[14/01 10:15 am] Ummu Basheer: 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com

       *Litafan Marubuciyar*



  *RAYUWAR NAJWA* Yana cike da ban tausayi, *A KAN K'ANWA TA* *SAMHA* nayi *ALK'AWARI* zamu zauna tare dan mu d'in *ZURI'A D'AYA* ne, babu *YAUDARA DA CIN AMANA* a tsakanin mu.



 *PAGE* *1*~*2*




 *Gudu* take yi sosai fatan ta d'aya ta isa gida, da alama daga makaranta take, Dan Uniform ne a jikin ta, shiga gidan tayi tana faman sauke ajiyar zuciya, da sauri ta d'auki buta ta shiga bayi.


 Wata datijuwa ce ta fito daga wani k'aramin Kitchen tana cewa"Yanzu haka y'ar banzan yarinyan nan ce ta shigo da gudu, kamar...." Maganar ta ne ya katse lokacin da taga ta fito.

 Kallon ta tayi tace" *DEEJA* Allah ya shirye ki, dama nasan kece zaki shigo haka"

 Yarinyan da aka Kira DEEJA ta rik'e k'ugu  tace" Ameen shiriya ta addinin musulunci" tayi fari da ido.


 Tsaki tsohuwar taja tace" idan kin gama rangwad'a sai ki wuce ki d'auki abinci kici"

 DEEJA tace"Cab ai Ina yanzu gidan su lantana zanje, tayi gulma na inji mairo dan haka dole inje inyi maganin ta"


 Tsohuwar tace" Kai wannan yarinya akwai jaraban tsiya, wuce ki cire kayan makarantar tukuna"


 Tsaki tayi take" ke fa *INNA* kin cika takura" tana fad'in hakan tayi waje da gudu, Dan dama fitsari ne ya matse ta shiyasa ta dawo gidan.

 Sallati INNA tayi tana cewa"Allah ya shirye ki DEEJA"



 Gidan su lantana DEEJA ta nufa tana zuwa ta aike wani yaro ya Kira ta, Lantana na fitowa DEEJA ta cakumi wuyan rigar ta tace" Wa na kama, magulmaciya kawai, to Mairo ta fad'a min gulma na da kukayi"

Zaro ido Lantana tayi tana had'iye yawu da k'yar ta hau rantsuwa akan ba ita bace Dan tasan halin DEEJA, yanzu sai tayi mata duka, gashi ita ba k'arfi.

Tsaki DEEJA tayi tace"ki bar wani rantsuwa ne yarinya yau sai kin gane kuren ki" ai Nan ta hau kokuwa da Lantana, sai dambe suke, Lantana da taji a zaba sai ta fara kuka tana ba DEEJA hak'uri, amma Ina ko sauraran ta Bata yi ba, can sai ga wani mutum ya zo wucewa, Nan ya daka musu tsawa amma DEEJA bata bari ba, sai da yayi magana yace" Kai kun ci gidan ku ba magana nake muku ba?"

Rik'e k'ugu tayi tace"yo ai ita ce ta fara tsokana ta"ta murgud'a Baki.

Ganin DEEJA ce yasa mutumin wucewa ba tare da yace komai ba, tsaki taja tace"Shigigi plus gad'are = bitazaizai, ko Ina ruwan shi da mu" juyawan da zatayi sai taga ashe Lantana ta shige gida da gudu, tsaki taja irin zamu had'u d'in nan.


Gida ta koma tana zuwa ta tarar da INNA tana daka, samun guri tayi ta fara murza ido cikin fuskar tausayi tace" INNA yunwa nake ji, Zan mutu"😔

 Hararan ta tayi tace"to sai ki mutu in gani"

Kuka ta rushe da shi da k'arfi ta fara cewa"wayyo Zan mutu, jama'a INNA zata kashe ni"

 D'aukar mafici INNA tayi ta jefa mata tace" rufe min baki ja'ira"

Da k'arfi tace"wayyo yunwa, *YAYA NA* zan mutu kazo ka cece ni"

Mik'ewa tsaye INNA tayi tace" Yi shiru in d'auko miki kar ki Kira min Yayan Nan naki"


 Da sauri ta mik'a mata abincin, karb'a tayi ta fara ci, can tace"Kai INNA ta kin iya girki fa sosai, sai dai kin cika massifa"

 A fusace tace" Uwa ki ce mai massifar, kiyi min shiru kar ki ishe ni tohm"

 Dai-dai lokacin ne wani Kyakyawan saurayi, fari ne amma ba sosai ba ya shigo gidan, DEEJA na ganin shi ta mik'e tsaye da sauri ta Isa gurin shi tana cewa"oyoyo YAYA NA"

 Murmushi yayi cike da k'aunar k'anwar ta shi yace"oyoyo *K'ANWA TA*, mene ne ya same ki naga idon ki ya canza?"

 Juyawa tayi ta kalle INNA tare da nuna ta da hannu cikin shagwab'a tace"ga ta Nan wannan INNA, sai da taga dama ta bani abinci" ta murgud'a Baki.

Rik'o hannun ta yayi suka zauna kan tabarma yana cewa"INNA ki bar min *K'ANWA TA* ta huta please"

 Da sauri DEEJA tace"to kin dai ji koh tsohuwa?"

Dariya INNA tayi tace"naji naji 'yan mata Kuma takwara ta HADIZA"

B'ata fuska tayi tace"YAYA NA kaji ta ko wai nice HADIZA" ta fara kukan shagwab'a.

Da sauri ya fara lalashin ta yana cewa"A'a ba haka sunan ki yake ba, INNA ki gyara kinji INNA?"cikin lalashi.

Murmushi INNA tayi tace" Kai Dan Allah k'yale ni haka, yo idan ba sunan ta bane sunan wace ce haka?" Tashi tayi ta shige Kitchen Dan kawo mai abinci.


 Fito da wani leda yayi na tsire ya mik'a ma DEEJA, karb'a tayi tace"YAYA NA Allah ya k'ara bud'i"

Yace"Ameen K'ANWA TA"


 INNA na zuwa ya mik'a mata nata, Nan tayi godiya, aiko ya tasa DEEJA a gaba yace ai dole sai sunci abincin tare duk da taci nata sai da suka ci tare course kusan kullum tare suke cin abinci.



 Washegari da safe

 DEEJA na gani anci uban kwaliyya irin na 'yan k'auyen Nan duk anyi d'ige-d'ige a fuska, d'an k'aramin bakin nan nata yasha jambaki har ta gefe, sai wani rangwad'a takeyi a dole irin ta had'u d'in nan sosai, kayan makaranta tasa ta fito.

INNA dake dama Koko ta gan ta, tab'e baki tayi tace" oh ni HADIZATU irin wannan kwaliyya haka, Allah ya kyauta"

 Turo baki gaba tayi tace"yo Wai ni Ina ruwan ki da kwaliyya ta ne dad'in abin ma nafi ki kyau"😏

Tuntsirewa da dariya INNA tayi tace"waya yaga gwagwan biri"

Ihu DEEJA tayi tace"wayyo ni YAYA NA"

 Da Sauri YAYA ya fito daga wani d'aki da alama ma barci yakeyi, Yana zuwa ya hau tambayar meya faru,

Cikin shagwab'a tace"ba ga tanan ba wai nice gwagwan biri"

Zaro ido yayi😳 yace"Haba INNA yanzu K'ANWAR tawa ce kike Kira haka, ke ko gajiya ba Kya yi da sasafen nan Zaki sa min ita kuka?"

Tsaki INNA tayi tace"na sa tan kasan Allah *BILAL* ka fita ido na, na gaji da irin abin da ke faruwa akan yarinyan nan, kullum cikin sa mutane magana take kullum a k'auyen Nan sai ta janyo mana magana bata da aikin yi sai tsokanan Yara, manyan ma bata k'yale su ba, Kai Kuma ka hau ka zauna kan maganar ta, to ba zai yuwu ba a toh"

Kallon K'ANWAR shi yayi yace"kinji na YAYAN ta zo ki karya ki tafi makaranta karki kula maganar INNA da kullum ba ya k'arewa"

Cikin shagwab'a tace"ni gaskiya YAYA NA bazan Sha Koko ba, shayi da biredi Zan Sha"

Da sauri yace"oya shigo d'aki na in had'a miki, INNA akwai ruwan zafi?"

Cikin takaici tace"sai dai ka d'aura, 'yan gayu masu Shan shayi, Koko dai yafi lafiya in gaya miki yarinya"

 D'akin BILAL suka nufa DEEJA ta juyo tace" eh na dai ji bazan Sha Kokon ba ehe"😏


 Nan ko Yayan ta ya had'a mata tea and bread mai kauri tasha sannan ta wuce makaranta, duk k'awayen ta sai da ta fad'a musu tea and bread ta karya da shi, haka akayi karatun shima sai tsokanan y'an aji take ana tashi ta gudu dan kar su kama ta su jibga😂.


 A can wani lungu ta tsaya ta jira su Mairo, suna zuwa duk suka tuntsire da dariya, d'aure fuska tayi ai Nan sukayi shiru cikin Jin tsoron ta, Nan tace" yau gonar malam Audu za muje mu samo mangwaro da gwaiba"

Nan dukan su, su ukun sukace"Angama ranki shi dad'e"


 Mairo, Lantana da Hansai sune k'awayen ta, Nan suka nufa gonar ai ko sunci sa'a ba kowa Nan suka shiga gonan suka hau bishiya suna tsinkowa amma fa DEEJA bata hau ba dan ita bata hawa bishiya sai dai tasa su hau Dan shegen tsoro ne da ita, suna saukowa kamar daga sama sai ga malam Audu da gudu ya biyo su, ai Nan suka ruga da gudu suna tsere, shi ko cewa yake"yau Naga mayun Yara masu kama da aljanu ke Kam DEEJA garejin Yayan ki zanje sai ya biya ni" ganin sunyi Mai nisa shi Kuma baya iya gudu sosai sai ya hak'ura akan zai je gurin Yayan ta dan ita ce shugabar su Mairo.


  Dai-dai wani lungu suka tsaya ganin ya daina bin su, da kan ta DEEJA ta karb'a mangwaro da gwaiban ta raba musu amma nata duk yafi yawa, duk da sun san bata kyauta ba haka nan sukayi hak'uri saboda sanin halin ta, sai a wannan lokacin ne kowa ta nufa gidan su.


 DEEJA na shiga gida taga ba kowa a tsakar gida sai ta fara yin a hankali kar INNA ta ji shigowan ta, aiko zata shiga d'akin kenan INNA ta fito bayi tana cewa"sarkin yawo sai yanzu?"

 Juyowa tayi tace"tun d'azu na shigo fa kina bayi Killa Kashi kike Dan na jima"☹

"Ke dalla rufe min baki, uwar ki ce ke kashin, y'ar banzan yarinyan kawai, ni wuce ki bani guri kin tsare ni da ido"

 Juyawa tayi ta shige d'aki tace"oho dai gaskiya na fad'a"🤷🏻‍♀











   ***************************





 Alarm d'in dake bedside ne ya fara bugawa alaman lokacin da akayi setting d'in shi yayi, Kwance yake kan bed ya rufa da blanket, da k'yar ya iya fito da hannun shi ya kashe Alarm d'in ya cigaba da barcin shi, bayan 5 minutes alarm d'in ya k'ara bugawa, da k'yar ya bud'e blanket d'in ya fito, Masha Allah nace ganin wani handsome guy Kyakyawan saurayi Yana sanye da pyjama, offing d'in alarm d'in yayi sannan ya shiga toilet yayi wanka ya fito ya shirya cikin suit sannan ya rataye rigar doctors a hannun shi, yayi kyau sosai fan's, d'aukar briefcase yayi tare da nufan downstairs, cikin tafiyar k'asaita ya sauko, a dining table ya tarar da kowa suna breakfast, k'arasawa yayi, Mommy'n shi ya fara gaishewa sannan ya gaishe da Aunty'n shi, cikin sweet voice ta amsa mai, Nan wata yarinya y'ar kimanin shekaru goma sha shida ta gaishe shi, ba tare da ya kalle ta ba yace"how are you *HANNA*?"

 Tace"I'm fine"

Tea kawai ya sha ya mik'e tsaye yana duba wristwatch d'in shi, kallon shi Mommy tayi tace"Son baka ci komai ba?"

 Yace"I'm okay Mommy"


 Aunty'n shi tace" sauri kake yi ne *ASHRAF*?"

 Yace Cikin Shirin fita"Yeah, Aunty *MEERAH* I have patients, I don't want to be late"

 Tace"okay bye"


 Fita yayi tare da shiga wata mota mai shegen kyau, straight Hospital ya nufa, Yana zuwa ba tare da wasting of time ba ya fara duba patients d'in shi, bayan ya dawo office ne yayi wasu aikin.


 In the night


 Bai dawo gida ba sai around 8:00pm Yana zuwa ya tarar da Aunty MEERAH tana wani aiki a laptop ga HANNA tana Assignment a gefe, tana ganin shi tace" Welcome back Ya ASHRAF "

 "Hey little" abin da ya iya cewa kenan yayi ma Aunty MEERAH sallama ya haura upstairs, Yana zuwa bedroom yayi wanka sannan ya fito.

Mik'a ma HANNA chocolates and sweet yayi, aiko da murna ta karb'a tana godiya,

 D'aukar remote control yayi ya canja tasha zuwa MBC Action, yace"Aunty where is mom?"

 Tace"she's in her room"

  Yace"hope she's okay?"

 "Yeah kawai ta kwanta ne" tace

   Girgiza kai kawai yayi, tare da d'aukar wayan shi yana buga game.

Rufe system d'in MEERAH tayi tace"won't you have your dinner?"

 B'ata fuska yayi kawai ya girgiza kai alamar A'a, idan da sabo to ta saba da halin K'anin nata dan Sam shi magana bai dame shi ba.

 Can ya mik'e tsaye ya nufa upstairs, bedroom d'in Mommy ya nufa, ganin T.V nayi ga wuta a kunne sai ya kashe komai tare da ja mata blanket ya rufe ta, rage gudun A.C yayi sannan ya rufe k'ofar, bedroom d'in shi ya nufa Wanda Yana d'an gaba can da nasu, Yana zuwa ya d'auko laptop ya hau duba wasu abubuwa.

 
   A parlour ko har HANNA ta gama Assignment d'in ta sannan MEERAH tace su nufa bedroom su kwanta, da yake kowa da bedroom d'in ta.


   












.


*TAKU CE UMMU BASHEER*✍🏻
[14/01 10:15 am] Ummu Basheer: 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *3*~*4*





 

 *DEEJA ce zaune gaban wani yaro dake tallan mangwaro, d'aukar mangwaron takeyi ko wane sai ta lugwigwita, duk ta gama matsa mai mangwaron, can ta d'auki guda uku ta mik'e tsaye tare da saitin hanyar gida tace mai" yaro kasan yanda ake gudun barewa?"

Girgiza kai yayi alamar bai sani ba, Nan tace" to ka kalle ni yanzu zan nuna maka" ai Nan ta ruga a guje, da sauri yaron ya bi bayan ta da tire d'in tallan shi.


  Da gudu ta shigo gidan har tana d'an buge INNA dake tsakar gida, d'akin su ta nufa tare da kulle k'ofar, Sallati INNA tayi ganin wani yaro ya shigo tace"Kai lafiya? Mai tayi maka?"

Nan ya fad'a ma INNA, cike da takaici tace"wannan fitinaniyar yarinyan Allah ya raba ni dake in huta, ai sai ki fito y'ar banzan yarinyan kawai"

Lek'owa tayi ta window'n d'akin tace" bazan fito d'in ba, salon ki buge ni Koh to nak'i wayon"☹

INNA zatayi magana kenan sai ga BILAL ya shigo gidan, ai ko Nan INNA ta fad'a Mai abin da DEEJA tayi, murmushi yayi yace ma yaron"nawa ne kud'in ka?"

 DEEJA dake lek'e ta window tace"Naira goma ne fa kawai"

Yaron yace"duk ta lugwigwita mangwaron Kuma a gida duka za'ayi min"

  Da sauri ta fito tana cewa"Mai k'arya d'an wuta, yaushe na lugwigwita mangwaron,yaro sai d'an banzan k'arya"

 INNA tace"kin ci gidan ku, ai ke ce sarkin k'aryan"

Rik'e k'ugu tayi tace"ba ruwan ki da ni ehe"


  Nan ya fito da kud'i ya siye duka tire d'in mangwaron, Yana cewa"gashi nan sai kiyi tasha"

Ai ko tsale tayi tace"Allah ya bar mu nida Kai, ke Kuma INNA ki bar wani kallo na ba Sha za kiyi ba"😏


 Dariya tayi tace"dama nace Zan Sha ne? Wannan ai sai ke ayi ta shiga bayi"

Rik'o hannun YAYAN ta DEEJA tayi tace"YAYA NA muje ka bani abinci a baki" ta k'are cikin shagwab'a.


 Tab'e baki INNA tayi tace"oho dai ke kika sani, ni wallahi na k'osa kiyi aure in huta"


  Da sauri tace"waya ce miki zanyi aure? Tab lalai ma tsohuwar nan, wato inyi aure a raba ni da gidan Nan ko, YAYA NA yayi ta siyo miki tsire ke kad'ai, to ba zanyi auren ba nida YAYA NA Kuma mutu ka raba ehe"👯


 Shi dai BILAL murmushi kawai yayi yace" K'ANWA TA, kar ki damu da maganar INNA, fad'a kawai takeyi"


  INNA tace"ka bar wani kare ta, gaskiya dai na fad'i Dan aure dole yarinya tayi a toh"

Kuka DEEJA ta fashe da shi, lokaci d'aya BILAL ya rikice ya rud'e, rik'o hannun ta yayi ya fara aikin lalashin ta, da k'yar ta hak'ura tayi shiru, sweets da biscuits ya d'auko mata a d'akin shi dan dama Yana ajiye mata, aiko Nan ta hau bud'ewa tana ci, tana aika ma da INNA harara.





  DEEJA yarinyan ce ko ince budurwa ce y'ar kimanin shekaru goma sha shida, kyakyawa ce ta gaske fara ce tana da dimples a kumatun ta idan tayi dariya ga Kuma fararen hak'oran ta Wanda suke a jere sai wushirya, idan tayi dariya sosai take yin kyau, Daga ita sai YAYAN ta, sai INNA wacce mahaifiyar baban su ce wato kakan su, iyayen su sun rasu tun DEEJA na k'arama,  BILAL YAYAN ta shine uwa da uba a gare ta.

YAYAN ta yana son ta yana ji da ita, duk abin da take so shi yake mata, Kuma duk abin da take so shima yana so, duk abin da ta tsana to shima ya tsana, Yana kula da ita sosai gashi ya shagwab'a ta, DEEJA akwai ta da tsokanar mutane, gata da shegen tsoro, Naman fad'a takeyi sosai haka Kuma baya Bari a duke ta, Dan k'auyen suna girmama shi sosai suna k'aunar shi Kuma suna shakar shi, duk abin da za'ayi ma DEEJA baya yarda dan ko rigima tayi da wasu sai dai ya bada hak'uri amma baya yarda a tab'a mai K'ANWAR shi, Yana da wani gareji na gyaran mota da Machine, Yana da wasu aminai  guda biyu *FA'IZ* da *KABIR* , suna tare a Koda yaushe, duk a garejin suke aiki tare suna matuk'ar girmama shi da k'aunar junan su, Kuma suna taya shi son K'ANWAR shi,duk basu da aure, dukan su zasuyi shekaru Arba'in, a cewar su suna jiran BILAL yayi aure sai suyi, shi ko yace babu ranar yin auren shi dama sunyi, amma sunk'i yarda.



 DEEJA tayi primary har zuwa secondary zuwa j.s.s 2, gashi tana da k'okari, Kuma YAYAN ta ke k'arfafa mata gwiwan yi Dan yace so yake ta Zama lawyer, to da yake tana son Zama lawyer d'in sai ta dage, Amma fa akwai ta da wasa, mutane dayawa na mamakin irin k'okarin ta a makaranta duk da bata jin magana ga tsokanan tsiya, Amma Allah ya bata kwakwalwa, haka Kuma tana zuwa islamiyya, tana k'okari sai dai Wasa yayi mata yawa, haddar Qur'an ko tana k'okari tana yi, duk da wannan rashin jin nata hakan bai Hana BILAL ganin Rayuwar ta ya ingan ta ba, sosai ya dage gurin bata tarbiyya na gari, ita dai tsokanan mutane da rashin Jin magana ne matsalan ta, Wanda YAYAN ta Yana ganin yarinta ce idan ta k'ara girma zata bari, duk abin da ke faruwa INNA Bata Jin dad'i, ta kanyi k'orafi, to shi dai BILAL lalashin ta yake da bata hak'uri amma fa a bayan idon DEEJA, sai ya goyi bayan DEEJA a gaban INNA amma tana barin gurin zai ba INNA hak'uri.



DEEJA kyakyawa ce shiyasa samarin k'auyen ke son ta Dan tafi duk wata budurwa a k'auyen kyau da tsafta da yin kwaliyya, samareen na son zuwa gurin ta Amma suna tsoron YAYAN ta, duk Wanda yace Yana son ta sai tasa YAYAN ta yayi mai duka, Dan ita tace bata son d'an k'auye, ita d'an birni d'an gayu take so mai tsafta, ba irin samareen k'auyen ba, DEEJA akwai iya kwaliyya amma fa na y'an k'auye Dan idan tayi jagira da sa jambaki sai kunyi dariya, lafta shi takeyi, Amma fa ita a dole tayi kyau kenan, sannan akwai ta da son yin girki gashi Kuma ba iyawa tayi ba, Amma YAYAN TA ya koya mata dafa indomie, Dan wani lokacin siyowa yakeyi ta dafa su ci abin su, INNA dai tace Allah ya tsare ta taci taliyar y'an chaina, mai kama da tsutsa.







 *Wannan kenan*











  **************************







 Cike da tafiyar k'asaita yake saukowa daga upstairs, cikin shigar shi na doctors, Mommy na zaune a parlour tana kallon News.

K'arasawa yayi ya zauna kusa da ita Yana gaishe ta cikin sanyin murya, amsawa tayi tana cewa"Son har ka fito, hope you have your breakfast?"

 Duba wristwatch d'in shi yayi tare da d'aga mata Kai, HANA ce ta fito cikin Shirin zuwa school, fuskar ta d'auke da damuwa tace"Mommy I'm late, Uncle John yau sai ya dake ni"😔


 Cike da tausayin y'ar ta tace"don't worry My HANA Bari brother d'in ki ya sauke ki a school"

Mik'ewa yayi yace"oh Mommy I don't want to be late, meya hana ta tafi da Aunty MEERAH?"

Tace"sorry son, Wai batayi Assignment ba sai yanzu takeyi and she's late, please ka kaita she's your little sister"

Hanyar waje yayi yace"let's go don't waste my time"


Da gudu tabi bayan shi, har tana buge shi da zasu shiga mota, hararan ta yayi course ya tsani irin rawar kanta da yanda take yi, sunkuyar da Kai k'asa tayi Dan tasan tayi laifi.




Sai da ya Kai ta School sannan ya wuce hospital.





 *ASHRAF* Kyakyawan saurayi ne d'an kimanin shekaru ashirin da biyar, fari ne Kyakyawan gaske fuskar shi na d'auke da saje mai ban sha'awa, mahaifin su ya rasu da jimawa tun HANA tana k'arama, Aunty MEERAH ita ce babba sai ASHRAF sai HANAN wacce ake Kira da HANA, yayi karatun shine a k'asar waje inda yayi karatun shi na likita ya Zama cikaken doctor Wanda yanzu hospital na kanshi yake da shi.


  
   ASHRAF Yana da natsuwa gashi miskili ne, zaman shi a k'asar waje bai sa ya d'auki mugayen halayen su ba, Dan baya Shan giya Kuma Mata basa gaban shi, course shi miskili ne, baya ba mata fuska bare har su ce suna son shi, baya son magana haka Kuma idan surutu yayi yawa kanshi har ciwo yakeyi, Yana da tsafta ga iya dressing, baya son k'azanta, haka Kuma akwai wani hali na mahaifiyar shi da yake da shi wato k'in talakawa, Mommy ta tsani talaka, toh shima yana k'yamatar su.






Akwai K'anin baban su ASHRAF suna Kiran shi da Daddy Yana da Yara biyu *SAIF* da *MUFEEDA*, matar shi wayayiya ce y'ar boko suna shiri da Mommy, Amma fa Sam Mommy bata cika shiri da Daddy ba Dan Yana da kirki akwai kyautata ma talakawa, Yana da fad'a, Kuma Yana k'okari gurin ba yaran shi tarbiyya sai dai matar shi ta b'ata tarbiyyan su Dan SAIF shaye-shaye da neman mata shine aikin shi, MUFEEDA ko bata da kunya ga shi tayi ta sa matsatsun Kaya, Ashe ma abin da iyayen basu sani ba shine ita y'ar lesbian ce, (Wa'izzubila).




Mommy tana son yaran ta sosai tana Kuma tausaya musu rashin mahaifi da sukayi a Rayuwa, tana ji da yaran ta irin sosai d'in nan fa, suna da Mai aiki wacce ta jima tana musu aiki, suna Kiran ta da Babba, zata kusa Kai INNA a shekaru, ta iya girki sosai tana Kuma kula da gidan yanda ya kamata, shiyasa dukan su suke son ta, MEERAH tana aiki a wani company na Baban ta Wanda yanzu nata ne, tana da mota Kuma y'ar gayu ce sosai, tana da kyau, ta iya dressing, Amma har yanzu Bata yi aure ba Kuma bata da niyyar yi.




 MEERAH, ASHRAF da HANA suna matuk'ar son junan su, Kuma kowa ne na respecting d'in na gaba da shi, MEERAH ma bata cika magana ba sarkin maganar dama HANA ce.


 Matsala d'aya ne suke fuskan ta, na rashin mahaifi Wanda suke Jin gidan wani iri kamar basa cikin nishad'i, sau dayawa Mommy ta kan rufe kanta a bedroom ta jima, cikin wani irin hali, gashi tana fama da ciwon Asma, da yake ASHRAF doctor ne, sosai yake bata kulawar da ya dace, sai dai shima yakan zauna yayi ta tunani shin meyasa Mommy da Aunty MEERAH baza su yarda da k'adara ba?, Kullum tunanin shi kenan.



