"Kana jina koh...matukar ka tabbatar da cewa baka jin dadin zama da shukrah toh ni na baka dama ka kara aure, domin bazan shiga hakkinka bah..mu muka hada aurenku da shukrah kayi biyayya bakayi gardama bah don haka yanxu ina baka goyon baya ka auri duk wacce kake so..Allah ya tabbatr da alkairi ya kuma xaba maka mace ta gari "
Yaji dadin kalamanta sosai yace

 "Nagode mama insha Allah zanyi yanda kika ce...ke dai ki cigaba da min adu'a"
"Ba damuwa tashi kaje ..Allah ya maka albarka ya baka nasara akan abunda kayi niyya..Amma pls ban amince maka da sakin shukrah bah, duk irin laifin da maka kada ka kuskura kace zaka mata saki kaji koh"
   "Nagode mama insha Allah zan kiyaye..Amma kina ganin baba zai amince kuwa bayan ya nuna baya so"
"Barni dashi zai sakko ne ..kaidai ka cigaba da Neman auren naka zan tayaka da adua"
"Ok Nagode mama "
Daga nan ya tashi ya shige dakinta sai ynxu yaji sauki a ckn xuciyarsa , abinci ya nema yaci sannan ya fara hira da waleed yana biye masa sunata shirme.


*****saura kwana 2 tafiyar tasu sun gama duk wani shirin da zasuyi umaima sai xumudi ake don kuwa tana matukar son kasar China ...da dare  mr president da shuairat Suka je yin sallama da iyayen shuairat , a falo Suka tarar dasu a zaune suna kallon news har ynxu baba yana fushi akan maganar auren bash..bayan sun gaisa mr president ya sanarda baba zancen tafiyar da zasuyi baba yace

"Ohh..ni bello! Mutanene sai yawace2* yau kuna nan gobe kuna can..wai Baku gajiya ne"
Dariya sukayi shuairat tace 
  "Baba yaushe mukayi tafiya? Tun bayan dawowarmu daga hong Kong fah babu inda muka sake xuwa"
Baba ya jefa mata wani irin kallo yace 
"Watannin salman nawa? Ba uku bane ko hudu..bayan komawarki gidan kunje Lagos ..yola..mayo..maiha..mubi..kano ynxu kuma zaku tafi kasace sunkai biyar"
Dariya sosai suke yi shuairat tace 

"Ai yana da kyau mutum ya zagaya duniya yasan abunda ke cknta idan har yana da halin yin hakan..dama baba kasan traveling yana daya daga ckn likes dina "

"Hmmm...Allah ya bada saa ya kaiku lafiya ya dawo daku lfy"
"Ameen"
Gaba daya Suka amsa haka Suka Dan taba hira daga bisani sukayi sallama Suka tafi.


Ku biyoni...😘😘😘
[2/21, 2:41 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*82*
By *Reefat yahya*

*salam masoyana ina son sanar daku cewa bana karban ko sisi akan littafaina na samu labarin cewa wasu suna fakewa suna karban kudi kafin su turawa mutane littafai na , duk wacce ta karbi kudi da sunana ban yafe mata bah Allah ne zai mana hisabi ranar gobe kiyama..don haka masoyana ina son kusani cewa duk wacce tace ku tura mata kudi kada ku amince suna yin hakan ne don cimma wata manufansu Nagode...Lov u all*

11pm jirginsu ya sauka a hong Kong ..Chinese president tare da yan gidansa su Suka karbesu tun a airport cki kuwa harda jankim, ta rungume shuairat tana murnar sake ganinsu nan kuwa ta karbe salman a hannun umaima haka Suka karasa ckn mota sannan Suka dau hanyar gidan president.
   Kyakkyawan masauki aka basu tare da lafiyayyen abinci, bayan sun huta sun ci abinci tare da gabatar da sallolin da ake binsu nan kowa ya shige daki don ware gajiya.shuairat ta fada wanka tare da salman bayan tayi masa wankan tayi nata sannan ta fito mr president ma ya gabatar da nasa wankan nan sukabi lafiyar gado ya kankameta a jiki salman kuwa yana kwance haka sukayi baccinsu mai dadi.d next day Suka shirya Suka fita yawon bude ido..sunyi kyau sosai umaima kam hnklinta a tashe yake don rashin ganin bash duk da tasan cewa tare xasu xo da shukrah.. Yinin ranar gaba daya hnklinta a tashe yake tana tunanin ko lfy har dare Suka koma gida sun gaji likis! Sallah suka fara yi sannan sukayi Wanka , a dinning table Suka hallara amma banda umaima.jankim se zuba musu hira take sultan ma yana zaune a gefenta mr president de se dariya yake ..kamar daga sama bash ya shigo tare da waleed ckn kananan kaya suke sunyi kyau sosai se qamshin turare ke tashi ya karaso tare da sallama fuskarsa dauke da murmushi , kamar hadin baki umaima ma ta fito a wannan lokacin tayi kyau sosai ..sanye take da pencil trouser fari da pink 3qtr gown mai Karen kyau tayi parking kitson calabar dake kanta da pink ribbon ga uban lipgloss a bakinta se sheki yake ..gaba daya kallonta suke musamman bash da ya gagara zama har ta iso ta jawo kujera ta xauna yana tsaye yana kallonta mr president ne yace
 "Basheer xauna mana...yaushe ka iso"
  "Uhmm..amm dazu nazo nagaji ne shiyasa na biya hotel nayi wanka na dan huta"

"Ok yayi kyau..u wlcm zauna kaci abinci"
Waleed kuwa kusa da sultan ya koma jankim kuwa se satar kallon bash take gayen ya hadu😜😜 bayan ya xauna ne shuairat tace

"Yaya ina ka baro shukrah"
  "Tana gida wllhi ..akwai bikin da zaayi a can Adamawa shine tace barata samu daman xuwa nan bah"
Shuairat ta tabe baki tace 
  "Ikon Allah..shukrah da son zuwa outside shine tayi rejecting? ..abun mamaki"
"Auren Ya'r uwar mamanta ne daz y"
"Ok Allah ya tabbatar da alheri "
   "Ameen"
Daga nan ya xuba abinci ya fara ci a hnkli..Amma gaba daya idanunsa na kan umaima wacce ta sunkuyar da kai tana shan fruit salad..shuairat ta lura da hakan tayi murmushi tace 

" umaima gskiya kinyi kyau sosai irin wannan kwalliya haka ai se ki rikita mutane "
Bash ya daga kansa Suka hada ido da shuairat ta masa gwalo yana hararinta mr president ne ya tashi yace

"Nidai bacci zanyi don na gaji sosai gudnyt evr1"
Nan ya juya ya tafi jankim ta tashi tare da sultan da waleed falo Suka koma tana basu tarihin kasar China da harshen turanci..shuairat ma ta tashi rike da salman tabi bayan mijinta.
Umaima ta tashi kenan taji Muryar bash yana cewa

 "Kema tafiya zakiyi ki barni"
Harara ta watsa masa tace
  "Me zan maka idan na xauna"
Murmushi mai daukar hnkli ya sakar mata yace

"Haba dad"s gal...we used to b gud frenz b4 bansan laifin me na miki ynxu kike wulakantani"
Sunkuyar da kai tayi tana kallon kasa don bazata jure ganin murmushn nan nasa me daukar hnkli bah..
 "Kinyi shiru umaima tel me..

"Ba komai" daga nan ta cigaba da tafiya 
"Pls.umaima dawo ki zauna"
   "Uncle bash kayi hkri bacci zanyi"
"Bazan hanaki bacci bah ..but pls kibani koda 15 mins neh"
Duk abunda takeyi hudubar shuairat ne nan kuwa tayi murmushi lallai plan nasu ya fara aiki

"Pls...pls ki taimaka min"
Ta juya ckn salon yanga tace
     "Ok..ur time starts now"
"Tnx..but dawo ki xauna "
"Hmmm..namiji kenan wato don matarka bata nan shiyasa kake kulani koh"
      "Bahaka bane umaima just listen to me"
  " go on..ina sauraronka" nan ta ja kujerar dake fuskantar nasa ta xauna yaja dogon numfashi sannan ya fara magana
" shawara nake nema"
"Uhmmm..."
"Aure nake son karawa umaima"
Da Sauri ta daga kai Suka hada ido tayi saurin dauke nata tace

"Uhmm...toh me nawa a cki"
"Taimako nake so umaima"
    "Uhmmm...
"Amm...jankim xan aura pls ko xaki iya taimakin ki mata magana"
Ta daga kai tana kallonsa ..lallai wannan Dan rainin wayo ne..hmmm wato ma..

"Ya kikayi shiru..pls ki taimakamin "
"Bazan iya bah ka sameta da kanka ko ka tura mom sultan"
Daga nan ta tashi tsaye tace 

"Time up..gud nyt"
ta juya ta fara tafiya yayi saurin tare gabanta yace
"Pls...ki taimaka am serious, yarinyar ne tana da kyau ga kuma hnkli nasan xamu xauna lfy da ita"
Xuciyarta na bugawa ta sunkuyar da kai ta cigaba da tfy ya sake shan gabanta yana leka fuskarta ga mamakinsa hawaye ne ya gani suna gangarowa a hnkli ..nan kuwa ya rude ckn rawar murya yace

"Umaima am rily sorry..I din min to hurt u pls kiyi hkri"
Ta turasa a gefe da gudu ta wuce xuwa dakinta.bisa gado ta xauna ta hada kai da guiwa tana rera kuka ..dama haka so yake? Dama namiji idan ya fahimci cewa kana sonsa haka xe wulakanta kah?  Haka ta cigaba kukanta me ban tausayi...bash kuwa zama ya gagareshi domin kuwa yau yaxo da niyyar faiyace mata sirrin xuciyarta , baiyi wani tunani bah ya wuce dakin da yaga ta nufa a hnkli ya tura kofar tana xaune tana kuka ckn hnxri ya karasa kusa da ita ya sunguna a gabanta yace

"Umaima am so sorry pls...kibar wannan kukan da kike I hate it"
Ta daga kai ckn jajayen idanunta tace
"Bana son ganin ka ..ka fitar min a daki I hate    u"
Ta sake fashewa da kuka, bash ya zama abun tausayi yace 

"Kiyi hakuri nasan na bata miki...but I have my own reasons"
   "To hell wit ur reasons... Leave now..I min now"
Ta fada ckn daga murya bash ya sauke numfashi a hnkli yace

"But I lov u umaima"
😳😳😳ckn mamaki ta daga kanta Suka kurawa juna ido yace
  "Yes if coz...i do Lov u from d very moment i saw u, ina son ki umaima "
Itakam ta kasa gane yanayin da take cki wai da gaske yau bash ne ya furta cewa yana sonta???????

.....

Hmm muje xuwa
....Lov u all😘😘
[2/21, 2:41 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*83*
By *Reefat yahya*


*am still emphasizing abt dos dat r collecting money o recharge cards b4 forwarding my novels,....... pls my fanz if som1 ask u abt money just ignore dat person tnx n love u all...mssg from Reefat yahya*

Kallon -kallo suke ..bash ya fara magana 
"2b frank..umaima I rily Lov u, in fact u r d 1st girl I ever Lov in my lyf...ina sonki umaima.na kasa furta miki ne saboda gani nake ban dace dake bah..a da can baya kina matsayin Ya'r shugabankasa nikuwa ni talaka ne kinga soyayyar baxata yiwu bah" 
    "Leave my room now... Bana son rainin hankali, ni zaka maida karamar yarinya?...pls uncle bash just leave plss...."
Idanunta sun cika da kwalla bash yasa hannu zai share mata tayi saurin buge masa hannun murmushi yayi sannan ya tashi tare da tura hannu ckn aljihu yace

"Dama nasan bazaki yarda da abunda na fada bah...but I want u to know dat I love u...n I'll never stop loving  up2 eternity"
Daga nan ya juya yabar dakin umaima kam kwanciya tayi a gado a hnkli wani sanyi ya fara ratsa xuciyarta wani farin cki ya lullubeta ...ikon Allah  kenan, dama bash yana sonta? Wow....alhamdulillh Allah Nagode maka" bitt...ta tashi ta fada toilet alwala tayi ta fito ta fara nafila...ohhh su umaim buri ya cika😀😀😍😍.

Da safe sun hallara a dinning table suna kari amma banda umaima saboda jiya batayi bacci da wuri bah..bayan sun gama karyawa kwata2* hnklin bash baya jikinsa saboda rashin ganin umaima yana tunani ko wani abu ya faru da ita...shuairat ta lura da halin da Dan uwan nata yake cki tayi murmushi tace
  "Ummm...su bby gal kam anata sharar bacci"
 Mr president yace 
   "Ba dole bah...jiya ina jin motsinta a falo I tink batayi bacci da wuri bah"
Gauron numfashi bash ya sauke Suka hada ido da shuairat tana murmushn gulma tare da daga masa gira ..ya shareta saboda mr president.bayan sun gama kowa ya wuce sabgarsa yaran sun wuce wajen wasa shuairat kuwa daki Suka shige tare da mijin ta, bash da jankim ne Suka rage a dinning.jankim tana jansa da hira ba laifi yana amsa mata a can daki kuwa shuairat ta kwantar da salman a kasa mr president yana gefe yana masa wasa tace zata duba umaima daga nan ta fice xuwa dakin umaima, tun a bakin kofa hancinta ya shaki wani dadaddan qamshin turare tana budewa kuma subhanallah....umaima ce ckn Chinese silk gown mai uban kyau armless gown ne pink touches of blue ta saka blue fashion earings na R&R tayi kyau sosai wani karamin blue veil ta yafa a kanta da ya sha gyara se shinning yake..shuairat tace

"Masha Allah...princess is looking gorgeous, kinyi sosai zaki haukatar da yaya Nah"
Umaima ta fada jikin shuairat cike da jin dadi tace

  "Wllhi jiya ya furtamin..yace yana sona..I can't bliv it"
  "Dakata malama! Irin azarbabi haka? Kinga..bawai haka zaki fito kina ta xumudi bah no! Ckn yanga da Jan hnkli xaki fito masa ki kame kanki idan kinje gaisuwa kawai xakiyi mai kingane ai"
  "Ok tnx mom sultan... I'll surely do dat"
"Yawwa..bawai kije kina wage baki bah..ki kame kanki ki ja aji kada kije ki fara xuba kamar aku"
Murmushi umaima take daga nan ta dauko wayarta tace

"Na tafi..kimin adua"
"Allah ya bada sa'a "
Shuairat tana mmkin irin son da umaima takewa yayn nata daga nan ita ma ta koma gun mijinta Suka cigaba da hirarsu.
A hnkli take tfy qamshin turarenta ne yasa bash ya daga kansa ya juya tare da kura mata ido..shi kadai xaune a dinning yana kurba coffee a hnkli don jankim ta tafi duba patients nata , umaima ta karasa kafin taja kujera bash ya rigata ya jawo wani kujera kusa da nasa ya nuna mata babu gardama ta xauna fuskarta dauke da murmushi tace

"Morning uncle bash"
"Morning.. But nifa bana son uncle din nan gara ma ki nemi wani sunan daban"
    "Toh kai ba uncle dinmu bane..yayan mom "
"Naji...but bana so"
Bata ce komai ba ta fara xuxxuba abinci ..samosa ne da source sai kuma chips da kwai ga kuma oda Chinese dishes , soyayyen kwai kawai ta dauka guda 2 sannan ta hada tea da jinseng coffee ta fara sipping a hnkli komai nata ckn yanga bash de se kallonta yake ita kuwa dadi kamar ta fasa ihu..ya katse shirun da cewa

  "Baki ce komai dangane da maganar da mukayi  jiya bah"
  "Aw..xancen jankim wai...maybe anjima xan...
     "Umaima! Ya kira sunanta da wani salo saura kadan ta kware😜😜 ya cigaba da cewa 
"Haba umaima... U knw i was just kidding about jankim, pls joke apart umaim ina son ki wllhi am serious"
Bata tanka masa bah ta cigaba da kurba coffee tana lumshe ido wani dadi takeji shi kuwa bash lumshe ido da take ya burgesa yana kara jin sonta a ckn zuciyarsa 

"Umaima pls naa...ya marairaice ta juya tana dariya tace
 "Uncle bash u r not serious"
Nan ta tashi rike da cup a hannunta dayan hannun kuwa rike da phn ta juya da niyyar tafiya yayi sauren tare gabanta yana mata wani kallon so ya marairaice yace

"Pls say somtin..
    "I don't have anything to say"
"Haba umaima ki tausaya min plsss...
"Uncle bash am sorry..is too late cos an riga an zabamin mijin da zan aurah"
"Waat.....????
Kawai bash ya yanke jiki ya fadi😳😳😳
Ckn razana umaima ta sake cup din hannunta ruwan ya xube a kafarta amma ko kadan bataji xafinsa bah ta fara jijjiga bash ..hawaye sun fara saukowa😰😰😰 nan nima na fara kuka nace shikenan mayb xuciyarsa ta buga.....

Fans ku taya umaima da adua Allah ya tashi kafadar masoyinta😜😜😜😜 idan ya mutu kuma😫😫😫


Lol...ku biyoni kusha labari😊😊😊
[2/21, 2:42 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*84*
By *Reefat yahya*


Umaima ta cigaba da kukan da take tana kiran sunansa a hnkli ta kwantar da kanta a kirjinsa tana rera kuka tana cewa
  "Uncle bash I so much Lov u pls ka tashi kada ka barni ..I can't do widout u pls .."
ta cigaba da kukan ta daga karshe ta yanke shawarar xuwa kiran shuairat da dad don haka ta tashi tana share hawaye kawai taji ya jawota ta fada jikinsa ya kankameta yana mata rada a kunne 
  "Don't leave me baby..I Lov u too"
Ckn raxana ta juya Suka hada ido yana murmushi ya lakuce hancinta yace
   "Ashe dai ana ana sona ..dama Jan aji ne"
  Ckn tsananin kunya umaima ta zame jikinta daga nasa da niyyar guduwa ya cafke hannunta sannan ya tashi tsaye yana rike da hannunta Suka wuce falo a kasan carpet Suka xauna suna mai fuskantar juna
  "Na tsorata ki koh?...sorry bazan barki bah har abada muna tare insha Allah"
Ckn jin kunya ta rufe fuakarta yasa hannu ya cire yana kallonta ckn so da kulawa yace

"Plss..umaima ki amince da soyayyata wllhi ina kaunarki pls ki yarda dani "
Bata ce komai bah ya daga habarta yana mata wani kallon sace xuciya😜 ya wani marairaice tamkar xeyi kuka yace 

  "Pls baby Nah...don Allah kiyi accepting dina don Allah..
Nan ma shiru batayi magana ya sake make kafada yace
    "Plss...don Allah fa nace"
Bata San lokacin da ta fara dariya bah tace
"Kai uncle bash.. Kamar wani karamin yaro "
  "Nidai ki amince da soyayyata pls"
"Ok fine...i'll tink abt it"
"Haba baby Nah..me abun tunani a ciki , kin sanni kinsan iyayena da halayena me abun tunani a cki"
  "Umm..I know but just give me somtym "
"Ah-ahh nikam bana so ..ynxu xaa bani amsata if not kuka zanyi"
   "Haba uncle bash..
"Haba baby...
Yana kwaikwayon abunda ta fada nan ta fara dariya ya kura mata ido sosai yake jin sonta na bin duk ilahirin jikinsa ya girgiza kai yace 

"Allah..ameen"
"Mene uncle..
  "Adua nayi ina rokon Allah a ckn xuci"
"Hmm..aduar ma sirri ce"
    "Ehhh..bana son kowa ya ji aduar tawa se mala'ku kawai da kuma ubangiji na"
"Uhmm..yayi maka kyau"
   "Umaima Allah kina da kyau sosai"
"Tnx.."
     "Ba tanx xaki fada bah.. Kice ina sonka my love"
Dariya take haka suka kasance duk nacin bash umaima taki nuna masa cewa ta amince da soyayyarsa.

