[07/07, 16:12] Nana Sales Aliyu Fbk Mai Quratu Group: NAGARTA WRITERS ASSOCIATION
*YARIMA FUDHAL*
*©FIDDAUSI S.A*
(QURRATUL-AYN)
01
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM.......!
DUKKAN YABO DA GODIYA SUN TABBATA GA ALLAH MAD'AUKA KIN SARKI MAI KOWA MAI KOMAI.
INA ROK'O AGARESHI YANDA YA BANI IKON FARA LITTAFIN NAN LAFIYA, YA BANI IKON KAMMALA SHI LAFIYA AMIN.
TSOKACI
WANNAN LITTAFIN K'AGAGGEN LABARI NE BANYI SHI DANCIN FUSKAR WANI KO WATA BA, FATANA KAWAI AL'UMMA SU AMFANA DA DARASIN DAYAKE CIKIN SA.
BANYAR DA WANI KO WATA YA JUYAMIN LITTAFINA TA KO WACCE SIGA BA DUK WANDA YA JUYAMIN LITTAFI KO YA CIRE SUNANA ZAN BARSHI DA ALLAH KAWAI.
**********************************
**
Gida ne tamfatsetse mai dogayen katangu da suka sha zane mai d'aukan hankalin wanda yake kallo, hakanne zai baka tabbacin cewa gidan sarauta ne.
Haka kuma girman gidan zai baka mamaki kai kace gari ne guda.
Gidan na d'auke da b'angare guda bakwai, banda filin shamaki da k'afa bata iya kaiwa k'arshen sa.
Soron fada shine soro na biyu a cikin gidan, sai kuma soraye uku da za ka sake wuce wa da zai sa da ka da farfajiyar gidan, a nan ne za ka ga b'angare har guda shida. B'angaren Mai Martaba sai b'angaren Mai Babban d'aki, sannan wajen Matan sarki guda biyu, sannan b'angaren yaransa, sai can ciki kuma b'angaren bayi ne tare da ma'aikatan gidan.
Sai kuma b'angaren kwara-kwaren sarki daban sannan kicin a can k'arshen gidan, sai shamakin doki da shamakin tsakar gida.
°°°°
Gidan ya hargitse baki d'aya, jama'ar gidan sai kai kawo suke daga tsakar gida zuwa sauran sassa na gidan.
Hakan ne zai tabbatar maka da wani muhimmin abu ne yake shirin faruwa a cikin gidan.
"Allah ya taimaki sarki ina mik'o gaisuwa, Yarima Fudhal na kan hanya duk kan jama'ar gari kowa na marhabin da dawowar sa".
Murmushi sarki ya yi wanda ba'a iya ganin sa sabida rawaninsa daya rufe rabin fuskarsa, amma duk wanda ya kalli fuskarsa zai san ya yi farin ciki da jin wannan maganar.
Fadawa suka hau fad'in' "Sarki ya amsa gaisuwa kuma ya yi farinciki da kyakkyawan albishir d'in ka".
Waziri Salmanu ya d'an rusuna gaban sarkin shi ma yana mik'a tasa gaisuwar tare da fad'in' "dole kowa yayi farin ciki ya mai Martaba, domin yau kimanin shekaru goma sha biyar kenan rabon Yarima Fudhal da k'asar nan, gashi kuma yau zai dawo k'asarsa cikin k'oshin lafiya tare da nasarori masu tarin yawa".
Shi ma Fadawa suka amsa masa da' "Sarki ya amshi gaisuwarka ya kai babban waziri ".
Haka dai kowa ya dinga kawo gaisuwarsa Fadawan sarki na amsa masa.
Sarki ya cika da murna da farin ciki ji yake kamar yajawo goben yaga Yarima kuma d'a mafi soyuwa a gareshi.
Mai Martaba Sarki Ubaiyd kenan, ya gaji sarautan a wajen mahaifinsa sarki Salmanu. Shi kad'ai ne d'a a wajen mahaifin nasa bashi da wa ba shi da k'ani. Shiyasa yakeji da iyalinsa sosai musamman Yarima Fudhal wanda yake ganin shi ne magaji a bayan sa.
Sai dai wani abu dake b'atawa mutane rai da Sarkin kuma basu da ikon magana akai shine.
Sarki Ubaiyd ya tsani a fad'i laifin yaransa, shi a ganin sa komai sukayi dai-dai ne.
Domin 'ya'yan sarki ne kuma jikokin sarki 'ya'yan masu fad'a aji a cikin k'asar, a ganinsa kome suke so suyi kuma komai sukai dai-dai ne.
Abin da mutane suka kasa fahimta kenan rashin 'ya'ya da yawane ya sa shi yin hakan, ko kuwa son nunawa duniya yaransa sunfi kowa ne?.
••••••••••••••
Mai Babban d'aki Hajiya Marka mahaifiya ce ga mai martaba sunanta na gaskiya Hauwa'u.
Mace ce kamila mai son addini ga faram-faram da son jama'a, ga kuma uwa uba fad'a aji in dai taja layi a gidan ko sarkin k'aryarsa ya tsallaka balle kuma sauran al'ummar gidan.
Fulani Bingel itace uwar gida a cikin gidan mace mai alkunya da addini da son mutane, tana girmama dukkan mutumin daya girmama ta ba tada wulak'anci ko kad'an gata da son ado. Yaran ta uku, mata biyu an aurar dasu Sadiya da Sa'idah sai autan su Yarima Fudhal.
Sai Fulani Sokoto mace ce fara doguwa mafad'aciya ce tak'in k'arawa. Gata makira tasan luggar tuggu kala-kala, duk bayin gidan suna tsoron ta ainun, domin sarki yana yarda da maganarta d'ari bisa d'ari.
Tana da yara biyu Mace da Namiji Jalil da Jalilah su kad'ai ne yaranta a gidan.
Sai uwar Soro babar kwarkawara ce ta sarki, Sauran kwara-kwaran sarki guda biyu duk babu wadda ta tab'a haihuwa a cikinsu.