 ASHRAF Yana da aboki Wanda tare suke aiki a hospital sunan shi *SALIM* suna shiri sosai, SALIM Yana da kirki gidan su gidan mutunci ne yayi aure kwanan nan, Yana da surutu shiyasa sometimes suke fad'a da ASHRAF.










*Cigaban labari*






DEEJA.........











*TAKU CE UMMU BASHEER*✍🏻
[14/01 10:16 am] Ummu Basheer: 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *TRUE LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *5*~*6*




 *Dedicated to my sweet sisters*


*Muneera*
*Maimounath*
*Hubbey*
*Real Me Dambuce*
*Aisha s bayero*
*Ummie Xee*
*Meelat Ahk*
*Ruky ce*
*Bee bee die*
*Beuty queen*



 *Oh my hand wlh bazan iya rubuta sunayen ku ba dan Kuna dayawa Kuma har cikin raina Ina k'aunar ku, Wanda ban ambace su ba su d'in na daban ne, nagode sosai da k'aunar ku gare ni, love you all*😍


 *Up*

        *Up*

              *Up*



  🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
               *Had'in Uwa*
          🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

  *By AYUSH ILIYASU*

  *My sweet sister Ina taya ki murnan Kamala litafinki da kikayi, Allah ya sa ayi amfani da darasin dake cikin litafin, gaskiya kin fad'akar Kuma kin nishad'antar a litafin ki na HAD'IN UWA, kina k'amshi Ina Miki feshin Humbra gaskiya ke d'in ta daban ce, Allah ya k'ara basira hazak'a k'warin ido tare da laushin hannu Ameen ya Allah*

🌹.       🌹.       🌹.

 *Sai mun jiki a sabon novel d'in ki Mai suna MATAR SARKI*


  🌹

         🌹


 *Sister Xaynab marubuciyar DOCTOR DEEJERT, this page is yours, gaskiya kina k'okari sosai a novel d'in ki, Allah ya k'ara basira ya kare ki daga sharin mahassada, Ameen, sosai nake Jin ki a raina, ke d'in ta daban ce, Ayi ta suburbud'o Mana DOCTOR DEEJERT, course Ina matuk'ar son shi bare kuma SAMAREEN BANA, Ina yin ku irin dayawan nan*

 🌹

     🌹


*Heart you all*❤













 *Cike*  gurin yake da mutane, sai faman raba DEEJA da wata yarinya fad'a akeyi amma ta dage ita fa dole yau ta buge ta, da k'yar aka raba su, mutane sai cewa suke DEEJA bata jin magana, duk abin da za'ayi mata sai ta rama Sam bata da hak'uri, YAYAN ta ya fita hali mai kyau, ita ko mutumiyar ta ku sai wani murgud'a Baki take da k'yar ta wuce gida.


Tana shiga gida ta tarar da INNA tana tankad'en garin tuwo, wuri ta nema ta zauna ta na uban Jan tsaki, can ta kalle k'ofar gida tace"Zan had'u da ke ce yarinya, shegiya mai fuskar aljanu, kamar ALJANAR FATIMA"

INNA tace"yau naji shirmen banza yo ai ke ce mai kama da ALJANAR FATIMA d'in"😂

 Tace" ai wallahi kuwa yasan duk k'auyen Nan ba Kyakyawa iri na, kema Kuma kin San hakan tsabar bak'in cikin ki ne kawai"😙

  Ajiye tankad'en tayi tare da nuna DEEJA da hannu tace" Kin ci gidan ku, y'ar banzan yarinya"☹

 Mik'ewa DEEJA tayi tana cewa"oho dai gaskiya na fad'a, Kuma ya za'ayi in ci gidan mu, a Ina kike so mu zauna, ke nifa kin takura min yanzu sai in Kira miki YAYA NA"😒


Tsaki INNA tayi ta mik'e tare da nufan DEEJA, ai ko tana ganin haka tayi waje a guje tana cewa" y'ar tsohuwa ba zaki iya kamani ba idan Kuma k'arya ne fito wajen muyi tsere"😂

 INNA tsayawa tayi tana maida numfashi tace"jarababiya Zaki dawo gidan ai"



 Ai ko lokacin magriba nayi ta fara sand'a ta shigo gidan, INNA na Jin ta, ta k'yale ta, bayan Isha'i sai ga BILAL ya shigo gidan, ai ko DEEJA na ganin shi ta nufe shi tare da cewa"YAYA NA yau kar ka kula tsohuwar can Aljanun ta sun tashi, tun safe take zagi na"😔

 Da mamaki yace"wasu irin aljanu Kuma K'ANWA TA?"

INNA ce ta fito d'aki cikin takaici tace"wannan yarinya akwai jarababiya, nice mai Aljanun Koh? Ke Sam Baki da kunya amma ba laifin ki bane duk Kai kaja" ta nuna BILAL.

Cikin sanyin murya yace"kiyi hak'uri INNA"

Share hawaye INNA ta fara tace" dama idan banyi hak'uri ba to mai zanyi? Nidai Allah ya kawo min ranar da Zan rabu da ke in huta"🤧


 DEEJA dake gefe sai gunaguni takeyi, tana hararan INNA, can tace" yo ni INNA ance miki Zan bar gidan Nan ne to never in my life"😏 (ni ko nace su DEEJA an iya turanci ko da yake YAYAN TA na koya mata).


 Zaro ido INNA tayi 😳 tace" meye neba kuma y'ar Nan?"

Rik'e k'ugu tayi tace"yo kullum sai in ce kizo in koya miki turanci, amma sai ki wani cemin in raba ki da masu jajayen kunne to miye zaki wani tambaye ni"😏


 BILAL ko k'unshe dariyan shi yayi dan suna bashi dariya to baya son yayi DEEJA ta fara rigiman yana mata dariya.


Nan dai aka shirya Kuma Dan dama fad'an INNA da DEEJA na lokaci k'adan ne.


 Bayan kwana biyu


DEEJA ce zaune a tsakar gida, ga kwandon kayan kwaliyya a gaban ta, madubi ne rik'e a hannun ta sai faman goga jambaki ake a leb'e ga lips d'in ta d'an k'arami, k'awayen ta ne suka shigo gidan Suma sunci uban kwaliyya, duk an zane fuskar da bile.

Lantana ce ta d'auki wani k'aramin powder tana cewa"laahh Kun ga wannan Bari in shafa"

Da sauri DEEJA ta k'wace tace"banza kawai, uban wa yace ki d'auka, pool kawai?" (Wai fool take nufi😂)


Mairo tace"shegiya mai Zaki shafa a wannan fuskar taki kamar ta an taka kashi"😡

 Hansai da yake ita ce mai sanyin cikin su tace"ni dai kuyi ku gama mu tafi yamma nayi"

 DEEJA ta turo baki tace" ank'i d'in, y'ar bak'in ciki to sai na gama kwaliyya ehe kiji in gaya miki yarinya"😏

 Lantana tace"Ina da kyan ki DEEJA ba abin da zai sa Ina kwaliyya, gayu Zan dinga ma su garbati d'an gidan mai gari"

Wani irin tsaki DEEJA tayi a fusace tace" wallahi zamu dambace yarinya, ni Ina ruwa na da wani Garbati, ance miki ni y'ar k'auye ce irin ki, dalla ku tashi mu tafi"😙


 INNA dake d'aki tana jin su tace" yaran Nan Ina zaku?"

Mairo tace" lahh INNA ki daina ce mana Yara fa kinga Hansai aure zatayi, ai min girma"

 Bud'e Baki tayi cikin mamaki tace"eh naga alama y'an Mata"😧

 DEEJA ce ta shiga d'akin tace"kakaros za muje rabon katin bikin Hansai ce, bye-bye sai mun dawo"

Fita waje sukayi suka bar INNA Baki a bud'e.


Suna tafe suna hira yayin da DEEJA sai tsale takeyi a hanya, duk namijin da ya ganta sai ya kale ta, amma suna tsoron zuwa saboda Yayan ta, can zasu wuce sai ga wani gaye yasa wando duk ya zazago ya tatare da hannu a dole shi ya had'u, tsayar da su DEEJA yayi yace"Y'an mata how far?"

Lantana ce ta gyara gyalen ta tana mishi fari da ido, DEEJA ko kallon shi ba tayi ba, Mairo tace" ai ba mu San shi ba Amma kayi gaba ka k'ara tambayar wasu(a tunanin ta tambaya yake)

Tsaki DEEJA tayi tace"banza ke Kika tsaya Mai magana"

 Jan wandon shi sama yayi yace"gaishe ku nake y'an mata a don gari, so sai Ina haka?"

Da sauri Lantana tace" rabon katin biki za muje"

Habawa ai Nan DEEJA ta buge bakin ta tace" banza shegiya kawai wuce muje dalla"😡

Taran gaban su yayi yace"magana nake muku ke Ina son ki" ya nuna DEEJA.

"Kan bala'i" lantana tace

 A tare suka d'ebo k'asa suka watsa mai tare da rugawa a guje, ihu ya fara yana goge idon shi Dan ya shigan Mai, sai Jan wandon shi yake sama Yana zamewa, Allah ya Isa kawai yake ma su DEEJA.


Sai da sukayi nisa da shi sosai sannan suka tsaya suna mai da numfashi, can Lantana tace"Wai meyasa Baki son duk wani d'an k'auyen Nan dake cewa Yana son ki ne?"🤔


 DEEJA tace"Allah ya kyauta, y'an k'auyen Nan k'azamai ne, basa wanka basa wanke baki, sai warin tsiya suke"🙊

Hansai tace"Amma kuma ai dole wata Rana kiyi aure"

Tsaki tayi tace"yo ni in ma zanyi auren meye zanyi da d'an k'auyen Nan, ke nifa d'an birni Zan aura d'an gayu kuma"😒


Mairo tace"yo Wai ni meye ma auren Nan?"

DEEJA tace"Dalla can wawuya ke Baki sani ba, to ai girki Zaki dingayi kina share d'aki idan anyi Miki jere irin na amaren Nan shikenan fa banza"🙄


Hansai dai cikin tunani tace"gaskiya ance min ba shi kad'ai bane amma dai na manta da meye ne"🤔

Nan dai suka tafi sukayi rabon chewing gum, Amma duk Rabin DEEJA ta zuga su Wai a cinye. Kuji fa Mai wayau.😂











**************************




Zaune yake a office d'in shi, Yana aiki a laptop ga A.C yayi yawa a office d'in, hankalin shi gaba d'aya baya jikin shi domin idan ya tuna halin da Mommy'n shi ke ciki yau da safe sai yaji hankalin shi ya tashi, Dan ya barta kamar Bata Jin dad'i, wayan shi ne yayi k'ara kamar bazai d'auka ba can Kuma daga yaga sunan Aunty'n shi sai ya d'auka, cikin tashin hankali naji yace"I'm coming, just wai for me" Nan ya kashe wayan tare da fita office d'in da sauri dai-dai lokacin aka tsuge da ruwan sama Mai k'arfin gaske.



A 360 yake gudu kamar zai tashi sama, Yana cikin mota ne Yana driving amma gaba d'aya hankalin shi baya tare da shi sai tunani yake da tunanin rayuwar gidan su, Yana dai-dai kan bridge sai tunani yake kawai sai wata k'atowar mota ya gani a gaban shi Nan ya fara k'okarin kauce Mata Amma Ina hakan bai yuwu ba kasancewar ana ruwan sama Mai k'arfin gaske da yake lokacin damina ne, kawai sai motar ta kauce ya bugi k'arfen bridge d'in tare da fad'awa cikin babban ruwan dake k'asan bridge d'in gaba d'aya ya fad'a tsundum.















*Innalillahi wa'ina illaihir-raji'un*












*TAKU CE UMMU BASHEER*✍🏻
[14/01 9:50 pm] Ummu Basheer: 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *TRUE LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *7*~*8*





*DEDICATED TO Rahmat Nalele*


 *This page is yours Aunty Rahmat, Allah ya k'ara Miki tsawon kwana ya Baki nasara akan abin da kike nema, Thanks for your love and support, I love you wujiga-wujiga, ke d'in ta da ban ce Ina yin ki, heart you ❤*













*BILAL* a garejin da suke aiki na hango shi k'asar wani mota da alama gyara yake, KABIR ne yazo kusa da motan tare da duk'ar da kan shi yace" barka da aiki, an Kira salla fa ya kamata muje muyi salla"




Fitowa yayi Yana cewa" ok gaskiya Bari muyi salla"


 FA'IZ ne yace"gaskiya lokaci na gudu yanzu har la'asar yayi?"

 KABIR yace" ai a kwana a tashi ba wuya yanzu, fatan mu dai Allah yasa mu cika da imani"

 "Ameen ya Rabbi" BILAL ne ya fad'a haka lokacin da ya fita waje. Nan suka bi bayan shi.



 Gefen ruwa suka samu tare da Zama a kan wani dutse, kasancewar garejin su na kusa da wani k'aton rafi ne, inda ruwa ke wucewa, amma garejin su yana can d'an gaba k'adan, alwala suka fara.


Kamar ance BILAL ya d'aga kan shi sai ya hango wani abu cikin ruwa, da mamaki ya kalle su yace"ku kalli wani irin Abu a ruwan Nan ko mene ne?"

Da sauri suka kalli ruwan cikin mamaki, FA'IZ yace" kamar mutum fa"

KABIR yace"Kai makaho riga ne fa, kasan ruwa ba irin abin da baya kwasowa"

BILAL yace"idan haka ne kenan ruwan zai iya kwashe mutum"

Da sauri suka mik'e lokaci d'aya tare da nufa cikin ruwan da sauri, BILAL ne yayi sauri jawo shi tare da taimakon su KABIR ya fito da shi, cikin mamaki FA'IZ yace"aiko mutum ne"


KABIR yace"to ya fad'a kenan"

BILAL yace"Ina Jin bai mutu ba Dan Yana numfashi" Nan ya fara Danna mai cikin shi a hankali ruwa ya fara fitowa ta cikin bakin shi sai dai bai bud'e ido ba, Nan BILAL yace su taimake shi su Kai shi gida.



Nan Koh suka kai shi har gida, lokacin INNA tana kitchen, da sauri ta fito tana sallati, ganin an shigo da mutum gidan ba alamar Rai a tare da shi, kwantar da shi sukayi a wani d'aki, da sauri INNA ta fara tambayar su meke faruwa? Nan sukayi Mata bayani, sosai ta tausaya ma saurayin.



Duk kallon shi suka hau yi cikin mamakin ya akayi ya fad'a ruwan Nan? Sai a lokacin na samu ganin fuskar shi, shin ko kunsan wane ne? ASHRAF ne, ganin Yana numfashi sai suka bar shi k'ila zuwa anjima ya farka,



DEEJA ce ta shigo gidan da gudun ta, da sauri INNA tace"ke yi a hankali, akwai mara lafiya"

Zama tayi kusa da YAYAN TA tace"in gaya maka YAYA NA, wata ce nace ta bani goruba shine fa Wai sai dai in k'wace, idan bazan siya ba, to ni Kuma na k'wace shine fa na gudu"😂

INNA tace"Allah ya shirye ki, wallahi duk ranar da ta kama ki ba ruwa na"

Cikin haushi tace"nifa bana son shishigi dake nayi ne? Shiga Sharo ba shanu kawai"😏

BILAL yace"yanzu K'ANWA TA me kike so ne, INNA please ki rabu min da ita"

Tsaki INNA tayi tace"Allah ya kyauta muku, ni Bari in d'aura tuwon dare kar inyi dare da shirmen ku"

DEEJA ta Harare ta tace"YAYA NA, waye ba lafiya?"

Cikin lalashin ta yace"Wani bawan Allah ne muka ganshi cikin ruwa, yanzu haka Yana d'aki a kwance"

Mik'ewa tayi tace"Bari in ganshi" ta nufa d'akin.

Ba damar ya hana ta Dan kar taji haushi, INNA ko na kitchen.

 Shiga d'akin tayi da tsalen ta, tsayawa tayi cak ganin wani Kyakyawan saurayi kwance kan katifa, k'arasawa tayi tace"Kai wannan Kyakyawan, Anya mutum ne? Yo ko ma dai aljani ne? Amma Bari in gani ai Zan Gane in mutum ne ma" Nan ta d'auki ruwa cikin jug ta dage iya k'arfin ta, ta watsa mai ruwan a fuskar shi.


A razane ya farka tare da ajiyar zuciya mai k'arfi, Zama yayi yana cewa"innalillahi wa'ina illaihir-raji'un"

Yar da jug d'in tayi tace"Ashe Kai mutum ne?" Tayi dariya.

Kallon ta yayi tare da kallon d'akin Yana mamakin Ina ne Kuma Nan? Tuno lokacin da yake office yayi har zuwa lokacin da yayi accident har ya fad'a ruwa, cikin ikon Allah ya fito daga cikin motar da taimakon Allah, tun bayan ya fito bai k'ara sanin inda kan shi yake ba sai yanzu da yaga wannan Kyakyawar yarinyan.


Kallon shi tayi tace"halan dai Kai kurma ne Koh?"🤔


 Kallon ta yayi bai ce komai ba, ganin Yana kallon ta sai ta fita tsakar gida Tana cewa"YAYA NA Ashe kurma ka d'auko, to gashi can ya tashi ai ni da na d'auka ma aljani ne"😒

 Mik'ewa tsaye BILAL yayi ya nufa d'akin yayin da INNA tace"y'ar banzan yarinya, ya akayi Kika san kurma ne daga tashin mutum yanzu haka ma ke Kika tashe shi"

Tace"oho dai, ni bazan kula ki ba"😜


Yana shiga d'akin ya tarar da shi a kwance, yace"Sannu ka tashi? Ina fatan ba inda ke maka ciwo?"

Rik'e kan shi yayi yace"Kai na ne kawai, Amma Ina ne Nan? Suwaye ku?"


 Yace"mun same ka ne cikin ruwa, shine muka kawo ka nan"

Godiya yayi mai tare da mik'ewa tsaye Wai zai tafi gida, wani irin jiri ne ya d'ebe shi,da sauri BILAL ya rik'e shi tare da zaunar da shi Yana cewa"kayi hak'uri ka zauna, kar ka fad'i Kuma zaka je gida ka Bari ka samu sauk'i"

Bai so hakan ba Amma sai ya samu kanshi da kasa yin mai gardama, INNA ce ta shigo d'akin tana yin mai Sannu, da k'yar ya amsa, DEEJA ce ta shigo d'akin tana cewa"d'an kyakyawa ya tashi"tana d'an tsale.

INNA tace"marar kunya Mai ya shigo dake ne, wuce ki fita"😡


 ASHRAF ko kallon ta yayi a ran shi cewa yake Amma yarinyan nan bata da kunya, DEEJA ko tsaki tayi ta fita tana cewa"to ai sai ki cinye d'akin"☹



 Da daddare INNA ta kawo ma ASHRAF tuwo, ai ko kallon kwanan bai yi ba, bare yaci. Bayan duk sun gama cin abinci ne BILAL ya shiga gurin ASHRAF tare da tambayar shi ya akayi ya fad'a ruwa, Nan ya fad'a Mai cewa daga office yake yayi accident Yana hanyar zuwa gida bayan an Kira shi mahaifiyar shi ba lafiya, Nan yayi Mai Allah ya kyauta Kuma yace yayi hak'uri ya kwana biyu, ba da San ranshi ya amince ba.


 Washegari da safe


BILAL ya ba ASHRAF waya Dan ya Kira iyayen shi, kar su shiga damuwa, number'n Mommy yasa ya Kira ta, Nan suka gaisa cikin tashin hankali take tambayar shi Ina ya tafi? Baya son hankalin ta ya tashi tunda bata cika lafiya ba, yace ai wani aiki ne na gagawa ya taso mai yayi tafiya amma zai dawo in two days, fatan alkhairi tayi Mai sannan ya tambaye ta lafiyan jikin ta,tace ai taji sauk'i, Nan sukayi sallama.


Lokacin da Mommy ta fad'a ma MEERAH tayi mamaki sosai Dan tayi ta Kiran shi wayan shi switch off tana tunanin anya tafiya yayi kuwa, bayan ta Kira shi ta fad'a Mai halin da Mommy ke ciki gaskiya yanda yake k'aunar Mommy ba zaiyi tafiya ba duk yanda akayi something is going on, amma dai bari ya dawo.









K'auye


DEEJA na gani ta ajiye ruwa a bayi ta fito, ASHRAF ne ya fito d'aki zaiyi wanka, shi gaskiya k'yamatar k'auyen ma yake gaba d'aya, yanzu ace kamar shine zaiyi wanka a irin bayin Nan, gashi dai da safe ba laifi da tea and bread yayi breakfast, da k'yar ya sha dan ba yanda zaiyi ne.

DEEJA na ganin shi ta tsuke fuskar ta, tsaki yayi a ranshi tare da nufan bayin, da yake Yaya duk ya siyo Mai abin da zai buk'ata.

Yana shiga bayin ya fito da sauri Yana cewa"oh my God meye ne a cikin ruwan" ya k'are kamar zaiyi kuka.

INNA tace"ai ko babu komai, meye ka gani?"

DEEJA dariya tayi ganin yanda duk ya b'ata fuska tace"D'an birni meye ya koro ka?"😂


Tsaki yayi cikin takaici bai ce komai ba, nufan bayin DEEJA tayi ta d'auko bokitin ta nufe shi, habawa ai da sauri ya shige d'aki cikin tsoro, DEEJA dariya har da rik'e ciki tace"INNA d'an birni na tsoron k'adangare ashe?"😂

INNA sallati tayi tace"ya akayi k'adangare ya fad'a, ko bayan kin Kai ruwan be?"

 Dariya tayi tace"kalle shi INNA kuto mai Jan Kai ne"😂

Baya tayi tace"wuce kije ki zubar da ruwan, Kai Kuma ASHARAP zo ka shiga wankan"


DEEJA tsaki taja tace"Wai waya ce miki sunan shi kenan ASHRAF ne fa"😏

INNA tace"ke ni raba ni da sunayen y'an birnin nan"


ASHRAF fitowa yayi cikin haushi kamar ya mari DEEJA yake ji, Dan a rayuwar shi ya tsani k'adangare, DEEJA na ganin shi ta fara dariya, banza yayi da ita yanzu ace kamar yarinyan nan tana Mai dariya ai ko zaiyi maganin ta, shiga wankan yayi da k'yar yayi ya fito ya shirya.



DEEJA tace"d'an birni kazo muyi yawo in nuna maka k'auyen mu da yafi ko'ina kyau"


Tsaki yayi yace"ni sa'an ki ne?"

Murgud'a Baki tayi tace"to kar kaje d'in sai me"😏


D'aki ya shiga cikin haushi.


























*Akwai drama fa tsakanin DEEJA da ASHRAF*😜






*Ashrafdeeja team*



*UMMU BASHEER*
[16/01 3:12 pm] Ummu Basheer: 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *TRUE LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *9*~*10*





*DEDICATED TO ALL MY FAN'S*



*Wannan shafin sadaukarwa ne gare ku massoyan litafin A KAN K'ANWA TA, Allah ya bar zumunci Ina k'aunar ku a duk inda Kuke*❤







 *ASHRAF* ne zaune a k'ofar gidan su DEEJA, sai tunani yake kawai har ya gaji da zaman k'auyen bare kuma Yana da aiki ga Family'n shi can amma Yana rayuwa a wani k'auyen,ya godema Allah da yake raye,Kuma shifa yanzu baya Jin ciwon komai, kawai zai k'ara kwana ne saboda Yana cin kunyar Yaya BILAL, Yana ganin girman shi.


Tun daga nesa ya hango ta tana tafe tana d'an tsale har ta iso gurin, sanye take cikin uniform na islamiyya, zata shiga gida kenan sai ta dawo da baya tare da kallon ASHRAF tace"D'an birni mai sunan y'an gayu Ina yini"


Hararan ta yayi yace"ke Ina Wasa da ke ne, haka ake gaisuwa?"

Murgud'a Baki tayi tace"to Dan ka samu ma na gaishe ka"😏

Tsaki yayi ya kauda Kai gefe, Zama tayi ta dinga zuba Mai surutu Wanda duk shirme ne da k'uruciya, da ta ishe shi sai ya bar gurin, aiko taji haushi Dan haka ta shige gida, INNA ta gani tana jajagen kayan miya.


Ajiye hijab d'in ta tayi tace"INNA yau dad'i zaki Mana ne?"


 Tace"eh mai bakin kwad'ayi, Jan miya zanyi da shinkafa tunda ASHARAP baya cin tuwo"


Tab'e baki tayi tace"ke kullum sai kin b'ata mai suna, yaushe Kika wani iya Jan miyar birni, ki kawo inyi" ta karb'a tab'aryan.

INNA tace"ke wuce bani guri ke d'in mai Kika iya"


Wucewa d'aki tayi tace" to sai kiyi mu gani, y'ar tsohuwa"☹


Tsaki INNA tayi ta cigaba da aikin ta.



DEEJA na ganin INNA ta gama miyar ta faki idon ta taje kitchen d'in ta bud'e miyar, aiko miyar yaji nama, sai k'amshi ke tashi, d'eban gishiri da yaji tayi dayawa ta zuba a miyar tana dariyan mugunta tace"wa yaga miyar birni"😂



Duk suna zaune har da ASHRAF zasu ci abinci, spoon d'aya ASHRAF yayi ya zubar da sauri, wani irin azababben zafi yaji bakin shi nayi ba shiri ya shanye ruwan jug gaba d'aya, BILAL da INNA sai tambayar lafiya take, DEEJA da yake tasan mai tayi ai dariya k'asa-k'asa takeyi, mik'ewa ASHRAF yayi yace ya k'oshi, kamar zaiyi kuka ya shiga d'aki, Kai Ina ai ya Zama dole gobe ya bar k'auyen nan yaushe zai iya da irin wannan rayuwar ta su.