Da yamma kowa ya dau wanka banda jankim wacce take gun aikinta yaukam har matar Chinese president tare Suka fita sunje yawo sun zagaya wurare da dama tana nuna musu gidajen tarihi mr president yana manne da salman a jikinsa duk inda sukaje hannunsa na sakale da hannun shuairat sultan da waleed kuwa suna makale da bash sun hanashi sakewa da umaima ita kuwa dariya take masa duk sanda Suka hada ido gwalo take masa ya cika yayi famm...se bayan isha Suka koma gida a gajiye.
      Kowa ya wuce dakinsa sultan da waleed kam bacci Suka fara yi tun a ckn mota dama sun ci abinci a restaurant don haka daki kawai bash ya kaisu Suka cigaba da baccin da suke. Umaima tayi wanka ta shirya ckn kananan kaya tea kawai take bukata don haka ta fito xuwa dinning table ta xuba ruwan xafi da Lipton ta saka Zuma instead of sugar..earpiece ne a kunnenta tana jin wakar *tum hi ho*na ~ashique~ ..tana matukar son wakar kamar Reefat😍😍wakar na sanyaya mata xuciya yana sata manta duk wata damuwar da take cki..a hnkli take sipping black tea nata ckn kwanciyar hnkli bata Ankara bah taji ana bin wakar ta juya Suka hada ido da bash ya cire mata earpiece na kunne 1 yana sauraron wakar yana bi ..murmushi yasakar mata yana daga gira umaima tayi saurin dauke kanta yasa bakinsa dai2* kunnenta yana bin wakar inda ake cewa
~zindagee abhi tum hi ho~ wani irin mutuwar jiki umaima take ji gaba daya jikinta ya mata nauyi tana kallon kasa yasa hannu ya daga fuskar tata ya kanne mata ido daya yace

"Ko zamuyi miming na wakar ne"
Ta kasa cewa komai ya hura mata iska a ido umaima ta tashi saye tace 

  "Me haka...pls bana so" ta juya tana tafiya ya rike mata hannu ta tsaya cak!
Yasa bakinsa ya sumbaci hannun tare da cewa 

"I Lov u my princess"
Da gudu umaima ta wuce zuwa dakinta don bash yana nemar xautar da ita...dama haka ya iya soyayya? Ta tuna muryarsa a lokacin da yake mata waka ...wow...tamkar shi yayi wakan ga husky voice dinsa 😍😍😍
"Oh God he is so....romantic I Lov him"
ta fada tare da rungume pillow tana murmushi ita kadai kamar wata xautacciya...qamshin turarensa ya gauraye dakin tana faman lumshe ido aikuwa tana budewa carab!! Idanunta sun fada ckn nasa wani kunya ne ya rufe ta nan ta cusa fuskarta ckn filo...murmushi yayi yace 

"Don't worry banji abunda kika fada bah..dama phn naki kika manta shine na kawo miki"
Daga nan ya juya yabar dakin yana murmushi.


      *******  Haka Rayuwa ta kasance sunyi 2weeks a hong Kong sannan Suka wuce Singapore....sunyi yawo sosai shuairat da mr president kam tamkar sabon ma'aurata soyayyar nasu ba'a magana haka nan bash yana nunawa umaima salon soyayarsa duk da cewa kunya ya hanata sakewa dashi Amma shi kam bai 
Damu bah...
Yau suna xaune a falon hotel da Suka kama a can Singapore, mr president ya fara magana 
"Umaima ina fatan baki manta da alkawarin mu bah...
Da Sauri ta daga kai tace 
  "Dad...alkawari kuma?
"Wateva..jiya daddy ya kirani yace suna jiran komawar mu cos iyayen yaron sun damu da xancen auren naku"
   "Aure kuma dad? N wane yaro kake nufi dad"

"Dan abokin daddy..suna jiran komawar mu xasu kai kudin aure sabida dama can daddy ya basu ixinin hakan "

"Waat?....kudin aure? Shine bazaa tambayeni ko ina son sa bah"

"Will u keep quite n listen...ki saurareni da kyau aurenki dashi babu fashi babu Wanda ya isa ya hana se Allah"
Mr president ya fada ckn daga murya 
Umaima ta fara kuka tace 

"Wllhi ni bana sonsa sai dai idan gawata xaa kai gidan "

"Wateva...idan ta kama gawar taki xaa kai se a binneki a can gidan nasa aure ne anyi angama idan kika kawomin wargi kuma gobe zamu koma a daura auren muga karshen tsiya"
Ckn bacin rai mr president yayi wannan furucin daga nan ya tashi ya wuce dakinsa shuairat tabi bayansa bash kuwa suma ne kawai ya rage baiyi bah..Amma matukar raxana kam ya raxana don mutuwar xaune yayi ko motsi ya gagara umaima fuskarta ya jika da hawaye ta juya Suka hada ido dashi nan ta tashi ta ajiye masa wani lafiyayyen mari har wayata ta subuce ta fadi😱😱😱...


Toh me laifinsa a cki?
Hmmm...ya zasuyi?
Shikenan bash ya rasa princess😫😫😫😫

Muje xuwa...Lov u all😘
[2/21, 2:42 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*85*
By *Reefat yahya*


Bash ya bude baki xeyi magana ta sake ajiye masa wani Marin tana kuka tana bugunsa ta zama tamkar wata xararriya tana cewa 

"Duk laifinka ne..kai ka jawo min wannan bala'in bayan kasan cewa duk duniya babu Wanda nake so sama da kai, shikenan ..gashi ynxu xaa rabamu hankalinka ya kwanata koh"
Ta cigaba da kukanta tana kai masa duka dakyar ya samu ya rike hannayenta se kiciniyar kwacewa take daga nan ya rungumeta gamm...a jikinsa tana kuka ta kwantar da kanta a kirjinsa wani sanyi ne ya ratsa xuciyoyinsu yana shafa bayanta a hnkli alamar rarrashi ..baa dau wani tsawon lkci bah tayi shiru se ajiyar xuciya take.. Yakai bakinsa saitin kunnenta yace
  "Am sorry...pls ki daina kuka I don't like it..yana dagamin hnkli"

Ckn wani murya mai ban tausayi tace 
"But uncle bash kana gani anason a rabamu"
    "Ki kwantar da hnklinki babu Wanda ya isa ya rabamu se Allah..idan Allah ya kaddara ke matatace babu Wanda xe hana hakan faru OK "..

Kai ta gyada masa haka ya cigaba da kwantar mata da hnkli ya rada mata "I Lov u*
A kunne se ynxu ta tuna yanayin da suke cki ..kunyane ya sa ta xame jikinta daga nasa tana rufe fuska yayi dariya yace
  "Anaso ana nokewa..bayan kin wani lafe min a jiki tamkar mage yanxu xaki nuna wai kina jin kunya"
Ckn shagwaba ta tura baki tace
        "Toh ba kai ka kwantar dani bah...ni nace maka ina so ne"
Dariya sosai yake yana tsokanarta tayi fushi ta wuce dakinta ta barsa a tsaye yana dariya.

**d next day bayan sun gama brk mr president bai fito ya karya bah yana can daki shuairat tana faman lallabashi batun auren umaima fir..yaki amincewa yace aure babu fashi dole ta hakura ta rabu dashi ..ya fito falo fuskar nan a tamke , yaran suna kallon cartoon bash yana danne2* a wayarsa chatin suke da masoyiyar tasa don tana daki bata fito bah bayan sun gaisa da mr president yace masa ya kula da yaran su xasu wuce Korea dashi da matarsa sai kuma salman..bash ya amsa masa ckn girmamawa.shuairat ce ta shiga dakin umaima tana kwance a gado tana chatin nan ta tashi xaune 
"Mom sultan anguwa zaki ne irin wannan kwalliya haka tamkar mai shirin xuwa dinner "
Murmushi shuairat tayi tace
  "Zamu wuce Korea shine naxo miki sallama"
     "Aw...mijin nake fushi yake damu koh..babu damuwa Allah ya tsare hanya "
  "Uhmm..rabu dashi xamuyi maganar insha Allah yayana xaki aura"
Ta tabe baki tace 
   "Hmmm..nidai na karaya, cos ban taba ganin dad yayi fushi irin haka bah..ko meyasa oho"
"Don't worry I'll handle him..bari muje Korea xamu daidaita lamarin"
      "Allah yasa"
"Ameen...insha Allah xamuyi nasara ki kwantar da hankalinki ki tayamu da adua"
"OK tnx..n safe trip"
"Tank u..ki kula da kanki da kuma sultan n waleed"
    "Ok..I'll "
Daga nan Suka rungume juna se kuma shuairat ta juya ta tafi.
Airport yaran Suka musu rakiya amma banda umaima daga can Suka hau jirgin xuwa *Seoul city of Korea* bash ya juya ya koma gida tare da waleed da sultan.

Da yamma Suka shirya ckn kananan kaya gwanin kyau wani filin shakatawa Suka je ..waleed da sultan na ckn cable car suna viewing wani mountain mai kyawun gaske umaima da bash kuma suna xaune a karkashin wata bishiya bash ya juya yana kallonta se murmusawa yake umaima tace

"Uncle bash kallon ya isa haka mana"
 "Ina ruwanki.. Ke nake kallo?..mutum da matarsa"
     "Ummm...Allah yasa"
   "Kefa na lura Ke matsoraciya ce...I told u not to worry Amma kin kasa kwantar da hankalinki"
Umaima ta marairaice tace 
    "Allah uncle bash bana son rabuwa da kai"
    "Mmm...shine baki taba cemin I Lov u bah"
 ta sunkuyar da kai tana wasa da yatsun ta yayi murmushi yace
"Ba ga irinta nan bah..shiyasa shukrah take burgeni cos bata jin kunyata ko kadan"
 Jin ya ambaci shukrah umaima ta hada rai se ynxu ta tuna cewa yana da wata a gida Ashe ba ita kadai bah..wani kishine ya turnuke ta , bash yana sane yayi maganar yana son ganin ko xataji haushi ya cigaba da cewa

"Kinga!.. Shawara xan baki ki daure ki rage wannan kunyan if not mijin nan naki na Lagos baxai...
Bata bari ya karasa ba ta jefeshi da wayar hannunta yana dariya nan ta tashi wai tayi fushi ta juya tana tafiya ckn axama ya dauki wayoyinsu yabi bayanta 

"Haba umaima daga baki shawara kuma se ya xama fada"
Tsaki taja tare da cigaba da tafiyan da take ya Dora hannunsa a kafadarta tayi saurin ture hannun yasake mayarwa ta ture haka Suka cigaba da abu guda..yace

"Smile mana amaryar mutanen lag ..smile plss.."
Ta juya tana shirin kuka yace
   "Ok sory sory...matar...mutanen lag "
A zatonta xai ce matar bash ne..nan kuwa tayo kansa da gudu yabar wajen tana binsa Suka fara guje2* gwanin shaawa wasu yan chinese suna daukarsu hotuna sai da umaima ta gaji ta fada kan wasu carpet grass mai kyau ..tana maida numfashi bash yaxo ya xauna a gefenta ta koma gefe ta kwanta fuskarta na kallon sama a hnkli take sauke numfashi.. Ya mirgino ya koma kusa da ita ya kura mata ido idanunta na kallon yanayin gajimaren dake sararin samaniya tana murmushi wani nishadi take ji bash kuwa ya shagala da kallonta se faman lumshe ido take dakyar ya iya furta mata 
"I Lov u my bby gal...I want to spend d rest of my life wit u"
    "I Lov u too"
Ckn mamaki ya juya Suka hada ido ta sakar masa wani kayataccen murmushi tace

"Yes of coz..I do Lov u wit all my hrt"
Nan ta fara mirginawa akan ciyayin tana murmushi haka nan shima yabi bayanta yace
   "I Lov u my swt hrt"
Tace "I Lov u too..Darling"
   "U are my hrt..
  "U are my soul..
"U are my air..
"U are my water..😜
"U are my world..
"U are my Paradise..
"U are my...my
"U are my everything😊😊

Hmmmm..ni Reefat nace abun ba sauki...tohfah *romeo n Juliet*

Hmmm ko burin masoyan zai cika???
Muje zuwa...Lov u all
[2/21, 2:42 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*86*
By *Reefat yahya*


Haka rayuwa ta kasance kwanaki na tafiya lokaci na shudewa mr president da shuairat sun share mako 2 a can *Seoul* soyayya kawai suke xubawa tamkar masoyan da Suka fito honey moon , a dayan bangaren ma hakan ta kasance tsakanin bash da umaima ..ko sau 1 bash bai nemi shukrah bah.
      Shuairat tana hada musu kaya a ckn jakan da Suka taho dashi  don jirgin yamma xasu bi xuwa hong Kong washe garin kuma xasu koma Nigeria. Mr president yana kwance da salman a saman kirjinsa shuairat ta juya tana kallonsu cke da so tace
  "Yobo...
tsaki ya ja yace
"Na gaya miki bana son sunan nan amma baki jin magana koh"
Ta fara dariya dama neman tsokana ce ta cigaba da cewa 
  "Haba yobo...sunan akwai dadi fah"
   "Mtsww..wane irin dadi ? Idan ana pronouncing kamar nayi amai wllhi.., ke kin wani dage mah kinsan meaning na sunan ne?

"Na sani mana..ba *honey* bah...haka naji suke kiran maxajensu"
  "Toh ni bana so...pls gara ki kirani honey direct akan wani yobo...kamar sunan mene oho!
Dariya sosai shuairat take masa bayan ta gama ta dawo kusa dashi ta xauna hannu tasa a hnkli tana shafa sumar kansa tana masa tafiyar tsusa tace
  "Swt hrt..magana xamuyi plss..
   "Yes...go on"
"Ahmm..dama maganar auren umaima ne"
    "Me ya faru "
"Pls swt hrt idan batason auren gara...
  "Um um madam...gara ma kiyi shiru da abunda kike son fada..aurene babu fashi undrstn?
"Haba mana my man...kasan fah...
  "Ayshata kiyi hakuri pls..kar maganar auren umaima ya jawo prblm tsakanina dake pls"
Shuairat ta tashi ckn bacin rai tace

   "Shikenan tunda ni baka daukeni a bakin komai bah..kuma don kana ganin bani na haifeta daz y"
Daga nan ta juya ta koma falo..mr president ya runtse ido yace
   "Na shiga 3 yazanyi da Aysha ta fahimci me nake nufi ne"
Kwantar da salman yayi a gadon yana masa murmushi yace
"Sorry son...ur mom is angry dole dad ya bada hakuri koh"
Yaron kamar yasan me uban nasa ya fada nan ya fara dariya mr president yasa kai ya fice xuwa falo ta jingina da kujera tana sheshshekar kuka😜😜kukan munafurci koh...hmmm.
Cike da tashin hnkli ya karisa kusa da ita ya jawota a jiki tana wani fusgewa ya kankameta sosai sannan ya fara magana 

   "Haba my lady kiyi hakuri pls...ynxu dan abunda na fada shine zakiyi fushi ki barni ..OK am rily sorry kiyi hakuri don Allah pls"
Bata kulashi bah ta cigaba da kuka gaba daya ta daga masa hankali ya cigaba da rarrashinta yana shafa kanta kamar wata karamar yarinya dakyar ta sagaita kuka tace
  " ynxu ne nasan matsayina kuma...
Ya tare numfashinta da cewa 
"Haba matata..ki daina irin wannan maganar pls I don't lyk it, ina son ki gane cewa bana son tilastawa umaima akan wannan auren but baxan faranta mata na bata ran mahaifina bah..daz y"
A hnkli ta daga kai tana kallonsa ckn mamaki tace

 "Kana nufin cewa daddy ne ya hada auren?
Kai ya gyada tare da cewa
   "Kin manta ranar da ya gaya mana wani abokinsa ne yake nemawa dansa auren?..shi daddy kai tsaye ya basu ixinin fitowa shiyasa nima bani da wani zabin "
 Ta kwantar da kanta a kirjinsa a hnkli sannan tace

"Dama yaya bash ne ke son aurenta"
Wani murmushi mr president yayi yace 
  "At last de ya fito ya gaya mata yana sonta kenan"
"Ehh...dama kasan suna son juna ne?
"Hmmm..na dade da gane cewa umaima tana matukar kaunar yayanki ..don kuwa lokacin aurensa da shukrah har rashin lafiya umaima tayi duk ina sane da komai kawai na xuba ido ne naga karshen gudun ruwansu"
Shuairat ta gyara kwanciya tace 
 "Ynxu me mafita?
"Mafita guda daya ne..kiwa daddy magana idan ya amince fyn, kinga yafi jin maganar ki idan ni na tunkaresa wllhi nasan rai na sai ya baci"
    "OK..Allah yasa ya amince"
"Ameen...don nima ina son farin ckin umaima kuma ko bayan raina nasan bash xe riketa da mutunci"
Haka Suka cigaba da hiransu kamar ba su Suka samu sabani bah...


