[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
NA
khadija usman
*BISMILLAHIR RAHMANIRRAHIM*
1⃣
Na rantse da Allah bazan yadda ba sai an biyani nikana tun
kin isa ma wlh kika sake kika je kika fadawa innata yaseen sai kinci ubanki cewar dije dake kara tattake garin dake zube a kasa kuma an barar din duk ranar da kika qara cemin dijan gala tame gari tuwon gidanku ma zanje in barar wlh
su Shatu dake gefe suna kallo ba damar suyi magana dije taci uwarsu dan haka sukayi gum ko yi hakurin sun kasa fada hafsi kuwa sai rizgar kukanta takeyi dan tasan yau idan taje gida kashinta ya bushe gurin delu dan saita mata dukan mutuwa kuma tasata nemo mata wani garin koda ta tuna ai saita kara bare baki dije ce ta kalleta tace wai ke uwar me nayi miki da kiketa min wannan kukan danma ban faffasa miki baki ba hegiya me idon gyada
shatu ce ta karaso kusa da ita tace kin san delu dukanta zatayi idan taje gida kin san dai ba imani ne da ita ba
shuru dije tayi na dan wani lokaci kamar wadda ta tuna wani abun sannan kuma tace toh kinga ke kika jawo wa kanki tunda kika tsoka ne ni amma kiyi haquri kinji tahi nasan yadda zamuyi amma sai kin bani hakuri
da sauri hafsi tace yi haquri dan Allah
toh naji ya sunana
Anti dije
wani farin ciki ne ya mamaye zuciyarta dan tana masifar son sunan nan na 'yan binni dan haka da sauri tacewa hafsi taso muje gidanmu in baki dawar ki kara kaiwa nikan
da sauri hafsi ta mike dan tasan ko yanzu takai nikan sai ta ci ubanta dan ta jima dan haka da sauri suka je gidansu dije koda suka je dije bata boyewa inna saudi komai ba aikuwa ta basu dawa suka kai nika har gida dije suka raka hafsi aikuwa delu kamar ta ari baki taita jarabar ta dayake 'yan dukan basa kusa sun dai samu rabon zagi amma bata daki hafsi ba
********
mota ce kirar honda Accord LC ta shigo cikin garin Gawo kasancewar rashin kyawun hanyar ga kuma da alama wanda ke cikin motar yasha tafiya mutum biyu ne ciki matasan samari kyawawa daka gansu kaga wadanda hutu da nera suka zauna a wajen tuki yakeyi kamar wanda aka yiwa dole kafin ya waiga ya kalli dayan yace cikin kasalalliyar muryarsa
Habeeb wlh nagaji dayawa na matsu mu qarasa cikin garin nan in yada zango kan gadon tsohon nan
wanda aka kira da habeeb yayi murmushi kafin yace hmm kaima kenan bare kuma ni dana sha tafiya kwana nan gashi yau ma son ganin wannan me ran karfen yasa na biyoka
hmmm kai dai bari ai wannan tsohon inaga rokon Allah yakeyi mana shiyasa bama iya daukar lokaci bamu ganshi ba ko daddy ma fa kullum shi batun shi baba malam kusan koyaushe yana kan hanya
toh Allah yaja da kwana dai
Ameen ya Allah
kam bala'i ta fada yayin da taga motar na kokarin shigewa alamar ma na ciki besan me yayi ba giginyar dake hannunta ta dauka ta saita glass din motar ta wurga cikin sa'a kuwa ta daki glass din side driver sannan taje ta hada da bakin habeeb wanda yagama amsawa da ameen yanzu
wani wawan birki ya taka tare da kiran ya Allah sbd ganin abun da yayi kamar a mafarki dubansa yakai inda habeeb yake yaga nan da nan bakinsa ya haye ya wani kumbura kamar bakin jaba ga kuma jini na zuba yaso yayi dariya harga Allah amma ba hali dole ya ambaci kalmar subahanallah ya fara kokarin bude motar ya fito danya zagaya gurin habeeb dan shi har yanzu baisan ta inda abin yafaru ba amma dai kawai yaga wulgawar abu
tsaye take ta rike kugu da hannu daya dayan kuma wata katuwar giginyar ce datafi ta farko girma
kwalliyar fuskarta kawai yagani yaji gabansa ya fadi dan wlh babu tantama wannan aljana ce
wa'innahu sulaimanu wa'innahu bismillahir rahmanir raheem ya fara ambata cike da tsoro da faduwar gaba domin dai babu tantama wannan aljana ce duba da yanayin ta gata fara sol saika ce zabiya ga kuma uban bakin kwalli data shafa a bakin nan kamar 'yar auta ga jagira cinku ta hade da kwallin dataja hawayen masoyi
jikinsa ne ya hau kyarma inda ita kuma dije take ta fahimci meyake nufi aikuwa a zuciyarta tace anzo gurin
harara taci gaba da wurga masa tanata juya ido inda shikuma hakan ke kara firgita shi cikin karkarwar jiki ya qarasa inda habeeb yake ya sunkuyar da kansa kasa sakamakon nauyin daya yi masa sbd giginyar ta bugi kansa ga haqorinsa guda daya daya fita ga bakin ya kumbura yayi tsayi kamar shantu cikin rawar jiki Nasir yakarasa inda yake ya bude murfin motar yana me karanta duk addu'ar data zo bakinsa dago kansa yayi ya dubeshi jin yanata kwarara addu'a sai ya fahimci lallai gamo sukayi domin ya hango aljanar tsaye da irin tasu giginyar ta Aljanu tanata juya ido duk da jirin dayake ji hakan bai hanashi rudewa ba shima ya kama kokarin fitowar nan suka kankame juna shida nasir wanda har kwalla yafara yi dan tsoro musamman duba da yayi da yanayin gurin babu komai sai tarin bishiyoyi da besan kona meye ba amma dai yasan harda na kuka kuma sune gidan aljanu
cikin wata irin murya da malkwada harshe dije tace ku bil adama daga ina
wani irin fitsari ne ya kufcewa naseer shiko habeeb ji yayi kamar ya suma dan kanshi saida ya amsa
ko bakwa ji ne ina tambayarku?
cikin in i na nasir yace yi....yi..ha.k..uri.daga Abuja Abuja wlh muka zo
shine aka ce dan kunzo daga binni kubi takan 'ya'yana suna tsaka da yin wasan su wato sbd kun raina mu ko
ah ah wlh ba...bahaka bane wlh ku kuke ganinmu bamu muke ganinku ba dan girman Allah kiyi haquri wlh bamu sani ba
toh naji zan hakura amma sai dai kubar abin hawanku anan ku qarasa da kafarku inda zaku ko kuma ni inkai ku
ah ah wlh mun gode suka fada a tare zamu karasa da kafarmu ina ke ina wahala akanmu
hahahahahaha
tayi dariya sannan tace saini dije uwar aljanu ku wuce amma fa bazan kyaleku ba duba da yadda kuka raunata 'ya'yana yanzu haka suna bangon duniya wajen me magani dan haka sai naje naga yadda jikinsu yake tukunna kafin in san wanne hukunci zanyi muku
kuuuuu cikin nasir yayi wata kara dan girman Allah kiyi hakuri wlh bamu san dasu bane ina mu ina aikata haka muna sane
toh naji ku tashi ku tafi gobe kuzo ku dauke wannan motar amma ba yau ba
to toh toh mun yadda wlh
sam habeeb yakasa tafiya yayin da naseer ne ya kamashi da kyar yasaba a kafada ya miki hanya bako waiwaye harda hadawa da dan gudu bako waiwaye
tunda dije taga haka ta zube a gurin tanata dariya harda hawaye a irin wannan yanayin su shatu suka qaraso suka risketa nan suka shiga tambayarta sam kin fada musu tayi gashi ba damar su matsa ta dankari banza dan karfi ne da ita kamar yaki inji su duk ta fisu karfi
sai da tayi me isarta kafin ta mike tace mu tafi
hafsi ce tayi karfin halin tambayarta ina gyadar da kika samo ?
ban sani ba tafada tana harararta
ai kuwa tayi gum suka ci gaba dactafiya da zarara ta tuno yadda bakin habeeb ya koma da kuma yadda taga Naseer yayi fitsari saita kuma kyalkyalewa da dariya sudai su hafsi nasu ido amma ba damar tambaya sai uwar gayyar ta so bada labari dakanta
*****
tafiya yakeyi ya hada zufa ga habeeb na cikin wani hali da taimakon Allah da taimakon wasu matasa daya sansu a gidan baba malam suka qarasa da shi gida
*vote*
*comment*
*share*
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
4⃣
*dole in faranta muku masoyan ta me gari*
*jinjina agareku da godiya me tarin yawa masoya na kamar*
*JATTAKO NOVELS FANS*
*SADNAF NOVEL FANS*
*KHADIJA NOVEL FANS*
*HAJJAJOH NOVEL FANS*
*da duk sauran groups din da ban ambace su ba kuna raina*
****
jikin habeeb har rawa yakeyi sbd tsananin bacin rai haka ma ga Naseer sunma rasa me zasu ce ganin yanayin da suke ciki yasa me gari rike hannunsu tare da cewa dije ta tafi gida aikuwa ko kafin ta fita saida ta qara musu gwalo kowanne a cikinsu ji yakeyi idan ya riketa zai iya shaketa har saita mutu
malam ne ya shiga tausarsu da naseeha da nuna musu halin kuruciya ne
dan kawai tanada kuruciya sai akace tayi wa mutane halin dabbobi cewar naseer
kallonsa habeeb yayi kafin yace ai wannan yama wuce halin dabbobi ai sai na jakuna da tumaki irin na kauyen nan ma
sosai ran me gari ya sosu ganin yadda kiri kiri suketa zagin dije bama hakan yafi bata mishi rai ba irin yadda yaketa tausar su amma suna ta nuna kiyayyar su gareta inda har suke fadin baxasu je gidan su ba sam kenan hakan na nufin zasu tsiro da lalacewar zumuncin gidansa hmmm lallai dole yasan abinyi dan haka baxata taba sabuwa ba tashi yayi ya barsu anan sunata mita suka fasa fitar ma ko ina
*****
kwana megari yayi yana saqa da warwara kafin daga baya ya cimma matsaya tunda asuba a masallaci da suka hadu da yaransa da jikoki gurin yun sallah ya tsayar da malam inusa yace yana son magana dashi cike da ladabi ya amsa ya tsugunna gyaran murya yayi kafin yace kasamu labarin abinda yafaru tsakanin yaran nan nawajen khamisu da dije?
eh nasamu lbr gurin su ayuba jiya da dare har na bata kashi ma sosai
toh Alhmdllh amma banso ka daketa ba sai dai nagama yanke wani hukunci wanda ban sani ba ko zai yimaku dadi a matsayinku na iyayen khadija
insha Allahu baba duk abinda ka yanke nasan me kyau ne bazai cutar damu ba
masha Allah Allah yayi maka albarka
Ameen
dama bawani hukunci na yanke ba illa na turata birni can gidan shi kamisu din inyaso tasamu ilimin zamani itama sannan su fahimci junansu da zumunci me karko dan iya jiya da suka san juna naga alamar gurbin kiyayya a idon yaran sbd kuruciya shiyasa nake son ta zauna gidansu nasan zata samu rayuwa me kyau kuma zata nutsu domin inka duba kiriniya irin ta dije abin se addu'a
jimm yayi kafin ya nisa yace toh baba malam badamuwa Allah yasa haka yafi alkhairi sai dai mahaifiyar ita dijen sbd kasan gidansu sun tashi da akidar kin karatun boko shiyasa ko yanzu ta hana dijen tayi
kada ka damu inka koma kace ina nemanta zanyi mata bayani da kaina insha Allah nasan zata fahimceni dan tanada saukin hali
hakane nan yayiwa mahaifinsa sallama ya nufi gidan zuciyarsa cike da damuwa dan yana son dije kuma gashi a halin dije kauye ma ya aka kare bare binni kawai ba yadda zaiyi ne akan umarnin mahaifinsu
ba karamin fama malam yasha ba kafin inna saudi ta fahimceshi inda daga baya ya yi mata nasiha nan ya fada mata yau zasu tafi dan harda shi
koda aka fadawa dije abin mamaki murna ta dinga yi dan tana son rayuwar binni da kuma karatun boko dan haka ta shiga hada kayanta inda innarta ta dinga kallonta zuciyarta na tunanin inda 'yarta zata rayu gidan hajiya zahida macen dake kyamar mutane ko zuwa sukayi saita nuna a fili daga baya ma tace ta daina zuwa kuma kamar abin magani duk abinda ta ce ya zauna a gun Alhaji khamis
'yan tafiya sun shirya tsaf yayin da ba wanda yasan da tafiyar dije har saida aka zo tfy sannan akaga da malam za'aje kowa yayi mamaki zuciyar su habeeb kamar ta buga akan dole suka yi shuru dije ta shige mota ita da malam akaita daga musu hannu inda kawayenta keta murna da kuma kewar uwar mazga yayin da dayawan mutane ke murnar ala raka taki gona
*DIJE A BIRNI*
tunda suka shigo garin abuja ta zuro kai ta glass tana leke kamar zata fado yayin da malam keta murmushi yana tsokanarta ita kota kansa bata bi ba kallonta kawai takeyi sukuwa mazaje bakin ciki kamar ya kashe su da gayya nasir ya qara daga glass ai kuwa saida dije tayi kara dasauri malam yace lfy ?
bakomai baba malam bari zan rama
zaki rama me?
kai dai ka bari kawai kasan bana cin bashi ba'acin nawa dole in anci nawa sai an biya
toh Allah ya kyauta
Ameen
sun karaso gidan Alhaji khamis aljannar duniya inda cikin sa'a suka riskeshi kuwa ba karamin farin ciki yayi ba ganin dan tsohonshi a gidanshi kasancewar matar gidan ta fita shiyasa basu sameta ba nan bada bata lokaci ba me gari ya sanar da dansa komai da dalilin kawo dije kwarai ya nuna jin dadinsa inda nan take me gari ya nuna baxai kwana bazai koma dole aka sa drivrr ya mayar dashi ranar
******* me aikin gidan Alhaji ya kira ya ce tasa dije tayi wanka sannan ta bata abinci kafin hajiya ta dawo
koda hajiya ta dawo ba karamar rigima aka kwasa ba dan saida Alhaji yayi mata jan ido kafin ta yadda da zaman dije a gidan
kuyi managed
yanzu aka fara zaman dije a binni yafi na kauye cakwakiya
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
2⃣
*ina neman afuwarku sakamakon jina shuru da kukayi a littafina ZARGI NE SILA Insha Allahu shima zan karasa muku shi nan kusa uzuri ne yasha kaina*
ba karamin tashin hankali baba malam ya shiga ba ganin halin dasu habeeb suka shigo cikin rudewa ya shiga tambayarsu lfy ko hadari sukayi
sam naseer baya cikin nutsuwarsa abinda kawai yake iya fada shine gamo mukayi malam aljana wlh aljana ce
subahanallah!!!
malam ya fada kafin ya ce aje a kirawo muntari me chemist don ya duba habeeb domin yaga yana jin jiki da alama
bayan an gama masa duk abinda yakamata ayi masa harda allura malam kuwa rubutu yayi musu tare da tofa musu addu'oi sbd dukansu sun firgice daga baya suka samu bacci su duka kowa yanata al'ajabin abun wai aljana toh ko a ina suka ganta oho
****
da wakarta ta shigo tana rerawa inda ko sallama batayi ba ta shigo innah dake zaune tana dama fura tace kai kai dije nidai naga ranar da zakiyi hankali wlh ace da girmanki amma kina abu kamar wata karamar yarinya ni wai makarantar Allan ma anya idan na turaki kina zuwa kuwa ?
turo baki tayi gaba sannan tace ina zuwa mana toh ba'a can na iya karatun sallah ba kuma dai bari in fada miki tsakani da Allah ina zuwa in labe wani lokacin bayan ajin su mairo ta gidan me gari in ta kallonsu ana koya musu karatun arna
haba inna saudi ta rike tace oh ni saude nagamu da ja'irar yarinya wato duk hanaki din danayi wato baki jiba ko saida kika dinga zuwa Allah ya shirye ki
Ameen dan kuwa yanzu ma a shirye nake kamar carbi
kasa magana inna tayi a ranta tana jinjina kiriniya irinta dije tarasa dalili ko dan taga ita kadai ce ohoo haka dai taci gaba da damun furarta ita ko dije ta shiga cikin daki ta kwanta a cewarta saitayi bacci kuma kada a tasheta tana kwanciya ta tuna da abinda yafaru dazu aikuwa ta sheke da dariya wadda saida inna ta taso ta lekata taganta sai dariya takeyi harda rike ciki girgiza kai kawai tayi ta saki labulen dan ita lamarin dije sai addu,a wani lokacin idan tayi abu kamar me aljanu
*Asalin labarin*
Malam muhammadu
dan asalin jigawa ne yanada mata hudu da tarin yara matarsa ta fari nada yara shidda maza ta biyu kuwa yaranta tara bakawai mata biyu maza ta ukun nada yara biyu duk maza sai Amaryarsa dake da yara goma sha daya tara maxa biyu mata Alhmdlh gidan akwai zaman lfy da hadin kai domin ya gina gidansa da zaman lfy dazumunci mariya itace matarsa ta uku itace keda yara biyu inusa da Auwalu duk cikin matan sa tafi hakuri da kawaici hakan yasa yaranta suma sukayi sanyun hali irin nata sam basu da hayanikuma dukansu manoma ne sosai yayin da dukansu sukai aure kuma barakallah dukansu suna nan da rai malam inusa nada mata daya wato saude Allah be azurtasu da haihuwa ba tsawon lokaci sai daga baya suka fara samu amma kuma yaran wabi sukeyi saida tayi haihuwa hudu haka kafin daga baya tasamu cikin dijee cikin hukuncin Allah kuma ita ta rayu khadija ta taso yarinya kyakkyawa fara ce sol irin fararen nan ne sosai sai dai fa batajin magana duk wata tsokana da caskale ta kware akai dan haka yara sa'anninta ke tsoronta inda har suka samata suna bata sani ba wato uwar mazga🤣
a cikin 'ya'yan malam muhammadu dayawa daga cikinsu sun sami cigaban rayuwa inda sukayi karatun boko wasu sun sami aiki a birni wasu kuwa kasuwanci yakaisu kuma cikin ikon Allah ansami daukaka da wadata inda malam muhammadu yake da matansa suke samun kulawa a yanzu haka shine matsayin me gari wanda su habeeb 'ya'ya ne ga dansa babba wato khamis dake aiki a abuja sam basu dade da dawowa daga U.S ba inda suka shafe shekara goma sha biyu a can dan a can sukayi karatun su na secondry har zuwa jami'a indadukan su suka karanci fannin likiktanci shi habeeh ganygoicial shi kuma Naseer consultant ne yanzu haka satinsu biyu da dawowa shine suketa zaga dangi dan suna son kauye basu da kyama sam
*cigaban labari*
uwar mazga nata sharar bacci cikin baccin ma mafarkin su habeeb tayita yi wai har da zawo naseer yayi aikuwa take ta qara rushewa da dariya wadda ta qara jawo hankalin inna ganin da tayi tanata bacci ba ruwanta yasata tashinta dan itafa ta gama gasgata aljanu ne da dije
*****
inna saudi ce ta fito dauke da kwarya cike da fura inda dije dake zaune gefen babanta yana cin tuwo tanata zuba mishi surutu inna saudi tace malam na fito bari inyi sauri inje in dawo inga jikin nasu dije taso muje ki rakani dan dare ne yanzu yafi mu tafi mu biyu
ah ah ni ba inda zani ai munyi fada da baba malam shiyasa jiya da hafsi tace min dijangala tame gari na barar mata da gari ni yanzu nayi yaji saiya zo biko
dariya sukayi dukansu inda malam inusa yace yi tafiyarki kinji kyale wannan uwar rigimar
ai bama saika ce ba ni nayi gaba saina dawo
a dawo lfy innata
Allah yasa
tasa kai ta fice
gyara zamanta tayi tace baba wai ni waye beda lfy ne a gidan me gari ?
yayyenki ne na abuja wai gamo sukayi da aljana a hanyar su ta shigowa gar......ai be qarasa ba yaga ta mike ta suri takalma tana bari inje in raka inna sai na dawo ta zura da gudu tabarsshi da sakin baki kafin daga baya yayi murmushi yace Allah ya shiryamin ke dije ta
****
bata riski inna a hanya ba dan ba hanyar datayi tsammani tabi ba kusan a tare suka isa amma innah sam bata ganta ba ta shige gidan bayan sun gaisa da surikanta ta shiga bangaren mai gari ta gaisheshi tare da su habeeb wadanda suka warware amma kumburin bakin habeeb na nan idan nasir ya kalle shi saiya qara fashewa da dariya iya kuluwa habeeb ya kulu jiyakeyi inda ba aljana bace tayi musu haka ba wlh da mutum ne bema san me zaiyi masa ba a haka inna ta musu sallama tana dada jajanta abin kafin ta miqe tayi musu sallama ta fita
a kofar gida ta riski me gari zaune bisa kujerar sa ta tsoffi ta lababa ta shige gidan indayana kallonta amma ya qyaleta dan yasan halin mutuniyar tunda bataso kulashi ba toh gara ya kyaleta
dakin kakarta ta je ta gaisheta da sauran matan gidan sunata tsokanarta malam yaje biko kenan
lababawa tayi ta dauki kwalli cikin kayan kwalliyar dake cikin wani karamin kwando kafin tace
goggo habi ance anyi baki a gidan nan suna ina ?
suna can sashen malam dan basuji dadi ba kam dan gamo sukayi.
zaro idoo tayi😳gamo fa a ina?
can tsallaken lawoli dan sai dazu jibrin yaje ya dauko motar su ma dan can suka barta
oh Allah ya kiyaye gaba bari naje in gansu
toh maxa kam dan dare yafara yi kizo ki tafi gida in kuma nan kwana to
ah ah niba zan kwana a nan ba
oh dai ke kika sani
sai da ta tsaya lungun bangaren ta zazzana kwalli ta fito aljanar sak👹kafin ta nufi dakin datake jiyo maganar su da alama waya daya yakeyi daga cikinsu
cikin sanda ta qarasa qofar dakin cikin sa'a tana zuwa ana kawo wuta inda haske ya gauraye dakin baki daya kasancewar habeeb ya juya bayane yana shan fura da kyar da dabara sbd bakinsa shi kuma nasir yana waya hankalinsa be kawo inda take ba shiyasa basu ga tsayawaer ta ba
Angaishe ku fitinannun bil adama masu kunnen kashi......
🤣🤣
🤣🤣
*vote*
*comments*
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
NA
khadija usman
*gaskiya naga soyayya yau Alhmdllh naga sakonninku masoya wannan buk din banyi niyyar posting yau ba amma gashi nayi muku kyauta sadaukarwa ga dukkan masoya dijangala ta me gari* 😘
3⃣
wata irin bugawa kirjinsu yayi a tare inda nasir ya bude baki da niyyar yin ihu tace kanamin ihu bakinka zai tsaya a haka har abada gum yayi banda zufa ba abinda ke ketowa ita ko se raba ido takeyi a dole aljana habeeb dake zaune bakinsa fal da fura dan yakasa hadiyewa karasawa tayi cikin dakin yayin da dukansu yau saida sukayi fitsari dariya ce fal cikin dije amma takasa yi ta gintse kallon kwaryar gaban habeeb tayi taganta cike da fura tab wadda duk iya shansu basu isa su shanye ta ba bare ma taga 'yan binni kadan suke cin abinci ko a film in an nuno hmmm tace a zuciyarta ta furta yau zakusha azabatul ula kallon su tayi taga yadda suke makyarkyata tace wato bakwajin magana ko ? ko a cikin bil'adaman naga ku takadirai ne kun takamin yara sunacan sun sami gocewar kashi a tsakiyar kansu amma ku kuna nan kuna shan fura ba ruwanku ko sannan danace kada ku dauki abin hawanku sai gobe shine kuka tura jibirila dan me gari ya dauko ko sbd kun raina izayar jinni toh tunda yarana suna halin jinya yanzu kuma bari in kwantar daku dan mai maganinsu ya fadamin yace sai sunyi shekara dari uku da saba'in kafin su warke abin takaicin ma gasu 'yan biyu ne ko yayesu banyi ba duk jarirai ne basu wuce shekara dari da ashirin ba gashi kunja musu jinya tun suna rarrafe dan haka tunda kuma ku biyu ne yanzu zan yi muku abinda kukayi musu kashin tsakiyar kanku zan malkwadar yadda zakuyi jinya tare
wayyo Allah nadan girman Allah kiyi haquri wlh wlh bamu san da yaranki a gurinba dan ya rasulillahi manzon Allah sallallahu alaihi wasallam dan binta 'yar ma'aikin Allah nanfa suka shiga rokarta duk da dai shi nasiri a iya bincikensa besan da wani kashi a tsakiyar kai ba amma ba mamaki a halittar aljanu akwai shi su kuma ta tsinka musu jijiyar kai yau sun shiga uku shi wlh da yasan haka ne wlh da be zo kauyen nan ba shiyasa mamy bata son su zo a fannin habeeb ma haka kukan zuci yakeyi yayin daya saki baki furar ta zubo dan iya tashin hankali yana ciki a rayuwarsa ba abinda ya ke tsoro irin aljani yau saiga shi garin tukin ganganci irin na naseer yaje ya tsokano musu su kunji fa sharri readers🤣
katse musu tunani tayi ta hanyar ce musu zanyi muku afuwa amma da sharadi
da sauri sukace mun amince wlh ko meye mun yadda mudai ki dena zuwa mana
toh in kun yadda zaku shanye furar nan duka yanzu
😳zaro ido sukayi waje tare da fashewa da kuka musamman nasir da a duniya ba abinda ya tsana irin fura
cikin marairai ce fuska da kuka ya hada hannunsa biyu yace dan girman Allah kiyi hakuri wlh bana shsn fura danasha amai zanyi ke zan iya kwanciya ciwo ma
oh to to tunda baka shan fura bari a sake maka hukunci zan daure cikinka kadaina kashi da fitsari tsawon shekara goma zan kanne maka ido daya zan toshe maka kofar hanci daya da rabin bakinka zan......
ya isa dan Allah kiyi hakuri wlh zan sha kafin tayi wata magana tuni sun fara shan furar inda suka dinga kokawa da ludayi a cewarta basa sha sosai zata kawo musu irin tasu ta aljanu aikuwa suka bada himma sosai inda suketa sha cikinsu ya cika dam gashi furar ko rabi batayi ba dan su a ganinsu ma kamar qarata akeyi bata ankara ba kawai taga sun fashe da kuka a tare abinda yabata dariya kenan wai babba da kuka abinda bata taba gani ba sai a talabijin dan haka batasan lokacin data kama dariya ba su suna kuka ita tana dariya gashi dai furar nan shanta suke
motsi taji alamar za'a shigo gurin ganin sun duka suna kallon fura suna kuka yasata saurin barin gurin ta labe bayan dakin dan wani lungu ta fara dirje bakin fuskarta
da sallama malam ya shigo gurin turus yayi ganin su sai gunjin kuka sukeyi suna shan fura
subahanallah ya fada yana me kiran sunan su jin muryar malam yasasu dagowa suna fadin yauwa malam aljana wlh tana dakin nan sun rude gaba daya yayin da itako tana jin suna aljana ta dira ta katanga tayi dakin kakarta tana fadin ni nayi gida dan nama fasa zuwa gaida bakin saida safe nazo
au da duk kina ina ja'irar yarinya nama aza kinyi gida
toh ban tafi ba sai yanzu nayi niyya ehee
mificin hannunta tajefo mata ta kauce tana dariya ta fice daga gidan
sosai naseer ke amai ya galabaita matuka inda hankalin malam yatashi sosai dan shima habeeb zazzabi ya rufeshi ba shiri malam yasa aka dauko mota aka nufi asibitin cikin gari dasu dan basu taimako dan shi lamarin yana bashi mamaki wai aljana kuma duka su biyu ke ganinta saida aka sa musu drip dukansu aka musu allurai kafin suka yi bacci amma a dan wannan lokacin duk sun rame
********
tunda abin nan yafaru bata qara zuwa gidan malam megari ba dan ita tama manta da wasu baki yau kusan kwana hudu kenan tadai ga innarta na yawan zuwa gidan me gari
yau da wuri ta tashi ta share gidan tsaf duk da shekararta sha hudu yanzu amma tana aiki sosai sai dai in bata so ba yau dinma dan tanason ta bi su sadiya cikin gari dan zasuje gidan yayar sadiyar ne dan haka takevtaya inna aiki dan karta hanata
****
a gajiye suke likis sbd tafiyar kasa da suka sha dan haka tasamu gefen hanya ta zauna tana mayar da numfashi kamar wadda tayi gudu cikin tsananin gajiya ta dubi sadiya tace yaseen bazan iya qarasawa gida a kafa ba wannan ai sai in mutu kafin inkai
to ai laifinki ne dije an bamu darinmu ta ihemu mu hau mahin kika tahi kikace a rabeta kowa ya kahe nahi to gahinan ai sawun mu ya fada mana dan ni wlh ji nakeyi kamar ba a jikina kafafuna suke ba
toh ni uwarku ce da in nace kuyi abu he kunyi a wane dalili toh wlh duk wadda taqaramin harri banyi abu ba tace nayi hena mazgeta hegu kawai
.gum sukayi sun san sauran dan duk wadda tace kala yanzu uwar mazga zata kaddamar musu
kunga ku tahi mu tare me mahin ya kaimu gida
to ina kudin ? cewar shatu
ku zo kuji dabarar dana shirya duk suka hada ka wunansu guri daya kome suka ce oho naga dai sun rushe da dariya sannan suka mike suka fara tarar dan mashin
sun tari mashin yakai goma ba wanda ya tsaya sai daga baya wani saurayi ya tsaya yace ina zaku ne 'yammata?
nan Gawo nawa?
toh ku bada nera sittin tunda ku uku ne
ah ah malam cewar dije uku hamsin in yayi maka
dariya abin yabashi wai uku hamsin dan haka yace to ku hau nan suka dane mashin dukansu sannu har suka iso cikin gawo dai dai gidan me gari inda dan wani tudu yake suka ce masa ya isa ya tsaya yanata zuba musu surutu sukuwa wannan ta kalli wannan ta kalli wannan da haka kuwa sai yaga hafsi da shatu sun kwasa a guje dije ta yunkura yayi caraf ya riketa aikuwa dan da nan kallo yadawo garesu inda yara suka fara taruwa harda 'yan manya manya kan kace me guri ya cika dam tuni lbr ya isko gidan megari yana zaune dasu habeeb dake shirin komawa gida gobe dan Alhmdllh sun sami sauki dan megari yayita amso musu taimako maganin iska kuwa da tsari duk anyi musu shi suna zaune suna tattaunawa akan gidajen da basu je ba yau zuwa gobe zasu je na kusa kusa na nesa kuma sai sun kuma dawowa ana haka aka zo aka fadawa me gari wai ga dije can tayi sata an kamata cikin sauri ya mike duk da jikin tsufa amma kalmar tayi muni sata!!!sata fa toh meta sata ?
ganin yadda maganar ta shigeshi yasa su habeeb tambayar sa wacece dije?
kanwarku ce diyar gurin inusa
ku tashi muje duka suka miki suka bi shi
koda suka iso gurin sun iske dandazon mutane an taru koda akaga me gari kowa ya ratse yabashi hanya ya isa gurin inda yaga dije tsaye me mashin ya rike mata hijabi itako ko a jikinta tanata gwagwiyar goruba
rasa ma me zai ce yayi inda ya qarasa yana fadin malam dan Allah sakarta mana
wlh baba bazan saketa ba sai an biyani kudina
nawa ne kudin naka?
naira hamsin ne
yanzu kai da duk akan nera hamsin katarawa mutane wannan jama'ar
toh ai hakkina ne naga kuma akan sana'ata ne
toh garin yaya kudi ya hadaku?
nan yakwashe komai yafada masa aljihu ya laluba ya ciro nera dari yabashi yace yabar canjin sannan yasaki dije malam yakama hannunta suka nufi cikin gida su habeeb sam basu lura ba dan suna waya ne da mumy sai da suka gama suka juya suka hango bayan me gari rike da hannun wata yarinya ze shiga gida nan suka nufi gidan suma
tsaye ya tadda matansa da sauran ahlin gidan duk tsaitsaiye suna jimamin abin nan yabasu labarin ainihin abinda yafaru kowa ya kalli dije wadda har yanzu bata cewa kowa kanzil ba tanata dai cin goribarta ana haka su naseer suka shigo kasancewar dije ta juya baya nan suka tambayu meya faru nan malam ya shiga sanar dasu cikin zolaya habeeb yace tab ashe kuwa yau sai na bawa budurwar kauye kashi dai dai nan dije ta juyo akayi ko sa'a tasha kwalliyar nan sai dai yau jambaki tasaka kanta kile sabanin baya
wani uban ihu naseer yasaki inda shima habeeb ya karba suka fara fadin gata nan itace suka kwasa da gudu sai dakin inna dudu suka rufo
mamaki ne yakama kowa yayin da dije ta zube a gurin tanata dariya ganin haka malam ya dauka shedananta ne dan haka be bi ta kanta ba ya nufi dakin da suka rufe anyi anyi su bude sunki dije ce ta taso tazo dai dai kofar windo ta leka tace in baku bude kofar nan ba saina kwakule muku idanu da sauri suka taso suka hau kokawar bude kofa tun daga nan malam ya fahimci karatun suna budewa dije ta kara fashewa da dariya zasuyi ihu me gari ya buga musu tsawa yace dama wannan ce aljanar datake tsorata ku?
eh itace wlh itace shi kanshi me garin yaso yin dariya ganin yadda duk jikinsu ke kyarma
to ai itace kanwarku diyar babanku inusa a shakiyancin dije nasan zata aikata fiye da haka
dimmm sukayi gaba dayansu inda suka kai dubansu ga dije wadda ta dallaro harshe tare da yimusu gwalo tace ni ba aljanah bace gyadata kuka takemin ta zube ina shirin in tsince naji fitsari na juya inyi koda na juyo naga kun takemin ita shine nayi maganinku
tunda tafara magana zuciyar mazan tahau lugude musamman. habeeb da yayi asarar hakorinsa guda na kasa saboda abin wayyo Allah
muje zuwa readers yawan comments yawan page
*vote*
*comment*
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
na
khadija usman
6⃣
*wannan shafin sadaukarwa ne ga dukkan member's na khadija fans novels hakika naga ruwan comments da kuma masu bina pc nagode sosai Allah yabar kauna*
ta jima zaune kafin daga baya taji alamun dawowarshi mika mata yayi tare da canjin tace ya rike canjin ta karbi maganin a bakar leda ta shiga cikin gidan
tunani ta shiga yi shin wai ta inama zata fara ne wai wazata fara yiwa illa habeeb,nasir,mamy,ko uwar mugaye yusra ah ah takan ya habeeb zan fara tunda shi yafara min mugunta
mikewa tayi ta shiga kitchen cikin sa'a ta riski basira na zuba coffee cikin cups kallonta tayi tace sannu da aiki Anty na
murmushi basira tayi yayin data kamo hannun ta cike da tausayawar abinda aka mata dazu tace sannu dije kiyi haquri da abinda ke faruwa gidan nan ki dinga taka tsantsan da hajiya dan wlh batada imani suna iya hanaki abincin kwana ukun dasuka ce dan haka kada kidamu zan dinga boye miki a daki da zarar kin tashi ci zan nuna miki inda zan dinga ajiye miki
dariya dije tayi kafin tace kada ki damu Anty ai daga yau har zuwa kwanakin da suka dibar min zanci abinda raina ke so ke dai kawai kisa ido kiyi kallo nice fa dije wlh a kauyenmu anno ba ake cemin duk gidan dana leqa saina sasu jinya dan haka sai sun san nice sukawa haka da naso in canza amma naga basu san kara ba gara ayi gwari gwari
mamaki ne yakama basira inda take kallon dije daketa zaro zance ba wakafi ba aya duk da take qaramar yarinya dan ita a ganinta bazata wuce shekara sha biyar ba amma ta iya tsara zance kamar redio amma kuma in akayi la'akari da dabara irin ta mutanen kauye wannan ba komai bane
farantin data dora kofunan akai ta dauka da niyyar fita dije tace ina zaki kuma Aunty ?
wadan can 'yan sudan din zan kaiwa shayi wai da yamman nan kin san su
ah ah kawo inkai musu ki huta ai kinyi aiki kin gaji naga ma kamar bacci kikeji dan haka jeki kwanta ki dan huta zan qarasa aikin kije ki
toh kadafa kije suyi miki wata muguntar kuma
ah ah ba komai ai haquri zan basu kada ki damu
mika mata tray din tayi ta fita dai dai wani dan corridor ta labe ta fito da ledar daga jikinta ta bude juya maganin tayita yi dan ta rasa na bacci dana kashi kawai shahada tayi ta babbala sachet daya a cikin biyun ta juye cikin daya kofin dayan na hannunta ta fara barewa shima da alama kam wannan shine na baccin tafada a bayanne dan naga shi inna ta siyawa Ahmadu lokacin data daukoshi yaye shima duka guda goma ta juye ta dinga juyawa har duka suka narke kafin ta mike ta boye sauran a wani loko inta dawo ta dauka ta nufi part dinsu
ta dan jima a tsaye kafin daga haya tayi knoking
shigo kawai basira taji ance murda handle din kofar tayi ta kunna kai parlon da sallamar ta habeeb zaune daga shi sai boxer da singlet yana zaune yana duba system dinshi da alama wani aikin yakeyi me muhimmanci duba da yadda yamaida hankalinshi gaha daya ga abinda ke gabanshi
shiko naseer jallabiya ce a jikinshi yana zaune yana danna waya da alama charting yakeyi
naseer ne ya amsa sallamarta inda ya dago idonsa tare da wurga mata harara uban me yakawoki dakin nan ?
um dama itace batajin dadi shine tace in taimaka in kawo muku
tsaki yaja kafin ya maida hankali ga wayarshi
qarasawa tayi ta durkusa ta ajiye cup daya a gabanshi sannan ta nufi gurin habeeb shima ta ajiye masa nashi shi kam ko kallonta beyi ba dan haka ta mike ta nufi hanyar fita
har takai kofa taji muryarsa yana fadin idan naqara ganinki a dakin nan wlh saina lahira yafiki jin dadi shegiya me siffar aljanu nunar rana kawai
itadai bude kofar tayi tay ficewarta inda shi kuma ya jawo coffee dinsa yafara sha jiyayi na yau yafi na kullum dadi dan wani kamshi da dan zaki zaki yayi dan haka ya dinga sirba baji ba gani shima naseer haka yayita sheqe abinshi inda shi kuma beji wani canji ba
hamma yake tayi baji ba gani yayin da yafara ganin uku uku dan haka ya mike ya nufi bedroom yana tangadi kamar dan maye sam yarasa wannan wane irin bacci ne yazo mai lokaci daya
naseer daya bishi da kallo yana ambatar lfy dai bros naganka ka sauya
cikin murya irin ta wanda bacci yakama sosai yace lfy qalau kawai bacci nakeji bari in dan matse duk da naga yamma tayi
ok a tashi lfy
bai bashi amsa ba ya shige ciki kawai shi ko yaci gaba da abinda yakeyi
yana cikin haka kusan minti talatin yaji cikinsa yayi wata irin murdawa da ya dan share amma daga baya yaji bazai iya ba dan kamar ba haya yakeji dan haka ya mike ya shiga toilet din dake falon yana ko shiga yafara antayo abinsa rai fesss
itako dije tana fita kicin ta koma ta tarar da basira harta koma daki freidge ta bude ta fara kwashe lemukan ciki kamar wadda aka sa guda biyu kawai ta bari ta dauko su ta bude tare da zuzzuba wannan maganin kashin aciki kowanne sachet daya daya kana ta mayar ta rufe alamar motsin tafiya taji cikin sauri ta rufe friedge din ta tashi ta nufi cabinet tajawo filet ta kama daurayewa kamar me wanke wanke
mamy ce ta shigo kitchen din tana kiran sunan basira ganin dije a tsaye tana aiki yasata tambayar ina basira ta shiga?