************
Kishingid'e take bisa kushin tasha ado kamar babu gobe sark'ar gwal ce dank'areriya a wuyanta hatta warwaro da 'yankunne zuwa zobuna duk na gwal ne. Tana sanye da wani dank'areren less fari da ta d'ora alkyabba bak'a akai.
Gefe guda farantin kayan marmari ne ajiye sai bayi uku mata zaune a gabanta suna mata hira jefi-jefi.
Jakadiyya ce ta shigo da sallamarta ta zub'e bisa carpet tana gaishe ta.
Fulani bingel ta amsa fuskarta cike da annuri tana duban jakadiyya da kanta yake k'asa.
Jakadiyya ta cigaba da magana ba tare da ta d'ago kanta ba'
"Gani Gare ki, naji ance kina nemana ?".
Fulani ta sake fad'ad'a murmushinta, kafin ta bud'e baki ta fara magana' "Inaso a shirya dukkan abinda ya dace domin tarbar Auta na, sannan a canja masa bayi wad'anda ki ka amince dasu".
"Angama ya shugaba ta".
Daga haka Jakadiyya tamik'e ta fice, ta nufi b'angaren bayi domin cika umarnin Fulani Bingel.
Nan da nan ta gama bawa kowa aikin sa, an gyare b'angaren su Yarima tsaf.
An kuma gyare masa d'akinsa duk da cewar baya nan amma d'akin fes domin kullum ne sai an share an goge shi.
"Yanzu Mama wannan Yayan namu na dawowa Sarki zai daina bi takanmu fa, baya nan ma ya aka cika bare kuma ya dawo".
Cewar Jalil kenan yana kishingid'e a gefan mahaifiyarsu.
Yaro d'an kwalisa kenan mai shekara ashirin da bakwai a duniya. Jalila dake kwance kan cinyarta taci gaba da fad'in' "ai ina jin ma mance zai yi muma 'ya'yansa ne, gaskiya Fulani ta cuce mu wallahi da take k'ok'arin rabamu da mahafinmu".
Fulani sokoto ta d'an tab'e baki tare da murmushi tana shafa kan d'iyar ta ta.
"Haba dai ita d'in me?, ai ko tana yawo da guraye k'aryarta ta rabaku da mahaifinku ku dai ku zuba ido ba ga ni ba?".
Sallamar d'aya daga cikin bayin gidan ne ya katse su daga tattaunawar da suke.
Baiwar ta fad'i gaban Fulani sokoto tayi gasuwa tana fad'in'
"Da girman kujerar ki uwar magajin gobe, hak'ika na jiyo wani batu mafi girma!".
Fulani sokoto ta mik'ar da Jalila da ke kwance bisa cinyarta tana duban Baiwar ta ta domin jin batun da tazo mata dashi.
"Ina jinki Ladidi".
"A gafarce ni Uwar Magajin gobe, albishir mafi muni ne ke tafe da ni, Fulani Bingel ta saka Jakadiyya ta canjawa Yarima Fudhal bayi,
bayan duk mun gama shirin mu a kan tsofaffin bayin nasa".
Fulani Sokoto rik'e kai kawai tayi ba tare da ta iya cewa komai ba tsabar takaici, ta yiwa Ladidi nuni da hannu akan ta tashi tafita, nan da nan Ladidi ta mik'e ta fice jiki na b'ari.
"Yanzu Mama meye abin yi?".
Jalila ke tambayar Fulani Sokoto da k'yar ta iya bud'e baki ta ba ta amsar.
"Zan yi tunani akan haka".
Ta mik'e tayi cikin d'akinta ta barsu nan cikin falon na ta.
*****
Jakadiyya ta sa aka jere mata 'yan matan bayin gidan kaf ta gama duba su duk ciki ba su yi mata ba kuma bata amince dasu ba, hakan yasa tace musu kawai su cigaba da aikinsu, ita kuma ta koma b'angaren Fulani Bingel.
Da shigarta ta fad'i a gabanta tana fad'in.
"Ayi hak'uri a gafarce ni na duba duk kan bayin babu wanda su ka yi, da za'a bani dama zuwa gobe da k'arfe bakwai sai a sake d'iban sabbin Bayi kafin zuwan Yarima".
"An baki dama, kiyi duk kan abinda ya dace".
"Nagode kwarai da gaske". Jakadiyya ta mik'e ta fice.
*UNGUWAR KWARI*
Unguwace da mutane da dama su ke mata ik'irari da unguwar talakawa.
Domin a ganin su babu unguwar da ta kai yawan miskinai da gajiyayyu a cikin fad'in garin kamar Unguwar Kwari.
Unguwace mara tsarin gidaje ga tarkacen bola kala-kala a cikin unguwar layi-layi, gidajen duk na k'asa mara sa kyan gani.
Amma duk da katutun talaucin da ya yiwa unguwar yawa hakan bai hana a samu wad'anda suke neman nakansu da guminsu ba. Duk da wasu jama'a nawa unguwar lak'ani da unguwar k'azamai hakan bai sa an rasa masu tsafta cikin su ba sabida ba duka aka taru aka zama d'aya ba.
Gidane na k'asa wanda katangarsa iya rabi ce kana iya hango dukkan abinda mutanan gidan suke yi a tsakar gidan.
Gidan na d'auke da d'akuna biyu kacal, sai kicin da wani kwarab'abb'an band'aki da yasha tsimmokara kala-laka domin kariya.
Gidan tsaf dashi an share shi tas ko ba tabarma sai mutum ya zauna duk da turb'ayace a k'asan.
Wata 'yar dattijuwar mata ce zaune bisa ledar buhu a tsakar gidan da sanda a gefanta.
Idanuwanta a rufe wanda shine zai baka tabbacin makauniya ce, magana take yi cikin d'aga murya'
"Aynu! Ke Aynu!! wai mai kike yi a cikin d'akin ne haka?".
Dattijuwar ke ta b'ab'atu bakin k'ofar d'akin da take zaune.
Gidan shiru kai kace sambatu take babu kowa a gidan, can aka d'ago yagaggen zaninda a ke rufe k'ofar d'akin da shi da sunan labule.