********
Umaima tana kwance a kasan carpet din falonsu  ita da waleed da sultan littafin kawa'idi ne a hannunta sultan yace
 "Anty umaima na iya wannan fah..dama mom tana koyamin tun ina karamin yaro"
Dariya sosai umaima tayi sannan tace
   "Iyye..su boy din mom an girma koh"
"Ehh mana...ynxu na kara girma baki ga na xama kato bah, next year xan kamo tsayinki "
    "Lallai yaro ka rainani"
Waleed yace 
 "Anty maima..nima na girma koh"
Ta shafa kansa tace
  "Yh..my swt hrt ya girma"
Sultan ya bata rai yace
"Meyasa ni bazaki cemin swt hrt bah"
Murmushi umaima take don kuwa sultan ya dago ta , waleed yana kama da mahaifinsa sosai shiyasa take son yaron  tayi saurin cewa
"Bana son yawan surutu oya..mu cigaba da karatun"
Daga nan ta bude littafin tana karantawa sultan yana gaya mata fassarar idan yayi mistake ta gyara mishi ..tana mai cewa
"Tunda ka iya farillan alwala da na sallah da mustahabbansu , ynxu xamu shiga babin wajabta akan wanka da sunnoninsu..Amma kafin..

"Anty na iya duka fah"
"Kai sultan..
"Allah na haddace wannan littafin gaba daya, mom ce ta koyamin"
"Ok lemmi test u...babun fi guslil masnuni"
Sultan yana murmushi yace
   "Babi a ckn bayanin wanka na sunna"
"Wa Amma guslul masnunu fa sab'un"
"Wanka na sunnah guda 7 ne"
"Guslun ki salaatil iyadaini"
  "Wanka domin sallar idin karamar salla da babban salla"
"Wa guslun li salaatil jumu'ati"
  "Wanka saboda sallar juma'a"
"Wa guslun li dukhuulil makkati"
  "Wanka saboda shiga makka"
"Wa guslun may....
Bata karasa bah saboda jin kararar faduwar Abu , gada daya Suka juya ..bash ne ya fasa wani flower da akayi decorating falon dashi ..ya dade da shigowa Amma babu Wanda ya lura dashi.umaima ta tashi a gigice ta taka xuwa inda yake tana kallon jikinsa tace 
   "BB baka ji ciwo bah"
"No am ok"
Yana mata kallon so..falon Suka karasa ya xauna masu aikin gidan Suka shigo suna gyaran wanjen.waleed ya hau saman cinyarsa ya xauna yace 
  "Abbana kaga bro sultan ya iya karatu Amma ni Mamana bata koya min"
"Don't worry soon kaima anti maima xata koya maka idan ta koma gidan mu da xama"
 " lahhh..da gaske xata koma gidanmu"
Sultan ya juya yana murmushi yace
  "Uncle bash aurenta xaka yi? ...ohhhooo.. Shiyasa take kiran waleed da sweety"
Dariya sosai bash yake umaima kuwa haushin sultan ya cikata nan ta tashi xata kama shi ya gudu bayan bash ya tsaya kamar daga sama Suka ji Muryar mr president yana cewa

"Don ya fadi gaskiya shine zaki dake shi"
😱😱😱 ckn mamaki Suka juya shuairat ta shigo fuskarta dauke da murmushi nan kuwa umaima ta ruga a guje Suka rungumi juna.


Ku biyoni....
[2/21, 2:42 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*87*
BY *Reefat yahya*

*salam readers ina mai Baku hkri akan postinng din page 81 da wata tayi wacce bansan ko wacece bah( don't mind she is just trying 2b popular ne😜😜) but pls a kiyaye ban amince wata/wani ya canza min story bah duk wanda ya sake yi Allah ya isa kuma I'll take serious action about it..tnx fans.Lov u all😘😘*


8pm jirginsu na private ya sauka a babban kamfanin mr president daga nan driver ya saukesu gida bash kuwa gidan iyayensa ya wuce ...
    Washegari sun hallara wajen cin abinci, umaima ta fito ta jawo kujera ta xauna tare da cewa
"Morning dad..morning mom"
Shuairat ce ta amsa 
  "Morning ya gajiya"
"Akwai fah...wannan ma flight kenan , Allah nayi bacci mai nauyin gaske"
    "Yawon da kikayi a can ai is not easy"
Umaima ta marairaice tana kallon dad tace
"Dad shine ko hi babu"
  Yana kurban tea ya kalleta yace 
     "How r u"
"Am fine dad how was nyt"
    "Alhamdulillh"
Shuairat tana kallon sultan tace
"Boy ina alkawarin mu"
Murmushi sultan yake tare da cewa 
  "Mom ban manta bah..kin manta ke kika gaya min cewa idan babba yana magana kada na sa baki "
"Hakane my boy Ashe dai baka mantuwa"
  "Morning anty umaima "
Ta shafa kansa tace
  "Morning mom's boy"
Daga nan Suka cigaba da karyawa...wayar mr president ne ya hau ruri numban daddynsa ne nan ya daga tare da sallama

"Daddy Nah"
"Boy an tashi lfy"
  "Lfy alhamdulillh ya momsi "
"Lfy kalau ya iyali"
"Duka suna nan lfy "
"Masha Allah..dama xancen yaran nan ne gode idan Allah ya yadda muna nan tafe "

"OK Allah ya kawoku lfy"
Daga nan Suka ajiye wayan tare, umaima wacce ta kura masa ido kirjinta na dukan 3-3 shuairat ma haka ..ya lura dasu Amma ya share ya cigaba da cin abincinsa daga bisani yace
 "Gobe su daddy zasu zo tare da wannan mutumin "
😳😳😳
Umaima ta xare ido ckn firgita ta juya tana kallon shuairat. Shuairat tayi karfin hali tace
 "Kana nufin....
Hannu ya daga mata yace
   "Bana son jin komai..ba sharawa nake nema bah"
Daga nan ya tashi ya haura staircase xuwa floor dinsu, umaima kam hawaye sharr..wani na bin wani shuairat ta rasa ya xatayi tace
  "Calm down princess evrtin will b fine"
Ckn Muryar kuka tace

"Wani irin fine mom..kina jin abinda dad ya fada, nidai shikenan an rabani da masoyina😫😫"
ta fashe da wani irin kuka mai ban tausayi shuairat ta hau lallashi daga bisani tace bari taje gun mijinta.
      A can dakin mr president yana kwance yayi nisa ckn tunani ..har ga Allah shima yafi son ganin farin ckn umaima yafi son ta auri bash ko ba komai ya dade yana tare da basheer yasan halayensa mutumin kirkine ga rikon Amana ..amma wancan yana Lagos basu taba ganinsa bah basu San halayensa bah , kawai babu yanda ya iya adua shine mafita Allah ya xaba musu mafi alheri.shuairat CE ta shigo tare da sallama dakyar ya amsa domin shima yana ckn damuwa a hnkli ta karisa kusa dashi ta xauna yana kwance yana kallon ceiling daga ganinsa xaka San cewa yana ckn matsala tayi shiru ta rasa abun fadi , ta matso kusa dashi ta Dora kanta bisa kirjinsa tana jin karan bugun zuciyarsa.sun dau 5mins batare da wani yyi magana bah ..peck ta masa a kirji sannan ta daga kanta tana mai kallonsa ckn wata murya mai sace xuciya ta fara magana

"Swt hrt...duk da bansan meyake damunka bah..but ina son ka kwantar da hnklinka ka mika lamuranka ga ubangiji shi zai magance maka komai ckn sauki xai sama maka mafita, saboda haka bana son ganin kana daga hnklinka plss...
Yaji dadin kalamn nata ya juya idanunsa suna kallon kyakkyawar fuskarta yace

   "Hakane my lady...Allah shike maganin komai, u knw wat? Ina son ganin farin ckn umaima but baxan iya rejecting offer din daddy na bah"

"Yeah..nasan kana son ta auri yaya but baka da ikon yin hakan, sabida daddy mahifinka ne baxe ji dadi bah idan ka nuna rashin amincewarka"
  "Daz wat am thinking Aysha..Allah bana son auren nan da xaa hada"
Shuairat ta jawosa a jiki ya kankameta kamar xeyi kuka yace

 "Ita marainiya ce nafison ta auri Wanda xe riketa har abada ..nasan halayen basheer na xauna dashi na tsawon lokaci bamu taba samun sabani dashi bah...
  "Is ok swt hrt Allah xai kawo mana mafita don't worry ok! I promise xanyi magana da daddy insha Allah xamuyi nasara "
 "Ok...Allah yasa"
"Ameen..Nagode Ayshata I Lov u so much "
"Lov u more swt hrt"
Daga nan ta tura bakinta ckn nasa sun fada duniyar masoya...

Umaima tayi kuka mai Ban tausayi sultan tun yana bata hkri har ya gaji ya daina.dakinta ta shige ta kulle kofa ta cigaba da kukan ganin bashi da amfani yasa ta Ciro wayarta ta kira bash bugu 2 yayi picking tare da cewa
  "Baby Nah..I rily miss u"
Nan ta fashe masa da kuka ckn tsananin tashin hnkli yace
  "Baby wats wrong.. Tell me don Allah wani Abu aka miki ne?
Kukan takeyi dakyar tace
  "Ina son ganin ka"
Murmushi yyi yace

"Oh bby shagwaba..I tot is somtin serious fah, kawai kice kin fara missing dina "
Bata ce komai bah ta cigaba da kukan da take ya sake cewa
 "C'mon is ok mana! Kukan ya isa haka pls..ok toh gani nan xuwa ynxu shikenan koh"
Kai ta gyada tamkar yana  ganinta daga nan ta kashe wayar..

-40minz later- 
Bash ya kirata akan cewa yana garden din gidansu yana jiranta , hijabi kawai ta Dora akan doguwar rigar dake jikinta ckn sanyin jiki ta karasa babban garden din gidan nasu Wanda yake dauke da manyan bishiyoyi da flowers masu kyau ga kuma swimming pool a gefe...yana xaune akan wasu fararen kujerun da aka tanada a lambun yana ckn suit ash color da red shirt a cki ya mata kyau sosai ta kura masa ido tana kallonsa har ta karasa tare da sallama shima kallonta yake ya tashi ya tsaya ita kuwa ta sunkuyar da kai tana mai kallon kasa ckn tsananin mmki yace
"Subhannallhi..bby kukan ne yasa idanunki Suka kumbura haka? Y...??
Shiru tayi ya cigaba da kallonta ya sake cewa 

"Tlk to me pls" 
Wani sabon kuka ta fara yi nan take bash ya rude hnklinsa ya tashi ya fara tambayarta me yake sata kuka..ta sagaita kukan tare da cewa

"Gobe zasu zoh.."
"Su waye"
"Daddy da wannan mutumin "
  "Wani mutum?
"Wanda xai aureni ...xasu..
Bata karasa vah bash ya jawota ta fada jkinsa ya rungumeta sosai tamkar ya maidata cknsa hawayene Suka fara bin kumatunsa jikinsa har rawa yake ita ma kukan takeyi da karfi bash yace

"No...!!! Bazai yiwu bah...babu wanda xai rabani dake ..no!! It can't hpn I will Neva allow dat to hpn , u r my wife insha Allah"

😳😳😳🤔🤔🤔tohfah....Allah yasa...
Wayyo xaa raba laylah n majnoon😫😫😫😫😫😰😰

Fans kun amince da hakan????
[2/21, 2:42 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*88*
By *Reefat yahya*


Mr president ne yayi gyaran murya tare da cewa
"Ina son ganinku"
ckn tsananin jin kunya bash ya raba jikinsa da na umaima nan Suka bi bayan mr president.. Falon kasa Suka xaune Kansu na kallon kasa daga nan ya fara magana
 "Bash na zauna tare da kai na lokaci mai tsawo bana taba bata min rai ko cin amanata bah, kai mutum ne nagartacce naso ace ka auri umaima don nasan ko bayan raina xaka rike iyalina bare kuma ynxu an xama daya..but unfortunately daddy yaxo min da wata magana mai girma Wanda ni kaina banso ace hakan ta kasance bah, amma da na duba cewa shi mahaifina ne bani da xabin da ya wuce na amince da hukuncinsa domin ko ni kaina idan ya umarceni da yin wani abu baxan tsallake bah talkless of ya'r da na Haifa..so am very sorry kuyi hakuri Allah ya zaba muku mafi alhri..umaima tashi ki koma ckn gida"
Ya mike ya haura sama ba tare da kara fadan wani Abu bah...ckn raxana bash ya daga kansa sun kurawa juna ido , umaima wacce idanunta sun cika da kwalla tunda dad ya fara magana hawayen suna gangarowa daga nan ta tashi ta fice tana kuka.
    Bash ya share minti 30 a falon ya rasa me Ke masa dadi a nan duniya..baisan yyi nisa ckn son umaima se ynxu da xe rasata, dakyar ya tashi jiki ba karfi ya kama hnya tfy yake tamkar xai fadi jiri yake ji , hka ya cigaba da takawa a hnkli har ya kai inda yyi parking motarsa ya budeta a hnkli ya shiga cki ya hada kansa da siteri hawayene Ke fita a idanunsa ya dde ckn wannan yanayin daga karshe ya tada motar maigadi ya bude masa gate ya tafi, umaima wacce Ke kallonsa ta tagar dakinta nan ta fada gado ta cigaba da rusa kuka babu mai rarrashinta.a can bangaren mr president ma ya shiga dakinsa jiki a mace shuairat ce take kwantar masa da hnkli da kalamai masu sanyaya xuciya.

Bash bai tsaya ko ina bah sai gidan iyayensa  dakin mama ya shige ya fada saman gado yana kuka wiwi kamar mace😆😆 mama ta fito daga dakin mijin nata taxo daukar abu a dakinta turus tana ta tsaya don ganin mutum akan gado ckn tsananin mamaki tace
"Lafiyanka kuwa"
Babu kunya bash ya tashi xaune yace 
  "Mama xasu rabani da umaima"
Mamakin nata ya wuce na farko domin kuwa bata taba Sabin cewa basheer yana kaunar umaima don ko alamar hakan bata taba gani bah duk tsawon xaman da sukayi da ita umaimar 
"Wace umaima kake nufi?
  "Umaim de wacce kika sani "
"Dama kuna soyayya ne da ita"
Ya tura baki ckn shagwaba yace 
  "Haba mama let's b serious.. Wani xaa aura mata bani ba fah, pls do somtin Allah ina sonta"
Hhhhh sabon salo wai namiji da suna hajara..bash da ya kasance yaro mai tsananin kunya yau shi yake fadawa mamansa wai yana son wata! Ikon Allah..wani Abu se soyayya so Baka San kunya bah..hmm

Mama tayi jugum ta rasa ta ina xata fara ita dai har ynxu mamaki take kan wannan lamarin dakin mijinta ta wuce nan ta sanar dashi halin da ake cki don shima ya sakko daga fushin da yake kan xancen Karin auren..tare Suka dawo dakin yana nan xaune ya buga uban tagumi take tausayinsa ya mamaye xukatansu baba ya rike hannunsa ya fara magana 
   "Haba babana...kayi hkri ka daure shi namiji da juriya aka sanshi , kuka baxai warware matsala bah pls stop crying"
Yasa hannu yana share masa hawayen ya cigaba da cewa
  "Meyasa tun da dadewa baka sanar dani cewa kana sonta bah..but kaga ynxu is too late don...
   "Pls baba is not too late..pls do somtin bana son rasa ta ka taimakamin"
Tausayi sosai ya basu..baba yace
  " is ok toh..stop crying zanyi magana da shi daddy ok"
Kai ya gyada masa yana goge hawayen da Suka bata fuskarsa, haka Suka cigaba da lallaba shi dakyar yayi shiru ya daina kukan da yake, baba yace masa ya tashi ya koma gidansa firr yaki yace musu a nan xai huta xuwa yamma bayan kuwa tunda ya dawo ko gaisuwar arxiki bata hadashi da shukrah bah.

*washegari*masu aikin gidan mr president sun dafa abinci kala2* sun gyara ko ina a ckn gidan se qamshin tyraren wuta da airfreshners Ke tashi a can kitchen kuwa qamshin girkine..gidan yayi fes ya kara kyau shuairat tayi wanka ta shirya sultan da salman  ckn kaya masu kyau se xuba qamshi suke , umaima tayi wanka tayi kwalliya ba laifi tana bin shawarar da shuairat ta bata.mr president kuwa fararen kaya ya saka har da babban Riga shuairat tana xolayarsa wai surukai xasu xo gaisuwa su mr president an tsufa..murmushi kawai yayi har ynxu de baya ckn walwala wannan ma don shuairat tana yawan jansa da magana ne tana son ganinsa ckn farin cki.
   10am jirginsu ya sauka mr president tare da driver Suka je airport ckn jin dadin ganin Dan nasa ya karasa sukayi huggin din juna daga can gefe kuma wani dattijo ne tare da dansa ba sai ka tambaya bah mr president ya gane cewa surukin nasa ne, ckn girmamawa Suka gaisa daga nan Suka shige mota driver yaja Suka wuce gida.kyakkyawar sauka aka musu bayan sun ci abinci Suka koma falo daga nan shuairat ta shigo tare da salman da kuma sultan.. har kasa ta sunguna Suka gaisa da daddy da kuma mahaifin yaron shi kuma ya gaisheta ta amsa ckn sakin fuska ta tashi xata koma cki daddy yace 
"Ah..ina zaki kuma, munxo Neman auren ya'rki ai kema magana ta shafe ki don haka yi xamanki "
Babu gardama ta xauna a can nesa daddy ya karbi salman yana masa wasa sultan kuwa yana manne da mahaifinsa.shuairat tana Satan kallon yaron yana da kyau ba laifi Amma be kai basheer Nash girma da kyau duka... Daddy ya kira umaima a waya babu bata lokaci ta fito ckn natsuwa ta gaisa dasu gaba daya daga nan ta koma kusa da shuairat ta xauna daddy yace 
"Kuje Ku tattauna Ku daidaita kawananku..gashi Ann sunansa ismaeel "
Umaima tayi shiru bata ce komai bah, shuairat ta xunguri kafarta ba tare da wani ya lura da hakan bah nan umaima ta tashi tana wani nokewa wai a dole kunya take ji..falon baki Suka nufa tana gaba yana baya ta bude musu ta nemi kujera ta xauna suna mai fuskantar juna.
Yabi ta da ido tanada kyau sosai shikam ya amince da zabin iyayen nasa ita kuwa tana satar kallonsa ba laifi yana da Dan kyau Amma ko kadan baki burgeta bah hasalima haushinsa take ji don shine silar rabuwarta da Rabin rayuwarta wato basheer!
"Umaima.. Sunana ismaeel kamar yanda kika sani, nayi makaranta nayi degree ina aikine a *NPA* dake can Lagos"