batajin dadi ne shine nake tayata kanta ke ciwo ta sha magani ta kwanta
wani wawan kallo mami ta watsa mata kafin tace hmmm ai dama aikin shiyafi dacewa dake a gidan nan maza ki daukomin lemo a friedge ki kawo mana dinning muna jira zamuci abinci
toh ta amsa ita kuma mamy ta juya ta fita
dariya dije ta fara yi tare da fadin komai kuke so zanyi muku amma ni da lfyr ku zan fanshe
lemukan ta diba ta nufi falon inda ta iske mamy da yusra har sun fara cin abincin ajiye lemon tayi da niyyar juyawa taji yusrah tace
ke aljana me siffar tumatur uban waye zai zuba miki lemon toh
dawowa tayi ta bude ta zubawa kowa ita gwara ma da suka ce ta zuba musu din dan da sun taba murfin da da kansu zasu gane an bude lemo a zuciyarta tana jinjina kalar muguntar da zata yiwa yusrah dan da Alama tata saita fi ta kowa barin gurin tayi da sauri ta nufi dakinsu
inda su hajiya aka baje koma aka dankari abinci da drinks. kasancewar lemon da sanyi kuma na roba ne shiyasa suka kusa shanye su dan kadan suka bari
sun dan jima suna hira kafin mamy taji cikinta ya murda alamar tanajin bayan gida
mikewa tayi ta shiga bedroom dinta ta afka toilet
ita ko yusra ta dan jima kafin itama taji yanayin na hajiyar itama ta mike ta shige dakin inda ta afka toilet tafara zabga nata tutun
*******
shi kam naseer abin ba'a magana domin kuwa ya zuwa yanzu ya tabbatar cikinsa yadan rikice dan haka ya dinga zarya zuwa toilet abun mashi har bashi tsoro yakeyi duba da yadda yaketa zaryar toilet ga muntar sa harya fara zafi
bangaren habeeb kuwa baccinsa yakeyi kamar wani matacce
bangaren su hajiya kuwa abin fa ya ci tura inda suketa zaryar zuwa toilet ganin abin yana neman wuce gona da iri yasata lalubar wayar habeeb dan ya zo yakawo mata magani ta kira yakai sau biyar be daga ba hakan yasa ta kira number naseer shima din shuru domin yana toilet ya na ta zabga abin tana kokarin kara kira yusra ta shigo dafe da cikinta tana dukawa mamy na bude baki da niyyar tambayarta taga ta kwasa da gudu tayi toilet din dakin itama cikinta sake murdawa yayi inda ta tashi da niyyar shiga toilet din taji shi gam a bame koda ta dan yunkura tana rawar disko irin ta wanda kashi inya matsi mutum taji kawai ya zubo mata
ku biyoni
*vote*
*comments*
*khady ce*✍
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
na
khadija usman
5⃣
cikin kwanaki kadan aka gamawa dije komai na makarantar ta arabi da boko kasancewar Alhaji khamis ba mazauni bane yasa dije ke fuskantar rashin jin dadin zama ga dukka mutanen gidan dan su nasir ba qaramar wahala suke bata ba saukinta daya bangaren masu aiki take shiyasa take dan samun rangwame duk tayi sanyi da dana sanin zuwa binni sam inbanda karatu ba abinda tamaida hankali akai
dawowarta kenan daga makaranta ta shiga tayi wanka dan dama bata son kazanta duk shakiyancinta man basira me aiki take shafawa duk da vaseline ne amma bawani duhu datayi koba komai cimar kauye da ta birni akwai banbanci kuma ga A.C dake ratsata daga school har gida dan makaranta me tsada aka sata kasancewar tayi primary daga nan inna tace bazata yadda taci gaba da karatun arna ba shiyasa ta hakura su kuma anan suka sata a J S S 3 bada jimawa ba jasu zana juinior waec kuma alhmdllh tana fahimta sosai ko yanzu data gama shafa mai niyya tayi tadanyi kwalliyarta amma data tuna in tayi anan za'a yi mata dariya hakan yasa tafasa yi tunda bata iya ta 'yan birni ba har yanzu dan kayan kwalliyarta tun na gida ne
fitowarta yayi dai dai da fitowar habeeb wanda ya zuwa yanzu yasa an mayar masa da hakorin roba a inda yasamu gibi baza'a taba ganewa ba tafiya yakeyi yana waya da alama hirar ta soyayya ce duba da yadda yaketa lumshe ido tare da karya murya
fitowa tayi zuwa kitchen dan tadau abincinta sanye take da riga da sicket na atamfa se yawo takeyi cikinsu kusa. dinkin kauye sam bata lura dashi ba har saida takawo kusa dashi kamshin hadadden turarensa na indunusia ya bugi hancinta wuceshi tayi ta shige tadauko abincin ta dai dai tazo fitowa sukayi karo miyar agushi ce da tuwon shinkafa duk ta hada a kwano daya hakan yasa malmalar tuwon tayi kasa yayin da miyar tasauka jikin farar T.Shirt din dake jikinsa ta gangara kasa aikuwa take ya saki wata 'yar qara sakamakon miyar nada dan zafi dan kun san manyan coolers na riqe zafi sosai
dan ja haya tayi kadan a dan tsorace dan sam bata bukatar wani abu ya hadata da wadan nan azzaluman dan haka kawai ma in sun so wahalar da ita sukeyi suyita cewa tayi musu kukan aljanu ko wani abun in takiyi su daketa bare kuma yanzu data tabbatar tayi laifi ai bata gama tunani ba taji saukar tagwayen marin dasai da kanta ya bugu da fredge din dake wurin wata qara tasaki wadda mamy ahigowarta kenan ita da naair da wata budurwa wadda bata santa ba nasir jaye da troly koda suka shigo suka ga meya faru iyakar kuluwa mamy ta kulu yayin da naseer ya fara bala'i yana qara fadin ya tsani yarinyar nan shiko habeeb tunda ya mareta huci kawai yakeyi yayin da yake qara jin tsanar yarinyar har cikin ransa
budurwar dake tsaye ce ta yamutsa fuska tare da fadin mamy pls where did u get dis poolish basterd girl?
hamm yusra she's from Alhaji's village !!amma gaskiya kinyi sake mamy dubi fa da abincin da zata cinye amma dai daddy yaqara yawan abincin gidan ko dan kin san mutanen qauye da ci basu san wani mentaining ba burinsu kawai ciki yadauka musamman tuwo basa masa wasa bare anga farin tuwo
tsaki habeeb yaja kafin yace ai zataci ubanta wlh yau bazata ci abinci a gidan nan ba
nasir ne yayi caraf da cewa iya yau kawai ai wlh sai jibi kafin taci
wlh ni kwana uku ma yakamata tayi dan ubanta intaji wuya dakanta zata koma kauye ai shegiya me siffar 'yan ruwa dariya duka suka sa banda habeeb da ya qara hambareta ya juya ya fice nan suka gama mata tujara kafin suka barta a gurin bayan mamy tasa basira ta kwashe tuwon daya zube ta kuma tabbatar kar abawa dije abincin dare
a gurin suka barta tanata kuka yayin da tayi me isarta data tuna innarta da baffanta can kuwa saita yi shuru ta furta a fili ina dalili zan zauna ana cutar dani yaseen bazan yadda ba gara in koma dijeta ta da dije masifa dije bala,i dije annoba jahannama ga fasinja uwar mazga bari inga wato kai kace yau bazanci abinci ba yau toh wlh kaine bazaka cishi ba har sai gobe kajawa kanka kai kuma uban 'yan mugunta kace bazanci ba har sai jibi toh kaima sai jibin kaci ku kuwa masu cewa sai nan da kwana uku toh kuwa sai lokacin zakuci dukanku dariya tayi ta mike tana taba inda ya mareta ta jinjina kai ta tashi ta shiga dakinta
kudin da daddy yabawata last week yace inta tashi siyen wani abun basaita tambaya ba dan haka ta boye su bata ma siye komai ba su ta je tadauko ta fito zuwa farfajiyar gidan
gurin bala driver ta nufa inda yana ganinta ya shiga washe baki
qarasawa tayi cikin sakin fuska ta duqa har kasa ta gaisheshi ya amsa cike da jin dadi kafi. tace dama aikoni akayi yace toh toh ya akayi?
gashi hajiya tace kasiyo mata maganin kashi
wane irin maganin kashi kuma?
eh wai bakuwar nan ce dasuka zo tare yau kwananta goma batayi kashi ba shine tace a siyo mata wanda zaisa tayi sannan wai da maganin na wanda in an yaye yaro ake bashi dan yayi bacci wai yaye za'a kawo mata yau shine tace a siyo mata shi
toh kaao kudin amma ina su Alhaji karami ai su suke shigo da magani gidan in ana buqata
wai mantawa sukayi shiyasa tace yasiyo sachet goma sha biyu biyu dan a ajiye sbd gaba
toh yafada tare da miqewa ya tafi dan akwai wani pharmacy nan bayan layin
guri tasamu tazauna dan ta jirashi har ya dawo
hhhhhhhh mudai je zuwa
waitng your's comments
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
TA ME GARI
NA
khadija usman
7⃣
wayyo Allah cikina mamy ta fada tare da dukan kofar toilet din cike da maseefa takama fadin wai ke yusra uwar me kikeyi a bandaki har yanzu ko kashin danko ne ai ya ci ace kin gama to waima ina na dakin da kike shine sai kin taho nan
a wahalce yusrah ta bude kofar toilet din kafin daga bisani tasa hannunta ta toshe hancinta kafin tace mamy wlh gudawa nakeyi dazu kam da dan dama dama amma yanzu kamar ruwa nake yinta ni tsoro ma nakeji kar inje ko amai da gudawa zanyi
cikin mamy ne yayi wata qara bata san lokacin data buge yusrah ba ta afka toilet itako yusrah bin wajen da mamy ta tsaya tayi da kallo tare da fadin mamy kema gudawar kk yi ashe?
******
kwance take kan katifa amma tunaninta nacan gurin masu zawon gidan dan haka ta mike ta fita zuwa falon akan idonta yusra ta fito tana tfy a dudduke kuma a botsare ta kuma dafe ciki kallonta dije tayi kafin tace sannu anty
harara ta wurga mata tare da fadin dan uwarki ciwo kikaga inayi da zaki cemin sannu
kuri tayi da ido takama dariya kasa kasa sannan tace ah ah dana ganki haka ne saina ga kinyi kama da masu ciwon zawo amma kiyi haquri tsaki tayi kafin taja qafa ta bar gurin inda dije na ganin ta shige ta kife a gurin tana dariya saida tayi me isarta kafin ta mike ta nufi kitchen tana shiga ta bude drower ta fito da bucket din da ake zuba kaji idan an soya ta zauna zaman dirshin tare da dauko lemo jin alamun ya huce ba sanyi yasata tunawa da ita ta kwashe su dazu ashe tsaki tayi ta mike ta nufi friedge din falo ta dauko exotic me sanyi ta zauna ta fara yagar naman tana shan lemo kuma saida taji kamar cikinta ze fashe kafin ta mike da kyar tana hamdala har tazo fita a kicin din ko me ta tuna kuma oho? sai naga ta juyo ta shiga store ruwa ta dauko carton daya ta nufi friedge dasu duka ta bude ta dura maganin nan a cikin kowacce gorar ruwa kafin ta jera su a friedge dan tasan suna cikin wannan halin bazasu buqaci lemo ba sai dai ruwa saida ta gama shirya su ta miqe tabar kitchen din takoma daki
******
sam yakasa gane meya rikita cikinsa haka lokaci daya dan ya zuwa yanzu yayi bayan gida sau ba adadi dan haka da himma ya qarasa inda wayarsa take ya dauka danya kira docter yusif abokinsa yakawo mishi magani ganin missed calls din mamy yasashi fara kiranta amma bata daga ba yasan bazai wuce zancen aiken datace zatayi masa ba shi kuwa a wannan yanayin dayake ciki ba inda zai iya zuwa dan haka jin bata dauka ba yasa shi kuma be sake kira ba dan haka ya kira doctor yusif yana dagawa yasanar dashi abinda zai kawo masa ya kashe wayar
minti talatin sannan doctor yusif ya iso direct part dinsu ya nufa yana zuwa lokacin naseer yana fitowa kenan daga toilet yana ganinshi ya mika masa hannu pls bani maganin nan kada in mutu dariya yusif yayi kafin yace lallai abin nan yadameka sosai so gashi ko karba yayi kafin yace pls dan bani ruwa a friedge din nan
yana dubawa yace ba ruwa sai lemo
kai pls kaje cikin gida ka daukomin pls
fita yayi yaje kitchen yadauko yana fitowa yaga mamy ta fito ta nufi dakin da yusra take
mamy ina yini?
juyowa tayi ganin yusif a tsaye yasata hamdala tare da fadin lfy qalau ya aiki ?
lfy qalau alhmdllh
abokinka kuwa yana nan dan nakira wayasu duka basu dauka ba
eh yana nan bejin dadi ne wai
subahanallah meke damunsa ?
wlh wai zawo yakeyi yanzu haka wani abun yaci kin sanshi sarkin ciye ciye a waje
sai yanzu tayi tunanin irin cimakar dasuka ta ci kuma duk laifin yusra ne ita tasa sai an siyo gashi nan taja musu shegiya gashi yanzu taja musu rudewar ciki
jin cikinta ya dan juya yasata fadin am kanaji yusif inka shiga wajen nasa ka kawowa yusra maganin itama tasha dan itama cikinta ya dan birkice
ok mamy ya fada tare da juyawa ya nufi hanyar fita
ka danyi sauri dan Allah
insha Allah yanzu zan dawo
be wani jima ba sai gashi yadawo aikuw a da sauri mamy ta nufi kitchen tadauko gorar ruwa tun a can ta bude maganin tasha dasauri ta nufi dakin yusrah ta bata itama tasha
********
toh fa abu kamar wasa gida ya kacame da 'yan zawo abincin da basira tayi ba wanda ya kalleshi se dije da duk abinda su mamy ke ciki ta sani hankalinta kwance ta zage ta dirki abincinta
******
washe gari sai wajen qarfe goma yatashi da kyar ya iya bude idonsa domin nauyin dasukai masa jikinsa yakeji wani iri duk ba kwari haka ya lallaba ya tashi ya shiga toilet dan yayi wanka yayi sallar magrib wanda shi a tunanisa bai jima yana baccin ba
ganin toilet din kaca kaca yasa ranshi ya baci shin wane dan iskan ne yayi haka da wurin yana cikin haka yaji an turo qofar da qarfi koda ya duba naseer ne baiko bi ta kanshi ba ya sabule wando ya fara nishi harda 'yan hawaye domin yazuwa yanzu gudawar ma taki zuwa sai majina toh inama yaci abincin dazai narke yazama kashi tun jiya yake yin abu daya ina yaga lokacin zaman cin abinci gara ma ruwa danshi yana sha sosai maganin da yusuf ya kawo masa kuwa duk ya shanye su amma a banza ga mamy ma ya kirata tace mishi itama hakan take amma tasan be rasa nasaba da ciye ciyen da yusra tasa sukai tayi tsakanin jiya da yau ya tsinewa yusra tare da ja mata Allah ya isa yafi sau nawa
zuba masa ido habeeb yayi ganin yadda yaketa faman nishi harda 'yar kwalla ga uwar zufa dayakeyi kuma inba abin ya girmama ba yasan ba yadda za'ayi naseer ya iya irin wannan lalurar a gabansa dan haka hankalinsa tashe ya nufi gurinsa yana fadin sannu bros meke damunka haka?
nishi yayi kafin yabashi. labarin cimar da sukayi jiya inda ya fada mishi su mamy ma nacan na fama
subahanallahi ai ban sani ba meyasa baku fadamin ba
duk da halin dayake ciki saida ya fella masa harara kafin yace ta ina za'a sanar dakai ka kwanta bacci kamar gawa kasan ko tashi nawa nayi maka amma bakaji ba
ya Allah wlh ni kaina ban san wane irin bacci nayi ba me nauyi haka yanzu haka wlh be isheni ba
kaga malam nidai dan girman Allah taimaka kasamin drip kar ruwan jikina su ida qarewa jini ya biyo baya
toh ai abari dai inyi wanka in rama sallolin da ake bina ko
toh yi maza kayi naseer yafada tare da mikewa yayi tsarki ya fita yana dafa bango
******
hankalin habeeb ba qaramin tashi yayi ba domin kuwa gidan duk na 'yan gudawa ne dole ya kwashe su duka ya nufi hospital dinsu dasu domin dole asa musu drip da sauran allurai wannan kashi sai kace annoba
itako dije komai akeyi akan idonta inda taketa dariya basira ta kalleta tace ke wai lafiyarki kuwa?
wlh qalau nake kawai murna nakeyi ina cikin farin ciki su da sun dauka in ta zama suna dimata kamar jaka ina kallonsu wlh kadanma suka gani daga yanzu duk wanda ya qara yimun wani abu na mugunta saina sa shi rawar nanaye😂
kallonta baseera tayi cike da mamakin maganar ta tace kina nufin kece silar rashin lafiyar 'yan gidan nan?
sosai ma kuwa Aunty ai baki sani ba ma wlh kadan suka gani tunda suka sa nadawo dijeta ta ainihi
kallonta kawai basira takeyi tare da yaba qoqari da muguntar yarinyar dole itama tayi hankali da ita dan kar wataran tasata rawar nanayen itama🤣
miqewa dije tayi ta tafi ta bude friedge ganin babu sauran ruwa ko guda daya yasata qara fashewa da dariya harda kwalla kafin tace sai ni dije uwar mazga ba'a min ba ma nayi bare anyimin
*****
kwanan su mamy biyu a asibiti duk sun rame inda gudawar ta tsaya cikin ikon Allah
yusracan dada ramewa hakora sun bayyana daddy dake zaune gefen gadon da mamy ke kwance yana ta fadan meyasa suka ci abinda sukaci waje wasu basa inganta tsaftar kayansu gashi nan sun jama kansu ai nan yagama me isar shi kafin daga baya ya shiga dawai niyar kula dasu
kwanansu biyu a asibiti ana musu karin ruwa kafin aka sallamosu zuwa gida
koda basira ta gabatar musu da abinci cewa sukayi basa ci kayan fruit kawai suka dinga sha dan sunyi losing Apetti basu jin dadin komai
itako dije rai fesss domin makarantart ake tafiya hankali kwance
yauma shigowarta kenan ta hange su mugaye a zaune cikin garden su uku sanye take cikin unifoam dinta riga da wando da farin hijab qarami
tana shirin shigewa taji muryar naseer na fadin
ke Aljana dan ubanki baki iya gaisuwa bane ?
qarasawa tayi inda suke daya bayan daya ta gaishesu ba wanda ya amsa sai baqon da suke tare dashi
mikewa tayi da niyyar tfy naseer yajawota ya zuba mata rankwashi aka sai da ta danyi kara bata san sanda ta furta kaci bashi a fili ba......
mu kara wuta
ku biyo ni
*vote*
*comment*
*Alqalamin khadiy* ✍
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
TA ME GARI
NA
KHADEEJA USMAN
8⃣
bana karanta littafin kowa a yanzu bayan *FAHIMTA,KUKAN KURCIYA,ZAINABU
Sune littatafan danake karantawa a halin yanzu dan haka ina son ayimin adalci koda anji labarina yayi kama da na wasu littafan da ake rubutawa yanzu dan Allah ina son ayimin adalci domin wlh nawa sakon danake son isarwa daban ko kadan bazan saci fasahar wasu ba zanyi amfani da tawa basirar da Allah yabani sbd da haka ina rokonku daku tayani da Addu'ar Allah yabani ikon faranta muku masoya ta me gari
wannan shafin nakine 'yar uwa rabin jiki fadimatuzzahra'u (mamy)fateema maman fateema (ihsan)ina sonki da kewarki
*************
me kika ce ya fada tare da kara kamo kunnenta ya murda da qarfi
qara tasaki tare da matso kwallar wahala cikin kuka tace
wlh bance komai ba
shegiya aljana aike sunan daya kamata asa miki kenan me siffar 'yan ruwa ya cikata tare da fadin bacema mutane da gani
kamar jira take kuwa ta kwashi jakarta ta zura da gudu tayi cikin gida
doctor yusif ne ya kalle shi tare da fadin wai kai man wane irin mugu ne ?
kawai kasa yarinya a gaba sai wahalar da ita kukeyi sai kace ba qanwarku ba haba dan Allah hakan ba kyau zaisa ta raina ku ai
kallon gefen ido habeeb yayi musu wanda shi tunda aka fara abun ma baice qala ba dan shi duniya babu abinda ya tsana irin yarinyar shiyasa ko zancenta baya son ayi
ganin irin diban dayakeyi masa ne yasashi fadin kai kuma meye ka tsare mutane da idonka irin na aljanun ainihi
hmmm kawai yace tare da maida kansa zuwa abinda yakeyi
naseer ne yace da kasan abinda yarinyar nan tayi mana wlh da kokai inta gaisheka baza ka ko kalleta ba bare ka amsa
toh me tayi muku har haka kuna ganin ta 'yar karama da ita ta yaya har zatay muku wanni abinda zaisa ku takurata haka
umm kai kake mata kallon qarama shegiyar me rai ce da kk ganinta nan ya kwashe komai na zuwansu kauye ya fada masa
yusuf dan dariya har da fadawo daga saman kujerar dayake kai yayi inda duka su biyun suka kulu habeeb tashi kawai yayi yabar gurin ya shige cikin gida shi ko naseer qumewa yayi yai banza da yusuf yanaji yanata mai magana ya kyaleshi dan haka ya mike yayi masa sallama yace ya tafi da harara ya rakashi yana fadin inka tafi kada ka dawo wata dariyar ya kumayi tare da fadin dole ai in dawo bil adama.
*******
tana shiga gidan direct dakin su ta wuce ta wurgar da jakar tare da cire hijabin ta zauna gefen katifa tana sharar kwalla tabbas yaxamar mata wajibi tabar gidan nan don me zata zauna aita cin zalinta kullum sai an sami wanda zaiyi mata wata muguntar indai anga taji dadi toh fa daddy na nan dan shine kawai ke nuna mata tsantsar soyayya da kulawa a cewarsa yaji dadin bashi ita da baba malam yayi sbd bashida diya mace toh itafa iyayenta ita kadai suka haifa yanzu tasan suna can suna kewarta kamar yadda take kewarsu wasu hawayen ne suka qara biyo kuncinta domin tunawa da tayi da yanzu suna can suna fama ita da innah akan rikicinta tana cikin haka baseera ta shigo dakin dauke da flate shake da jellop rice da pure water dan shine ruwansu da hajiya tace su dinga sha yanzu yanzu ma ta hango shigowar dijen ne ta windon kicin shiyasa ta biyota da abincin dan ita dai Allah ya jarabceta da son yarinyar nan ganinta da tayi tana kuka yasata qarasawa kusa da ita tana tambayarta lfy khadija?
fadawa tayi jikinta tare da fadin nagaji Anty gida nake son komawa ina son ganin innata nagaji da zama da muguntar da akeyimin a gidan nan babu gurin wanda nake jin dadi daga gurinki saina gurin daddy in yana gari ni gara nakoma kauye yafimin akan zaman nan din yanzu na tsani birnin bana so
hannu tasa ta share mata hawaye tare da fadin ah ah kadeeja dena kuka mana kin manta ke kika cemin so kikeyi kiyi karatu kizama lawyer ki dinga taimakon mutane da iyayenki ba?ke fa kika cemin so kikeyi innarki da baffanki su dawo birni ki gina musu katon gida innarki ta dena daka baffa yabar zuwa gona kenan kin fasa?haba dijangala ta me gari kin san dai bayan wuya se dadi wata rana se labari duk irin cin zalinki da sukeyi wata rana zasu dena ke da zaki girma ki zama hajiya ga gida ga babbar mota ku biyo layi keda me garinki kinsa shi a gaba eye kuma ma idan kince zaki tafi ni ki barni dawa?ai kafata kafarki domin ni dake yanzu mutu ka raba dan haka bana son in kara jin kin sami damuwa akan mutannan kiyi haquri kinji duk me haquri natare da riba tashi maza kici abincinki kada ya huce
maganganun basira sunyi tasiri a zuciyar dije shiyasa ta dan kwantar da hankalinta amma fa wlh ta quduri aniyar duk wanda yayi mata saita rama bakomai zata haqura ba
abincin taci kafin ta tashi tayi wanka inda basira keta bata labaran ban dariya har ta warware gaba daya
*******
haka rayuwa taci gaba da tafiya yayin da dije keta fuskantar muzgunawa itako tanata musu kalolin mugunta amma har yanzu basu dagota ba duk da ya zuwa yanzu ta qara girma kyanta na fulanin asali yaqara bayyana yayin da makerin budurci na nan na kera dije yayin data hadu da qawaye 'ya'yan masu kudi 'yan gayu duk a gunsu take koyar duk wani abu first class yanzu batada aiki sai karatu koda yaushe tana daki ko kicin tana taya baseera aiki sam dijen yanzu ta canza babu wata hayaniya taxama so cool ba yawan surutu su kansu mutan gidan wuyar haduwa sukeyi kasancewar batada amfani a wajensu yasa basu wani damu da rashin ganinta ba ya zuwa yanzu me gari yazo yakai sau hudu kuma ganinta dayakeyi ta canza yasashi jin dadi da kwanciyar hankalin qara barinta gidan kawun nata
******
a dai dai wannan lokacin ana shirye shiryen auran matasan gidan yayin da naseer zai auri yusrah 'yar qanwar mamy shi kuma habeeb zai auri sajida diyar abokin daddy ce babanta ambasserddor ne sajida yarinya ce fist class maqura ce gurin wayewa tanada ilimi sosai amma bata aiki kusan sa'ar habeeb ce dan da kadan ya girme mata amma kasancewar shi namiji ne me son classic lady kuma dayake batada wani girman jiki shiyasa yaji ya kamu da sonta inda suke zuba soyayya ta bugawa a jarida
yau bikin saura sati uku anata hidimar gyara gidan shiyasa kowa yake busy yusrah kam a gidan mamy take domin mahaifiyarta sun rabu da mahaifinta tun tana qarama maman ta kuma wani auren amma a saudiyya suke zaune da mijin kuma mahaifin yusrah ya hanata 'yarsa gashi kuma matar dayake aure batada kirki hakan yasa yusrah gudowa gidan mamy inda kusan nan ta qarasa girmanta
******
yusrah ce zaune da kawayenta a main parlor suna ta tsara yadda hidimar bikin zai kasance
dije ce ta fito sanye da riga da wando indian design kanta babu dankwali sai yalolon gashinta da bashida cika sai matuqar tsawo datasa band ta kama shi ta kuma tufke jelar tayi gammo da ita tun zuwan daddy wancan lokacin ta karbi kudi a gurinsa ta siyo kayan sawa masu kyau da tsada dan ya fada mata komai take so ta tambayeshi kada taji tsoro shiyasa yanzu batada matsala da duk wasu kayan kyale kyale ga qawarta rufaida Aliyu na sayo masu sosai dan itama yarinyar akwai son daukar wanka kuma babanta yanada kudi sosai gashi tanada yayye maza itace kuma auta shiyasa take fantamawa
kitchen ta nufa domin dauko ruwa dan ya zuwa yanzu ta sauqaqawa kanta shan pure water itama faro take sha kamar kowa na gidan
tana daf da shiga ta ji yusra tace keeeee
da kamar ta share sai kuma taga be dace ba dan tasan da ita take dan haka saita tsaya tare da juyowa ta kura mata idanunta masu kama dana mejin bacci
wata kawar yusra ce wow yusrah ina kuka samu wannan kyakkyawar baturiya zance ko balarabiya ne ma oho
me aikin mu ce
me aiki?
kalisat ta tambaya tare da juya lamarin son kudi irin na iyayen yarinyar wannan a yanzu ai jari ce ko tace kadara amma fa hadari ce ga duk gidan da sukayi gangancin daukarta aiki yanzu a ganinta bazata wuce shekara sha bakwai amma dubi yadda take ina ga takai ashirin kuma yusrah ce ta katse mata tunaninta ta hanyar cewa ke me kike so a kawo miki ?
hmmm ni indomie ma ya isa me dan yaji pls juyawa tayi ga sauran kawayenta tace ku kuma fa dayar tace ita kunun aya take so dayar kuma wai jellop din macaroni d kifi sai drinks ko wanne ita kuwa yusrah cewa tayi farfesun kayan cikin rago take so ta kuma hada mata zobo
murmushi dije tayi kafin tace iya wannan sun isa ko kuna buqatar wasu abubuwan
tsawa yusra ta daka mata tare da fadin kijini da munafukar yarinya ina ruwanki da sun ishemu ko basu ishemu ba ai mun san abinda muke buqata shiyasa muka fada miki iya su din dayalla wuce kibawa mutane wuri kiyi abinda nasaki
Allah ya huci zuciyarki Aunty
ta juya ta shiga kitchen tana shiga kamar abun arziki duk abinda suka lissafa ba abinda bata hada ba kuma harta gama Anty basirra bata shigo ba sai da ta jera komai akan wani qaton tray kafin ta nufi parlon yusrah na ganinta ta qara hade fuska wai ita oga
tsugunnawa tayi tare da fadin gashi anty nagama nan ta shiga ajiye wa kowa abinda ya buqata tana gamawa tayi hanyar fita waje yusrah ta rakata da harara kasancewar an dan fara hada hadar biki mamy sun tafi dubai hado lefe shiyasa gidan shuru
kharleesart ce ta fara dibar indomie din domin taci da zafinta domin kuwa yadda ta ganta a ido ga kamshi tanayi tasan zatayi testing tana sawa a bakinta da sauri ta dawo da ita domin wani tsinnanen yaji ne wa nda yake barazanar dauke harshenta
kallonta yusra tayi dai dai takai spoon din hanta bakinta da dukan kuzarinta da sauri ta fito da ita domin wani dan iskan daci dataji ga shi ba alamun maggi ko wasu kayan dandano a ciki shukrah wadda itama dai dai nan ta bude fillet dinta ta diba takai bakinta wani kafirin tsami daya kashe mata haqora tayi saurin hadiyewa maryam kam tana kai kofin kunun aya taji wani mugun gishiri daya kusa dauke mata fatar harshe
miqewa yusrah tayi ta shiga dandana abincin kowa jin abinda taji da sauri ta furzar cike da bacin rai ta miqe da niyyar fita ta jawo dije ta kime ta son ranta dan yau bata san ma kalar dukan dazatayi mata ba watakil saita sumar da ita a yadda takejin zuciyarta
alamar bude falon taji anyi kuma an mayar an rufe ta cikin labule
cike da masifa ta nufo gun ta yaye labulen wata razananniyar qara tayi sakamakon ganin dije idanunta a wurqile ta wani markwade harshe hannunta rike da wata zabgegiyar bulalar ice ga kuma wuqar da ake sara qashi da ita nufo ta tayi ita kuma ta fara ja baya sauran ma duk miqewa sukayi cike da tsoro kowacce na neman maboya
gidan ubanwa zaku ? dije ta fada da wata malkwadaddiyar murya
jikinsu ne yahau kyarma suka qanqame juna suna shirin yin ihu tace duk wanda yayimin ihu a cikinku saina tsaga bakinsa da wannan wuqar ta daga wuqar hannunta qanqame juna suka qarayi suna kuka barinma yusra data qame guri daya dan ita tsoron me aljanu takeyi sosai
ubanwa yasa kusa godiyarmu aiki saboda bama so ta wahala muka girka muku irin girkinmu kuma kuce bazaku ci ba ke harda tashi da tafiya kice zaki kamota ki daka ko ta nuna yusarah
baki na rawa kamar mejin sanyi tace wa..ll..a...hi ah ah bulalar hannunta ta daga ta zuba mata zatayi ihu tace kul kikamin kuka inba haka ba zan sa 'dana yazo ya yini yana dukanki da bulalar qarfe
kama bakinta tayi ta rike tana mutsu mutsu tsananin azabar bulalar daya shigeta ba'amagana jikinta yasaba da hutu gashi yau an daketa da bulalar aljanu wai a hakan ma danta roba ce inaga ansa mata ta qarfe dan haka ta qara gum da bakinta
meye nufinku musha wahalar girka muku abincin kuce bazaku ci ba ko me?
mu din banza cewar maryam wlh zamu ci yanzun nan zamu
ci ko?
da sauri suka shiga girgiza kai eh eh wlh mu mun isa musaku wahalar banza
toh kuyi maza kowacce taci abinda tasa a dafa mata inba haka ba saina sa aljani duna yaxo yayi muku durar kabaki
toh toh munji zamu ci wlh kuyi haquri bayin Allah
kowacce ci takeyi tana kuka duk harshensu ya amsa ga zufa gashi basa son ko kallon fuskar ta ai dama dagani kasan wannan kyan ba'a banza ba harda hadin aljanu
saida suka cinye komai tass bnda kuka da majina da dallo harshe ba abinda sukeyi sunata budar baki sannan ta miqe tace daga yau ko kallon banza kuka karawa godiyarmu wlh saina ci ubanku kuma naji kun fadawa wani wannan abinda yafaru duk saina biki gidajenku ni kadai nasan mezan muku ku tashi ku fita waje zan tafi inbar godiyata tayi bacci
da gudu suka nufi qofa harshe a waje baki bude kamar irin mayu suna fita suka zube gurin shukrah data sha kunu aya me gishiri amai kawai takeyi itada yusrah suko su kaleesart banda kartawa ba abinda cikinsu keyi alamar y yamutse kenan
suna fita ta rushe da dariya tare da hada kwanukan ta nufi kicin tana fadin shegun banza wlh kadan kuka gani dan na fuskanci saina gyara muku zama tana wanke kwanukan data bata tana dariya a haka harta gama ta fita ta dauki ruwanta ta koma daki har yanzu dai basira bacci takeyi Allah sarki kodan yawan aikin datakeyi ne
sukuwa suna nan zaune duksun baza baki sun baje a gurin banda kuka da kakari da nishi ba abinda sukeyi motar su naseer ta kunno kai
*alqalamin shady*✍
*vote*
*comments*
*with* 08066364077
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
TA ME GARI
NA
KHADIJA USMAN
9⃣
narasa bakin da zan godewa masoya wannan littafin sai dai ince Allahu yabar qauna yaqara bani kwarin gwiwar faranta muku ko yaushe 😘
******
ko gama parkin habeeb beyi ba naseer ya balle murfin motar ya nufi gurin su da sauri yana tambayar lfy meya faru meya sameku naga duk kun shanya baki a iska?
yusra da bakinta ya kacame da daci ne ko bauri ji takeyi bakin duk ya dade itace tayi qarfin halin ce mishi abinci mukaci me yajin bala'i
kallonta yayi duba na rainin hankali kafin yace wannan wane irin rashin sanin ciwon kai ne ta yaya zaku je kuci abunda kuka san zai yi muku illah yanzu dan Allah dube ku kunyi wani zugwi zugwi daku kamar mayunwatan 'yan boko haram dayalla ku tashi ku shiga ciki
kada kai su maryam suka shiga yi tare da fadin ah ah mudai basai mun shiga ba dan Allah dai ka taimaka ka bamu maganin wankin ciki pls
habeeb ne ya qaraso gurin yana tambayar sa lfy ? nan ya sanar dashi wai yaji suka sha fada yayi musu sosai akan illar da yaji keyi kafin yace su shiga ciki kafin yakawo musu magani dan kar yajin da suka sha yayi effected dinsu dan yaga sunsha da yawa shiko naseer fada yayita yiwa yusrah duk yadda yaso su khaleesart su shiga parlor ki sukayi har sai da habeeb yakawo musu maganin suka tafi ita ko yusrah da sanda ta shiga ta wuce dakinta inda ta fada toilet tanata brush kamar zata qarar da kamfanin makilin sai yunkurin amai takeyi dan ji takeyi gaba daya makogoronta kamar ya qone 🤣
******
tun daga wannan rana wani kallon rashin mutunci ko na raini be qara shiga tsakanin dije da yusrah ba har saida mamy ta dawo zuwa lokacin daddy na nan domin shirye shiryen biki kudi sosai dije ta karba gurin daddy dan yin siyayyar nata kayan bikin a cewarta tunda ba'asa da ita a anko ba baruwanta nata zatayi rufaida da husna qawayenta sune suka tafi siyayyar tare kudi sosai suka kashe dan har ciko sukayi mata tare da qara mata wata siyayyar direct shagon wani me yi musu dinki rufaida ta kaisu suka kai kafin suka wuce gida duk sun gaji
suna sauketa suka wuce ita kuma ta nufo gate din gidan ta qaramar kofa ta shiga inda tana shiga ta iske su yusrah da qawayenta tare da naseer sai abokansa da alama suna tattauna harkar bikin ne
ta so ta wuce su amma ganin yadda yusra ke binta da harara yasata yin kwana ta nufi gurin da suke cike da takunta na 'yammatan zamani wadan da inuwar budurcin bata dade da sauka bisa kansu ba riga da siket ne na wani blue din material a jikinta wanda aka yiwa ado da kyalkyali na yellow din flowers dan haka tasa takalmin me matsakaicin tsini tare da siririn mayafinta yello kanta babu dankwali hakan ne ya qara bayyanar da yalwataccen gashin kanta dayasha gyara yanata walqiya da dan murmushi akan fuskarta ta nufo gurin su inda hankalin Amir abokin naseer ke kanta
wow so beautifull bros ya dan daki kafadar naseer do u look what i see?
dagowa naseer yayi domin ganin me Amir ke kodawa haka ganin wadda ke nufo su ne yasashi sakin sirirn tsaki tare da juyawa yaci gaba da maganarsa dasu maryam
duk abinda yayi dije ta lura dan haka ta qara fadada murmushinta ita ko yusrah baqaramin dadi taji ba da yadda naseer din yayi
cikin siririyar muryarta tayi musu sallama da sauri qawayen yusra suka amsa tare da wage baki kamar ze yage dan fara'ar da suketa yimata hakama abokan ango dukansu kamar masu tallar makilin a ranta tace ikon Allah sukuma wadan nan haka Allah ya hallice su babu aji bare aje maganar jansa
cikin salon karya harshe tace barkanku da hutawa Aunti's dina
har rige rigen amsawa sukeyi cikin sakin fuska
ykk qanwar mu ya kuma shirye shiryen biki?
all is fine so ya gajiya da yawace yawace ?
duk alhmdllh
toh fatan dai yayana be barku kunata dibar kura a bakin zannuwa ba
cike da rashin fahimtar maganar ta suka juya suka kalleta
nup kada ku damu bawai ina nufin wani abu bane naga kun zubamin ido kamar zaku hadiyeni ina nufin fatan dai yana cika muku jaka da tsaba ko dan nasan halin yaya naseer badai mammako ba
sai yanzu yadago ido ya dubeta tare da sakar mata harara amma sai yaga ta waske tare da fadin
sannunku abokan ango ykk?
lfy beauty cewar Amir dayafi kowa zakewa
yayi kyau tafada kafin taci gaba fatan dai kuna cikawa 'yammatan jakunkunansu ko dan nasan halin samarin yanzu duk 'yan kamus ne
dariya Amir yayi tare da gyara tsayuwarsa danya qara burgeta yace ah ah qanwarmu ai mu ba irin wadanda kk sani bane mun bude bakin aljihu basu da matsalar komai
hmm au hakane ?
ta tambaya tare da yatsina fuska
sosai ma kuwa ai gasu nan indai ba butulci zasuyi mana ba sun san mun bude bakin aljihu sunata kwasa
hakan yayi kyau abokin ango dan wahalar banza😂ta fada tare da qoqarin barin gurin
yake kawai Ameer yakeyi bakin ma yaki rufuwa dariya ce ko kuma murmushi duk ya rasa tayi itako ta sa kai da nufin barin gurin sai kuma ta dawo ganin yadda yusra ke yi mata wani kallon raini tare da naseer dake harararta
gaban naseer taje ta dan rusuna tare da fadin gani yaya?
ubanwa ya kiraki ?
ubana mana
ta fada tare da qifqifta ido kasan ance babban wa magajin uba kaga ko ai kai ubana ne ko?