BILAL da INNA abincin suka ci Dan sanin meya same ASHRAF, ai ko a tare suka zubar da na bakin su, cikin mamaki da azaba INNA tace" ya akayi miyar yayi yaji da gishiri? Bayan lafiya nayi Miya na"😡

DEEJA tace"ai ke za'a tambaya"😒


Haushi da takaici duk ya rufe INNA ai Bata San lokacin da ta rank'washi DEEJA ba, wani irin ihu DEEJA tayi sai da ASHRAF ya fito cikin d'aki da Sauri, BILAL cikin fushi ya mik'e tsaye yace"haba INNA mai yasa kike takura ma K'ANWA TA ce, da kiyi Mata wani abu gara kinyi min dan *A KAN K'ANWA TA* bazan iya jurewa ba"


DEEJA ihu ta sake tace"Wayyo Allah na ta fasa min Kai, YAYA NA ka taimake ni wayyo"😫

INNA tace"rufe min baki ai ban fasa ba ma tukun, yanzu haka y'ar banza ke ce kika b'ata min miya"😡

BILAL yace"yi hak'uri K'ANWA TA, Bari in siyo Miki paracetamol dan nasan dole kiyi ciwon Kai"da sauri ya fita.


 ASHRAF dake gefe gaba d'aya ya cika da mamaki wannan wani irin k'auna ne tsakanin YAYA da K'ANWAR shi? Lalai akwai wani k'aunar jini Mai k'arfi a tsakanin su, tunda yazo ya lura da yanda suke, gaskiya bai tab'a ganin irin wannan k'aunar junan ba, sai yaji sun burge shi, amma fa Yana Jin haushin DEEJA yanda take rashin kunya, ganin bata bar ihun ba yace" ke marar kunya, kiyi mana shiru, duk kin cika gidan da ihun ki"🙉


Kallon shi tayi ta turo baki gaba tace"ba ruwan mutum da ni, ai gidan mu ne"😒


Tsaki yayi yayin da INNA tace"ai ASHARAP wannan da kake gani ba shiru zatayi ba gara mu fita harkar ta, zatayi ta gama ai"😆


Tashi tayi tace" ni dai ki fita harkar na ai kinsan dai YAYA NA Yana ji dani"😉

ASHRAF bai San lokacin da yayi murmushi ba.







 Bayan kwana biyu



ASHRAF da DEEJA kullum cikin fad'a suke duk da baya mata magana, ita ko tayi ta tsokanan shi, da yin mai abubuwa iri-iri, tun Yana Jin haushin ta har ya saba dan yasan halin ta ne,  INNA tana sa shi cikin nishad'i, bare kuma yanda BILAL ke kula da shi da yanda yake ji da K'ANWAR shi Yana burge ASHRAF, a yau ne yayi Shirin tafiya domin ya Kira driver zai zo d'aukan shi.



DEEJA ce ta fito daga gidan su Hansai dan gobe ne auren ta, ganin wata had'adiyar mota a gaban gidan su ne ya bata mamaki, ga yara sun cika gurin suna kallon motan, cikin gida ta shiga Nan taga ASHRAF tsaye Yana ma su INNA sallama kamar zatayi kuka tace"d'an birni tafiya zakayi?"😔

Kallon ta yayi Nan take yaji kamar ma kar ya tafi, Dan gaskiya sun d'an shak'u cikin kwanaki biyun nan da yayi.


INNA ne tace"Eh tafiya zaiyi ai zai bamu kewa"🤧

 DEEJA tace"wayyo da gaske tafiya zakayi?"😰

D'aga kai yayi alamar eh, yace" but Zan dinga kawo muku ziyara inshallah, Kuma Ina godiya sosai da taimako na da kulawa dani da kukayi"

Nan sukayi sallama, ya shiga mota, DEEJA ya hango a gefe kamar zatayi kuka, shima d'in daurewa kawai yayi ya tafi, Yana Jin ba dad'i.



DEEJA ta kalla INNA tace"gaskiya za muyi kewar d'an birni Koh"☹

Tace" kewa Kam ya zama dole dan ASHARAP akwai kirki ba ruwan shi da magana"🤧


 Turo baki tayi tace"yo nice mai maganar kenan?"😙


 Tace"oho ai kin sani"😆


Shiga d'aki tayi tana gunaguni, Wai a dole INNA tana takura mata.





 ABUJA





  A parking lot driver yayi parking, Nan ASHRAF ya fito, da sauri yaga HANA ta fito, cikin murnan ganin shi take mai barka da zuwa cikin murmushi da farin ciki ya tare ta suka shiga cikin gida.


Mommy da MEERAH ne a parlour, suna ganin shi suka mik'e, Mommy murnan dawowan shi take, yayin da MEERAH ke tunanin ko meyasa me shi dan taga cikin kwana biyu ya rame, bayan sun gaisa ne yaci abinci yayi wanka sannan ya sauko downstairs.



 MEERAH ce kad'ai a parlour tana dane-dane a system, k'arasawa yayi yace"Aunty MEERAH it seems like you want to talk to me?"

Murmushi tayi tace"oh har ka gane, wait tell me what you're hiding from us?"

Murmushi yayi ba b'oye mata komai ba ya fad'a mata, ta tausaya ma K'anin nata sosai tace Kuma kar ya bari Mommy taji hankalin ta zai tashi, haka akayi kuwa bai fad'a mata komai ba.







 Kullum cikin tunani yake, Yana tuno da Rayuwar da yayi a k'auyen su DEEJA, gaskiya sosai yaji yana kewar su bare idan ya tuno da Kyakyawar fuskar DEEJA sai yaji wani iri bare kuma idan ya tuno lokacin da take murgud'a Baki, he really likes that, idan tana dariya ba k'aramin kyau take ba, duk lokacin da ya tuno fad'an da suke da shi sai yayi ta murmushi.





 After two weeks



 ASHRAF ne zaune a office, yayi nisa a tunani har SALIM ya shigo bai sani ba har sai da ya d'an buga table sannan ASHRAF ya dawo hayyacin shi, cikin mamaki yace"when do you arrived here?"

 Tsaki yayi yace"ai nasan baka ji zuwa na ba, tunanin mai kake ne haka?"
Girgiza kai yayi cike da damuwa, Zama SALIM yayi yace" come-on friend fad'a min what's wrong with you?"


Kamar ba zaiyi magana ba can yace"I don't even know what to do, na fad'a maka rayuwar da nayi a k'auyen Nan, I don't know why sai tunanin yarinyan nan nake, komai zanyi sai na tuna ta, look ko aiki bana iyawa, I don't know why?"


 Murmushi yayi yace"friend gaskiya ka fad'a cikin love tsundum"😃

Kallon shi yayi cike da mamaki yace"LOVE? Like how?"

Tsaki SALIM yayi yace"I'm telling you the truth, wallahi kana son yarinyan nan ne, just believe me"


Kamar zaiyi kuka yace"please stop saying that, hakan ma ba zai yuwu ba, k'aramar yarinya ce fa sa'ar HANA Kuma ma y'ar k'auye, Sam yarinya bata da natsuwa, look she's not my type"


SALIM yace"ni dai gaskiya na fad'a ma, Kuma ai shi so ba ruwan shi da kyau, kud'i ko shekaru ni Ina ga kawai kace ka nema soyayyar ta hakan zai fi"

A fusace yace"kasan Mai kake cewa? Because you don't know her that's why you're saying that, ni ba son ta nake ba"

Yasan ko zai kwana yana fad'a Mai cewa son ta yake ba zai yarda da shi ba kawai sai ya k'yale shi, idan yayi wari zai ji, basu sake maganar ba Nan sukayi wani hiran.


 After one week


Gaskiya yanzu ya yarda da cewa son DEEJA yake so Kuma ba k'adan ba, komai nata na burge shi, muryan ta mai sanyi ne, dariyan ta Yana birge shi, tsokanar ta da tsiwan ta Yana bashi dariya, Yana samun kan shi cikin nishad'i duk lokacin da ya tuna ta, gaskiya ya Zama dole ya shirya yaje k'auyen domin ganin hasken idanun shi, sahibar shi, course he's really in love with her.





Shiryawa yayi cikin k'ananan Kaya, yayi kyau sosai,sai k'amshi yake, fitowa yayi cikin Shirin tafiya, Mommy dake zaune HANA tana mata massaging a kaf'a da mamaki tace"ASHRAF sai Ina haka? Naga kana sauri"


K'arasawa yayi kusa da ita yace"I'm going to meet SALIM ne he's waiting for me"

 Tace"okay sai ka dawo"


   Yace"yauwa, do you need something?"

  Tace"no ba komai"


Nan ya nufa parking lot tare da fito da wata shegiyar mota mai masifar kyau sosai, ya shiga ya d'auki hanyar k'auye.








DEEJA ko tun bayan tafiyar ASHRAF take jin wani iri, ko bikin Hansai bata wani cikin farin ciki, haka dai take Jin ba dad'i wani lokacin bata san meyasa ba, a haka dai aka kwashi tsawon kwanaki, Wanda a yau ma ta tsokana wani mai gona sun je ita dasu Lantana sun samu gwaiba dasu lemo shine yazo k'ofar gidan su Wai sai an biya shi, to gashi YAYAN ta baya Nan, INNA dake ciki sai faman massifa take.


Dai-dai lokacin ne ASHRAF ya iso k'ofar gidan, habawa ai Nan mutane suka dinga kallon motar Dan ya had'u over bare kuma na cikin motar wato ASHRAF. Fitowa yayi habawa DEEJA na ganin shi tayi tsale tare da tafa hannayen ta tace"INNA ga D'an birni ASHRAF"



 Gaishe da INNA yayi tare da tambayar ta meke faruwa, Nan ta fad'a mai, Nan take kuwa ya bashi kud'i ya bar gurin sannan suka shiga cikin gida sai satar kallon DEEJA yakeyi, Yana Jin wani irin son ta.










# *Ashrafdeeja team*





*UMMU BASHEER*
[16/01 5:36 pm] Ummu Basheer: 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *TRUE LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *11*~*12*













 *Shimfid'a* mai tabarma INNA tayi ya zauna, yayin da DEEJA ta zauna a gefen shi, INNA ce ta kawo mai ruwa tana cewa"ke Kuma tashi ki bamu guri, ko ke nayi ma shimfid'a?"


 Turo baki tayi tace" ni dai ki k'yale ni, Ina ruwan ki da ni"😙


 Murmushi ASHRAF yayi cike da k'aunar ta yace"INNA ki bar ta hira za muyi"😍

 Tab'e baki tayi tace"Ai in dai DEEJA ne sai ka kore ta"😆


 Wani irin kallon ta yayi cikin murya mai dad'i wanda bai san Yana da shi ba yace" wai haka *MY DEEJERT*?"

 Da sauri ta d'ago kai ta kalle shi wani iri taji yanda yayi mata maganar ji takeyi kamar yafi kowa iya Kiran sunan ta, Kai sunan ma ya fita daban wato deejert, murmushi yayi ganin ba tace komai ba.


Nan INNA ta zauna suka k'ara gaisawa da tambayar shi mutanen gidan, Can DEEJA ta mik'e da sauri ta shiga kitchen sai gata ta fito d'auke da wani samira, ajiyewa tayi kusa da shi tace"D'an birni kamar nasan zaka zo nayi d'an malele, kaci akwai dad'i sosai"

Lokacin da ta bud'e samiran sai da gaban shi ya fad'i ganin bai tab'a cin abin ba gashi yayi wani iri, dauriya yayi ya d'auki d'aya ya fara shi, "oh my God" shine abin da yace a ran shi saboda wani irin d'aci da yaji ga gishiri da yaji, INNA dai barin wurin tayi.


Cikin murna tace"yayi dad'i ko? Ai na iya sosai"😃


Da k'yar yace"gaskiya kin iya yayi dad'i"😰

K'ara tura mai kwanon tayi tace"ka k'ara ci akwai yawa idan ma bai ishe ka ba akwai wani"😃

Da sauri yace"A'a ya ishe ni wannan ma zan tafi da shi gida ne"😳


 Mik'ewa tsaye tayi tare da yin tsalen murna tace"yeeee ai na iya d'an malele"😂

 Shi dai da k'yar yaci guda uku zuciyar shi na tashi, gaskiya bai cin Yana son ta baya son ran ta ya b'aci da ba abin da zai sa yaci wannan jagwalgwalon, ni ko nace so hana ganin laifi.


Ruwa yasha sosai sannan ya kalle ta tare da cewa"yanzu ki bani labari?, Samareen ki nawa?

 Da sauri tace"Kai yo ai ni banda Samaree nifa yarinya ce"😳



 Kamar zaiyi dariya ya daure yace"waya fad'a miki haka? Yanzu ai kin girma saura aure"

Tace"ni fa ba auren da zanyi, ko Kai ma bak'in ciki kake min dan in bar gidan nan"😒

 Murmushi yayi yace"A'a but idan zakiyi aure ai sai kin bar nan"

Turo baki tayi tace"Kai nifa bazan yi ba ehe"😙


 Lalai akwai aiki ja a gaban shi, yace"shin kinsan cewa ke d'in kyakyawa ce?"😍


  Cikin farin ciki tace"dagaske kake?"🙈


Gaba d'aya wani irin nishad'i yake ji tabbas ya mutu akan k'aunar ta, kallon love yayi mata yace"sosai ma ai ke d'in tamkar tauraruwa ce mai haskawa a cikin duhu, you're beautiful"


Kalaman shi sun sanya ta cikin wani iri, cikin kunya ta rufe ido, dai-dai nan ne INNA ta kawo mai d'umamen tuwo tace"ASHARAP kaci tun da zafi-zafin shi, kar ya huce"


 Wayyo shi Kam ya shiga uku so suke su sa cikin shi ya b'aci dan bai Saba da irin cimar Nan ba, fara ci yayi kamar Yana tauna magani kamar yayi kuka yake ji.

 DEEJA ko cewa tayi"ke wai INNA sau nawa zan gyara miki sunan shi ne? Sai kiyi ta wani b'ata mai suna"😏


 INNA tace"y'ar banzan yarinya, wallahi ki kiyaye ni"


  Tace"oho dai gaskiya na fad'a Miki, ki gyara mai suna dai"🤷🏻‍♀


 ASHRAF dake cin tuwo kamar yayi kuka sai suka bashi dariya, yace"INNA ta ki k'yale ta duk yanda Kika kira yayi"


 Cikin haushi DEEJA tace"au haka zaka ce ma"😡

Da sauri yace"A'a ba haka nake nufi ba, kin san tsofafi basa iya Kiran suna dai-dai" ya k'are a hankali kar INNA taji.


Dariya DEEJA tayi tace"tsohuwar nan ai mai ran k'arfe ce tak'i mutuwa in huta"😂


 INNA tace"kin ci garin ku y'ar banza to bazan mutun ba"☹



Dariya DEEJA tayi-tayi , yayin da ASHRAF ke ta kallon ta cikin love tana matuk'ar burge shi ba k'adan ba, ya d'an jima suna hira sannan YAYA BILAL ya dawo gidan suka gaisa sannan ASHRAF yayi musu sallama ya tafi.







A hanya sai da yayi parking yayi amai sannan ya samu sukuni, kwanon ko da ta bashi yarwa yayi a gurin, Dan har ga Allah ba zai iya k'in karb'a bane shiyasa yazo da kwanon, lokacin da ya Isa gida wani irin farin ciki yake ji domin yaga masoyiyyar shi.






DEEJA ko lokacin da ya tafi sai taji wani iri da ma bai tafi ba.




 Bayan sati d'aya


 ASHRAF ya shirya zuwa gurin DEEJA domin ya sanar da ita irin son da yake mata, sanye yake cikin Kaya irin na India black riga da white d'in wando yayi kyau sosai, lokacin da sukayi waya da SALIM dariya ya dingayin mai, yace ai gara yaje tun yanzu kar wani ya k'wace mai ita, shi dai bai ce mai komai ba tsabar haushin dariyan da yake mai.





Haka kawai DEEJA ta samu kan ta cikin farin ciki yau, wanka tayi ta shirya cikin wani Riga da skirt red mai ratsin black, Wanda YAYAN TA ya sa aka d'inka mata dan ko da yaushe cikin yin mata d'inkin kaya yake, gaskiya tayi kyau, dan tana da shape, kayan kwaliyya ta d'auko ta zauna ta tsantsara kwaliyya, jambaki har gefen baki,ga eye shadow da ta lafta, har eyeliner an jashi sosai, da ta gama sai da tayi murmushi ta kalla INNA da ta saki Baki da hanci tana kallon ta,tace"INNA ya Kika gani ne"


 Tsaki tayi tace"ke Koh wani irin aljanu ne suka shige ki? Wannan irin kwaliyya haka, uhm shiyasa nace kina kama da Gwagwan biri"😂

Mik'ewa tsaye tayi ta rik'e k'ugu tace"ke INNA mai yasa ke a rayuwar ki kin cika black stomach ne?"😏




 Tab'e baki tayi tace"ke Kika san bla stoma ai"☹




Dariya tayi tace"da Allah ki daina mata ma turawa yaren su"😆



 Wani yaro ne ya shigo yace"Wai Ana Kiran DEEJA inji lado d'an gidan mai gari"


 Tsaki tayi tace"kace bata Nan, uwar mai zai bani?"😏


INNA tace"kin ci gidan ku, yaron mai gari ne fa wuce ki je" ta nufe ta, ai ba shiri ta fita waje tana zuwa ta gan shi yaci uban glass ga wando duk ya sauko Wai a dole gayu kenan.



Tsaki tayi tace"meye ne?"👯

 Washe yellow d'in hak'oran shi yayi yace"Son ki nake yi, Kuma Zan aure ki, kinsan ni d'an mai gari ne abin da nake so shi za'ayi"


 Tace"Amma dai ka Raina ni kamata kace Wai kana so na, d'an k'auye, k'azami da Kai, yo ni ko mai garin ne bai Isa ba bare Kai, dallla wuce kafi in Kira maka YAYA NA"😙


 Kwatsam ko sai ga shi Nan ya dawo gida, k'arasawa gurin yayi Yana tambayar lafiya, aiko DEEJA ta fad'a mai, tsaki yayi yace"Kai lado bar Nan gurin, kar Kuma in sake ganin ka"


Lado yace"yo daga kawai nace Ina son ta"

Cukume mai wuya BILAL yayi idanun shi jajazur yace"k'ara mai-maitawa?"

 Lado yaji wuya Nan ya fara zaro ido Yana cewa" Dan girman Allah, ka sake ni, wallahi ba son ta nake ba"


 DEEJA ko sai tsale takeyi tana cewa"mazge shi YAYA NA"


 Sakin shi yayi aiko ba shiri ya ruga a guje, BILAL ko Jan hannun ta yayi suka shiga gida.






 Da shigar su gida ko 10 minutes ba'ayi ba sai ga motar ASHRAF yayi parking a k'ofar gidan, sallama yayi ya shigo, Nan suka gaisa inda yake ta satar kallon DEEJA Dan he really missed her, sai dai kwaliyyan ta ya bashi dariya, haka dai suka gaisa inda DEEJA tace"d'an birni in kawo ma d'an malele?"😃



 Da sauri yace"A'a yau na k'oshi sosai a gida"😳


 Tace"To zaka zo shine sai ka ci abinci ba sai ka bari sai kazo Nan ba"😙


Murmushi kawai yayi Yana ma Allah godiya da taimake shi, yau da yayi amai ba k'adan ba, haka sukayi ta hira inda yayi musu sallama yazo zai tafi Nan yasa Yara suka dinga shiga da kayan abinci irin su taliya, shinkafa,dasu wake, sai wani jaka mai kyau Wanda cike yake da kayan kwaliyya dasu sweets, chocolates da biscuits.


Kallon DEEJA yayi cikin sanyin murya yace" Deejert Ina son muyi magana, dafatan kina saurare na?"

 Tace"eh ai Ina da kunne"😃


 Murmushi yayi yace" tun Ranar da na Fara ganin ki zuciya na ta kamu da son ki, Deejert Ina k'aunar ki, Kuma son da nake miki da aure ne"


 Kallon shi tayi tare da zaro ido tace".............😳






























# *Ashrafdeeja team*






*UMMU BASHEER CE*
[18/01 1:12 pm] Ummu Basheer: 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *TRUE LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *13*~*14*




  *This page is yours Sister Maimounath, Allah ya bada nasara akan Exam's d'in da zakiyi Allah ya bada sa'a Ameen, we're going to miss you Sis*😍




  *My K'awas Badeeyerh (beuty queen) kina rai na ban manta da ke ba, Ina yinki irin sosai d'in nan tawan*❤



  🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂

       *HAPPY BIRTHDAY UMMIE GARKUWA*

🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂



 *Ina tayaki murnan zagayon ranar haihuwar ki Allah ya k'ara tsawon kwana, UMMU BASHEER wishing you Happy life, Happy birthday once again GARKUWA*

🌹.        🌹.        🌹.      🌹.











 *DEEJA* tace" da gaske kake yi?"😳

 Gyara tsayuwa yayi yace"of course I mean it, Ina son ki Deejert, Zaki aure ni?"


  Rufe ido tayi cike da kunya tace"Eh Nima haka...."🙈 Da gudu ta shige gida cikin farin ciki da kunya wai d'an birni na son ta.


Murmushi yayi cike da farin ciki he can't believe it wai Deejert d'in shi na son shi ita ma, shiga mota yayi ya d'auki hanyar Abuja cike da nishad'i.



 INNA ta na ganin DEEJA ta shigo tace"ke 'yar nan lafiyan ki kuwa?"

 Tsale tayi ta rungume INNA tace"Kunya nake ji, Wai Yana Sona Kuma za muyi aure"🙈


 Zaro ido INNA tayi tace"wa kenan DEEJA?"😳


 K'ara rufe fuska tayi tace"shi nake nufi man"🙈

 INNA cikin mamaki tace"shi wane, ko bashi da suna ne"🤔

 Sakin INNA tayi tace"ke k'wakwalwan ki baya aiki ne to ina nufin d'an birni ASHRAF"😙


  Tace"ke yarinyan nan ban son k'arya ASHARAP d'in ne ke son ki?"☹

  Tace" Yo ni k'arya Zan miki? Ai sai kiyi tayi"😏


INNA sai mamaki take, wato dagaske ne, to ita dai zata sa musu ido na kwana biyu taga iya gudun ruwan su.





  Wani irin soyayya ne ke tsakanin ASHRAF da DEEJA, mai wuyar fassaruwa, da k'yar yake kwana biyu bai gan ta ba, tabbas son ta yayi mishi illa, Yana son ta Kuma ita ma tana son shi, sau dayawa sai dai tayi-tayi mai shirmen ta yana dariya, ko ya dinga d'aukar ta pictures tana dariya Dan ya hana ta yin kwaliyyan mahaukatan Nan, ita Kuma Yana burge ta, iya magana, iya dressing ga kyau Dan ASHRAF Kyakyawan gaske ne, Samareen k'auyen sai haushi suke ganin tak'i su ga Kuma shi ASHRAF kyakyawa ne, duk abin Nan dake faruwa Yaya BILAL bai sani ba tunda ba zama yake a gida ba sai dai ASHRAF yaje garejin su ya gaishe shi, sau dayawa Yana mamakin meye ne ke kawo ASHRAF sosai, ni ko nace baka San ya sace ma k'anwar ka zuciya ba😂.




An d'auki tsawon wata d'aya a haka, sai soyayya suke, ranar weekend ne ASHRAF yazo k'auyen, DEEJA na gani a d'aki sai faman shafa powder take, INNA dake tsakar gida tace"Idan kin gama fentin fuskar sai ki fito, ASHARAP na jiran ki"


Can sai gata ta fito, tayi kyau fuskar Nan anyi d'ige-d'ige, sai dai bata sa jambaki ba, wani lace ne a jikin ta pink, sai d'an k'aramin hijab black, k'arasawa tayi tare da yin fari da ido tace"Nayi kyau ko?"


 Murmushi yayi yace" sosai my Deejert kinyi kyau"😍


 Tsale tayi cikin murna, b'ata rai yayi yace"Amma nace miki bana son kina tsale ko? Ke yanzu kin girma"


  Da sauri tace"na daina to, Amma dai ba kayi fushi ba ko?"😔

   Yace"No Deejert, but ki daina kinji?"


 D'aga kai tayi alamar toh, sannan suka fita waje dan a yau Yana son zagaye k'auyen course Yana bashi sha'awa kasancewar lokacin damina ne, ko'ina yayi Kore Shar gwanin ban sha'awa, sai k'amshin k'asa ke tashi Dan ba'a jima da ruwa ya d'auke ba, suna tafe suna d'an hira duk yawancin maganar ta shirme ne biye mata kawai yakeyi.



  Yana mamakin kan shi wani lokacin ganin shi d'an masu kud'i, Amma Yana soyayya da y'ar k'auye Kuma yarinya sannan kalla yanda yake yawo a cikin k'auyen.


 DEEJA ce ta hango wata yarinya da sauri ta nufa gurin ta tace" wa na kama, shegiya mai kan kwakwa"😏

 Da sauri yarinyan tayi yunk'urin guduwa ai ko DEEJA ta rik'o ta tace"Yau sai nayi k'ul-k'ulin kubura da ke mai kama da Maya"😡

 ASHRAF ne yace"ki k'yale ta mu tafi"

  Tace"A'a sai nayi maganin ta yau"👯


  D'aure fuska yayi yace"kizo mu tafi nace, ko ba Kya ji ne"

 Tab'e baki tayi tace"Zan kama ki ne hmm"☹

  Abin da ya k'ara bata haushi shine yanda yarinyan ke ta kallon ASHRAF, tace"to kur yafi k'arfin ki, dalla wuce kafin in zabga miki Mari"😙

  Ganin tana b'ata mai lokaci sai ya rik'o hannun ta su tafi aiko sai santsin gurin ya jasu suuuu suka fad'a a tab'o, gaba d'aya kayan su, sun b'aci cikin zafi ya mik'e tsaye ganin yanda ya b'aci Allah ya sa ma ba mutane sosai da yaji kunya, ni ko nace ai idan DEEJA ce yanzu aka fara😂.

Tsaki yayi kawai ya juya zuwa gidan su DEEJA, bin shi tayi a baya.


  INNA na ganin ASHRAF ta fara sallati tace"oh ni HADIZATU lafiya? Meye ne ya same ka?"

Ranshi duk ya b'aci bai ce komai ba, sai ga DEEJA, Nan INNA ta tambaye ta.


Gyara zama tayi tace" santsi ne ya kwashe mu INNA, mu ka tafi suuuu sai a tab'o"😂

 Haushi duk ya cika shi, INNA tace"kin ci gidan ku yanzu Kika sa ASHARAP d'in ya fad'i?"