Wata 'yar budurwa ce da shekarunta ba zasu wuce goma sha biyar zuwa da shida ba ta fito da ga cikin d'akin. Tana sanye da wata kod'add'iyar atamfa da ba za ka iya tan-tance kalar taba bare ganin zananta, hijabin jikinta bak'ine amma ya zama ja tsabar dad'ewa da gajiyar wanki da rana.
Fuskarta watsai bak'ace amma ba can ba, tana da manyan idanuwa da gashin ido dana gira zara-zara, sumarta har kusan girarta hakan ne zai saka kasan tanada yawan gashi sai pink lips d'inta, duk da bak'ace. Amma leb'anta pink a tak'aice dai kallo d'aya ba zai sa ka fahimci kyawunta ba.
Wato dai tana da wani sihirtaccen kyawu na ban mamaki da ba kowa ke iya sanin hakan ba.
"Gani Ummata ina shiryawa ne fa, mai zan siyo miki?". Tayi maganar cike da shagwab'a.
Murmushi Umman tata tayi, tana mai mik'o mata wata duk'unk'unanniyar Naira hamsin "Ungo Aynu maza je ki kisiyo mana garin kwaki da sugar musha, nasan baki karya ba ko?".
"Ehh Ummana bari in je in dawo to".
"To ki dawo lafiya akula da hanya".
"Amin". Aynu ta amsa tana mai sanya wani talitsattsan silifas da k'iris ya rage ya hudo k'asa ta sanya ta fice tana 'yan wak'e-wak'enta.
Awaje taci karo da wani mutum dake jingine jikin wani icen dalbejiya, bai da k'afa d'aya sai guda d'aya yana
dogarawa da sanda.
Durk'usawa tayi har k'asa na ji tana fad'in' "ina kwana Baba?".
"Lafiya k'alau Aynu, kin tashi lafiya?".
"Lafiya k'alau Baba, Ummata ta aikeni ne".
"Ki dawo lafiya a kula da hanya". Cewar Baban nata kenan. Ta mik'e ta ci gaba da tafiya abinta.
[07/07, 16:13] Nana Sales Aliyu Fbk Mai Quratu Group: *YARIMA FUDHAL*
NAGARTA WRITERS ASSOCIATION®
©FIDDAUSI S.A (QURRATUL-AYN)
02
Mintuna kad'an da fitar ta sai gata ta dawo hannunta rik'e da leda bak'a k'arama, da sallamarta ta shigo cikin gidan Ummanta dake zaune bakin k'ofa kamar yanda ta fita ta barta ita ce ta amsa mata sallamar tana fad'in.
"Har kin dawo Aynu ?".
"Ehh Ummata kinsan shagon Malami babu nisa ai".
"To dauko kwano ki jik'a sai ki d'ibarwa Babanki ki d'ibi naki".
"To Ummata".
Ta amsa tana mai shiga cikin d'akin na su, sai gata ta dawo hannunta rik'e da babban kwano da kofuna guda uku.
Ta juye garin a cikin kwanon taje ta zuba ruwan da ta d'ebo tun asuba dake basu da ruwa sai asuba famfon unguwarsu yake zuwa.
Ta d'auraye garin sannan ta sake zuba ruwa ta dawo ta zauna ta dauki sugar ta sanya a ciki ta juya, ta zubawa Ummanta ta mik'a mata sannan ta sake zuba wani ta d'auka ta kaiwa Babanta d'akinsa yana kwance ta shiga da sallamarta yamik'e ya zauna yana amsa mata sallama.
Durk'usawa tayi ta ajiye masa kofin garin tana fad'in.
"Baba gashi inji Umma".
"To sannun ki nagode sosai Allah muku Albarka !".
"Amin".
Ta amsa tare da mik'ewa ta dawo tsakar gidan inda Ummanta take ta zauna gefan ta tare da janyo ragowar garin ta hau sha.
YAMMACIN RANAR
Da yamma sai da ta kammala komai da zatayi a gidan, sannan tayi shirin islamiyya tayiwa Ummanta sallama ta tafi.
"Assalamu alaikum mutana nan gidan nan?".
Wata mata 'yar dattijuwa take ta kwad'a sallama cikin gida.
"Amin wa'alaikissalam Tasalla kece a gidan namu?, Bismillah shigo".
Umma ta amsawa matar sallama tana daga cikin d'aki.
Matar ta shiga d'akin ta zauna bisa 'yar guntuwar katifar dake yashe tsakar d'akin da bata da maraba da tabarma.
Suka gaisa da Umma tamik'awa Umma bak'ar ledar da ta shigo da ita tana fad'in.
"Gashi Umman Aynu dama abinci ne na kawo muku".
"Amma kuwa mungode Allah ya saka da alkhairi kamar kinsan tun safe Aynu ba taci komai ba wallahi, yarinyar nabani tausayi sosai k'arama da ita amma tana fuskantar gararin rayuwa !?".
"Haba Umman Aynu !, kada kice haka mana !, ko wanne bawa da irin jarabtarsa arayuwa, barema yau ina tafe da kyaky-kyawan albishir gareku ina kyauta ta zaton wasu matsololin naku zasu kau".
"To Allah yasa Tasallah wanne albishir ne haka?".
"Wato gidan Sarkin da Zainabu tawa take aiki zasu d'auki sababbin ma'aikata shine nake ganin mai zai hana Aynu taje ko Allah zai saka a dace".
Umman tad'an jin jina kai kafin tace.
"Anya kuma?, nifa kin san bana son abin da zai saka inyi nesa da Aynu ko kad'an".
"Ki yarje mata tayi aikin nan domin zaku samu alkhairi aciki, duk wannan abincin da ki kaga ina kawo muku daga gidan Zainabu ke zuwa dashi, bayan haka kuma ga kud'in da ake biya duk wata".
"To zan duba ingani Allah yasa a dace".
Cewar Umma kenan, Tasallah ta dubeta karo na biyu.
"Bawai zaki duba ba amincewa zakiyi domin nasan Babanta bashi da matsala akan hakan !, nazo miki da wannan maganar ne sabida ina da yak'inin zaku samu sauk'in rayuwar data tsananta a gare ku ne".