rasa me zaice mata yayi sai yusrah datayi qarfin halin fadin ke wai wannan wane irin iskanci ne haka anan kinga sa'anninki ne
miqewa tayi tare da fadin ah ah wlh ko daya daga sa'annin baffana sai yayyena sai kuma wadanda ban sanma a wanne mataki zan ajiye su ba dan nasan da sunyi aure da wuri da ko a haihuwar raquma nice auta cikin 'ya'yansu tana gama fadar haka ta qara gaba tabar kowa shaye da mamakinta
kwafa yusra tayi tana jinjina rashin mutuncin dazata yiwa yarinyar danta lura tashen balaga takeji
******
tun daga wannan lokacin babu wanda ta kuma haduwa dashi kowa yana cikin hidimar biki inda suketa shirye shirye
****
rana bata karya yau saura kwana biyu daurin aure yayin da mutanen qauyen gawo suka iso dije ce ta sama musu masauki danta lura indai ta hajiya mamy ne sai dai su wulaqanta dije tasa ran zuwan innarta amma sai taga ba'a zo da ita ba har kuka sai da tayi nan aka shiga rarrashinta ita da basira suka shiga dawainiya da mutanen inda daga baya ta bar baseera ta tafi dansu rufaida nata jiranta dan suje qunshi tunda batada waya da sauri ta fita ta bar gidan tana zuwa kuwa ta tarar suna jiranta nan suka shiga mota suka tafi sunata mata mita dan rufaida akwai son biki kai kace bikin yayanta za'ayi
anyi musu qunshi ja da baki tare da gyaran jiki barakallah masha Allah sunyi kyau sosai matuqa sai dare suka dawo gidan duk wanda yaga dije a cikin mutanen kauye saida ya yabata masu taya iyayenta murna nayi masu hassada a zuciya nayi
ranar akayi kamun yusrah inda aka gabatar da komai cikin wadata
****
yau ake dinner dan haka kowa yake burin qure wanka
sauri takeyi ta qarasa part din da 'yan garinsu suka sauka dan zasu je gurin makeup da sukayi booking sam bata lura da shi ba hakan yasa ta dan bugeshi kadan
wata irin angaza yayi mata kafin tayi wani yunkuri yakai hannu da niyyar marinta cikin sauri ta kauce
a hasale yafara magana ke wace irin mahaukaciya ce iye dan ubanki bakya ganin gabanki in kina tafiya kamar budurwar qauye au ashe fa banyi kuren harshe ba itace wato ke kin girma ko shine rannan harda yiwa mutane rashin kunya ke ga 'yar birni wai tsaya ma duk wannan saurin da rawar jikin da kikeyi duk na menene?
idan ma na zuwa gun dinner ne wlh kiyi saurin fasawa dan wlh naga qafarki a gurin saina ci ubanki saina babbala ki gurin manyan mata ne wato classic lady ba irinku wadanda ko dadewa da yayeku ba,ayi ba wuce ki bani guri shegiya me siffar aljanu
kalamansa sunyi mata zafi matuka ta so yin kuka amma saita ga meye nata nayin kuka a wanne dalili hmmmmm kawai tace tare da qarawa gaba taje tayi abinda zatayi ta fito tana fita still ta hadu da yusrh daqawayenta suma da alama fita zasuyi dan su shirya tagansu da akwati
yauwa ke zonan dan uwarki
kin kula su tayi tasa kai da niyyar ficewa
wani sauri yusrah tayi tare da fadin ke ina miki magana kina jina nasan duk wannan rawar kan da rawar kafar da kikeyi danki fita bazai wuce dan kije gun dinner bane to wlh kk sake naga kafarki a gurin nan sai kinci kut........dan gurin manyan guys ne da big girls ba cakuri cici irinki indai ba tsintar bottle din da akasha drinks zaki tsinta ba
wucewarta tayi batare data tsaya qara jin me yusran zata ce ba tana fita ta shiga tunanin maganganun su duka biyun wato suna nufin ita batakai wadda zata je bikinsu ba?suna nufin ajinta yayi low dayawa da har zesa takasa taka gurin?juya maganar ta shigayi cikin ranta ta jima tana saqa da warwara kafin daga baya tasami mafita murmushi tai tare da yin kwafa a fili ta furta
big guys
classic lady's
a kafta😜
******
shiri sosai kowanne bangare keyi musamman bangaren amaren dan ko wacce so takeyi taga ta burge ta bada kala cikin taron dan haka kowacce ke babban shiri
dije ce ta shigo gidan direct part din mamy ta nufa dake upstairs tasan su yusra na can na shiryawa a zaune ta same su ana shirin fara yiwa yusrah kwalliya da sallamarta tashiga dakin wasu sun amsa wasu kuwa suna sabgar gabansu da qarasawa tayi inda yusrah ke zaune tanata hura hanci tace sannu Anty
meye kuma ?
ta fada tare da hararart
ba komai dama zuwa nayi in baki haquri akan abubuwan da suka faru a nasan nayi miki laifi kiyi haquri nasan idan bamu samu lokaci yau na rokeki ba nasan bazan samu wata damar ba kuma pls aunty kiyafemin
kada kai yusra ta shiga yi tare da girgiza kafa nasan dai badan Allah kika rokeni ba nasan bazai wuce dan kije gurin dinner dinnan bane kuma wlh bazaki ba kinji na rantse dan haka wuce ki tafi munafuka
lah wlh Aunty bahaka bane ka.....naji ta katseta fice kawai nan duk ba sa'anninki qara matsowa tayih arda fadawa jikinta aunty na zanyi missing dinki sosai finciketa tayi tana fadin zan ciuwarkifa ina wasa dake ne
sim sim ta juya ta fita yayin da wasu daga cikin qawayen yusrah ke mata fadan rashin kyautawar datayi duk tayi banza dasu
tana fita ta saki dariya tare da fadin woa ni dije wato ke kin saki baki in baki haquri kedin banza
waya ta fito da ita ta shiga dannawa ganin akwai password a jiki yasata buga tsaki ta bar gurin direct part din mazan gidan ta nufa duk da tasan zuwa yau ya cika da baki dan tasan dole akwai masu zuwa daga nesa
koda ta isa mamaki tayi dan ba kowa tura qofar tayi a hankali ta shiga 'yar magana ta jiyo daga bedroom taji muryar naseer na fadin ai ni inaga daga yau nayi musu sallama shiyasa gara in kwashe su tun yanzu inkai su can tunda yanzunma dole saina dauki kayan dazansa ba gara inyi me gaba daya ba
habeeb yace gaskiya ka kawo shawara me kyau nima bari nabi sahunka kawai na huta
sadaf sadaf ta dinga yi inda ta hangi wayarsa da wallet ajiye saman center table......
toh ko me dije ke shirin yi ?
na gaji typing akwai wahala inyi ma ba comments😜😜
gara na rage
*vote*
*comments*
*with* 08066364077
daga alqalamin khady✍
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
NA
Khadija usman
1⃣2⃣
ba qaramin farin ciki innah tayi ba da ganin dije ta canza tayi kyau ta wuce ma tunanin yadda take so ta zama ita kanta dijen tayi farin cikin ganin innah inda suka bude shafin hira danma yamma ce zabbi inna tasa aka yankawa dije ta kwashi gara kuwa inda ko da wasa bata sanar da innah zaman da takeyi a binni ba itama innar ganin canzawar dijen yasa tabar tunanin da takeyi a baya na ko dijen na cikin wahala
sai bayan isha'i suka sami zama da iyayenta inda sukaita taba hirar yaushe gamo nan dije ta dubi innah tace
wai ni innah ina ko su hafsy da shatu
ai sunyi aure tun tuni sai dai kam ita hafsy abun ba dadi dan dan yayar delu ne ya aureta kin san ko gurin delu ba dadi take ji ba dan haka koda yaron ya nuna yana so duk da ba yaron kwarai ne ba ta ce dole sai anyi gashi dama yanada wata matar yanzu in kinga hafsy sai kin tausaya mata wlh ga wahalar miji gata kishiya abun ba'a magana wlh gwanin ban tausayi
tsayawa tayi da cin abincin da takeyi kafin tace Allah sarki hafsy wlh na tausaya mata aure a qarancin shekarunta haka ai an cuceta
inna ce ta kalle ta tare da fadin to me kike nufi ? bata isa auren bane ko kuwa?
wlh inna in kikaga irin yadda nake tausayawa wadanda ake yiwa aure da wuri sai kinyi mamaki musamman yanzu da naje nayi rayuwa cikin wayayyun mutane bazaki fahimci ana cutar yaranmu na karkara ba sai kinga yadda in sun tashi haihuwa suke shan wahala yanzu ba da bane amma har yanzu kunki ku gane ni yanzu ma a abuja waye zai kalleni bare ma har yazomin da maganar aure ai gani zaiyi nayi masa qanqanta
inna ce ta riqe haba tana kallon ikon Allah tare da jin kalaman dije wadda ta dage sai zuba sharhi takeyi can ta nisa tace au ke nan ma kina nufin baki isa aure ba kenan?
wlh ban isa ba a birni dai kam musamman 'yan boko gani zasuyi anyi min auren wuri dube ni fa duka nawa nake
um gaskiya na ganki fa gashi nan kirji ba komai
hmm inna kenan to wlh akan 'yammatan abuja ni ko kirgar dangi ban fara ba mutanen da zaki ga nonuwansu kamar jarka ai me qananan halitta ce zaki gansu kamar kaina
ke dije ke dije kiji tsoron Allah to a baro ake tura musu shi ko
hmm ai inna yanzu duk yadda na fasalta miki bazaki yadda ba kawai mubar maganar wace unguwa hafsy take?
tana can alqaleri
insha Allahu gobe ko zanje ai nasan ma gidan yayar delun idan naje sai a rakani
ai bama saikin sha wahala ba a cikin gidan suke
toh Allah yasa ma in gane danni yanzu kananun hanyoyin nan duk na manta su
duk da duhun dake dakin be hana inna wurga mata harara ba tare da fadin ai dayake can a sama kike yawo
wlh kuwa kamar kin sani ga hanyoyi nan kamar filin ball ka kure iya tafiyarka kamar zaka bangon duniya
ganin inta biyewa dije zatai ciwon baki yasata sauya akalar hirar tare da fadin ya zaman naki yake to a gidan kawun naki ince dai babu wata matsala
ai innah in ana batun matsala ma karki dinga kawota gidan nan mutanen kwarai ne sosai zamana dasu kamar ma hadiye juna yanda kika ga talaka da kudi ko ince miki buhari da talaka sosai suke kula dani ke tsakani da Allah bakiga yadda suke kula dani ba nima kuma ina binsu sau da qafa
to Alhmdllh naji dadi sosai ashe zahida ta canza hali wlh kullum da tunaninki nake kwana nake tashi ina tsoron kada kema kidau dabi'ar arna tunda kinje ansaki makarantarsu
inna kenan ke har yanzu baki bar maganar arnan nan ba wai waya fada miki karatun boko na arna ne kawai dan ka je ka koyi ilimi sai a ce maka arne
ai ku tuni kunyi nisa bakwajin kira dan haka ni ya isheni haka kije ke kika sani kiyita yi ba ruwana
amma ai zaki samin albarka dai?
albarka ai kullum sata nakeyi
toh nagode innata
suna tsaka da hirar baffa ya shigo aka shiga yi dashi saida suka raba dare kafin kowa ya kwanta
asuba tagari
*******
tunda safe dije ta karade gari duk gidan data san yakamata ta shiga ta shiga a gidan me gari ta yada zango inda suka kwashi hirar su da mutan gida aka sha drama duk wanda yaga dije sai yayi mamakin ta kasancewar ta canza inba an fada maka ance dije bace da wuya ka ganeta ta zama 'yar gayu komai ya canza bata samu zuwa gidan hafsy a ranar ba sai washe gari
tunda safe ta shirya cikin riga da siket na atamfa kasancewar an fara sanyi yasa ta dora wata babbar rigar sanyi a saman dressing dinta qaramin mayafi ta yafa tare da sa hill dinta baki tare da hand bag data zuba wasu 'yan kayan da zata kaiwa hafsy ta fito ta tarar da inna na gyaran masarar da za'ayi tuwo yau
sannu da aiki innah
yauwa me shigar 'yan duniya yanzu ke duk kin dauki dabi'ar mutanen nan dubi.......bata bari ta qarasa ba ta qarasa jikinta da rungumeta tare da fadin pls inna ya isa tare dakai mata kiss a kumatu tana dariya ta saketa ta nufi hanyar fita saina dawo inna
oh ni saudatu na shiga uku yanzu kuma wannan dabi'ar wace iri ce ita babba dake da cizo a kumatu wato shi cizon ma yanzu an banbanta shi dana binni dana kauye me makon nayi miki magana ki cijeni da haqori saiki turamin baki ki dunguremin kumatu Allah ya shiryamin ke dije
****
dan mashin din daya sauketa ta tsaya bawa kudi yara tuni sun zagaye ta yayin da wasu matan da 'ya'yansu suka kai musu rahoton baquwar baturiyar da akayi yasa suka fara tururuwar leqowa ta katanga
ganin ta nufi gidan ladidi me kosai ne yara suka qara duruwa a qofar gidan da sallama ta shiga gidan inda ta iske bakowa a tsakar gidan qara sallamar tayi kafin taji an amsa daga can ciki
hafsy ce ta fito sanye cikin riga da zani na atamfa duk sun kode iya hannun rigar kadai ya isa ayi maka rafar kasan riga harda tattara🤣
duk ta wani cakude tayi kalar tausayi
ganin bakuwar dake. tsaye ne yasata kafeta da ido gani takeyi kamar tasan fuskar amma zaiyi wuya ma dan tana ganin a talavijin ne dan haka dai ta dan saki rai tace sannu baiwar Allah
itako dije tunda ta ganta tausayinta ya kamata ji takeyi kamar tayi kuka duk nawa suke ita da hafsy yanzu fa suke shekara sha bakwai amma in suka jera kana iya rantsewa ta haifi dije ganinta a haka ya raunana zuciyar dije sosai ganin cewar bata ganeta ba yasata yin murmushi tare da fadin
*dijan gala tame gari ba auren talaka ba talaka noma da sassabe*
hafsy najin dije ta fadi haka ta saki wata dariya tare da farin ciki tayo cikin dije da niyyar ta rungumeta sai kuma ta fasa ta shiga kallonta tana fadin dagaske kece dije?kece kika zama haka ? anya kuwa?
rungumeta dije tayi kafin ta fashe da kuka nice hafsy meyasa kika fasa rungumata ko baki son rabata ne ?
ah ah dije indai kece dijeta dana sani kuma uwar mazga me bani kashi bazan ki rabar jikinki ba illa dai kada in shafa miki datti kin ganki kuwa dije tabbas Allah na sonki ji yadda rayuwa ta sauya miki ni kuwa dubeni duk na tsofe banda bauta da wahala a hannun uwar miji da kuma kishiya da shi mijin kanshi ba abinda nake tsinta dubi yadda kika koma kamar ba'a duniya kike rayuwa ba wlh dije nayi miki murnar tafiyarki binni dama nice nasamu koda kwatan abinda kika samu ne ta karasa maganar tana kuka
dena fadar haka hafsy Allah na sonki bai kuma manta dake ba ba kuma dan na fiki bane nima yasa nazama haka ki yadda da kaddarar ki kizama mai juriya da haquri har ki samu kici jarabawar ki yanzu dai muje dakin ki tukun
dakin ta suka shiga sai kace dakin tsohuwa qaramin gadon qarfe ne shima duk ya tsufa dakin ko kyan gani babu sallaya ta shimfidawa dije a gurin ta zauna inda suka shiga hira sunata nishadi tare da tuna baya
dije na lura da yadda hafsy keta mutsu mutsu dan haka ta tambayeta lfy?
dan marairaicewa tayi tare da fadin wlh dije narasa yadda zanyi ne abincin dazan sama miki naketa tunani yanzu gashi yadda kike din nan da wuya ki iya shan ruwan gidan dan na rijiya ne
kada ki damu hafsy maza samo yaro yasama mana abinda zamu ci
jiki ba kwari ta mike ta fita neman yaro inda bata sha wahalar samu ba kuwa dan sun cika qofar gidan suna jiran baturiya ta fito su qara kallonta
dubu daya dije t bawa yaran tace su siyo taliya sai kayan miya da maggi aikuwa da gudu suka karba sai kace a mota suka tafi sai gashi da wuri sun dawo dari tabasu tace su raba aIkuwa murna ba' a magana
tashi hafsy tayi ta hura wuta sunada ice fitowa tayi sukayi girkin tare har suka gama kuwa cikin mutanen gidan ba wanda ya dawo ranar hafsy ta barge haushin yunwar kwana da kwanaki kuwa dan ta debi girki daman ga mutumin kauye da son taliya kallonta dije ke yi cike da tausayawa kafin ta tambayeta matsalarta duk yanayin zaman da takeyi a gidan da kowa saida ta fada mata aikuwa take dije ta danna wata uwar ashar tsumi ya motsa nan ta shiga zazzaga bala'i kallonta hafsy tayi taga yadda ta rikede lokaci daya ta koma dijengala dinta ta da 'yar takife jahannama ga fasinja uwar suburbuda da mazga sai da tayi me isarta kafin ta nisa tace ina 'yan gidan suka tafi?
shi yana bakin kasuwa ita kuma kihiyar tawa da innarsa sun tafi suna can gidan su abokiyar zaman nawa dan kinsan duk gidan nan tsoron ta sukeyi har hi me gidan hi yasa ma inna ke binta kamar ita ta haifi dan
girgiza kai dije tayi tare da fadin hukuncin ta kanta zai fara kenan?
dafe kirji hafsy tayi tare da fadin na higa uku dije wane hukunci kum?kaddai kicemin har yanzu muguntarki na nan nidai rufamin asiri wlh karsu rama akaina
dayalla rufawa mutane baki kin san ni idan na tashi rama abu to da basira nake amfani an fada miki gaba duka zan afka musu ni nasan me zanyi musu uwar ita kishiyar taki zanci wlh ni ba ruwanaa
ke dije rufawa kanki asiri wlh wannan inta tauheki ko qafarki baza'a gani ba ruhehiya ce hi yasa ma fa ita kanta inna da hi hamidan din ke tsoronta dan mullikekiyar katuwa ce ance aljanu ne suka hura mata iska wai data hararesu
kallonta dije tayi tare da fadin ke hafsy a ina taga aljanin da har zata hararesu ?
ance tun tana qarama
kafin dije tace wani abu suka tsinkayo muryar hamidan na fadin iskancin banza da wofi wace shegiyar ce ta shigomin gida tasan kuma inna da hansai basa nan har aka taramin yara a qofar gidan yana fada ya qaraso dakin
tunda hafsy tajishi jikinta ya kama rawa ta dinga kallon dije tana yarfa hannu ita kuwa dijen ko'a jikinta illah zuge jakarta da tayi ta lalubo siririn farin glass dinta ta manna a fuskarta tare da qara gyara zamanta
yaye dan yalolon labulen dakin yayi tare da fadin nace wace hegiyar ce ta higar min gida bada izini na ba
cikin rawar murya hafsy tace am dama.....da...ma um...daga...kinga barshi in gabatar masa da kaina daga abuja nake ma'ana birnin tarayya nasan kasan sunan garin ina daya daga cikin hukumar farin kaya ta 'yan sanda masu bincike inda muke bi kauyuka muna bincika yadda suke gudanar da zamantakewar aurensu hakika mun kuma samu yadda mukayi tsammani dan gashi nan mun gani a gidanka sbd haka yanzu basai nayi wani bincike ba zan kira waya jami'anmu na 'yan sanda masu sa kaki suzo su tafi dakai mun same ka dai lafuffuka da dama duba da yadda na riski matarka duk da bata cemin komai ba ta rufa maka asiri amma banga alamar kana kula da ita ba ji yadda dakinta yake ji suturar jikinta gashi tun zuwana na aunata naga bata ci tana qoshi koma taci ta koshin bata samun me kyau dan haka zamu tafi dakai can ofishin 'yan sanda mafi kusa kafin gobe a wuce dakai abuja daga nan sai musan abinyi dakai hukuncin daurin rai da rai ko kuma daurin shekara hamsin
tunda tafara maganar hantar cikinsa ta kada jikinsa yafara mazari
*kun san ance shege na kauye sai tsoron 'yan sanda* 😂
gurfanawa yayi a gurin tare da fadin wlh wlh ranki ya dade alqu'arn idan da laifina a ciki in mutu a tsaye
yaseen laifin hansai ne da innah
qara hade rai tayi tace au wato ma kanada wasu matan kenan?
ah ah guda daya ce kuma itama kaddara tasa na aureta ko hafsy?
nidai ban sani ba cewar hafsy da tayi zuru tana kallon dije ikon Allah tare da yabawa da basirar ta
ah ah hafsy duk wanda yaga yanayin zamana da hansai yasan kaddara ta hada auranmu amma wlh bada son rai ba ranki ya dade in kina yiwa Allah kiyi haquri wlh ban san an fara wannan binciken ba
oh wato sbd shi zaka daina kenan
kafin yabata amsa sallamar su inna ta karade gidan tare da sababi ganinsa da hansai tayi a bakin kofar hafsy yasata tahowa gadan gadan kofar dakin tare da fadin munafiki uwar me kuma kakeyi a anan
alama yakeyi mata da hannu yi shuru yana mata nuni da cikin dakin
uwar miye a cikin dakin da kake nunamin mutuwa tayi ko me
inaga dai cewar inna da itama ta nufo dakin gadan gadan suka qaraso ya kauce ya basu guri
koda dije taga hansai duk rashin tsoronta saida ta ji gabanta ya fadi wata narkekiya ce duk da batasa yawan shekaru amma kam akwai kiba
ganin dije da sukayi a hakimce gata 'yar gayu yasasu dan rage sauti tare da kallon hamidan wacece ita kuma wannan din?
hukuma ya fada kamar me rada daga garin su baba buhari take nan ya kwashe duk bayanan da dije tayi masa ya fada musu
cike da rawar jiki harda rusunawasuka gaida dije suma nasu sharhin ta rattabo musu aikuwa nan duk jiki ya hau tsima suka shiga bata haquri ganin duk sun rude yasa tace su fita zatayi waya duk suka miqe suka fita suna makyarkyata hansai ce karshen fita dan da kyar ta mike bayanta dije tabi da kallo a ranta tace jar ubancan wannan duwawun ai sai inyi matakala dasu in zan hau katanga
suna fita ta kalli hafsy tace y kikaga ni
jinjina kai tayi dan ta kasa magana tasan dije ta ballo musu ruwa
magana tafara yi kamar me waya cikin daga murya ok sir,yes sir su ta dinga fadi kafin daga baya ta ce su shigo ta gama
duk sunyi tsiru tsuru a gabanta se raba ido sukeyi
naso naqarasa muku banida carji afuwan
*vote*,
*comments*
*with 08066364077*
*Alqalamin khady* ✍[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
NA
KHADIJA USMAN
1⃣1⃣
*wannan shafin na sadaukar dashi ga dukkan member's na khadeeja fans novels na yaba kwarai da comments dinku dan haka ma nace daga yanzu ku kadai ne zaku sami tame gari*
bayan an dan gama caccashewa ne kowa ya koma gurin zamansa yayin da wadanda suka san yusrah naseer zai aura da suka ga ba itace a gurin dinner din ba sun cika fam da mamaki wasu suka barje haushinsu akan kudinsu suka dinga bazawa naseer liki dan a ganinsu yusrah ce ta shirya rashin mutunci musamman dangin babanta amma dangin mamanta a cike suke danma dayawansu basu san wace ce dije ba
ana haka aka sanar da amarya da ango su yanka cake su habeeb ne suka fa
ra inda yaba amaryarsa itama ta bashi cikin gogewa da kwarewa sannan aka zo kan su dije da nata gogan 😜
shiya fara yankawa ya wawuro tabkeke ya nufi bakinta cike da mugunta ta gane nufinsa dan haka ta shirya tare da bude dukkan bakinta ya tura mata nan take aka dauki tafi raf...raf..raf...sannan itama ta mika hannu da niyyar dauko wanda zata bashi dan mitsitsi ta yanko tare da nufar bakinsa ya so yaki bude bakin amma ganin dayayi ido yayi yawa akansu ga pic anata dauka ga masu video coverage hakan yasa ya dan bude bakin kadan ga mamakinsa sai gani yayi tasa masa a hankali dan gefen bakinsa ne ya baci da cake din be ankara ba yaji takawo bakinta saitin gurin ta ziro harshenta ta lashe tare da dora masa kiss a bakinsa qamewa yayi kamar gunki guri kuwa ya kaure da hayaniya da tafi wasu ko da suka san yusrah zai aura suka shiga rattaba nasu luguden leben shi kanshi naseer din cike yake da tararradi domin yasan yanada tarin 'yan qalu bale daga abokansa zuwa friends dinsa amma yasan ai laifin yusrah ne tunda ita taso dizga shi gara ma da akayi hakan dan ya fita kunya amma fa ba abinda zai hanashi cin uwar yarinyar nan
ansa taken nigeria a gurin wanda shi ke nuna taro ya tashi ko kafin naseer ya ankara ya nemi dije sama ko kasa ya rasa itako wata 'yar loko tasamu ta labe ta ta cire daurin kanta ta lababa ta sirnane zuwa gurin motarsu tana zuwa ta bude ta shige baya sai ganin su rufaida tayi sunata raba idanu kallonsu tayi tare da fadin ku kuma lfy naga kunata muzurai?
hmm ai dole muyi cewar husna ke kin san yadda kirjina ke bugawa kuwa haka kawai kija amana shegen duka ji fa abinda kikayi khadeeja bakiji yadda wasu dangin amaryar ke fadin sai sunci ubanki shiyasa muka silale dan da kin dada bata lokaci wlh guduwa zamuyi
rufaida tace ai gara ke ni ai idona idon naseer shaqeni zaiyi a dau gawata bare kuma yusra
kai dayalla can matsoratan banza ni wlh dana san ma haka zakuyita min da ni kadai zanyi aikina kun san zan iya ina ruwana da duk hukuncin da zasuyi min nasan dai duk wanda yayimin cikinsu wlh sai in hana daukar amaryar ma gaba daya ko inyi abinda zaisa 'yan bikin kowa ya......bata qarasa ba suka ga shigowar motar yusrah a miliyan ko kwakkwaran parkin bata gama yiba ta bude ta fito ta nufi qofar holl din da gudu tuni mutane sun fara fitowa ta kutsa kai ta cikin su inda tana shiga tafara ruwan ashar tare da ball da duk abinda tayi kacibis dashi hange takeyi taga inda zata ga tsinnanun maciya amana amma bata gansu ba riqeta aka shiga yi inda ta dinga ihu da zage zage nan ta shiga sanar da danginta da qawayenta masu ganin laifinta sakon da naseer ya tura mata na karta shirya da wuri wato hakan na nufin yanzu ya tafi da dije gurin professional walimar daya ce an shirya musu wlh saiya san yayi mata haka duk saita ci kut.....🙊su haka aka rirriketa ana mata fada amma tayi banza dasu ta dinga rashin mutuncinta
shiko naseer tuni suka fice da sauran abokan shi kuma su habeeb tuni ya saita shima da tashi amaryar
naseer na kallon zuwan yusrah amma ya qyaleta
kowa yagama fitowa inda kowa ya shiga abin hawansa inda kowa yakama gabansa kusan su dije ne karshen fita dan duk su rufaida a tsorace suke ji sukeyi bazasu iya driven ba inda dije ta cika fam gashi bata iya driven sosai ba shiyasa ganin suna neman bata rai yasata fadin na rantse da Allah cikinku kowacce bashi taci kuma seta biya
ah ah khadeeja rufa mana asiri wlh ba haka bane kada kija mana wani bala'in
to tsayuwar me mukeyi ku wuce mu tafi mana
jiki ba kwari suka ja motar suka nufi gida a hanya dije tace kunga ku wuce dani gidanku kawai mukwana can dan ni gobe ma kauye nayi😃
bikin fa?
wanne biki ai inba so nakeyi a hada da jana'izar gawata ba gara in gudu qauye harsai jarababbun nan sun bar gidan daga baya in dawo dan in suka san gaskiyar abinda yafaru inaga naman jikina zasuyita yanka har sai sunga nakai takarda😋
dariya suka sa tare da fadin ashe khadija tanada tsoro
hmm ai tsoro halak ne haka kawai a taba lfy ta a jawa me sona asara mijin dazan aura duk yaga tabo a jikina me yafi raina?gara in san nayi koba komai tsawon shekara uku danayi banga innata ba zan fanshe
a haka har suka qaraso gidan su rufaida suna shiga sukayi wanka sukayi sallah tare da cin abinci suka kwanta bacci
*****
gida fa ya kacame inda mamy ta kira naseer cikin bacin rai tace tana son ganinshi
bai wani jima ba yazo yana shiga dakinta ya iske yusrah kamar mahaukaciya fuskar nan ta hade da majina da hawaye idanunta duk sun kumbura alamar tasha kuka
cikin ladabi ya gaisheda mamy ko amsawa batayi ba ta shiga tambayarsa dalilin daya sa ya aikata abinda ya aikata
bayani ya shiga yi mata inda nan take yusrah ta karyata tare da fadin wlh qarya ne mamy kinga text din fa dayamin
karba mamy tayi ta karanta tare da fadin ubanwa to ya tura wannan saqon ?
karba yayi ya duba yakaranta yaga number sa ce kuwa
cike da mamaki ya kalli mamy yace na rantse da Allah wlh wlh bani na tura sakon nan ba tabbas number ta ce amma banida masaniya akanshi amma mamy ai itama ta turamin wata cousin sister dinta tace wai dreesing dina beyi ba saina dawo na sake wani
caraf ta amshe da fadin wlh qarya ne ni babu wanda na aika nan aka shiga musu
ganin haka yasa mamy daka musu tsawa tare da fadin kai ban son iskanci
ya akayi ka hadu da dije a gurin to
be boye komai ba ya fadawa mamy
nisawa tayi kafin tace amma wannan anyi shegiyar muguwar yarinya yanzu nagane bakin zaren cikinku akwai wanda yayi mata wani abun tayi maku ramuwar gayya kenan
nan kowa ya shiga fadin abinda yafadawa dije akan zuwa gun dinner din
koda naji yanzu naji batu amma ko wannan uwarta ta haifi fitina da kanta zako tasan tayimin haka wlh saita gane batada wayo nan ta gama fadin duk abinda zata fada suma kowannensu a zuciyarsa ya gama kiyasta hukunci. dazai yima dije niko nace to ayi dai mu gani in tusa zata hura wuta🙊
*******
washe garin ranar asabar aka daura auren habeeb khamis da sajida A lawan tare da na yusrah Abubakar da angonta naseer khamis duk akan sadaki dubu dari dari inda dinbin jama'a suka shaida duk dangin kauye maza sunzo harda ko mahaifin dije da megari
ansha yinin biki inda karfe takwas aka dauki amare zuwa gidajensu dake wuse zone 2 gidan yayi matukar kyau tare suka gina shi gate daya ne amma kowacce part dinta daban babu kuma abinda aka banbanta wajen ginin konai iri dayane
har aka gama shagalin biki ba wanda yaga idon dije duk masu son ganinta kuwa sai washe garin ranar ta dira a gidan koda ta iso 'yan garinsu nata shirye shiryen komawa kauye dan haka itama ta hada kayanta suna can falon baki ta iske su bakaramin dadin ganin mahaifinta tayi ba inda shima yaji dadin ganin tilon 'yar tasa ganin yadda ta canza tayi kyau ga kuma nutsuwa
shima a bangaren me gari dadin yaji inda ya shiga sa musu albarka
koda tace zata bisu bawanda yayi hanzarin hanata dan ta yi kokari dan haka koda aka tashi tafiya da ita aka shiga mota sai bayan ta shiga ne mami ta ganta inda ta ciji yatsa takira daddy akan meyasa za'a tafi da dije yace zata ganin gida ne duk yadda taso ya hana bata samu shiga ba a ranta tace zaki daw ki sameni
su dije an dau hanya yayin da zumudi da farin cikin dokin ganin innarta yasa take gani. kamar motar bata gudu tayi bacci ta tashi yafi sau nawa kafin a isa sai kusan yamma suka iso gida zo kuga murna gurin dije
*WELCOME BACK TO VILLAGE DIJE*
*vote*
*comments*
*with 08066364077*
insha Allah indai nasami lokaci zaku jini zuwa dare
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
NA
Khadija usman
1⃣2⃣
ba qaramin farin ciki innah tayi ba da ganin dije ta canza tayi kyau ta wuce ma tunanin yadda take so ta zama ita kanta dijen tayi farin cikin ganin innah inda suka bude shafin hira danma yamma ce zabbi inna tasa aka yankawa dije ta kwashi gara kuwa inda ko da wasa bata sanar da innah zaman da takeyi a binni ba itama innar ganin canzawar dijen yasa tabar tunanin da takeyi a baya na ko dijen na cikin wahala
sai bayan isha'i suka sami zama da iyayenta inda sukaita taba hirar yaushe gamo nan dije ta dubi innah tace
wai ni innah ina ko su hafsy da shatu
ai sunyi aure tun tuni sai dai kam ita hafsy abun ba dadi dan dan yayar delu ne ya aureta kin san ko gurin delu ba dadi take ji ba dan haka koda yaron ya nuna yana so duk da ba yaron kwarai ne ba ta ce dole sai anyi gashi dama yanada wata matar yanzu in kinga hafsy sai kin tausaya mata wlh ga wahalar miji gata kishiya abun ba'a magana wlh gwanin ban tausayi
tsayawa tayi da cin abincin da takeyi kafin tace Allah sarki hafsy wlh na tausaya mata aure a qarancin shekarunta haka ai an cuceta
inna ce ta kalle ta tare da fadin to me kike nufi ? bata isa auren bane ko kuwa?
wlh inna in kikaga irin yadda nake tausayawa wadanda ake yiwa aure da wuri sai kinyi mamaki musamman yanzu da naje nayi rayuwa cikin wayayyun mutane bazaki fahimci ana cutar yaranmu na karkara ba sai kinga yadda in sun tashi haihuwa suke shan wahala yanzu ba da bane amma har yanzu kunki ku gane ni yanzu ma a abuja waye zai kalleni bare ma har yazomin da maganar aure ai gani zaiyi nayi masa qanqanta
inna ce ta riqe haba tana kallon ikon Allah tare da jin kalaman dije wadda ta dage sai zuba sharhi takeyi can ta nisa tace au ke nan ma kina nufin baki isa aure ba kenan?
wlh ban isa ba a birni dai kam musamman 'yan boko gani zasuyi anyi min auren wuri dube ni fa duka nawa nake
um gaskiya na ganki fa gashi nan kirji ba komai
hmm inna kenan to wlh akan 'yammatan abuja ni ko kirgar dangi ban fara ba mutanen da zaki ga nonuwansu kamar jarka ai me qananan halitta ce zaki gansu kamar kaina
ke dije ke dije kiji tsoron Allah to a baro ake tura musu shi ko
hmm ai inna yanzu duk yadda na fasalta miki bazaki yadda ba kawai mubar maganar wace unguwa hafsy take?
tana can alqaleri
insha Allahu gobe ko zanje ai nasan ma gidan yayar delun idan naje sai a rakani
ai bama saikin sha wahala ba a cikin gidan suke
toh Allah yasa ma in gane danni yanzu kananun hanyoyin nan duk na manta su
duk da duhun dake dakin be hana inna wurga mata harara ba tare da fadin ai dayake can a sama kike yawo
wlh kuwa kamar kin sani ga hanyoyi nan kamar filin ball ka kure iya tafiyarka kamar zaka bangon duniya
ganin inta biyewa dije zatai ciwon baki yasata sauya akalar hirar tare da fadin ya zaman naki yake to a gidan kawun naki ince dai babu wata matsala
ai innah in ana batun matsala ma karki dinga kawota gidan nan mutanen kwarai ne sosai zamana dasu kamar ma hadiye juna yanda kika ga talaka da kudi ko ince miki buhari da talaka sosai suke kula dani ke tsakani da Allah bakiga yadda suke kula dani ba nima kuma ina binsu sau da qafa
to Alhmdllh naji dadi sosai ashe zahida ta canza hali wlh kullum da tunaninki nake kwana nake tashi ina tsoron kada kema kidau dabi'ar arna tunda kinje ansaki makarantarsu
inna kenan ke har yanzu baki bar maganar arnan nan ba wai waya fada miki karatun boko na arna ne kawai dan ka je ka koyi ilimi sai a ce maka arne
ai ku tuni kunyi nisa bakwajin kira dan haka ni ya isheni haka kije ke kika sani kiyita yi ba ruwana
amma ai zaki samin albarka dai?
albarka ai kullum sata nakeyi
toh nagode innata
suna tsaka da hirar baffa ya shigo aka shiga yi dashi saida suka raba dare kafin kowa ya kwanta
asuba tagari
*******
tunda safe dije ta karade gari duk gidan data san yakamata ta shiga ta shiga a gidan me gari ta yada zango inda suka kwashi hirar su da mutan gida aka sha drama duk wanda yaga dije sai yayi mamakin ta kasancewar ta canza inba an fada maka ance dije bace da wuya ka ganeta ta zama 'yar gayu komai ya canza bata samu zuwa gidan hafsy a ranar ba sai washe gari
tunda safe ta shirya cikin riga da siket na atamfa kasancewar an fara sanyi yasa ta dora wata babbar rigar sanyi a saman dressing dinta qaramin mayafi ta yafa tare da sa hill dinta baki tare da hand bag data zuba wasu 'yan kayan da zata kaiwa hafsy ta fito ta tarar da inna na gyaran masarar da za'ayi tuwo yau
sannu da aiki innah
yauwa me shigar 'yan duniya yanzu ke duk kin dauki dabi'ar mutanen nan dubi.......bata bari ta qarasa ba ta qarasa jikinta da rungumeta tare da fadin pls inna ya isa tare dakai mata kiss a kumatu tana dariya ta saketa ta nufi hanyar fita saina dawo inna
oh ni saudatu na shiga uku yanzu kuma wannan dabi'ar wace iri ce ita babba dake da cizo a kumatu wato shi cizon ma yanzu an banbanta shi dana binni dana kauye me makon nayi miki magana ki cijeni da haqori saiki turamin baki ki dunguremin kumatu Allah ya shiryamin ke dije
****
dan mashin din daya sauketa ta tsaya bawa kudi yara tuni sun zagaye ta yayin da wasu matan da 'ya'yansu suka kai musu rahoton baquwar baturiyar da akayi yasa suka fara tururuwar leqowa ta katanga
ganin ta nufi gidan ladidi me kosai ne yara suka qara duruwa a qofar gidan da sallama ta shiga gidan inda ta iske bakowa a tsakar gidan qara sallamar tayi kafin taji an amsa daga can ciki
hafsy ce ta fito sanye cikin riga da zani na atamfa duk sun kode iya hannun rigar kadai ya isa ayi maka rafar kasan riga harda tattara🤣
duk ta wani cakude tayi kalar tausayi
ganin bakuwar dake. tsaye ne yasata kafeta da ido gani takeyi kamar tasan fuskar amma zaiyi wuya ma dan tana ganin a talavijin ne dan haka dai ta dan saki rai tace sannu baiwar Allah
itako dije tunda ta ganta tausayinta ya kamata ji takeyi kamar tayi kuka duk nawa suke ita da hafsy yanzu fa suke shekara sha bakwai amma in suka jera kana iya rantsewa ta haifi dije ganinta a haka ya raunana zuciyar dije sosai ganin cewar bata ganeta ba yasata yin murmushi tare da fadin
*dijan gala tame gari ba auren talaka ba talaka noma da sassabe*
hafsy najin dije ta fadi haka ta saki wata dariya tare da farin ciki tayo cikin dije da niyyar ta rungumeta sai kuma ta fasa ta shiga kallonta tana fadin dagaske kece dije?kece kika zama haka ? anya kuwa?
rungumeta dije tayi kafin ta fashe da kuka nice hafsy meyasa kika fasa rungumata ko baki son rabata ne ?