"Aw..daz gud Allah ya taimaka"
ta kirkiro wani murmushn da bai kai har xuci bah..ba karamin daurewa take bah har take kulashi tana yin hakan ne don bin umarnin shuairat..
 "Dafatan xaki bani hadin kai mu xauna lfy don faranta ran iyayenmu"

"Ohh..kana nufin tilasta maka ake son yi..kenan baka son auren?
   "No..ba tilastani akayi bah, bin umarnin iyayena ne "
"Just tell me idan kana da wacce kake so kada ka boyemin"
"Ah.ah nidai na amince da auren ki domin kin kwantamin a rai..u have all d qualities dat I want"
Murmushn karfin hali take masa wani sa'in kuwa ta faki idonsa ta watsa masa harara karar bude Kofa da akayine ya jawao hankulansu umaima tana daga kanta sukayi ido 2 da bash 😳😳😳😳😳😳

Muje xuwa
[2/21, 2:42 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*89*
By *Reefat yahya*


*pals need ur pryrs pls...Allah ya biya min bukatata idan alheri ne ....Lov u all*


Fuskar basheer babu annuri ko kadan ya hada girar sama da ta kasa yana kallon umaima ismeel ya juya don ganin me umaima take kallo bash kam ko kallo bai isheshi bah gun umaima ya dosa ckn wani irin murya yace
"Ina son ganin ki ynxu"
Ya juya xai tafi tayi karfin halin cewa
   "Uncle bash ga ismaeel nan , ismaeel dis my uncle basheer"
Kafin bash yayi magana ismaeel ya tashi ckn girmamawa ya mika masa hannu babu yanda ya iya dole ya mika nasa nan Suka gaisa daga nan bash yayi gaba abinsa umaima ta tashi tamkar wata munafuka ta kirkiro murmushn dole tace
  "Amm..yi hkri pls 10 mins ina xuwa"
 "Olryt no p"
Daga nan ta fice yana nan tsaye a bakin kofa daga waje sai cika yake yana batsewa tana fitowa bata kula dashi bah kawai jin an fisgo hannunta yasa ta firgita ta juya Suka hada ido dashi idanun nan nasa sunyi ka kamar jini ze fita da karfi yake Jan hannunta bai tsaya da ita bah se ckn dakin baki ya wurgata saman gado ita kam tsoro ya cika xuciyarta don bata taba ganinsa ckn wannan yanayin bah nan kuwa hawaye ya fara fitowa a idanunta ta fara kuka Mara sauti ..wani wawan tsawa ya daka mata seda na fadi a kasa😜😜 ckn daga murya ya fara magana

"Shiru! Shiru nace.. Just keep quite my fren, ina can ina rashin lfy xan rasaki Ke kuma kina nan hnkli kwance kuna soyayya koh"
  "BB am...
Hannu ya daga bai bari ta karasa maganar bah ya cigaba da cewa 
"U have notin to say umaima.. Kin nuna min halinku na mata halin yaudara da cin amana n ...
  "Dakata ..kaima ka nuna min halinku na maza halin rashin hakuri da kuma mugun zargi, did u even kia to ask me ya akayi na xauna ina magana dashi...da xan so wani baxan xauna na bata shekaru da dama ina xaman jiranka bah ..dama Ku maza haka halinku yake, excuse me pls"
ta tashi xata bar dakin bash yayi Saurin rike mata hannu ta kwace sannan ta gyara tsayuwa fuskarta na kallon gefe jikinsa ya mutu da jin kalamnta shikam kishi ya rufe masa ido har ya fara ganin tmkar soyayya suke da ismaeel musamman idan ya tuna murmushin fuskarta a wannan lokacin da ya shiga ya samesu..Muryar umaima ce ta katse tunanin da yake 

"Idan baka da abun fadi ni xan tafi cos na bar bako shi kadai"
Yayo kanta kamar xai cinyeta yace
  "Baki da hnkli ne..wai meyake damunki ne har kina xancen wani bako a gaban idona"
Ta marairaice fuska

"Bb is risky fah..idan daddy yaje nemana bai sameni ba fah ? 
 " sai yazo nan ya sameki ..kinga daga nan xai San lallai baki son auren n am sure baxai miki auren dole bah" 
Haka dai bash da umaima Suka kasance daga karshe ma xama sukayi suna ta hirarsu irin ta masoya sun manta da wani ismaeel a can.
    Ismaeel yana xaune yana danne2* a wayarsa bayan yan mintuna ya duba agogan dake daure a hannunsa ta share 30 mins bayan kuma tace 10 mins anyways.. Ya gyara kwanciyarsa a kujera ya cigaba da danna wayarsa.a can falo kuwa suna hira ckn faraa , wayar baban ismaeel ne yayi ruri daga nan ya daga ya fita waje shuairat ta gyara xama tace 

"Daddy wata alfarma nake nema"
   "Fadi bukatarki ya'ta"
"Daddy xancen auren nan da xaayi ina ganin gara a hakura "
  "Sabida me?
"Umm..umaima bata son auren tana da wani Wanda take so"
Dariya yayi sannan ya juya yana kallon mr president Wanda tun da Suka fara maganar bai sanya bakinsa a cki bah..daddy yayi murmushi yace
"Wato mijin naki ne ya turaki koh"
Shuairat tayi saurin girgiza kai tace

"Bahaka bane daddy, kawai gani nayi umaima...
"Aysha!
  "Naam daddy"
[2/21, 2:42 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*90*
By *Reefat yahya*


Daddy ya cigaba da maganarsa
"Aysha kada ki biye ma mijinki , shi boko yasa a gaba idan na biye masa cewa xaiyi sai ta gama masters b4 ya aurar da ita"
  "Daddy bahaka bane..dama
Hannu ya daga mata nan tayi shiru da bakinta..yace
 "Zancen aure babu fashi , kuma na fasa jiran ta gama makarantar ma..bari Alhajin ya shigo"
Shuairat xata CE wani Abu baban ismaeel ya shigo tare da sallama daddy yace a kira ismaeel a waya su taho da umaima.
         Yana can xaune a falon har ynxu babu umaima babu labarinta wayarsa ta hau ruri mahaifinsa ne ya daga yace 
"Ku samesu a falo"
Daga nan ya kashe wayar ta tashi ya wuce falon da suke.ya karasa cki tare da sallama bayan ya xauna daddy yace
 "Ina umaima?
"Uhm..tun dazu ta tafi, wani uncle waye..uhmm 
Shuairat tayi carab tace 
   "Lahh..har ynxu basu dawo bah..dama ni nace suje ta xabi kalan furniture's da take so ita da uncle bash"
Idanunta Suka fada ckn na mr president ya harareta tayi Sauri ta tashi tsaye tace
   "Bari na kirasu daddy ina zuwa"
Daga nan ta fice bata jira jin amsar su bah.
Bangaren baki ta fara xuwa tana nemansu taji murya kasa2* a dayan dakin nan ta tura kofar fuska a murtuke ta samesu suna xaune suna hira ckn kwanciyar hankali harara ta watsa musu tare da cewa

 "Sai ku nuna ma duniya akanku aka fara soyayya"
Umaima ta tashi ta karasa kusa da ita
"Lfy mom sultan"kwafa tayi tare da cewa
   " zaku gane ai ..kixo ana Neman ki"
Jikinsu yyi sanyi bash yace
  "Sisy any progress?
"Wane irin progress..Abu yana Neman tabar barewa"
"Wat hpn"
   "Muje dai kuji da kunnenku"
Daga nan ta juya tayi tafiyar ta umaima da bash kuwa sunyi jugum kowannensu yana tunani daga bisani Suka wuce falon.
Bayan kowa ya xauna daddy ya fara magana

"Ismaeel ina fatan babu matsala"
"Ba komai Abba mun daidaita mun amince da juna"
Ckn Sauri umaima ta daga kanta sukayi ido 2 dashi ta sake sunkuyar da kan, daddy ya cigaba 
 "Masha Allah..dama haka muke son ji Allah ya muku albarka"
"Ameen" kowa ya amsa banda bash da umaima 
"Ynxu tunda sun fahimci juna ni na saka rana nan da wata 1 "
Tare Suka hada daga kai suna kallon juna babu Wanda ya lura dasu sai mr president ya kawar da fuskarsa tamkar baisan meke faruwa bah..hawayene Suka fara gangarowa a fuskar umaima ba shiri ta tashi tabar falon baban ismaeel yace 

"Meyake damunta Alhaji naga kamar kuka take yi"
Murmushi daddy yake w
Sannan yace
  "Babu komai nasan ta tuna da mahaifiyarta ce"
  "Ka tabbata..? Kodai bata son auren ne"
"Ko kadan ..nasan tunowa tayi da marigayiya zainab Allah yajikan ta yasa ta huta"
  "Ameen"
Haka Suka cigaba da hira bash ma barin falon yayi ya koma bangaren baki ya xauna ya buga uban tagumi yana Neman mafita.
    Jirgin yamma su daddy Suka bi Suka koma Lagos mr president ma hankalinsa yaki kwanciya sai ynxu ya fara jin tausayin Ya'r tasa shi da kansa yaje har daki ya sameta yana bata hakuri dakyar ta daina kukan da take.

****bayan kwana 2 bash ya kwanta zazzabi ya rufeshi ya tare a gidansu yaki komawa gidansa , kullum shukrah tana xuwa dubansa ko kallo bata ishe sa bah.gashi umaima ta kashe wayoyinta gaba daya hnklinsa a tashe yake mama tana masa nasiha akan ya rungumi kaddaara Amma Sam baya sauraronta ya xama kamar wani xautacce daga karshe ya tashi ya shirya ckn kananan kaya yayi kyau sosai duk da ramar d yayi ya fada sosai , mama ta shigo dakin rike da magungunasa ckn mmki ganin yana fesa turare da alama fita xaiyi tace

"Babana ina kuma xaka je ..kaida baka da lfy"
     "Na warke mama.."
"Toh ina xa ka?
"Zanje ganin umaima domin wayoyinta a kashe suke, xan duba ko lfy"
"Lfy kalau suke dazu munyi waya da Ya'r uwarka da akwai wani Abu ai kasan xata gaya min"
    "Naji...Amma nikam sai naje"
Daga nan ya xare makullin mota yyi ficewarsa.
      Umaima tana xaune a dai2* windon dakinta taga shigowar motar bash nan kuwa da gudu ta fito har tana tuntube masu aiki sai kallonta suke bata kulasu bah tayi hanyar last floor na kasa a bakin kofa Suka ci karo turus yaja ya tsaya...sun Dade sun kurawa juna ido daga bisani yayi karfin hali yace

"Meyasa zaki kashe min waya?
  "Uhmm...dama
dama me? Just tell me dat baki damu da halin da muke cki bah, kina nan ckn kwanciyar hnkli ni ko ina fama da jinya"
Wato Kalmar da tafi tsana kenan a ce duk son da take masa Amma se ya goranta akan shiyafi damuwa da ita....
Idanunsa sun kada sunyi ja yace 

"Umaima nasan kina sona Amma tsoronki ya hana ki fito fili ki nuna musu cewa baki son auren ni kike so ki aura y??
Kuka ta fara Mara sauti ya harde hannunsa a kirji ya tsaya yana kallonta daga bisani yace

"Mafita xaki kawo ba kuka bah pls"
ta cigaba da kukan 
"Haba mana bby u knw I hate doz tears ki bari pls bana son ganin ki ckn wannan hali"
Ckn Muryar kuka tace

   "Toh Bb ya xanyi..wane mafita xan kawo ? Ni gaba daya kwakwalwata ta toshe na rasa samun mafita kuma next week ance xaa kawo lefe"

"Wat???😳😳 next week? U know wat umaima kawai ki kira yaron ki CE masa baki sonsa kina da wani daban , daz d only solution"
   "Bb ar u sure it'll work?
"Am very sure baby Nah try it"
"Ok muje na dauki phn dina yana can daki"
"Ok lets go"
Daga nan ta shiga gaba yana biye da ita a baya Suka haura xuwa sama don daukar wayarta.

Shin xata kira ismaeel kuwa??
Zai amince da bukatar tata??
Hmmm...muje xuwa
Lov u all😘😘
[2/21, 2:42 PM] Reefat: 💞 NI DA SHUGABAN KASA💞
*91*
By *Reefat yahya*


A hanyarsu ta xuwa daukar waya Suka ci karo da shuairat tabi su da wani irin kallo sannan tace 
" dad naki yana son ganinki ynxu"
Gaisawa sukayi da yayan nata sannan tayi wucewarta sum sum umaima ta tafi falon baban nata yana xaune da jarida a hannusa ta shigo tare da sallama ta nemi waje ta xauna
  "Gani nan dad"
"Ki shirya gobe zaku wuce Dubai shopping Ke da Aysha"
A hnkli ta daga kanta tana kallonsa sannan tace
    "Dad...
"Bana bukatar jin komai daga gareki tashi ki tafi Allah ya Baku xaman lfy"
Kuka ne ya kubce mata da gudu tabar falon a hanya ta hadu da bash yana tsaye ya jingina da bango da alama ita yake jira..
"Lfy my bby "
bata iya furta masa komai bah ta wuce bangarensu a kujera ta fada tana kuka mai ban tausayi  bash ya shigo ckn tashin hnkli ya xauna kusa da ita ya fara magana ckn kwantar da murya 
"Bby kullum ina gaya miki bana son wannan kukan naki amma baki ji pls stop it"
Haka ya cigaba da bata baki dakyar ta sagaita kukan ta sanar masa abunda yake faruwa shiru basheer yayi yana jin wani radadi a ckn xuciyarsa ya rasa ma wani mataki xe dauka daga nan ya tashi ya fita ba tare da ya furta ko kalma daya bah.
         Umaima ta cigaba da kukan da take  bash kuwa bai tsaya ko ina bah sai gun mahaifinsa wani sabon hauka ya tada musu mama kam se kuka take tana tausayawa dan nata , suna lallabashi tamkar kara tunxura shi suke baba ya rasa ya zayyi kawai ya fice ya koma dakinsa ya xauna. Mama ce ta cigaba da rarrashinsa dakyar ya tashi ya ci abinci.


***washe garin...mr president ya raka shuairat da umaima airport jirginsu ya daga xuwa Dubai ya rage dashi da sultan kadai a gida. Umaima se kuka take shuairat tana rarrashinta a haka Suka kasance a ckn jirgin ma babu abunda take sai kuka. 
     Bash yana xaune a ofishinsa yayi jugum..tunanin duniya ya addabesa ynxu shikenan an rabashi da umaima ?? Yau saura 3weeks auren ta da wani bashi bah ..kwankwasa kofa akayi sectry dinsa ne ya shigo ya shaida masa yayi bakuwa ba tare da wani dogon tunani bah yace a shigo da ita.yana xaune ta shigo qamshin turarenta ya gauraye ofishin gaba daya ba shiri basheer ya daga kansa fara ce Sol daga ganin hasken nata na mai ne tana tauna cingam ji kake kas! Kas!! Wata shaidaniyar doguwar Riga ce a jikinta Wanda ya matseta gam Rabin kirjinta duka a bayyane fatee kenan...hannu ta daga masa ckn salon Jan hankali tare da cewa

"Hi basheer am fateemah "
    "Aw daz gud..fateema me Ke tafe dake ?
"Well..actually ba wani Abu bah illa so da kauna"
Ckn Sauri ya daga idonsa ya jefa mata wani mugun kallo bata ji ko darr ba ta cigaba da cewa 

"Na Dade ina kaunar ka baaheer, a rayuwata ban taba son wani namiji bah sai kai..pls ka amince muyi aure"
Wani murmushi yayi sannan yace

"Wai ba kece Ya'r uwar shukrah da ta kawo mata ziyara kwanakin baya bah"
   "Yeah...u r right anyi haka Ashe dai baka manta dani bah"
Ya juya idanunsa tamkar mai shirin yin bacci ya nuna kofa tare da cewa
"U can leave pls..
"C'mon basheer kasan nafi matar ka da komai kuma ynxu ita bata da wani amfani tunda ba haihuwa xatayi bah"
Ya bude ido sosai yana mamakin kalamanta ya akayi tasan shukrah baxata kara haihuwa bah??...wato shi ya rike maganar as sirri bai sanarwa kowa bah amma ita tana can tana yada kanta tana tona masa asiri..tirr da halaye irin nata.
   "Kayi shiru my love, ko kana bukatan lokacin tunani?
Ya watsa mata wani mugun kallo tare da cewa 

"Tunani? Koda a ce matan duniya sun kare kece autar mata , wllhi na hakura gara na mutu banyi aure bah akan na aure ki fateema"
Daga nan ya tashi ya bude kofa yace 
"Out..now"
Ta gyara xama tana wani juya idanu taji saukan mari tass! Sai da taga taurari..ya nuna ta da dan yatsa yace

"Ki lura da inda zakiyi iskancinki ni ba sa'ar yin ki bane  , ki kula..kada na kara ganinki fita ki ban waje "
Ya karasa maganar ckn tsawa nan take ta fisge Jakarta tayi waje hawaye na bin kuncinta Marin ya shiga sosai😆😆😆 tunda take a rayuwar ta babu Wanda ya taba cin xarafinta irin na yau, taxi  ta tare ta gaya masa inda xata je ta biya kudin Suka dau hanya.
      Shukrah tana xaune tayi nisa ckn tunani hawayene Ke sauka daga idanunta taji kamar motsi nan ta tashi Suka yi ido 4 da fatee ta rike kugu tana murmusawa ckn xafin nama shukrah ta cafke wuyar rigar ta

"Azzaluma me kike nema a gidana"
Wani irin dariya fatee take sannan tace
    "Haba sahibar ki ce fah"
"Zan kasheki fatee kowa ya huta"
   "Allah sarki yarinya har kisa kika koya..abun yayi sosai idan kin kasheni se ki karasa rayuwarki a gidan kurkuku umaima kuwa ta aure mijinki suyi rayuwarsu ckn so da kauna"
Shukrah ta sassauta rikon tana kallonta murmushi fatee tayi a karo na 2 daga bisani ta cigaba da cewa

"Oh...Ashe dai kinyi tunani mai kyau, ina son kisan cewa ba wai naxo Neman gafara kan abubuwan da na saki aikatawa bah ah 'ah..nazo ne don sanar dake cewa burina na son auren mijinki bai cika bah, kuma mijinki yana yan yana shirin kara aure nan da sati 3 xai auri umaima Ya'r gidan shugabankasa na da.ynxu haka suna kasar waje tare da aminiyarki suna siyayyan aure kuma.....