  Tace"gaskiya INNA sai mun Kai ki makarantar yak'i da jahilci"😙


 A fusace tace"uwar ki za'a kai, b'ace min da gani"😡


Dariya tayi ta shige d'aki dan cire kayan, Haka INNA tasa ASHRAF a gaba akan dole yayi wanka, da yaso tafiya haka ne dan DEEJA ta b'ata mai rai, wanka yayi Allah yasa Yana da wani kayan a mota sai ya canza, Haka yayi ta rawar sanyi ga mura sai atishawa yakeyi, ko sallama basu yi da DEEJA ba ya tafi.





Lokacin da ya Isa gida Mommy ta ga yanayin shi Nan ta fara tambayar shi ya akayi Ina yaje, Kuma wannan muran fa Dan taga lafiyar shi k'alau da safe, Bai wani tsaya b'oye-b'oye ba ya sanar mata cewa akwai yarinyan da yake so.


Cikin farin ciki ta tambaye shi wace ce yarinyan Kuma 'yar waye a Nigeria? Nan ya fad'a mata sunnan k'auyen su DEEJA da aikin Yayan ta.

 Cikin firgice Mommy ta tashi tace"kana nufin 'yar k'auye kake son aura?"

  Yace"Eh Mommy, meya faru?"

Tsaki tayi tace"ni kullum buri na ka aura wayayiyar mace 'yar mai kud'i ba Wai k'aramar yarinya ba, 'yar k'auye talakawa, Ina Sam hakan ba zai yuwu ba"



 Kallon ta yayi idanun shi jajazur yace" Mommy please don't say that, I really love her"

Cikin b'acin rai tace"ASHRAF ni kake fad'a ma cewa kana son wata?, To Bari in fad'a maka tun wuri ka cire ta a ranka" tana fad'in haka ta bar bedroom d'in shi course dama har d'aki ta biyo shi.

Gaba d'aya ya rasa meke mai dad'i haka ya kwana cikin damuwa.


 Washegari yaje ya samu Aunty MEERAH dake zaune a backyard kasancewar weekend ne ba aiki, tana zaune tana dana system, ni Koh ummu basheer nace aikin ta kenan ita.



 Tana ganin shi ta ajiye system d'in a gefe tace"my brother, are you okay?"

Zama yayi a kan grass carpet da take zaune yace"I'm not okay Aunty MEERAH please help me, kiyi Mommy magana please"

 Tace"what happened?"


Nan ya fad'a mata yanda sukayi da Mommy, ta tausaya ma K'anin nata ganin ya fad'a tarkon soyayya gashi Mommy na son ba shi matsala, hak'uri ta bashi sannan tace zata nemo mai mafita.





 B'angaren DEEJA kuwa ganin kwana biyu ASHRAF bai zo ba sai ta fara damuwa tana tunanin ko Yana fushi da ita ne, sai ta zauna tayi ta tunani har YAYAN TA ya gane, daya tambaye INNA sai ta fad'a mai batun soyayyar DEEJA da ASHRAF, yayi mamaki dan bai tab'a kawo wani Abu ba, Kuma yayi farin ciki dan ya lura ASHRAF nada halaye na gari Wanda zai sa ya bashi DEEJA, Kuma yana da natsuwa yasan zai kula mai da K'ANWAR SHI, ya kuma amince da shi, bayan ya bar gidan ne ya nufa gareji, Yana zuwa ya fara ba su KABIR labari Suma sunyi farin ciki, FA'IZ ne yace"Amma kana ganin ba wani matsala Koh?"


  Dariya yayi yace"idan ma da matsala bazan d'auka ba Dan *A KAN K'ANWA TA* Zan iya yin komai in har bai kauce ma hanyar addini ba"


 KABIR yace"gaskiya Amana ce a gare ka mu Kuma muna taya ka rik'e Amana muna bayan ka"



  BILAL yace" *A KAN K'ANWA TA* na hak'ura da farin ciki na, *A KAN K'ANWA TA* muke Rayuwa a  k'auyen nan domin farin cikin ta Kuma *A KAN K'ANWA TA* nayi *ALK'AWARI* Zan sata farin ciki"


 Duk murmushi sukayi inda FA'IZ ya goge d'an guntun hawayen shi.













 ASHRAF na bedroom d'in shi Aunty MEERAH ta shigo cikin riga da wando tayi rolling d'in veil d'in akan ta ga wani sunglass da tasa, murmushi tayi tace"brother ka shirya yau Ina son ka Kai ni Inga K'ANWA TA Kuma in-law na"

Murmushi yayi dan rabon da yaji farin ciki tun bayan ya fito gidan su DEEJA har suka zame a k'asa.


Shiryawa yayi cikin farin shada yayi kyau, kan shi ba hula, sai dai Sam baya son irin shigar da Aunty'n shi keyi gashi gidan surukai za taje, but babu daman yayi mata magana yanzu sai ta ma fasa zuwa, fad'a ma Mommy cewa sukayi zasu wani company na Baban su, Dan su duba gurin.









Da missalin k'arfe 2:00 pm suka Isa k'auyen............


















*MUJE ZUWA MASU KARATU*




 *TAKU CE UMMU BASHEER*
[20/01 6:24 pm] Ummu Basheer: 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *TRUE LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *15*~*16*



  *Dedicated to Real Sadnaf*


    *S🅰BON S🅰LOON Y🅰UDARA*



  *Up*

       *Up*


             *Up*


  *Congratulations sister Ina taya ki murnan Kamala litafin ki Mai sunna SABON SALOON YAUDA, Allah ya k'ara basira da d'aukaka, Allah ya sa ki Fara wani lafiya Ameen*

❤❤❤❤❤❤❤❤❤

   *TAKI  CE UMMU BASHEER*

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹





 *Da missalin* k'arfe 2:00pm suka Isa k'auyen, direct gidan su DEEJA ASHRAF ya nufa, bayan yayi parking ne suka fito tare da yin sallama suka shiga gidan.



 DEEJA na zaune tana aikin nata wato tunanin ASHRAF, INNA ko kula ta Bata yi ba dan har ta gaji da mata magana, ganin ASHRAF ya shigo tare da wata kyakyawar mace yasa ta mik'e tsaye da sauri tace"ASHRAF Kai ne?"

Murmushi yayi mata, inda INNA ta shimfid'a musu tabarma suka zauna sannan suka gaisa, Aunty MEERAH sai kallon DEEJA takeyi, Kamar ta San fuskar ta.

ASHRAF ne ya gabatar musu da Aunty MEERAH, suka k'ara gaisawa, sai lokacin Kuma DEEJA ta fara Jin kunya, Nan ya nuna ma Aunty MEERAH DEEJA a matsayin wace yake so, tayi mamaki sosai ganin yarinya ce sa'ar HANA wai ASHRAF yake so, ai ko Mommy idan ta gan ta ba zata yarda ba.



 Yaya BILAL ne ya shigo gidan, Aunty MEERAH na ganin shi ta mik'e tsaye cikin razana da firgici ta nuna shi da yatsa tace" *MALIK* Kai ne?"


  Cike da rud'ani yace" MEERAH kece a gidan mu, mai kikeyi a k'auyen nan?"


 Cikin tashin hankali tace"gidan ku?, Kana nufin DEEJA K'ANWAR KA CE?"

  Yace"Eh K'ANWA TA ce"


 Dukan su kallon su suke basu san meke faruwa ba, Cikin zafi MEERAH tace" ASHRAF daga yau ba Kai ba yarinyan nan, ko ita kad'ai CE rage mace a duniya baza ka tab'a auran ta ba"


 Cikin firgici yace"what do you mean? Wai ma meke faruwa, do you know him?" Duk ya jero mata tambayoyi.


 Cikin tsananin mamaki da tashin hankali BILAL yace" ASHRAF ita yayar ka ce?"

 Amsa mai ASHRAF yayi, ba k'aramin mamaki BILAL yayi ba cike da takaici yace" daga yau bana son ka k'ara zuwa gidan Nan, Kuma na raba ka da DEEJA ba Kai ba ita"

 Da sauri ASHRAF ya rik'e hannun BILAL idanun shi jajazur yace"ka taimake ni kar ka raba ni da ita wallahi Deejert ita ce rayuwa ta, I can't live without her please"

 Fusge hannun shi yayi cikin zafi yace"get out of my house now" ya nuna mai hanyar fita.

 Aunty MEERAH tace"ba sai ka kore mu ba, Amma Ina son ka sani ASHRAF ba zai tab'a auren k'anwar ka ba"

 Jan hannun ASHRAF tayi tace"let's go, na fad'a maka baza ka tab'a auran ta ba"

K'wace hannun shi yayi yace"let's go off me, waye ne shi? Kuma meye dalilin da yasa kike fad'in haka? I just want to know what's happening?" Ya k'are cikin damuwa tare da kallon DEEJA wacce ta daskare a gurin tana tunanin ko meke faruwa.

 BILAL cikin zafi yace"you will never understand, just get out of my house"



 Tsaki MEERAH tayi tace" wannan ai ba gida bane, sai dai gidan kaji"tana fad'in haka ta fita.

 A fusace BILAL ya rik'e hannun ASHRAF ya Kai shi har waje Yana cewa"idan na k'ara ganin ka a k'auyen Nan da sunan kazo gurin K'ANWA TA to zaka ga abin da Zan maka, domin *A KAN K'ANWA TA* bazan jure ba" yaja tsaki ya rufe k'ofar gidan.


  ASHRAF kamar zaiyi kuka idanun shi jajazur da k'yar ya shiga mota, ko driving ya kasa sai MEERAH ce tayi driving ita ma dauriya kawai takeyi.




 BILAL na shigowa INNA tace"na riga na gane meke faruwa, yanzu Kuma na gane ko wane ne ASHRAF, shiyasa nayi shiru dan zuciya na wani iri yake min, Amma na yarda da k'adara" ta share hawayen da suka zubo mata.




DEEJA ko da ke tsaye da k'yar tace"YAYA NA wace ce wannan matar da ta shigo, Kuma meyasa zaka ce wai kar ASHRAF ya k'ara zuwa gidan Nan bayan kasan yanda muke son juna"

 Tsawa ya daka mata yace"bana son tambaya, Kuma daga yau na raba ki da shi baza ki tab'a auren shi ba"

Wani irin ihu DEEJA tayi tace"wayyo Allah na, na shiga uku na lalace, YAYA NA kar kace haka"

 Ba zai iya jure jin kukan ta ba kawai sai ya bar gurin, d'aki ya shiga, ya kulle tare da Zama a k'asa ya rik'e kan shi Yana girgizawa, abin da ya d'aure min Kai shine ganin Yana hawaye.


 DEEJA ko kuka ta saki tace ma INNA"Dan Allah INNA ta kice ma YAYA NA kar ya raba ni da ASHRAF, Ina son shi, Kuma Ina son inyi aure inje birni, in dinga Hawa mota da gidan bene"😭



 Share d'an guntun hawayen ta INNA tayi tace"gaskiya DEEJA abin da kike so ba zai tab'a yuwuwa ba, ki bar maganar ASHRAF, kinji y'ar Nan"


 Mik'ewa tsaye tayi tace"ni wallahi shi nake so, wayyo na shiga uku, wayyo ASHRAF"🙆🏻



 ***********************








 Lokacin da suka Isa gida, suna shiga parlour suka tarar Mommy tana kallon News, tana ganin yanayin yanda suka shigo sai hankalin ta ya tashi, cikin rud'ewa ta fara tambayar MEERAH meke damun su?.



 Da k'yar MEERAH tace"shin Mommy ko kin san wane ne ASHRAF yake son aura?"


Girgiza kai tayi tace"A'a wacce ce, y'ar wani mai kud'in ne?"


Kamar MEERAH zatayi kuka tace"Mommy ki bar maganar wani mai kud'i idan da mai kud'in ne kawai da sauk'i, ba kowa ce yarinya yake so ba illa *K'ANWAR MALIK NASIR, KHADIJA* ZURI'AR ALHAJI RUFA'I" tana fad'in haka ta fashe da kuka mai k'arfi.




 Mik'ewa tsaye Mommy tayi da sauri yayin da wani irin jiri ke d'iban ta, Sai a lokacin ne ASHRAF ya gano dalilin da yasa MEERAH ke fad'a mai hakan, shi kanshi ya firgita Kuma yayi mamaki ba k'adan ba.


Cike da bak'in ciki Mommy tace" kana hauka ne, to wallahi baza ka tab'a auran ta ba, daga yau ka rabu da ita ko da kuwa ita ce autar mata to wallahi bazan tab'a yarda ka aure ta ba"


Idanun shi jajazur yace" Mommy meyasa zaki hana abin da Allah ya hallata? Akwai aure tsakani na da ita meyasa Zaki ce haka?"

 A fusace MEERAH tace"Are you out of your sense? Mommy'n kake fad'a ma hakan?"

Mommy tace"ki bar ni da shi, idan shi ba shi da zuciya mu muna da shi, ka rasa macen da zaka aura sai ZURI'AR ALHAJI RUFA'I, 'YA ga ALHAJI NASIR da HAJIYA MAIMUNA?  To wallahi ko zaka mutu ne baza ka tab'a auran ta ba"



  Cikin wani irin hali yace"Mommy please save my life, I swear I can't live without her, Mommy Ina k'aunar ta"


 A fusace tace"yaushe ka Zama haka ne? Yanzu ni kake fad'a ma baza ka iya rayuwa idan babu wata mace ba? To wallahi bazan yarda ba, just get out of my side"




 Upstairs ya nufa zuciyar shi na wani irin mai zafi, Yana zuwa ya shiga toilet ya sakar ma kanshi shower, ko yaji sanyi, bayan ya fito kawai ya zauna sai tunani yake.





***********************



 Cikin sati biyun nan ta b'angaren ASHRAF da DEEJA suna wani irin cikin hali ne, ita kullum cikin kuka take da rok'on YAYAN TA akan ya amince da ASHRAF Amma Sam yak'i kula ta, ASHRAF ko na cikin damuwa sosai haka SALIM zaiyi ta bashi hak'uri, Amma shi gaskiya ba zai iya hak'ura da DEEJA ba course yana mata wani irin so ne ba k'adan ba, Kuma a shirye yake ya aure ta baya jin tsoron wani abu.



  A yau yayi Shirin zuwa k'auyen su DEEJA, Dan gaskiya Yana buk'atar ganin ta he really missed her, sanye yake cikin wani Riga navy blue da wando black yayi kyau sosai sannan yasa sunglass, lokacin da ya sauko downstairs ya tarar da Mommy a kitchen, gaishe ta kawai yayi, amsawa tayi tana tambayar shi Ina zai je, office kawai yace mata zai je sukayi sallama ya tafi.



*********************




 DEEJA na zaune kan turmi, tana Wasa da wani zoben azurfa da ASHRAF ya bata, su Mairo ne suka biyo mata zuwa islamiyya, tsaki tayi tace"Kai yau bazan je ba"😙



Lantana tace"halan har yanzu tunanin d'an birni kikeyi?, Ai da nice ke guduwa zamuyi da shi muje can birni muyi auren mu, muna hawa mota muna zuwa gurin Shan abin Nan Mai dad'i"😋(Wai Ice cream)


 Tsaki Mairo tayi tace"ke fa banza ce yo wallahi in nice ba guduwan da zamuyi, rok'on iyayen mu kawai za muyi idan sun gaji ai zasu yarda suyi mana aure"



DEEJA da ta gaji da surutun su tace"Kun ishe ni fa, kawai ku tafi Islamiyyan, daga Nan ku karb'o min kud'i na da na ba Indo bashi idan Kuma tak'i ba ku kuyi mata shegen duka". Ni ko nace duk da halin da kike ciki DEEJA🤔



 Bayan tafiyar su ne INNA ta fito daga d'aki cikin Shirin fita tace"halan dai ba zaki  islamiyya bane?"


 Kawar da Kai tayi gefe ba tace komai ba, INNA tace"to nidai Zan je dubo yaron gidan Larai da ya k'one sai ki kula da gidan"

 Toh kawai tace mata, sannan INNA ta tafi.





 Tana zaune taji k'arar mota a waje ai da sauri ta fito, motar ASHRAF ne ta gani yayi parking tare da fitowa, hawaye ta fara lokacin da ta gan shi, shi ko cike da farin ciki ya k'araso kusa da ita yace"idan kuka zakiyi sai in tafi"


 Da sauri ta fara share hawayen tace"yo ba Kai bane sai yau ka zo"😒

 Handkerchief ya mik'a mata ta share hawayen yace"bana son kina min asaran hawaye, Kuma kinsan halin da ake ciki"


  Turo baki tayi tace"to meyasa baka zo ka ba YAYA NA hak'uri ba, ai zai hak'ura, kawai ka tafi ne ka bar ni"😙

Da sauri yace"bazan tab'a tafiya in barki ba duk wuya duk runtsi muna tare"😍




Nan dai suka d'an yi hira, duk shirme take fad'a mai shi Kuma ya biye mata yana ta dariya daga baya ya bata wasu jakun -Kuna  cike da chocolates, biscuits da Sweets, sukayi sallama ya tafi.



Lokacin da INNA ta dawo DEEJA ta fad'a mata ta nuna mata abin da ya kawo mata, INNA duk da bata son DEEJA da ASHRAF Amma tana son ASHRAF d'in, Dan yana da halaye masu kyau, Kuma dagaske Yana son DEEJA.



DEEJA tace"INNA dan Allah kice ma YAYA NA yayi hak'uri muyi aure da ASHRAF Kinga kema sai mu tafi tare Kuma a mota"



 INNA tace"shirmen banza yo an fad'a Miki haka ake auren, idan Kuma mota ne ban so"


 Tace"to karki so ke dama ba'a Miki gwanin ta ai"😏


  Tace"auren ASHARAP ne dai baza kiyi ba"


 Kamar ta fashe da kuka tace"Ai YAYA NA naso na zai Kuma Mana aure"😫




 Shigowa gidan yayi yace"INNA me Kika ma K'ANWA TA?"


Ai ko Nan INNA ta fad'a mai abin da ke faruwa, yace ai ko DEEJA ta cire ASHRAF a zuciyar ta Dan ba zata aure shi ba.


Kuka sosai DEEJA ta fashe da shi tace"YAYA NA ka fad'a min meyasa da kana son ASHRAF to mene ne yayi maka yanzu?"



 A fusace yace"baza ki aure shi ba nace, Kuma baza ki tab'a sanin meyasa nace hakan ba, idan Kuma ya sake zuwa k'auyen nan zanyi maganin shi" ya bar gurin.



 Kuka sosai DEEJA ta k'ara fashewa shi, INNA taji tausayin ta sosai.









 Haka ASHRAF ya cigaba da zuwa k'auyen yana Kuma ba Yaya BILAL hak'uri har ya samu nasara ya hak'ura yace ya yarda ayi auren, Dan dama shi Yana son ASHRAF d'in halayen shi Yana burge shi ya tabatta zai rik'e mai K'ANWAR shi da kyau Kuma ya yarda da irin son da yake ma DEEJA.





DEEJA da ASHRAF ba k'aramin farin ciki sukayi ba, inda ASHRAF ke ta tunanin ta Ina zai tunkare su Mommy da maganar cewa bai hak'ura ba Kuma za suyi aure.





SALIM ya samu ya bashi shawara tare suka je har gidan Daddy (K'anin mahaifin ASHRAF).



Sunci sa'a Dan Yana gida bai fita ba, bayan sun gaisa ne suka d'an yi hira akan dai labaran duniya, bayan Nan ne SALIM ya fad'a Mai abin da ke tafe da su, sannan ASHRAF ya fad'a Mai komai har da ko wace ce DEEJA, Kuma Daddy yayi farin ciki sosai Dan haka yace kar su damu zai je ya samu Mommy da maganar sannan Kuma zai je da aminan shi su nema Mai auren DEEJA Dan haka kar ya damu sosai ko yayi farin ciki sannan suka yi mai sallama suka tafi, SALIM sai tsokanan ASHRAF yakeyi.





















 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *TRUE LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *17~18*












*Daddy* ne ya nufa gidan su ASHRAF, bayan sun gaisa da Mommy ne ya fad'a mata abin da ya kawo shi Akan maganar ASHRAF ne, ai ko Mommy taji haushin yanda ASHRAF ya je ya fad'a ma Daddy.


 Tace"duk da kasancewar kasan macen da yake son aura Kuma a Haka ka goya mai baya kenan?"

 Yace"k'warai da gaske, tunda banga abin da zai sa kice hakan ba zai yuwu ba to ni bazan sa miki ido ba kiyi abin da Kika ga dama ba"

Ran ta a b'ace tace" to ni dai gaskiya bana son auren ban Kuma yarda ba"

 Shima a fusace yace"kin hana MEERAH yin aure kin goya Mata baya, yanzu kamar MEERAH ace shekarun ta kusan talatin amma tana gida, ga masu son ta dayawa Anna kin biye mata tak'i yin aure, to Haka kike so in zuba Miki ido shima ASHRAF d'in yak'i Yi  kenan bayan yaga wacce yake so sai Kuma ki hana shi to bazan yarda da abin da kikeyi ba, Kuma idan da ace ana mutuwa a dawo Mahaifin su ya dawo kina tunanin zaiji dad'in yanda kike ma yaran shi ne? To ni ma mahaifin su ne Kuma Inshallah aure za'ayi shi babu fashi" barin gidan yayi.



Yayin da ran Mommy duk ya b'aci, Kuma tasan tabbas za'ayi auren babu fashi kamar yanda yace Dan shi akwai kafiya Akan abin da yasa a gaba.




 Haka ko akayi inda Daddy da aminan shi suka Isa k'auyen su DEEJA, hannu biyu aka tarbe su inda aka yanke ranar d'aurin aure ASHRAF da DEEJA sati biyu masu zuwa Dan Daddy yace a shirye yake haka ma BILAL a shirye yake ba amfanin sa lokaci mai tsawo.



Lokacin da ASHRAF yaji ba k'aramin farin ciki yayi ba sai dai Mommy hankalin ta ya tashi, Sam ba haka taso ba, MEERAH kan ta bata ji dad'i ba, ba yanda zasu dole suka fara shirye-shiryen aure, HANA ko sai farin ciki takeyi.



Mommy tace Sam ita bata yarda ASHRAF ya tare a wani gidan ba, dole Daddy ya yarda da haka kar taga kamar yak'i yarda da abin da bata so, a matsayin ta na mahaifiyar ASHRAF, Dan haka an gyara bedroom d'in ASHRAF dake upstairs, kasancewar bedroom ne babba Dan har da sate d'in kujeru ta gefe d'aya, daga ciki Kuma bed ne da wardrobe sai su dressing mirror, sannan akwai wani corridor ta ciki ne akwai toilet shima yana da girma Kuma akwai wani dogon dressing mirror da yake cike da kayan shafe-shafe, komai white and purple ne, toilet ne kawai pink and red, gaskiya tsayawa fad'a muku irin tsaruwan d'akin ba zai yuwu ba but ya had'u over.






 Wata Mata ce wacce ake Kiran ta da HAJIYA BILKISU, ita ce tazo ta zauna a gidan su DEEJA inda ta dage tana gyaran DEEJA sosai, tsawon sati d'aya tana Mata gyara dasu dilka, da irin kayan had'in mu na Mata, kullum abincin DEEJA shine fruit har zuciyar ta tashi yake ta gundura dasu, sai dai tayi kyau fatar ta yayi smooth ga wani irin haske da tayi, komai nata ya ciko, da Kun ganta Kun ga Amarya.



Shiri sosai ake, inda aka kawo kayan lefe gaskiya yayi ba k'arya, komai yaji a kayan, ita DEEJA sai murna take zata hau mota taje gidan bene, sosai HAJIYA BILKISU ke son DEEJA kamar 'yar ta.



B'angaren ASHRAF shiri yake sosai, abokanan shi sun shirya Mai dinner amma Sam yace shi baya so, a cewar shi za'a kalle Mai mata, yak'i amincewa dole suka hak'ura.




Ana gobe d'aurin aure anyi walima inda aka gayato wata malam tayi wa'azi sosai Akan zaman takewar aure, DEEJA ranar taci kwaliyya sai famar magana k'asa-k'asa takeyi dasu Mairo Wai Bata gayace wasu k'awayen ta ba Amma sun zo, tsabar kwad'ayi, har tana bada sak'o Wai idan ta tafi birni suyi ma wa'incan dasu kazo duka, kuji fa.









  Ranar d'aurin aure






 Ranar Amarya DEEJA anyi kwaliyya sosai Wanda HAJIYA BILKISU ce ta d'auko Mai yin kwaliyyan, wayyo fan's kar ku so kuga yanda DEEJA tayi bala'in kyau kamar a sace ta a gudu, sai canza mata Kaya ake iri-iri.


Abin da yafi bani mamaki shine ganin wasu manya-manyan motoci da sukayi parking wasu Kyakyawan Mata ne suna dayawa suka shigo gidan sai gaisawa suke da INNA alama sun San juna sosai. Wasu Kyakyawan Mata su uku na gani sunyi kama da DEEJA, d'aya tana da yaro sai sauran su biyu, aiko suna ta ji da DEEJA sai wata Mata wacce mahaifiyar su ce sai jawo DEEJA take a jikin ta tana Kiran ta da 'yar ta, har abin ya ishe DEEJA tace ita basu tab'a ganin juna ba amma ta ishe ta da cewa y'ar ta.😂






 Da missalin k'arfe 2:30pm aka d'aura auren *ASHRAF BILYAMIN DA KHADIJA NASIR (DEEJA)* Akan sadaki mafi daraja Naira dubu hamsin, inda duban mutane suka shaida d'aurin auren, Nima na shaida nasan Kuma fan's sun shaida.



Ango ASHRAF sai murmushi yake Yana gaisawa da mutane, DEEJA ko da aka ce an d'aura sai murna take.




Motoci ne na gani na fad'a sukayi parking inda za'a d'auki amarya, lokacin da za'a tafi da DEEJA taga fa dagaske zata bar gidan su zata bar Yayan ta da INNA ai sai ta fara kuka tana cewa ta fasa auren ba inda zata aiko da k'yar Yayan ta ya shawo kanta ta amince, sannan yayi mata nasiha sosai ya bata abin salla (praying mat), da Al-QUR'AN. Can sai ta fara kuka tana rik'e shi da k'yar aka raba su sai kuka takeyi, Nan aka sata a mota aka d'auki hanyar Abuja.