ah ah dije indai kece dijeta dana sani kuma uwar mazga me bani kashi bazan ki rabar jikinki ba illa dai kada in shafa miki datti kin ganki kuwa dije tabbas Allah na sonki ji yadda rayuwa ta sauya miki ni kuwa dubeni duk na tsofe banda bauta da wahala a hannun uwar miji da kuma kishiya da shi mijin kanshi ba abinda nake tsinta dubi yadda kika koma kamar ba'a duniya kike rayuwa ba wlh dije nayi miki murnar tafiyarki binni dama nice nasamu koda kwatan abinda kika samu ne ta karasa maganar tana kuka
dena fadar haka hafsy Allah na sonki bai kuma manta dake ba ba kuma dan na fiki bane nima yasa nazama haka ki yadda da kaddarar ki kizama mai juriya da haquri har ki samu kici jarabawar ki yanzu dai muje dakin ki tukun
dakin ta suka shiga sai kace dakin tsohuwa qaramin gadon qarfe ne shima duk ya tsufa dakin ko kyan gani babu sallaya ta shimfidawa dije a gurin ta zauna inda suka shiga hira sunata nishadi tare da tuna baya
dije na lura da yadda hafsy keta mutsu mutsu dan haka ta tambayeta lfy?
dan marairaicewa tayi tare da fadin wlh dije narasa yadda zanyi ne abincin dazan sama miki naketa tunani yanzu gashi yadda kike din nan da wuya ki iya shan ruwan gidan dan na rijiya ne
kada ki damu hafsy maza samo yaro yasama mana abinda zamu ci
jiki ba kwari ta mike ta fita neman yaro inda bata sha wahalar samu ba kuwa dan sun cika qofar gidan suna jiran baturiya ta fito su qara kallonta
dubu daya dije t bawa yaran tace su siyo taliya sai kayan miya da maggi aikuwa da gudu suka karba sai kace a mota suka tafi sai gashi da wuri sun dawo dari tabasu tace su raba aIkuwa murna ba' a magana
tashi hafsy tayi ta hura wuta sunada ice fitowa tayi sukayi girkin tare har suka gama kuwa cikin mutanen gidan ba wanda ya dawo ranar hafsy ta barge haushin yunwar kwana da kwanaki kuwa dan ta debi girki daman ga mutumin kauye da son taliya kallonta dije ke yi cike da tausayawa kafin ta tambayeta matsalarta duk yanayin zaman da takeyi a gidan da kowa saida ta fada mata aikuwa take dije ta danna wata uwar ashar tsumi ya motsa nan ta shiga zazzaga bala'i kallonta hafsy tayi taga yadda ta rikede lokaci daya ta koma dijengala dinta ta da 'yar takife jahannama ga fasinja uwar suburbuda da mazga sai da tayi me isarta kafin ta nisa tace ina 'yan gidan suka tafi?
shi yana bakin kasuwa ita kuma kihiyar tawa da innarsa sun tafi suna can gidan su abokiyar zaman nawa dan kinsan duk gidan nan tsoron ta sukeyi har hi me gidan hi yasa ma inna ke binta kamar ita ta haifi dan
girgiza kai dije tayi tare da fadin hukuncin ta kanta zai fara kenan?
dafe kirji hafsy tayi tare da fadin na higa uku dije wane hukunci kum?kaddai kicemin har yanzu muguntarki na nan nidai rufamin asiri wlh karsu rama akaina
dayalla rufawa mutane baki kin san ni idan na tashi rama abu to da basira nake amfani an fada miki gaba duka zan afka musu ni nasan me zanyi musu uwar ita kishiyar taki zanci wlh ni ba ruwanaa
ke dije rufawa kanki asiri wlh wannan inta tauheki ko qafarki baza'a gani ba ruhehiya ce hi yasa ma fa ita kanta inna da hi hamidan din ke tsoronta dan mullikekiyar katuwa ce ance aljanu ne suka hura mata iska wai data hararesu
kallonta dije tayi tare da fadin ke hafsy a ina taga aljanin da har zata hararesu ?
ance tun tana qarama
kafin dije tace wani abu suka tsinkayo muryar hamidan na fadin iskancin banza da wofi wace shegiyar ce ta shigomin gida tasan kuma inna da hansai basa nan har aka taramin yara a qofar gidan yana fada ya qaraso dakin
tunda hafsy tajishi jikinta ya kama rawa ta dinga kallon dije tana yarfa hannu ita kuwa dijen ko'a jikinta illah zuge jakarta da tayi ta lalubo siririn farin glass dinta ta manna a fuskarta tare da qara gyara zamanta
yaye dan yalolon labulen dakin yayi tare da fadin nace wace hegiyar ce ta higar min gida bada izini na ba
cikin rawar murya hafsy tace am dama.....da...ma um...daga...kinga barshi in gabatar masa da kaina daga abuja nake ma'ana birnin tarayya nasan kasan sunan garin ina daya daga cikin hukumar farin kaya ta 'yan sanda masu bincike inda muke bi kauyuka muna bincika yadda suke gudanar da zamantakewar aurensu hakika mun kuma samu yadda mukayi tsammani dan gashi nan mun gani a gidanka sbd haka yanzu basai nayi wani bincike ba zan kira waya jami'anmu na 'yan sanda masu sa kaki suzo su tafi dakai mun same ka dai lafuffuka da dama duba da yadda na riski matarka duk da bata cemin komai ba ta rufa maka asiri amma banga alamar kana kula da ita ba ji yadda dakinta yake ji suturar jikinta gashi tun zuwana na aunata naga bata ci tana qoshi koma taci ta koshin bata samun me kyau dan haka zamu tafi dakai can ofishin 'yan sanda mafi kusa kafin gobe a wuce dakai abuja daga nan sai musan abinyi dakai hukuncin daurin rai da rai ko kuma daurin shekara hamsin
tunda tafara maganar hantar cikinsa ta kada jikinsa yafara mazari
*kun san ance shege na kauye sai tsoron 'yan sanda* 😂
gurfanawa yayi a gurin tare da fadin wlh wlh ranki ya dade alqu'arn idan da laifina a ciki in mutu a tsaye
yaseen laifin hansai ne da innah
qara hade rai tayi tace au wato ma kanada wasu matan kenan?
ah ah guda daya ce kuma itama kaddara tasa na aureta ko hafsy?
nidai ban sani ba cewar hafsy da tayi zuru tana kallon dije ikon Allah tare da yabawa da basirar ta
ah ah hafsy duk wanda yaga yanayin zamana da hansai yasan kaddara ta hada auranmu amma wlh bada son rai ba ranki ya dade in kina yiwa Allah kiyi haquri wlh ban san an fara wannan binciken ba
oh wato sbd shi zaka daina kenan
kafin yabata amsa sallamar su inna ta karade gidan tare da sababi ganinsa da hansai tayi a bakin kofar hafsy yasata tahowa gadan gadan kofar dakin tare da fadin munafiki uwar me kuma kakeyi a anan
alama yakeyi mata da hannu yi shuru yana mata nuni da cikin dakin
uwar miye a cikin dakin da kake nunamin mutuwa tayi ko me
inaga dai cewar inna da itama ta nufo dakin gadan gadan suka qaraso ya kauce ya basu guri
koda dije taga hansai duk rashin tsoronta saida ta ji gabanta ya fadi wata narkekiya ce duk da batasa yawan shekaru amma kam akwai kiba
ganin dije da sukayi a hakimce gata 'yar gayu yasasu dan rage sauti tare da kallon hamidan wacece ita kuma wannan din?
hukuma ya fada kamar me rada daga garin su baba buhari take nan ya kwashe duk bayanan da dije tayi masa ya fada musu
cike da rawar jiki harda rusunawasuka gaida dije suma nasu sharhin ta rattabo musu aikuwa nan duk jiki ya hau tsima suka shiga bata haquri ganin duk sun rude yasa tace su fita zatayi waya duk suka miqe suka fita suna makyarkyata hansai ce karshen fita dan da kyar ta mike bayanta dije tabi da kallo a ranta tace jar ubancan wannan duwawun ai sai inyi matakala dasu in zan hau katanga
suna fita ta kalli hafsy tace y kikaga ni
jinjina kai tayi dan ta kasa magana tasan dije ta ballo musu ruwa
magana tafara yi kamar me waya cikin daga murya ok sir,yes sir su ta dinga fadi kafin daga baya ta ce su shigo ta gama
duk sunyi tsiru tsuru a gabanta se raba ido sukeyi
naso naqarasa muku banida carji afuwan
*vote*,
*comments*
*with 08066364077*
*Alqalamin khady* ✍
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
NA
khadija usman
1⃣3⃣
*rawa da girgiza zanyi gabanku in jujjuya💃💃💃 zanyi muku albishir comments dinku na burgeni💃💃💃*
*gaskiya naga soyayya a zahiri da badini jinjina gareku masoyana nasan soyayyar tame gari ce ta shafeni ina matuqar godiya gareku Allah yabar qauna*
*sadnaf ina tayaki murnar samun lfy Allah ya qaremu da lfy da duk musulmin Allah baki daya,Aunty safiyya huguma kema ina miki fatan samun lfy me dorewa Allah yasa anyi aikin a sa'a*
****
kallonsu dije tayi taga yadda jikinsu ke makyarkyata ita abunma sai ya bata dariya dole saida ta dan murmusa kafin ta maida kallon ta garesu tace na kira waya azo a tafi daku sbd haka ku tashi mu tafi dan bana son jira
magiya suka shiga yi kuka wi wi dan inna mairo harda fyace majina suna wlh ba laifinta bane hansai ce shima din hamidan duk akan hansai suka dora laifin ganin da tayu duk suna son zamewa su barta ciki yasata sakin kuka tare da fadin munafiki wlh qarya ne duk da laifinsu suma kuma ni yauhe ma nasa ku quntatawa 'yar mutane bakai ka gani ka auro ta ba ko nice inna da dole innace kayi abu se kayi ?
ah ah hansai kiji tsoron Allah ki fadi gaskiya wlh 'yan sanda basuda imani ko kadan kikkilemu zasuyi ko digon jininmu baza'a samu ba sbd haka ki karbi laifinki kawai a tafi dake ni a barni da dana se 'yata hafsy ta qarasa maganar tana miqa hannu da dafa kan hafsy data maqure guri guda tana kallon ikon Allah
kunga duk nagaji da surutu sbd haka kutashi mu tafi kawai ta fada tana me qoqarin mikewa
hansai ce ta miqe da kyar ta kalli dije kafin ta kaikaice ta ce ke dayalla gafara can dan kinga ma ana lallabaki wlh dukanku ina iya hadawa inci uwarku ba inda zani hukumar hegiya dan haka kin dade baki ce su shigo din su tafi dani ba
ganin yadda taketa bala'i da kumfar baki yasa fa zuciyar dije bugawa daram dararam dam dan ita kanta tasan idan ta bari wannan me kama sa jinsin ordisay din ta damketa to fa wlh saita ci kut......🙊
gara ta lallaba ta zame dan taga alamar wannan kaddarar hafsy ce koba kamai ta tayata da addu'a kawai 🤣
ganin da hansai tayi kamar dije ta tsorata da ita yasata qara sakin sababi duk da itama qarfin halin ne dan wlh da za'a tsaga kirjinta tsab zuciyarta zata fado ta fito
kallon tsaf dije tayi mata ta lura da sababin da takeyi na iya baki ne a ranta tace kin gama yawo yarinya amma a fili saita ce
keeeeeee!!!!!
shutup your magout maout ina magana kinayi kin san wacece hukuma kuwa ?kinyi lafuffuka da dama kuma masu girma ciki harda na zagin hukuma dan haka dole ki karbi hukuncinki tare da masu mara miki baya dan haka kuna batamin lokaci pls ku wuce muje
hamidan ne yace yanzu dai ranki ya dade laifin waye ya shafeni ni?
oho dai koma laifin waye ai kai ka sani ni ba ruwana danme zaka auro yarinya ka maidata baiwa suma iyayenta saina sa an tafi dasu tunda basu kula da yarinyarsu suka dauka duka bata
kinga ranki ya dade wlh wlh laifin duk na hansai ne ko inna?
eh wlh itace da anyi abu saita ce zata zane mutum kota zaune shi sbd haka muke yi mata biyayya duba da yanayin hallitar da Allah yayi mata
oh yanzu nagano bakin zaren kana namiji matarka kw juyaka kenan to waye mijin cikinku?
nine wlh amma a suna
toh yanzu ka zabi daya shin zaka barta matsayin mijin ko kuma zaka dawo mikin in yaso a dai daita?
wlh zan koma cikakken namiji ma
toh masha Allah wane mataki zaka dauka yanzu?
sakinta zanyi dama ta isheni wlh
nisawa tayi taga dai ba kyau raba sunnar ma'aiki kuma ta lura da yadda hansai jikinta yayi sanyi daga jin an ambaci kalmar saki saita bata tausayi tace to yanzu zanyi muku wani adalci guda daya zan rufa muku asiri kowa yazauna muyi magana zama sukayi duka inda su kansu suke mamakin yadda suke bin maganar yarinyar kodan fa hukuma ba sauki
ganin su nutsu yasata zame gilashin idonta abin mamaki ji nayi su dije an afka wa'azi gadan gadan ta shiga yi musu nasiha da taushin murya
Allah kenan duk cikinsu nutsuwa sukayi sunaji inda duk jikinsu yayi sanyi saida ta gama kafin tabi kowa tanaa fada masa laifinsa tare da sanar dasu inta kaisu abuja irin hukuncin da za'a musu amma yanzu in sunji nasiha zata san yadda zatayi a kyalesu amma fa daga wannan lokacin zasu yawaita kawo ziyara qauyen kuma kowannw lokaci suna iya zuwa
da sauri suka amsa sun yadda inda daga baya dije tace ta sallamesu su tashi su fita wai zata yiwa hafsy gwajin cutar caskalaxation 🤣
duk suka miqe suka fita jiki ba kwari
sun jima da hafsy tana yimata nasiha akan rayuwa kafin ta bata abinda tazo mata dashi tace zata tafi amma kafin ta koma abuja zata dawo sai dai kada ta bari su rainata itama kuma kada ta raina kowanne cikinsu a haka sukayi sallama hafsy harda kuka tanama dije godiya
sai yamma ta dawo gida babu wanda ta fadawa abinda tayi washe garin ranar tasamu zuwa gidan su shatu ita kam ba laifi da sauki abin in akayi la'akari da auren kauye dama an san dole sai anyi wannan bautar
********
haka kwanaki suka dinga tafiya inda hutun dije ya qare daddy ya kira yace ta dawo gida koda me gari yafada mata bata so ba amma dole ta fara shirye shiryen komawa duk cikinsu ita da iyayenta suna kewar tafiyar tata
********
to bari mu leqa gidan amare kuma anyi taro lfy kowa ya kama gabansa yayin da aka bar angwaye da amarensu kasancewar kowa auren soyayya sukayi yasa suke cikin farin cikk da walwala da kulawa da juna naseer da yusra kam kullum addu'arsu Allah yakawo dije domin sun zauna sun tattauna akan abinda ya faru sun gama gano itac silar komai dan haka kowa ya qudiri aniyar yimata nasa salon rashin mutuncn toh fa zama ya fara zama domin yau kusan sati biyu da aurensu kullum daga gidan mamy ake kawo musu abinci su duka inda suka saki jiki suke shan amarci sosai ba ruwansu
a bangaren habeeb ma abin maliyan luqwi domin yasamu yadda yake so sajida ta kware a fannin soyayya macece me tsananin kissa da kisisina irin su ne matan daba boka ba malam amma karfar baka kadai ta wadatar suyiwa mutum kwaf daya duk irin yadda ta lura msmy na ji da yusra hakan yasa ta qara jawota jikinta itama domin ta lura yusrah da sauranta har yanzu
******
yau dije ta shirya dawowa iyayenta sunyi mata nasiha matuka daddy ne ya turo aka dauketa sai birnin tarayya🚗
kusan magarib suka iso gidan direct dakin su ta nufa bata bi takan mamy ba dan tasan ko ta dawo ko bata dawo ba gurin mamy duk daya ne dan haka dokin ganin basira kawai takeyi koda basira ta ganta kuwa rungumeta tayi suka shiga murnar ganin juna sai da tayi wanka tayi sallah kafin taci abinci sam basu samu haduwa da kowa na gidan ba dan ita harga Allah tama manta da wata cakwakiyar data tafi ta bari
*vote*
*comment*
*with 08066364077*
*Alqalamin khady*✍
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
TA ME GARI
NA
khadija usman
1⃣4⃣
tun sassafe ta shirya ta tafi makaranta a can suka hadu da su rufaida aka shiga hirar yaushe gamo tare da tambayarta yadda tabaro mutanen gida
bayan ta dawo a parlo ta iske mamy zaune ita da wata hajiya saudat qawarta tana duba wasu kaya da sallama ta shigo parlon ta tsugunna ta gaishesu cikin fara'a hajiya saudat ta amsa amma ita ko mamy ciki ciki ta amsa dan har yanzu tana kule da yarinyar tarasa wane mataki yakamata ya dauka akanta amma kawai bari ta turata gidan su naseer tasan acan su zasuci ubanta ba ruwanta koda abu ya biyo baya sunfi kusa
am kinaji na cewar mamy
dije da har ta mike ta fuskanci da ita take dan haka tace eh mamy
maza idan kin shiga ki shirya ki fito kizo habu ya kaiki gidan yayyenki ku gaisa da su kije kiga amare tunda kin gudu bakije kinga gida ba koh ?
ta karasa maganar tana murmushin mugunta
tunda dije taga mamy na murmushi tasan akwai abinda ta shirya mata dan haka cikin ranta tace dena gaigaye mamy nima da shirina zan tafi gudun bacin rana amma a fili saita ce to bari inje in shirya
yauwa to yi sauri kinji
dije dariya ma abin yaso bata a iya shekarin datayi a gidan nan tana iya cewa bata taba samun dariya ko magana irin haka ba a gurin mamy amma yau sai gashi wai ita take yashewa baki dan kawai tasan inma taje ubanta zataci
da sauri ta shirya ta fadawa basira inda zata sannan ta debi guzurinta a 'yar qaramar hand bag dinta ta fito saye da doguwar riga arebian gown cofee colour inda ta sanar da mamy ta fito wasu kaya ta bata tace ta kaiwa yusra zata kirata a waya tarasa dalilin daya sa mamy harda wani farin ciki takeyi dan ta turata gidan a ranta tace wlh kome zai faru sai dai raba biyu kowa yaji jiki
suna tafiya ita da baba habu driver sun zo dai dai wani store tace dan Allah ya tsaya tana zuwa ba musu ya tsaya ta shiga gutin ba jimawa ta fito tace su tafi yaja mota kuwa suna tafe suna hira har suka qaraso gidan
tabbas gida yayi kyau matuka babu makusa inda cikin sanyin jiki ta fito ta nufi bangaren dama dan bata san ya tsarin gidan yake ba
tana zuwa bakin parlourn ta shiga kwankwasawa an dan jima kafin taji ance yes come in
murda handle din kofar tayi ta shiga parlourn tabbas ya hadu iya haduwa ba qarya inda ta shiga da sallama dauke a bakinta ga mamakinta sai gani tayi yusra na washe baki tare da fadin oyoyo sister ta taso da niyyar rungumeta
qamewa tayi a gurin tana kallon ikon Allah murmushi yusrah tayi tare da qarasawa ta rungume dije itama dijen ganin yadda tayin yasata itama yin hakan ta dan jima a haka kafin ta saketa ta kamo hannunta tare da fadin qaraso ki zauna ya gajiyar tafiya ance shekaran jiya kika dawo kinyi gudun hijirar gashi kin dawo kin same mu ya mutan gidan duk lfy suke dai ko?
ita dai dije yake kawai takeyi dan tasan wlh wannan faran faran din da dalili hmmm koma meye ai zan gani bari na biki yadda kk so sakin jiki tayi suka shiga hira tamkar ba yusran data sani ba amma dije ta tabbatar da dalilin yin hakan aikuwa suna tsaka da hira taga wayar yusra tayi qara dauka tayi tare da barin falon ta shige bedroom dinta takai wajen minti 30 kafin ta fito ta sake neman guri ta zauna tare da fadin me za'a kawo miki sister ban dai yi girki ba nasan ze biyo da take away so something with drinks duk akwai su ba matsala
um um ba abinda zan sha ga sakonki inji mamy ta miqa mata ledar hannunta karba tayi tare da fadin tnx
yusrah ce ta kara kallon dije kafin tace naga kinki sakin jikinki ki manta da komai kawai kinji
no ba haka bane tashi ma zanyi in tafi naga yamma tayi
kije ina? cewar yusrah a dan hade rai
gida mana kinga bamuyi da baba habu ya zo ya daukeni ba gara in tashi da wuri dan taxi zan shiga
ah ah wlh bazai ma yiyu ba kizo gidan nan baki hadu da yayanki ba ai bazai ma sabu ba nasan ya kusa dawowa kawai ki jirashi ta karasa maganar tana murmushin da ita kadai tasan dalilin yinshi
tsaf dije ta karanceta a ranta tace hmm kin girmeni amma baki fini wayo ba tabbas in kuka min abinda ban gamsu dashi ba toh naku salon muguntar da zanyi muku saiya ci uwar wannan a fili kuwa cewa tayi ok to bari in leka bangaren ya habeeb ko
ok ba matsala muje in rakaki miqewa tayi ta suka fita
part din sajida zaune suka sameta sanye cikin riga da wando three quater sai wata 'yar mitsitsiyar riga wadda da kadan ta rufe cibiyarta kanta yasha qananan kitso jikin nan sai kamshi ke tashi sajida bata da kyau kwarai amma akwai wanka domin irin matan nan ne masu son komai suga sune a farko shiyasa komai nata yake kan gaba ko cikin friends dinta
da fara'arta ta tarbesu amma ta rasa dalili tun ranar da ta tambayi habeeb meye alaqar su da dije ya fada mata da ganinta da tayi gurin dinner taji sam bata ra'ayinta ko da ta ganta yanzu gabanta saida ya fadi amma sbd halinta na 'yan duniya kuma goggiyar 'yan boko yasata sakin fuska nan ta karbi dije hannu bibbiyu abinci me rai da motsi takawowa dije inda ta bude ciki taci t koshi dan dama yunwa takeji tunda dawowarta kenan daga skull mami ta tunkudota nan ba laifi amaryar habeeb ta iya girki amma dai gaskiya basu dace ba cewar dije dan wannan ai kusan sa'arsa ce
sun dan taba hira kafin suka tashi suka koma part din yusrah inda suna shiga yusra ta shige ciki tace ma dije tana zuwa miqewa tayi itama ta shiga toilet din dake parlour ta dauro alwala tazo tayi sallar la'asar
bayan ta idar ne ta koma kan kujera ta kama kallon wani film da ake haskawa a bollywood film din yatafi da hankalinta hakan yasa sam bataji tsayuwar mota a gidan ba illa jin sallamarshi kawai da taji yayi
amsawa tayi ga mamakinta shima din cikin sakin fuska ya shiga fadin ah ah mutanen kauye yaushe aka dawo?
kallon mamaki tayi masa tare da fadin shekaran jiya
to an dawo lfy?
lfy qalau suna gaisheku
hmmm muna amsawa
ok bari na shiga ciki in dan watsa ruwa
shiru tayu bata bashi amsa ba a ranta tace kinga dije anya kuwa bazaki tashi ki gudu ba ba mamaki mutanen nan shirya yankaki suka yi dan kin san dai ko giyar wake kika sha bamai yimiki dariya irin wannan amma da ganin yadda suka miki kin san da mugunta a zuciyarsu dan haka tunda qafafunki ki tashi ki fece kafin a karya miki su miqewa tayi ta nufi qofa harta daga labulen ta tsinkayi muryar yusra na fadin ina kuma zaki?
am dama zan tafi ne tunda ya dawo
cikin hade rai tace mamy bata fada miki cewar sai kinyi kwana biyu zaki koma ba
zaro ido tayi tare da fadin kwana biyu fa a nan gidan?
eh ko bazaki zauna ba?
to amma ai ban taho da kaya ba kuma ma skull dina fa?
iyeeeh lallai yarinya wato skull dinki da yaushe kika fara bokon yau she ma ministry tasan da zamanki shine zaki fadamun makaranta to bari ma kiji da ke kin dauka abinda kikamin kisha a banza wlh duk duniya bawanda ya isa ya hana inci ubanki ba duka ba zagi amma zaman prison zakiyi a gidan nan na tsawon kwana biyu cikin awa biyu kika barar min da burin danaci a bikina toh ke cikin kwana biyu sai duk wanda ya ganki ya tausaya miki dan haka kada ki kuskura ki fita a gidan nan dan dama an sanar da me gadi kada yabari ki fita
kirjin dije fa ya shiga lugude inda takeji kamar ta arta bata san tanadin da sukai mata ba tasan ma makaman yakin su sunfi nata dan haka ta yunkura da niyyar artawa taji ya riketa haba classic lady ina zaki kuma ai kinzo gida kuma sai jibi ya fada tare da hade rai mutsu mutsun kwacewa takeyi inda ya riqe hannun da karfi riqo bana wasa ba hakan yasata sakin qara don jinda tayi yana barazanar ballata wurgi yayi da ita gefen kujera inda saida kanta ya dan bugu kafin ya dauketa da wani wawan marin dayasa ta ganin star wata qarar ta saki yayi saurin aza hannunshi a saman bakin shi alamar tayi mishi shuru
kasa shirun tayi inda nan ya shiga fyadarta yusra na gefe tana dariyar mugunta saida ya gama canzawa dije hallitar fata abinka da fari duk jikin sai yayi ja yayi rudu rudu kafin ya kyaleta ya zauna yana maida numfashi
cikin daurewar fuska yace dan uwarki ubanwa yasa kiyi min abinda kikaimin
shiru tayi in banda shasshekekar kuka ba abinda takeyi da alama dije akwai zuciya
yusar ce ta taso cikin daga murya dan uwarki ba magana akeyi miki ba ta karasa maganar cikin daka tsawa
uwarki ce😠
sukaji ta ce 🙊
cikin zaro ido kusan a tare suka fadi
me kikace
cikin jan kuka da majina tace cewa nayu uwarki ce kuma wlh tunda kuka taba mana godiyarmu duk sai kunci ubanku
kallon kallo aka shiga yi shi naseer yana nazari da tunanin rainin hankalin yarinya itako yusra ta tuna da yadda suka kwashe kwanakin baya amma kuma kai ai da gani wannan ba irin wadan can bace dan haka a hasale tayo kan dije da niyyar dukanta wata irin zabura dije tayi kayo cikin yusra ganin da yusra tayi dije tayo kanta yasata sakin ihu tayi bayan naseer
ke ni zaki yiwa iskanci cewar naseer wlh zan babbala ki
itako dije ko'a jikknta ta nufosu tana qara barw baki miqa hannu yayi da niyyar riqota aikuwa tayi caraf da hannun a bakinta ta dankara masa cizo kuma gam ta rike hannun qara ya saki wadda tasa yusra saurin barin gurin ta ruga da gudu tayi bayan kujera duk yadda yaso ta saki hannun ki tayi saida taga jini yana bin yatsansa besan sadda yakai mata mangari ba aikuwa zafin da taji ne yasata tashi ta dane bayansa ta shiga yakushinsa tako ina baji ba gani cizo duk ta dabaibayeshi ga azabar da hannunsa keyi ga jini nabin yatsan dan ta dauke mai fatar koma cinyewa tayi oho waya sani
duk yadda yaso yaraba dije da jikknsa abu ya faskara gashj tana kuka tana yakushinsa duk ta damalmale masa jiki ta hada masa jini da majina cikkn daga murya ya kira sunan yusra sakamakon wani dankareren cizon da dije ta mallara masa a kunne hakan yasa shi finci kota da iya qarfinsa ta fada kan kujerar da yusra ta labe a bayanta riqe da waya jikinta na makyarkyata tana son yin kira takasa nemo number ma ido biyu sukayi da dije aikuwa ta kwalla wata qara wadda duk gidan ya amsa kanta dije tayi ta cakumeta aikuwa yusra memakon ta tabuka wani abun sai kawai ta bude baki ta shiga kurma ihu nan ko dije ta fara caskala ta itama harda rabon nata cizon a kumatu
ganin tana shirin kashe masa mata yayo kanta ai kafin ya qaraso ta saki dije ta qara nufarsa ba shiri shima ya juya dan ko kadan bazai so ta qara dane shi ba yarinya kamar mayya sai shan jini takeyi
habeeb na zaune a parlour shida sajida suka tsinkayi ihun yusrah da sauri suka taso suka nufo part din suna zuwa suka shiga kokarin budewa dan lokacin da naseer ya kamo dije da niyyar duka yusrah ce harda rufe kofa dan haka suka shiga bugawa yana fadin nasir nasir lfy bude mana
yusra ce ta nufi kofar danta bude dije tasha gabanta tanata kada kai tana bude baki naseer ko nacan yasa tissue yanata qoqarin goge jinin dake bin hannunsa da bayan kunnansa fuskarsa kuwa tuni duk ta hade tayi burdin burdin dan tasha yakushi
da dabara yasamu ya qaraso ya bude kofar
ya salam meya faru haka naganku a wannan yanayin ?
kafin yabada amsa yaji kukan dije daga cikin parlourn
leqawa yayi aikuwa ya ganta ta fara jifa da duk abinda ke falon tanayi tana kuka
tambayar nasir yayi meke faruwa nan ya sanar masa dalili
gurin dije ya nufa inda take kokarin jefo da wani fishers dishuis ya riqeta gam tare da hadata da jikinsa ya rungume ta tsam ya shiga yi mata addu'o'i a kunne
dije na jinsa tayi luf tare da qara gyara kwanciyar kanta a kirjinsa dukansu sai suka tsinci kansu cikin yanayi me wuyar fassarawa dije kam sai sauke ajiyar zuciya takeyi tare da qara shakar daddadan kamshi turaren dake jikinshi har take taji wani bacci na shirin kwasheta
jin shirun da sukayi ne yasa naseer leqowa dan duk su yusra da sajida gayyar tsorone hakan yasa suka kame a waje
yanayin daya gansu ciki duba da yadda yaga habeeb ya wani rufe ido bakinsa saitin kunnen dije gashi kuma ita ta wani lafe a jikinshi
duk radadin da ilahirin jikinshi keyi mishi sai yaji ya dena ji yayin da yaji zuciyarsa tayi masa wani irin zafi dan me zai rungumeta haka to me hakan ke nufi
jin shirun da matan sukayi ne yasa su dan shirin leqowa dan da alama abun ya lafa tunda sunji shiru aikuwa suna leqowa idon su yasauka akan abinda naseer ya kurewa gani
daram dammmmmm gaban sajida yayi dubs da yadda taga mijinta rungume da wata mace bata san lokacin datayi kansu ba tana zuwa tajanye dije daga jikinsa dije najin an jata tayi saurin qara langabewa ta zube a gurin
shi kuwa bude idonsa yayi a hankali ai kuwa ya saukesu cikin na sajida data kafeshi da ido ckin tuhuma waigawa yayi ya kalli inda dije ta sheme kafin ya maida dubansa ga naseer yace sai ku maidata gida tunda kun rama
yana gama fadar haka ya juya ya fice a dole sajida ta bishi itama............
*vote*
*comment*
*with 08066364077*
*Alqalamin khady*✍
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
TA ME GARI
1⃣5⃣
team dijeee kuna qarawa wutar nan fetur sai dai fa kuma hmmm a dai yi shuru yanzu muci gaba da gashi
ga masu tambayar littafin daga farko masu kirana da masu yimin mgn ta pc pls ku taimaka ku dinga tambaya a group dina in baki ciki kiyi min magana zan tura link kiyi join nasan mutan gidana akwai karrama bako da kin tambaya zasu hau tururuwar tura miki dan akwai su da karamci 👍
ina mugu mugun ji daku member's na khadeeja fans novels😘
******
ita kam yusra ko ta kan dije dake kwance bata qara biba ta lallaba ta shige daki shima naseer din binta yayi inda ba shiri dole ya dauki emergency care box suka nufi part din habeeb yayi musu dressing kafin suka dawo ind take kwance har yanzu tana nan yadda suka barta itako dije bacci ne ma yadauketa a gurin sai sauke ajiyar zuciya takeyi cikin baccin
koda suka shigo suka risketa a hakan naseer ya kalli yusra yace ke jeki tasheta ta tafi gida
wani kallo tayi masa kafin tace kai ka tasheta mana
ah ah naga dai ai ke yafi cancanta daki tasheta tunda ke kika sa aka kawo miki ita
hmm lallai to ai sai kayi duba cikin ni dakai wayafi wani shan jiki kaga kenan wanda yafi wahala shine yafi matsuwa da a barshi ya huta ni zaka danawa tarko inje in tabata tayimin yadda ta yi maka ka ganka kuwa?ta fada tare da sakin dariya
kulewa naseer yayi kafin yace ban ganni ba amma na ganki ki duba gefen bakinki da kuma kumatunki ga dankwalelen cycle nan an zana miki na musamman dan haka ki wuce kije ki tasheta ta bar gidan nan ina zaman zamana ke da mamy kunja an rudamin jiki yanzu ta ina zan doshi zuba ruwa duk yarinya tabi ta yage mutane sai kace kura nk ina zargin ma a garin nan akwai damusoshi alamu sun nuna cikinsu ta girma ga kuma 'ya'yan aljanu nidai wannan yarinyar ba qaramar jaraba baba malam ya jefo mana ba
kaga ni wlh duk ba wannan ba yanzu dai ka samo min maganin da zansha wlh ji nakeyi fuskata duk ta daure
hararar ta yayi kafin yace toh duk azabar da kk ji bata kai ya wadda nake ji ba
suna tsaka da maganar dije tayi juyi tare da yin miqa alamar zata tashi
da gudu suka kwasa suna rige rigen shiga daki wajen shiga dakin ma yusra ta riga shiga inda tana shiga dai dai naseer ya kawo kai danya kutsa ai kuwa ji kk yi bamm tare da wani sauti qummmm goshinsa ya daki qofar ko zafin daya ji baibi ta kai ba ya danna qofar ya qarasa sa key din kafin ya jingina bayansa da kofar suka shiga maida numfashi kamar wadanda suka yi gudu ko wani aikin wahala
jin goshinsa yayi kololo ne yasashi sa hannu ya taba yaji zafi kuwa kallon yusra yayi dake zaune gefen gado tana mayar da numfashi kafin yace kinga maza ki kira mamy ta turo a kwashi yarinyar nan
da sauri ko ta dauki wayarsa ta shiga kiran layin mamy
tana dagawa yusra tace yauwa mamy pls ki turo a dauki yarinyar nsn pls
jin hakan da mamy tayi yasata fadin baku kuka ce a barta tayi kwana biyu ba meye kuma na cewa ta dawo yau ko har kun gama huce fushin naku ne?
ai gara kawai ta tafi din inba haka ba...fizge wayar naseer yayi tare da fadin hello mamy
au kana kusa ashe ya akayi ne naji kunce a turo a dauketa yau ince ko kaci ubanta dai ko
yasan halin mamy inya fada mata abinda ya faru zata iya sasu daukar wani matakin shi kuma a nashi tunanin ya lura duk lokacin da ya yima yarinyar wani abu toh sai yaga shi yafi cutuwa qara maimaita tambayar tayi hakan ya katse mishi tunanin dayake yi ko baka jina?
tun yaushe ma ai ba qaramar lallasata nayi ba i hp dai daddy ma baya nan dan ban son ya ganta a wannan yanayin gashi kuma yusra kinsan ta da rigima tace lallai saita koma yau dan wai kada inyi kisan kai ganin yadda na lugwiguita mata jiki
ah to indai haka ne gara ta dawo din dan daddy'n ku yana nan kada kuma ya ganta yace meya sameta ta fada mishi gaskiya kasan shi fa akan yarinyar nan kamar wanda aka sihirce dan haka inaga kawai ku barta ta qara kwana kafin nan ta dan murmure sai ta dawo bayan ya tafi ni kuma in barje nawa haushin
no mamy ai duk hukuncin daya kamata ayi mata zan gama yi mata kedai barni da ita kawai amma dai ki turo a dauketa din kawai
tunda kun matsa dai to ka kawota mana kaga ma saika san abinda zaka fadima daddy'n naku ka fadi wani laifin tayi ka hukuntata
nikam yadda nake din nan ina zan iya fita ki ganni ya fada a zuciyarsa
ya naji kayi shuru
naga ne zaiyi wuya in samu lokaci dan inada meeting karfe 8 din nan na dare gashi zai daukemu lokaci kuma kinga ni inama zan sami time har inkawo ta kawai dai ki turo din inya so kisan me zaki fadawa daddy inya ganta ko kuma kawai ma ki hana haduwar ta so
ok to hakan yayi bani yusra
mika mata wayar yayi suka qara magana ta kashe wayar
******
shi kuwa habeeb ba qaramin fama yasha ba kafin sajida ta fahimceshi saida yasha aikin rarrashi tare da fada mata kalaman da suka kwantar mata da hankali kafin suka koma normal
****
ita ko dije koda ta farka ganin wai hartayi baccin gaske daga na qarya ganin yadda suka kwasa da gudu dazun duk tana kallonsu jin duk jikinta na ciwo ga kuma fatarta data tashi inda naseer ya daketa tunawa da abinda tayi musu kuma yasata sakin dariya tare da fadi a fili ta furta wlh tunda kuka yimin haka sau kun sani wato ni kuka kawo ga jaka kuyita dimata har kwana biyu hhhhhh bakusan dije bane na gwada muku kalata ta fuskar rahma kunki fahimta yanzu aka fara game din let's see who's d winner between us dakin dake pacing dinta ta nufa koda ta shiga hakan ya nuna mata bedroom din yusra ne dan haka kanta tsaye ta nufi toilet din dakin heater ta kunna har ruwan yayi dumi kafin ta fara yin wanka tanayi tana wash tare da matsar kwalla tana kuma ayyana irin fansar da zata dauka akan su
niko nace dije banda kuma kisan kai 🤣
ta jima sosai kafin ta gama ta dauro alwala tana fitowa ta bude wardrope ta shiga neman kaya sai kace dakinta tasan duk kayan yusra sun mata yawa duk da ba wai sosai ba dan haka ta shiga neman ko doguwar riga ce cikin sa'a ta samu kasancewar rigar nada madauri saitayi mata dai dai bayan tayi sallah ta fito farlon inda ta hango mutan gidan nata zuro kai ta qofa suna leqe
duk tana lura dasu ta share su ta zo parlour ta zauna tare da dora kafa daya kan daya ta shiga tunanin meya kamata tayi musu ne ma
ba ta jima ba ta tsinkayi bugub qofar falon tare da sallama kwarai ta dau murya ta baba habu driver ce amsawa tayi tare da fadin ana zuwa
su kuwa mutan gidan sunaji aka fara takaddama nasir yace yusra ta fita ita tace shi ya fita kowa yaqi fitowa cikin hasala yace wlh dai kinji kunya wai wannan 'yar mitsitsiyar yarinyar tasa ki kasa fita dan tsoro
mun dai ji kunya ni da kai idan kai ka kirani babba akanta amma akanmu fa nida ita ai kaine kai kuma yakamata ka fita ka sallameta tunda kaine me gidan ni kam bazan je ba dan ko yanzu ban gama jin zafin ciwon jikina ba haka kawai yarinya ta zo ta qaramin wani ciwon kana gani ma dan raini harda samin kaya ni inka fita ma kaja mata kunne ta ciremin kaya wlh ko inzo inci mata uwa
bude qofar gayi tare da fadin zo ki je da kanki ki fada mata zuwa da kai ai yafi sako maza zo ya fada yana me nuna mata hanya
wlh ba inda zani dan ba sunana saratu ba zan iya zuciya in shake yarinya har saita mutu kaga ko maganin kada ayi kar a fara wuce ka sallameta tabar min gida
yaso ya qara magana amma ya qyale yasan halin yusra akwai rai ni gara ya koma mata nasir din kada taga damar sa
cikin hade rai ya fito tare da nufo inda dije ke zaune
ko kallonta beyi ba ya wuceta ya nufi qofar falon bayan ya bude suka gaisa da baba habu kafin yace bari ya kira dijen ta fito su tafi
yana shirin shiga sukayi kacibis da ita
ke maza inda abinda zaki dauka dauko ki wuce gida
to tace tare da rabashi ta wuce
a ranshi yace wannan duk wanda ya aureki ya aurarwa kansa masifa da kudinsa
bakin mota ta nufa shi kuma yana ganin haka ya koma ciki
tana qarasawa bakin motar ta dubi baba habu tace
baba dan Allah inda hali aromin wayarka in kira daddy
mika mata yayi yana washe baki bayan ya matso number Alhajin
flashing tayi inda daddy na zaune yana cin abinci yaga shigowar kiran habu driver kuma yasan ya tafi dauko khadija hajiya ta fada masa dan haka yssan ba mamaki akwai magana shiyasa ya yi dialling number
muryar dije yaji dan haka cikin sauri yace lfy diyata?