Shukrah bata bari ta karasa maganar ba shaketa sosai tamkar xata kai fatee lahira ckn daga murya tace

"Karya kike bakar munafuka me bakar aniya..
  "Wllhi da gaske nake , idan baki yarda bah ki kira aminiyar taki ki tambayeta suna ina xata gaya miki"
Shukrah ta xame ta xauna a kasa ta tallabo kanta dake faman tsarawa a hnkli ta CE
"Fatee da gaske baban waleed zai auri umaima ? Kuma har ansa rana shine baxai sanar dani bah"
"Ehh..dama ina da masu bani labarin duk wani movement din mijinki su Suka gaya min abunda yake shirin faruwa"
Shukrah ta fashe da kuka mai ban tausayi fatee kam ta warce Jakarta tace

"Toh shukrah sahiba! A rungumi kaddara a kiyaye gaba kinga tafiyata sai wata rana tunda ma Allah yaso ki mijin naki yaki amincewa da aurena da kukan zaifi na ynxu don haka ki godewa Allah umaima xaa kawo miki ba niba"
Daga na tasa kai tayi ficewarta tana faman gyara gaban rigarta tana kunkuni tana cewa
"Boka kuwa xeci uwarsa ba ni xai yiwa karya bah...hmm gashi bukata bata biya bah wllhi xai gwammace kida da kara2"
🙄🙄🙄

Muje xuwa
[2/21, 2:42 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*92*
By *Reefat yahya*

*sorry fans bana yawan posting dese days pls bear wit me kunsan duniya up n down 😁😁 just busy hre n dre ne kawai..Lov u all, godiya gareku masoyana masu turamin mssgs ta private da masu kirana a waya tnx a lot Lov u all*


Fatee tana son raba tsakanin shuairat da shukrah shiyasa ta sanar da ita cewa basheer zai auri umaima..tana barin gidan ta xarce filin jirgin kasa don komawa kd.
       Shukrah kuwa babu abinda take sai aikin kuka tana jin xuciyarta tamkar xata fito fili wani haushin shuairat take ji tasan tabbas aikinta ne hada auren bash da umaima lallai sai ta dauki mataki akansu duka xata nuna musu kuskuren da Suka tafka..umaima kuwa xatayi regret.

A can UAE wato birnin Dubai shuairat ce take shiga da fita xuwa kasuwanni daban2* umaima dai se kallo don bata xabi ko cokali bah haka nan shuairat ta fita sabgarta kullum a kasuwa suke yini idan sun koma masaukinsu kuma shuairat xata kira masu gyaran jiki a gyarata duk da bata so.
  Haka Suka kasance har tsawon sati 2 sannan sukayi haramar dawowa 9ja.
Bayan dawowarsu da 2days aka kawo lefe akwati set3 da tulin kaya masu kyau da sada, daga nan aka soma shirye2*n biki yau saura 1 week ciff.duk yadda bash yaso ganin umaima abun ya faskara saboda shuairat ta gindaya mata sharuda sosai bata xuwan ko ina kullum tana ckn dakin baccinta gashi an kwace wayarta bata aiki se kuka, ga yan uwa sun fara xuwa  shuairat se shiga da fita take Sam bata da lokacin xama ita ta kira tela yaxo har gida ya karbi dinkunan da xaa yi, mr president ya bude bakin aljihu ya xuba kudi sosai duk abunda ake bukata sun rigada sun siya ..
    Shuairat ce kwance a dakinta salman yana gefe yaron ya girma yayi wayo sosai gashi da girman jiki tamkar ya'yan turawa ga fara'a ga kyau tubarakallah..mr president ya shigo yana waya bayan ya gama ya juya gun matarsa suna fuskantar juna 
" sorry my Lady gskiya kina kokari Allah ya miki albarka"
"Ameen my man"
tana murmushi ta koma kusa dashi ta xauna tare da cewa 
  "Nasan ka gaji kwanta na maka tausa"
Babu gardama ya mike akan gado kwanciya yayi rub da cki nan ta fara masa tausa har wani lumshe ido yake tamkar mai shirin bacci shuairat tace

  "Dad umaima"
"Uhmm..
"Pls gida nake son xuwa "
   "Yaushe?
"Ko xuwa anjima "
"Ba damuwa ki shirya driver ya kai ki"
"Tnx swt hrt"
Ta manna masa peck a kumatu murmushi yake haka ta cigaba da masa tausa har bacci yayi awon gaba dashi.
     Ta gama shirinta tsab ta shirya salman sun yi kyau sosai ta sanar da masu aiki kan cewa su kula da umaima xata je gidansu baxata Dade bah, daga nan ta wuce gun mota driver ya ja Suka dau hanyar xuwan gidan su.
Falon babanta ta fara xuwa yana xaune da carbi a hannu dayake baa dde da yin sallar axahar bah..yana ganinta fuskarsa ya fadada da murmushi yace 
  "Ya'r baba..Barka da xuwa"
   "Yawwa..
Waje ta nema kusa dashi ta xauna yasa hannu ya karbi salman yana cewa 
   "Waii...haka kike fama da wannan lukutin Alhajin yana wahalar min dake"
Dariya kawai take musu gskiya salman akwai nauyi kamar my boy *haneef*😊😊.
Mama ta shigo tare da sallama ta tabe baki da ganin shuairat tace

"Oh..ni Fatima wato kedai kin nuna kinfi son mahaifin naki a kaina ..ah yayi kyau"
  "Fateema wai kishi kike dani"
Baba ya fada yana dariya shuairat ta tashi ta fada jikin mama 
  "Mamana I miss u"
"Ba wani nan kin nuna kinfi damuwa akan mahaifinki"
"A'a mama kema kinsan ina sonku gaba daya"
Suna dariya mama ta dauki salman tana cewa
  "Maigida nasan kai kam kafi sona koh"
Salman se wage baki yake kamar yana jin abunda take cewa baba ya karbe maganar yana cewa 
"Wannan Dan lukutin maigidan naki yana ramar min da ya' "

"Alhaji kodai kishine"
"Haba..kishi da wannan maigidan ba chefene"
Suna ta raha daga karshe Suka gaisa mama ta kawo mata ruwa tasha Suka baje suna hira shuairat tace

"Ina majnoon neh kwana 2 bana ganinsa "
"Waye kuma majnoon"
Mama ta tambaya tana mai kallon shuairat
  "Hhhhh.. Yaya bash mana"
Duka mama ta kai mata nan ta goce tana dariya tace
  "Ehh..mana ai sunan ya dace dashi majnoon baban soyayya ko romeo ne"
"Bayan kun hanashi Ya'r taku me kuma xaki fada"
"Eyya mama rabone babu"
     "Kiji dashi...Allah xai bashi wata"
Baba de se dariya yake musu haka shuairat ta yini har bayan sallan laasar ta tashi da cewa xataje gun shukrah kafin ta koma gida daga nan sukayi sallama tana rokon mama akan cewa don Allah taxo bikin , har mota Suka rabu nan driver ya ja Suka wuce gidan bash.

Shukrah tana xaune ta buga uban tagumi tunani fal a ckn xuciyar ta kamar a mafarki taji sallamar shuairat bata amsa bah shuairat tasa kai ta shigo falon tana faman sauke salman tare da cewa
"Kai mata kina nan shine baki amsa sallama ta bah, tunanin me kike haka"
Wata muguwar harara shukrah ta jefa mata tare da Jan dogon tsaki tace
 "Allah wadaran naka ya lalace..mutum yayi asara tunda munafurci da hassada yasa a gaba"
Ckn rashin fahimta shuairat tace 
  "Ke kuwa waya tabo ki da yamma haka"
Dama jira take nan shukrah ta tashi tsaye tace

"Ke shuairat kada ki mayardani shashasha..kina jina, bayan kin gama hada munafurcin ki xaki xo kina raina min wayo..
  "Haba shukrah meyayi xafi haka?
"Ehh..lallai kin nunamin halin yan duniya.ni kike tambaya? Hmm..shuairat kenan tsabar rashin kunya da bushewar ido har xaki iya fuskantata ki...
"Dakata madam! Bana son kwana2* ki fito fili ki gayamin meke faruwa"
     "Danakari! Lallai yarinya kina da mugun rainin hnkli..bayan kin gama munafurcinki xaki dawo ki fake ki nuna Ke baki San komai bah??


Shuairat tayi jugum..wai meke faruwa ne?
Me shukrah take nufi??
Ni Reefat nace🤔🤔   kodai xancen auren ya tabbata ne??
Toh...muje xuwa dai

*Dr Reefat*😘😘😘
[2/21, 2:42 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*93*
By *Reefat yahya*

Shuairat taja wani gauron numfashi tace
"Look bestie..let's sit down n..
  "Bestie! ..hmmm tsohon suna "
Shukrah ta tare numfashnta sannan ta cigaba da cewa
"Shuairat a da can baya idan wani ya gayamin cewa xaki iya aikata abunda kika min a ynxu  wllhi baxan taba yarda bah amma ba abun mmki bane dama haka amintaka ta gada...cin amana da yaudara da munafurci"
  "Haba shukrah wat r u talking about.. Nifa kin sani ckn duhu"
"Kinga malama ki tattara ki barmin gida Nah ..ko sai nan ma xaki nunamin gidan Dan uwanki ne? 

"Pls shukrah let's talk abit "
"I don't want to...just get out now"
Shukrah ta fada tana nuna hanyar fita nan shuairat ta sabi salman tasa shi a kafada ta kama hanyar fita idanunta sun cika da kwalla tana mamakin sauyin halin shukrah kuma ta rasa gane dalilin.driver yana ganinta yayi saurin bude mata gidan baya ta xauna ya tada mota Suka koma gida.
    Tana isowa ta share hawayen da ya bata mata fuska sannan ta karasa ckn gida baki ne a cike da falon suna ganinta Suka fara mata sannu da dawowa itama tana musu barka da xuwa se rawar jiki sukeyi a kanta wata ta karbe salman tana cewa 
"Fine boy ya kke"
Dangin mahaifiyar umaima ne da kuwa wasu daga ckn yan uwan mr president sauran kuma washe garin xasu taho , shuairat ta shiga musu hidima se yabonta ake bayan ta tanada musu komai duk cewa masu aiki sun Riga sun kawo musu abinci har magrib ta samu ta koma dakinta tayi sallah bayan ta idar ta samu ta watsa ruwa har ynxu salman yana gun yan uwansa don haka ta shirya a nitse ta saka wata simple doguwar riga Mara nauyi ta fesa jikinta da turare nan ta kwanta a gado kalaman shukrah ne Ke yawo a kwa2lwarta ta rasa gane inda maganganun Suka dosa, mr president ya shigo har ya karasa kusa da ita ba tare da ta sani bah hannu taji ana shafa fuskarta yasa tayi saurin dagowa ya jawota a jiknsa ya rungumeta tamkar jira  take nan ta fashe masa da kuka dakyar ya rarrasheta ta daina kukan wani light kiss ya mata na 2 mins sannan ya kwantar da kanta a saman kirjinsa tayi luff ta kwanta sosai ckn Muryar rada yace
"Tell me...
Babu gardama ta xayyana masa komai bata hakuri yake bata yana nuna mata cewa ta kwantar da hankalinta wataran xasu shirya daga nan ya fara mata wasu abubuwan da yasa ta manta da damuwar da take cki.

Washegari ...daddy da momsi Suka zo ga gida de a cike makil babu masaka tsinke a ckn dangin nata ne shuairat ta xabi kawaye 4 ta basu anko din ta shirya dinner hadadde bayan an daura aurene xaa yi , umaima kam tace ba ruwanta a cki ko walimah baxata yi bah..dakin umaima ta shiga ta xauna a gefen gado umaima ta tashi xaune tace
"Don Allah mom sultan ki taimaka ki barni naga uncle bash..wllhi ba dadewa zanyi bah kawai sallama zamuyi"
"Bbu inda zaki..so kike ki jawo min magana gun daddy koh, toh wllhi babu ruwana a cki"
    " haba mana...eyya mom plsss"
ta marairaice shuairat tace 
"xan kirashi yaxo nan gidan ya sameki"
" ehh..na amince don Allah ki taimaka"
Ta bata tausayi ba kadan bah..nan ta cire wayarta yayi ringing har ya katse baa daga bah, ta sake kira har sau3 daga bisani ya daga a wahalce yake magana
"Salamu alaikum"
Gaban shuairat ya fadi badai rashin umaima ne ya kwantar dashi haka bah ya salam! Muryarsa ne ya katse tunanin da take
"Baki jina ne"
"Yaya ina ji meyake damunka naji voice naka somhw"
tsaki yaja yace 
  "Wani Dan xaxxabine yake damuna amma naji sauki"
"Ahm..dama umaima ce take son ganin ka "
"Da gaske? tana ina?
"Yaya..tek it easy pls, kaxo gida ynxu amma kada ka bari mr president yasan da xuwan naka ok"
   "Ok gani nan xuwa"
Nan ya kashe wayar tausayinsu ne ya kama shuairat jikinta ya mutu ta juya ga mmkinta hawayene a idon umaima tace

"Mom sultan kin gani koh...wllhi yana sona nasan yana ckn tashin hnkli ynxu"
"Umaima kiyi hakuri babu ynda muka iya umarnin iyaye ne Allah yasa hakan shine mafi alheri "
     "No...ba alheri bane ni nasan aurena da uncle bash shine mafi alkairi "
Nan ta fashe da kuka shuairat tana bata hakuri dakyar ta sagaita kukan daga nan ta tashi tayi wanka ta xauna xaman jiran masoyin nata.
  Har yamma babu labarin bash ga layinsa bayya shiga umaima ta birkita shuairat gaba daya ta xama tamkar wata mahaukaciya tun suna boyewa har jamaa Suka gane sun fara tambayar shuairat ko lfy shuairat de ce musu take kan umaima ta tuna da mahifiyarta shiyake sanyata yawan kuka.
   Da dare suna xaune sunyi jugum shuairat ma ta shiga damuwa don rashin samun layin Dan uwan nata gashi tana kiran layin iyayen nata basa dagawa babu halin ta fita kuma don mr president baya gida.haka ta hakura momsi ta shigo dakin suna Dan taba hira sama2* dakyar Suka lallaba umaima ta yarda taci abinci, kadan ta ci ta kwanta.
11pm mr president ya shigo a wannan lokacin shuairat ta gama shirin bacci ta kwanta amma baccin yaki xuwa , ya shigo tare da sallama ta tarbesa tare da kawo masa abinci bayan ya gama wanka ya fito ya ci abincin sarai ya lura da halin da take cki amma ya share nan ya hau gado ya kwanta ckn sanyin murya ta kirasa
"Swt hrt!
"My lady yaya?
"Uhm..dama numban yaya bash ne baya shiga"
    "Meya faru kuma meyasa kike nemansa"
"Uhm..dama ..daman "
Sai kuma tayi shiru ta rasa karyar da xata shirya ya kura mata ido yace 
  "Ina sauraronki"
"Uhm..numban mama ne idan na kira bata dagawa shine nake son ji ko lfy"
Murmushi yayi ya jawota yace

"Don't worry lfy suke babu abunda ya faru ok"
ta tura baki tare da marairaicewa
 "How sure are u ko suna lfy"

"C'mon trust me..lfy lau don dazu na raka daddy yaje gun baba "
"Lfy dai koh?
"Uhm..kawai gaisuwa ce cos idan ya shiga hidimar bki baxai samu damar xuwa bah, kuma yayi inviting dinsa xuwa daurin aure "

"Ok yayi kyau"
Daga nan shiru sukayi kowa da tunanin da yake ya rungumeta sosai sannan ya kashe bedside lamp sukayi baccinsu.
*asuba ta gari masoya👌🏼*

~Gobene fah..👯👯👯rengem rengemgem gobe ne daurin auren umaima fah...rengem..rengem..gem..💃🏼💃🏼💃🏼dafatan xaku xo fah...rengem👯👯👯👯~ *dis1 naa gobe.. Oyakaka..original gobe..* 😁😁😁lolx don't mind me
U r all invited 2d wedding hop xaku xo fans..tohm duk mai xuwa ya daga hannu👆🏼👆🏼

😜😜😜sai naji daga gareku..Lov u all *Reefat CE*
[2/21, 2:42 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*94*
By *Reefat yahya*


*yesss oooh...2day na 2day...auren umaima n basheer😜😜*

12pm bash yana kwance a falon mahaifinsa baba ya fito ckn shirin jumaa yasha manyan kaya farare sol dasu se xuba uban qamshi yake..ya harari dan nasa tare da cewa
"Kwanciyan me kake min a falo baxaka je masallaci bane"
Ya marairaice kamar zaiyi kuka yace
   "Allah baba bani da lfy I dnt tink xan iya xuwa "
  "Bana son shashanci ka tashi maza ka shirya ynxun nan mu tafi don a can xaa daura auren umaima nasan take-taken naka salon kar kaje daurin auren ne kuma dole se kaje wllhi"
"Baba pls...
     "Bana son maganar banxa ka tashi maxa ina nan ina jiranka"
Sum sum ya tashi ya koma dakin da yake zama ckn kankanin lokaci yayi wanka ya fito blue shadda yasa kayan sun masa kyau ba kadan bah ga qamshin turare kala2* ya ajiye hula sannan ya fito baba ya bisa da harara daga nan Suka wuce central mosque a can xaayi daurin auren.
    Umaima tana kwance ta duba agogon dake makale a bangon dakin Karfe 1:10 shikenan saura kiris ta xama matar ismaeel , shuairat ce ta shigo tare da sallama abinci ta kawo mata farfesun kaxa ne yasha hadi sosai ta tura plate din agaban umaima ckn tamke fuska tace
  
"Maxa ki cinye ki bani plate ynxu"
"Mom sultan wai fushi kke dani"
   "Mtsww..toh me! Ke kin damu kanki akan mutumin da bai damu dake bah, da a CE yana sonki ai da yaxo tuntuni amma saboda bai damu ba kinga ya nemeki ne? Kina nan kina Neman halaka kanki "