 Around 8:00pm suka Isa cikin gidan su ASHRAF, lokacin da aka fito da ita tana cikin gyale ne dan haka Bata ga gurin da kyau ba, lokacin da aka shiga da ita gurin Mommy tasa Mata Albarka sai murmushi kawai take musu Bata nuna musu komai ba zuciyar ta ko zafi yakeyi ganin y'ar k'aramar yarinyan da ASHRAF ya aura sa'ar HANA ce.



Har d'akin ta aka kaita sannan duk sukayi sallama Dan ba za'a kwana a d'akin amarya ba, Wanda suka zo daga k'auye Kuma wani gida Mai kyau aka Kai su suka kwana da safe a maida su k'auye.














DEEJA.............















*Akwai drama a first night d'in DEEJA 😂 har Naga masu cewa sai sunyi lek'e to nak'i barin ku su sister Maimounath😜*







*Nasan da cewa kunyi confused, ku biyo ni next page Dan Jin ainihin tarihin iyayen ASHRAF da DEEJA*










 *TAKU CE UMMU BASHEER*





[21/01 3:08 pm] Ummu Basheer: 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *TRUE LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *19~20*







  *DEDICATED TO*

 *ALK'AWARI Fan's Group*
 *RAYUWAR NAJWA Fan's Group*
 *ZURI'A D'AYA fan's Group*
 *A KAN K'ANWA TA Fan's Group 1*
 *A KAN K'ANWA TA Fan's Group 2*



  *Heart you all my fan's, this page is yours, Allah ya bar zumunci da k'aunar juna, sosai nake yin ku my fan's, Ina son ku kamar yanda Kuke Sona, duk wuya duk runtsi ana mugun tare sosai,  I LOVE YOU ALL*

🌹 .      🌹.      🌹.   🌹. 

🌹.         🌹.      🌹.   🌹.


   🌹.

         🌹.

             🌹.







 *DEEJA* na zaune akan bed fuskar ta a rufe da gyale,duk ta gaji da gyalen gashi ance kar ta cire har Ango ya shigo ita ko ta gaji, can sai taji alamar shigowa, ASHRAF ne ya shigo, murmushi yayi lokacin da ya ganta, k'arasawa yayi ya hau bed d'in tare da cire mata gyalen, ba k'aramin kyau tayi ba cikin Swiss lace orange and silver colour ga heavy make-up da akayi Mata, murmushi tayi Mai Wanda sai da ya gigice tsabar kyau d'in da tayi ga wushiryan ta ya fito, kamar yayi kissing d'in ta but sai ya fasa tare da nufan wani fridge ya d'auko fresh milk da cups dama already ya siyo, sai gasashen kaza, Nan ya umarce ta da taci aiko zama tayi taci ta k'oshi sannan tasha fresh milk, shi ko k'adan yaci sai kallon ta yake, Nan yace suyi Alwala, bayan sunyi sukayi sallama, ciro mata wani night gown yayi Mai santsi yace tasa, toilet ta shiga tasa sannan ta fito, ba k'aramin kyau night gown d'in yayi mata ba white colour ne, kwanciya tayi tana hamma Wai a dole barci take ji.


  Kwanciya yayi kusa da ita tare da rungume ta, zumbur ta tashi tace"wayyo meye ne?"

 Murmushi yayi tare da k'ara rungume ta yace"I love you my wife"

 K'okarin k'wacewa take yi amma ta kasa, turo baki tayi tace"ni fa ka k'yale ni"😙

 Had'a bakin shi da nata ya fara kissing d'in ta cike da k'auna, wani irin yanayi suka shiga, DEEJA jikin ta ne ya d'auki rawa, da k'yar ta iya ture shi da k'arfi, tace"Wayyo na shiga uku dama Kai d'an iska ne?"😫

Rik'o ta yayi yace"oh come-on baby, nifa mijin ki ne"

 Tace"A'a ni dai wallahi sai na fad'a ma YAYA NA"😰


 Rungume ta yayi yace"I'm sorry please"

 Da sauri ta mik'e tsaye ta nufa wardrobe tana Ciro kayan ta da aka jera, tana cewa"ni wallahi k'auyen mu Zan koma bazan zauna ba, bayan ance mota Zan dinga Hawa, Ashe Kai d'an iska ne"😫

 Dafe kai yayi gaskiya DEEJA akwai rigima da k'yar ta amince da shi Dan haka zai barta su d'an Saba ta saki jiki da shi, cikin rarrashi yace"baby na kiyi hak'uri nifa ba d'an iska bane, Kuma ba abin da Zan Miki, oya zo ki kwanta"


Turo baki tayi sai yaji kamar yayi kissing d'in ta course lips d'in ta akwai dad'in tsotsa, Haka suka kwanta tare ba abin da yayi mata.







 








 

  *Asalin tarihin iyayen ASHRAF da DEEJA*



  *Shekaru goma da suka wuce*









 *Malam Audu* Yana da Mata Mai sunna HADIZA, Allah ya azurta su da samun Yaro namiji Mai suna NASIR, sun bashi tarbiyya dai-dai gwargwado basu da hali suna da rufin asiri dai, suna zaune a wani k'auye ne, inda Malam Audu mahaifin NASIR yayi k'okari NASIR yayi karatun shi na boko har zuwa secondary, to a wannan lokacin ne malam Audu Allah yayi mai rasuwa, sunji rasuwan, gashi basu da komai haka suka ciga ba da Rayuwa inda NASIR bai k'ara zuwa makaranta ba kasancewar basu da hali, daga k'arshe dai NASIR ya fara shiga cikin birnin Kano domin fara sana'a, sosai ya dage Yana d'an yin k'wadago, a hankali har ya fara d'an sana'ar sai da su rake a gefen titi.



 Wata Rana Yana zaune sai ga wata k'atowar mota mai shegen kyau yayi parking, wani babban mutum ne ya fito tare da shiga wani super market ya fito, lokacin da ya fito Ashe ya yar da wallet d'in shi bai sani ba, to NASIR ya gani da sauri ya d'auko ya bishi Yana cewa"Yalab'ai ka Yar da abin ka"

Cikin murmushi mutumin ya juyo tare da yin mai godiya, yaji dad'i sosai yanda bai gudu Mai da wallet ba sai ma bashi da yayi, gashi akwai abubuwan shi masu muhimanci, gani yayi ya koma gurin sai da raken shi ya cigaba da sana'ar shi, mutumin sosai yaji tausayin shi ganin halin da yake ciki, Dan Haka ya Kira shi yace Yana son bashi aiki ya tambaye shi game da iyayen shi, shi da mutumin su kaje har k'auye gurin mahaifiyar NASIR wato INNA inda ALHAJI'N ya rok'e ta da ta bar Mai NASIR ya zauna a gurin shi zai bashi aikin yi, INNA taji dad'i sosai Kuma tayi Mai addu'a duk da bata san wane ne ba tasan mutumin k'warai ne.






 ALHAJI RUFA'I shine sunan mutumin Nan, Yana zaune ne a Abuja Mai kud'i ne sosai naban mamaki, Yana da Yara guda uku, biyu maza, *MA'ARUF* da *MUHAMMAD* sai Mace Mai suna *NANA FATIMA* sosai yake ji da yaran shi matar shi Mai suna *HAJIYA ZAINAB* tana da kirki sosai da son mutane, Dan Haka Family d'in sun karb'e NASIR hannu biyu, domin basu da wulak'anta d'an adam, inda ya fara Zama a gidan kamar yaron gidan, Yana zuwa makaranta Kuma ALHAJI RUFA'I Yana zuwa aiki da shi har da yaran shi.








 ALHAJI BILYAMIN mutum ne Mai kud'i sosai su biyu iyayen su suka haifa daga shi sai K'anin shi(Daddy) Allah yayi ma iyayen su rasuwa. A lokacin BILYAMIN yana aiki tare da ALHAJI RUFA'I, NASIR da BILYAMIN aminan juna ne, tare suke aiki.


 NASIR da NANA FATIMA suna matuk'ar son junan su, lokacin da ALHAJI RUFA'I ya gane yayi farin ciki inda ya had'a su aure, har gidan ALHAJI RUFA'I ya gina musu Dan su zauna, a wannan lokacin ne BILYAMIN shima yayi aure ya aura wayayyiyar mace'yar boko.




 MAIMUNA ta haifa 'da namiji inda aka sa mai suna *ABDUL-MALIK*, bayan shekaru hud'u BILYAMIN matar shi ta haihu 'ya mace sunan ta *AMEERAH* suna matuk'ar son yaran su. Ba'a jima ba sai ta k'ara haifar wani yaro Mai suna *ASHRAF*.






 Wani lokaci ne kwatsam NASIR ya gano cewa ALHAJI RUFA'I Yana yin wani sana'ar na yin safarar k'wayoyi da hodar iblis(Cocaine) zuwa k'asar waje,Ana shigo Mai da shi ta b'oye, ba k'aramin razana NASIR yayi ba bai tab'a sanin haka ba, gashi ya lura BILYAMIN shima yana sana'ar Cocaine d'in, a hankali NASIR ke ma BILYAMIN nasiha da nuna mai ya bar wannan sana'ar domin Sam bashi da kyau, sau dayawa BILYAMIN Yana Jin haushin haka, bare ma akwai wani abokin shi Mai suna *ILIYASU* Wanda Yana bak'in cikin abotan dake tsakanin NASIR da BILYAMIN Dan Haka shi ke k'ara zuga shi akan ya daina kula NASIR, Haka ko akayi sai BILYAMIN ya daina kula NASIR.





 Wani irin gaba BILYAMIN yake da NASIR shi Kuma lokacin da ya Gane sai ya rabu da shi tunda ya daina kula shi, tun daga Nan sai suka daina had'uwa, gaba d'aya sai aminan takan su ya watse.





  A yanzu haka HAJIYA MAIMUNA ta k'ara haifar y'ar ta wacce taci sunan mahaifiyar NASIR wato *KHADIJA* shekarar ta shida kenan, iyayen ta na matuk'ar ji da ita,




  Mommy ma ta sake haihuwa ta haifa yarinya wato *HANAN*, a wannan lokacin ALHAJI BILYAMIN ya tura yaron shi ASHRAF k'asar waje domin yayi karatu, ita Kuma AMEERAH ta gama karatun ta kenan ta dawo k'asar. Mahaifin ta na matuk'ar ji da ita. Komai nashi ta sani har safarar k'wayoyi da yakeyi sai dai ko a jikin ta a cewar ta ai ba wani Abu bane.




 Yanzu ABDUL-MALIK Had'ad'en saurayi ne, Mai ji da kyau, shi da mahaifin shi kamar aminai suke, suna shawara da junan su.




















  *Wannan kenan muje zuwa*







 *TAKU CE UMMU BASHEER*
[23/01 2:02 pm] Ummu Basheer: 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *TRUE LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *21~22*




  *I'm sorry fan's nayi mistakes gurin sa sunan mahaifiyar su DEEJA, nasa NANA FATIMA instead of HAJIYA MAIMUNA, kuyi hak'uri nasan you're confused, yanzu zan cigaba da sa mata HAJIYA MAIMUNA, thanks for understanding me.*



  *Dedicated to Aunty Rahmat Nalele*


  *This page is yours Aunty Rahmat, Allah ya kare ki daga sharin mahassada, makkiya da magulmata, ke d'in ta daban ce, naki saloon ba irin nasu bane, kinyi gaba na baya sai labari, ke tauraruwa ce a cikin duhu mai haskawa, more grace to your shining elbows, kin cancanta fiye da haka gare ni, wallahi sosai nake yin ki my Aunty, Allah ya bar zumunci da k'aunar juna, Allah ya k'ara Miki basira da hazak'a k'warin ido tare da laushin hannu Ameen*


    🌹
                🌹           🌹            🌹

        🌹.                          🌹


             🌹.                    🌹
 
                🌹.               🌹
   
                        🌹


 *Makarantar* su DEEJA da HANAN d'aya ne, akwai wani lokacin da ABDUL-MALIK (Bilal) shine ya kawo DEEJA school d'in, dai-dai Nan ne MEERAH ta shigo da motar ta aiko shi Kuma yazo yin reverse kawai sai ya buga mata, ai ko cike da massifa ta fito, cikin shigar doguwar riga, knocking d'in glass d'in motar shi ta fara a fusace.


 Shi ko tun lokacin da ta fito yake kallon ta duk ya fita hayyacin shi, lokaci d'aya zuciyar shi ya kamu da son ta, wannan shine love at first sight, fitowa yayi daga cikin motar tare da sakar Mata da wani irin murmushi, lokaci d'aya taji jikin ta yayi sanyi, ganin MALIK ya tayar mata da hankali gaskiya guy d'in ya had'u tace a ranta, lokaci d'aya taji wani irin son shi a zuciyar ta.


Hak'uri ya bata Yana cewa Bari yasa driver ya Kai motar garage a gyara, murmushi kawai tayi tace ai ba komai, Nan take ta Kira wani driver sai gashi da wata motar, sallama suka yi, Nan suka rabu da yake ita ma ta kawo HANA school ne.





Kussan kullum sai sun had'u a school d'in da suke kawo k'annen su, a Haka har suka Saba da junan su, har ya Kai suna waya, wata rana MALIK yaga gaskiya gara ya fad'a mata cewa yana son ta, ai ko ranar da ya fad'a mata ba k'aramin farin ciki tayi ba, daga k'arshe dai suka fara wani irin soyayya mai wuyar fassaruwa, course they really love each other.








 Wata rana yake sanar da MEERAH cewa Yana son turo iyayen shi dan a neman mai auren ta, ai ko taji dad'i sosai, lokacin da ya fad'a ma Baban shi, yayi farin ciki 'Dan nashi zaiyi aure, lokacin da ALHAJI NASIR yayi bincike sai ya gani ashe yarinyan ALHAJI BILYAMIN, MALIK ke son aura, Dan haka yace gara ya nemo wata matar domin ya San da wuya ALHAJI BILYAMIN ya bada auren 'yar shi, ba k'aramin tashin hankali MALIK ya shiga ba, Nan ya had'u da MEERAH yake sanar da ita abin da ke faruwa ai ko ita ma hankalin nata ya tashi, domin Abba'n nata Yana yawan bata labarin ALHAJI NASIR da yanda ya tsane shi, kuka ta dingayi sosai tace zatayi mai magana ko Allah zai sa ya amince Dan gaskiya ita baza ta iya rabuwa da MALIK ba.





  Zaune yake tare da mutanen shi har dasu ILIYASU, shigowa tayi ta gaishe su sannan cikin shagwab'a tace"Abba na, na samo mijin aure"

 Gaba d'ayan su dariya sukayi, cike da k'aunar 'yar shi yace"fad'a min my Daughter d'an waye a garin nan?"

Murmushi tayi ta daure tace"Sunan shi ABDUL-MALIK ina matuk'ar k'aunar shi, d'an ALHAJI NASIR ne ZURI'AR ALHAJI RUFA'I"


Gaba d'ayan su zaro ido sukayi yayin da Abba ya mik'e a fusace yace"shin kina hauka ne, ki rasa wanda zaki so sai 'Dan ALHAJI NASIR? To hakan ba zai yuwu ba, shin ko kin manta irin gabar dake tsakanin mu ne da shi? Ki samu wani mijin Amma ba ZURI'AR ALHAJI NASIR ba"


 Mik'ewa tsaye tayi cikin kuka tace"Abba wallahi Ina son shi, bazan iya rayuwa Babu shi ba ka taimake ni please"

Wani gigitacen Mari ya d'auke ta da shi yace"ai ko mutuwa zakiyi baza ki aure shi ba, get out of here, nonsense" he shouted.



 Da gudu ta fita tana kuka, tana zuwa ta fad'a jikin Mommy tana kuka, ita Kuma Mommy rarrashin ta takeyi tana cewa tayi ma Abba'n ta biyayya.



 Lokacin da MEERAH ta bar parlour'n ne, ILIYASU yace ai bai kamata yayi mata hakan ba wannan ai dama ne ya samu na tarwatsa ALHAJI NASIR Dan Haka yayi ta zuga shi sauran ma suka goya bayan shi, mutum d'aya ne yace Sam abin da suka shirya bai Dace ba, sunan shi *MUSA* yana da kirki Kuma baya son yanda ALHAJI BILYAMIN yake huld'a da ILIYASU domin ya gano ILIYASU had'a su fad'a kawai yakeyi, ko bi takan maganar MUSA ba suyi ba, ALHAJI BILYAMIN yace ba ruwan MUSA yasa musu ido kawai.




Da daddare MEERAH na kwance kan bed a d'akin ta sai ga ALHAJI BILYAMIN ya shigo, tana ganin shi ta share hawayen ta, Zama yayi kusa da ita yace ya amince ta aura MALIK tunda shine farin cikin rayuwar ta shi Kuma baya son b'acin ran ta, ba k'aramin mamaki MEERAH tayi ba ganin da farko yak'i yarda yanzu Kuma ya yarda duk da hakan taji dad'i sosai, Nan yace next week tace MALIK ya turo iyayen shi domin asa ranar auren su.



 Ba K'aramin farin ciki tayi ba, Kiran MALIK tayi ta sanar mai, yayi farin ciki sosai da Kuma mamakin yanda mahaifin ta ya amince, Nan ya sanar da ALHAJI NASIR, shima yayi mamaki sosai sai dai yace Allah yasa hanyar shiryawan su ne, k'ila ta Nan zasu cigaba da huld'a, yayi kuma addu'a Allah ya kare su daga sharin mak'iyya.







 Sunyi shiri sosai ALHAJI NASIR da wasu aminan shi guda biyu sai Abokanan MALIK guda biyu Wanda tun suna yara suka girma tare wato *KABIR da FA'IZ* , har da MALIK d'in Dan ALHAJI BILYAMIN yace azo har da shi.






 Ranar da baza su tab'a mantawa a rayuwar su ba.




  Mommy da kanta ta zab'a ma MEERAH kayan da zata sa saboda ranar ne su iyayen MALIK zasu zo domin sa ranar aure, cikin wani lace red da ratsin black, tayi kyau sosai.



   Da missalin k'arfe 5:00 pm suka shiga gidan su MEERAH, sosai aka tarbe su, an kawo musu abinci da su juices, ba tare da tunanin komai ba suka ci sannan suka k'ara gaisawa.


Babban abin da ya basu mamaki shine ganin wasu mutane masu black d'in Kaya sun shigo fuskar su akwai masks, ALHAJI BILYAMIN yace"naji dad'i sosai da kuka zo har gida na ba tare da na Sha wahala ba, kaga mutanen Nan sune zasu kashe ku sai su tafi kunga kenan police da mutane za suyi tunanin Arm robbers ne suka shigo gidan suka kashe ku"

A tare mutanen Nan suka zagaye su da bindigogi, cikin razana da matuk'ar mamaki ALHAJI NASIR yace"ya za'ayi haka, meyasa zaka yaudare mu?"


Kafin ya bashi amsa har wani mutum cikin masu black kayan Nan ya harbi  d'aya daga cikin aminin ALHAJI NASIR, cikin razana MALIK ya fito da bindiga a aljihun shi domin saboda tsaro ya rik'e, Dan zuciyar shi Bata gama yarda da ALHAJI BILYAMIN ba.


Nan aka Fara harba-harbe, wasu na b'oyewa a bayan kujeru, ILIYASU ne na gani ya fito da bindiga tare da Harbin ALHAJI NASIR sannan ya harbi ALHAJI BILYAMIN, dai-dai lokacin MALIK da MUSA suka ga ILIYASU yayi Harbin, da gudu MALIK ya Isa gurin mahaifin shi Yana Kiran shi.



MUSA ganin haka yasa ya harbi ILIYASU a k'afa,


 Cikin rud'ewa da tashin hankali Yana rik'e da bindigan yayi setin ALHAJI BILYAMIN, yayin da yake girgiza mahaifin shi kasancewar ALHAJI BILYAMIN da ALHAJI NASIR suna fuskantar juna ne,



Dai-dai lokacin ne Mommy da MEERAH suka shigo Dan Jin k'arar harbi a gidan, ba k'aramin razana sukayi ba ganin MALIK ya sai ta bindiga gurin ALHAJI BILYAMIN, shi ko bai ma San meke faruwa ba girgiza mahaifin shi kawai yake ganin ba numfashi a tare da shi.



 Mommy ko rungume ALHAJI BILYAMIN tayi tana Kiran sunan shi, MEERAH da gudu ta cakumi wuyan rigar MALIK tana cewa"ka kashe min Abba na, meye ne yayi maka a rayuwa da zaka harbe shi?!"


 Cikin rud'ewa yace"A'a ba ni na kashe shi ba!"

 Ihun Mommy ne yasa ta sake shi tare da k'arasawa gurin Abba'n ta ganin baya numfashi ne yasa ta fad'i k'asa sumamiyya.







Police ne da Ambulance suka shigo inda aka d'auki gawan su zuwa Dan tabattar da cewa ko sun rasu, yayin da police ke bincike, ILIYASU dai yayi nasarar guduwa duk da Harbin shi da MUSA yayi.





Innalillahi wa'ina illaihir-raji'un ALHAJI BILYAMIN da ALHAJI NASIR sun rasu da aminin ALHAJI NASIR, Nan aka kaisu gidan su tare da yin musu wanka da yin musu salla, aka kaisu gidan su na gaskiya, Allahu Akbar kullu nafsin za'ikatul maut dukan Mai rai sai ya d'and'dani mutuwa Allah kayi Mana cikawa da imani, Ameen.


 Ba K'aramin razana HAJIYA MAIMUNA (mahaifiyar su MALIK) tayi ba da  mutuwar ALHAJI NASIR mijin ta, Wanda sanadiyar hakan zuciyar ta ya buga ta rasu bayan kwana uku da rasuwan ALHAJI NASIR, ba k'aramin tashin hankali MALIK ya shiga ba mutuwar iyayen shi lokaci d'aya ya girgiza shi, baya cin abinci baya magana, kullum Yana kulle cikin d'aki,



MEERAH satin ta biyu a hospital Bata San inda kan ta yake ba, Mommy ko da yaushe cikin kuka take ga damuwa gashi tana da Asma, lokaci d'aya ta samu ulcer ga hawan jini.




 MUSA shine Wanda ya Kira  ASHRAF ya sanar da shi, ba k'aramin razana da tashin hankali ya shiga ba, Nan ya dawo Nigeria, a gaskiya yayi rashin mahaifin shi mai son su da k'aunar su, MUSA yayi mai bayanin abin da ya faru cewa ILIYASU shine Wanda ya aikata kisan, sosai ASHRAF yayi bak'in ciki, sai dai ya fad'a mai kar ya fad'a ma su MEERAH domin yasan baza su tab'a yarda ba, daga Nan MUSA bayan anyi bakwai ya bar garin Abuja.







Halin da MALIK ya shiga shine yasa mahaifiyar NASIR wato INNA tace su dawo k'auye su zauna da ita zuwa wani lokaci, da yake ita tak'i yarda ta dawo Zama a gidan NASIR d'in, ALHAJI RUFA'I ya amince da hakan ganin halin da MALIK d'in yake ciki.








Lokacin da MEERAH ta dawo hayyacin ta cewa tayi ita sai ta Kai MALIK court, to K'anin ALHAJI BILYAMIN ne ya hana ta wato Daddy, tayi bak'in ciki sosai, tun daga wannan lokacin ne ta tsani MALIK, tana zargin shi ya kashe mata mahaifin ta haka ma Mommy ke gani duk sun tsane shi.










 Bayan shekaru goma





 MALIK ya canza sunan shi zuwa BILAL, a Nan k'auyen Kuma ya bud'e gareji shida aminan shi Wanda sukace baza su rabu da shi ba, domin farin cikin K'ANWAR shi yasa ya cigaba da Zama a k'auyen domin Yana matuk'ar son ta shine uwa da uba nata, Haka Kuma Yana son MEERAH sai dai yasan baza ta tab'a auren shi ba, Kuma yasan zargin da take Mai, ya bar duniyar su a hannun Yayan Mahaifiyar su wato Muhammad, shike kula da komai nasu, Kuma shine matar shi tazo tayi ma DEEJA gyara tsawon sati biyu, D'ayan Yayan Mahaifiyar su shine yake da Yara Mata guda uku Wanda suke son DEEJA, Kuma BILAL (MALIK baya zuwa da DEEJA cikin Abuja but shi Yana zuwa ya gaishe dasu ALHAJI RUFA'I, Wanda a yanzu yayi nadamar abin da ya ke aikatawa ya daina safarar k'wayoyi, tun bayan mutuwar 'yar shi mahaifiyar su DEEJA.













 MEERAH tak'i yin aure domin har yanzu tana son MALIK sai dai har yanzu zargin shi takeyi, Kuma bata san inda ya koma da Zama ba, ASHRAF ya dawo Nigeria da Zama domin yanzu babu mahaifin su, shine zai kula da mahaifiyar su da 'yan'uwan shi, Wanda yayi karatun doctor har Yana da hospital, sau dayawa Yana fad'a ma Mommy da MEERAH cewa ba MALIK ne ya kashe musu mahaifin su ba Amma sunk'i yarda, shiyasa ko da yaushe Mommy ke cikin damuwar rashin mijin ta, MEERAH tana aiki a wani company na mahaifin su, ita ma takan zauna tayi ta kuka idan ta tuna mahaifin ta, da Kuma k'aunar da take ma MALIK.





 ASHRAF ko ya yarda da k'adara yasan Kuma haka Allah ya tsara musu a rayuwa. Kullum cikin yin musu nasiha sosai yake.





















 *Wannan shine Asalin tarihin iyayen ASHRAF da DEEJA Kuma wannan shine abin da ke tsakanin MEERAH da BILAL wato MALIK*







 *Cigaban labarin*





















*TAKU CE UMMU BASHEER*
[24/01 1:28 pm] Ummu Basheer: 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *TRUE LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *23~24*





  *This page is yours my brothers and sisters*


 *Sister Maimounath*
 *Badeeyerh my K'awas*
 *Daddy'n Faty*
 *Hussaini 80k*
 *Ayman*


     🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
  *Allah ya k'ara muku tsawon kwana, Allah ya albarkaci Zuri'ar ku, Allah ya biya muku buk'atun ku, Ameen*

   
   🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
 *Sister Maimounath Allah ya ba Mama lafiya, My K'awas Allah ya Baki lafiya, Ameen ya Rabbil Izati*😭

 
  🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹






 
  *Washegari da safe*


*Bayan* sun tashi ne DEEJA tayi wanka, ta shirya cikin wata atamfa blue da ratsin pink, sannan fa aka damb'ara kwaliyyan k'auye, different performs ta fesa sai k'amshi take, a dole fa ita ta had'u over, Sannan ta fara gyaran bedroom da side d'in kujeru, Air fresh ta d'auko ta fesa Dan tana ganin Yayan ta na fesawa a d'akin shi, Kuma dama ance kullum ta dinga gyara bedroom d'in su, to dama ita akwai tsafta.