lfy qalau daddy dama naga baba ne yazo daukata kuma ni gaskiya daman um....dama...kinga fadi kawai kanki tsaye khadija me kk bukata
dama cewa zanyi munyi magana ne da Aunty yusra da ita matar yaya habeeb shine suka ce in dawo nan da zama toh shine nace su fada maka wai bazasu iya ba shine nace ni bari na fada maka
dadi daddy yaji dan haka cikin sakin fuska yace kaji su to ai wannan ba matsala bane duk dayane ai naji dadi kwarai
to nagode daddy gobe abawa baba habu yakawomin unifoam dina zan wuce school in mun taso sai in biyo in dauki kayana
toh badamuwa Allah yayi muku albarka
ameen daddy ta kashe wayar tare da miqawa baba habu tace ya tafi kawai
ita ko ta juya ta koma cikin gidan
tana shiga falon ta tarar da su zaune jin bude kofar suka jiyo suna ganin dije kusan a tare suka furta lfy?me kika dawo yi kuma
bata tamka musu ba saita fara kokarin zama saida ta zauna kafin tace naji kunce kuna son nayi muku kwana biyu ne shine nace bari in zauna din yafi kada in tafi kuga rashin kyautawata ko mamy tayi fada
mun shiga uku🙆♀
🤣🤣
*vote*
*comments*
*with 08066364077*
*Alqalamin khady✍*
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
1⃣6⃣
*ina neman afuwan mutane pls dan Allah ku dinga min adalci nasan masoya basa yawa kuma daukaka daga Allah take ina iyakar kokarina wajen ganin na faranta ran kowacce a cikin masoya na idan kun tambayeni littafin daga farko ko wani page din ban tura muku ba kuyi min uzuri kun san jiki da jini kuma inada abin yi amma nake sadaukar da lokacina dan nishadin ku duk wadda take son littafin tayi magana group nasan zata samu pls afuwan dan Allah na kuma gode da soyayyarku gareni Allah ya bar kauna ya qara zumunci*
***
kut......in kin isa Allah ya tsinen ai wlh bazan zauna da 'yar jagaliya a gidana ba cewar yusra ta fada tana huci
shima nasir cikin hade rai yace ke ina wasa dake ne ?wlh tun muna mu kadai ki tashi ki tafi gida waye zai yadda ibola ta zauna masa a gida har kwana biyu ko ki tashi wlh ko in babbala ki a kwasheki a kaiki
gani sukayi ta miqe yusra da dama tun tuni ta miqe tsaye ta riqe kugu ganin dije tayo kanta yasata kwasa da gudu tayi bayan naseer wanda shima ganin dijen ta miqe ya danji wani abu a zuciyarsa amma fa gara ya nuna mata shima namiji ne dan haka saiya dake ya tsaya yana fadin ke yusra meye haka ban son iskanci
saida ta qaraso gabansa kafin ta kalleshi ido cikin ido shiko kawar da kai yayi domin shi in yana kallon idonta sai yaga kamar idon mage bare yanzu daya qara tabbatarwa kansa yarinyar nan ruwa biyu ce wato mutum aljan😂dan haka be son hada ido da ita kada yaje ko maguzawan ne akanta arnan farko su nuna masa basu san hasken addini ba
tsinkayar muryarta yayi tana fadin
haba yayana yanzu kawai dan nace zan kwana biyu gidan ka kk korata bayan kuma tun farko ku kuka nemi da in zo inyi kwana biyu a wajenku ai ko ba komai nayi muku haka dan zumunci amma tunda bakwaso shikenan
jin kalaman datayi yasashi sauke a jiyar zuciya domin yasan yanzu zata ce zata tafi amma me ?
sai ji yayi tace tunda na fuskanci baka son in zauna gidanku hakan na nufin tun yanzu zumuncinmu zai samu rauni kuma nasan megari bazaiji dadi ba bare iyayenmu dan haka na yanke shawarar zamana a gidan nan har sai ranar da nayi aure
😳
me?
la'ilahaillah anta subahanaka inni kuntu minazalimin
a'uzubillahi minasshaidanir rajim
ka manta baka hada da ayatul kursiyyu ba
cewar yusra dake bayan naseer wanda keta kwarara addu'o'i kawai dan dije tace zata zauna a gidansu
itako dije dariya ma abin yabata cikin zuciyarta tace ikon Allah sai kallo
ganin yaki yin shuru banda ruwan dala'ilai ba abinda yakeyi hakan yasa dije fadin haba ya naseer meye naga kanata addu'a ko wani abun ne yafaru ?
kinga khadija dan girman Allah da ma'aikinsa na rokeki ki taimaka ki koma gida kinji
to wai sbd me?
ta tamvaya
yasan sha'anin jinni be zama lallai yarinyar tasan meta aikata musu ba kuma baya son tasani dindan haka saiya waske yace kawai kinga mamy nada hawan jini ga shi ma yau mura take fama da ita matsananciya ina ma zargin limoniya gareta kinga gara kije ki zauna kusa da ita nasan zaki taimaka mata da wasu abubuwan
hakane kam yakamata in koma
yauwa qanwata ya fada a dan raunane
yusrah ma harda gyada kai tare da fadin wlh kam gara kije dan tayi kewarki
toh shikenan ta fada tare da fadin
ni zan wuce toh saida safe
Allah ya tsare ya kiyaye a sauka lfy
qofar falon ta nufa har ta isa sai kuma ta tsaya ta juyo yake sukayi mata tare da wiving din hannu ita wlh dariya ma suka bata dan haka saida ta dara tare da fadin
lah ya naseer meya sameku ne a fuska kaida aunty yusra naga duk kunji ciwo
saurin kallon juna sukayi kafin daga baya suka hada baki wajen fadin Accident
subahanallah accident kuma?da kura ko kuma da kare dan wannan ai naga ciwon kamar bada mota ko wani qarfe akayi shi ba ko
da biri mukayi fada naseer ya fada yana yashe baki
.biri kuma a ina?
ai da yake akwai shi a nan gidan toh shine ina masa wasa ya yakusheni yusra ma haka
.wow gaskiya wlh har kunsa nafasa tafiya sbd wlh ina son biri dama
.wayyyoooo 🤣
dan girman Allah ki tafi kawai gobe zan kawo miki shi
ah ah nidai ina son ganinshi wlh
ai nasa an kasheshi
what ?
kisa fa?
akan me?
.sabd yaji mana ciwo har haka saina lura gaba gaba zai iya daukar rai ma
amma ko wannan biri sai kace ba dan nigeria ba
ah ah dan boko haram ne
au dama dabbobi ma suna zama 'yan ta'adda
ai.....kaga dan Allah ka barta ta tafi dare yanayi kuma gashi taxi zata shiga Allah ya kaiki lfy sister cewar yusrah dake tahowa danta dan tura dije
au ni kinga ma fa na manta wlh aunty ashe fa baba habu ya tafi ko yanzu ya zanyi to ni dije ta fada tare da rike haba
.akwai abinyi kawai kinga bari nadauko miki kudi kishiga taxi tunda baki da su ko
ah ah barsu kawai inaga inada su a jakata zasu isheni zuwa gida
to a gaida su daddy zasu ji tace tana qoqarin fita
tana ficewa kuwa yusra ta rufe qofar tare da sauke ajiyar zuciya haka shima naseer din
bakin gate ta nufa gurin me gadin gidan inda ta samu guri tazauna suka shiga hira kamar sun san juna tun da can gumi fa ta hadu da anka nan kayan zance ya hadu sukaita zubawa kuwa kafin daga baya taji qarar mota a waje koda suka leqa baba habu ta gani da kayanta a akwati kin kim kim musa me gadi ne ya karbi kayan tace ya tafi kawai nan ya juya ya musu saida safe
ganin dare nayi ne yasata miqewa tare da fadin toh baba musa zan shiga ciki saida safe ko
toh hajiya mu kwana lfy
Allah yasa ta fada tare da jan trolly dinta
harta nufi part din su yusrah kuma saita fasa ta tsaya ta danyi jimm kafin ta juya akalarta zuwa part din su habeeb tana zuwa ta shiga knoking a hankali a daidai wannan lokacin suna zaune suna hira tare da dan taba kallo jin ana buga kofar yasa shi fadin waye a hankali
shiru tayi sai da ya qara maimaitawa kafin tace nice
jin muryar mace yasa sajida saurin miqewa ta nufi kofar tana fadin kece wa?
khadija!!
bude qofar tayi sukayi ido hudu da dije inda gaban sajida ya yanke yafadi ganinta da tayi da jaka dirkekiya
lfy ?
ta tambayeta cikin dan hade rai
kallonta dije tayi ganin yadda tayi mata tambayar yasata itama hade nata ran kafin tace lfy lau mana ta karasa maganar tana me kutsa kai palon
sai yanzu ya dago ya dubesu shima ganin dije da jaka yasashi mamaki tare da fadin ke lfy naganki da jaka haka kamar me shirin barin gari
guri ta samu ta zauna tare da fadin lfy lau wlh nadauka daddy ya kiraka yayi maka bayani ai shine yace in zauna inyi kwana biyu anan nama shirya zan tafi sai gashi yasa an aikomin da kaya na toh da zanje part din ya naseer sai naga kaine babba kada kaga ban kyauta ba gara in zauna anan ko
hmmm haka
tunda yace haka be qara fadin komai ba illa juyawa da yayi ya kalli sajida dake tsaye kikam ta zuba musu ido maida kallonsa yayi ga tv din itama sajida ganin haka yasata samun guri tazauna dan nesa dashi
sun jima a haka banda karar tv babu abinda kk ji a falon itako dije duk jikinta ciwo yake mata gashi tana jin yunwa ga bacci data fara ji
gyaran murya tayi kafin tace am yaya nace ba
kallonta ya juyi yayi jin yadda take son yin magana dashi lallai ma yarinyar nan yafada a ranshi
itako ko'a jikinta tace wai azumi kukeyi ne a gidan nan?
cikin rashin fahimtar magsnarta yace kamar ya ban gane ba kina nufin na nafila ko me?
ah ah na dare nake nufi naga ne ko ruwa ba'a bani ba ga yunwa da nakeji kamar hanjina zai tsinke toh naga kada inyi nauyin baki tunda ni bana azumin gara a in magantu kada in cuci kaina
binta yayi da kallo wanda tarasa na meye shi kanshi ya kasa tantancewa ko kala be ceba taga ya miqe tare da daukar wayarsa ya nufi dakinsa
ganin hakan datayi yasata fadin to ko masauki a tausaya a bani ai ko tunda abincin bazai samu ba nazo gidan economic masu auna ci da ciyar da wani
rasa me zai ce yayi kaji yarinya sai kace irin kurege shi sam be son yawan magana bare wasa dan haka cikin dan hade rai yace ki tambayi matar gidan mana ai itace da gidan yana gama fadar hakan ya shige daki
sajida data tsaya kallon ikon Allah tare da nazari inda daga karshe taji dadin yadda habeeb din yai sannan tasaki ranta tare da fadin oh khadija baki abin magana ga gajen haquri tashi muje in nuna miki inda zaki sauka
ok ta fada tare da mikewa dakinta dayan takaita inda tace ta zauna a kawo mata abinci
ah ah ni ai a gidan nan nafi qarfin a kawomin kice dai in tashi in dibarwa kaina kawai in hidimtawa kaina kada kizo inga laifinki kin san hausawa sunce mu dangin miji ba'a iya mana
kallonta sajida tayi tare da nazarin yarinyar wannan yarinyar fitinanniya ce ta qarshe amma zanyi maganinki ta fada a ranta........
naso inyi muku yafiv haka amma kaina ciwo yakeyi bacci😚
*vote*
*comments*
*with 08066364077*
*alqalamin khady*✍
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
TA ME GARI
1⃣7⃣
nayi adungure na wulwula na heqo na mazgo gaisuwa ta tare da jinjina ga dukkan masoya ta me gari tare da jinjinar ban girma ga members na khadija. fans novels 1 da khadija fans novels 2 ina ganin comments dinku gaskiya kuna yin dije da yawa 😘
miqewa tayi ta tabi bayan sajida wadda ke ganin ikon Allah ganin da gaske take bin nata zatayi yasata juyowa tare da fadin
haba qanwarmu ai kya tsaya inyi dawainiya dake ko iya na yau ne ko a matsayinki na bakuwa kamar yadda kk fada
dakatawa dije tayi tare da fadin ah ah matar yaya bawai fa wani dalili yasa nace ki bari in nemawa kaina d'a'amin ba kawai sai dan kin san iyawa mutum sai Allah kuma gashi naga bakisan da zuwana ba kada in saki wahala kije kawai ki kula da mijinki dan naga alamar ke yake jira bakin ciki ya cika masa zuciya kije ki rarrasheshi
kallonta sajida tayi tare da fadin wane irin bakin ciki kuma ?
ah bakin cikin zuwana mana shin wai be baki labarin abinda ke tsakaninmu ba?
dammmm gaban sajida ya fadi cikin karfin hali tace meye tsakanin kun ?
ah lallai da sauran ku tunda har yanzu be fada miki ainihin sahihin abinda ya hadani dashi ba
zuciyar sajida fa tafara cunkushewa jin yarinyar na ambatar wai alaqa tsakaninta da habeeb shin me hakan ke nufi?wace alaqa ce kuma?to ko dai ya so yarinyar ne ?kai no habeeb dake son babbar mace wadda ta iya tattali irinta me zaiyi da wannan berar wadda inba kayan fitina da jaraba ba ba abinda ta ginu akai dan haka cikin dan hade rai tace ai ke yakamata ki sanar min alaqar ba shi ba
kallonta dije tayi ta nazarci matar tun dazu ta karance ta akwai kishi dan haka saita kiyasta a ranta kawai inta yi mata wani rashin kyautarwa wlh ta hakan zata azabtar da ita
itako sajida haushin yarinyar ta tsinci kanta da ji dan sai yanzu ma taga meye dalilinta na tsayawa ta biye mata yarinyar da bata wuce sa'ar kausar ba autar su dan haka saita sa kai da niyyar ficewa daga dakin muryar dije taji na fadin
.yauwa Aunty jeki bashi haquri ni bawani dadewa zanyi ba zan koma gida amma dan Allah a dan taimaka a qara yawan abincin gidan kar ayi la'akari da girman mutum shi ci ba'a nan yake ba kada ki ganni siririya wlh rainon kauye ce dan haka a taimaka kada a tauye ma cikina hakkinsa kuma kada ki manta kice masa ya baki labarin zuwansu qauye last
ko ta kanta sajida bata bi ba tasa kai ta fice itama ta fito sajida na kokarin shiga dakinta ta tsinkayi muryar dije na fadin
aunty inane madafa?
kamar ya ?
ashe fa matar yaya 'yar gayu ce na manta wlh
i mean kitchen?
nuni sajida tayi mata da hannu inda tai shigewarta daki
tana shiga dije ta kwashe da dariya tare da qarasawa kitchen din ruwan tea kawai ta hada tasha dan duk jikinta ciwo yakeyi har yanzu musamman gurin da nasir ya riqeta a nan ta shanye shayin ta gama ta koma masaukinta tare da bude jakarta ba kayan bacci ciki dan haka ta kwanta abinta a haka da kayan yusra🤣
tana shiga dakin ta sameshi gaban mirrow yana fesa body spray a dan hade rai ta qarasa ta karba ta shiga fesa masa duk yana lura da yanayinta kasancewar ta mace me iya tattali da soyayya sajida ta waye kwarai ta san hanyoyin mallakar miji cikin sauki ba boka ba mallam tasan kissa kala kala hakan yasa ta mamaye zuciyar habeeb domin shi dama dan son rayuwa ne kuma saiya samu me tarairayarsa duk yadda yake da jin kai da miskilanci to fa a gaban sajida tamkar yaron goye yake kuma yana iyajin zai iya mata komai a rayuwa dan haka koda yaga yanayinta yasan akwai damuwa damuwar kuma bazata wuce akan zuwan dije ba dan yasan sajida akwai kishi dan haka saida yabari sun gama shirin kwanciya kafin ya jawota jikinsa cikin salon tasa soyayyar ya shiga fadin
what's wrong with my princess ?
uhmm ?
shuru tayi kafin zuwa can yaji tace
mece sahihiyar alaqarka da khadija?
cike da mamakin tambayar datayi mishi yace kamar ya ban fahimta ba inaga ai kinfi kowa sanin matsayinta a gurinmu ko?
hmmm amma ai tace in tambayeka ainihin sahihiyar alaqar dake tsakaninku wai a kauye shine nake son jin ko akwai wata a qasa ne
murmushi yayi a zuciyarsa tare da fadin lallai yarinyar nan bala'i ce ko ince annoba ifritu wato tayi nazarin hallayar sajida harta zurma ta ita kuma duk da girmanta da shekarunta ta kasa fahimta wannan akwai shegiyar yarinya wato so takeyi ya bata labarin abinda tayi musu a qauye abinda ya barshi a sirri baya fatan matarsa tasan abin kunyar daya faru shine take son fallaso shi ai wlh gobe korata zaiyi gidan nasir suje can su karata tunda su sun saba wristilling da ita
jin yayi shuru ne yasata fadin kayi shuru baka bani amsa ba
oh baby matsala wlh wlh kinji na rantse miki wlh babu wata alaqa tsakanin mu in ba matsayinta na qanwa garemu ba ke ni wlh banma santa ba sai zuwan da mukayi time din da muka dawo nigeria daga nan tsohon nan ya hadomu da ita shine silar zamanta a gidanmu so banda wannan alaqar banga wata ba amma ban san dalilinki na tambayata ba
hmm ai dole in tamvaya ganin yadda kayi mata dazu a gidan naseer kuma gashi yanzu ta dawo nan amm.......shiiiiiii ya fada tare da dora yatsan shi a saman lips dinta haba baby ya kk son maidani baya ne me kk tunani namijin dake da mace kamarki shine zai iya hango wata to kisani wlh inda ana ciro zuciya to dana ciro mikitawa kinga yadda nake sonki nake ji dake ke wlh ni ko wacce mace kallon 'yan daudu nake musu kuma ma in zaki hadani da wata ina laifin ma ki hadani da ta kwarai saiki hadani da hambirin hayam wlh kin cuce ni kin san yadda na tsani yarinyar ma kuwa wlh sbd daddy yasa nake raga mata kuma bana son raini shiyasa kika ga ban. fiya shiga shirgin kowa ba sai naki ke kadai keda habeeb kisawa ranki ko'a lahira bazan miki kishiya ba bare gidan duniya da sai naga wadda taimin zan aura dai ko ? to duk ba wadda tayimin sai fadimatuz zahra'u sajida,batula,Aliya,kamila,sharifa,zakiyya.....zai ci gaba ta katse shi ta hanyar mannewa da jikinshi tare da aika masa da rikitattun sakonnin da suka sa ya kasa qarasa wa ya shiga maida martani ita ko ta dage wajen ganin ta biyashi tukwicin kalamansa masu tsadar gaske a wajenta nan suka lula duniyar masoya
Asuba ta gari
*******
ana kiran sallar asuba a kunnen dije koda ta farka tayi sallah ta yi addu'ointa kamar yadda ta saba kafin daga baya ta miqe ta afka kitchen break fast me rai da motsi ta hada sannan ta jera saman dinning kafin ta koma daki wanka tayi tare da shiryawa cikin unifoam dinta sannan ta fito saman dinning ta nufa ta fara karyawa amma bataji alamar mutan gidan sun shirya fitowa ba gashi har kusan 7:15 sai da ta gama karyawa tsaf kafin ta miqe ta nufi dakin dataga sun shiga jiya
kwankwasawa ta shiga yi
ya akayi ne waye ?
taji muryar sajida na fadi
au to bakuwar gidan ce naga shuru ne me gidan be fito masallaci ba shine nace bara in sanar muku ana shirin tada sallah ya gaggauta koya samu jam'i don kin san sallah in rana ta fito ba kyau gara a yita da duhun asuba
bude qofar sajida tayi tare da kallon dije jin abinda ta fada mata wato dai so takeyi tace basa tashin asuba kenan shine ta fada a fakai ce ganin ta cikin shirin makaranta yasata fadin to tasalla munji mun tashi ai a bari mu gama kimtsawa sai mu fito ko?
ah ah in dan ta dije anty ku koma bacci nidai kiramin me gidan a sallameni in tafi naga zan makara
gyaran murya yayi daga bayan sajida shirye yake tsaf cikin kayan suit ash colour sunyi masa kyau matuqa cikin hade rai yace lfy nake jin hayaniya
lfy qalau yaya dama zuwa nsyi ince na shirya zan tafi school
toh a dawo lfy
to wa zai kaini?
au dama baki taho da me kaiki din ba yayi maganar yana me fitowa a dakin sajida ta biyo shi suka nufi waje inda suka bar dije tsaye da sakin baki
ganin da gaske fita zasuyi gashi dai bataga ya karya ba oh yanzu nagane ta fada a zuciyarta wato sbd ni aka ki yin abin kari a gidan nan hhhhh tayi dariya kadan ashe kuwa akwai kura dan wlh ko da bala'i sai naci na qoshi tana ta sambatun ta har suka fice bata sani ba saida taji alamar rufe kofar kafin ta juya a hankali tabi bayansu
.direct gurin motar sa ya nufa yana zuwa ya bude mazauninsa ya shiga inda yabar murfin bude sajida ta tsaya riqe da murfin suna maganar su ta masoya
tana fitowa ko ta kansu bata bi ba ta nufi part din nasir ta shiga kwankwasawa
nasir da suke tsaye suma suna bankwaba da juna yaji ana buga kofa yayi saurin sakin yusra ya nufi kofar yana fadin sai mun dawo dan yana kyautata zaton habeeb ne dan ya fada masa in zai wuce asibiti zai wuce dashi dan yanason yaga likitan fata dan yadda kura ta yayyageshi🤣a cewarsa
yana bude kofa sukayi ido biyu da dije
.besan lokacin daya furta
la'ilahailla anta subahanaka inni kuntu minazzalimin
lfy me ya kawoki da sassafen nan ?
ganin yadda yayi yasa dije kusan sakin fitsari dan dariyar data guntse
yusra da tana dab da shiga daki taji yayi wannan addu'a yasata dawowa dan taga meya gani aikuwa itama na ganin dije tace ya salam meye kuma kika manta ai da kin fadawa mamy ta kira waya ai sai a aika miki shi
ai badaga gida nake ba anan na kwana
cikin hada baki sua ce a ina din?
a gidan y habeeb
sauke ajiyar zuciya sukayi kusan a tare kafin nasir yace
Alhmdllh qanwarmu sarkin hankali ai gara da kk kwana a can ni yanzu ma kinga abuja zamu tafi ni da yusra dan haka basai kin zo mana sallama ba in zaki tafi ki gaisheda su mamy tsarabar ki insha Allah daban take in mun dawo yana fadar haka ya juya ya koma suka kullo kofa harda sa key
dariya dije tasa kafin ta gaji ta mike ta nufo inda su habeeb suke wadanda duk abinda ke faruwa suna kallo sai dai basu san me suke fada ba sun dai ga komawar nasir da dariyar da dije tayi
tana qarasowa bata ce qala ba ta bude murfin baya ta shige ta qame ta kalli window
cike da mamaki a fuskar kowannensu sajida ta bude baki zatayi magana ya dakatar da ita ta hanyar daga hannu kafin cikin hade rai ya juya yace
ke dan ubanki bakida hankali ne meye na shiga motar mutane uban waye drivern ki?
cikin marairaice fuska tace kayi haquri yaya wlh dama tsayuwar da mukayi da yaya nasir ne yace in fada maka wai daddy yace ka ajiyeni a school daga can zan wuce gida ma nafasa zaman
jin ta ambaci tafiya yasa sajida saurin fadin ai kawai ba komai sweety ka ajiyeta din inaga shi nasir din yafasa fitar tunda kaga ya koma watakil dan yaga za'a fita da jerry dinsa ce
jin sarauniya tayi magana yasashi fadin ok kawai
sallama sukayi inda ya fita daga gidan be ko bi takan naseer ba
kasancewar yasan school din tasu direct can ya nufa da ita yana tsayawa ta bude ta fita tare da fadin saina dawo yaya
.ki dawo ina?
gidan ka mana ai ni naga wuri .........
*vote*
*comments*
*with 08066364077*
*Alqalamin khady*✍
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
NA
khadeeja usman
1⃣8⃣
*ina matuqar godiya da addu'arku gareni Alhmdllh nasami sauki tare da kuzari da karsashin ci gaba da suburbudo da sambado tare da sheko muku ta me gari uwar mazga hakika kuna dadamin qwarin gwiwa ta yadda nake jin zan iya yini zungur ina muku typing amma sbd halin yanayi zan bawa kaina haquri inyi muku na 'dan lokaci zakufi jin dadin sa😂*
tana gama fadar haka ta juya ta shige makaranta ta barshi da sakin baki inda ya shiga fadi a fili wlh bazan yadda ki zauna min a gida ba bari kawai in kira daddy ince masa ki koma can kuma sai yace kai nasan halin yarinyar nan yanzu haka bazata koma bs kawai fadamin tayi dan inyi haushi sbd ta mayar dani kare hmm zanyi maganinta haka yayita tuki yana sambatu da masifar ba gaira ba dalili har ya isa asibitinsu yana zuwa ba jimawa ya fara aiki
itako dije tana shiga cikin makaranta direct office din principal ta wuce ta sanar dashi daga yanzu a dinga biyawa daukarta da motar makaranta ta fada musu inda ta koma dayake dama a cikin bill din makarantar harda kudin transport suke hadawa sai dai in ka so kasa a kawo danka amma su ba ruwansu shi yasa koda dije ta fada ba'a samu matsala ba
tana fitowa ta nufi class nan suka hade dasu rufaida aka shiga hira kafin malami ya shigo suka fara lesson
****
Amarya kenan kin ganki kuwa yadda kika canza kinyi wani kyau dake kamar wata black american
dariya sajida tayi kafin tace ke laila wlh banda sharri
wlh ba maganar sharri fadamin meye sirrin ne me habeeb ke baki
kulawa da soyayya ta fada tare da yin fari da ido
shegiya qawata kodai to har an sama mana baby ne
baby fa kika ce tun yanzu ?ai sai mun shekara kafin inyi ciki ke yadda habeeb yake dan son rayuwa yanzu in nayi ciki ai sai a hankali shima kanshi yafi son mu huta ai
tafawa sukayi tare da fadin kusha sha'aninku bird loves naso inga habeeb ranar aurenku inga bakin nan sai gashi ina malesia na tsinkayi lbrn bikin gashi ba halin in dawo sbd wani uzuri
.hakane kam Allah be nufa dake za'ayi ba yanzu gashi kinzo har gida ai bari in tashi in sama miki abinci ko me kike so ta tambayeta tana qoqarin miqewa
komai ma kin san ni banida zabi
ok ta fada tare da kokarin miqewa ta shiga kitchen
da sallamarta ta shiga falon inda ta iske laila hakimce da remote tana canza tasha batare data juyo ba ta amsa sallamar har saida ta ji dije nayi mata ina yini kafin ta maido da dubanta gun
wani kallo tabi dije dashi ta amsa gaisuwar a yatsine ko ba'a fada mata ba tasan wannan qanwar habeeb ce domin kuwa tana kallonta ta hango kamar su sai dai kawai ta fi shi haske dan ita fara ce sosai hmm tab di lallai akwai aiki wato har an fara kawo 'yan leken asiri lallai sajida batada hankali ita ina zata yadda da a kawo mata wata dangin miji ai ko kawowa za'ayi gara a ce ta dauko a danginta balle wannan yarinyar da gani idonta feke yake
tund dije ta lura da kallon da matar ke binta dashi taga kuma ta lula duniyar tunani kawai saita qarawa wutar ta mai tayi shigewarta dakin data kwana jiya
laila na tsaka da tunani sajida ta fito hannunta dauke da jallop din makaroni daya sha kayan vegetables da busashshen kifi sai kamshi yakeyi
qarasowa tayi kusa da ita taja mata dan qaramin center table din dake gefen kujera ta ajiye mata abincin tare da komawa ta qaro mata ruwa da lemo ta na ajiyewa ta zauna ita kuma laila ta sauke gwouron numfashi tare da fara cin abincin
saida ta gama tsab kafin ta kalli sajida tace
qawata wani abu nagani a gidanki daya dagamin hankali
.cikin razana sajida tace me kk gani ?
wata yarinya nagani yanzu ta dawo da alama kanwar mijinki ce naga daga makaranta ta dawo sajida ina tunaninki ina iliminki da wayewarki suka tafi tun yaushe aka daina yayin 'yar zaman daki wannan budurwar yarinyar ai kawota kawai akayi ta hanaku sakewa inba haka ba su dai ba ci suka rasa ba ba sha ba bare ace sun takura ne suka kawota nan dan haka wlh kisan abinyi ke banda ma uwarsu daya ubansu daya ai da sai ince ko kawota ma akayi ta gama gane miki sirri karshe ta aure miki miji
rasssss gaban sajida ya fadi tare da nazarin maganar laila
ganin yadda duk yanayinta ya fara canzawa yasa laila qara dogon sharhi aikuwa nan sajida ta fada mata tsakanin habeeb da dije da dangantakarsu ai kuwa nan laila ta dinga kwarara wa sajida ruwan zuga tare da fadi mata illar zama da dangin miji dan mijinki na babba sai a kawota nan a kaita gidan naseer mana nan sajida ta fada mata yadda suka kwashe dasu naseer
tab iskancin banza ajanun banza aljanun wofi mu za'a gwadawa aljani ni danayi gadonsu dari ba daya ne akan kakata data mutu suka dawo kaina dan dama tun tanada rai munfi da ita shiyasa koda ta mutu suka ce ni suke so wlh duk qaryar rashin mutunci takeyi yarinya qarama da kicifi tun yanzu
ganin yadda laila ta dage tanata zazzaga masifa ne yasa sajida fara lallaminta domin da alama akwai aljanun fa a nan dan yadda ta fara daga murya
itako dije tunda ta shiga daki tayi wanka ta canza kaya ta nufo falon domin nemawa kanta da'amin inji ta saita tsinkayi maganar da laila keyi saida ta gama ji tsab har takai lokacin da sajida ke rarrashinta babu wanda ya lura da fitowarta direct kitchen ta nufa tana shiga ta shiga gyara duk wani abu da sajida ta bata tare da dora nata girkin kasancewar kitchen din rufe yake hakan yasa basuji kamshin girkin ba bare kuma girkin na mugaye ne dama dirka dirkan kulolin data gani ta dauka ta juye a ciki shinkafa ce fara sai miya datayi leqowa tayi falon inda ta gansu laila har yanzu tanata ma sajida famfo qara lababawa tayi ta dauko abincin cikin sanda ta ajiye saman dinning din kafin ta koma kitchen din ta gyara sji fes kamar ba'ayi amfani dashi ba
kafin ta kuma lababawowa ta shige dakinta tare da mayar da unifaom dinta sannan ta fito da rarrafe ta zagaya bayan kujera ta labe
jin kamar qofa tayi motsi yasa su saurin waigawa sajida da zuciyarta ke kusa dan sai ysnzu ma ta tuna da yarinyar cewa tayi gida zata tafi to uban me ya dawo da ita bari ta tashi taci uwarta kawai inya so ta kadata ta koma gidan su nasir suje can su qaraci gayyar rashin hankalinsu can inma kashe su aljanun zasuyi su kashe su sai me nan ta miqe laila ta dafa mata baya suka nufi dakin suna zuwa suka tura qofar ga. mamakinsu bakowa toilet sajida ta nufa ta shiga fadin ke khadija !! khadija!!
jin shuru yasata tura qofar ta leqa bakowa cike da mamaki ta juyo ta dubi laila tace kika cemun ta dawo kuma?
ban gane nace miki ta dawo ba to karya zanyi miki ko me?
ta fada cikin hade rai
to kuma gashi bata nan duk da nasan munyi magana da habeen da safe cewa gida zata wuce
toh nidai naga yarinya ta shigo kuma da unifaom fara ce siririya ko
tabbas itace amma ai muna falon ko dai kafin in fito ta fice baki lura ba
wlh ba wani fita datayi dan tana shigowa kina fitowa sai dai in wani salon munafircin ne na qannen miji kinga irin abinda nake fada miki ba nan fa suka shiga neman dije gani duk sun leqa basu ganta ba yasa sajida fara zargin kodai aljanun laila ne suka fada mata qarya gashi ba damar tace ah ah tasan halin laila yanzu sai su hau sama ganin basu ganta ba duka cike da mamaki suka fito suna tunanin ina ta shiga
itako dije tun shigarsu dakin ta miqe ta koma kitchen nan ta hau safa da marwa na shirya kaya a saman dinning duk wani ruwa da kalar lemo saida ta hada a gurin saisa ya cika tab da kayan ciye ciye kafin tayi saurin fita zuwa qofar falon ta cake tana jiransu fito
tana daga tsaye taji alamar sun dawo falon dan haka ta turo kofar ta shigo da sallamarta tare da nuna alamun gajiya a tare da ita
kallonta suka shiga yi musamman laila da taga yadda ta shigo din itako sajida ta shiga karyata maganar laila dan duk wanda yaga dije a wannan lokacin yasan dawowarta kenan basu gama tunanin na sukaji dije ta buga tsalle tare da fadin
yehhhh dan dunga yaushe kuka karaso bayan saida nace ku bari mu taho tare ashe kun sato hanya kun taho lah ashe akuyatu ta fanshe ni dan tayi muku girki
dukansu juyawa sukayi suka kalli inda take magana
ganin gima giman kuloli ga dinning din cike da kaya yasa sajida sakin qara tare da nufar bayan kujera dan ta buya itama laila ta mara mata baya
habeeb ne ya shigo dauke da sallama a bakinsa inda yana shigowa yaga dije tsaye na fadin
aunty laila taso ga dan kutungayya wannan aljanin dake saki yawan munafurci yana son ku gaisa
da kyar ya mayar da
kofar ya rufe inda ya saki baki yana kallon sajida data leqo kai jiki na karkarwa
ganin hakan da yayi yasa shi fahimtar yarinyar nan ce yanzu hska tayi musu wani abun dan yasan iskancinta ai kuwa yau saita ci ubanta daga yau bazata qara ba nufarta yayi gadan gadan da niyyar cafkarta ya nadeta kawai sai gani yayi tayi gurin dinning tana fadin kada ki damu darwanatu ai kowa zai ci abincin nan waya isa kiyi girki aki ci duk ds nasan duk kayan 'yan gidan ne
ah ah kada ku damu basai kun kawo naku ba ku barmu da namu kalar
kutttt habeeb ya hadiyi wani yawu dan sai yanzu yakai dubansa ga saman dinning dinsu wanda yaga dirka dirkan kuloli ga kuma kayan ciye ciye nan tab akai dubansa yakai ga sajida wadda ya zuwa yanzu banda rawa ba abinda jikinta keyi cikin rada ya shiga tambayarta abinda ya faru hankali ta fada mishi duk abinda tasani da yadda laila ta fada mata dawowar dije da kuma yadda ta duba basu ganta ba
jin murysr dije sukayi na fadin ah ah ai basai kun dauko su ba dukansu yanzu zasu taho muci gaba daya ai kada ku damu dukansu na jin haka suka juya da niyyar kwasa da gudu amma me? kafin su kai ga fita suna rige rige da gwara kawuna dije tayi caraf ta riqe habeeb wani ihu ya saki dan in baku manta ba na fada muku habeeb akwai tsoro
dariya dije takeyi iya yinta ta kuma riqe habeeb wanda ya kama ihu iya yinsa tare da karanta ayatul kursiyyu a fili naseer da yusra ne suka fito daga part dinsu jin ihun naseer ganin laila da sajida sun rukunkume juna suna rawar dari a bakin falon yasasu qarasawa tare da tambayarsu lfy duk sun kasa magana inda naseer yayi ta maza shida musa me gadi da shima ya karasso yanzu jin ihun me gidan suna shiga suka ga dije zaune dirshan a gaban habeeb ta riqe masa maka kam tana dariya harda kwalla shiko ya bude baki yana ihu da addu'a naseer yasan kwanan zancen dan haka ya kasa qarasawa sai musa ne ya qarasa koda ya isa nan ya tsugunna ya fara bawa dije haquri domin yasan wannan aikin na jinni ne
kallon sa tayi tace nice dai dijen da ka sani ga dai aljanun can akan dinning suna walima
kallon gurin duk sukayi suka ga abinda ke kai kowa yafara zufa yana neman hanyar fecewa inda habeeb najin muryar musa ya shiga magiyar yace ta sakeshi
zan sakeka amma su dan dukununu sunce yau sai mun tayasu murnar zagayowar haihuwar dan autan su dan haka dole kowa na gidan nan ya zo yaci abin cin can
nan aka shiga kallon kallo su kuwa matan na waje tuni suka sheqa pary din yusra suka kulle inda sajida ta dubi laila tace kin gani ko gashi nan harda irin na kanki sunzo min gida ina zaman zamana gashi kinsa sun kawo ziyara kin san suna binki meyasa kika zomin bayan kin san ni dul lamarin iska tsoronshi nakeyi
cikin kuka laila tace wlh ni banida aljanu ki dena jamin jaraba kada suji su dafemin
ina na kan naki dari ba dayan ?
ai sun barni tun da aka yayeni wayyo ni wlh gida zan tafi tunda abin harya kai haka baxan kara zuwa gidanki ba ashe har uwar aljanu kk aje a gida
duk kansu tsorace suke sunata kukan nadama wai🤣
su kuwa mazan nacan dije fa tace sai kowa yaci abincin nan kafin su dan dukununu su bar gidan nan jin in ba'aci bazasu tafi ba yasa habeeb saurin amsa duk zasu ci shidai tunda ta sakeshi
a gaba tasasu suka nufi dinning inda musa jikinsa ke bala'in rawa hakama naseer suna qarasawa sukaja kujera da niyyar zama dije ce ta da karfi tace ya naseer ka jefar da tunguji ba ruwana
da sauri ya ja da baya tare da kwalla kara habeeb da yake kokarin zama ji yayi tace shikenan ya zauna akan iya tsibbanatu qara yayi tare da zamewa qasa ji kakeyi kwal ya kwale da gefen table din yayin da qugunsa yayi qara.......