Tayi shiru domin taji ko Umma za tace wani abu, jin da tayi ba tace komai ba yasa ta cigaba da magana.
"Sannan aiki a gidan ya dan ganta da b'an garen da kake aiki, kinga Zainabu Fulani Bingel takewa aiki albashinta dubu goma sha biyar ne, wad'anda ke aiki b'angaren Fulani Sokoto suna d'aukan Dubu goma, to kinga ko dubu goman ne ina laifi a wajen wanda baya dashi?".
"Kinsan Jakadiyyar gidan Yayar Babar muce, shi ya sa ban ji komai ba nakai Zainabu aiki gidan sabida tana da kirki wallahi baza tab'a bari wata b'araka ta b'ullo ta gefen suba".
"Hakane Tasallah !, bari Aynu tazo sai muyi maganar, mu ko b'angaren dubu goman ta samu Allah yasa masu albarka".
"Amin, haka ya kamata kice ai".
Nan suka cigaba da tattau nawa kafin Tasallah tayiwa Umma sallama tana fad'in.
"Idan ta amince zatayi ki turota da safe kamar shida da rabi domin anaso bakwai tayi musu acan".
"Insha Allah zatazo kin san Aynu akwai himmar sammako ai".
Suka sanya dariya ta fice daga gidan, tabar Umma nan zaune tana tunani.
Batafi mintuna talatin da tafiya ba Aynu tayi sallama da sauri ta shigo gidan ta ajiye jakarta tayi maza tad'auki buta ta shig e band'aki mintuna biyar tafito ta shiga cikin d'akin ta tadda Ummanta zaune tana lazimi, Aynu ta zauna gefanta tana fad'in.
"Sannu da gida Ummata".
"Yauwa Aynu kin dawo lafiya ko?, fatan anyi karatu da yawa?".
"Lafiya k'alau Ummata, nayi karatu sosai kuwa".
"Masha Allah a dage sosai".
"Insha Allahu Ummata".
"Duba cikin kwanun da ke can rufe akwai abinci ki d'auka kici".
"To Ummata".
Tamik'e ta dauko ta zauna har tasa hannu zata fara ci sai kuma ta dubi Ummanta ta da tambayar.
"Umma kinci abincin kuwa?".
"Ehh naci 'yar gidan Umma, har Babanki shima yaci wannan nakine kici abinki".
Aynu tasa hannu ta ci gaba da cin abincin ta.
"Ummata waye da aikin ladan nan haka?".
"Kema ko ba'a fad'ab ba kinsan wace ai, Tasallah ce Babar Zainabu ta kawo mana d'azu".
"Amma Umma babu abinda zamuce da Maman Zainab sai dai Allah yasaka mata kawai".
"Amin dai, yauwa inkin gama inason magana da ke".
"To Ummata nagama ai, bari in wanko hannuna".
Tafice daga cikin d'akin hannunta rik'e da kwanun data gama cin abincin.
[07/07, 16:15] Nana Sales Aliyu Fbk Mai Quratu Group: *YARIMA FUDHAL*
NAGARTA WRITERS ASSOCIATION®
FIDDDAUSI S.A (QURRATUL-AYN)©
03
Notes...............kuyi hak'uri nayi mistake a page 1 MAI BABBAN D'AKI ita ce mahaifiiyar Sarki, UWAR SORO babbar kwarkwara ce, Zakuga nasake post nashi na gyara ne.
*** *** ***
Ta wanko hannunta ta dawo ta zauna kusa da Ummanta, Ummanta ta kamo hannunta tarik'e kafin ta fara magana.
"Aynu !, kiyi hak'uri abisa yanda kika tsinci kanki a rayuwa, ki sani komai yake faruwa da bawa haka Allah yatsara masa tun kafin zuwansa duniya, nasan ke mai hak'uri ce Aynu, ina rok'anki ki k'ara akan wanda kikeyi, domin bahaushe na cewa mahak'urci mawadaci, nasan wata rana sai labari".
Ta danyi ajiyar zuciya na wani lokaci, kafin taci gaba da magana.
"Mahaifinki shine ya hanamin fita neman na kaina, a cewarsa bazanyi bara ba, kamar yanda shima bazaiyi ba, amma kuma duk wani hanyar samunsa ta kulle, gashi ni bana da ido bare inyi koda sana'ar k'arfice a gida, yau Tasallah tazomin da batun idan mun amince zata kaiki gidan sarki aiki, ana samun abinci sannan da albashi duk wata".
Murmushi ne ya sub'ucewa Aynu duk da 'yar kwallar dake saman idonta, tarik'e hannun mahaifiyarta ta k'am tana fad'in.
"Amma kun amince ko Ummata?, dannima ba nason bara wallahi gara nayi ko wanne aiki indai za'a biyani mu amfana".
Ummanta itama murmushin tayi.
"Ya zamuyi Aynu?, ai dole mu amince sabida bamu da wani zab'i daya wuce amincewar tamu".
"Kai amma naji dad'i Ummata kinga yanzu zamu samu kud'i mud'inka kaya musayi ta barma da katifa da takalmi, sannan kuma ga abinci, yanzu bamu ba yunwa ko Umma?".
"Uhmmm Aynu kenan, sarkin buri arayuwa Allah dai ya warware mana !".
"Amin Ummata".
Daga haka suka cigaba da hira, Ummanta tanayi mata nasiha akan ta kula da kanta tayi biyayya kada tayi abinda za'a tsa neta ko ta b'atawa wani rai, sannan ta gargad'e ta akan ta zama mai hak'uri a duk inda tasamu kanta.
WASHE GARI....!
Washe gari tun asuba Aynu ta tashi tayi sallah tad'ebo ruwa ta cika gidan, tayi dukkan aikace-aikacen data saba kullum, tazo ta zauna gaban Ummanta ta gaisheta taje ta gaida Babanta ta dawo ta zauna tana jiran gari yad'anyi haske ta fita, domin babu agogo a gidan nasu.
A nanma nasihar Ummanta tayi ta mata, kafin tayi mata sallama ta lek'a d'akin Baban nata tayi masa sallama shima ya biyota da addu'a ta fice daga gidan.