"Haba kinfi kowa sanin irin son da uncle bash yake min..ni nasan ba lfy bah...
   "Dallah malama..ki ci abinci ki tashi ki shirya"
Tana kumbure2* haka tasha farfesun don bata ga alamar wasa a fuskar shuairat.
Bayan ta gama ta shiga bayi ta Dade kwance ckn jacuzzi tana lumshe idanunta hoton fuskan bash kawai take gani nan hawaye ya cika mata ido ta dauki tsawon minti 40 tana kwance , shuairat ce ta kira sunanta daga waje nan ta fara wanka daga bisani ta fito.
       3:10pm an shiryata tayi kyau sosai ckn wasu dankareren leshi mai kyawun gaske umaima tayi kyau kamar a saceta a gudu a harabar gidan aka fito da ita masu daukar hotuna ne birjik ga nan yan uwa da abokan arxiki ma ga yan gayyan sodi irinsu Reefat😆😆 ga masu watsa labarai daga gidan telebijin da yan jarida , gidan de a cike makil da jamaa umaima de daurewa take tana kokarin boye halin da take cki shuairat ansha kyau ta xama tauraruwa sha kallo ga salman da sultan ma haka, abun de gwanin burgewa.
Momsi ta fito Suka fara daukar hotuna sunyi family pix kala2* dakyar na samu na dau kala 3nida shuairat da amarya se kuma Wanda mukayi tare da salman da sultan😜😜😜.
       Horn muka ji a bakin gate take maigadi ya wangale kofar motoci ne birjik har na kasa tantance ko guda nawa ne, securities na fara gani ckn bakaken suits nace ah abun na manya ne☹☹..Nigerian president ne a gefen mr president (dad) ga Chinese President daga barin hagu se kuma new faces da bansan ko su wanene bah daga gani dai kasan shuwagabannin kasacen duniya ne don daga irin shigar kayansu da masu tsaron dake xagaye dasu xaka gane hakan.ga can daddy a baya tare da abokanansa manyan mutane se kuma ismaeel na hNgo fuskarsa dauke da murmushi sai kuma bash daga can gefe yana ta gaisawa da mutane yNa dariya fuskarsa kamar gonar audugA..haaa..am confused🙄🙄 ya naga bash haka?? ..uhmmm.
     Dakyar mr president tare da tawagarsa Suka samu hanyar shiga ckn gidan saboda jamaa sunyi yawa babu masaka tsinke. A can babban falon gidan Suka xauna daddy kuma yana dayan falon tare da tawagarsa , abinci da na sha aka ajiye musu suna ci suna taba hira ana dariya daga bisani yan jarida Suka fara daukan hotuna don yadawa a gidan labarai, shuairat da umaima sun shigo falon anyi hotunan tare dasu ana tayasu murna.har 5pm ana abu guda dakyar shuairat ta jawo umaima Suka koma bangarensu a daki Suka xauna shuairat tace
  "Ki shirya anjima xaa ne dinner"
Idanunta sun cika da kwalla tace
  "Allah na gaji baxan iya xuwa bah"
"Shikenan bari naje na sanar da dad "
Ckn Sauri tace

"Ah'ah pls kiyi hkri xan shirya ynxu"
Murmushi shuairat tayi sannan tace 
"Kije falona babu kowa a can angon yana son ganin ki"
   "Eyya mom..Allah na gaji sosai"
"Ok bari na kirashi yaxo ya sameki "
Bata jira amsa bah tayi waje dama su 2 ne kawai a ckn dakin sauran jama'an suna can kasa suna faman daukan hotuna. Umaima ta hada kanta da guiwa ta fara rusa kuka..shikenan yau ta xama matar wani !
Kofar dakin aka bude ta cigaba da kukan da take ba tare da ta daga kai bah..a hnkli ya xauna kusa da ita ya jawota a jikinsa , qamshin turaren da har abada baxata manta dashi bah ckn Sauri ta daga ido tare da cewa
"Uncle bash😳😳
Murmushi ya sakar mata mai sanyaya xuciya , nan kuwa ta turesa gefe tana hawaye tace

"Kasan de ynxu na xama matar wani"
"Har abada Ke matata CE mutuwa CE xata rabamu"
  Wani murmushi mai ciwo tayi tana girgixa kai tare da cewa
"Kana magana tmkar baka San yau an daura aurena bah"
"Yes ofcoz an daura auren ki but da masoyinki aka daura auren"
Ya karasa magana tare da lakuce masa hanci ckn rashin fahimta tace

"Bangane bah"
"Yes umaima Allah ya cika mana burin mu an daura mana aure n...
Bai samu damar karasa maganar ba ta fada jikinsa ta rungumesa gam hawaye wani na bin wani..murmushi bash yayi tare da daura hannayensa shima ya rungumeta 😍😍😍
Sun kasance ckn wannan hali har na lokaci mai tsaho sannan umaima ta xame jikinta sai kuma kunya ya kamata tasa tafin hannu ta rufe fuska wai ita kunya🙄🙄🙄 daga baya kenan wai anyi sadaka da karuwa...😬😬😜.

Toh ya akayi abun ya juya aka daura da basheer???
🤔🤔🤔🤔🤔🤔🤔
Fans ..just ignore d typing errors cos bana editin
[2/21, 2:42 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*95*
By *Reefat yahya*



Fuskokin nasu dauke da Murmushi suna kallon juna ..a hnkli bash ya jawota ya rike mata hannu tare da kura mata ido yace
"Baby no more kunya pls..kin xama matata u r mine n am urs murna xakiyi ki godewa Allah da ya cika mana burin mu"
ta daga kai tace
  " but Bb ya akayi hakan ta faru har daddy ya amince aka daura mana aure"
"Ni zan baki amsa"
Shuairat ce ta shigo fuskarta dauke da murmushi ta cigaba da cewa
   "Yau da safe na samu labarin but naki na gaya miki cos I want 2 surprise u"
Nan kuwa umaima ta ruga a guje ta rungumi shuairat tana dariya tace
 "Tnk u so much mom..nasan da taimakon ki akayi wannan auren Nagode sosai Allah ne kadai zai biyaki tnx a lot"
  "Mention not dia "
"Toh mom ki ban labarin ya akayi ..am waiting"
"Umaima hoo..irin xumudi haka"
Kunyace ya rufe ta nan ta koma gefen gado ta xauna bash kam se kallonta yake kamar wani tsohon maye ta birkita masa kwakwalwa ta kara kyau ba kadan bah..shuairat CE ta fara magana
"Jiya daddy yaje gun baba tare da dad naki sun dade suna hira har daddy xai dawo sai yake tambayan ina yaya don tunda yaxo be ganshi bah, aka ce masa yaya bashi da lfy yana bacci daga nan Suka dawo gida.yau da safe naje gun daddy bayan mun gaisa yake tmbyta ya me jiki ckn rashin fahimta nace masa waye ba lfy? Ckn mmki shima yace baki san yynki bashi da lfy bah? Nan hawaye ya cika idanu na hnklin daddy ya tashi ya fara bani hkri yace da yasan baa gayamin da baxai tmbyeni ba gashi ya dga min hnkli, nace masa ba batun rashin lfyn ne Ke sani kuka bah illa tausayin halin da yaya xai shiga nan gaba..daga nan na xayyana masa komai.fada yake ta inda yake shiga ba ta nan yake fita bah wai akan wane dalili xaa boye masa wannan lamarin, nace tun farko naso sanar da kai but baka saurareni bah daga nan ya kira baba nan ma fada yake akan cewa meyasa baba be sanar dashi bah.a takaice de haka ya kira ismaeel da babansa ya basu hakuri ya nuna musu yarinya bata so , haka Suka hakura har xuwa lokaci daurin auren ko shi yaya bai San cewa dashi xaa daura auren bah.toh kinji de yanda abun ya faru"

Wani dogon numfashi umaima ta sauke tare da cewa
"Ikon Allah kenan..tabbas wani baya auren matan wani, matar mutum kabarinsa hakika rabo in ya rantse babu mai hanawa don nikam tuni na fidda ran sake haduwa da Bb..Allah Nagode maka da ka cika min burina , mom Nagode miki da kokarin da kikayi kuma daddy ma dole na gode masa"
  "Kai umaima ko Ya'r kunyan nan babu"
ta rufe fuska tana dariya shuairat ta tashi tsaye tare da cewa
"Ki shirya ynxu masu makeup suna nan tafe kinsan akwai dinner nima na tafi idan nayi sallah xan fara shiri na"
Basheer yayi murmushi yace

"Wait..sisy kina nufin kema xaki he?bayan kece mmn amarya"
Harara ta watsa masa tace
     "Toh bari kaji har mijina ma sai yaje don abun tuwo na maina ne ...kuma a ckn gidan nan xaayi"
ta juya gun umaima tace
    "Ke kuma ki xauna ki biye masa har lokaci ya kure Ku gaku nan romeo n Juliet , an de daura auren xamu gani ko xaku hadiye junanku"
Dariya sosai suke shuairat ta yi hanyar kofa bash yayi saurin cewa 
   "Kixo gidan mu ki ga yanda xaa hadiye juna ...ki xo na koya miki Lov yarinya"
"Ahaaff...wllhi karyan mutum yace xai koya min soyayya , duk kalan Lov da xakuyi de wasu sun Riga sun gama ..toh wai ma wane darene jemage bai gani bah"
   "Daren goma sha hudu"
Ya fada yana dariya tsaki shuairat ta ja ta bar dakin umaima ta hararesa ckn salon so tace
   "Mom ce fah..she is ur in law u have 2 learn hw to respect her"
"Lol..babu mai shiga tsakanina da baby so ki xuba mana ido kawai"
   "Ni baby ! Ita baby! So which 1...gskiya ka xabi daya"
😳😳😳😳☹☹uhmm ni Reefat nace toh fah...umaima tun ynxu🙄🙄🙄🙄Dakyar bash ya fita ya barta ba don yana so bah nan ta fada wanka.

8:30pm garden din gidan mr president ya cika makil da jamaa an kawata wajen da kujeru da furanni masu kyau ga nan decoration de gwanin burgewa ga wutar lantarki ya haska wajen..yan mata da samari wasu suna xaune a bakin swimming pool suna ta hira manyan mata kuma suna can xaune daga masu cin abinci se masu shan drinks idan ka duba wani fannin kuma mr president ne tare da manyan mutane irin su US president Chinese president Nigerian president da dai sauran kasace daban2* daddy ma yana can tare da manyan abokanansa yan siyasa da yan kasuwa da ma talakawan gaba daya.amarya da ango sunyi ado sun sha kyau sai daukansu hotuna ake ana yadawa a social ntwrks suna can tare da frenz dinsu suna hira tare da xagayawa suna gaisawa da jama'a, shuairat tana xaune tare da manyan matan ministoci da shuwagabanni suna ta hira ckn nishadi.matured dinner irin Wanda baa taba yin irinsa ba a duk fadin kasar bcos babu irin kade-kade ko rawa da sauransu cool music kawai Ke tashi kowa na shaanin gabansa kyaututtuka kuwa wrapping ake sai a mikawa amarya da ango sannan security ya karba ya ajiye a wajen  da aka tanada domin ajiye kyautar.gwanin shaawa jamaa da dama sun halarci taron Wanda baxan iya lissafa su bah.
Washe gari aka dauki amarya aka wuce da ita gidan mijinta dake can central area bayan shuairat da sauran yan uwan mamanta sun mata nasiha sosai..mr president kam yaki haduwa da ita don ya tuna da mahaifiyarta yinin ranar gaba daya a ckn daki ya kasance , shuairat ce take lallabashi.da yamma akayi fansa a can gidan iyayen shuairat shukrah ma ta daure taje fansar.
[2/21, 2:42 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*96*

Bayan an gama biki lfy jama'a sun watse amarya ta tare a dankareren gidan ta Wanda an narka uban dukiya a cki.da safe ta tashi ta gyara gidan ta kunna turaren wuta tare da fesa room freshener gidan ya dau qamshi ta fada wanka ta shirya ckn atamfa tayi kyau sosai ta ajiye daurin nan a gaban goshi se xuba qamshi take ta gaji sosai don bata saba da aiki bah gskiya dole a kawo mata masu aiki tana nan tsaye a gaban dressing mirror bash ya tura kofa ya shigo tare da sallama ta amsa ba tare da ta juya bah rungumota yayi ta baya ya kwantar da kansa a kafadarta suna kallon juna ta ckn mirror fuskokinsu dauke da murmushi tace
"Morning BB"
"Morning dia hw was ur nyt"
"Alhamdulillh...
"Kinyi kyau baby Nah"
"Kaima kayi kyau my BB"
    "Nifa bana son wannan sunan "
"Bb ne baka so y?
"Ehh..nidai ki canza min bana so"
"Toh wanne kake so"
"Oho..
"Uhmm..na tuna *HP*
"Hp?...meaning?

"Honey pie"
Dariya sosai yake sannan yace 
"Toh BB fah? Me ma'anarsa"
    "Basheer Bello"
"Lah..sai na gayawa baba kina kiran sunansa direct"
   "Eyya fah..yi hakuri toh, ba na daina bah..daga yau sunan ka HP"
      "Ok tnx my baby"
Nan ya manna mata peck a kumatu ta bata fuska tace 
  "Toh nima bana son baby"
"Meyasa?
    "Cos haka kake kiran mom sultan kuma ni baxanyi sharing bah"
"Lallai yarinya..kishi kike da mom naki, ai zan gaya mata"
Ta fashe da dariya tace
   "Rufamin asiri pls..Bahaka nake nufi bah"
Wayarta ya hau ruri shi ya juya ya dauko yana dubawa yace

"Kinga Ya'r halak koh..wllhi baby ce"
Ya kara a kunne tare da cewa
  "A ina kika taba ganin ana kiran amarya da sassafe haka?
Daga bangaren shuairat tace
  "Toh Mara kunya ga nan surukinka yana jin duk abunda kake fada"
😳 ba shiri yayi saurin mikawa umaima wayar ta karba

"Hello mom ina kwana"
Dariya sosai shuairat take daga bisani ta amsa
   "Lfy ya kuka tashi"
"Alhamdulillh ..ina sweetie salman n sultan da kuma dad"
"Lfynsu kalau..dama brkfast na ba driver ya kawo muku"

"Ok Nagode mom..dama mom nace gidan yayi kato dayawa pls a turomin masu aiki"
  "Kai umaima..
"Allah mom gidan shegen girma ne dashi"
    "Toh da kin dauka xaman auren wasa neh"
  "Haba mom..pls ki taimaka kinsan xanje skul "
  "Ok naji...but Ke xakiyi girki da kanki"
"Insha Allah babu matsala xanyi"
"Ok toh..ki kula da kanki idan akwai abunda kike bukata ki sanar dani "
  "Ok Nagode..ki shafamin kan sweetie Nah"
   "Ok bye.."
Daga nan Suka katse wayar ta juya tana kallon bash tace

"Muje muyi brkfast "
Ya hada rai yace
"Waye sweetie kuma"
Dariya ta basa tace
  "C'mon salman ne fah"
     "Oh ho! I tot wani ne ai"
    "Ba kowa..kai kafi kowa sani duk duniya babu Wanda nake so fiye da kai so meyasa zaka damu"
Murmushi yayi sannan ya dagata cak! Kamar karamar yarinya Suka fito falo.


Bayan 5days da gama bikin umaima akayi resuming skul nasu 2weeks ta kara akai sannan ta fara xuwa.da yamma misalin 5pm ta dawo gidan a gajiye ta fada a saman kujerar falon matar da take mata aiki shigo tare da sallama
  "Sannu anty kina kokari wllhi"
    "Uhmm..ya xamu yi se hkri "
"Allah ya taimaka"
"Ameen Nagode.. Maigidan be dawo bane"
    "Ya shigo de dazu tare da wani yaro mai kama dashi"
Murmushi umaima tayi tace
          "Waleed dansa ne fah"
Ckn mmki matar tace 
"Au dama yana da wata mata bayan Ke"
  "Ehh..gidanta daban shiyasa baki taba ganinta bah"
Daga nan umaima ta tashi ta koma dakinta ta watsa ruwa ta fito ckn kankanin lokaci ta hada musu abincin dare couscous ne da miyar hanta se kuma lemun kankana da ayaba da kuma fruit salad, bayan ta gama tayi sallar magrib tayi assignment dinta ta gama sannan tayi isha har ynxu bash bai dawo bah ko me ya rikeshi oho! Kwalliya tayi ckn wata Ya'r karamar Riga iya guiwa tayi kyau sosai lipgloss kawai ta shafa se farar hoda da turare shikenan... Amma tayi kyau kamar a saceta a gudu har 9pm bash ya shigo tana nan xaune a falo yayi sallama cki2* ta amsa murmushi yayi don yasan laifinsa na rashin dawowa da wuri.
        Ya karasa kusa ya xuba guiwowinsa a kasa tare da kama kunne yace
     "Am sorry anty maimah"
Yadda ya furta sunan dole ya ba mutum dariya nan kuwa ta fashe da dariya hannu tasa ta jawo kunnensa har ya sake wata Ya'r kara yayi narai2* da ido yace
   "Ahh..akwai xafi fah"
ta tura goshinsa tace
"Zaka sake"
"No...am sorry wllhi ina gun baba ne muna wata er magana ne dashi"
      "Toh tashi..last warning"
"Ok mah!
Daga nan ya tashi tsaye batayi aune ba ya dagata sama yana dariya yace
   "Sai na rama abunda aka min amma ni nawa se yafi wannan"
ta shagwabe fuska 
"Haba HP..ni wani Abu na maka ne"
"Zaki gane yarinya hmmm..
Daga nan Suka wuce wajen cin abinci a kan cinyarsa ta xauna tana bashi a baki shima haka, bayan kowane loma daya sai anyi kiss daya😱😱 ...hmmm wannan wane irin Lov ne chabb🙊🙊Bayan sun gama bash ya shiga wanka yana fitowa sukayi shirin bacci ya kankameta a jikinsa yace

"Let's sleep nagaji sosai wllhi"
  "Da magana xamuyi but tunda ka gaji is ok sai gobe we'll talk abt it"
    "No...just say it now ina jin ki"
"Ok tnx...dama nace gashi munyi 3weeks tare kuma har yau baka koma gun Mmn waleed bah, nidai nasan 1week ya kamata muyi tare but har mun kara 2weeks akai gani nai....
Hannu ya daga mata yace
    "Wannan ba maganar ki bah..kwanta kiyi baccin ki let's nt talk abt dis"
    "No HP pls..b serious kaga ynxu laifina xaa gani wasu xasu ce daga xuwana na rabaka da matar kah n ...
  " I said is non of ur business"
Umaima ta ja bakinta tayi shiru sai kuma ta juya masa baya ya runtse ido ya jawota a jiknsa ta fara kukan shagwabah