*vote*
*comments*
*wit 08066364077*
*Alqalamin khady*
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
TA ME GARI
na
khadeeja usman
1⃣9⃣
naji rokonku masoya amma kuyi haquri bazan iya yi muku typing sau biyu a rana ba ku tuna fa dukanmu matane munada uzuri a gabanmu karantawa ba wahala cikin qanqanin lokaci zaka gama amma typing akwai wahala ina son nishadinku shiyasa na ke bada lokacina nake muku typing fatana kuyi haquri mu qarasa da yadda muka fara idan nasami dama zan iya yi muku fiye da biyun ma a rana
wata azaba yaji amma ba halin yin ihu ya zuwa yanzu dan duk a rude yake ganin yanayin da duk suke ciki yasa dije cewa
lah sannunku kunga fa yanzu sun fara fushi gara ku tashi a gaggauta walimar nan su kama gabansu kaga dan dukununu kuyu haquri ku debo naku kujerun ku basu wannan su zauna ta fada tare da qara gyara zaman kujerun gurin
cikinsu duk wanda ka kalli fuskarsa kasan kadan yake jira ace arrr ya arta dan haka cikin himma suka fara qoqarin zama a dan dosane
itama dijen zama tayi ta kame guri daya tare da fadin toh ku zuzxuba mana arwanatu
😳 sukayi sunata raba idanu jin ta ambaci a zuba abincin kowanne yana kissima yadda zai kwashi wannan girkin na aljanu itako dije ta kame tana kallon kowa a ranta banda dariya ba abinda takeyi
can kuma sai ta miqe zumbur kamar wadda ta tuna wani abun suma miqewar sukayi dan su yanzu duk wani motsin yarinyar tsoro yake basu ganin duk sun miqe ne suma yasata fadin ina kuma zakuje?
binki zamuyi cewar naseer da kyar
ai nima ba tafiya zanyi ba zanje ne na kirawo matanku suzo su taya autaress murna suma
yauwa Alhmdllh dan Allah kirawo su din
cewar habeeb da ya zuwa yanzu ya dora laifin faruwar komai akan sajida dan a bayanin data masa ya fuskanci bakuwarta ce silar komai
toh ku koma ku zauna mana in kirasu
duk komawa sukayi suka zauna inda ita kuma tasa kai ta fice a falon ta nufi part din su yusrah dan tasan suna can
tana fita naseer ya kalli habeeb cikin marairaicewar fuska kamar zaiyi kuka yace bros nifa wlh lamarin yarinyar nan tsoro yake bani wannan wace irin masifa ce tunda muka fara ganin yarinyar nan bamu taba wanyewa lfy ba wannan ai ita ce da tauraruwa me wutsiya gani yayi habeeb da musa nata mishi alama daya yi shuru sai daga baya ya fahimci me suke nufi ganin musa nayi masa nuni da saman dinning hannu yasa da sauri ya kama bakinsa kamar qaramin yaro suka shiga raba ido🤣
tana zuwa part din ta shiga kwankwasawa laila da sajida da suke jiran tsammanin warabbuka sukayi saurin nufo kofar dan sun san yazuwa yanzu komai ya kamalla barin ma laila data matsu tabar gidan dan ita yusra ta shige daki ta kulle kanta ta shiga kiran wayar mamy amma bata daga ba
da sauri sajida ta bude kofar batare da tambayar waye ba aikuwa sukayi ido biyu da dije da gudu ta nufi ciki inda suka fara rige rigen tserewa ita da laila amma dije ta shigo tana fadin meye haka aunty ?
jin tace Aunty kuma cikin muryarta ya dan sa sajida tsayawa amma ita kam laila tayi bayan kujera tanata rarrafawa dan ta samu ts fece
jiki na rawa sajida ta tattaro karfin halin daya rage mata tace ya...ya...akayi ina su habeeb
kallonta dije tayi kafin tace ban gane ina su yaya habeeb ba gasu can a part dinki yayi baki yace in fada miki wai in kin gama gudun tsoron kizo ku gaisa
kuri tayi tana kallon dije jin cewar har habeeb yace ta zo yasata yin tunanin komai ya zama normal ba mamaki malamai ya kirawo ai gara ayiwa gidan addu'a gaba daya da alama komai ya lafa dan taga yarinyar ta warware dan haka cikin dan qarfin hali ta maze tace toh jeki ina zuwa
ok ta fada tare da fadin ina Aunty yusrah itama yakamata taje a gaisa da ita dan bakin daga family dinmu ne na qauye
toh bari na kirata tana ciki cewar sajida data juya ta nufi dakin da yusra ta kulle tana zuwa ta shiga buga qofar yusra dake can bayan gado manne da waya ta qanqame jiki tanata faman kiran wayar mamy wadda sai yanzu ta samu ta dauka tana dagawa kuwa yusra ta shiga fadin pls mamy kizo ki taimakemu wlh jaraba da annoba kika kawo mana ashe cikin kwana daya datayi a cikin biyun da kkk ce tasa kowa yasan da zamanta mamy pls n'd pls kizo ki dauketa ta koma gidan ni nayafe mata duniya da lahira
jin da mamy tayi yusra na kuka yasata fadin calm dawn mana yusrah ki ci ubanta mana karfinki tafi ko kuwa shi naseer din tafi qarfinshi ne iye
bazaki gane ba mamy duk yadda na fada miki nidai dan girman Allah kizo ki dauketa
.to amma ai naji tace wa daddy'n ku ku kukace ta zauna tayi muku kwana biyu dan haka ma nabar maganar dawowar tata
wlh mamy na rantse da Allah bani bace wall.....kinga ya isa wai meya ke faruwa ne kk kuka haka dukanki takeyi ko yankar naman jikinki
wlh mamy ni gara ma ta dakeni da masifar da nake gani nidai mamy kizo ki dauketa dan Allah suna tsaka da maganar ta tsinkayi bugun kofa aikuwa ta fashe da kuka tare da fadin kin ji ta ko mamy dan Allah kiyi sauri kixo
jin haka da mamy tayi yasata saurin kashe wayar ta miqe dan ta sanar da daddy su taho
jin taki budewa ne yasa sajida yi mata magana saida taji muryar sajida kafin ta bude tana leqo kai tace ya ake ciki
dan juyawa sajida tayi bayanta taga dije bata hangota nan ta sanar da yusra sakon da dije ta sanar mata
tab wlh ba inda zani
ah to ni ina ruwana kiyi zamanki kin san dai ba mamaki malamai ne suka zo daga kauyensu dan inaga sun san da zaman lalurar ta inaga shiyasa sukayi addu'a muma gara muje kar abin ya shafe mu bayan sun tafi tunda abin har yakai ga ana min girki da walima a gida ai ni nafi kowa shiga uku
sun dan jajja kafin yusra ta yadda ta fito da kyar laila ta fito a bayan kujera suka bi bayan dije kamar abin magani amma ganin ko'a jikinta yasa su yadda da almatsutsan sun sauka ya zuwa yanzu
koda suka qarasa part din nan aka shiga kallon kallo kowa ya kasa shiga sai da dije ta juyo ta kalle su tace ya haka ku shiga mana
laila ce tace ah ah ni daga nan ma wucewa zanyi ki mikomin jakata da takalmi in kin shiga Allah ya bada zaman lfy
ai wlh baki isaba sai dai ki shiga ki dauka in kin matsu
wace matsuwa nayi ai ba dole a mota fa nike kinga bari in tafi a haka na turo daga baya a karbar min
dije ce ta kalleta tace haba aunty ta ya zaki shiga mota a haka ba takalmi me yayi zafi haka ?
ai ni sai yanzu na tuna ma ashe bada takalmi nazo ba suna mota har jakar
sakin baki sajida tayi tana kallon laila da duk ta birkice kamar ba itace daxu ke ruwan bala'I ba dan haka cikin quluwa tace ah ah tsirara kika shigo gidan ba takalmi ne kadai baki zo dashi ba amma ai karki manta mukullin motar na ciki ko?
innalillahi wa'inna ilaihir raji'un cewar laila a fili
ba yadda ta iya dole suka tura qofar suka shiga suna shiga suka hangi mazan tsaye kamar ace arr su arta ita ko dije suna shiga ta mayar da qofa ta rufe tare da fadin sannunku da zuwa ku qarasa ayi walimar daku ku kadai ake jira
nan fa guri ya hautsine zasu sa ihu tace lah aunty kada kuyi ihu wlh kunayi zasu sa bakinku ya qara girma
nan fa jikin kowa yahau makyar kyata kasancewar dinning din kujeru takwas ne nan tajawa kowa daya ya zauna duk wanda ka kalla matsar kwalla yakeyi inda duk suka dubi kayan dake gurin wanda suka kalli kwalbar carbont din dake gurin gaba daya sai idanunsu yake musu gizo suke ganin kamar jini ne🤣 kunji fa sharri😜
bude kular tayi ta leqa 'yar mitsitsiyar shinkafar dake can kasan kular ta hango dan dama fa iya wadda zata iya ci kawai ta dafa jaraba ce tasata zubawa cikin wannan kular
lahhhh amma ko baku kyauta ba akuyatu ai bani kadai nace muku ku ragemun ba suma fa duk zasuci irin girkin ku amma shine kuka rage iya cikina ta fada tare da dan hararar kujerar daba kowa
jin ta ambaci an cinye abinci sai ita kadai aka ragewa yasa kowannensu hamdala a zuciyarsa juyowa tayi ta kallesu taga duk sun kafeta da ido dariya taso kwace mata amma ta danne tace toh kunga har sun gama cin nasu abincin kunyi jinkiri amma ai ga kayan drinks nan kuci ni bari inci wanda suka ragemin din nan ta shiga kokarin zuba shinkafar harta gama ta fara ci cikinsu ba wanda ya motsa bare ya dauki wani abun
shi kam musa ji yakeyi dazai samu dama da inya fece bamai sake ganinsa tunda aikin gadin ba dole bane
itakam dije tanata cin abincin ta hankali kwance su kuwa sai muzurai sukeyi
sai da ta gama tasha ruwa kafin ta juyo ta kallesu tace sunce tunda baku cin irin wannan bari su kawo muku irin nasu
da sauri aka shiga rubibin daukar abin ci inda saboda tsabar sharri habeeb daya dauki apple wai jinta yayi kamar goribar data bushe wai kawai dan ta aljanu ce🤣
kowa a gurin yana shan abu kamar magani kuma yana kuka itako dije sai surutun ta takeyi ita kadai hakan ke qara firgita su sukuwa suka shiga 'yammatan hawaye
su mamy na qarasowa suka shiga yin horn jin shuru ba'a bude ba yasa habu fitowa ya bude gate din da kanshi ya shiga da motar
mamy cikin tashin hankali ta bude murfin motar ta fito ita da daddy wanda suka nufi part din da basu san ko na waye a ciki ba suka shiga bugawa
jin ana buga kofar da dan karfi ga alamar magana yasa su naseer qara rudewa dan duk a tunanisu ko abincin da suka ki cine abubuwan suka gayyato wasu
dan haka suka qara kidimewa tare da qoqarin tura duk abinda ke hannunsu baki
dije ce ta miqe ta nufo kofar a ranta tana fadin wane me tsautsayin ne kuma
tana bude qofar taga su daddy mamy na qoqarin tureta ta shiga tana fadin suna ina?me kk yi musu jin muryar mamy ne yasa yusra da su naseer bude murya suka sa kuka.......
*kai kai naso inci gaba amma....*
*vote*
*comments*
*with 08066364077*
*Alqalamin khady*✍
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
NA
Khadija usman
2⃣0⃣
*A gaskiya mutane basuyi mana adalci ba duk da nasan masu qarancin ilimi da tunani ne sukayi abinda sukayi kowa fa da ra'ayinsa duk wadda taga bazata iya novels kyauta ba ra'ayinta ne ban kuma ga laifinta ba haka mu da mukaga zamuyi kyauta muma ra'ayinmu ne dan haka bai kamata ayita magana daya ba har takai ga anyi mana rubdugu ana zagin iyayenmu gaba daya dan girman Allah ina rokonku ku dinga mana adalci reader's ku duba irin wahala da westing time din da muke yi duk dan mu faranta muku ina rokon afuwar duk wanda magana ta ta batawa rai🙏*
cikin rudewa da tashin hankali mamy ke fadin ya salam me zan gani haka me yake faruwa ta fada tare da qarasawa cikin falon ta nufi inda su yusra suke
daddy ne ya shigo shima inda dije na ganinsa ta shiga yimasa sannu da zuwa cikin nuna farin cikin ganinshi ta fara fadin oyoyo daddy gwamma da kuka zo wlh kunzo a dai dai sai ayi tare daku
daddy ne ya dubi sauran mutane yaga yadda fuskokin su suke amma kuma yaga dije qalau da alamun farin ciki a tare da ita ga kuma mamy data azalzaleshi cewar ba lfy gidan yaran ya taso suje dan haka ya juya ya kalli inda mamy take tana tambayar yusra dake ta kuka me ke faruwa
caraf dije tayi tace ai wlh daddy ban san haka nake da farin jini ba sai yau kai wlh naga soyayya kasan fa yau na cika shekara goma sha bakwai to ni nama manta sai dazu na tuna shine nake fadawa yaya shine fa yace wai dole sai anyi qaramar walima toh shine fa aka dan hada kayan sha wai kafin su shiryamin bikin birthday din wai shine fa Aunty yusra tace bata yadda ba a gidan ta za'a shirya party din shine itama aunty sajida tace ah ah sai dai ayi anan toh shine fa aketa rigimar yanxu haka ashe har kun samu labari
duk qamewa sukayi jin abinda dije ta karkace baki tana fadi yayin da yusra ta tsaida kukanta dan bataga amfanin yinsa ba ya zuwa yanzu kutmelesi lallai wannan yarinyar kashesu zatayi kawai
itako mamy jin abinda dije tace ya qara bata ranta wato ma har rigima yaranta keyi dan kawai su shiryama wannan me kama da mutanen boyen party lallai ma wato dai inta fahimta saude da yunusa ba qaramin shiri sukayi ba kafin su turo yarinyar nan duba da yadda komai yake tafiya game da yarinyar daga kan daddy yanzu har gashi yaranta ma zasu fara dawainiya da ita kamar ba su ne suke nuna tsanar yarinyar ba a fili a bar ma tasu to matansu fa ji yusra yanda take kuka ashe ma akan wannan ne take cewa ta zo yarinyar zata kashe su to sbd kawai ba'ayi iskancin tuna ranar haihuwar bane a gidan su ko kuwa? lallai yazama dole ta dauki mataki dan wannan yarinyar daga ganinta ba alkhairi bace
daddy ne yace kai amma yaran nan kun fiya shiririta wlh kai yanzu habeeb harda kai da girmanka akayi wannan abin dakai habeeb da tun dazu yayi zugum yanata raba ido sbd tsoron Allah yayi masa yawa yama rasa gane inda batun ya dosa sai da ya ji muryar daddy na fadin wlh dai in an girma asan an girma yanzu dai kun ajiye iyali dukanku ba yara bane yanzu gashi ina zaman zmana kun tasoni akan wani shirme naku
dukansu shuru sukayi suka shiga rarraba idanu domin kuwa ba halin suce qarya ne ba haka bane aljanun dake wurin suyi kulin kulifita dasu suce sun qaryata uwar dakinsu dan haka kowa ya shiga mirgina kai da raba ido ita kam laila fatanta bai wuce ta bar gidan ba
dije ce ta katse wa kowa tunanisa inda tace cikin 'yar shagwaba daddy ku taso kuma ayi daku
ah ah ni bada ni ba cewar daddy wannan aikin ku ne na yara a dai bani ruwa ya isheni
miqewa dije tayi ta dauko masa gorar ruwa ta dauki cup ta zuba masa inda ya karba yana kaiwa baki da niyyar sha yaji naseer na fadin kada kasha daddy pls
sauke kofin yayi kafin yace sbd me ?
kafin ya bashi amsa dije tace sbd tunanisa akwai sanyi ne to babu wani sanyi ka dauka ka fini son daddy din ne dazan bashi ruwan dazai cutar dashi kaga ya naseer wlh ba ruwana idan ka hadu da fushin......hmmm bari dai inyi shuru ta qarasa maganar tare da kashe masa ido tana dariya kasa kasa
ganin yadda tayi ne yasashi yin gum da bakinsa mamy dake gefe duk tana lura da yadda komai ke faruwa ganin hakan yasata sakin ranta tare da fadin
oh wato daddy'n ku kadai kuka sani ni ko tayi ma ba'aminba to ba damuwa godiya nake
ah ah mamy wlh ba haka bane cewar habeeb munga kamar a koshe kike ba kya buqata
au dama ana gane mutum ya qoshi da ruwa kenan?
ah ah no ba haka bane barii inje in kawo miki wani ya fada yana qoqarin mikewa duk tana hankalce dashi hakan yasa ta shiga nazarin tabbas akwai abinda ke faruwa boye mata sukayi dole ne kuma ta bincika dan haka saita maxe tare da fadin no shi wannan ba nasha bane
ai duk sunyi expire cewar sajida dasai yanzu tayi magana tun shigowarsu duk mamy ta karanci halin da kowa ke ciki
expire kuma duk kayan gurin
eh wlh habeeb ya fada da sauri
musa ne ya mike tare da fadin to ni fa zan koma bakin aiki wanda a ransa ya ayyana yana fita hada kayansa zaiyi yayi kauye bai ko jira amsar kowa ba yasa kai ya fita aikuwa yana fita dije tabi bayansa yana gab da shiga daki yaji ta kira sunansa aikuwa da gudu ya afka dakin be ko tsaya rufewa ba jiki na rawa daga labulen dakin tayi ta tsaya daga waje kafin ta dan leqo kanta tace nasan ya zuwa yanzu so kk yi ka bar gidan nan ko to wlh kasake ka bar aiki a gidan nan ko kasa kafarka ka fita sainasa inna arwanatu ta shanye mun qafafunka da hannaye inga ta inda zaka moru inka musa ka tafi din tana gama fadar hakan ta juya ta koma cikin gida musa kuwa kuka ya shiga yi harda sharbar majina ganin hakan bazai fishsheshi ba ya miqe ya dauki buta ya daura alwala ya samu guri ya zauna a cewarsa gara ya dinga zama cikin tsarki da alwala shina kariya ce nan ya shiga karanta ayatul kursiyyu
tana shiga ta tarar da daddy ya mike yana fadin tafiya zaiyi dan ita mamy tace ya wuce sai anyi murnar da ita jiki na rawa laila ma ta miqe ta dibi kayanta dan tasami hanyar kubuta ba wanda taiwa sallama ta fice
daddy har yakai bakin kofa ya tsinkayi muryar habeeb na fadin am daddy dama maganar khadija ne
dakatawa daddy yayi tare da juyowa dauke da murmushi akan fuskar sa yace ai kada ka damu tayimin bayanin komai nan da can ai duk dayane
da sauri habeeb yace daddy baka fahimceni bane ina nufin batun....caraf dije tace wai batun zuwa makaranta ta ai nayima principal bayani kada ka damu nace a dinga zuwa daukata
da sauri naseer yace a dinga zuwa daukarki kamar ya?
eh ai kasancewar na dawo nan da zama shine naga ba sai anyi wahalar daukar min driver ba kawai su dinga daukata da motar ina
gidan wa kk dawo da zama suka fada da bayyanar tashin hankalin maganarta a fuskokinsu har suna hada baki
sai dai in gidan naseer cewar habeeb
ah ah gidanka dai
naka dai
jin suna neman kwafsa mata yasa ta fadin kai brothers meye haka in dai dan nice kada ku bata ranku ina gidan kowa zan iya yini nan in kwana can ko kuma in dinga kwana daddaya ko bibbiyu dan haka daddy kada ka damu bari in bika in kwaso sauran kayana daya kamata tana gama fadar haka ta fice tayi wajen mota daddy kuwa juyawa yayi yace to sarakan rigima ni ba ruwana gata nan ta raba muku rigima ai
yasa kai ya fici yabarsu duk da bugun zuciya
mamy da duk abinda akeyi bata ce qala ba saida daddy ya fita kafin ta kalle su tace su zauna kowa ya zauna ta dan jima kafin tafara magana tace ina son sanin abinda ke faruwa a gidan nan tsakanin jiya da yau dan idona ya ganmun wasu ina son qarin bayani dukansu suka shiga rattaba mata bayani kuwa
jinjina kai ta shiga yi tare da naxari zuwa can ta nisa tace idan na fahimta wannan yarinyar annoba ce kenan a gida na nasan aninda zanyi badai tace zata dawo nan ba da zama to yau zan fada muku abinda zakuyi mata tasan ta dawo da zaman kamar yadda ta buqata nan ta shiga yi musu bayanin tare da fada musu matakinda zasu dauka dazai sa sai dije ta koma kauye da qafarta ta fada tare dayin kwafa ta miqe tayi musu sallama ta fito su habeeb suka biyota inda ta shiga motar habeeb danya maidata gida
itako dije koda sukataho ita da daddy ta sanar dashi tana son yasai mata waya koda qarama ce dan su dinga gaisawa tunda yanzu sun danyi nisa ba musu kuwa suka shiga wani shagon saida waya ya siya mata qarama dai dai ita a cewarsa saita gama secondry kafin yasai mata babba harda layi yasai mata kafin suka wuce gida suna zuwa kuwa ta shiga hada kayanta baseera tayi kewar rabuwarsu amma ta tausayawa su habeeb da zasu zauna da dije
komai nata saida ta hada tsab aka loda a mota ta ta shiga ita da habu driver ta nufi gidan su habeeb....... ...........
*wlh drmar nan fa yanzu aka fara kudai ku biyoni*
*vote*
*comment*
*with 08066364077*
*Alqalamin khady*✍[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
TA ME GARI
NA
khadeeja usman
2⃣2⃣
kai kai kai gaskiya na fuskanci mutane ma sunfi son dije dani zan fa koma 'yar adawarta dan na fuskanci hmmmm bari dai kawai nayi shuru
bazan gaji da nuna farin cikina ga daukakin masoya tame gari ba a kullum ina ganin sakonni tare da kira ban san adadi ba ngd da addu'oinku gareni ina matuqar sonku tare da ji daku
****
luv birds suna manne da juna suna sallama an rako miji suna qarasawa bakin qofar falon sajida aka shige gaba ana kwarkwasa aka zira key dan a bude ji tayi yaqi shiga shiko habeeb dayake ganin kamar tana hakan ne dan qara salon jan hankalinsa yasashi fadin pls baby aimun afuwa a barni haka kin san sauri nakeyi
cike da salo wai ita irin baby din nan tace wlh ba haka bane sweety key din ne yaqi shiga ban san dalili ba
qarasawa yayi ya karbi key din ya shiga zurawa ganin da gaske fa yaqi shiga yasa shi qara azama amma still dai haka
haka ma a bangaren su naseer suna can suna kokawar bude qofa amma taqi buduwa
dije na tsaye tana jin ki..ki..ki ..ki anata dannar kofa jin sun jima sunayi tasan ya zuwa yanzu duk sun wahala ransu ya baci dan haka ta qarasa jikin qofar tare da kwankwasawa da sauri habeeb yace waye ?dan ya matsu ya fita
ni ce nan cewar dije
hasbunallahu wa'nimala wakeel ya fada a fili wannan jaraba har ina wato yarinyar nan dawowa tayi kenan kamar tasan meyake fada a zuciyarsa sai ji yayi tace
ina nan dama ba inda naje anan na kwana badai ni kuka sa na kwana a waje ba to naji ni na kwana a waje cikin duhu da sanyi da sauro to ku kuma ku yini cikin haske da A.C ga fanka ba sauro bare kuda kuzauna kuyita kallon juna ta qarashe maganarta tare da yin dariya tace wlh kuma naga wanda zai bude ku muddin ina nan a haka zaku tabbata ni naji ina nan zan dinga kwana a nan waje ku kuma kuyi zamanku cikin gidanku ai yafi
jikin window suka dawo habeeb yayi slide dinsa tare da leqowa yafara mata magana cikin bacin rai dan ya zuwa yanzu yafara tunzura da lamarin yarinyar gara kawai yafara cin ubanta inya so kome zai faru ya faru ba aljanu ba ko kukar bulukiya ce akanta be shafeshi ba
keeee dan ubanki ni sa'an wasanki ne ya fada yana me nunata da yatsa ta ciki
ah ah kai ba sa'an wasana bane dan inaga lokacin da aka haifeni ma kai ka zama saurayi da ace ma anyi auren wuri da an ajje kamata
kai ya fada tare da dukan qarfen dake tsakiyar jikin window wlh idan baki zo kin bude qofar nan ba wlh wlh kinji na rantse sainayi miki abinda iyayenki bazasu gane ki ba dan zan manta da komai inci uwarki
yatsina fuska tayi tare da fadin iyayenmu bazasu gane mu ba dai dan yaseen sai dai a qona gidan nan ta fada tare da juyawa ta nufi part din su naseer wai ta leqo su suma
tana zuwa suma ta kwankwasa suma haka ta rattaba musu bayani sai dai sabanin habeeb shi naseer hakuri ya shiga bata tare da rokon ta budesu ya shiga sanar mata meeting garesu kuma wlh in basu halarta ba zasu sami matsala
tunani tayi taga ko ba komai bai kamata tayi musu haka ba coz wannan fannin da ban amma kuma sai dai naseer yafi habeeb dan shi ya karaya da wuri ya bada kai bori ya hau dan haka nan ta shiga kici kicin kunce igiyar amma ta kasa tana tsaka da haka ta hango habeeb ya nufo gurin da take gadan gadan cike da mamakin yadda akayi ya fito ta kwasa a guje tayi hanyar gate ya so binta amma ya kasa dan shi bazai iya gudu ba sam duba da yadda yaga ta zura a guje kamar iska na qara mata gudun
kwafa yayi tare da qarasawa bakin kofar su habeeb da suma suke ta leqe ta window kamar maguna cikin dan zafi yace kai kuma dayalla malam saika bude ta kitchen ka fito sam naseer ya ma manta da wata qofa ta baya ta cikin kitchen sai yanzu sim sim ya juya ya nemo key din ya bude ya fito yana fiwo ko kallonsa habeeb beyi ba ya juya ya nufi bakin motarshi shima ganin hakan yasa be tamka mishi ba ya shiga tashi motar shima suka fita
ita ko dije cikin sa'a tana fitowa daga gidan ta ga motar makarantar su aikuwa ta afka aka wulla da ita
***
sam yarasa mafita game da lamarin dije yarinyar da gani kasan batada lfy duba da yanayin kiriniyarta da fitina gashi yanzu inya ce ta koma gida daddy zaiga kamar da wani abu ko ma yaga laifin mamy duba da yadda mamy ke nuna kin dangin daddy to yanzu meye mafita? yana tsaka da wannan tunanin naseer ya turo kofar office din tare da sallama
amsawa yayi tare da yi masa nuni daya zauna suyi magana
zaman yayi duk da shima yana son suyi magana dashi dan ita ta kawo shi amma bari ya fara jin tashi
bayani ya shiga koro mishi akan dije nan yake tambayarshi meye mafita ,?
wlh nima maganar dana zo da ita kenan gaskiya ya ksmata asan abinyi ni a ganina tunda dai yarinyar nan irin naci ce dangin laquwa kawai mu haqura ta zauna din kamar yadda ta nuna ta na son zaman tare damu sai dai mu kiyaye bata mata rai tare da duk wani abinda mukasan zai sa sabani tsakaninmu tunda dai kaga ita dangin ifritai ce da an tabata sai mutum yaji jiki mu samu mu gagganda mu aurar da ita cikin qankanin lokaci dan na fuskanci batada wani wayo kaga saimu dan sami wani galmashuran mu hadata dashi mu lallabata cikin salama a rabu lfy
Ajiyar zuciya habeeb ya sauke tare da fadin to ai duk ba wannan ba a ina zata zauna ? dan ni gaskiya zamanta zai kawomin matsala da sweety na duba da yadda yarinyar ke da rawar kai ita kuma sweety na ga kishi kuma ma ni bana son harkar hayaniya wlh ni ko kallon yarinyar nayi gabana faduwa yakeyi kada taje taci gaba da gayyato aljanun nan suna watanda da kayan gidana dan kaga ko na jiya fa maimakon suzo da nasu to nawa fa duk suka nakasa
jimmmmm naseer yayi ya shiga nazarin maganar habeeb lallai fa akwai matsala to ammaai ko su aljanun in ka lallabasu basa cutarwa a cewarsa
dan haka ya nisa yace wannan ba matsala bane saita zauna inda nake ko?
Alright indai kaga ba wata matsala ai shikenan amma wlh yarinyar nan ko yau dana kamata inaga saina kusa kasheta
dariya naseer yayi yace ka kusa kasheta ita kuma ta kasheka gaba daya ba ko kuma tasa ka kukan.....bari dai nayi shuru ya fada yana rufe baki tare da dariya qasa qasa
to dadin abin dai kowa yanada abin fadi
gaskiya ne amma na wani yafi na wani ba naseer ya fada yana qoqarin miqewa dan tafiya shima miqewar yayi yana fadin na sa an kira me gyaran doors din nan inaga ya zuwa yanzu an gyara
ok ya fada tare da sa kai suka fice gaba daya
*****
itako dije sam ta manta ma da tsiyar data shuka sai da aka kusa tashinsu ta tuna dan haka ta shiga tunanin mafita kawai in koma gida ince wa daddy nafasa zaman nan shi yafi min alkhairi dan wlh wannan me siffar mugun dawan ya rikeni kwanana ga kare yaje ma yayimin rauni a zo aurena a ragemin farashi
to wai ke dije yaushe kika fara tsoro ne kece fa uwar mazga jahannama ga fasinja dije Annoba fitinatu cewar wani bangare na zuciyarta
ke banza da ne nake amsa wannan sunan amma yanzu tunda na fara shan ruwan alwalar la,asar naji nafara sanyi ita kadai take ta surutunta a zuciyarta har aka tashi ta shiga motar komawa gida jikinta a sanyaye
ta jima zaune a unguwar nesa da gidan taki shiga kamar abin dole danma suna ci suna koshi a makarantar amma da yau taci ubanta da yunwa duk da tunanin matakin da habeeb zai dauka a kanta ya hanata sakewa taci abincin
*niko nake su dije anyi laushi ne*😂
tana nan zaune har magariba ta gabato ta hango dawowar su habeeb nan ta shiga neman mafita zuwa can kuwa ta saki murmushi dan tunawa da tayi da wata dabara
qafar wandonta ta shiga nadewa duka biyu zuwa gwiwa ta bubbuda qafafu ta gyara saiti shi kuwa musa ya wangale gate motocin na shiga yayin da matan masu gidan kowacce ta fito dan tarbar mijinta anci kwalliya dan tarbar miji suna gama shigewa musa ya fara qoqarin maida gate aikuwa dije ta kwaso a guje ta nufo ciki yana gaf da ida rufewa ta afko kamar an jefota tana fadin ku gudu gasu nan ku gudu ku gudu ai musa be ko tsaya qarasa turawa ba ya afka dakinsa ya banko ji kake garam
su kuwa mata anata kwarkwasa sun nufo parking space inda mazajensu suka parka suna qoqarin fitowa sukaga ahigowar dije na fadin ku gudu gasu nan ganin yadda take a sukwane yasa naseer da yusra kwasa suma a guje inda sajida ta juya itama da niyyar guduwar shims habeeb haka ji kakeyi kummmm kawunansu ya hadu yayin da hancin habeeb ya fashe jini ya fara biyowa itako sajida bakinta ya bige shima har da jini amma ko ta kan juna basu bi ba suka shiga rige rigen tserewa yayin da ita uwar gayyar tuni ta shige parlor ta tsaya tana mayar sa numfashi a wannan yanayin suka shigo suna kokarin danna kofar da aka gyara dazu suka aa key nan habeeb ya sunkuya tare da safe kai jin jini na bin gefen hancinshi ita ko sajida sai yanzu taji zafi kamar kada ta taba aikuwa taji baki yayi suntum dan da nan jambakin datasa ya hade da jini da maiko abin saiya qarawa bakinta style 😂
sun jima haka kowa na mayar da numfashi kafin dije ta dago ta dubi sajida taga yadda lokaci daya halittar bakinta ta sauya aikuwa duk yadda taso hadiye dariyarta kasawa tayi sai da ta dara dariyar da takeyi ne yasa habeeb dagowa dan tambayarta me takewa dariya ai kuwa shima yayi tozali da bakin sajida da ya samu qarin armashin kwalliya.....
*wayyo cikina*
😂😂😂🤣🤣🤣
*na kasa qarasawa*
*vote*
*comments*
*with 08066364077*
*Alqalamin khady*✍
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
NA
Khadija usman
2⃣1⃣
*A gaskiya banida bakin da zan gode muku masoya ta me gari a duk inda kk ina matuqar alfahari daku ngd sosai Allah ya qara qauna da zumunci luv u all😘*
suna qarasawa gidan habu ya shiga fito mata da kayanta inda ta tsaya tunanin to ina zata dosa gidan habeeb ko na naseer ?kai gidan ya habeeb ya kamata in fara zama tukun musa sai sim sim yakeyi tare da ladabi dashi aka dinga jidi kayan dije zuwa qofar part din habeeb kasancrwar magariba tayi yasa suna gama ajiye mata kayan suka juya shida habu dan yin sallah ita ko dije ta shiga knoking ta jima tana bugawa amma shiru kk ji ba'a bude ba tun dije nayin bugun marmari harta koma yin na qarfi amma still shuru jin ba ada niyyar budewa yasata juyawa ta nufi part din naseer canma bugun ta shiga yi still ba wanda ya bude ta jima anan din ma nan fa ran 'yammata ya fara baci wato ni zasuyi wa haka ko? to ko basa nan ne ta fada a zuciyarta tabbas da alama basa dan da suna nan tasan bazasu ki budewa ba kodan abinda ya faru dazu da wannan tunanin ta nemi guri ta zauna jin ana sallar magariba yasata miqewa ta nufi bakin gate gurin musa ta dauki buta tayi alwala bata ko tambayeshi mutanen gidan na ciki ba ta koma can gefe ta shimfida dankwalinta ta tada sallah
tana tayarwa taji ana danna horn musa ya bude habeeb ne ya shigo aikuwa yana gama parking ya fito ya nufi part dinsa a kofar yaga kayan dije murmushi ya sake tare da fiddo wayarsa ya kira sajida tana dagawa yace zo ki bude nadawo zuwa can sai gata ta bude masa ya shiga suka mayar da kofa suka rufe
saida ta idar da sallarta a nutse kafin ta miqe ta nufi part din ta kuma bugawa shima still banza akayi da ita ta gaji da bugu sannan ta nufi gun musa take tambayarshi ko matan gidan basa nan ne nan yake shaida mata duk suna ciki zamewa tayi ta zauna a ranta tace au wato ni za'ayiwa wulakanci dan na nuna ina son zama hhhh tayi dariya kadan kafin tace yaseen zaku san kunyi min haka nasan duk dan in koma gida ne to wlh ko kasheni zakuyi ba inda zani shi dai musa nashi ido dan yanzu hirar ma dayake yi da ita ji yayi bazai iyaba dan haka yana kallon ta tanata dariya ita kadai be ce kala ba zuwa can ma ya shige dakinsa ya banko bayan ya rufe gate din kamar yadda ya saba
ita ko dije ko 'a jikinta saima tunanin data shiga yi na inda ya kamata ta kwana ta jima zaune a gurin har aka kira sallar isha'i ta miqe tayi kafin ta kuma zama tana neman mafita zuwa can ta miqe ta nufi gurin kayanta jakarta ta zuge ta fito da wayar da daddy ya siya mata gashi bata sata carji amma ai da akwai na ciki bari ta kunna ta yi amfani da ita haka to wai ma uwar me zakiyi da ita din ta fadawa kanta a hasale (niko nace su dije za'a huce haushi akan waya ne) ba kaiii ya salam ta fada a fili nan ta shiga kakkanta sauran kayan tana jansu gefe guda harta gama duk ranta a bace yake kawai tuna irin saqar rashin mtuncin da zatayi musu tasan sun shirya mata hakan ne dukansu an fada musu ita tana jin tsorone wlh nan zata kwana tasan kafin gari ya waye ta yi mafarkin irin abinda zata musu da wannan tunanin ta shiga neman abinda zata shimfida ta kwanta ganin bazata samu ba yasata dauko dankwalayenta da siket dinta dan batada zani ta shiga shimfidawa har ya danyi tudu yadda zata kwanta hijab babba ta dauka ta kwanta ta rufe ko ina na jikinta
*niko nace haba dije sai kace mayya ki koma gida mana*🤣
****"
su kuwa su naseer shawarar mamy suka dauka ita tace suyi mata hakan tasan idan taga basu bude ba dole ta koma gida ai dan haka duk bugun da takeyi suna jinta sun san itace dan tun zuwansu da habu sun ganta itama sajida habeeb cewa yayi ta bari inya dawo zai kirata saita bude masa kawai dan haka duk sun saki jiki ya zuwa yanzu dije ta koma dan sun san dai duk ifritancin ta bazata kwana farfajiyar gidan nan ba ita kadai koda kuwa ita ce aljanar da kanta
***
dije fa dare yayi baccin nan fa ba dadi dan sanyin kasan tiles din ga kuma sauro duk da ta rufe ko ina na jikinta amma sai ta ji kamar suna bula hijabin suna cizonta ga kukansu daya dameta duk ta rasa abinyi oh ni dije na shiga uku ta fada tana me sosa qafarta dataji kamar sauro ya cije ta wlh da da inda zan samu turmi na rantse da Allah da saina dauko shi cikin daren nan na shiga daka koda shinkafa ce inya so kowa kada ya rintsa ta kiyasta kalolin mugunta a ranta sunkai kala hamsin a haka tayita saka da warwara tana ja musu Allah ya isa tare da tunanin me zatayi musu gobe ta huce kuma wlh ko da bala'i saita kwana cikin gidan nan tanata wannan saqar zucin bacci ya kwasheta har akayi sallah bata sani ba sai da sanyin asuba ya kadata kafin ta tashi taga gari har yayi haske salati tayi tare da miqa ta miqe ta nufi dakin musa tana zuwa ta tarar da buta bakin kofar dauka tayi tazagaya cikin flower tayi fitsari kafin ta dawo tayi alwala sai da tayi sallah ta fara shirin zuwa school duk da yunwar da take ji gashi ko wanka batayi ba jiya da dare bare kuma yanzu haka dai ta kimtsa dan tana gudun makara kasancewar yanzu suna S.S.3 ne suna ta shirye shiryen fara S.S.C.E gashi kuma dama dije bata wasa da karatu duk iskancinta dan haka ta shirya ta kankanta kayanta a gefe harta ta juya da niyyar tafiya kuma sai ta tsaya jimmm
dariya naga tayi kafin ta juya ta koma gurin ta nemi guri ta zauna ta shiga fadin wlh na ma fasa zuwa school din in na tafi ai nabar baya da kura kenan hhhhh ta saki dariya kafin naga ta miqe ta ciro waayarta ta kunna time ta duba taga 7:10 dan haka tasan duk inda masu gidan suke ya zuwa yanzu sunata shirye shiryen zuwa office dan haka ta miqe ta shiga zagaye a gidan ko me take nema ohoo
ta jima tana zagaye gidan kafin daga baya ta taga wata igiiya daure daga bayan dakinda alama ta shanya ce dan haka ta je ta fara kokari. kuntowa
tasha wuya kafin ta kunce ai kuwa tana zuwa ta shiga dariya tare da nazarin ta ina zata fara
qofar ta kalla aikuwa nan ta shiga neman salon da zatayi qaramar jakarta ta bude ta dauko kifiyar tsifa nan ta shiga turawa guri. mukullin ta jima tana malqwayawa hada cije baki kuwa har saida taji wani abu yayi 'yar qara kafin ta zare kibiyar wadda ita kanta dan wahalar da aka bata saida ta malkwaye danma irin me kwarin nan ce ta kusa saida ta tabbatar ta gama lalata inda makuli zai iya shiga kafin ta fara neman dabarar daure kofar wata irin dauri tayima kofar na fitar hankali wanda ita kanta in ance ta fadi ta inda ta fara bazata iya ba tana gamawa ta koma part din naseer shima yadda tayiwa habeeb din haka tayi musu duk ta hada zufa sai da ta kammala kafi. ta tsaya ta riqe kugu ta shiga fadin yau sai inga yadda zaku bi ku fito wlh sai kun san na kwana a waje naga me zuwa ya bude ku ta fada tana haki kamar me shirin yin dambe
****
su kuwa dukansu suna ciki suna shiri dan yau sunada meeting da zasuyi dan haka sukayi waya akan kowa ya shirya cikin lokaci sam sun manta ma da wata aba dijeee
*da babu gara ba dadi manage pls*
*vote*
*comments*
*wiith 08066364077*
*Alqalamin khady✍*
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
NA
khadija usman
2⃣4⃣
*har kullum bakina bazai gaji ba haka alkalamina bazai gaza ba wajen nuna godiyata ga daukakin masoya na wlh banida bakin dazan gode muku dashi bisa addu'ar da kukeyimin ina rokon Allah yaqara bani ikon faranta muku Allah yasa ko bayan nagama muku ta me gari kuci gaba da bibbiyata tare da nunamin soyayya fiye da yanzu ina mugu mugun sonku fiye da yadda kuke son ta me gari* 😘
gadan gadan ta nufo dije ita ko sai murmushi takeyi tana tsaye kyam cikin shirin zuwa makaranta
ganin da habeeb yayi dije na dariya tana kuma tsaye tana jiran karasowar sajida babu ko alamun tsoro a tare da ita bare tasa niyyar guduwa hakan yasa yasan akwai abinda ta shirya dan haka cikin daka tsawa yace
keeeee!!!!sajida bana son shashanci me kk shirin yi haka ?