Yau wani nishad'i ta keji arayuwarta domin ita dama burinta na rayuwa bai wuce yanda zata taimaki iyayenta ba, wad'anda sukai d'awainiya da ita tun tana cikin ciki, duk da gararin rayuwa da taulacin dasuke fama dashi amma hakan bai hana musu ganin sun kyautata mata ba, sai taci kafin suci, sai ta sha suke sha, intayi kuka suyi kuka idan tayi farin ciki suyi farin ciki, ba dan yanda rayuwa ta juyewa mahaifinta ba tasan bazai tab'a bari taje wani guri aikatau ba, tasan iyayenta sun sota arayuwa to itama meyesa ba zata kyautata musu ba?.
Haka ta isa gidan Babah Tasallah tana sak'e-sak'e cikin ranta, da sallamarta ta shiga gidan, Zainabu dake shara ta amsa mata sallamar tana fad'in.
"Uwar 'yan sammako k'arfe shidda fa? Amma har kinzo!".
Aynu tayi murmushi ta bata amsa da fad'in.
"Amma aikin san da zafi-zafi akan daki k'arfe".
"Da gaskiyarki 'yar gidan Umma".
Babah Tasallah ta fad'a tana mai fitowa daga d'akinta, Aynu ta d'urk'usa ta gaisheta ta amsa fuskarta fal murmushi tana tambayarta ya ta baro Ummanta ta, Aynu ta bata amsa da.
"Lafiya k'alau take, tace ma agaishe da ke".
"Ina amsawa, shiga d'akin ki zauna kafin da rabin tayi".
Aynu ta shiga ta zauna, Zainabu ta gama shara ta kawo musu abin kari koko da k'osan da Babah Tasallah tayi tun asuba, suka karya dan kada su tafi da yunwa.
6:30.
Shida da rabi dai-dai suka isa gidan Sarkin tun awaje Aynu ta saki baki tana kallon girman gidan da tsaruwarsa, sabida ita ba ta yowa nan haka, to mema zai kawota tunda ita dai bayawo take ba, Zainabu ma tayi nacin suzo tak'i zuwa sai yau da aiki yakawota.
Bata k'ara tsinkewa da al'amarin gidan ba sai da suka shiga soron fad'a anan ta sha kallo kafin su wuce zuwa ciki gidan, nan kuwa mutuwar tsaye takusa yi, aranta tana fad'in.
"Dama akwai masu irin arzik'inan aduniya?, Allah yabasu kud'i da mulki amma basu damu da talakawansu ba".
"Ke Aynu!, me kike kallo ne? ki nutsufa, duk abinda kika ga munayi kema kiyi".
Cewar Zainabu kenan tana mai tab'ota, domin taga tad'daga kai sama tasaki baki tana kallo.
Wajen Jakadiyya suka wuce kai tsaye, suka gaisheta anan suka tadda 'yan mata guda hud'u a tare da ita, 'yan matan suka hauyiwa Aynu wani kallom gani-gani kamar sun ga kashi, ita dai hankalinta yana ga kallo, bama tasan sunayi ba.
"Ga yarinyar da nake fad'amiki, 'yar gidan Malam Nasiru gurgu ce".
Babah Tasallah ta gabatar da ita wajen jakadiyya.
Jakadiyya ta k'arewa Aynu kallo kafin tace.
"Allah sarki ! Yarinya k'arama da ita kuwa, Allah yasa dai ta samu domin mutum uku ake buk'ata kuma kinga ga guda hud'u sun zo tun d'azu, ban zaci zaki kawo taba domin kina k'ila wa k'ala akan zuwan nata, amma dai bari inkaisu wajen Fulani Bingel itace zata zab'a".
Babah Tasallah tace.
"Amin dai insha Allahu zata samu".
Aynu kuwa jin ance Allah yasa ta samu tuni 'ya'yan hanjin cikinta suka murd'a gabanta yahau bugun sha uku-uku.
Jakadiyya dai ta d'ebesu su biyar suna binta abaya har b'an garen Fulani Bingel, Aynu har tuntub'e take tsabar kallo.
Suna shiga Jakadiyya ta zub'e gaban Fulani, suma sukayi yanda tayi suka kwashi gaisuwa, Aynu ta d'ago kai tana duban Fulani mace kyakykaywa mai haiba tasha ado da wani light blue d'in leshi dayasha adon stone...., jitayi an mintsineta ta gefanta dayake tana kusa da Jakadiyya tajuyo taga dukkansu kowa kansa ak'asa itama ta duk'ar da nata.
"An samo guda biyar duk da uku ake da buk'ata sai a azab'a ko?".
Fulani ta gyad'a kai, tare da bada umarnin duk su mik'e tsaye, ba musu suka mik'e kansu duk a k'asa, ta bisu d'aya bayan d'aya da kallo, kafin tace ta gefan Aynu tayi gefe, sannan ta kuma zab'ar wata guda d'aya, yarage saura mutum d'aya ke nan?.
Jikin Aynu sai rawa yake ta tsananta addu'a sosai Allah yasa azab'e ta cikon ta ukun, domim sungama sa rai akan wannan aikin.
Cikin ikon Allah akace Aynu ta koma cikin mutum biyun da aka fara zab'a, tuni ta saki wata nan-nauyar ajiyar zuciyar.
"Wad'an nan ukun sunyi, biyun ki kai su kicin suyi aiki acan, ku kuma koware kanku".
Ko wacce ta tsaya ita kad'ai aka nuna ta farko.
"Kece zaki dinga kula da abincinsa, wannan kuma ta kula da sharan falo da goge-goge, sai ke !".
Akayi nuni da Aynu, gabanta yafad'i, tana jiran taji mai za'ace.
"Wannan yarinyace shiyasa nazab'eta, ke zaki dinga kula da gyaran d'akin kwanansa, ki kuma tsaftace band'aki ko da yaushe, sai kije ki basu kayan da zasu saka ku jira zuwan Yarima domin yana hanya anje tarbarsa".
Jakadiyya tazube agaban Fulani tana fad'in.