"Am sorry dear..I din min 2hurt u pls kiyi hkri"
Nan ya cigaba da bata hkri daga karshe ta bada kai bori ya hau ance idan kida ta canza dole rawa ma canza😜😜 wata duniya daban Suka fada...
   Nasan wasu an baxa👂🏼 ana jiran 1st nyt koh..tohmm ya wuce Ku  domin umaima ta kirani a phn tamin gargadi😉😜

👍🏼👍🏼lov u all
[2/21, 2:43 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*97*
By *Reefat yahya*


Yau umaima ta cika 1mont a gidan basheer ta shirya xai ajiyeta a gidansu se murna take ta gama shirinta tsab ta fito ya tsaya ya kura mata ido bbu ko kiftawa ta karasa kusa dashi tace 
    "Kai HP wane irin kallo ne haka"
"Alhamdulillh Allah Nagode maka da ka mallaka min umaima a matsayin matata"
Murmushi tayi tare da cewa 
"Let's go honie kaga lokaci na tafiya"
   "Oh haka ma xaki fada koh..naga alama Ke baki dami dani bah se murnar xuwa gida kawai kike ni kuma tun ynxu na fara missing naki"
   "Hp rigima koh..yini fa xanje ba kwana bah kake wani xancen missing dina"
"Toh an fasa tafiyar ma ki bari se next week"
Ta shagawabe fuska tace
   "Don Allah ka bari bana so"
   "Haba baby girl Nah ...smile toh"
Dariya suke ya rike hannunta Suka wuce mota shi ya bude mata ta shiga ya rufe kofar sannan ya koma bangaren driver ya xauna daga nan Suka wuce gidan mr president.
      Murna sosai suke sultan ya makale Ya'r uwar tasa nan Suka xauna ana ta hira daga bisani bash yyi sallama ya tafi.bayan axahar shuairat suna xaune a daki tare da umaima tace
    "Yawwa mom ki ma bb Nah magana tun bayan auren mu har yau bai koma gidan Mmn waleed bah"
😳😳 shuairat ta xare ido ckn tsananin mmki tace
   "Waat? Wata daya?.. Anya lfynsa kuwa...hmm bari yaxo ya sameni gskiya somtin is wrong"
"Allah babu yanda banyi dashi bah yaki komawa ..idan na kawo maganar ma se munyi fada wllhi"
    "Barni dashi xai shigo ya sameni Allah se na hadashi da baba"
Haka Suka cigaba da yan hirarrakin su har xuwa dare bash yaxo daukar ta nan shuairat ta nemi yin magana dashi umaima ta tafi gun dad ta basu waje.
Shuairat ta hada fuska tace
     "Yaya wat is wrong wit u..da hnklinka da tunaninka xaka share 1month kana danne hakkin matarka?..haba yaya ina amfanin ilimin da kke dashi..
   "Baby ki bar maganar nan "
"No yaya let's talk abt it pls.."
     "Ok fine..since kowa yana bani laifi let me explain, da banyi niyyar gayawa kowa wannan magana bah cos is my secret but now I have to" nan y xayyana mata komai duk irin xaman da suke da shukrah har xuwa lokacin da yaji batun family planning da komai..hawaye ne ya cika idanun shuairat tace
"Allah sarki bestie... Wllhi nasan zugin bad frenz ne if not da ba haka take bah..ni nasan ba laifinta bane yaya kayi hakuri ka yafe mata pls"
    "Hmm..baby kenan"
"Allah yaya trust me nasan akwai wata a kasa ba haka kurum bah..duk da haka de ka daure ka yafe mata n pls ka raba musu kwana kana shiga hakkinta Allah"
"Naji..xanyi naxari akai"
  Daga nan shuairat ta fara masa nasiha mai kashe jiki yayi shiru yana sauraronta 
 "My yaya kasan shi xaman aure sai da hkri duk irin kaunar da kuke nunawa juna wata ran dole Ku samu sabani amma hakuri shine maganin komai..kuma hakkin aure ba abun wasa bah  musamman adalci tsakanin matayen ka, shiyasa Allah yace Ku auri mata 2 ko 3 ko 4 idan xaku iya yin adalci a tsakaninsu idan baxaku iya bah Ku auri 1 Ku bata dukkan hakkin ta na ci da sha sutura da sauran hakkin aure. Shin kana son ranar gobe kiyama ka tashi ckn mazajen da basu nuna adalci tskanin matayen su? Haba yaya ina amfanin karatun da kayi idan har baxaka yi aiki dashi bah"
Haka de shuairat ta cigaba da masa nasiha tare da kawo masa hadisai da ayoyin Qur'an jikinsa yyi sanyi sosai umaima tare da mr president da suke tsaye a bakin kofa sunyi shiru suna sauraronta wani shaukin sonta ne mr president ya tsinci kansa a cki ..tabbas shikam yyi dace a duniya Allah ya hadashi da mace ta gari hawayen farin cki ne ya cika idanunsa ya tsaya kim ya kura mata ido ya daina sauraron me take fada sai bakinta kawai yake kallo ya shagala da kallon taji a jikinta kamar wani na kallonta nan ta juya idanunta Suka fada ckn nasa murmushi ta sakar masa ta sunkuyar da kai daga naN Suka karasa shi da umaima xama sukayi nan mr president ma ya dora nasa nasihar yana musu fatan xaman lfy daga nan sukayi sallama bash ya dauki matarsa Suka koma gidansu.
        Mr president ya kasa hakura suna fita ya jawo matar tasa a jiki ya rungumeta gam tamkar xai maidata ckinsa tayi lamo a jikinsa tana jin bugun xuciyarsa a hnkli ya rada mata a kunne
"I Lov u so much Ayshata Allah ya barmin Ke har gidan aljannah"
    "Lov u more swt hrt"
Ya sassauta rungumar yana kallon kyakkyawar fuskar ta yace 
      "Ina da albishir da xan miki but se kin bani goro Nah"
"Aw rily..muje toh ynxu xan baka kuwa"
Daki Suka wuce ni kuma na tsaya a falo nace abun yafi karfina dole na hakura har xuwa lokacin fitowar su.
Bash da umaima ma hakan ta kasance soyewarsu kawai suke ni Reefat nace oh..duk inda naje ana ta xuba Lov kawai toh ina zan samu labarin ne☹☹
Da safe around 10 bash yayi parking a ckn gidan shukrah ya fito se xuba qamshi yake ya bude kofar falon tare da sallama tana xaune ta buga uban tagumi ckn sanyin murya ta amsa sallamar ya nemi kujera ya xauna dakyar ta bude bakinta ta gaida shi y amsa ba yabo ba fallasa yana satar kallonta ta rame kuma tayi sanyi dayawa ba haka yasan ta bah, ita ma satar kallon nasa take yayi kyau sosai hnklinsa kwance wato shi bai damu da ita bah ..wani guntun kwalla ne ya xuba a fuskanta tayi saurin goge wa yayi kamar bai ganta bah..ya katse shirun da cewa 
"Kina bukatar wani Abu ne?
Ckn rawar murya tace 
   "Dama..ina son xuwa ganin waleed "
"Yaushe kika fara damuwa da dan naki"
Kukan da take boyewa ne ya kubce mata ckn Muryar kuka tace
  "Don Allah kayi hakuri ynxu ganinsa ne kadai xai ragemin radadin da nake ji pls ka taimaka min"
Ya tabe baki tabbas yaji tausayinta amma dole ya hora ta ya tashi tsaye yace
  "Maybe anjima xan kawo shi"
  "Nagode "
Bai ce komai ba yasa kai ya fice.ta koma ta xauna ta cigaba da kukan da take lallai rayuwa kenan..ta fara tuna rayuwar da sukayi a baya har xuwa lokacin haduwarta da fatee a watsap da kuma irin gurbatattun  shawarwarin da tayi amfani dasu gashi yau an rabata da mahaifarta an kuma rabata da masoyinta na gaskiyA..tana ji tana gani ya auri wata babu yanda ta iya sallama taji ta daga kanta Suka hada ido carab da shuairat😱😱 ..

....
[2/21, 2:43 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*98*
By *Reefat yahya*


Dakyar shukrah ta amsa sallamar ckn jin kunya idan ta tuna abubuwan da mata a baya batayi tsammanin xata sake xuwa gidan bah..Allah sarki shuairat bata chanja hali bah har ynxu tana nan yadda tasan ta.shuairat ta xauna fuskarta dauke da murmushi tace
"Shegiya anji jiki koh..naga kin rame nasan kinyi regretin "
Murmushin karfin hali shukrah tayi tana mamakin hali irin na shuairat Sam bata fushi bata dauki duniya a bakin komai bah bata...
  "Bestie tunanin me kike haka..kinga yanda kika xama kuwa"
Hawaye ne ya fara saukowa nan ta fashe da kuka shuairat ta kwantar da salman ta dawo kusa da ita tace 
   "Pls..am here now kuka ya kare ki share hawayenki ki gayamin meke faruwa"
Haka kuwa shukrah tabi umarninta ta share hawayen tare da kwashe labarin komai ta xayyana mata shuairat tayi tsaki tare da cewa
 "Daman nasani ai...tun ranar da na sameta a gidan nan nasan lallai kina ckn hadari amma baki saurareni bah, haba shukrah ya xaki yarda da wacce baki taba gani bah baki San daga ina ta fito bah daga haduwa a watsap shikenan? Haba kinsan koda a ce mutanen duniya xasu taru gaba daya su cutar dake kinsan baxan taba kasancewa daya daga cknsu bah , shukrah na xauna dake tun muna yara na dauke ki ne a matsayin Ya'r uwata ta jini bawai aminiya kawai bah..shukrah ba gori xan miki bah amma ina son ki sani cewa nice silar auren ki da yaya"
Shukrah ta xare ido ckn tsananin mamaki shuairat ta cigaba da cewa
    "Yes...hakane shukrah ina son ki sani cewa xan iya mallaka miki duk abunda nake dashi a duniya bcos na dauke ki ne as my blood sister but meyasa xaki amince har mutane su shiga tsakaninmu? Y shukrah? U knw I Lov u"
Nan shukrah ta rungume shuairat suna ta kuka mai ban tausayi dakyar Suka sagaita kukan shuairat tace 
    "Ynxu duk ba wannan bah..ina son ki daura damarar gyara rayuwar aurenki ba don ance miki baxaki kara haihuwa Ke shikenan kin gama rayuwar aure bah no! Shukrah ki daidaita da mijinki Ku xauna lfy ki nemi lahirarki ki ajiye komai a gefe pls..
Shukrah tana kuka tana Neman gafara tana cewa
        "Nasan duk duniya bayN iyayena bani da sama dake shuairat ki yafe min don Allah ba laifina bane sharrin shaidan ne"
Harararta tayi ckn wasa tace
  "Ba wani sharrin shaidan dolancin ki ne ya jawo hakan"
"Ehh..koma menene de na amince ki kirani dashi nasan na cancanci hakan "
  "C'mon ni baki min laifin komai bah..kedai ki bawa yayana hakuri Ku xauna lfy , shukrah kinsan Ke aminiyata CE kuma yar uwata umaima kuma ya'ta ce don haka ina Neman alfarma a wajenki pls ki danne xuciyarki ki daure Ku xauna lfy kishin hauka ba naki bane, babu ruwanki da ita ki kame girmanki kiyi sabgar ki pls"
"Insha Allah bani da matsala da wannan"
   "Yawwa ..haka nake so kawata"
Shukrah ta sake rungumarta har ynxu bata 
Daina kuka bah shuairat tace 
  "Haba kukan ya isa pls hajiya" murmushi tayi sannan ta juya gun salman tace
"Kinga har na manta da dana , rabona dashi tun kuna wankan jego"
Shuairat tayi dariya tace "baxai kira ki mom bah yana fushi dake"
     "Ah ah yayi hakuri don Allah" daga nan ta dauki yaron katoto dashi tana cewa tubarakallah.shuairat ta tashi ta fara gyara gidan shukrah de se kallonta take tana jinjina mata a ckn xuciyarta shuairat tace
"Malama ba kallo xakiyi bah ki sauke wannan lukutin kixo mu kama aiki bamu da lokacin xama se mun gama gyara gidan nan"
Shukrah na murmushi ta nemi xani ta goya shi wannan suka cigaba da aiki, bayan sun gama gyara koina yayi fes Suka kunna turaren wuta se qamshi Ke tashi daga nan Suka fada kitchen lafiyayen girki sukayi abinci kala 3 Suka dafa.shukrah ta fada wanka tayi ado Wanda rabonta da kwalliya tun ranar fansan auren umaima , tayi kyau sosai ta fito fes shuairat ma ta watsa ruwa sannan tayi ma salman wanka ta chanja masa kaya daga nan Suka ci abinci bayan sun gama Suka cigaba da hirarsu, shuairat ta kawo mata tsaraba tun xuwansu China Hutu ..English wears ne masu kyau da kuma Chinese gowns da turaruka masu tsadan gaske shukrah kam se hawaye take shuairat na mata dariya tace
"Ke..namanta ma ban gaya miki bah, an sama min admission a new Delhi maybe next week xamu tafi"
"Da gaske wow na miki murna bestie Allah ya bada sa'a
   "Ameen sahibata "
Daga jin wannan sunan shukrah ta hada rai shuairat tace
"Yaya de? "Mtsw..sahiba da kika kirani dashi ne ya tunamin tsinanniyar yarinyar can"
Dariya sosai take mata haka Suka cigaba da hira har bayan azahar shuairat ta kira driver nan sukayi sallama bayan ta tabbatar ta bawa aminiyar tata shawarwarin yanda xata shawo kan mijinta da kuma wasu bayanan sirri😜😜Daga nan sukayi sallama har bakin mota Suka rabu ckn kewar juna.

Karfe 8pm ya shigo har ta fidda ran ganinsa ya shigo tare da waleed wani farin cki ne ya lullubeta take ta rungumi Dan nata se kuma hawaye ya cika idanunta bash yayi saurin kawar da kai gefe dakinsa  ya wuce dakin an gyara shi tsab se qamshi Ke tashi nan ya fada wanka.shukrah kuwa se nan nan take da waleed kamar xata hadiyeshi tana kaunar yaron nata haka ta xuba masa abinci ita take basa a baki har ya koshi ta dauko masa chocolate yNa xaune a samN cinyRta yana xuba suru2 dai2* nan bash ya fito ckn jallabiya qamshin turarensa ya mamaye falon shukrah tana satar kallonsa yayi kyau sosai waya yake daga ji tasan umaima ce yana lallabata akan ta kwanta tayi bacci wani kishine ya turnuketa dakyar take karanta innalillh nan ta Dan samu sauki ta daure dakyar tace masa 
" a xuba maka abinci ne" yana faman danna waya ya amsa da
"Barshi kawai bana jin yunwa" waleed yace 
"Abba ba dazu a mota kace yunwa kke ji bah"
"Na koshi my dear muje kayi wanka ka kwanta koh"
     "Abba ba xamu koma gidan mama ba"
"Sorry nan xamu kwana se gobe mu koma koh"
   "Toh"daga nan ya ja hannun yaron Suka wuce dakinsa shukrah tayi niyyar share sa amma ta tuna shawarwarin shuairat dole ta kwantar da kai.. Haka ta tashi tabi bayansu tace xata ma waleed wanka babu gardama ya amince ta masa wanka tare da shafa masa mai uban ya fito da kayan barcinsa aka sanya masa nan ya kwantar dashi tare da tofa masa adu'oi ya kwanta a gefensa ya cigaba da danna waya.
   Shukrah ta gaji da tsayawa ta koma dakinta ta sake wanka tare da saka er rigar baccinta mai daukar hnkli ta fesa turaruka daban2* sannan ta koma dakin nasa. waleed yayi bacci shi kuma yNa nan yana danne2* a wayarsa da alama chat yake da matarsa ta xauna a gefen gadon ckn sanyin murya tace
"Bbn waleed ka yafemin nasan nayi kuskure kuma..
   "Na yafe miki shukrah don't worry jeki ki kwanta "
Hawaye ne ya cika idonta a hnkli Suka fara sakkowa bash ya cigaba da abinda yake , sheshekar kukan nata ne ya janyo hankalinsa ckn Sauri ya daga kansa dama tunda ta shigo bai kalleta bah se ynxu...wow tayi kyau sosai shi kansa yasan tafi umaima diri cos tana da Dan jiki kadan take ta burkita masa lissafi ckn kasala yace 
    "Me na kuka kuma bayan nace na yafe miki ..haba shukrah ki daina kukan pls"
Bata sauraresa ba ta cigaba da kuka a hnkli ya sakko daga gadon ya dawo bangaren da take cak ya dagata sai  dakinta ya dira ta kan gado yace 
"Kiyi hakuri ki daina kuka na hakura ok..am sorry too nasan na miki laifi also ki yafemin" ckn dabara ta rungumesa yana jin dumin jikinta de labari ya chanza 🙈🙈 bakinsa ya tura ckn nata nan Suka fara kissin juna passionately tabbas yasan yayi missin nata ko kuma in ce sunyi missing din juna about 3months ko fiye da hakan..hmm a wannan daren shukrah taji jiki 😜😜 bash kuma se sambatu yake.