tsayawa tayi cike da jin zafinsa ta juyo tace mataki zan dauka tunda kai ka kasa ta yaya zan zauna qaramar qanwata tana min iskanci wannan wace irin jaraba ce tunda yarinya tazo ta hanani sakewa ni da gidana sannan kai ka zuba mata ido tamkar kana tsoronta to gara na kawo qarshen wannan rashin mutuncin nata wlh nagaji ko ta bar gidan nan ko kuma wlh a fita da ita da ambulance
ido dije ta zaro😳ambulance fa kk ce Aunty na shiga uku kice dukan jinya zakimin to amma bakomai da sauki tunda bana mutuwa bane ko banza na mori zaman jinya dan naga in anje dubiya mutum yana tara abin arziki gashi ko ba komai ka dada samun kulawa gurin dangi dan haka kada ki damu zo ki daki iya yinki har ki gaji amma fa ki lura gurin bugun kada ki dakeni inda zanji zafin da hankalina zai fita in fama miki ciwo naga bai gama sabewa ba ni nama fasa zuwa makarantar zo ki jibgi rabonki yau hau ce ta hauni
rawa zuciyar sajida ta shiga yi jin furucin yarinyar anya kuwa wannan yarinyar ba jinsin shedan bace kai gaskiya da sake lahaulawala quwwata illahbillah Allah ka rabamu da wannan jaraba
shima habeeb a nasa bangaren haka ya shiga zancen zuci duk yadda akayi wannan yarinyar jinsin aljanu ce duba ma da yadda take da kyau ga farinta sak na aljanun sannan ga shegen rashin ji shiyasa ma take ita kadai gun iyayenta dama ance aljanu kishi garesu shiyasa ta hana iyayen haifar jinsin bil adama gashi yanzu ta zo ta addabe su su iyayen nata nacan suna cikin kwanciyar hankali ita kuma tana nan tana gasa su
muryar ta suka tsinkaya tana fadin Aunty tunanin me kk yi kada ma kice na tauye miki haqqinki gurin yin dukan ban barki kinyi yanda ranki ke so ba bari kawai in tube ki zabi inda yayi miki ki daka amma dan Allah ki dan daki gurin nama nama dan kin dai ga yadda nake ba wani naman kirki ne dani ba tana gama fadar haka suka ga ta shiga kokawar cire hijabi tana qoqarin cire jakar bayanta
basu tsinke da lamarin ba sai da sukaga ta shiga kiciniyar daga riga da alamar zata cire
ke meye haka kikeyi bakida hankali ne ya fada a dan hasale
rasss nake yaya kai dai kawai ka tsaya kasha kallo in zaka iya gara kabarta ta huce haushinta amma dan Allah ko da na suma ban samu nasarar ganin yadda aka fita dani aka sani a mota ba ko kuma ganin wanda ya daukeni ba ku taimaka ku dauki hoto ku ajiyemin sannan a sanar da masu zuwa dubiya musamman daga kauye in sun tashi riko abin dubiya su biyo da zabi da kaji kuma danyi kada a yanka ko a soya a kawowa aunty tayimin dahuwar 'yan birni inci in more sannan dan Allah aunty ki lura gurin dukan kada ki taba fuskata ki daki iya jiki sbd kar bakina ya nakasa ya hanani cin abincin daren yau sai dai in sha kunu da safe
*oh su dije jaraba wato magana ta fada musu a fakaice* 😏
ci gaba tayi da kokarin daga rigar wai ita a dole cirewa zatayi wanda inda cirewar gaske ne da tuni ta cire amma yanzu daga ta kama can sai ta kama nan ganin da sajida tayi yarinyar na kokarin yin tsirara gaban mijinta kun santa kuma da kishi haksn yasa bata san lokacin data kama hannunsa ba tajashi sukayi ciki tana ambatar ta shiga uku ba tana shiga dakin tasa key ta zauna gefen gado ta dafe kanta shima din habeeb zaman yayi dukansu aka rasa me magana
itako dije tana ganin yadda sajida tayi ta saki rigarta ta kama dariya tare da daukar jakarta da hijabinta ta nufi waje tana dariya tana fadin waya gaya miki da cirewar zanyi yadda zamani ya koma yanzu maza da mata duk suna iya ma mutum fyade inje ku nakasani ke da mijinki kunga araha yanzu ba gashi na kubuta ba dan wannan me qirar mazan inda ta riqeni wlh baxan sake moruwa ba inaga sai dai na koma kauye a cikin wannan yanayin ta qaraso bakin gate yadda yake tun jiya haka yake wato hakan ya nuna musa be fito ba tun jiya daya shiga kenan sai yanzu ta tuna abinda ya faru nan ma dariyar ta kuma yi taso leqa musa amma sai ta tsinkayi horn din motar makarantar su dan haka da sauri ta fita ta shiga suka wuce
****
ni fa gaskiya bazan iya ba wlh wannan jaraba har ina yarinya kamar 'yar shedan na fuskanci wata rana in tana gidan nan saita sa anzo an dau gawar mu daga Aljanu sai shaidanu duk sun cika mana gida nidai wlh asan yadda za'ayi
tunda ta fara maganar yake kallonta harta gaji tayi shuru
dan jim yayi kafin yace to yanzu ya kk so ayi korarta zanyi ko kuma me?
bance dole ka koreta ba amma ta koma gidan naseer tunda ai ba kai kadai bane dan uwanta
kina ganin komawarta can din shine mafita ? kada fa ki manta gida daya muke kuma ina son ki fuskanci wani abu game da yarinyar na fuskanci duk abinda ta lura mutum baya so to shi tafi yi yanzu kinga ai shi naseer be nuna mata abinda nake nuna mata kamar dana nuna bana son zamanta a nan amma kinga ai nan din ta dawo so inaga mafita daya ce mu lallaba ta har a hankali zansa ta bar gidan amma ki duba fa yadda taketa samu yin accident muna daga gida wuta bazata bi da khadija ba sai dai ruwa ruwan ma na sanyi dan ya zuwa yanzu na fuskanci yarinyar batada hankali
shiru tayi tana nazarin maganar sa zuwa can cikin sanyin murya da marairaicewa tace amma honey ni ba zaman nata ba kaga fa cousins kuke da ita ina jin tsoron kayi mata wani kallo ba matsayin qanwa ba
siririn tsaki yaja tare da fadin kinji matsalarki ai ke kishi yanzu ke ni me zanyi da wannan figigiyar yarinyar kamar kazar mayu wadda inda nayi auren wuri dana haifeta ko ke kanki kin san inda kinyi aure on time da yanzu kinada kamarta dan haka ban son shirmen banza mafita muke nema yanzu bana son shashanci
shikenan zanyi kokarin danne zuciyata amma pls cikin qanqanin lokaci mu san abinyi tabar gidan nan
insha Allah dan na fiki matsuwa da hakan
ah ah wlh nafika
eh to yanzu kam kin fini tunda dubi yadda aka haramta miki sa jambakin safe ba ya qarasa maganar yana kunshe dariya
ganin yadda ta kalli madubi ta bata rai yasa shi matsowa kusa da ita ya fara aikin rarrashi
******
koda dije ta dawo daga makaranta direct part din yusra ta nufa ita kadai ta iske zaune a falo tana kallo harga Allah batayi murnar ganin dije ba duk da zaman kadaicin ya dameta dan me gidan ya fita masallaci ita kuma sajida batada wani sakewar fuska inba gaban mijinta ba nan fa sbd kissa kamar ta hadiyeka amma da zarar an barku ku kadai zata cukule dan haka bata fiya shiga inda take ba yake kawai take yiwa dije bayan ta zauna ta gaisheta
suna a haka dije ta miqe tace bari ta koma part din sajida har bakin kofa yusrah ta rakota ita ko dije abin ma mamaki yake bata ganin yadda inta je guri tace zata tafi ake murnar tafiyarta fiye da murnar zuwanta
koda ta shiga falon da sallama dauke a bakinta ta iske sajida zaune ita da wata mata da yara biyu cikin sakin fuska suka amsa mata su duka
qarasawa tayi harda dan rissinawa ta gaida matar ta amsa mata cike da fara'a nan ta juya ta gaida sajida itama da fara'a a fuskarta ta amsa mata karo na farko kenan a zamanta a gidan
shigewa tayi daki tana zuwa ta cire kagan makaranta ta shiga toilet danyin wanka da alwalawa dan gabatar da sallah
tana shiga Amina ta kalli sajida tace Amarya wannan qanwarki ce halan na ganta kyakkyawa da ita masha Allah ga hankali
murmushi sajida tayi a ranta tace me hankali a gwiwa dai amma a zahiri tace eh qanwata ce tunda qanwar oga ce
kai gaskiya na gaba da hankalinta wlh anan take da zama kenan?
eh sajida ta fada a takaice
suna tsaka da haka dije ta fito sanye da doguwar riga ta atamfa kanta ko dankwali babu ta qaraso gurinsu tana hamma tare da fadin Aunty wlh yunwa nakeji
kije ga abinci can saman dinning tayi mata nuni da hannu
juyawa dije tayi a ranta tana yaba acting irin na sajida wato dan taga bakuwa shine take nuna kamar ba komai tsakaninsu hmmm to bari itama ta biye mata gara taci ta koshi kafin ta fuskanci qalu balen gaba
tana tsaka da cin abinci su habeeb suka shigo su dua ukun habeeb,naseer,sai doctor yusif suna shigowa suka zauna naseer ya cire waya ya kira yusrah ba jimawa kuwa saigata tazo nan fa aka shiga hirar yaushe gamo itakam dije saida ta tabbatar ta koshi kafin ta qaraso falon ta shiga gaishesu dukansu suka amsa cikin sakin fuska
juyawa tayi taja yaran sukayi cikin dakinta ta shiga yi musu wasa
sai da akayi sallar la'asar kafin su yusuf suka fara shirin tafiya suna harrakawa dije ta gito da yaran
kallonta doctor yusif yayi kafin yace Auntyn yara kun gaji da wasan kenan da har muna shirin bar miki su
murmushi tayi kafin tace to ai ni koda an barmin ina so wlh
to tunda kina so ki bisu gidansu kiyi kwana biyu cewar sajida aikuwa Amina tayi caraf tace wlh kuwa da naji dadi dan dama in Abban Anwar ya fita rasa 'yan hira nakeyi kinga sai kiyi mana weekend ko sister
me zai hana ai ko cewa kk yi ta dinga zuwa duk week tana muku weekend bakuda matsala dan haka ke jeki shirya ki zo ku tafi cewar habeeb
mamaki ne ya cika zuciyar dije ganin yadda ake ta tallarta dan haka saita maxe tayi kamar bata ji su ba
naseer ne me fadin ai khadija batada matsala akwai dadin zama dan haka Allah ya taimaka
haka sukaita tunzura har saida Amina ta dameta ta dauko kayanta kala biyu ita kam taga ikon Allah yau
koda suka zo shiga mota har rige rigen bude mata mazan da matan keyi koda ta shiga ta zauna da sauri suka rufe ji kk yi bammmm ita abin nasu ma dariya ya fara bata
dan haka saita bude motar da niyyar fitowa
cikin hada baki suka tambaye ta
ina zaki kuma?
kallonsu tayi daya bayan daya kafin tace mantuwa nayi zan koma in dauko
da sauri habeeb yace wa sajida matso ta fada miki abinda zaki dauko mata basaita fito ba idanma yana nesa ne to ki fada mata sai ta dauko akwatin in kin dauka saita mayar kada ki samu damuwa 'yar qanwarmu..........
*Allah ya raka taki gona dije* 😂😂🤣🤣
*vote*
*comments*
*with 08066364077*
*Alkalamin khady* ✍
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
TA ME GARI
NA
khadija usman
2⃣3⃣
oh ni dije naga takaina jiya kamar za'a cinyeni danya kawai dan banyi posting ba toh inaga kawai dijen nan tura ta zanyi gidan kowa tayi maku kwana daidaiya in huta nima i luv u all my fans😘
shi kanshi duk yadda yaso ya maze kasawa yayi duba da yadda yaga bakin sajida lokaci daya ya koma kamar na jaba sam yama manta da ciwon nashi nan shima ya shiga dariya
sajida kuwa ta zubawa sarautar Allah ido ganin duk su biyun shi da dije sai babbaka dariya sukeyi hakan yasa tayi tsammanin ko abinda ya biyo dijen ne ya shige jikinsu dan haka saita fara ja baya tana neman hanyar shafcewa
cikin dariyar harda rike ciki ya nunata da yatsa ya na fadin kin ganki kuwa sweety kin kalli yadda bakinki ya koma kuwa ?
tabawa tayi da hannunta taji yayi suntum sai yanzu na fuskanci meyake yiwa dariya itako dije cikin dariyar ta juya kallonta ga habeeb tace wlh yaya kaima bakaga hancinka ba har ya malkwade shafawa yayi shima ya danji zafi sai yanzu ya dan nutsu kafin ya rike kansa ya samu guri ya zauna tunawa da yayi da gudun da suka sheko to ko uban me ya koro yarinyar oho
cikin wannan yanayin ya dago da kyar yace ke su waye suka biyo ki ne?
tsayar da dariyar tayi kafin tace ba fa wasu bane qawaye na ne na skull shine mukace ayi rige rigen zuwa gida to shine fa na sheqo a guje.......
dukansu sakin baki sukayi suna kallonta inda zuciyar su ta shiga sama da kasa kowannensu yama rasa abin cewa tana gama fadar haka kuwa ta juya tayi cikin daki tana dariya
dukansu sun kasa magana sajida da ya zuwa yanzu takejin kamar ta shake yarinyar ta mutu kowa ya huta takeji wannan jaraba har ina yanzu duk wannan gudun famfalakin data sa su ashe shirmenta ne na banza da wofi dama ga haushinta da take ji tun safe tama rasa hukuncin daya kamata tayi mata
haka shima habeeb ransa ya gama dagulewa wato ma duk wannan gudun data sa su ashe kawai na iskanci ne yanzu dubi yadda ta mayar masa da bakin mata tamkar na jaba duk soyayyar da aka kwadaita masa yau amma yarinyar nan tayi masa bakin cikinta tunda ta yaya zai fuskanci wannan bakin na sajida a haka
itama sajida a nata bangaren hakan take domin yau ta kudiri aniyar shayar da shi soyayya ta musamman amma sai gashi wannan matsiyaciyar yarinyar ta bata masu shiri ji yadda hancin mijinta ya wani maude abin haushin ma ga gobe yusuf zai zo da matarsa yanzu haka zasu zo su gansu sun canza kamanni kai wannan yarinyar Allah ya hadata da marurun rayuwa wannan jaraba har ina ga yadda ta kwaso a guje wlh ita ta dauka ma 'yan boko haram ne suka shigo anguwar ashe wai shirmenta ne gashi dai ta zama budurwa amma ba hankali tana tsaka da wannan tunanin taji muryar habeeb cikin dariya yana fadin sweety duk tunanina ne hakan ya fada yana me qara kunshe dariya iya kuluwa ta kulu amma itama data kalleshi taga yadda hancinsa ya wani bude yayi dirimm dashi ai saita fara dariyar itama ganin tana kallonsa tana dariya yaga yadda bakinta yakeyi shima sai dariya
haka suka dinga yi sam sun manta da dije wadda tun da ta shiga daki itama ta zube ta fara tata dariyar ganin yadda lokaci daya halittar mutan gidan ta canza gashi ta kubuta daga hukuncin laifin dazu sai da tayi me isarta ta miqe ta shiga toilet tayi wanka ta canza kaya kafin ta fito falon
koda ta fito bata iske kowa falon ba da alama sun shige ciki dan haka kai tsaye ta bude kofar ta fita ta shiga jido kayanta tana kaiwa dakin datake kwana
sai da ta gama tsab kafin ta duba saman dinning taga an shirya shi tsaf da abinci mai rai da motsi komawa tayi tayi sallar magrib inda ta zauna tana karatun kur'ani har aka kira isha'i tayi kafin ta miqe ta fito falon bata iske kowa ba nan ma da alama masu gidan basu da niyyar fitowa dan haka ta zauna ta fara harraka abincinta sai da taci ta koshi sannan ta kai plates din data bata kitchen ta dauraye su kafin ta koma falon ta zauna kenan kuma saita mike ta fice daga part din gaba daya
su kuwa masu gidan suna can cikin daki zazzabi ne ya rufe sajida yayin dashi ma gwaskan kansa ke masa ciwo ko yunwar ma ba ji sukeyi ba dan sajida ta rasa bakin cin abincin ji takeyi ya zuwa yanzu kamar bakinta ba'a fuskarta yake ba dan haka da kyar sukayi sallah suka kwanta aka shiga zaman kurame
part din su naseer ta nufa tana zuwa ta shiga bubbugawa a wannan lokacin suna zaune a falo sunyi jugum suna jiran ko ta kwana jin ana buga kofar yasasu kallon juna amma kowa ya kasa motsawa nuni naseer ya shiga yiwa yusra data je ta duba waye hararsa tayi tare da maqe kafada alamun taki din bata rai yayi wai shi me gida ya zare ido alamun ta tashi amma taki jin anata bugawa ya lallaba ya miqe cikin sanda ita ma yusra ta mike ta qarasa daga bakin bedroom dinta a cewarta idan abun gudun ne saita shige daga nan
kamar barawo yazo sata haka naseer ya dinga sanda kafin cikin murya me kamar rada ya ce waye?
ni ce cewar dije
jin muryar dije yasashi fadin lfy dai ko?
eh lfy ta bashi amsa tare da fadin fatan dai duk kuma lfy kuke
bai bata amsa ba illa sauke ajiyar zuciya da yayi tare da bude kofar ya ko ganta tsaye murmushi ta sakar masa tare da rabashi ta shiga ciki ya mayar da kofar ya rufe amma besa key ba saboda tsaro inji shi yusra dake can kurya tana kallon duk abinda ke faruwa har dije ta samu guri ta zauna kafin ta dan dawo falon tana yake nan dije ta gaisheta dukansu suna son su tambayeta meya faru dazu suna jin tsoro dan haka sukayi gum ganin babu me niyyar magana yasa dije takalo hira daga um sai um um haka aka dinga hirar itako dije da ba gajiya takeyi ba ta dinga digo da hira ganin da sukayi batada niyyar shuru yasa duk suka bingire suka shiga baccin karya ganin datayi sunyi bacci yasata miqewa ta fice batako tashe su ba su kuwa masu baccin karya ashe na gaske harya sacesu basu sani ba karshe dai nan suka kwana
****
tun asuba da dije ta tashi tayi sallah bata koma bacci ba wardrope ta bude ta shiga jera kayanta ciki tunda ita batasan da maganar zamanta gidan naseer ba dan haka ta shirya kayanta tsaf komai ta ajiye inda zata buqata dakin yayi kyau matuka data qara gyarashi kasancewar yau friday yasa take son shiga school da wuri dan da wuri suke tashi ta fuskanci 'yan gidan basa tashin asuba a cewarta dan haka ta ce bari ta samawa kanta abin kari ta wuce abinta
ga mamakinta koda ta fito saita iske saman dinning da kayan jiya karasawa tayi ta bubbude taga yadda ta barshi jiya haka yake to ko me ya hanasu cin abinci oho ita harta manta ma da abinda ya faru jiya dan haka saita shiga kitchen dan samawa kanta abinda zata ci harta yi niyyar yin nata ita kadai sai kuma taga rashin dacewar hakan duk da batasan dalilin yin hakan da sukayi ba amma dai tasan ba haka kawai bane dube dube ta shiga yi ganin botikin gyada da tayi yasata fasa dafa tea ta dama kunun gyada cikin qankanin lokaci ta gyara wake tare da markada shi ta soya kosai lafiyayye ta fito falon dashi ta kwashe kayan sama ta mayar kitchen ganin abincin ba abinda yayi yasa ta juyeshi ta sa a friedge tana fitowa ta ga sajida ta fito da alama bata jin dadi ganin yanayinta cikin kulawa dije ta shiga gaisheta ta so ta shareta amma saita amsa da kyar itako dije bata kawo komai ba ta dauka ko ciwon ne ya jiki aunty dije ta kara fada
hararar ta tayi qasa qasa bata ko amsa ba ta nufi kitchen dan sama musu abinda zasu ci dan da yunwa suka tashi
ganin da dije tayi ta nufi kitchen yasata fadin Aunty ga abin kari na hada mana gaba daya naga kamar bakyajin dadi
jim tayi kamar ta shareta sai kuma ta tuna da masifaffiyar yunwar da suke ji dan haka cikin hade rai bako walwala ta dawo ta nufi dinning sai yanzu ta lura da ba abinda ta dafa jiya da yamma amma bata damu ba ta juya ta nufi daki bata wani jima ba saiga shi sun fito ita da habeeb dukansu yau inka gansu babu wata walwala a tare dasu
gaisheshi dije tayi ya amsa ba yabo ba fallasa itako dije a ranta tace dama kun saki ranku dan indai nice tunda na ce zan zauna a gidan nan ko naman jikina zaku na yanka saina zauna din
kujera taja ta zauna nan ta zuba kunun ta a cup ta dibi kosai a plate bata ko kalli inda suke ba ta fara afkawa cikinta
bakaramin dadi yaji ba ganin kunun gyada da kosai yana son kunu sosai kowanne iri hakama kosai itama sajida tsintar kanta tayi da son cin kosan wanda ada sam bata ko son jin sunansa bare ace taci
zuzzuba musu tayi nan suka shiga aikawa kasa da hanci ba qaramin dadi sukaji ba su duka dan haka ko bakinsu ba'aji dije ce ta cinye nata kosan ta miqa hannu da niyyar debowa cikin kula danta qara taga wayammm
binsu tayi da ido inda ta kalli plate din gaban kowa taga shi habeeb saura uku ita kuma sajida sauran daya bata ko tsaya wata wata ba ta dauke nsu gaba daya cikin sauri suka kalleta amma ko'a jikinta taci mayar gabanta ta zauna ta fara ci
habeeb ne yayi qarfin halin fadin ke wannan wane irin iskanci ne mu sa''aninki ne ?
ah ah amma kuyi haquri naga ne ai ana barwa qarami dan ragowa ko zai bukaci kari to ku kuma naga kamar bakusan babba da yaro ba gashi ni ban koshi ba kuma ciki be san ayi masa kara ba musamman cikin kauye tunda ya riga ya saba da hatsi shiyasa na yi muku haka amma idan baku koshi ba ai naga akwai duk kayan hadin a gidan ni da ba manomiya ba kuma ban nemo na kawo ba bare ace zan hana kaga sai chair lady ta shiga ta qara maku wani tana gama fadar haka ta miqe ta shiga dakinta danta shirya ta wuce school
dukansu binta sukayi da ido sajida data gama kuluwa tace wai ni dear tsoron yarinyar nan kk yi ko kuma me? ta yaya kana gani yarinya tanawa mutane rashin mutumcin dataga dama amma ka kyaleta
to ke me zai hana ki dauki mataki ya fada yana me kokarin mikewa dan barin gurin
au hakama zakace ko?
to shikenan zan kuwa dauki matakin kamar yadda kace amma wlh matakin dazan dauka baxai yiwa kowa dadi ba dan ni ba ruwana da wata alakar dake tsakaninku ko kuma ran daddy'nku da zai baci wlh baxai yiyu ba ni ban haihu ba amma a fara kawomin jidalin dangin miji tun yanzu duka yaushe mukayi auren da har za'a wani kawomin wata watanma dangin dangarera inda ma qanwarka ce uwa daya uba daya amma cousin wlh ma an raina min hankali ta tafi gidan naseer mana ko dole sai nan yarinya sai jaraba da fitina baki kamar reza tunda ta diro gidan nan narasa kwanciyar hankali daga ni har sauran jama'ar gidan amma kun kasa daukar mataki ji yadda ka tsaya qanwar cikinka tana fada ma magana to wlh yau zanyi maganin
abun ta fada tare da kokarin miqewa shi kuwa habeeb da tunda ta fara magana ransa ya fara baci tsaye yayi ya zuba mata ido
itako dije ta fito kenan da niyyar tafiya ta ji sajida na sababi tsayawa tayi tana kallonta har zuwa lokacin data mike ta nufo ta gadan gadan tana kumfar baki
a inda dije take bata ko matsa ba ganin sajida ta nufota yasata fadin um um Aunty um um fa ina tausaya miki wlh kada ki qaraso
sajida da masifa ta rufewa ido ko jinta bata nuna tayi ba sai qara nufota takeyi yayin da dije tana daga inda take tafara dariyar mugunta abinda yabawa habeeb mamaki da tsoro kenan........
*sai kun dinga hakuri da duk yadda kuka samu duk yadda naso in samu lokaci fiye da haka baya samuwa*
*vote*
*comments*
*with 08066364077*
*Alqalamin khady*✍
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
NA
khadija usman
2⃣6⃣
*ina jinjina gareku khadija fans novels 1,2,da kuma 3 tare da tame gari fans gaskiya na yaba sosai da comments dinku ina kuma godiya da addu'arku gareni kamar yadda kukemin kuma Allah ya biya muku bukatunku*
*bazan manta daku ba kuna raina kuma ina ganin comments dinku gaskiya ina godiya Allah yabar kauna*
*jattako novels fns*
*sadnaf novels fns*
*zauren mai dambu group*
*Hikayar marubuta*
*online writters groups*
*Arewa novels fans*
*da duk wadanda ban fade su ba suna raina wlh ina kuma mugu mugun ji da ku*
ah abin harda zagi kuma hajiya babba
ai dole in zage ki ke yanzu inba kin rainan wayo ba ta yaya zaki cemin wai sabulu ya bace a jikinki ko da dan mitsili ne bare kuma girman kwanon sha anya ma kuwa kinsan kwanon sha kuwa?
a haifeni a kauye kice ban san kwanon sha ba hajiya ni ko na sanshi kawai ki yadda da maganar da na fada miki
na rantse da Allah bazan yadda ba dan ko'a tarihi ban taba jin makamancin abinda kk fadamin ba sai kace sabulun aljanu
*yauwa anzo wurin dije ta fada a zuciyarta*
au to wai da ke kin dauka sabulun na mutane ne?
to amma ai ke kikace wanda ake siyo muku na kuwa san babanki ne ke siyowa ko kuma ai mutum ne shi ko kuwa kina son kicemin yasan dandalin aljanu acan ya siyo muku
to da nace miki ana siyo mana ai bakiji nace miki ga wanda ya siyo ba ko?
eh kuma fa hakane amma ke inba karyar jaraba ba a ina kikaga aljanun da har zasu siya miki sabulu
murmushi dije tayi kafin ta nufi kofa ta murza mata key ta dawo ta rufo toilet ma sannan ta fara leqe leqe kamar munafuka
hajiya ta bita da kallo kafin tace ke wai uwar me kk leqawa haka sai zagaya ni kk yi kamar kin kama akuyar mayu
shiiiiii dije ta dora hannunta a saman bakinta ina zuwa kedai
saida ta gama 'yan dube dubenta kafin ta kalli hajiya tace wani sirri zan fada miki bana son kowa yaji shiyasa
sirri kuma?
wane irin sirri duk ke 'yar nan duk duniya ki rasa abokin da zakiyi sirri dashi sai ni anya ba yankani kike shirin yi ba kuwa dan ni wlh inda abinda nake tsoro yanzu bai wuce mutuwa ba in kin san abinda zaki aikata min kenan gara ki sanar dani dan manzo
kai hajiya wlh kin fiya tsoro to dama maganar da kk takalo ce ta Aljanu kin ganni nan to inada su sunkai miliyan daya a kaina
innalillahi wa'innailaihir raji'un miliyan daya fa kika ce ?to ni dai ko a mazahabar jama'u ban taba jin kan mutum ya dau Aljani fiye da dari ba daya ba shima cikon na darin danna mutuwa ne shiyasa amma ke kice har miliyan daya sai dai in kece aljanar da kanta
to Alhmdllh tunda kin fahimta shikenan
na fahimci me ?ba dai da gaske ke din aljanar bace?
eh ah'ah
rabi mutum rabi aljan nake
😳ke 'yar nan fadamin gaskiya in san abinyi tun wuri
ai gaskiyar kenan abinda yasa ma kikaga na tsaya haka sbd naga yadda kika karbeni ni shiyasa ni bana cutarwa da kike ganina ina rayuwata ne cikin bil'adama amma ina azabtar da duk wanda yake kuntatawa jama'a su kuwa masu shiga tsakanin masoya ko ma'aurata kashe su nakeyi gaba daya masu gani ba kyalewa kuwa kamar masu tanka halittata su kam bakin nake murgudewa in tsiyayar da idanunsu ta yadda bazasu moru ba sannan in.........
wayooo na shiga uku hajiya ta fada da karfi
yusuf da Amina da tun dazu suka zo da niyyar susha hira da dije suna dab da shiga suka tsinkayi hirar hajiya da dije akan sabulu suka tsaya suji yadda zata kaya ai tunda sukaji dije tacewa hajiya ita aljana mutum.ce yusuf ya tuna da yadda naseer ya basu labari dije tayi musu aikuwa nan ya kama dariya Amina ta kalleshi kasa kasa take tambayarsa
janta falo yayi ya fara bata labari kafin yace nasan ta fuskanci halin da muke ciki shiyasa ta bullo mata ta wannan hanyar
marairaice fuska Amina tayi kamar zatayi kuka tace haba Abban Anwar baka tunanin hakan ya cutar da ita kaga fa tsohuwa ce in jininta ya hau fa?
hakanma bazai faru ba nidai kawai fatana Allah yasa wannan yarinyar ta zama silar shiryuwar hajiya ta barmu mu zauna lfy kinga ni tashi mu zaga ta bayan window musha kallo kinji my choice
jiki ba kwari ta mike ya kalleta yace haba mana ki saki jikinki pls kin san dai hajiya mahaifiyata ce bazan so abinda zai cutar da ita ba ko nasan halin yarinyar a sai dai ta firgitata kamar yadda ta firgita wadancan kartin tunawa tayi da labarin daya bata aikuwa ta kama dariya suna tsaka da haka suka jiyo ihun hajiya da gudu suka fita suka zaga ta window suka danyi slide dinsa kadan suka kama kallo
ni fa ki daina min ihu me nayi miki ?
kinga dan Allah yake muminar aljana kiyi haquri daga ganinki hwlh anga me afuwa wlh ban aikata ba duk abinda kika ga inayi ciwon sanyi ne yake tabani badan ma kar ince ki tambayi yusuf ba nasan bai sani ba da nace ki tambayeshi to tun ina budurwa na hadu da matsalar sanyin kwakwalwa inya bugani sai inta abu irin na marasa hankali ni dama tunda na ganki nasanke ba mutum bace amma da naga kuna yanayi da su habibu saina yadda ashe ke mutum aljan ce nasan suma basu sani ba amma ina rokonki da kada ki kasheni inada marayu kinga ni ke kula dasu gashi......
to wai laifin me kikayine da zan kashe ki?
nasan nayi kuma kema nasan kin sani kawai kina son kiyimin kisan rashin imani ne bayan kin murgudemin baki kin tsiyayarmin da idanu ki tausayamin ki duba tsufacda furfurata ki duba qananun yarana
au har yanzu kina haihuwa dama?
ah ah yusufa da farida mana in an hada da irin shekarunki ai kinga su jarirai ne ko?
hakane ina zuwa
kaya ta ciro tasa dan sanyi takeji kafin ta dawo ta zauna akan bedside drower ta dora data kan daya
kafin tace hajiya
cike da rawar baki ta amsa ya zuwa yanzu tayi zaman dirshan bisa tiles
na'am ranki ya dade me haskrn sallah dan naga ke din musulma ce ko a cikin aljanun kinada imani bakya wasa da ibada
duk naji yanzu dai ki fadamin dalilinki na hana yaranki sakewa da iyalansa kika zo kika takura musu kika......
kinga duk basai kin fada ba nasan kin sansu wlh sharrin ciwon sanhi ne kamar yadda na fada miki amma ina nan ina neman magani
oh kenan shi kesa kike aikata abinda kikeyi ?
sosaima kuwa ni tsorona ma kada yasa in aikata kisan kai gara in nemi magani tunda wuri
ai indai magani ne kin gama samu dan ni har maganin dayafi nashi ma ina bayarwa
cikin hajiya ne yace quuuuuuu cikin sauri ta yamutsa fuska tace ah ah bama sai kin bayar ba dayake na karbi wani ina kan aiki dashi yau ma wa'adin zai cika nasan gobe na warke
to shikenan naji amma yanzu dole ki karbi hukuncinki na yin katsalan dan da tanka halittar Allah da kuma shiga shirgin daba naki ba
haba yallabiya kiyi haquri sharrin shaidan ne da kuma....
ganin da dije tayi duk hajiya ta hada zufa duk da sanyin A.C dake dakin ga kuma fanka saita bata tausayi dan haka ta rage abinda tayi niyyar yimata sbd gudun kada taje jinin tsohuwa ya hau ta shiga uku garin gyara ayi barna
shikenannaji tunda kin bada haquri kuma kin smu maganin cutar dake damunki ba matsala zan kyaleki amma daga yau kullum da dare zan dinga kwana gidan nan sannan da rana zan ding zuwa zagaye batare da kowa yasani ba inga halin da ake ciki idan naga baki warke ba sai in dora da nawa maganin
wlh nama sn zan warke
sannan kada ki sake inji in fadawa kowa ni ba cikakkiyar mutum bace dan ba wanda yasani
wace ni ai ni banida wannan subutar bakin nifa banda yanzu magana ma bata dameni ba ta fada tana me marairaice fuska
sai da dije ta dan yi murmushi ganin yadda ta danyin
ita ko hajiya da qarfinta ta yunkura tace Allah ya baku haquri ni zan tafi dan wlh bacci nakeji
kije ina ai ke tare zamu kwana dake da waya kawoki?
wlh dama zuwa nayi in shiga bandaki tsautsayi ya ritsa dani
oh dama anan kike shiga toilet din dakinki babu ne ko
me?
kaddara wlh kaddarar haduwa da ke tkawoni
ko kafin dije ta bata amsa har takai bakin kofa dije na shirin yin magana taga tsohuwa ta bude kofa ta sheqa da gudu ba ko waiwaye
aikuwa nan ta fada saman gado ta dinga dariya su yusuf ma dariyar suka shiga yi suka zagayo koda suka shigo dakin dije nata dariya saida yusuf yace sannu da gama rikitamin uwa
bata daina driyar ba gnin hakan yasa amina tace kaga mu gudu fa kar a ritsa damu ko na gasken sunzo
nan suka juta suka fita har sun wuce yusuf ya nufi dakin hajiya yana zuwa ya tura yatji shi bame gam ya kwankwasa amma shiru kk ji dariya yayi a fili yace Allah yasa ki gyara Ameen
*vote*
*comments*
*with 08103271722*
*Alqalamin khady* ✍
[12/12, 10:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*TA ME GARI*
NA
khadija usman
2⃣5⃣
*kuyi haquri masoya ta me gari wlh banjin dadi ne kwana biyu na gode sosai da addu'oinku gareni masu kirana da masu turamin sako duk ina godiya*
ita dije abinma dariya yabata ganin da gaske sukeyi yasata fadin
ah ah a barshi ma nafasa daukar
yauwa 'yar albarka kuje kawai yusuf Allah ya kiyaye sai munyi waya cewar habeeb
shikam yusuf dariya yaketa yi ciki ciki dan yasan wannan tunkuda dijen da sukeyi wlh ba banza ba
haka yaja motar sa suka fita mutan gidan nata daga musu hannu kamar dangi sunzo rakiyar mutum zashi saudiya🤣
suna ganin sun fice a gidan duka suka ce Alhmdllh Allah ya raka taki gona
ameen inji matan nan kowa yayi nasa wuri da matarsa
******
saida ya biya ya dan yi musu siyayya kafin suka wuce gidan
ba karamin mamaki dije tayi ba ganin haduwa da tsari irin na gidan doctor yusuf lamarin bai qara rikitata ba saida suka shiga palon gidan gaskiya masha Allah ya hadu iya haduwa
suna shiga ita da yaran suka qarasa saman kujerar suna tsalle ita kuma ta qarasa a hanki ta zame qasa dan ta zauna yayin da taga doctor yusuf yayi wuf ya shige daki tare da ledar daya yo musu siyayyar da ita yana shigewa kuwa ta tsinkayi muryar wata dattijuwa na fadin
to to andawo jaraba ta dawo da yau bakina shuru gidan tsit na yi bacci na cike da annushuwa da mafarki me dadi amma yanzu daga dawowarku har kun ajiye shaida ina shi yusuf din yake naga duk na ganku amma shi ban ganshi ba ince dai ba wani abun ya siyo kuka munafunce ni aka shige dashi ciki ba ko?
ikon Allah cewar dije data tsaya tana kallon sababi
jin dije tace ikon Allah yasata juyawa gurin sai yanzu ta lura da ita
to ita kuma wannan sadakan yallan daga ina iyayen kwashe kwashe?
yusuf ne ya fito cikin fara'a yace qanwar su habeeb ce ta zo mana weekend
washe baki tayi tare da fadin ah ah Allah sarki nako ga kama kamar an tsaga kara kice ke 'yar gida ce ai na dauka kina daya daga cikin irin kare arzikinka ta fada tana me wurgawa Amina harara
Amina wadda idan da sabo ya zuwa yanzu ta saba da halin hajiya hauwa dan haka ta qara dukar dakai sbd bata son tayi wani motsin kirki yanzu a qarewa iyayenta sababben zagin yau da kullum tun da ta auri yusuf take cikin wannan halin da hajiya hauwa wadda mahaifiya ce ga yusuf din a cewarta bata so ya auri 'yar talaka ba wadda zasu qarar da arzikinsa gara ya auri 'yar masu kudi to da yake da rabo gashi harda yara biyu
haka kawai ta tattara kayanta ta dawo gidan da zama kullum bata bacci har sai taga shigowar yusuf kuma ta tabbatar be shigo da komai ba da kanta take kulle qofar falon ta rike key din a gurinta da asuba ta zo ta bude wai duk dan kar aje ko ya boye abinda ya siyo a mota saita yi bacci ya dauko
iya kyautatawa yusuf nayi mata duk wani jin dadi ya dauke mata shi amma sam bata gani taki barinshi ya sarara
su biyu ne yaranta daga shi sai qanwarsa farida wadda yanzu haka tana aure a kd ne bata fiya zuwa ba sbd batajin dadin yadda mahaifiyarsu keyi gashi amina nada kirki sosai
to ku haka ake bakuwa kusata ta zauna qasa ta fada tana me karasawa inda dije take zaune
tashi kinji ai daga ganinki ke jinin arxiki ce kin saba da hutu ji fatarki ina ke ina zama a kasa tashi ki zauna kinji duk inda yayi miki ki zauna ki mike kafa ai tunda jinin su habibu ce ke bakida matsala dan yaran kirki ne sun san mutunci
ita dai dije ta kasa magana haka hajiya ta dinga tantadinta harta gaji aka kira sallar magrib kowa ya kama gabansa Amina ta kai dije dakin da zata zauna
bayan tayi sallah ne tana zaune kan dadduma Amina ta shigo dakin da sallamarta dauke da faranti a hannunta
amsawa tayi tare da qara gaisheta ta amsa cike da fara'a kafin ta ajiye ta nemi guri ta zauna tace ya bakunta
.sunkuyar da kai dije tayi kafin tace Alhmdllh nan da can ai duk dayane
to Allah yasa haka kika dauka harga zuciyarki
wlh dagaske nake Aunty
ina yaran ne?
kin san suyi jaganiya yauban gaji ina musu wanka har sunyi bacci
toh da wuri haka ?
wlh kuwa ga abinci nan kici sai dai kiyi haquri da abinda kk gani ban sani ba ko baki saba da cin irinshi ba kiyi haquri tun safe kafin mu fita hajiya tasa aka dafa amma dayake kin zo da kafar dama nasan gobe za'a canza insha Allah
yauwa Aunty dama abinda ya dan dameni nake tunanisa yanzu kenan
meyasa kika zauna tana ci miki mutunci haka duk da ban sanki ba ban san halinki ba amma na yaba miki Allah inda nice ko hmmm da tuni an wuce gurin
kallonta Amina tayi tare da yin 'dan murmushi kafin tace kuruciya kenan ai ko kece khadija ba abinda zakiyi illah hakuri ko dan albarkacin kina auren danta sannan ko ba komai nasan wata rana sai labari tayi duk yadda take so nasan wata rana in ance tayimin ba bazatayi ba
tabdijam wlh Aunty baki sani ba ne irin wadannan tsoffin zeyi wuya subar mutum ya sarara gasu da shegen tsawon rai yanzu wannan saita iya qara hamsin ko ma fiye nan gaba
dariya Amina tayi tace kai khadija to ya za'a gansu kuwa lokacin
ai qanqancewa sukeyi kiga sunata komawa kamar masu cutar tamowa qarshe sai dai kiga ana sasu a baro in kuma sunada gata ne zakiga ana turasu a keken nan na jarirai da suke koyon zama
kai khadija😂
Allah kuwa Aunty halan baki taba gani ba?