"Angama Fulani".
Muma muka zube tare dayin yanda tayi, muka mik'e da baya da baya muka fice, ashe wai ba'a juya musu baya sai mutum yaje bakin k'ofa, araina nace ikon Allah wani abun sai gidan sarauta.
Da murnata muka isa inda mukabar su Babah Tasallah nasanar musu an d'aukeni, suma sunyi farin ciki sosai, Babah Tasallah tayiwa Jakadiyya sallama ta tafi gida, mu kuma akayi wani d'aki damu.
Muna shiga nan naga abin mamaki, d'akine ciki da falo shak'are da kaya kala biyu pink da blue sai kace a shago, nan akace mu d'auki blue set biyu tare da abin wuya murjani da abin hannunsa da 'yan kunne.
Jakadiyya tabarmu cikin d'akin muka sanya kayan, kayan kuwa da Jakadiyya ta nunawa kowa yad'auka dai-dai jikinmu kamar angwada.
Muka fito d'as damu kowa duk inda muka wuce sai kallonmu ake, ban saniba kyau mukayi ake kallonmu ko akasin haka?.
Mai makon mu koma cikin gidan sai naga kowa yana fita waje anjeru tun daga bakin k'ofar shiga gidan har zuwa soron fada, ashe pink d'in unifoam na b'angaren Fulani Sokoto ne, b'angaren Fulani Bingel blue, sai naga maza sunyi nasu layin mata ma haka, Allah ya taimake ni na tsaya kusa da Zainabu, mintuna kad'an da tsayuwarmu aka buga wata uwar bindiga data sanya 'ya'yan hanjina kad'awa, na dank'e hannun Zainabu k'am, ita kuwa tana tamin dariya tana fad'in.
"Sarkin tsoron tsiya".
K'asa-k'asa take maganar da dariya.
Ana gama buga bindigar kuma sai ga jiniyar kwanon motoci tana tana kawo kai.
[07/07, 16:15] Nana Sales Aliyu Fbk Mai Quratu Group: *YARIMA FUDHAL*
NAGARTA WRITERS ASSOCIATION®
FIDDAUSI S.A (QURRATUL-AYN)©.
04
•••
Sarki ne da muk'arrabansa suka fara sau kowa fadawa suka ke wayesu suna yi musu kirari.
Babban abinda yabani Mamaki ya kuma d'auremin kai, shine sauran fadawan da suke tsaye bisa layi sai naga kowan ne mutum ya kwanta bisa cikinsa, Sarkin yataka yabi takan bayansu, har sai da yashiga cikin fada, suka mik'e suka kewayeshi yazauna bisa karagarsa, sanna suka dawo suka tsaya jiran fitowar yarima.
Ya ziro k'afarsa guda d'aya sai da yad'au mintuna sama da biyar kafin ya sake ziro d'aya k'afar cike da izza da k'asaita yafito yanda mahaifinsa yayi shima haka yayi takan bayan bayin fada yabi.
Sai da yashiga soron fada shima sannan sauran 'yan uwansa mata masu aure da su Jalil da Jalila suka fito suma suka nufi fada, amma su bata kan mutane suka bi ba.
Ni kuwa abin ya tsaya min arai sosai, haka muka juya muka nufi cikin fadar zuciyata cike da wasi-wasi da ko kwanton al'amura na wannan masarauta, na fahimci wani abu guda d'aya ga masarautar tun yanzu, wato dai basu d'auki wani talaka abakin komai ba.
Sai da yarima yayi gaisuwa ga mahaifinsa Sarki Ubaiyd ya rungume d'an nasa cike da so da k'auna, kafin yamik'e yashige cikin gidan mu kuma mu da wasu mazan fada muka take masa baya.
Kai tsaye wajen Mai Baban d'aki muka nufa wato mahaifiyyar Sarkin kuma Kaka a wajensu Yarima, nan muka zube tsakar d'akin tana zaune abinta tasha irin shigarnan ta mutan da wadda suke kira da suna b'anti-b'anti, asa riga a d'aura zani har saman k'irji sannan a kawo wani zanin ad'aura k'asan wanan zanin, abun hannu da na wuyanta duka azurfa ce, mace mai fara'a, anan sun shafe kusan awa guda suna gaisawa cike da barkonci, kafin su fito su nufi b'angaren Fulani Sokoto.
Fuskarta wasai ta karb'esu, har da rungume Yarima wai sabida murna, muma kanmu dake sabbin zuwa ne mund'auka da gaske tana farin ciki da dawowarsa sab'anin yanda sauran mutan gidan suka sani.
Muka fito muka nufi b'angaren Fulani Bingel wato mahaifiyarsu Yarima Fudhal.
Muna shiga muka zube muka sake d'iban gaisuwa, ni kuwa da man nagaji da tsayuwa ina zama sai naji wata rahama ta ziyarce ni, musamman da naga sunyi kaman basu san muna wajen ba, araina nace.
"Ma huta ma wannan azaba har ina ?, da man haka aiki yake a gidan saraunata?".
Sun shafe kusan a wanni biyu suna gaisawa, suna hira cike da so da k'aunar tare da murnar dawowarsa lafiya, amma shi abin mamaki wayarsa ce a hanunsa yana danna-dannesa.
Sai idan sun tambayeshi abu ya basu amsa da ehh ko a'a, amsar bata wuce haka abin ya bani mamaki sosai, na lura su basa damuwa darashin ko inkula d'insa, ko haka halinsa yake? Oho.
Mik'ewa yayi alamun yana buk'atar yaje ya huta sukayi sallama, mu kuma muka dafo masa baya muka fito.
Yana shiga part d'insa yayi kwanciyarsa bisa lallausan carpet d'in dake shinfid'e tsakar d'akin ya ta da kansa da kusun, Jakadiyya ta zube a gabansa tana fad'in.
"Fulani taba da umarnin canja maka bayi, gasu nan guda uku".
Ta nuna ta farko.
"Wannan sunanta Naja'atu, wannan kuma Saima".
Sannan ta nuna ni.
"Ita kuma wannan Aynu, sune zasu dunga kula da nan wajenka yanzu".