  ASHRAF ne ya shigo d'auke da tray na kayan breakfast, yayi mamakin ganin ko'ina k'al-k'al, ajiye tray d'in yayi a center table yace" Let's have breakfast baby"

 Sai lokacin ta d'ago kai yaga kwaliyyan ta, habawa ai bai san lokacin da ya tuntsire da dariya ba, turo baki tayi cikin haushi tace" meye ne ko banyi kyau bane?"😙

   Rik'e dariyan yayi yace"No baby you're looking beautiful"

 Cike da shagwab'a tace"nifa ka daina Kira na da baby ni ba jaririya ba ce"☹


  K'arasawa yayi ya rik'o hannun ta Yana cewa"bazan sake ba my love"😍

 Murmushi tayi, Nan ya fara feeding d'in ta har sai da ta k'oshi sannan yace ta ba shi.

  Cewa tayi"Wai meyasa kake irin abin y'an iska ne? Ance min ba'a ba mutum abinci a baki"😦


 Dafe kai yayi yace"shikenan tunda ba Kya so na"🤦🏻‍♂

 Da sauri ta d'auki spoon d'in hannun ta na rawa ta Kai bakin shi tana cewa"A'a wallahi Ina son ka fa"

 Cikin Jin dad'i ya fara cin plantain and yam with eggs sausage, a Haka har ya k'oshi sannan yace ta sa hijab d'in ta suje ta gaishe da Mommy, d'aukan tissue paper yayi ya goge mata kwaliyyan sai turo baki takeyi Wai ya b'ata mata kwaliyyan ta. wani white hijab tasa sannan suka sauka downstairs tare.



  Mommy na zaune a parlour suka k'arasa gurin. Zama DEEJA tayi a k'asa gefen Mommy tace"Ina kwana"

 Ko kallon ta Mommy ba tayi ba, sai da ASHRAF yace"Mommy she's greeting you"

 Sannan ta amsa ciki-ciki, DEEJA tab'e Baki tayi a ranta tace ki ma gode na gaishe ki. Ni ko nace surikar ki DEEJA😂.

  Aunty MEERAH ce ta fito cikin wani matsatsen Riga da skirt, da mamaki DEEJA ke kallon ta a ranta tace ashe wannan y'ar iska ce.🙊


 D'aure fuska MEERAH tayi tace"ke Baki iya gaisuwa bane?"

 Kamar baza ta gaishe ta ba sai ta tuna ance mata banda rashin kunya, sai ta gaishe ta, Kuma bata amsa mata ba, tun daga Nan ba Wanda ya sake magana har ASHRAF ya fita.

 Kitchen d'in gidan ta shiga Kai gaskiya ko'ina na gidan yayi mata kyau, oh wai yau ita ce zatayi rayuwa a irin wannan gida Mai shegen kyau, HANA ce ta gani, tace"ke ce k'anwar ASHRAF ko?" Ta nuna ta.

 HANA tace"eh, matar brother"

 Tab'e baki tayi tace" duk ya fi ku kyau"

 Murmushi tayi tace"eh Amma ke ma ya fi ki kyau"😜

 Tsaki tayi tace"Dalla banza bai fini ba"😏


 Kamar tayi kuka tace"ni d'in ce banza? I swear I'm going to tell Mommy"😫

 Da gudu ta fita, DEEJA na ganin haka tayi upstairs da sauri.


 Mommy ko ranta ya b'aci daga zuwan DEEJA har ta fara tab'a Mata y'ar autan ta, Aunty MEERAH ma taji haushi.




 Around 9:00pm


 ASHRAF ne ya shigo bedroom ganin DEEJA kwance kan bed tana kuka yasa yayi sauri jawo ta Yana cewa"oh my God, what's happening to you?"

 Fuskar ta duk hawaye tace"ni dai gurin YAYA NA da INNA ta zanje"😭

 Harshen shi yasa ya fara lashe hawayen Yana cewa"please ki bar min asaran hawaye na, Zaki gan su kinji my love?"

 Bud'e Baki tayi da niyar magana ai kawai sai ya had'a bakin su ya fara kissing d'in ta passionately, shiru tayi Jin sweet mouth d'in shi cikin nata, can gogan naku duk ya rikice sai ya fara k'okarin cire mata riga, sai k'okarin k'wacewa take yi, uhm ai lokacin da yaga breast d'in ta rikicewa yayi cafkar su yayi ya fara tsotsan su kamar Yana Shan sweet, numfashin ta kamar zai d'auke Haka take ji, Kai nidai kunya nake ya Isa d'auko muku ruhoton haka🙈.






 A wannan Daren DEEJA Tasha azaba har da cizon shi da yak'ushi tayi amma bai ko saurara Mata ba sai da ya d'auki budurcin ta, gashi tak'i tsayawa duk ya ji mata ciwo, ya tausaya mata sosai da kanshi ya kaita toilet yayi mata wanka, da gasa mata jikin ta, kuka ta dingayi sosai, sai rarrashin ta yake yana sa mata  albarka, a ran shi sai cewa yake Ashe aure rahma ne har ya samu natsuwa, DEEJA ita ce macen da ya fara sani a matsayin y'a mace a rayuwar shi,da k'yar barci ya d'auke ta, ni ko nace Wai ba kace sai kunyi sati ba.🤔





 Washegari da safe


 Around 11:00 am ta farka daga barcin da take yi, ASHRAF na kan kujera yana aiki a system yaji motsin tashin ta, da sauri ya k'arasa.

Rik'o ta yayi yace"sorry my love, akwai inda yake Miki ciwo yanzu?"


  Cikin shagwab'a tace"ba Kai bane, Ina tace maka akwai zafi Amma kak'i kula ni, Kuma Kai mugu ne"ta k'are cikin hawaye.


Rungume ta yayi yace"I'm sorry please forgive me my love"

D'an k'ara ta saki cikin Jin wani irin azababben ciwo ta k'asan ta, da sauri ya rik'o ta Yana Mata Sannu, da k'yar tayi breakfast sannan ya bata magani tasha, sai da yayi Mata d'inki, saboda ciwon da taji, sai da yayi mata alluran barci sannan yayi d'inkin because tak'i tsayawa. Sai tausayin ta yake ji.



 Bayan d'an wani lokaci ta farka, sai taji sauk'in zafin, Amma fa tak'i kula shi tace mugu ne.😂










 *Ashdee one love*🌹



  *Manage this my fan's*😍


 *TAKU CE UMMU BASHEER*
[06/02 3:41 pm] Ummu Basheer: 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *TRUE LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *25~26*





  🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂
        *HABBY BIRTHDAY BASHEER*
🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂

  *I'm wishing you long life and prosperity may Allah bless you and guide you, Allah yasa ka Zama mahadacin Al-QUR'AN Ameen*

🍰🍰🍰🍰🍰🍰🍰🍰
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

 *Massoyan litafai na nagode sosai da addu'oin ku ga Basheer Yana mik'o sak'on gaisuwar shi zuwa gare ku thanks for the love and care, love you with all my heart*

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

 *Ga cake kuyi sharing duk da nasan ba zai ishe ku ba,🎂 Ina surukai na suke, ko da yake ai Kuna dayawa, y'an matan basheer na dayawa😂,to ba dan kar ace nayi son Kai ba da na ambato ku*😜

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹


 *WANI AL-AMARI*


 *Na Real Mai dambu ce*


 *Congratulations Sister for the complications of your amazing novel, Ina tayaki murnan Kamala litafinki Allah ya k'ara basira hazak'a k'warin ido tare da laushin hannu Ameen, Allah ya kare ki daga sharin mak'iyya da mahassada Ameen*

 *Ja muje tawan Ina biye dake a cikin litafin ki Mai suna KISHIYA TA JIHADINA*

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹


 *Sister Sajida marubuciyar y'ar mahaukaciya this page is yours na baki kyauta, kina k'amshi Ina Miki feshin Humbra, up up up*

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹







 *Ranar* yini tayi cikin d'aki shi Kuma gogan naku na faman tarairayar ta, har zuwa dare sannan HANA ke tambayar shi ita dan su Mommy basu damu da ita ba, ce Mata yayi Bata da lafiya kawai, lokacin da za suyi barci kan kujera ta kwanta Dan da gaske ta tsorata da shi, ganin Haka sai ya nufe ta yace ta koma kan bed.

 Kamar zatayi kuka tace"nifa ka k'yale ni"😫

 Cikin rarrashin ta yace"come-on baby babu abin da Zan Miki bai Dace ki kwanta a Nan ba"

 Tace"Kai nifa Nan Zan kwanta Dan ni ba y'ar iska bace Kuma fa sai na fad'a ma YAYA NA abin da kayi min"😒

 Zaro ido yayi yace"haba baby da gaske kike? Wannan ai sirrin mu ne, bai kamata kowa yaji ba"

 Murgud'a Baki tayi ta juya baya alamar Kai ka sani, da k'yar ta yarda suka kwanta tare a bed, ba yanda zaiyi tunda yayi mata d'inki da sai yayi second round Dan yayi tasting d'in zuma, daurewa kawai yayi sai dai ina cikin dare ya rungume ta Yana kissing d'in ta tare da cire mata, lokacin da yaci karo da breast d'in ta masu kyau farare tas ga nipple d'in ta jajazur ai sai ya rikice ya rasa natsuwar shi, bakin shi ya Kai kan nipple d'in ya fara Mata wani irin wasa, cikin barci taji wani irin dad'i har tana k'ara bank'aro Mai su, ai Nan ya cafke ya fara tsotsan su, ai su DEEJA shiru kake ji, ni ko nace an je duniyar ma'aurata😂. Babu abin da yayi mata Amma yanda kuka San baby to kwana yayi Yana tsotsan breast, sai kace Habeeb na cikin litafin Aunty Maimounath HUBBEY.🙈


Washegari da safe

 Taji sauk'i sosai Dan har tana tafiya normal sai dai nipples d'in ta da suke Mata d'an zafi irin ba'a Saba da tsotsan su ba. Saukowa tayi downstairs Nan ta tarar da su Mommy na zaune, gaishe su tayi sai rufe fuska take gani take kamar sun San abin da ya faru tsakanin ta da ASHRAF,🙈


Kitchen ta shiga ita da HANA tana taya ta wanke-wanke Dan Mommy nasa yaran ta aiki saboda tace gara su iya Dan aure zasuyi.

 DEEJA ce ta d'auko wani plate tana cewa"ke HANNE Haka ake wanke-wanke to Allah bai fita ba"😙

 HANA tace"wace ce Hanne Kuma?"☹

  Tace"yo wace ce in ba ke ba, ji min yarinyan nan"😏

  Kamar HANA zatayi kuka tace"ni wallahi ba suna na kenan ba"😫

 Tab'e baki tayi tace"oho dai ni haka Zan Kira ki Dan akwai wata yarinya a k'auyen mu sunan ta kenan"😜

 A fusace HANA ta bar kitchen d'in, DEEJA ma bin bayan ta tayi, suna shiga parlour HANA tace"Mommy kin ga matar brother Wai Hanne take Kira na dashi"

 Mommy tace"yau na shiga uku da jaraba, ke d'in ce kuma Hanne?"😦

 Abin dariya yaba Aunty MEERAH tace"oh su little sister an Zama y'an k'auye"😂

 DEEJA tace"yo ai dama sunan ta kenan, Dan ma bance miki Hannetuwa ba"😒

Mommy cike da fushi tace"ke  you are stupid, autar tawa kike ma Haka"

 ASHRAF dake zaune yana danna wayan shi takaici duk ya ishe shi, Ganin DEEJA zata k'ara wani maganar ne ya mik'e tare da jan hannun ta zuwa upstairs, suna shiga bedroom yace"Wai meyasa kike haka ne?",

 Turo baki tayi tace"to ni meye nayi?"

 Tana bashi sha'awa idan ta turo baki, ai nan ya had'a bakin su ya shiga kissing d'in ta in a passionate way, har sai da ya gaji Dan kan shi ya sake ta, ita ko hawaye duk a fuskar ta tace"nifa wannan iskancin ya ishe ni, Wai har da had'a baki idan ba k'azanta ba"☹

 Rik'o ta yayi yace"baby how many times have I told you that wannan ba iskanci bane, uhm?"

K'ara turo baki tayi tace"oho dai ko dad'i babu"😙

  Kamar yayi dariya yace"oh haka Kika ce then let's see it"

Ai Nan ya fara k'okarin rik'e ta, tana ganin haka ai ta tsorata suka Fara tsere a bedroom d'in, cikin wasa.



 Cikin kwana biyu sun shak'u da junan su Dan basa iya barci idan ba tare ba, baya mata komai ya barta ta warke, sai dai fa da daddare Yana jagula ta son ranshi, ta b'angaren DEEJA da su Mommy ko ba ruwan ta dasu sai idan ta tsokana HANA Nan Mommy zatayi ta mata fad'a ita ko, ai ko a jikin ta bata damu ba.



 Da missalin k'arfe 10:00 pm


Wani night gown iya gwiwa green colour ASHRAF ya ba DEEJA yace tasa, ba k'aramin kyau rigan yayi mata ba duk ya fito da ainihin surar ta, breast d'in ta ya ciko a cikin breast cuff d'in.sai k'amshi take.

Shi Kuma Yana sanye da singlet da doguwar wando, Yana danna laptop  time to time Yana sipping coffee, lokacin da ta fito ai ya kusa k'warewa, cikin kunya ta k'arasa kan bed d'in tana rufe jikin ta da blanket, ajiye laptop da coffee yayi a gefe.

 Rungume ta yayi Yana shinshinar wuyan ta Yana sa harshe Yana lashewa, ai wani irin shoking take ji. Juyo da ita yayi ya had'e bakin su Yana tsotsan lips d'in ta, wani irin yanayi suka shiga, gaskiya daren yau ba zai iya hak'ura da ita ba, can ya cire mata riga sai ga abin da yake so sun bayana a tsatsaye dasu wato breast, Nan fa ya cafko su ya fara tsotsan su, zuwa can DEEJA taji zai wuce gona da iri, ai Nan fa ta fara ture shi tana kuka sai Kiran sunayen INNA da YAYAN TA takeyi, gogan naku ko bai ma San tanayi ba, to nidai fita nayi na rufe musu k'ofar su.





Da k'yar ya iya barin ta a daren Nan amma fa ta wahala, sai rarrashin ta yake, Yana bata hak'uri da nuna Mata ai wannan shine rayuwar aure, da k'yar tayi barci.










Da safe Duk suka had'u a dinning room sukayi breakfast, kasancewar ranar Monday ne duk suna da aiki ranar Kuma ASHRAF zai koma aiki, Cikin Shirin tafiya yana sanye da kayan doctors ya k'arasa gaban ta tare da rungume ta yace"I'm going to miss you my love"

 Turo baki tayi tace"ba wani Nan ai gara ka tafi dan you are wicked"😙

Cafko bakin yayi da nashi ya fara kissing d'in ta, da k'yar ta ture shi tace"wallahi sai na fad'a ma YAYA NA"😦

 Yace"oh my love Wai sai yaushe zaki daina wani Kiran min YAYAN Nan naki?"🤦🏻‍♂

 Hararan shi tayi k'ara rungume ta yayi sannan ya tafi.





 After two weeks


Cikin satin Nan DEEJA tayi fama da ASHRAF dan shi irin mazan Nan ne masu buk'ata, idan dare yayi gaban ta har fad'uwa yakeyi, tun bata Saba ba har yanzu ta saba, gashi shi Kuma baya gajiya da ita dan ita irin matan Nan ne da ba'a cika samun su a cikin Mata ba, wato shu'ura sune matan da suke da ni'ima ko da ace basu Sha maganin Mata ba, suna da wani irin ni'ima na mussaman to DEEJA tana cikin su, shiyasa kullum yake manne da ita.


ASHRAF yasa ta a school d'in su HANA class d'in su d'aya,S.S.S 2 har Islamiyyan su d'aya, sosai ta dage da karatu shi kan shi Yana mamakin baiwar da Allah yayi mata na k'wakwalwa, Kuma ya siyan Mata  phone Mai kyau da tsada sai murna take, shi da kan shi yasa Mata number'n YAYA BILAL, ai yanzu ko da yaushe cikin waya suke har da INNA.



 Kwance take kan bed tana duba wani chemistry text book, fitowan shi kenan daga wanka Yana sanye da Bathrobe hannun shi d'aya Yana rik'e da K'aramin towel Yana goge gashin kanshi, k'arasawa gurin ta yayi ya rungume ta, turo baki tayi cikin shagwab'a tace"ni dai zaka jik'a min book na"

K'ara rungume ta yayi yace"you are so sweet my wife tell me what's the secret?" Yayi kissing d'in ta.

Tace"ba wani secret, nidai k'yale ni"😏

Cire bathrobe d'in yayi ai da sauri ta rufe ido, dariya yayi Yana k'okarin cire mata d'an k'aramin top d'in dake jikin ta, kukan shagwab'a ta sa mai, ai da sauri ya had'e bakin su ya fara tsotsa, can yayi nasarar cire rigan Nan breast d'in ta suka fito Yana ganin su ya rasa natsuwar shi sai sucking d'in su yake, zuwa can suka shiga duniyar ma'aurata.





Washegari da safe DEEJA tayi Shirin ta cikin uniform white d'in Riga mai kyau gaban shi anyi wasu bottoms,sai wando navy blue da white hijab, light make-up tayi tasa maroon d'in jambaki wow ya ku kaga farar mace da maroon, cikin shirin tafiya office ya shigo bedroom d'in, ganin DEEJA na kwaliyya abin ya bashi haushi Nan take ya nufe ta.................
















*Ashdee one love*💘




*Kuyi hak'uri kunji ni shiru kwana biyu I'm very sorry my fan's*




*TAKU CE UMMU BASHEER*
[06/02 3:41 pm] Ummu Basheer: 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *TRUE LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *27~28*



 *Dedicated to Aisha Ali Garkuwa*

 
 *Aunty Aisha wannan shafin naki ne na baki shi kyauta, Dan Allah duk mun k'osa ki fara Mana posting d'in HUKUNCIN ALLAH, massoyan ki na jira Aunty, Allah yasa ki Fara a sa'a, Allah ya Baki ikon fara mana posting, Allah ya k'ara basira, sai mun ji daga gare ki, UMMU BASHEER ce mai k'aunar ki,*


🌹.      🌹.     🌹.     🌹.






*Ganin DEEJA* na kwaliyya abin ya bashi haushi Nan take ya nufe ta Yana zuwa ya k'wace kit d'in make-up d'in, cikin kishi yace"Wai bana hana ki kwaliyya ba idan zaki school so kike Maza suyi ta kallon min ke?"

 Tace"to Dan nayi kwaliyya shine wani abu ai ba Mai kallo na"😙

 Zama yayi tare da d'aukar tissue paper ya fara goge mata fuskar, DEEJA ko haushi ya ishe ta tayi kwaliyya ya goge mata, kallon lips d'in ta yayi tare da Kai nashi kan ta ya tsotse lips d'in tass babu wannan lipstick d'in😂, ture shi DEEJA tayi tace"Allah ya Isa na mugu kawai"😏

  Da sauri yace"ni kike cema mugu baby?"😳

 Tace"yo ai Kai ne ka goge min kwaliyya na"☹

  Yace"ok ai zamu had'u later in the night you'll tell me the truth" Yana fad'in haka ya fita.

DEEJA tace"na shiga uku na, yau akwai drama"🙆🏻

 Ho su DEEJA anji maza😂


  Hijab tasa ta sauko downstairs, HANA ce ke faman zuba ma Mommy shagwab'a akan sai ta bata kud'i za suyi class party. DEEJA tace"ke HANNE wai ke halan Baki da wayau ne, kizo muje zan fad'a Miki abin da zakiyi banza kawai"😏

 Ba HANA kad'ai ba har Mommy sakin Baki tayi tace"ke Ashe rashin kunyar ki ya wuce tunani na to wallahi sai nayi maganin ki Shasha kawai"

 HANA tace"ni wallahi Mommy ki fad'a mata ta daina Kira na da HANNE ni ba y'ar k'auye bace"😫

 DEEJA tace" HANNES ki wuce dai mu tafi, kar muyi late"😒

 Mik'ewa tsaye Mommy tayi tace"wannan yarinyan akwai shegiya" nufo ta tayi da sauri tayi waje da gudu, Mommy cike da haushin ta tace"Zaki dawo ne marar tarbiyya"

 Daga waje DEEJA ta murgud'a Baki tace"Yeeee anji kunya dai, da kin biyo ni da kin Sha k'asa"😂

 ASHRAF dake gefe Yana waya Cox bai tafi ba, ranshi a b'ace ya daka mata tsawa yace"ke are you mad? Mommy ne kike ma haka?"

Da sauri ta juyo tace"Au ashe kana Nan"🙊

 Tsaki yayi yace" duk sai nayi maganin ki, wuce ki shiga mota ku tafi"

HANA ce ta fito suka shiga driver ya Kai su har school, suna Shiga DEEJA tace"ke Mommy ta baki kud'in ne?"

  Tace"bata bani ba Wai sai gobe"☹

  Tsaki tayi tace"shiyasa nake ce maki banza"😏

 Tace"Wai to meye ne?"🤔


  DEEJA tace"ai wayau zakiyi musu kawai yarinya" tayi dariya tare da fad'a ma HANA magana a kunne duk a tare suka yi dariya sannan suka shiga class.




Lokacin da suka dawo gida su Aunty MEERAH da Mommy na zaune a parlour, gaishe su sukayi sannan DEEJA ta hau upstairs ta canza Kaya zuwa wani pink and purple d'in material, saukowa tayi, Aunty MEERAH ce tace ta kawo mata cup a kitchen ta had'u Mata da juice a fridge Dan ita ma dawowan ta kenan.


Tana Shiga kitchen ta d'auko wani cup, sai dai daga can sama ta hango jerin cups masu kyau, tsale tayi ta amma bata Kai ba sai tasa kujera ta d'auko ai kafin ta sauko tsantsin hannun ta gashi dama bata rik'e da  kyau ba ai kuwa sai cups d'in suka fad'o k'asa suka fashe.

 K'arar fashewar glass cups d'in ne yasa su Mommy shigowa kitchen d'in da sauri, ganin irin aikai-aikain da DEEJA tayi mata yasa ta fara sallati, DEEJA sarkin tsoro da sauri ta sauko, ko kafin tayi magana Aunty MEERAH ta zabga Mata wani irin azababben mari Wanda tunda aka haife ta ba'a tab'a Mata ba, wani irin ihu Mai k'arfi tare da tsale tayi tana dafa gurin.

A fusace Mommy tace"we'll you shut up your mouth idiot"

 Aunty MEERAH tace"yarinyan nan Mai kama da aljanu dama Tara ki nake, shiru kawai nake miki, marar kunya, wato Mommy kike ma rashin kunya, yanzu Kuma kinzo kin fasa wannan glass cups d'in ko kin San shekarar su nawa a gurin ba Wanda ya tab'a fasawa sai ke Mai kama da mayu Koh?"

 Wani irin ihu DEEJA ta k'ara yi tace"wayyo YAYA NA, zasu kashe ni"😭

 A fusace Mommy tace"zakiyi Mana shiru ko sai na k'ara Miki?"

 DEEJA shiru tayi sai hawaye dake zuba ka shaidar mari Nan a fuskar ta, HANA dake gefe sai share hawaye takeyi Dan akwai ta da tausayi.

Aunty MEERAH tace"we'll you get up and sweep the place, nonsense"


  Fita sukayi sannan DEEJA ta d'auko broom and parker ta share gurin, HANA ce ke Bata hak'uri, komai ba tace ba, sai ajiyar zuciya takeyi kawai.




Da missalin k'arfe 8:00 pm,


ASHRAF ne ya dawo ganin Mommy a parlour yayi ya gaishe ta sannan tace yaci abinci,sai da yaci ya nufa bedroom d'in su, duk ya k'osa yaga DEEJA, Shiga bedroom d'in yayi Nan ya tarar da ita a kan bed tayi shiru, ya Saba kullum ya dawo zata zo da gudu tayi hugging d'in shi cikin farin ciki Amma yanzu ko lafiya.


  K'arasawa yayi ya d'aga ta Yana tambayar ta meke faruwa, rungume shi tayi tana kuka sosai, gaba d'aya duk ya rikice he's speechless, ganin shaidan Mari a fuskar DEEJA ya d'aga Mai hankali gashi sai kuka take Tak'i magana, a fusace ya sauko downstairs HANA ya gani tana Assignment d'in ta, Nan ya tambaye ta aiko ta fad'a mai abin da ya faru, ranshi ya b'aci sosai, straight bedroom d'in Aunty MEERAH ya nufa.


 Tana ganin shi tace"lafiya na gan ka Haka?"

Cike da b'acin rai yace"Aunty yanzu abin da kikayi ya Dace kenan, kar ki manta DEEJA Amana ce a gare ku, Kuma Mata ta ce ita"

A fusace ta mik'e tsaye tare da d'aga Mai hannun ta tace"Amana? Amana fa kace ASHRAF, wait are you my elder brother da har zaka zo kana gaya min Haka, ok to hell with the Amana"

 Shima a fusace yace"ban san meyasa Kun k'i ku gane gaskiya ba, bansan wani irin k'iyaya Kuke ma DEEJA ba, Sam bai Dace Kuna Mata Haka ba"

  Tace"shut up bana son DEEJA Kuma na tsane Zuri'ar ta"

 Yace"Don't say that ni nasan kina son Yayan DEEJA har yanzu, weather you like it or not you still loved him"

 A fusace tace"get out of here"

 Murmushi yayi yace"no need to send me a way, I'm going but Mark my words you loved Yaya MALIK"

Fita yayi yayin da ta rushe da kuka tana jin wani irin azababben k'aunar MALIK a zuciyar ta.