*ina theme shukrah Ku fito mu taka👯👯*

*theme umaima nko??*😏😏
Lols...
[2/21, 2:43 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*99*
By *Reefat yahya*


Albishirn da mr president yayi wa shuairat dama na samun admission ne , ya sama mata makaranta a new Delhi can kasar India. Bayan kwana2 shuairat tayi sallama da en uwa da abokan arxiki jirginsu ya daga xuwa delhi tare Suka tafi da mr president sultan kuma ya koma gidan umaima a can xai cigaba da xama.
        Sun sauka lfy mr president dama ya kama musu gida.bayan sati 1 shuairat ta fara xuwan skul salman kuma an kaishi day care mr president yana gudanar da harkokinsa ckn kwanciyar hnkli, haka rayuwarsu ta kasance ckn so da kulawa kullum suna waya da en gida salman ya kara haske ya girma yyi kyau sosai, sunyi shekara 1 a can da yake shuairat suna Hutu a makarantar tasu donhaka Suka shirya kawo xiyara a Nigeria.
Bash tare da umaima da sultan su sukaje tarbansu a airport umaima ta kankame shuairat tana dariya tace
  "Wow..mom kin kara kyau gskiya xaman Delhi ya karbeki "
"Rily...
"Yeah...Allah kinyi kyau sosai"
Suna dariya ta juya gun dad yana dauke da salman tace
    "Oh..sweetie an kara girma irin wannan jiki haka"
Tasa hannu ta karbesa sultan ya karasa kusa da shuairat yNa cewa
"Mom I rily miss u"
"Miss u more my boy.. Daz y nace tare da kai xamu koma"
    "Allah mom...gskiya naji dadi"
Bash ya gaisa da surukin nasa ckn jin kunya umaima ma haka tana wani sunne kai sabida katon cki ne da ita yakai 9months haihuwa ko yau ko gobe. Shuairat ta CE
 "Umaima da karanbani ..ina Ke ina daga salman a ckn wannan condition din da kke cki"
    tasa hannu xata karbeshi ta cigaba da cewa
    "Duk laifin dad ne yaro ya iya tafiya da kafafunsa amma kullum yana hannu tamkar wani jariri"
Mr president yayi carab yace
  "Aa aa hajiya kada ki wahalar min da yaro bani shi a nan"
Yasa hannu ya karbe salman yaron se dariya yake daga nan Suka shiga mota se gida.
   An share gidan ko ina fes fes ga abinci an jera musu a falo Suka xauna gaba daya ana ta hira masu aiki na shigowa suna musu Barka da xuwa mr president ya shige cki ya barsu shuairat tana murmushi ta kalli umaima tace
   "Mom 2b"
Kunya ne ya kamata ta rufe fuska tana dariya tace 
 "Mom ki tayani da adua Allah a tsorace nake kullum ckn fargaba nake kwana"
"Dong worry insha Allah zaki sauka lfy babu wata matsala..ba kina tofa yasin da na gaya miki ki yawaita yi bah"
   "Ehh ..ina yinsa ever month"
"Masha Allah...Allah ya raba lfy"
   "Ameen mom Nagode"
Salman ne ya shigo tare da sultan yana tafiya irin tasu ta yara a hnkli yake takawa sultan na masa wasa se dariya yake gashi yana koyon magana umaima tabi yaron da ido daga bisani ta juya gun shuairat tace

"Allah mom kin iya haihuwa..bana gajiya da kallon sweetie "
Dariya sosai shuairat tare da cewa
  "Kedai kina son sweetien nan naki..Allah yasa ki haifi mai kama dashi"
"Ameen wllhi da naji dadi kuwa..nayi nayi muje scanning HP Nah yaki amincewa wai mu jira lokaci"
   "Hmm ai halin  yaya se a slow..anyway kwana nawa ma ya rage, Allah de ya saukeki lfy"
  "Ameen"sallama Suka ji daga bakin kofa shukrah ce ta shigo tare da waleed se kuma bash yana biye dasu a baya 
 "Oyoyo anty shuairat"
"Wani irin anty ..bayan kin ki xuwa daukata a airport ai takardar saki xan baki"
  "Wayyo...mijin a min afuwa"
Dariya suke shukrah ta karasa ta xauna kusa da shuairat umaima ta mata Barka da xuwa ta amsa ba tare da ta kalleta bah , bash ne ya jawo hnklinsu yana yi wa umaima magana da cewa
   "Baby akwai abinda kke bukata ne"
 "Aa ba komai"
"Babu inda yake miki ciwo"
    "Babu"
"Ok ki kular min da kanki da kuma baby Nah xan fita se dare xan dawo mu koma gida koh"
ta shagwabe fuska tace
    "Haba HP ba anan xan kwana bah"ganin abun nasu ba karewa xaiyi ba 
Shuairat ta wayance  tace 
   "Kwana kuma? I tot da dawo wankan jego ne "
Bash ya harareta da cewa 
    "Wankan bom ne...babu inda xata dawo a gidan mijinta xata haihu a can xatayi wanka"
"Oh..yaya ko kunya babu Allah ya bada saa ka tafi nikam ka katse mana hirar mu"
Yana dariya ya juya yace 
  "Mmn waleed na tafi"
"A dawo lfy" ta amsa a gajarce daga gani kasan ranta a bace.bash ya juya yayi tafiyarsa umaima tayi saurin bin bayansa ko me xata gaya masa oho!
 Idanun shukrah ya cika da kwalla shuairat tayi saurin cewa

"Haba bestie karki ban kunya mana..ynxu dan wannan abun ne xaisa ki kuka? Idan ta haihu kuma sumewa xakiyi kenan.. Pls act maturely ki danne xuciyarki nasan cin fuska ne amma kiyi hkri kiyi behavin kanki kada raini ya shiga tsakaninku"
Shukrah ta share hawaye tana mai cewa

"Ba haushinsu nake ji bah...haushin kaina naji ni na cuci kaina "
  "No...kaddara ce babu Wanda ya isa ya hanata afkuwa so just take hrt ki yarda da kaddarar ki kuma ki godewa tunda kin samu kina da daya , wani har ya koma ga mahallicinsa ma baxai samu ikon ganin jininsa don haka yana da kyau bawa ya kasance mai yawan godiya a duk halin da ya tsinci kansa a cki"
  "Maganar ki gskiya ce Nagode Allah bar xumunci"
Shuairat ta cigaba da kwantar wa shukrah hankli umaima ta shigo kallo daya ta musu ta dauke kai tayi wucewarta.haka Suka cigaba da hira har lokaci sallah yyi Suka gabatar da sallah tare da cin abinci, umaima bata fito bah don haka shuairat ta ynke shawarar duba ta.
    Tana kwance a dakinta ido 2 shuairat ta shigo tare da sallama cki cki ta amsa tamkar bata so shuairat tace
   "Ki fito ki ci abinci" "na koshi" 
    "Lfynki kuwa..so kike ki kashe abunda Ke cikin ki da yunwa , tashi maxa ynxun nan"
"Allah ni nace miki bana jin yunwa"
Shuairat ta tabe baki tayi ficewarta shukrah kuwa tana ganinta ta hada rai shuairat ta koma ta xauna ta fara magana ta ga shukrah na amsawa kamar bata so , umaima ce ta fito fuska a hade ta bude fridge ta debo ruwan sha shuairat tace
"Haba umaima...ya xaki sha ruwan sanyi a ckn halin da kke cki "
"Haka nake so"
Tayi shiru tana mamakin wannan sauyin ckn kankanin lokaci ta juya gun shukrah itama ta hada rai nan shuairat ta gane matsalar ta tashi tsaye ckn masifa tace
"Nifa baxaku maida ni er iska bah...kowacce ta hada rai toh wllhi ni ba munafuka bace ga fili na bar muku kuyi abunda kuka ga dama"daga nan ta haura xuwa dakinta mr president yana kwance ta shigo ckn bacin rai yana kallonta yace
"Wa ya tabo min my lady"
  "Mtsww...aikin banxa, nema suke su mayar dani munafuka wllhi karyansu"
"Su waye?  "Umaim da shukrah man"
"Aw...kice min aminiyarki da ya'r ki matan yayanki"
Wani kallo ta jefa masa tare da cewa "meaning"  "meaning notin ..kedai ki bi a hnkli" haushi taji nan ta fada toilet se cika take tana batsewa mr president kam dariya ta basa ya girgixa kai yace "oh Aysha ba dai rigima bah"
Har dare basu sanyata a ido bah har xuwa lokacin da bash yaxo daukarsu shukrah ta shiga gidan gaba ta xauna umaima tare da waleed Suka xauna a baya, ta cika tayi fam a haka Suka karisa gida.

Bayan kwna 3 da xuwan su shuairat momsi da daddy Suka kawo musu xiyara a wannan Daren umaima ta haifi kyakkyawar erta mace murna a gun bash baa magana shukrah kam kuka ta kwana yi a wannan Daren. Haka en uwa Suka yi ta xuwan Barka.

😍😍
[2/21, 2:43 PM] Reefat: 💞NI DA SHUGABAN KASA💞
*100*
By *Reefat yahya*

*last page*

Ranar suna yarinya taci sunan maman umaima wato zainab anyi shagali sosai mai jego sun sha hotuna tare da en uwa da abokan arxiki a gidan mijinta ta xauna aka hadata da wata tsohuwa ta xauna da ita , bayan 2weeks shuairat taje gidan iyayenta da gidan shukrah da kuma umaima sukayi sallama wannan karon tare da sultan xasu koma hakan kuwa akayi jirgin yamma Suka bi sai Delhi.

   1yr leta ...shuairat ta kammala degree nata dama kos din shekara 2 ne tayi ynxu ta fara masters sultan yana js2 salman kuwa yana da shekara 2 da rabi ya gara girma yayi wayo sosai sai shegen surutu muryarsa radau babu maganar da be iya bah .mr president ya bude wani kamfani a nan Delhi na sarrafa gwalagwalai😜 a China kuma yana da kamfanin sarrafa motoci , idan aka zo gida Nigeria kuma abun baa cewa komai don babu inda zaka shiga ka kira sunansa a ce da kai baa San shi ba..yayi kaurin suna yana da kamfanoni da dama ga gidajen mai da sauransu.bash Ke kula masa da harkokinsa na Nigeria se bayan wata 1 yake xuwa , umaima ta sake haihuwa namiji ta Haifa aka rada masa Suleiman suna kiransa Abbas zainab kuma Ummi ake kiranta.rayuwarsu ta kasance ckn so da kulawa umaima ta gama tana kula da daya daga ckn kamfonin mahaifin nata dake Abuja arxiki ya bunkasa babu harkan talauci shukrah ma mijin nasu ya gina mata katafaren boutique tana harkar kasuwanci ckn kwanciyar hnkli a jarida ta samu labarin an damka fatee tana gidan yari a can Kaduna.
          Shuairat na kwance a kasan kafet ga katoton cki Wanda xai kai wata 6 idanunta a lumshe suke da alama bacci take ji mr president ya shigo ya xauna kusa da ita 
      "Pls my lady ki tashi bana son kina kwanciya a kasa ko so kke ki cutar min da ya'
Harararsa tayi tace "wato ni idan naga dama na mutu koh..dama ai Ku maxa haka kuke kunfi son ya'yan Ku fiye da komai mu mata...
"Pls not again Aysha ba haka nake nufi bah ki tashi don Allah"
"Ni ka rabu dani don Allah" ta sake gyara kwanciya ya rike kai haka yake fama da wannan ckin se masifa da shagwaba haka laulayin yaxo mata Abu kadan ta fara fada ko kuma ta fashe da kuka ..ya ja dogon numfashi ya marairaice "haba mom sultan kinsan ba kyau mace ta dinga kwanciya sanyi na shigarta is not gud pls"
"Ni a nan xan kwanta" yasa hannu ya dagata duk da nauyin da ta kara haka ya dagata xuwa daki ya shimfidata a gado nan kuwa ta fara kuka ya xauna a gefe yana lallabata dakyar bacci yayi gaba da ita. Bayan magrib ta farka ta gabatar da sallah sannan tayi wanka , wata doguwar farar Riga ta sa mai dogon hannu a hnkli take tafiya ta fito falo suna xaune sultan yana koya wa salman ABCD mr president yana kallon news ta shigo babu ko sallama fuska a hade salman ya daga kai Suka hada ido yayi dariya yace "lah...mother conpesho(confessor) bhai!( sunan da yake kiran sultan dashi wato yaya da harshen Hindu) bhai ka tuna film da muka kalla na mother conpesho..irin rigarta ne mummy ta shaka" yana magana da harshen yara masu koyan magana wata uwar cafka shuairat ta kai masa ta matse bakin tana huci tace "nice mother confessor? Uban wa yace ka kalli film har xaka rike sunayensu..ban hanaku kallon film bah" ta juya gun sultan cikinsa ya duri ruwa ya sunkuyar da kai yace 
"Mom kiyi hkri wllhi...
"Rufemin baki daga yau nayi seizing laptop dinka " salman yana kuka ta turashi gefe nan mr president ya jawosa yana lallabashi yaron se kuka yake ita kuma ta xauna tana karkada kafa ta cika tayi fam ..sultan kuma jin an ambaci xaa rabashi da laptop nan ya fara kuka ya tashi xai koma dakinsa shuairat ta daka masa tsawa tare da cewa "dallah dawo nan ka xauna ina kake tunanin xaka je , ni Saar ka ce don na maka fada xaka tashi ka tafi..ynxu Ku rufemin baki Ku tashi Ku cigaba da karatu ko na tattaka yaro a nan wajen" sum-sum ya dawo ya xauna salman ma ya hadiye kukan da yake don yana tsoron maman nasu bata daukan wargi , mr president de sai kallo kawai yake musu bai tanka bah bayan ta gama yace "my lady can we talk" bata ce komai ba ta tashi ta koma daki yabi bayanta da ido daga bisani ya tashi ya wuce dakin tana kwance a bisa gado tayi matashi da filo se karkada kafa take ya xauna dab da ita tare da rike mata hannu "my lady pls ki rage yawan fadan da kike wa yaran nan xasu fara jin tsoron xama inda kike" "naji xan rage amma kasan yara idan an sake musu kadan shikenan se kaga tarbiyarsu na Neman lalacewa kuma gskiya kana sake musu too much" murmushi yayi yace "oh wannan babyn rigimammiya ce gata da yawan fada ga kuma shagwaba" ta gyara kwanciyarta ya jawota a jikinsa yace "baki ci abinci bah Ayshata y? "Ni bana jin yunwa" "pls ki daure ki ci koda dan kadan ne nikuma I promise u xan kawo miki icecrm" bitt ta tashi xaune ckn jin dadi tace "da gaske ..wllhi kuwa xan ci muje mu fara siyan icecrm b4..
"Haba my lady bani nace xan siya miki bah..trust me" ta tura baki tace "toh ba Kaine ka daina siyamin bah kana biyewa munafukar jankim wai ka hanani yawan shan sanyi da zaki" "yau kuma gum Jan takin ce ta xama munafuka..lallai babyn nan se a hnkli" ta tura baki wai fushi take bata Ankara ba taji bakinsa ckn nata nan ya rikita mata kwakwalwa tuni ya mantar da ita xancen wani icecrm😍😜.
   Da safe tana xauna a falo da kofin tea a hannunta salman da sultan Suka shigo bayan sun gaisheta ta amsa ba laifi mr president ya shigo ya xauna tare da manna mata peck a kumatu murmushi tayi ta cigaba da kurban tea nata salman yana xaune yayi shiru mr president yace "fine boy meke damunka" ya bata fuska yace "ba mom ce ta daina kirana da sweetie bah" me zasuyi idan ba dariya bah mr president yace "ah toh..lyk mother lyk son shagwabar de gado ce" murmushi shuairat tayi tace "com here " ba gardama ya karasa kusa da ita ta ajiye cup din hannunta ta daga shi tana nishi "uhm..my sweetie ina sonka kaji..but ka daina kallon film kayi karatu ka xama likita kamar anti jankim.. Ba kacemin kana son saka fararen kaya irin nata bah" "ehh..Jan yiwa bhai allula koh" "ehh..har dad ma zaka masa" murmushn jin dadi yayi shuairat ta kalli sultan tace "zo nan engineer sultan Suleiman.. Ko injiniya ss ne" sultan yana dariya ya dawo kusa da ita ta hadasu ta rungumesu tare da cewa "I Lov u koh..mom tana sonku Allah ya rayamin Ku ya muku albarka" "ameen"Suka amsa har da mr president daga nan tace su koma daki suyi karatu tunda weekend ne babu makaranta da yamma kuma kullum ita take koya musu karatun Qur'an. Mr president ya rungumeta yace "I Lov u Ayshata kina burgeni kin bani komai na rayuwa Allah ya sakar miki da gidan aljannah" "ameen my man Lov u more" wow...Lov birds😍😍😍..

*3montz leta* shuairat ta sauka lfy ta haifi ya' mace kyakkyawa aka rada mata fateema( sunan mama) suna kiranta umaisa, daddy momsi baba mama umaima bash shukrah tare da ya'yansu Suka shiga jirgi xuwa Delhi bayan suna sun kara 2weeks sannan Suka dawo Nigeria. Umaisa Nada shekara daya da  watanni 10 shuairat ta sake haihuwa wannan karon namiji ta Haifa aka rada masa bello suna kiransa saleem, a wannan lokacin ta kammala masters dinta tace karatun ya isheta haka Suka dugunxuma xuwa Nigeria tare kyawawan ya'yansu. 
      Yaran mr president 5 umaima sultan salman umaisa saleem.yana ji dasu tamkar ya hadiyesu amma yafi ji da salman da umaisa musamman ma umaisa yarinyar ta hadu sosai kamar ya'yan larabawa , umaima kuma ya'yanta 6 maza 3 mata 3 ..Ummi Abbas Ahmad feena Azeez shukrah. Suna xaune lfy kalau gwanin shaawa, shuairat ta kara kyau tayi maintaing na jikinta batayi kiba har can bah amma ta cika tayi kyau sosai an xama manyan mata naira ta xauna musu masha Allah.
     Suna xaune a makeken falonsu ga yan jaridar tambari magazine sun xagayesu ana musu interview tare da daukansu hotuna saboda mr president ya tsaya Dan takarar shugabankasa kuma ana sa ran xaiyi nasara ga nan yaransu a gefe suma ana daukarsu hotuna wani Dan jarida ne ya matso kusa yace wane heading xaa saka a fuskar magazine din tarihin rayuwarku" shuairat tayi carab! Tace *ni da shugabankasa* murmushi mr president yayi nan ya fara tuna ranar da Suka fara haduwa..ikon Allah kenan.
*ALHAMDULILLH....*
anan xan dakata da wannan littafin nawa as usual bana wuce 100pages a novels dina😜😜 saura kuce am laxy ehen....

Nagode wa Allah subhanahu wataala da ya bani ikon kammala wannan littafin ckn rai da lfy...godiya gareku masoyana da kuke bani karfin guiwa da kuma shawarwari Nagode da kulawarku Lov u all...masu turamin sako da masu kirana ina godiya gareku Allah yabar mu tare..
*gaisuwa gareku*
Anty baby ( ummu Suleiman shuaib yan awaki)
Hadiza Salish Sharif
Abdulazeez sani 
Shehu usman Mohd
Maryam k/mashi
Adda benah
Kheeleesat haiydar
Ummi Aisha
Batul Mamman 
Maman shakur
Da sauran writers...
  *blood is thicker dan water*...sis Reedat (Mmn haisam)
Sis teemah (Mmn afra)
N mie...(Mmn haneef)

*jinjina* gareku (grps)
Matan gidan gyara
Nisa'ul jannah 
Professional writers
Duniyar novels
Manshat novels
FGGC yola class of 2012...
N to all fans of *nida shugabankasa* Lov u all

*maryam jika my PA😀👍🏼  jinjina gareki tare da kaneem dost* na gode da taimakon da kuke min😍
*nanasticaly Nah ban manta dake bah..tare da xeetah n teemah lov*...
Allah yasa mu dace...





Download Ni Da Shugaban Kasa Littafi Na Daya Complete