Idanmu da muke tsaye munyi magana to shima yayi magana, ko d'ago kai bai yiba bare ma yasan suwaye ke zaune awajen, kawai danna-dannenta yake abinsa a wayarsa mai kama da littafi danni banko tab'a ganin irin taba sai yau a hannun yarima.
Jakadiyya bata damu da amsawarsa ba ko rashin ta, ta dubemu tana fad'in.
"Ku biyoni muje".
Muka fice da sauri muka bi bayanta, kicin muka nufa kai tsaye aka mik'o mana tire guda uku manya ko wacce a cikinmu ta d'auki d'aya, Naja tad'auki mai kuloli manya, Saima ta d'auki mai k'ananun kuloli da flat -flat da kofuna akai, ni kuma aka bani mai kayan mar-mari aciki (Fruit).
Muka d'auka muka kai d'akin Yarima yana nan inda muka barshi, muka ajiye a gefensa Naja tad'auki flat ta zuba masa wani had'ad'dan farfeson kayan ciki, sannan ta zuba soyayyar hanta a cikin wani flat da ban, ta sake d'auko flat ta zuba masa da faf-fan naman kai, sannan ta koma gefe ta zauna.
Ita Kuma Saima a she duk kulolin data d'auko dambun nama ne aciki kala-kala ta zuba masa itama ta koma gefe.
Ni kuwa nayi diri-diri na rasa ya zanyi masa da kayan fruit d'in dana d'auko, na dubi su Naja naga ko kallon inda nake basuyi ba, na d'ago ka na dubi Yarima, da niyyar tambayarsa gabana yayi wani mummunar fad'uwa, sai a lokacin naga irin tsan-tsar kyawun da Allah ya zuba masa, domin duk shige da ficen da muke kai na ak'asa yake ban yarda ko kad'an na kalleshi ba.
Farine amma ba can ba mai matsakaicin tsayi ne, sumarsa bak'ace har zuwa sajensa da gashin baki, yana da manyan idanuwa mai cikar gashin girane daka ganshi zaka san ma'abocin son k'amshi da tsafta ne kuma masoyin son ado ne, zan iya cewa yafi kama da Fulani Bingel domin kamanninsa da ita sunfi fitowa fili mutum ne mai haiba da kwarjini sosai.
Da sauri na mai da kaina k'asa nafasa tambayar tasa, nima na koma gefe kamar yanda naga su Naja sunyi.
Mun shafe wajen mintuna talatin a zaune har zaman yafara gundura ta, sannan naga yamik'e ya zauna, yajawo flat d'in farfeson kayan ciki, Naja tamik'e da sauri ta d'auki Spoon ta mik'a masa yasaka cokalin a hankali ya d'ebi kad'an yakai bakinsa, ya hau taunawa kamar mai cin magani, ya ture gefe haka yayi ta bin farfesun ko wanne flat cokali d'aya ya keyi ya ture, kafin ya koma kan dambun daman shinema naga yad'anyi cokali uku zuwa hud'u, ya ture su gefe ya k'urawa kayan marmari ido na wani lokaci can yaja tsaki, sai jin kakausar muryarsa mukai ta daki kunnuwanmu .
"Wace takawo kayan fruit?, Je ku kiramin Jakadiyya".
Yayi maganar kamar mai koyan magana, kuma umarni da tambaya duk a lokaci guda, hanjin cikina naji yak'ulle cike da tsoro na k'arasa inda yake na durk'usar.
Mai makon yasake magana sai gani nayi yamik'e tsaye, ban zata ba sai ji nayi ya jefe ni da tire d'in kayan marmarin duk sukayi kaca-kaca afalon Allah yasoni babu wanda ya tab'a jikina, amma duk da haka na takure waje d'aya jikina nab'ari.
Jakadiyya ta shigo da saurinta ta durk'usa tana nema min afuwa, nima ganin yanda tayi yasa nima na durk'usa kanmu a k'asa muka fara neman yafiya.
Bai ce komai ba ya shige cikin d'akinsa kawai ya barmu nan zaune.
Cike da tsoro namik'e nahau tsince kayan marmarin, Jakadiyya tace insameta b'angaren Shamaki, suka fice ita dasu Saima suka barni, nan da nan na share wajen na gyare tsaf, sannan natafi filin shamaki.
Nan na iske sauran ma aikatan gidan wasu na aiki wasu na hirarsu ciki har da Jakadiyya, naje inda take na durk'usa ta dubeni kafin ta fara magana.
"Mai kika yiwa Yarima?".
Nan na bud'e baki na bata bayanin dukkan abin da yafaru, shiru tayi nad'an wani lokaci kafin ta cigaba da fad'in.
"Idan aka kai kayan marmari yayyan kawa ake a ajiye a gefen su, wani lokacin kuma a hannunki zaki rik'e kina yankowa kina mik'a masa yana ci, idan abinci ne zubawa zaki ki ajiye masa ki zauna gefe har saiya gama ci wannan aikin su Naja ne, sannan dole ki dinga zuwa da wuri kamar k'arfe bakwai na safe ki gyare ko ina na d'akinsa ki share, ki wanke toilet tsaf ki saka turare, idan ya shiga wanka kafin ya fito ki gyare gado da d'akin ki kunna turaren wuta, amma ke aikin ki uku ne wanke toilet d'innan da share cikin d'akin, sannan ki kai masa dukkan abin da yake da buk'ata ina fatan kin fahimce ni".
Kai kawai na gyad'a mata domin nakasa magana, ta mik'omin wata leda viva tana fad'in.
"Ingo naki abinci kije gida, gobe kizo da wuri".
"To nagode".
Nafad'a ina mai mik'ewa na baro shamaki na nufi d'akin da muka canja kaya na d'auko kayan dana cire tare da set gudan na unifoam d'inmu.
Zan fito daga gidan kenan muka gamu da Zainab zata tafi gida ita ma da murnarta ta tarye ni muka fito tana fad'in.
"Ashe baki tafi ba?, naga farkon zuwa ana tafiya da wuri?".