ah ah Allah bai taba gwadamin ba
to kuwa kiyi addu'a sosai dan ga alama nan a gidanki
dariya Amina tayi tana qoqarin mikewa tace ni dai ci abincin kafin in dawo musha hira
to tana dai bari ayi hirar ko?
ai na fada miki ke da sa'a kika zo gidan tunda har fada tayi wai laifinmu ne da bamu kirata munce zamu taho dake ba gashi yanzu munja mikk cin tazarce dan haka kada ki damu ke din da hajiya kun jone
murmushi dije tayi a ranta tana kissima yadda zata saita hajiya
Amina na fita dije ta jawo farantin gabanta din ta bude
wake da shinkafa ne mai da yaji ai kuwa dije dadi taji maimakon taji haushi dan ta dade marabinta da ci a ranta tace inba ma dai abin da izgili ba ai wake da shinkafa abin marmari ne dan dai kawai anyi hakan ne da mugunta
sai da taci ta koshi sannan tayi sallar isha'i tana tsaka da sallar taji an turo kofar dakin
au to ana nan ana gaida ubangiji kenan to Allah ya amsa ta nemi guri tazauna
saida dije ta gama addu'ointa kafin ta juyo tayi mamaki ganin hajiya zaune amma saita maze ta shiga gaisheta
cike da fara'a ta shiga amsawa kafin daga baya ta fara zubawa dije surutu ganin da dije tayi tasamu abokiyar yi yau yasata cire hijabin datayi sallah ta gyara zama
kallonta hajiya tayi kafin tace Allah me halitta kenan
yanzu ke wannan farin nske baya damunki ji beki fa waima da dare kenan ina ga rana
au dama fari yana damun mutum sai kace na Allah ya isa
eh mana kin ganki kuwa nifa inba idona ne yakemin gizo bahar wani yellow yellow naga kinayi ko ma dai harda shawara farin nan naki
ah ah ba shawara bace ai da kin lura da kyau da zakiga kwayayen lantarkin da aka jona min suna kawo wuta😠
rike baki tayi tare da nuna al'ajabi tace wuta kuma a jikin mutum yarinya?
eh mana ai zamani ne yazo da hakan ke kanki nasan da'a zamaninku akwai wannan fasahar to wlh da ke za'a fara gwadawa a kanki
ah ah wallahi daina jamin jafa'i tunda Allah ya tseratar dani oh ni hauwa'u yanzu har takai ga bature yayo wayar da za'a jona jikin mutum to meye amfaninta
ga amfaninta nan kin gani irinku masu gani suki kyalewa yake haskawa hanya yanzu ba gashi har kinga yadda fatata take haske ba
uhmmm lallai lamarin babba ne ta fada tana me rike haba
itako dije kuluwa tayi cewar da tayi farinta da kuma shawara ke damunta shiyasa ta matsu ta tashi ta tafi ganin taki tafiya saima qara malkwado wani zancen takeyi yasa dije miqewa ta shiga toilet batare datace da ita ko kala ba
wanka tayo ta fito daure da towel a jikinta
aikuwa caraf sai ji tayi tace oh ni 'yasu ke ko wannan yarinyar kina cin abinci kuwa ? ji kashin wuya kamar a zuba tiyar hatsi
ai in kinji ci daya ma kenan ni ko ke cin abinci wannan kashin wuyan nawa da kika gani wani sirri ne bari ma in fada miki daya a ciki ko wanka da kikaga nayi yanzu bada sabulu nayi ba dan ni sabulu na najikina
😳 jikinki kamar ya?
ai sbd ramar tawa da tayi yawa wata rana ina wanka lokacin an siyo mana wani sabulun wanka girmansa yakai kwanan sha to shine fa ina cikin wanka dashi na nemeshi na rasa nayita nema ban gani ba hae na haqura nace bari nayi da ruwa kawai ina zuba ruwan naga kumfa na tashi shine fa na fara lalube koda na duba sai naga ashe lokacin da nake murzawa ya subuce ya fada cikin kashin wutan nan nawa da kika magantu akan shi to da nayi niyyar in dauko shi kawai sai nace bari in barshi na huta idan na tashi yin wanka ba saina sha wahalar murza sabulu ba
qarya kikeyi dan uwarki 🤣🤣🤣
taji hajiya ta fada
😂😂😂
*managed pls*
*vote*
*comments*
*with 08066364077*
*Alqalamin khady* ✍
[12/13, 2:06 PM] +234 703 100 3999: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀
TA ME GARI
NA
khadeeja usman
2⃣7⃣
up
up
up
irin wannan cigiya haka masoya tame gari lallai dije tasha jaje to an nemota da kyar tace a gaisheda masoyanta dan haka ina muku fatan alkhairi tare da jinjina da miqa godiyata gareku masoya ta me gari masu yimin magana ban samun amsa musu da wuri suyimin uzuri ba lallai dan an gani online ya zamana ina kan whatsapp bane ta yiyu wani uzurin nakeyi amma naji wasu masu abar a kusa sun fadamin magana amma banji haushi ba nasan so ne ya kawo hakan amma kuyi haquri
jin da hajiya tayi ana buga kofar yasata saurin shigewa toilet ta rufo har saida taji bugun ya lafa ta jima a cikin toilet din jin da tayi an daina bugun yasata dan bude qofar ta ziro kai kasancewar a tsorace take sai taji kamar muryar dije na fadin ku bita bandakin ku kamota ai kuwa da sauri ta fito ta fara qoqarin shiga cikin wardrope din amma kasancewar ba irin wadda mutum zai iya shiga bace abu ya gagara ganin hakan yasa ta tura kanta kasan gado tare da jan ciki harta shige duk wani motsi da zatayi gani takeyi dije na kallonta yayin data dinga karanto duk wata aya data sani kai harda hadisai gashi ba damar tayi juyi haka ta kwana a gurin batare da tayi baccin kirki ba har aka kira sallar asuba a kunnenta kafin ta zamo ta fito ta shiga toilet da kyar tayo alwala aikuwa tunda tahau sallaya taketa jera salloli tare da addu'ar Allah ya kareta daga sharrin jinni🤣
ita ko dije saida tayi me isarta kafin ta miqe ta dauro alwala ta haye gado ta kwanta cikin zuciyarta tace oh ni dije ina karya da aljanu ina cin uban mutane Allah yasa dai basa ganina bakuma sa jina kada su zo daukar fansa tana wannan tunanin ko itama taji kamar motsi a dakin aikuwa da sauri taja bargo ta rufe har kanta ta fara karanta ayatul kursiyu
ni ko nace su dije ashe ana....... 🙊
*****
washe gari yusuf na dawowa daga masallaci gari ya danyi haske dan dabi'arsa ce inyaje sallar asuba baya dawowa sai gari ya waye tarr yana shigowa ya riski hajiya a falo da gima giman jakunkunanta cike da mamaki ya karasa gabanta ya duka ya shiga gaisheta
ga mamakinsa amsawa tayi cike da fara'a kafin tace kun tashi lfy dai ko ?
duk lfy kalau am ya naga wadan nan jakunkunan kuma na miye?
nawa ne dama na yanke shawarar komawa gidana jira nakeyi ma ka shigo ince kasa a gyara shi yanzu dan nasan yayi kura
a zuciyarshi yace lallai khadija kin iya saiti
amma a fili saiya marairaice fuska yace haba hajiya me yayi zafi haka laifin me muka miki da har zaki ce zaki bar gidan nan lokaci daya kuma da gaggawa haka idan munyi miki laifi ne ai saiki fada mana mu gyara inma ita Aminan ce tayi miki wani abu ai saiki fadamin in dauki mataki a kanta dan baxan lamunci a bata miki ba
kafin ya gama rufe baki sukaji budewar kofa Amina ce ta fito sanye da dogon hijab dinta tare da carbi a hannunta fitowarta yayi dai dai da fitowar dije itama kusan a tare suka qaraso falon suna zuwa Amina ta gaisheda hajiya ta amsa cike da sakin fuska sabanin da dasaita samu rabon zagi
koda dije ta karaso gurin kowa ta shiga gaidashi koda ta zo kan hajiya ta gaisheta sam kin amsawa tayi sai dai ta maido mata da gaisuwar itako dije ta ci gaba da gaisheta jin ta kuma maido mata yasa tace hajiya aini ya kamata in gaisheki ranki ya dade
dukansu kallonta sukayi ganin yadda ta ke duddukar dakai itako dije tace
haba hajiya meye abin ranki ya dade anan dan Allah ki bari kada kisa su yaya su zaneni
duka fa kikace wane mutum ai ba wanda ya isa ya tabaki ya kwana lfy inaaaaaa ai kinfi karfin kowa
ganin yadda takeyi yasa dije saurin dakatar da ita ta hanya fadin wadannan jakunkunan fa baki akayi a gidan?
yusuf ne yace inafa baki a rigimar hajiya ce a motsa wai ita dole saita koma ainihin gidanta data fara zama kiji fa kawai rana tsaka tace zata tafi ai dole mu binciki kanmu ko mu tambayi dalili dan ni bazan taba yarda ta tafi ta barmu ba bayan kowa a gidan nan yasaba da ita
aikuwa dole in tafi in barku ko kuna so ko bakwa so dama can lalura tasa na zauna daku ba komai ba dan in kula da yadda zamanku zai gudana insa muku ido kasan ku yara farkon aure sai ana lura daku dan kun fiya rawar kai yanzu kuwa naga kunyi hankali ai gara in tattara in koma inda nafi wayo ko
haba hajiya gaskiya ni ban goyi bayan ki tafi ki barni ba in su Anwar suka tafi school ni da wa zan dinga zama yana debemin kewa cewar Amina
haba 'yar albarka ai zaki saba da sannu kinji kada ki damu zan dinga zuwa lokaci zuwa lokaci ina duba ku ai
kallonta dije tayi kafin tace au kice ma kin tafi baki tafi ba kenan tunda zaki dinga zuwa
ah ah ina nufin su in sun sami dama su dinga zuwa dubani ni me zanzo nayi a gidan yara kuma
dukansu saida sukayi dariya kasa kasa a haka suka tsinkayi muryarta tana fadin
ke Amina maza tashi ki dora abin kari mana kada abar bakuwa da yunwa a ranta tace duk da nasan ya zuwa yanzu Allah kadai yasan irin abincin data dibga taci na mutane taci nasu na aljanu amma a fili taci gaba da cewa ki debe duk abinda yakamata a girka kinji harda farfesun kajin nan duk ayi kada su lalace
toh Amina ta amsa tare da mikewa ta nufi kitcheen a ranta tana hamdala tare da godewa khadija data zama silar ganin wannan ranar a gurinta tana shiga ta shiga hada kayan break masu rai da motsi irin wanda yakamata ace wanda ya taka matsayi irin na yusuf ana ci a gidansa
tana tsaka da aikin dije ta shigo da sallamar ta ta qarasa inda take
ah ah haba ranki ya dade ke da kanki a kitchen kuma
dariya dije tayi kafin tace kai Aunty kema kin zama hajiyar kenan
ba dole ba irin wannan aiki da kikayi shekara da shekaru muna zaune da mata yau kinsa zata bar gida rana tsaka
au to tunda bakya son ta tafi bari inje in dakatar da ita ai ba matsala
ni na isa wlh ta tafi na dinga zuwa gaisheta ai kedai Allah yayi miki albarka wlh kin gamamin komai duk da cewa uwar miji uwa ce amma ita tata matsalar tasa na gundura da zamanta yanzu kuma Allah yakawomin mafita kice wai ta zauna ai sai dai kice in shirya yin rakiya
dariya dije tayi kafin tace ai na dauka kin fi son zaman nata ne da sai ince tasha zamanta kawai ta qarasa maganar tana dariya
itama Amina dariya tayi nan dije ta kama mata aikin suka gama sunata hirar hajiya akan abinda yafaru jiya
yau kam gida ko yara sun san ya canza inda kowa yaci yasha cikin nishadi bayan an gama ne yusuf yasa wani yaronsa yace yaje yasa a gyara gidan hajiya aikuwa cikin qankanin lokaci aka gama komai ya kira ya sanar masa an gama
.saida yadan qara sayen wasu abubuwan aka dan kwaskware gidan abinka da masu abin cikin qanqanin lokaci aka gyara ko ina fess tunda dama bawani komai gidan keda ba kawai kura ce
koda aka tashi tafiya hajiya kuka ta fara yi a ranta tana ta jama dije Allah ya isa data rabata da kujerar ta ta mulkin mallaka a gidan danta wadda bata tashi yin ritaya yanzu ba amma ko wannan ko'a cikin aljanun ta cika marar imani nan dai ta dinga sharbar majina har gida aka rakata yayin ita da dije ke zaune a bayan mota ko motsin kirki hajiya ta kasa har suka isa
sam ba wani farin ciki a fuskar hajiya hakan yasa dije rabawa ta bayanta ta rada mata a kunne naga alamar cutar sanyin nan bata rabu dake har yanzu dan haka zan kawo miki magani anjima kuma wlh kada ki sake inga kafarki kwana kusa kin koma gidan nan duk abinda kike buqata ki kira ki sanar za'a kawo miki in na bukaci kije zanzo cikin dare in sanar mikk kije naga yanzu kina ta kuka nasan kukan da kikeyi ko na miye ki kiyaye
gyada kai hajiya ta shiga yi a hankali tace naji ranki ya dade yusuf da duk abinda dije keyi yana lura da ita dan haka ya saki murmushi a ranshi yace khadija hooo duk wanda ya aureki zaisha fama
haka suka gama zama a gidan hajiya bayan yusuf ya kira wata qanwar hajiya akan ta zo su zauna tare sannan yasa a nemo musu mai aikin da zata dinga kula da gidan tare da me gadi nan sukayi musu sallama bayan ya vasu kudi tare da sanar dasu gobe zai dawo in Allah ya yarda
haka hajiya tanaji tana gani suka fice zuciyarta kamar ra fashe amma ba halin bayyanawa tana tsoron mutum aljan
*****
yau kwanan dije biyu a gidan yusuf kuma yaune zata koma gida yayin da kallo daya zakayi ma masu gidan ya zuwa yanzu ka tabbatar suna cikin nutsuwa
tunda akayi sallar la'asar dije ta shirya ta zo ta kame a falo
masu gidan ne suka fito suna dariya da alama hirar tayi musu dadi ganin dije da sukayi a zaune yasa su fadin
ah ah ranki ya dade dan yanzu sunan da suke fada mata kenan tunda sukaji a bakin hajiya me zamu gani haka kamar an gaji damu?
murmushi tayi. kafin tace ba batun gajiya illa dai inason in koma ne dan nayi kewar mutanen gidan
hmm kajita sai kace ba ita tacemin nan da can duk daya ne ba cewar Amina
bar ma ta wannan su wadanda take cewa tayi kewar tasu tunda tazo ko waya basuyimin ba sabanin da da kullum sai munyi waya da safe kinga alama ta nuna su basuyi kewarki ba kamar yadda kike cewa ke kinyi ta su
to ya za'ayi su kira kuce sunyi rashin kunya inaga shiyasa suka ki kira
ah ah ko dai ko dai??
ko dai me ?
ko dai an gwada musu irin na hajiyata ne shiyasa suka shiga taitatayinsu
dariya tayi kafin tace ina ni ina yiwa ysyyena haka kunga ni duk ba wannan ba gida nake so na kuma gama shiryawa a zo a kaini ko in hau taxi
rufa mana asiri ai mu bazamu yadda mu batawa mumina rai ba haba wane mu tashi maxa ki kimtsa in maida ke salin alin
ni nagama shiryawa ina yarana muyi sallama
nofal na bacci Anwar kuma yana gidan hajiya ko kin manta
ok hakane to bari mu mike mu saita hanya ta fada tana kokarin miqewa
Amina tace ta jirata inda tshiga ciki ba jimawa ta fito dauke
da leda a hannunta ta damkawa dije da farko kin karba tayi saida Aminar ta nuna rashin jin dadinta sannan ta karba fayi godiya har bakin mota ta raka su inda dije ta kame kyam a baya ba yadda basu yiba ta hau gaba tace ita tafi jin dadin zaman baya dole suka haqura suka kyaleta
a hanya ya tsaya ya qara mata siyayya inda suka nufi gida koda suka iso yamma ta danyi kasancewar yau weekend duk bamai zuwa aiki yasa mutan gidan suka zo garden suka zauna duka suna hira ana nishadi gabansu kayan fruit ne sai lemuka da ruwa inda duka suke hira ana babbaka dariya sam sun ma msnta da wata wai ita dije tunda kowa ya warke🤣
horn din da suka jiyo ne daga bakin gate yasa suka maida hankalinsu gurin inda sukaga motar yusuf ta danno kai kasancewar gilashin gaban a bude yake yasa ba'a suka ga ba kowa ciki sabanin na baya dayake a rufe🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*AWESOME WRITER'S ASS..* 🏮
(Place of excitation n'd pleasant writer's)
*TAME GARI*
NA
Khadeeja Usman
4⃣4⃣
*Kuyi hakuri nasami miss number ne a page din daya gabata amma fatan zaku fahimce ni*
Itama yusrah jiri-jiri ta Fara gani,hakan yasa ta nemi guri ta duka tare da dafe kanta datake ji lokaci daya Yana Mata wani mugun ciwo.
Shi kuwa Daddy Yana Gama musu jagora tare da Nuna musu kowanne sashi na bangaren amaryar sa wayarsa ta Fara ruri alamun Ana Kiran sa,hakan yasa ya fito ya nufo wajen,sai da ya gama wayar sannan ya nufo wajen daya hangi su mamy Amma ya Nuna Bai gansu ba Dan ya Kara kuntata musu Dan yasan ya zuwa yanzu sun shiga kidima da wani yanayi na kasa tantance meya ke faruwa.Yana fitowa ya hange su kuwa yashe a kasa,ita ko yusra h tana duke,cikin ko in Kula ya karasa inda suke,duk da yaga halin da suke ciki Amma ya Nuna Kamar Bai damu ba,Daya daga cikin direbansa ya Kira,cikin kankanin lokaci kuwa sai gashi Nan ya Kira su Habeeb yace suzo su taimaka asa uwarsu da matansu a mota akaisu asibiti.
Dukansu hankalinsu ya tashi ganin halin da suke ciki,musamman Naseer Daya san Yusrah nadauke da ciki Kuma yaga halin datake ciki,babu Bata lokaci suka sasu a mota suka nufi asibiti dasu,shi ko Daddy baiko bi ta kansu ba Dan ya San ya zuwa yanzu abinda ke damunsu kishi ne,Kuma burinsa ya cika,Dan haka Ya fito da waya ya Kira Hajiya baturiya yace Mata ya maganar da sukayi fatan komai ya kammala.
Amsa Masa tayi da an Gama komai ya zuwa yanzu dama jiran wayar sa takeyi.
Shikenan zuwa goben sai ayi komai ko?
Shikenan Allah yakaimu
Ameen!
Nan sukayi sallama ya Kira restaurant din dayayi order abinci cewar su kawo yanzu,aikuwa ba Bata lokaci sai gashi sun kawo abinci Mai Rai dai lafiya,Nan fa mutanenmu suka shiga kwasar gara da harrakawa.
***********
Itama yusrah kafin a karasa asibitin ta karasa sumewar hakan yasa ko da suka Isa duka daki Daya aka Basu tare dayi musu taimakon gaggawa kasanceawar tun suna hanya suka Kira Yusuf dayake Yana asibitin suna zuwa kuwa aka antaya wa su Hajiya mamy zurkudediyar alluran bacci,bayan an Gama musu duk abinda ya kamata an tabbatar sun farfado.
Suna asibitin Daddy ya Kira su yace su zo Yana son ganinsu.
Sun Dan jima kafin su zo suna zuwa yajasu part din mamy.
Bayan sun zauna ne yaga sun nutsu yayi gyaran murya tare da Yin addu'oi na musamman sannan yafara magana.
Nasan a matsayinku na 'ya'ya agareni nayi muku abinda ku kuke ganin ban kyauta muku ba,duk da cikinku babu Wanda ya nunamin hakan baiyi Masa dadi ba sai dai nasan kunyi shuru ne Dan kuyimin biyayya,Alhamdulillah naji dadi Kuma nayi farin ciki da Allah yabani yara masu biyayya
"Allah yayi muku albarka".
Ameen!!
Suka amsa gaba daya
Sannan Daddy yaci gaba,kuyi hakuri da auren Dana daura muku batare Dana tambayi Ra'ayin Daya daga cikinku,ko kuna da ra'ayin Kara aure ko bakuda shi,to banayi hakan bane Dan wani abu,ko dan na Bata ran matanku da mahaifiyarku ,sai dai nayi ne Dan gyara da duba duk abinda zai je ya dawo Nan gaba idan nabari abinda matanku da mahaifiyarku sukayi yaci gaba da faruwa,shiya sa nadauki wannan matakin,to Amma Ina son ku sani,Kamar yadda ban nemi izininku ba nadaura muku aure,haka Suma yaran da aka daura muku auren dasu babu wadda aka nemi Jin ra'ayinta Kuma suka amince,to dukanku munji dadi da kukayi mana biyayya Allah yasa yadda kukayi mana Allah yabaku masu Yi muku Kuma.
Ina son Kamar yadda kuka mini biyayya ku rike amanar da Allah ya Baku ku Kula da matanku,kuyi adalci tsakaninsu,ku tabbatar kunyi adalci dan gudun tashi da shanyayyen barin jiki ranar gobe kiyama,ku rike amanar da kuka dauka kuyi kokarin sauke nauyin dake rataye a wuyanku,Allah yayi muku albarka ya albarkaci aurenku da zuriyarku baki Daya,Ameen!!
Nan yaci gaba dayi musu nasiha Mai ratsa jiki da zuciya,sai da ya gama kafin ya shiga sanar musu plan din daya shirya akan su mamy har sai sun gane kuskurensu,Nan ya fada musu shirin dayayi gobe,dukansu sunji sun Kuma gamsu Dan haka ya fada musu plan dinsa na farko Daya shirya.
Kuyi managed
*Alkalamin khady* ✍🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*AWESOME WRITER'S ASS..* 🏮
(Place of excitation n'd pleasant writer's)
*TAME GARI*
NA
khadeeja Usman
4⃣5⃣
Washe garin ranar mutanen da suka rako amare daddy ya saita musu hanya,da Sha Tara ta arziki,inda kuwa ya tafi da tsananin farin ciki abinda aka musu,wasu Kuma da murnar zuwa makkan Nigeria (wato Abuja) .
Tun a ranar Daddy ya gwangwaje da amaryarsa mariya wadda a ranar tsohuwar soyayya ta motsa inda aka nunawa juna farin cikin kasanceawa ma'aurata.
A bangaren Naseer ma haka abin yake domin a dakin amaryarsa ya kwana inda suka Sha soyayya Kamar Daman can su masoya ne,yayi mamakin Zainab din matuka Dan baiyi tunanin wayewarta takai haka ba,Bai Kuma tunanin zai sameta yadda ya sameta din ba,Dan ya samu gamsuwa da ita dari bisa dari,Dan haka ko da gari ya waye da kanshi ya dinga Kula da ita,inda ita Kuma ta dinga narke Masa abinda ya qara sukurkuta shi kenan,ya Manta da cewar ma Wai auren Hadi aka musu.
A bangaren Habeeb kuwa shi harya Manta ma da batun wata Dije,tunaninshi kawaii halin da mamy ke ciki da Kuma Rabin ranshi wato sajifa,gani yake yi matakin da Daddy yace a aiwatar a kansu yayi tsauri Dan ko ba komai a barsu suji da damuwar da aka Dora musu Mana,gashi shi bashida niyyar rike Mata biyu Amma an kakaba masa,tunanin. Yadda zasu kwashe da sajida kawaii yakeyi,Daya gaji da tunanin ya mike ya nufi asibitin dan ganin halin da suke ciki.
Itama Dije a nata bangaren baccinta ta mazga Tama Manta Wai gidan miji aka kawota.
***
Yau kwanan su mamy biyar a asibiti,kullum allurar bacci aketa narka musu, musamman da aka tabbatar su biyun jinisu ya Dan hau,ita Kam yusrah Naseer da kanshi yake dada antaya Mata a cewarsa baya so tazo ta rusa Masa budget din cin amarcinsu.
Daddy ne ya iso asibitin,inda ya bada umarnin a dauki su mamy a maida su gida yau ayita ta kare.
Hakan kuwa akayi,cikin kankanin lokaci aka kwashe su a amblance aka antaya dasu gida,kasancewar duk baccin sukeyi babu Wanda ya damu,illah daukar kowacce da akayi aka kaita dakinta.
*****
Sannu a hankali mamy ta bude idonta,Wanda sai yanzu ta tabbatarwa da kanta da gaske ne mafarki takeyi Ashe, Alhamdulillah! Ta furta,tare da qoqarin mikewa,Amma saita ji ta kasa duk jikinta ba kwari,ga cikinta da take ji Kamar ankwashe Mata kayan cikinta,Kira ta shiga kwalawa Baseera Amma a banza Dan muryar ma Bata fita sosai,jitayi an bude kofar Dan haka ta dakata da Kiran,Daddy ne ya shigo bakinsa dauke da sallama,amsawa tayi da kyar,a ranta tana mamakin yadda take Jin jikinta,karasowa yayi Yana tambayrta lafiya?
Amsawa tayi da lafiya kalau,kawaii jikina ne nakejin ba Dadi,ga wani tsinannen matsiyacin mafarki da nayi,Wanda ya dauke ni tsawon lokaci ina yinsa ni ban farka ba,Kuma ban daina Yinsa ba, ga wata bakar yunwa da nakeji.
Murmushi Daddy yayi kafin yace,to yanzu dai kije kiyi alwala kiyi brush kizo kiyi sallah sai ki nemi abinda Zaki ci,ai ni Alhaji ban San ma sallar Kota kwana nawa zan Rama ba Dan wallahi nasan na Dade ina baccin Nan gashi baka Nan bare Kuma ka tasheni,su Kuma wadan can sakarkakarun yaran basuyi hausar su zo su duba ko ina raye ba,bayan ni a mafarkin nawa harda su na gani saboda son da nake musu da kulawa,kaga dai kamani inje in wanke bakina inzo in danci abinci sannan nayi sallah,duk maganganun da takeyi murmushi kawai Daddy keyi,Dan haka ya mike ya kamata din yakaita toilet ya fito,zuwa yayi ya sanar da Baseera ta hado tea Mai kauri ta kawo yanzu dakin mamy.
Komawa yayi ya zauna jiranta ta fito,nan yaji tana kwala mishi Kiran yazo ya kamata ta Gama ,suna Zama Baseera ta kwankwasa kofar ya Bata izinin shigowa,Nan ta kawo abinda aka umarceta ta juya ta fita,Saida ta shanye Tass ta Dan Kara kwanciya Yana Nan zaune har ta danji dai dai kafin ta mike ta nufi toilet ta dauro alwala tazo ta Fara sallar,batare da sanin ko ta kwana nawa zata Rama ba,Nan ya fice ya barta Yana hango cakwakiyar da za'a kwasa.
**************
Ita Kam Sajida rasa abinda ya faru ya dawo mata,Dan haka ta rasa abinyi itama dai yunwar takeji sosai,Abu daya ne Bata sani ba shin tun jiya ne taga abinda ya faru,ko kuwa yau ne,idan har gaskiya ne abinda ta gani me hakan ke nufi kenan? Ita Habeeb yayiwa kishiya ko me? Wacece? To koma dai wacece zata San ta shigo gidan da ba'ayi mijin dan mace biyu ba,dole ta nemi mafita,tabbas sun tarkowa kansu fitina,kowace ce yarinyar zata bar gidan da kafarta,da ire-iren wadannan tunanin ta mike a daddafe duk da jirin da take ji a haka ta shiga toilet ta wanke bakinta ta fito, direct kicin ta nufa ruwan zafi ta Dora yanayin dumi ta sauke ta juye a cup tasa spoon ta dinga diba tana Sha a hankali harta shanye,sannu a hankali taji cikinta Yana warwarewa ta Dan jima tsaye, sannan ta Dora ruwan tea ta hada Mai kauri tasha,Saida taji ta danji dai-dai sannan ta koma ciki tayi wanka Tayo alwala ta zo ta Fara sallah.
*****
Kwance take jikinsa tanata rusa kuka rarrashinta yakeyi akan ta daure Tasha tea din Daya hada Mata,
Cike da maseefa take fadin bazan Sha ba,macuci azzalumi,duka duka yaushe mukayi auren da har zakamin kishiya,idan har da gaske ne abinda nagani wallahi saika sake ni macuci kawai!
Daure zuciyarsa yayi da dukkan kalamanta Dan yasan akwai ciwo, Dan haka cikin taushin murya ya ci gaba da rarrashinta ko Dan abinda ke cikinki ki daure Kisha tea din Nan,
Ai dama nasan Dan abinda ke cikina kake wannan rawar kafar,to wallahi ko zan mutu bazan Sha ba sai dai kasani ko da mutuwa nayi,daga Kai har mahaifinka bazan taba yafe muku ba,Allah ya is........wata wawiyar hankada yayi mata ta fadi kasa,daga hannu yayi da niyyar Kai Mata duka yaji an rike hannun,waigawa yayi dan ganin Wanda ya rikeshi, Zainab ya gani batare data saki hannun nasa ba ta shiga girgiza Masa Kai,haba hubby! Me kk shirin yi? Duka ko me? Ni wallahi harka Fara tsorata ni,Namijin duka ai ko a tarihinshi baida want girma da daraja a gun matarsa dama mutane baki Daya!Sam Bai Dace dakai ba,ka tsaya ka saurari uzurinta,ba mamaki kayi Mata rashin adalci ne,Amma Bai kamata ka daketa ka hanata Kuka ba,ta karasa maganar tana Mai sakar Masa hannu,kayi hakuri na shigo muku wayarka aketa Kira Kuma naga Kiran gaggawa ne shine nakawo Maka,inata sallama naji shuru shine naji hayaniyarku na shigo kuyimin afuwa,tana fadar haka ta juya har takai bakin kofa ta tsinkayi muryar yusra na fadin,
Bakar munafuka ina ruwanki,wallahi tun kafin na Gama da wannan kasurgumin munafikin zan dawo kanki,wallahi tun kafin na waiwayo ki ki tattara ki koma gidan ubanki!.
Karasa ficewa tayi batare data tanka Mata ba,tana fita Dije dake tsaye tana dakon fitowarta Dan Jin news,Dan tun dawowarsu daga asibiti Dije tasan akwai aiki Dan tun ranar zuwansu taga abinda ya faru ta Kuma San abinda zai biyo baya shiyasa ta kitsawa Zainab abinyi,tana ko fitowa Dije tace,maza siyarmin da jaridar ya akayi?
Kama hannunta Zainab tayi kafin tace,muje kawai kedai na lura wannan shegiyar saina Nuna Mata banbancin rayuwar kauye da birni,
Me kike ci na baka na zuba! Kyalesu kawai nasan karatun Zama dasu zan biya Miki kema ki haddace.
Zainab na fita ya juya ya kalleta tare da fadin ke mind u'r tongue up to now idan wannan bakin bakin naki ya Kara furta wata kalma anan gurin wallahi sai nayi Miki dukan mutuwa stupid kawai! Yana Gama fadar hakan yasa Kai ya fita yabar Falon Rai a bace.
*******************
Waya Daddy yayi musu yace Yana son ganinsu duka dasu da matansu a main parlour,sun Dan dauki lokaci kafin suka iso dukansu su shidan,Zama sukayi a kasa Daddy ne da mama mariya zaune a saman kujerar zuwa can saiga mamy ta fito.
Kallo ta Fara bin kowa dashi kafin idonshi ya sauka akan Daddy da mariya.
Kai ni kharima na shiga uku!! Wannan wane irin nataccen mafarki nakeyi? Wai ko gamo nayine?
Mikewa Daddy yayi ya kamo hannunta tare da fadin ki nutsu kharima,ki shiga hankalinki ki fahimci abinda zan fada Miki,
Ah ah!!
Kada kace mun duk abinda ya faru gaskiya ne!!
*Toh fans ku Bata amsa kafin daddy*
*Alkalamin khady* ✍🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
*AWESOME WRITER'S ASS..* 🏮
(Place of the excitation n'd pleasant writer's)
*TAME GARI*
NA
khadeeja usman
4⃣6⃣
Kamarya!! Na kwantar da hankalina,bayan Ina ganin gayyar mutanen garinku a gidana,wato bayan wannan kodaddiyar Mai zubin mayun,harda Karin mutum biyu aka samu,no wonder,ashe shiyasa na dinga mafarkai kaje gidan marayu da sansanin 'yan gudun hijira ka debo mutane ka kawo su gidan nan,Ashe wannan gayyar ne suka bugo Mana sammako,ni wannan rashin son 'ya'ya irin na saude da inusa ban San Ina zasu kaishi ba,inba haka ba 'yar kwaya Daya ku gagara riketa,duk nasan kwadayi ke dawainiya da su,shine wato Dan sunga ita ta samu gurin Zama shine harda tattago wasu da hadota dasu,to wallahi Sam bazan lamunta ba dole su tattara su koma inda suka fito a yau basai gobe ba.Ta karasa maganar tana wani huci,idonta na kan mama mariya dake hakimce kan kujera,Jin maganganun da mamy ke Fadi yasata harde kafa Daya kan daya.
Duk abinda ta fada baisa Daddy ya Nuna Mata bacin ransa ba ko kadan,Dan yasan abinda zataji yanzu shine zai daga hankalinta,ya wargaza nutsuwarta,dan haka cikin sanyin murya ya Fara Mata magana.
Haba uwar gidana,me yayi zafi haka,kada fa ki Manta kece sarauniyar gidan gaba Daya Kuma shugaba a cikin gidan,ai irin wannan Bai Dace da tauraruwa Kuma lantarkin gida ba,Dan haka kiyi hakuri kizo kisamu guri ki zauna kiji me zan fada muku.
Wani sanyi taji a ranta,Wanda yasata sakin karamin murmushi ya lura da hakan,ita ko a zuciyarta tana ayyana idan har Zama suka zo yi to kuwa saita maida su kamar bayi,Dan duk masu aikin gidan sallamar su zatayi,daga mazan har matan Kai har maigadi ma,da wannan tunanin ta karasa ta zauna tana karkada kafa da hura hanci,Nan surukan suka shiga gaisheta,sabanin yusrah data mike ta fada jikinta tare da sakin kuka Mai sauti.
Cikin kidima ta shiga tambayrta me aka Mata ?
Cikin kuka ta Fara fadin wallahi mamy kice Masa ya sakeni,Dan wallahi bazan Kara Zama dashi ba,mugune Azzalumi Wanda Bai San kima da darajar soyayya ba,wallahi na tsaneshi,idan har Bai sakeni ba wallahi zan kashe shi daga shi har matsiyaciyar yarinyar.
Ban gane ba? Wace yarinya ce wannan da take Neman tarwatsamin farin cikin yarana?
Nuna Zainab yusrah tayi da hannunta.
Au! Au! Kice ku naku shirin na musamman ne,wato da tuggu da makirci Kika iso gidan,shine daga zuwanki yau Kika Fara shiga tsakanin Mata da miji ko? To wallahi baki Isa ba,inma uwarki ce ta kitsa Miki daga wannan bakin kauyen naku to kisani zaman maraya Dana karkara akwai bambamci,to Wai ma uwar me Kika kulla da har yaran da suke masifar son junansu kamar Laila da majnun suka samu sabani,har take cewa ya saketa?
Mamy Wai aurenta yayi.
Ke bana son iskanci wanne irin aure Kuma?to kodai kema kin shiga tarzomar mafarkin ne kamar yadda nayi?
Sajida dake zaune take Jin tamkar zuciyarta zata tsake ta fito,Dan ji takeyi duk wani abu da zasu ji to ko Rabin abinda takeji bazai kaiba,Amma sanin abinda ta shiryawa zuciyarta yasa ta danne tare da sakin murmushin dayafi kuka ciwo tace,tabbas mamy ba mafarki yusrah tayi ba gaskiya ne cewar duk mazajenmu sun Kara aure kamar yadda Habeeb yayi mun bayani, sakamakon rashin Jin maganar su da mukayi muka baro kauye Wanda sai yanzu nakejin tabbas bamu kyauta ba,abinda mukayi am........
Ke dayalla dakata ni bama na fahimtar ki sosai,shin mazajen naku ne suka Kara auren batare da ni mahaifiyar su na sani ba ? Shin Kuna nufin kucemin Kuma daga kauye suka dauko matan nasu? Kai wallahi karya ne.
Wallahi mamy gaskiya ne abinda Anty ta fada Dan Dana yiwa Naseer magana Akan inbai sakeni ba saina fada Miki sai yace ai harda kema anyi Miki Wai ina kyautata zaton ma itace wannan zaune kusa da Daddy.
Wayyo! Wayyo! Na shiga uku ni karima,kishiya da girmana Hamisu da gaske ne abinda suke fada? Ka fadamin inji ni aka yiwa kishiya,? Kishiya ma daga kauye? Wallahi bazai yiyu ba,nasan shirin mahaifinka ne,Dan ya tozarta ni,ni da zuri'ata,wallahi Bai Isa ba saina warware wannan mugun kullin da akaimun,yanzu na fahimci abinda ya faru,Amma yanzu zanyi maganin abun,Ina son yanzu ba sai andau lokaci ba Kai Habeeb da Naseer a matsayina na uwar data haifeku,ku warware wannan tsinannen auren yanzu ku sakar musu yaran su kafin nima nasan abinyi akan tawa,ta karasa maganar tana huci.
Dukansu kallon juna suka tsaya yi,yayin da shi Kuma Daddy ya tsaya Yana kallon mamy Dan yayi tsammanin fiye da hakan ma daga gareta,Saida maganganun data fada akan mahaifinsa sun Bata ransa Amma shi yasan matakin dauka yanzu.
Magana nake muku cikin tsawa ta fada,wadda dukan su su hudun suka shiga yanayin damuwa shikam Naseer a yanzu ji yakeyi daya saki Zainab gara tace ya saki yusra Dan ko zagin data Masa ya Isa ya saketa,shi kuwa Habeeb duk da baijin wani son Dijen a ransa Amma baijin ya tsani auren ko ita kanta,Kuma shi a tsarin shi ma babu saki ko da wa ya aura,Dan haka duk sukayi shuru.
Wallahi idan har baku sake su ba yanzu-yanzu na rantse da Allah saina tsine muku...
Ke kuma ki sani adadin sakin da sukayi kema adadin naki kenan! Cewar daddy Daya Mike cikin bacin Rai,yasan inda a abinda mamy ta tsana Bai wuce ace tabar gidansa ba,matar da ko 'yan uwanta Bata son zuwa wajensu,Dan haka ta girziza da jin furucinsa Wanda yasata saurin dagowa ta kalleshi.
Yes! nasan kinji abinda nace,
Yanzu Alhaji kana nufin idan yaran Nan suka saki wadannan 'yan kauyen Nima sakina zakayi?
Tabbas kuwa sakin ma uku!!
Idan Kuma na janye fa?
Aurenki na Nan.
Shikenan na janye furucina Amma Kai kana ganin kayimun adalci? Kayiwa yaran adalci?
Wannan ke kike ganin haka Dan haka na sallami kowa ku tashi ki tafi maganar da naso yi ayita wani lokacin,kuje Allah yayi muku albarka.....
*Alkalamin khady* ✍
Download Tame Gari Littafi Na Daya Complete
2 Comments
Masha Allah
ReplyDeletekhalifaibrahimdala112@gail.com
ReplyDeleteThank you for this comment