Lokacin da ya shigo bedroom Haka yayi ta rarrashin DEEJA, har ta hak'ura sannan aka Sha love, ya dirje ta kamar kayan wanki.😂🙈








 Washegari da safe
















*Ashdee one love*💘


 *Manage this my fan's Ina k'aunar ku sosai*😍










 *TAKU CE 💁🏼 UMMU BASHEER*
[06/02 3:41 pm] Ummu Basheer: 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *TRUE LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *29~30*


 *Congratulations Sister Sajida Ina taya ki murnan Kamala litafinki Mai suna 'YAR MAHAUKACIYA*

  *Up up up*

 *Kin fad'akar Kuma kin nishad'antar da massoyan ki, Allah ya k'ara Miki basira hazak'a k'warin ido tare da laushin hannu Ameen, Allah ya Baki ikon Fara yin Mana wani lafiya, Ameen*




  *Innalillahi wa'ina illaihir-raji'un, Allah ya Baki lafiya Sister FATY AXLAND, rashin ki kusa da mu wani iri ne, Allah ya tashi kafad'un ki, Allah ya Baki lafiya, Allah yasa kafara ne, muna matuk'ar kewar ki, Allah ya Baki lafiya takwara ta, lafiya Mai amfani, Ameen ya Rabbil Izati*😭


 *Sisters Ina buk'atar addu'an ku Basheer ba lafiya, shiyasa Sam ban samu time ba, please need your prayers, Thanks*


🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹




 *Washegari da safe*

 Kasancewar ranar weekend ne, DEEJA da yake tana son yin girki Kuma ta dage sai ta koya, kitchen ta Shiga inda ta tarar da gwogwo wace take musu girki, gaishe ta tayi, cikin fara'a ta amsa Nan DEEJA ta fara taya ta aiki tana kallon yanda take komai, bayan sun gama ne DEEJA ta shirya komai a dinning table, Dan duk mutanen gidan na barci, bedroom ta nufa, ta Shiga toilet tayi wanka sannan ta fito ta shirya cikin Swiss lace peach colour, tayi kyau sosai lipstick pink tasa sannan ta sa wani Necklace and earrings na fashion designer, sai shining take like star, sai k'amshi takeyi, ASHRAF dake barci yaji k'amshin turaren ta, bud'e ido yayi yace"Baby zo kiji"ya mik'a mata hannun shi.

Turo baki tayi cikin shagwab'a ta rik'e hannun shi,jawo ta yayi ta fad'a kan k'irjin shi, rufe su yayi da blanket Yana kissing d'in ko'ina a jikin ta, kukan shagwab'a ta sa mai, da sauri ya had'e bakin su Yana tsosa, ture shi ta fara cikin Wasa tana cewa"ni dai ka Bari"

 Da k'yar ya iya barin ta yace"baby ke d'in ce akwai sweet"

 Rufe ido tayi da sauri ta tashi tace"kaje kayi wanka muyi breakfast"

Mik'ewa tsaye yayi Yana rik'e da ita Wai sai dai suyi wankan tare, da k'yar tayi Mai wayau ta gudu.



Bayan ya shirya ne ya sauko downstairs inda ya tarar da duk sun tashi za'ayi breakfast, gaishe su yayi da k'yar Aunty MEERAH ta amsa Cox Bata son Mommy ta fahimci akwai wani abu.

 Bayan sun gama breakfast ne ASHRAF da DEEJA suna zaune a kan kujera dake cikin bedroom d'in su, sai kitso take Mai da gashi, Wai yak'i yin aski ai gara tayi mai kitso kawai, murmushi kawai yake Mata Cox Yana son ta shirmen ta da k'uruciyar ta na bashi sha'awa, rik'e hannun ta yayi ta tsaya, bakin shi ya Kai kan lips d'in ta yayi kissing d'in ta, cike da shagwab'a tace"ka Fara ko?"😒

Hannun shi yasa cikin rigar ta Yana Wasa da breast d'in ta, lumshe ido tayi da alama tana Jin dad'i, can dai ta mik'e da sauri zata gudu. Rik'o ta yayi yace"ki shirya za muje gidan su INNA"

Habawa ai tsale tayi ta rungume shi cikin farin ciki sosai take Mai godiya, k'ara shiryawa tayi Kuma tayi kyau, sannan suka nufa parlour inda suka tarar da Mommy sukayi mata sallama, har HANA tana cewa zata bi su, wani mugun kallo Mommy tayi Mata da yasa tasha jinin jikin ta, Bata bi su ba.



 Da missalin k'arfe 1:00 pm suka isa k'auyen, ba k'aramin farin ciki INNA tayi ba ganin jikan ta, YAYA BILAL ma yaji dad'i sosai ganin K'ANWAR shi tana cikin kwanciyar hankali, Haka dai suka dinga hira, DEEJA har gidan Hansai taje inda ta tarar da ita da tsohon ciki sai tausayin ta take ji, tana cewa ita gaskiya bata son ciki indai Haka ake wahala, K'arfe 5:00 pm suka bar k'auyen, DEEJA sai kuka take Wai Bata son bin shi, ni ko nace ai auren kenan.






 Bayan sati biyu



  DEEJA ce sanye da Arabian gown black tayi rolling d'in veil d'in a kanta sai ta fito Sak balarabiya, ASHRAF da ya ganta sai da yayi ta Mata pictures a wayan shi cox she's looking pretty.


Gidan Abokin shi SALIM ya Kai ta, hannu biyu matar ta tarbe su, Mai suna Ummie, tana da kirki ga son mutane, bayan sun gaisa ne taja DEEJA bedroom d'in ta inda suka fara hira, duk da cewan Ummie ta lura DEEJA akwai yarinta Amma Haka ta dage sukayi hira har ta Bata wasu magungunan Mata, tare da fad'a mata yanda zatayi, da kanta ma ta fara shirya ta inda suka shiga kitchen ta had'a kankana da ruwan zogale tare da peak milk na ruwa(Mata ku dinga gwada wannan sosai fa yake aiki), kasancewar su ASHRAF sun d'an fita,   shine suka samu damar abin da suke so, ranar dai sai dare yazo ya d'auke ta, sosai taji tana k'aunar Ummie Cox tana da kirki sosai.



 A wannan Daren DEEJA tasha azaba Dan mutumin naku k'in barin ta yayi, sai da ta fara kukan shagwab'a sannan ya hak'ura ba Dan yaso ba, ni ko nace aikin ki Ummie yayi kyau.😂




 A Haka rayuwa yaci gaba da tafiya, tsakanin DEEJA da ASHRAF soyayya suke gudanarwa mai k'arfin gaske, sannan Kuma tana zuwa makaranta da islamiyya yanzu ta fara natsuwa, sai dai d'an tsokana Wanda a jikin ta yake a hankali k'ila zata Bari, Haka take faman tsokanan HANA Mommy tayi ta fama da su tana fad'a.


B'angaren Mommy da Aunty MEERAH kuwa sun takura ma DEEJA ko da yaushe cikin yin mata fad'a suke Dan suna ganin ai YAYAN TA ne sanadiyar kashe ALHAJI BILYAMIN mahaifin su ASHRAF, a gaskiya DEEJA Sosai take hak'uri da su tana musu biyayya Kuma bata fad'a ma kowa har ASHRAF bata fad'a mai, in tak'aice muku DEEJA na Shan wahala gurin Mommy.

 Aunty MEERAH tana matuk'ar k'aunar MALIK Amma tak'i yarda ta gane cewa bashi bane ya kashe mata mahaifin ta dan har yanzu tana zargin shi.

 Wata rana kwatsam sai ga MUSA Wanda ya kasance abokin ALHAJI BILYAMIN, ziyara ya kawo musu, sosai sukayi mamaki, Nan aka sauke shi a guest room, bayan ya huta ne suka k'ara gaisawa sannan ya bayyana musu abin da ya faru tsakanin su ALHAJI BILYAMIN da ALHAJI NASIR,! Sunyi matuk'ar girgiza da Jin ainihin abin da ya faru! Duk da Haka Mommy ba tace komai ba Amma a ranta ba Wai ta yarda bane tace dai su MALIK ne sanadi!


MEERAH kuka sosai ta dingayi Ashe MALIK bai kashe mata mahaifin ta ba, ashe mahaifin ta shine Wanda ya yaudare iyayen MALIK, sannan Malam MUSA ya gyara zama inda ya fara basu labarin abin da ya faru cikin shekaru goman Nan da suka shud'e kamar Haka.

 Yace"Bayan mutuwar ALHAJI BILYAMIN nayi bincike sosai Dan gano ainihin k'auyen da ILIYASU yake, lokacin da na gano da kaina naje k'auyen, Dan insa a kama shi, sai dai na tarar da bai ma San inda kanshi yake ba Yana fama da kaf'ar shi Wanda na harbe shi a gurin, k'afan duk ya rub'e, ga ba kud'in magani, ganin irin azaban da yake Sha sai na k'yale shi domin ya d'and'dani azaba yasan cewa kashe mutum ba Wasa ba bare har mutane biyu, sai na k'yale shi, Bayan shekaru biyar naje wani hospital sai Naga wani gurgu ba shi da kaf'a d'aya da alama ya rub'e ne an yanke, naji tsoro lokacin da ya rik'e ni Yana Kiran suna na Yana neman gafara na, sai daga baya na tuno fuskar nashi Ashe ILIYASU ne, kamanin shi duk sun canza, yayi ta rok'o na Akan in yafe Mai Kuma in zo in neman mai gafarar ku, sai dai nayi k'okarin zuwa sai Kuma Allah bai nufa ba sai yanzu, shekarun baya da suka wuce naji labarin rasuwan shi, yayi Kuma mutuwar wulak'anci" ya numfasa sannan yace"Ina baku hak'uri sosai Allah Kuma ya jik'an ALHAJI BILYAMIN da ALHAJI NASIR, Allah ya raba mu da sharin mutane da mahassada, Wannan shine ainihin abin da ya faru"

 "Ameen ya Allah" su kace a tare. Mommy cikin share hawaye cikin tunanin mijin ta sannan ta bar gurin yayin da MEERAH ke ta rusa kuka da nadama da tir da halin da mahaifin ta yayi a lokacin kafin mutuwar shi.

Har gurin gate ASHRAF ya rako shi lokacin da zai tafi Yana Mai godiyan ziyaran da ya kawo musu. Nan suka yi sallama ya tafi Yana musu fatan alkhairi a rayuwar su.


 Jikin ASHRAF yayi sanyi domin shima ya tuno da rasuwan mahaifin su, straight bedroom d'in su ya nufa, DEEJA dake zaune da sauri ta tashi tsaye cikin mamakin meye ne ya samu mijin ta lokaci d'aya ya canza Dan Bata tab'a ganin shi a cikin irin wannan yanayin ba, da sauri ta rik'o hannun shi tana tambayar meke faruwa.


 Zama sukayi kan bed inda ya rungume ta, idanun shi jajazur, rungume shi tayi tana shafa Bayan shi tare da bashi hak'uri duk da bata san meke faruwa ba, k'ara rungume ta yayi da d'an k'arfi Yana sauke ajiyar zuciya, a tare suka kwanta kan bed d'in, kissing d'in shi ta fara, Cox ya d'aga Mata hankali da yanayin shi, k'ara rungume ta yayi suna kissing d'in juna kamar zasu cinye lips d'in su, da k'yar ya sake ta ya rungume ta suna sauke ajiyar zuciya a tare.








Cikin satin Nan gidan ya Zama wani iri, domin tuno da rasuwan ALHAJI BILYAMIN.


 Bayan wata d'aya


 MEERAH na cikin damuwa k'aunar MALIK take ba k'adan ba, gaba d'aya ta canza burin ta d'aya shine taga sun dawo da soyayyar su sunyi aure, duk da tasan Mommy ba zata yarda ba Kuma tana tunanin anya MALIK zai aure ta kuwa? Ganin yaudaran da mahaifin ta yayi ma na shi.

 Ranar Friday ta shirya cikin wani Arabian gown light blue tayi rolling d'in veil a kan ta, wow tayi kyau sosai black handbag and shoe tasa sai dai bata yi make up ba Dan yanzu burin ta shine taga Masoyin ta, d'aukar key d'in mota tayi ta nufa parlour tayi ma Mommy sallama akan za taje gidan wata friend d'in ta.



 
 Lokacin da ta Isa k'auyen parking tayi a k'ofar gidan su DEEJA, tare da fitowa ta Shiga ciki, INNA na zaune tana sauraren Radio taji anyi sallama tare da shigowa.

Ba k'aramin mamaki tayi ba ganin MEERAH, Tace"Lale barka da zuwa ga guri ki zauna" ta nuna mata kujera dake gefe.

Zama MEERAH tayi ta gaishe ta amsawa INNA tayi cikin fara'a tana tambayar mutanen gidan da jikar ta DEEJA, Ruwa INNA ta kawo Mata tasha sannan gurin ya d'auki shiru tsawon 10 minutes sannan MEERAH tayi magana inda tace"INNA nazo neman gafara ku ne bisa abin da mahaifina yayi Wanda Sam ban sani ba"

Cikin mamaki INNA ta tambaye ta meke faruwa, ba tare da b'ata lokaci ba MEERAH ta sanar da INNA komai da Malam MUSA ya fad'a musu, sosai INNA tayi kuka tana tsine ma ILIYASU, Nan take ta tuno da d'an ta ALHAJI NASIR, hak'uri MEERAH tayi ta Bata sannan tayi shiru.

MEERAH tace"INNA MALIK baya Nan ne? Ina son neman gafarar shi in fad'a mai gaskiya"

INNA tace"eh baya Nan Bayan ya dawo masalacin juma'a shine ya wuce gareji"

 Da mamaki tace"INNA gareji Kuma?"

 Tace"eh ai tun bayan rasuwan iyayen ku ya dawo Nan yake aiki a garejin domin yace baya buk'atar rayuwar Jin dad'i gara yayi rayuwa a k'auye Kuma duk saboda A KAN K'ANWAR SHI yayi hakan"

 Cike da mamaki tace" A KAN K'ANWAR SHI?"

INNA tace"eh, Bari in Kira wani yaro ya raka ki can garejin" mik'ewa tsaye tayi ta nufa k'ofar gida ta samu yaro ya raka ta.

MEERAH ko ba k'aramin mamaki tayi ba, Ashe dai Yana k'aunar k'anwar shi sosai tunda gashi Yana rayuwa a k'auye Bayan yanda tasan shi d'an gayu ne ga kud'i ga kyau ga halaye masu kyau but ji yanda yake rayuwa a k'auyen Nan.



Lokacin da ta Isa garejin yaron ya Shiga ya Kira MALIK (sorry Zan dinga Mai amfani da ainihin sunan shi maimakon BILAL), MALIK yayi mamaki da yaron yace Wai wata y'ar gayu Mai mota na Kiran shi, sai ya fara tunanin ko yarinyan Yayan Mahaifiyar shi ne shiyasa ya fita.


 Ganin MEERAH ya bala'in d'aga mai hankali ga tsananin mamaki, ita ko tana ganin shi ta fashe da kuka sosai.

K'arasawa gurin ta yayi yace"zubar hawayen ki tamkar ruwan dalma ne a cikin zuciya na, Zan so ki taimake ni kiyi shiru ko Zan samu natsuwa"

Jin kalaman shi yasa ta k'ara kukan wato har yanzu shima yana k'aunar ta kenan? Mik'a mata handkerchief yayi Mai k'amshi yace ta share hawayen, karb'a tayi ta goge tana cewa"Tabbas nayi kuskure da na guje maka Wanda hakan ya faru ne akan rashin sani, Amma nayi *ALK'AWARI* bazan sake barin ka ba duk da mahaifina yayi *YAUDARA DA CIN AMANA* gare ku, zanyi burin mu zama *ZURI'A D'AYA* domin Kyakyawan halayen ka" ta k'are cikin hawaye.


Murmushi yayi yace" nayi matuk'ar farin cikin yanda Kika ce haka, Zan rayu dake kamar yanda *ASEEM* ya rayu da *NAJWA* (RAYUWAR NAJWA litafi na) "


Nan MEERAH ta fad'a mai duk abin da Malam MUSA ya fad'a musu, shi kanshi sai da hankalin shi ya tashi sosai, Nan dai sukayi hira da yin ma iyayen su addu'a, sannan suka yi exchanging d'in number'n su, har gurin motar ta ya raka ta sai da taga tafiyar ta sannan ya Shiga gurin INNA suna jimamin abin da ya faru.





  *LOVE*💖


 Wani irin soyayya ne Mai zafin gaske a tsakanin su domin yanzu kullum cikin yin waya suke, Haka Kuma sun shirya yin aure a tsakanin su duk da suna tunanin Mommy ce matsalan su, Mommy bata tab'a lura akwai wani soyayya a tsakanin MEERAH da MALIK ba Dan ta cire shi a lissafi ma, sai dai tana matuk'ar ba DEEJA wahala, yanzu MEERAH idan Mommy nama DEEJA fad'a sai ta dinga kare ta Wanda Mommy takan yi mamakin hakan. Yanzu MEERAH na matuk'ar son DEEJA domin soyayyar dake tsakanin ta da yayan DEEJA d'in.













*Ashdee one love*💘


 *Masu karatu shin Kuna ganin DEEJA zata yarda YAYAN TA ya aura MEERAH kuwa? Shin YAYAN nata zai iya yin abin da K'ANWAR SHI take so Dan kar ku manta yace A KAN K'ANWA TA Zan iya komai, to ya kenan? Ku biyo ni Dan Jin yanda zata kasance.*





 *TAKU CE💁🏼 UMMU BASHEER*
[06/02 3:41 pm] Ummu Basheer: 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *TRUE LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *31~32*


 *Dedicated to Ayushert muh'd*

 *This page is yours, na kine ke kad'ai, sosai kike fad'akar da Kuma ilimantar da mu a cikin litafin ki na KAINUWA, Allah ya k'ara basira da hazak'a k'warin ido tare da laushin hannu Ameen, ke d'in ta daban ce Allah ya kare ki daga sharin mak'iyya da mahassada Ameen*




  *Doctor Deejert*

 *Up*

   *Up*

       *Up*


 *Congratulations Sister Xainab, Ina tayaki murnan Kamala litafinki da kikayi Allah ya k'ara basira da hazak'a Ameen, gaskiya kin fad'akar da mu massoyan ki, sai mun jiki a sabon litafin ki, can't wait*

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹


 *Sister Xainab da sis Maimounath, ku ne dai kuka koya min Dan ba ruwana🙈, K'awas Badeeyerh Ina Bayan ki muna tare*😂







 *Soyayya* tsakanin MALIK da MEERAH ya wuce yanda Kuke tunani domin yanzu har had'uwa suke yi ba tare da sanin kowa ba, Rana d'aya MEERAH ta rasa yanda zatayi Cox tana buk'atar shawara Dan yanzu aure suke son yi ita da MALIK, ASHRAF ta samu da maganar Dan babu wani kunya da zata ji tunda tana k'aunar MALIK, ASHRAF baiyi mamaki ba Cox already yasan tana k'aunar shi till now,  shawaran da ta Bata taji dad'i sosai Dan cewa yayi taje ta samu Daddy da maganar yasan Daddy zai amince idan yaso yaje ya samu Mommy yanda akayi nashi.


Haka kuwa tayi Dan taje ta same shi Kuma yaji dad'i Dan gaskiya Yana son yaga tayi aure ita ma Nan yace kar ta damu zasuyi magana da Mommy, cikin farin ciki ta Kira MALIK ta fad'a mai shima yaji dad'i, addu'an su dai shine Allah yasa ta yarda.




Daddy da kanshi ya same ta da maganar ai ko ta girgiza sosai Dan Bata tab'a tunanin hakan ba, nan ta nuna ita fa Sam bata yarda ba da k'yar Daddy ya shawo kanta  yayi mata nasiha sosai inda jikin ta yayi sanyi, ba'a son ranta ba dai.


 Wani gida Mai shegen kyau MALIK ya gina ya tare shi da INNA, lokacin da ASHRAF ya Kai DEEJA ai kamar ta zauna a gidan tsabar farin ciki, INNA ce ke bata labarin auren da MALIK zaiyi da MEERAH, hankalin ta ya tashi, wato MEERAH da Bata da kirki tana mugunta mata shine yanzu YAYAN TA zai aura, kuka ta fashe da shi sosai ai ba shiri MALIK da yaji kukan ta ya shigo Yana tambayar lafiya?

Cikin kuka tace" gaskiya ni YAYA NA bana son ta, muguwa ce, ka aura wata kawai Amma Banda Aunty MEERAH"😭

 Hankalin shi a tashe yace" yi shiru K'ANWA TA, Amma tana da kirki fa, nasan tana son ki"

 Tace" ni dai wallahi bana son ta"😫


 Cikin rarrashin ta yace"ya Isa Haka K'ANWA TA, abin da kike so shi za'ayi"


 Sannan ta hak'ura, ASHRAF yazo suka tafi gida, shi dai ya lura ranta a b'ace Amma baiyi tunanin wani abu ba, a tunanin shi kewar su INNA take yi.




 Wannan shine ana wata ga wata, domin DEEJA tace Sam bata yarda da auren ba yayin da MALIK ya Shiga tashin hankali Dan Yana son farin cikin K'ANWAR SHI Amma Kuma Yana matuk'ar k'aunar MEERAH Haka dai su KABIR sukayi ta bashi hak'uri suka ce yayi auren Dan yarinta ke damun DEEJA, shi dai baya son b'ata Mata rai.


B'angaren MEERAH ta Shiga tashin hankali, Haka tasa DEEJA a gaba tana Bata hak'uri da nuna mata cewa tayi nadama kuma tana son ta, ita dai DEEJA ta dage Bata so, Haka ma da ASHRAF yaji yace ta fad'a ma YAYAN TA cewa ta yarda da auren, kuka ta sa mai da yace Haka, ita gaskiya tak'i yarda Nan yace sai ta fad'a mai dalilin da yasa tak'i yarda, Nan ta fad'a mai komai Akan abin da MEERAH tayi mata,  ya tausaya mata sosai, Kuma ya bata hak'uri tare da nuna mata tayi hak'uri komai ya wuce tunda yanzu MEERAH na bata hak'uri, tsananin k'aunar da take ma mijin ta ASHRAF sai ta amince domin ta tuna lokacin da ita ma YAYAN TA yak'i amincewa but in the end Kuma ya amince Dan Haka Kiran shi tayi a waya tace ta yarda da auren komai ai ya wuce, sosai yaji dad'i Nan take ya Kira MEERAH a waya, da k'yar ta d'auka Dan haushi take ji, Wai meyasa zai ce sai k'anwar shi ta amince za'ayi auren Bayan suna son junan su Kuma manyan su sun amince, Nan ya sanar da ita ai ko tayi murna sosai.




 Ansa ranar d'aurin auren MALIK da MEERAH Nan da sati uku masu zuwa, inda zasu tare a Nan gidan da ya Gina, Nan aka Fara shirye-shiryen biki.



 Bayan sati biyu


 Biki saura sati d'aya kenan inda DEEJA tayi ta ma ASHRAF kuka Wai sai ya barta taje gidan su domin a Fara shirye-shiryen biki da ita. Ba Dan ya so ba ya barta, shi da kanshi ya Kai ta.


 Sai ana gobe d'aurin aure ta dawo gidan ta, inda akayi Arabian night, ranar ba k'aramin kyau tayi ba kamar ita ce Amaryan, ASHRAF ko sai mak'ale Mata yake, Dan ma gurin babu maza da bazai barta ba.


 Washegari da missalin k'arfe 2:00 pm aka d'aura auren ABDUL-MALIK (Bilal) NASIR tare da AMEERAH BILYAMIN, akan sadaki mafi daraja Naira dubu hamsin dubamin mutane sun shaida d'aurin auren Mai cike da tarin Albarka, ni ko nace wannan shine tsananin rabo, tunda gashi ko Bayan iyayen sun rasu Kuma anyi auren Allah ya Sanya alkhairi.





 Around 8:00 pm aka d'auki amarya zuwa gidan ta, gaskiya gida yayi kyau sosai domin Side d'in INNA da ban nasu da ban, guri yayi kyau Masha Allah, Nan aka watse aka bar Amarya da Angon ta, ni ko nace Sai da safe.




  Bayan mutane sun watse, DEEJA tayi wanka tasa wani irin nighties masu shegen kyau ga wani irin k'amshi Mai sanyi da dad'i dake tashi a jikin ta,  tana zaune gaban dressing mirror tana shafa lotion, ASHRAF ne ya shigo hannun shi rik'e da leda.


 K'arasawa yayi ya rungume ta Yana shak'ar k'amshin ta, cikin wani irin yanayi yace"baby I love you and I missed you"

 Mik'ewa tsaye tayi tare da nufan bed tana cewa"I'm feeling sleepy"😒

  Da sauri ya nufe ta yace"no baby don't said that, nayi kewar ki and you know nayi k'okari tun last week fa"🤦🏻‍♂

  Cikin shagwab'a tace"yo ai kasan fa......"☹

 Katse mata magana yayi ta hanyar had'e lips d'in su ya fara kissing d'in ta in a passionate way, ni ko fita nayi waje tare da rufe musu k'ofa.










 Bayan wata d'aya


  Mommy na takura ma DEEJA sosai, komai na gidan ita takeyi har girki wani lokacin ita keyi, ASHRAF bai tab'a sanin haka ba saboda cikin watan baya Zama kullum Yana gurin aiki, sai dare idan ya dawo, Sam baya samun time sai weekend Wanda Yana d'an lura da hakan sai dai da yayi magana Mommy zata haushi da bala'i.





Mommy ce zaune da matar Daddy suna hira inda Mommy ke fad'a ma matar Daddy wacce ake Kiran ta da Ummie cewa gaskiya ita ba ta son DEEJA bare yanzu da taji shiru ko ciki Bata da shi gaskiya ita tana son ASHRAF yayi wani auren, murmushin mugunta Ummie tayi a ranta cewa take ai fad'uwa yazo dai-dai da Zama, Dama ga 'yar ta MUFEEDA sai kawai ta aure ASHRAF domin dama Ummie irin matan Nan ne masu son abin duniya, bare tasan irin dukiyar da su ASHRAF ke da shi, Haka Kuma tana k'okarin SAIF yaron ta ya aura HANA Nan gaba.


Gyara zama tayi tace..................










 *Ashdee one love*💘






 *TAKU CE 💁🏼UMMU BASHEER*
[06/02 3:41 pm] Ummu Basheer: 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *TRUE LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *33~34*






*Kuyi hak'uri kunji ni shiru kwana biyu, I'm very sorry, bana samun times ne kuyi managing wannan, Thanks for the love and, care love you all*




 *Gyara* Zama tayi tace"Mai zai hana mu had'a MUFEEDA da ASHRAF?"

Cikin sauri ta kalle ta tace"kina ganin zasu so junan su?"

Dariyan samun nasara Ummie tayi tace"ko ma basa son junan su zasu so daga baya, tunda yanzu muna da iko dasu Dan Haka ni Ina ganin ba matsala in dai MUFEEDA ce"


 Mommy tace"to shikenan hakan ma yayi Kinga sai ayi auren zumunci kenan"

Nan sukayi ta hira tare da shirya yanda bikin zai kasance.




Lokacin da Ummie ta koma gida ta samu MUFEEDA da maganar, da sauri MUFEEDA ta mik'e tsaye Jin abin da Ummie'n ta fad'a, Tace"Ummie yanzu fa an daina irin wannan auren ya kamata ku waye mana"

Cikin haushi Ummie tace"wato kenan mu ne bamu waye ba ko? Fool kawai ana neman Miki gidan hutu kina kaucewa to ba zai yuwu ba dole ki aure ASHRAF" ta bar gurin.


Tsaki MUFEEDA tayi a ranta tace wannan Ummie'n Sam bata waye ba sai kace old school, Wai auren dole, ni wallahi yanda nake Jin dad'in harka da Mata ba abin da zai sa na aura namiji (Wa'izzubila Allah kayi Mana tsari), Nan tayi ta Jin haushin Ummie Dan ita ko k'adan Bata son ASHRAF Kai ita maza ne ma bata so, ita DEEJA ce ke bata sha'awa tana son yarinyan, Dan Haka ta Kira wata K'awar ta a waya ta fad'a Mata abin da Ummie tace Nan K'awar tayi ta zuga ta Wai Kar ta yarda ta amince da auren.



 Mommy ce zaune a parlour tana jiran dawowan ASHRAF daga aiki, shigowa gidan yayi da alamar gajiya a tare da shi, rigar doctor d'in shi na rik'e a hannun shi, da k'yar ya rik'e briefcase d'in shi tsabar gajiya, k'arasawa yayi ya gaishe da Mommy sannan ya mik'e tsaye ya nufa hanyar upstairs. Dakatar da shi tayi tare da umartan shi ya dawo ya zauna za suyi magana.

Zama yayi Yana sauraren ta, inda ta sanar mai da maganar had'a auren shi da MUFEEDA!

 A razane ya mik'e cikin matuk'ar tashin hankali yace"Mommy Dan Allah Kar kice haka Ina son Mata ta, Kuma ni bani da sha'awan auren Mata biyu, please Mommy Kar kiyi min Haka"

A fusace tace"shut up bana son Jin komai Dan ba shawaran ka nake nema ba wannan umurni ne"

Kamar zaiyi kuka yace"No Mommy please don't say that, I really loved her"

 Daka mai tsawa tayi tace"get out of here nonsense, yanzu Kai Dan baka da kunya har zaka kalle ni kace Wai kana son matar ka, idan ba rashin kunya ba"

Ranshi a b'ace ya nufa upstairs. DEEJA na kwance Dan har ta fara barci sai gashi ya shigo, da sauri taje ta rungume shi tare da sakar mai kiss a kumatu, daurewa kawai yayi baya son ta gano wani Abu,  sai da yayi wanka yasa pyjamas sannan ta kawo mai abinci, da k'yar ya iya cin abincin, sannan suka kwanta barci.

 DEEJA jikin ta yayi sanyi domin ta lura akwai abin da ke damun shi, Zama tayi cikin shagwab'a tace" nifa na lura akwai abin da ke damun ka, kawai you don't want to tell me ne"

 Zama shima yayi tare da hugging d'in ta yace"no baby babu komai, kawai aiki ne yayi min yawa a office, that's why"

Tace"are you sure?"

 Kiss d'in forehead d'in ta yayi yace"very sure my baby"

 Nan suka shiga duniyar ma'aurata, Bayan sunyi wanka har DEEJA tayi barci Nan ya zauna Yana ta tunani Cox shi gaskiya baya son MUFEEDA yarinyan Bata da tarbiyya ko k'adan Kuma sannan Yana tunani Dan yasan DEEJA baza ta yarda ba, gashi idan tak'i yarda YAYAN TA zai k'i yarda shima, dole yasan yanda zaiyi Kar auren ya yuwu.a Haka ya kwana cikin tunani da bak'in ciki.




An d'auki tsawon sati biyu, Amma Sam ASHRAF da MUFEEDA sunk'i yarda, gashi baya son DEEJA ta sani.


 Matar SAIF ta haihu, ASHRAF da kanshi ya Kai DEEJA, ai ko tunda taga baby'n taji tana son haihuwa ita ma, yaron kyakyawa, Bayan sun dawo gida Haka tasa ASHRAF a gaba da kuka sosai fa.


 Yace"baby Wai mene ne?"


 Cikin kuka tace"ni wallahi baby nake so, Gaskiya kayi min ciki Nima in samu baby irin nasu SAIF"😫


 Habawa ai bai san lokacin da ya fara dariya ba, maganar ta ya bashi dariya yace"I'm sorry baby, Allah shine mai bayarwa, Dan Haka muyi addu'a Allah ya ba mu"

 Tace"to tashi mu Fara salla Dan gaskiya Ina son baby, inyi ta Mata wanka da kwaliyya"😂


 Nan dai sukayi ta addu'a.



 Washegari da Rana

Mommy ce ka fad'a ma Aunty MEERAH auren da zasu  had'a na ASHRAF da MUFEEDA, sosai tayi mamaki Kuma gaskiya bata son auren domin tasan MUFEEDA Bata da tarbiyya, Ashe DEEJA na jinsu Wanda shigowan ta parlour'n kenan, ai wani iri ihu ta tayi, da sauri su Mommy suka kalle ta, inda Mommy tace"ke Baki da hankali ne? Zaki zo kina Mana ihu?"

Da sauri DEEJA ta rik'e k'afar Mommy tana kuka tace"Dan Allah Mommy Kar kiyi ma ASHRAF aure, wallahi Ina son shi, Dan Allah kar kisa ayi min kishiya"


 Ture ta Mommy tayi tace"you are very stupid, dole sai yayi aure Dan na tsane ki"

 Idanun DEEJA jajazur ta kalle Mommy tace.................














*Ashdee one love*💘




*TAKU CE💁🏼 UMMU BASHEER*
[06/02 3:41 pm] Ummu Basheer: 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *TRUE LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *35~36*






 *DEEJA* idanun ta jajazur ta kalle Mommy tace" Mommy meye nayi Miki Kika tsane ni Haka?,idan wani Abu ne ki fad'a min sai in gyara, wallahi bana son kishiya ki taimake ni Dan Allah"


 A fusace tace"ni dai na tsane ki ne kawai Kuma aure babu fashi sai anyi, Dan Haka tashi ki bani guri"

Cikin sanyin jiki ta bar gurin tana share hawaye.

Aunty MEERAH tace" Mommy gaskiya hakan bai Dace ba, gaba d'aya nawa DEEJA take da har za'ayi mata kishiya, Mommy Dan Allah ki janye maganar Nan"


 Hararan ta tayi tace"Sannu uwa ta, to bazan janye ba"

 Tace"Mommy na rok'e ki daki janye, idan da nice za'ayi ma kishiyar Zaki ji dad'i, duk abin da kayi ma y'ar wani za'ayi ma naka, ko HANA baza ki so daga auren ta ayi mata kishiya ba"


 Jikin Mommy yayi sanyi domin tasan gaskiyan MEERAH ne,


 
A ranar DEEJA tayi ta kuka sosai, ASHRAF na dawowa ta fad'a mai sai kuka take yi, hankalin shi ba k'aramin tashi yayi ba, Haka yayi ta rarrashin ta da k'yar tayi barci ranar.



Cikin kwanaki biyu duk ta fita hayyacin ta ga wani irin azababben ciwon Kai da take fama dashi, shi kanshi ASHRAF hankalin shi a tashe yake,Bata son cin abinci sai ta d'an rame tayi haske, Mommy Kuma ta dage sai ASHRAF ya aura MUFEEDA.


B'angaren MUFEEDA Koh tayi-tayi, Ummie ta janye maganar auren tak'i Dan Haka kawai sai ta bar gidan tsawon sati biyu ana neman ta ba'a gan ta ba, Dan Tace baza ta dawo ba sai an fasa auren ta da ASHRAF Dan ita Bata son maza a cewar ta.





Ranar Thursday


 Driver ne yaje school d'in su DEEJA ya d'auko su, suna Shiga DEEJA tace ya kaita gidan YAYAN TA, cikin mamaki HANA ke tambayar ta meyasa?

 Tace"ke nifa bazan koma gidan ku ba, tunda Wai kishiya za'ayi min, gara in koma gidan YAYA NA Wanda ke so na"😙


 HANA tace"gaskiya Kam Nima dai bana son Aunty MUFEEDA, y'ar iska ce"☹

 DEEJA ta zaro ido, HANA tace"eh wallahi ranar tazo gidan mu shine ta rungume ni har tana cewa in cire Riga na, ai ko guduwa nayi, shiyasa bana son tana zuwa gidan mu"


DEEJA tace" toh Nima dai Naga tana sa kayan y'an iska"🤔

Driver ne yayi parking a k'ofar gidan YAYA MALIK Nan DEEJA ta fito tare da Shiga ciki, straight side d'in INNA, tana zuwa ta fad'a jikin ta tare da sakin kuka mai k'arfi.

Da sauri INNA ta fara tambayar ta meke faruwa, da k'yar ta fad'a Mata komai, INNA sai sallati takeyi domin tasan DEEJA yarinya ce bai kamata idan kishiyar za'ayi mata ba ayi Mata yanzu Dan irin wannan sai a cuce ta, Nan ta dinga Bata hak'uri sannan tace tayi wanka taci abinci.


 Bayan tayi wanka tasa wani kayan Dan dama akwai wasu kayan ta a gidan, sai da daddare sannan ta nufa side d'in Aunty MEERAH, inda ta tarar da YAYAN TA ya gama dinner.


Bayan sun gaisa ne tasa Mai kukan shagwab'a, ya tambaye ta mene ne sannan ta fad'a mai, Aunty MEERAH ko shiru kawai tayi,

DEEJA tace" ni daga yau na dawo Nan gidan bazan koma can ba"😒


 Yace"Kar ki damu K'ANWA TA ba kishiyar da za'ayi Miki"

 Da sauri cikin hararan Aunty MEERAH tace"in dai akayi min to Kai ma sai kayi ma Aunty MEERAH"😏


A tare suka zaro ido suna kallon ta, Aunty MEERAH tace"ke ni sa'ar ki ce?"

YAYA yace"na yarda K'ANWA TA, Dan Haka MEERAH kiyi ma Mommy magana ta bar wannan auren ko Kuma Nima inyi aure"

Zaro ido tayi cikin tashin hankali tace"A'a hakan ma ba zai yuwu ba, Inshallah za muyi magana da Mommy kinji My Sister DEEJA?"

 Tace"naji dai"😏



Shi ko MALIK ya fad'a hakan ne kawai Dan MEERAH ta shawo kan Mommy ba Wai zaiyi ba ne.



B'angaren ASHRAF ko yana dawowa yaga bai ga DEEJA ba hankalin shi ya tashi, Haka yaje ya tambayi HANA Nan ta fad'a mai cewa tana gidan YAYAN TA, ba k'aramin tashin hankali ya shiga ba Dan yasan YAYAN DEEJA ba zai yarda ta dawo ba in har yaji mai ke faruwa. Haka ya koma bedroom sai Kiran wayan DEEJA yake but tak'i d'auka, Haka ya kwana jikin kewar ta.



 Washegari da safe

Bayan yayi Shirin office sai da ya biya ta gidan YAYA MALIK, Bayan sun gaisa ne, ASHRAF ke bashi hak'urin abin dake faruwa, Sannan ya nufa side d'in INNA, inda ya tarar dasu suna breakfast,


DEEJA na ganin shi ta bar parlour'n, Gaishe da INNA yayi hankalin shi na kan bedroom d'in da DEEJA ta Shiga,


INNA tace ya Shiga bedroom d'in tunda ita gudun shi takeyi, kamar jira yake ya Shiga, Yana zuwa ya rungume ta, ture shi tayi tana cewa ya k'yale ta, Nan yace tayi hak'uri ta koma gida, ai Nan tasa mai kuka ita baza ba, ba Dan yaso ba ya tafi ya barta.




Aunty MEERAH hankalin ta ba k'aramin tashi yayi ba akan maganar YAYA MALIK, gidan su taje tayi ta ma Mommy kuka, ita ma za'ayi mata kishiya Kuma ita Bata so, gaskiya ta janye maganar auren ASHRAF da MUFEEDA.




Cikin sati biyu ASHRAF da Aunty MEERAH harda HANA sun sa Mommy a gaba da cewar Kar ayi Auren, Dan kullum sai ASHRAF yaje gurin DEEJA Amma tak'i kula shi, tace sai dai ya fasa auren, MEERAH ma tana cikin tashin hankali domin yanda DEEJA ke birkice ma Yayan ta da kuka Haka shima zai zo ya birkita MEERAH cewa tasa a fasa auren ko yayi aure, HANA ko tana goyon Bayan YAYAN TA ne.



Ummie dole yasa ta hak'ura da had'a auren ba Dan taso ba, Nan ta sanar da Mommy cewa Ta fasa auren Dan MUFEEDA Bata so, Mommy dama kamar jira take, Nan ita ma ta fasa tunda yaran ta basa son auren.


Daddy dama yasa musu ido ne kawai bai bi ta kansu ba,



Lokacin da Mommy ta Tara yaran nata ta sanar dasu an fasa auren rungume ta suka yi suna farin ciki.




ASHRAF da kanshi ya dawo da matar shi gida tunda an fasa auren, MEERAH kuma ta samu kwanciyar hankali YAYA MALIK ya fad'a mata dama Wasa yake Mata, dad'i taji sosai.



Ummie taso had'a Auren HANA da SAIF d'an ta,Amma tana tsoron kar a kuma yanda akayi nasu ASHRAF dan haka sai da ta tambaye SAIF ko akwai wacce yake so, ai Nan ya fad'a mata akwai wace yake so, shiru kawai tayi ba Tace komai ba,








 Bayan wata d'aya




ASHRAF ya gano cewa DEEJA na d'auke da ciki Dan Haka Yana bata kulawa na mussaman, Ashe ma Aunty MEERAH nada ciki ita ma, ai Nan fa akayi ta farin ciki.





Wata Rana ASHRAF ya samu cigaban karatun shi da yake nema a London, ai Koh Nan suka shirya shi da DEEJA, sukayi ma yan'uwa da abokanan arziki sallama, yayin da jirgin su ya d'aga zuwa London.




 *LONDON*




 Rayuwar farin ciki shine ya cigaba da gudana tsakanin ASHRAF da DEEJA, yayin da suke kula da cikin inda ya Kai wata Tara ta haifa'da namiji, YAYA MALIK da INNA sun zo inda ya bar INNA ta zauna Mata, zuwa yaron yayi wayau.


Ranar suna yaro yaci sunan mahaifin ASHRAF wato BILYAMIN suna Kiran shi da KHALIFA, su Mommy ma duk sun zo da HANA,


Bayan sati d'aya Aunty MEERAH ta haihu inda aka samu y'a mace wacce taci sunan Mahaifiyar su DEEJA wato MAIMUNA, ana ce mata little, Mommy ce ta zauna Mata har aka yi 40 days sannan ta koma gida ita da HANA.





 KHALIFA nada wata shida INNA ta matsa ita fa dole ta dawo Nigeria ta gaji da k'asar turawa Haka, Nan ASHRAF da kanshi ya dawo da ita, satin shi d'aya a Nigeria ya koma LONDON.


Rayuwar farin ciki ya cigaba da gudana inda DEEJA ta fara karatun LAW yayin da ASHRAF ke karatun shi suna kula da Yaron su KHALIFA.









*BAYAN SHEKARU HUD'U*


  *AFTER 4 YEARS*



 Wani Had'ad'en park ne Mai cuke-cuken flowers masu kyau, ga mutane sai harkar gaban su suke, wani Kyakyawan yaro ne d'an kimanin shekaru 5 na gan shi rik'e da Balloons Yana gudu, wata kyakyawar mace ce sanye take cikin riga da wando tasa kayan sanyi a sama Wanda ya Kai har gwiwan ta, kanta tayi rolling d'in veil, sai bin yaron take da gudu so take ta kama shi,



Da sauri yaron ya rungume wani Kyakyawan mutum Yana cewa"help Daddy don't let her catch me"


 ASHRAF kenan Wanda ya d'aga yaron sama, yayin da Kyakyawar macen Nan ta iso wato DEEJA, da Sauri ASHRAF ya tare ta Yana cewa"oh my God why are you running? After you know you're carrying my unborn child"


 Ko kula shi batayi ba sai k'okarin rik'e Hannun KHALIFA take, Nan ASHRAF yace "What's happening?"

 Cikin shagwab'a tace"dukan shi zanyi Allah, Bayan ya shanye min Ice cream na"

Dariya ASHRAF yayi yace"My love stop behaving like baby now, he's our son not your little brother"

 KHALIFA ko gwalo yayi mata, ai ko haushi duk ya cikata Nan ta bar gurin ta nufa mota.



Da sauri suka bi Bayan ta suka Shiga mota suka nufa gida sai tsokanan ta suke.




Suna zuwa gida ta nufa bedroom ta k'yale su, da sauri ASHRAF ya bita  Yana rarrashin ta tare da sanar da ita cikin satin zasu koma Nigeria, habawa ai Nan ta hau murna ta manta da wani fushi da takeyi, ta hau shiri, sai dariya ASHRAF ke Mata.








 









*Ashdee one love*💘



 *TAKU CE💁🏼 UMMU BASHEER*
[06/02 3:41 pm] Ummu Basheer: 🌹 *A KAN K'ANWA TA* 🌹

                   🌹

     { *TRUE LOVE STORY* }



   *NA*

*UMMU BASHEER*


® *REAL* *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
    (We don'nt only entertain and educate,but we touch the heart ❤of reader's📚)_


#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com



 *PAGE* *37~38*


    *Last page*

  
    *THE END*





   *Cikin* satin suka Kamala Shirin su na tafi Nigeria, ASHRAF ya damk'a ma SAIF aminin shi komai na ginin gidan shi, inda aka Gina wani gida mai shegen kyau, duk SAIF ke kula da komai, sai dai su dinga waya da ASHRAF, yanzu an gama komai na gidan, inda Aunty MEERAH da HANA suka je suka k'ara shirya gidan da kyau, Dan Nan su ASHRAF zasu sauka.



 Sun gama shirin su inda ASHRAF ke sanye da suit, DEEJA Kuma tasa wani Arabian gown peach colour tayi rolling d'in veil a kanta tayi kyau sosai, cikin ta Wanda yake cikin na wata bakwai yayi mata kyau a jikin ta, Airport suka nufa inda jirgin su ya d'aga zuwa Nigeria.





 YAYA MALIK  da Aunty MEERAH su kaje har Airport ya d'auko su, cike da farin cikin ganin K'ANWAR SHI, DEEJA na ganin YAYAN TA cike da farin ciki ta rungume shi tsabar murna, ASHRAF ya mik'a mai hannu sukayi musabaha, sannan suka gaisa da Aunty MEERAH, Nan suka shiga mota tare da nufan sabon gidan su.



 Gidan yayi musu kyau sosai, Four bedrooms ne, akwai guest room sai na Yara dana ASHRAF sai na DEEJA, tsarin gidan yayi sosai, har da swimming pool da garden ko'ina grass carpet ne, daga waje Kuma interlock ne, parlour'n babba ne Dan kujeru set biyu aka zuba. Komai white and purple ne, kitchen ma yayi kyau sosai.



Dama already Aunty MEERAH tayi girki ta kawo musu,Bayan an gaisa akayi lunch aka gaisa, sannan suka tafi, Dan sun bar yaran su a gida, yanzu yaran su Aunty MEERAH biyu ne, Akwai little sai Mommy wacce taci sunan Mommy.



The following day


'yan'uwa duk sun zo musu barka da zuwa ga Kuma tayasu murnan sabon gida, ranar sunyi ta bak'i, Matar SAIF ma duk sun zo harda y'an'uwan DEEJA na gurin mahaifiyar ta duk sun zo.


An d'auki tsawon sati d'aya suna fama da jama'a, sannan ne suka je gidan Mommy duk da dama sunje ranar Nan da daddare, Mommy dai sai kunyar DEEJA take domin tasan da ta takura mata ga tsanar da take nuna mata, yanzu Koh har mamakin wayewar ta take da yanda tayi kyau, gashi yanzu ta k'ara girma, tayi wani irin kyau.


Mommy dai ta kasa samun natsuwa sai da ta rok'a gafarar DEEJA, ita ko cewa tayi ai ba komai ya wuce Dan dama ita Bata rik'e ta ba,

Sun yini ranar a gidan sai dare suka koma gidan su.



Bayan sati d'aya aka Fara shirye-shiryen bikin HANA Dan ta samu wani saurayi police ne, suna son junan su har ansa rana an gama komai, biki saura sati d'aya yanzu, sai shirye-shirye akeyi.




Ranar Saturday aka d'aura auren HANAN BILYAMIN da Angon ta ABUBAKAR SADIQ SALEH.


 DEEJA ce a bedroom d'in su nada sai faman shiri take Dan sai yanzu ta samu tayi wanka, Riga da wrapper zani ne akayi Mata but yayi mata k'adan gashi Kuma Ankon biki ne, sai faman turo baki take tana tsaki,


ASHRAF ne ya shigo sanye yake cikin farin shada yayi kyau sosai kamar shine Angon, k'arasawa gurin ta yayi tare da shafa cikin ta yace"Kai do you mean this clothe you're going to wear? Look yanda ya matse min baby"


 Tace"Kuma ni shi Zan sa amma rigar yak'i Shiga"😚

 Rik'e ta yayi ya fara k'okarin cire mata, ture shi tayi tace"nifa ka k'yale ni"😒

. Yace"come-on my love Kinga yanda rigar ya matse min baby kuwa? Gaskiya just remove it"

 Tace"Ankon biki ne fa, please ka bar ni"😫


Dole Haka yasa ta a gaba sai da ta cire kayan tasa wani gown na atamfa blue and silver yayi mata kyau sosai sannan tasa fashion designer na necklace da earrings.


Ranar akayi yini da daddare aka Kai HANA gidan ta, ASHRAF ko yak'i yarda DEEJA ta koma gidan Mommy Nan ya wuce da ita gidan su, sai faman shagwab'a take Wai meyasa zai dawo da ita, shi dai sai rarrashin ta yake domin Daren yau special ne.








Bayan wata biyu DEEJA ta haifa Kyakyawan yaron ta Mai kama da baban shi, ranar suna aka sa mai NASIR, suna Kiran shi da Junior, Haka rayuwa yaci gaba da tafiya cikin kwanciyar hankali.









 *Four years later*




 Wata ce na gani Kyakyawa tana sanye da kayan lawyers, sai murmushi take yayin da ta nufa cikin gidan ta, *Barrister Khadijert Nasir(DEEJA)* kenan wace take a matsayin barrister kenan, lokacin da ta Shiga parlour'n shiru taji ga ko'ina yayi duhu, kasancewar yamma gashi Curtains d'in a sauke ne ga kauri, ajiye handbag d'in ta tayi tana mamakin ko lafiya gidan shiru Bayan lokacin dawowan yaran islamiyya yayi, tsaki tayi a fili tace"Ya Allah, yanzu kenan driver bai d'auko su ba"🤦🏻‍♀

 K'arar fashewar wani abu taji kamar balloon a firgice ta juyawa, Nan haske ya gauraye ko'ina a parlour'n yayin da ASHRAF ya fito shida yaran shi, suna cewa"Surprise"😍

Ajiyar zuciya ta sauke tana cewa" Mai kuka shirya min ne Haka har Kun bani tsoro"

 A tare su kace"Habby Birthday"🎂

 Wani irin farin ciki ne ya rufe ta Dan ta manta yau birthday d'in ta ne, kallon parlour'n tayi ko'ina anyi decorations d'in shi, ga balloons red and white sai gurin yayi kyau sosai.

*Nima ku Taya K'anin BASHEER Birthday ABDUL-K'ADIR yayi shekara d'aya*🎂🍰🍦🍧



 Cikin farin cikin tace"I'm surprised honey, Thanks so much"😍😘


Kiss d'in forehead d'in ta yayi yace"my pleasure baby"😘



 Cake ya kawo inda ta yanka duk tasa musu a Baki, lokacin da tazo ba ASHRAF sai da ya bud'e Baki ta shafa Mai a fuska,😂

Da gudu ya fara bin ta hannun shi d'auke da k'aton cake yace sai ya Rama, sai zagaye parlour'n suke su da yaran su.


What a nice happy Family😍












*Ashdee one love ke muku fatan alkhairi*💘



*Alhamdulillah*

*Alhamdulillah*


 *Anan na kawo k'arshen litafina Mai suna A KAN K'ANWA TA*


 *Ina rok'on Allah ya yafemin kuskuren da nayi a cikin litafin nan, Allah ka raba mu da sharin shaid'an da fad'awa halaka Ameen ya Allah*


 *My fan's where are you, Ina mik'o sak'on gaisuwa na ga dukan massoyana masu karanta novels na, wa'inda ban sani ba da wa'inda na sani, ku sani cewa ni UMMU BASHEER Ina k'aunar ku tare da yin muku fatan alkhairi*



 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

 *Wannan karon nazo muku da sabon salo wato zanyi k'okari Inshallah indinga muku litafi guda biyu a lokaci d'aya, idan Allah ya bani ikon yi zaku jini Inshallah*


*Ku kasance tare Dani a cikin litafaina masu zuwa wato BA MU DACE BA, da Kuma CUTAR KAI*




 *TAKU CE DAI UMMU BASHEER MAI K'AUNAR KU*


Download Akan Kanwata Littafi Na Daya Complete