"Uhmm ke dai bari ! ai Allah ne ya tarfawa garina nono dan da tuni ankore ni".
"Subhnallah ! garin yaya?".
Zainab ta fad'a tana mai zaro ido waje.
Nan dai na bata labarin abin da ya faru, ta d'anyi shiru kafin tace.
"Sai kiyi hankali sosai da taka tsan-tsan, mancewa nayi wallahi inyi maki bayanin ayyukan gidan, amma yan zuma bari infad'a miki tun da Allah yarufa mana asiri ba'a kore kiba".
Muna tafe tana yimin bayani har muka iso dai-dai layin mu mukayi sallama na shige gida ita kuma ta wuce zuwa gidan su.
Ina shiga Ummata ta tarbe ni cike da murna nan na zauna inata zuba mata labarin gidan sarki, ita kuma ta nata gargad'ina inkula sosai inyi abinda ya kaini ka wai ban da sha shanci, har dai da taji batun b'angaren Yarima zan dinga yin aiki, taji kuma irin tsarin aikin nawa, nan dai tayi tamin nasiha ban sanar mata abin da ya faru ba ko kad'an nayi shiru da bakina a ganina ba abin da zan sanar mata bane.
Na dauko kwanuka na juye abincin dake cikin ledar sai naga dukkan abincin da muka kaiwa Yarima ne, nan muka baje muka kwashi gara cike da farin ciki har na mance rabon da tsokar nama ta shiga baki na, Baba na dawowa na kai masa nashi abinci yakarb'a yaci yana ta samin albarka.
[07/07, 16:16] Nana Sales Aliyu Fbk Mai Quratu Group: *YARIMA FUDHAL*
NAGARTA WRITERS ASSOCIATION®
FIRDAUSI S.A (QURRATUL-AYN)©
05
*WASHE GARI*
Washe gari ma tun da na tashi da asuba ban koma ba, nan da nan nayi dukkan abin da na sabayi kullum sannan na d'umama mana ragowan abincin da nazo da shi jiya, naci na barwa su Ummata sauran.
6:30am
K'arfe shida da rabi agidansu Zainabu tamin, ko da nazo ta gama shiryawa itama tana jira na muka yiwa Babah Tasallah sallama muka tafi.
Muna isa gidan da Jakadiyya muka ci karo tana ta zirga-zirga, muka gaisheta ta amsa tana k'ara gargad'ina akan inkiyaye sosai nace.
"To insha Allah".
Muka wuce Zainabu tayi b'angaren Fulani Bingel ni kuma nayi b'an garensu Yarima da yake b'angaren Yarima Fudhal dana Jalil a had'e suke daga ciki ne aka rabasu amma k'ofar falon ko wanne d'aki tana kallon d'ayar.
Da sallamata na shiga falon babu kowa ciki sai k'arar fanka da Tv kawai ke tashi.
Na nemi guri na zauna ina kallon k'ofar cikin d'akin nasa zuciyata na bugu, innayi kamar in tashi in shiga sai inji na kasa, ahaka na shafe kusan mintuna talatin a zaune, da k'yar dai nayi k'arfin hali na mik'e na sanya kai cikin d'akin muryata k'asa-k'asa nayi sallama.
Wani sanyi da k'amshi ya doki hancina, na d'aga kai ina kallon d'akin naga d'akin nasa kamar ba a nigeria ba, kayan cikin d'akin nidai tun da nake ban tab'a ganin irin suba, ga wata uwar katifa gado guda yana kwance abinsa abin mamaaki sai naga idonsa biyu yana dai sana'ar tasa danna waya.
Na k'arasa na zube na gaishe da shi bai amsa min ba kamar yanda bai ko kalli inda nake ba, na mik'e da sauri na shege toilet na fara wanke shi domin ina tsoron insake yin wani laifin.
Na wanke tas na sanya turarukan toilet sannan nafito domim insanar dashi cewa na gama, bai kalle niba illa zubo dogwayen k'afa fuwansa da yayi bisa lallausan carpet d'in dake shimfid'e tsakar d'akin, daga shi sai boxer abinsa, ya sanya takalmin da nagani gefan katifar yashige toilet.
Abin ya bani mamaki sosai ta kalmi a kusa da katifa, nan dai na mik'e a gaggauce na gyara katifar tasa na share ko ina na goge, akan mudubin sama nasha mamaki sai kace wani mace, kayan shafe-shafe kala-kala duk ciki babu wanda na tab'ani haka nagama k'are masu kallo danni ba wani iya karatun kirki nayi ba bare in karanta.
Naso yin karatun boko arayuwata amma Allah bai yarjemin ba, iya kacina primari 5 na daina zuwa sabida halin rayuwa na talauci daya sanyamu agaba, islamiyya ce dai nake zuwa har yanzu sabida ita sun d'aukemin biyan ko wanne kud'i dan sun san halin da muke ciki suna tausayawa rayuwata ainun, gashi itama ina ina neman dai na zuwa sabida wannan aikin.
"Tab ! bazai yuyuba yau kam dole inje islamiyya, domin bazanyi biyu babu ba".
Na fad'a a fili ciki-ciki ina mai cigaba da gyara d'akin.
Ashe ma har yafito bansani ba ina can ina zancen zuci, sai da naji ana tab'a kwalaben kan mudubi sannan na lura da yafito, ban ko kalli inda yake ba na fice falo abina.
Saima na gani a falon tana shirya masa abin kari, muna had'a ido da ita ta jefeni da wata uwar harara, ni kuwa nad'auke kai na kamar ban san tana yiba, nayi zamana abina ina jiran umarnin Yarima.
Sai dai kuma naga ba'a gyara falon ba amma tajere masa abin kari.
"Meye zai dame ni ma tunda ba aikina bane?".
Nayi maganar cikin rai na, sai da muka shafe awa guda zaune sannan mukaji takun fitowar Yarima, muka mik'e tsaye kanmu a k'asa ya tako cikin takun k'asaitar nasa k'amshinsa mai sanyi ya cika falon, ya nemi guri ya zauna ba tare daya ko dubi inda muke ba bare abincin da aka jere masa.
"Ohh ikon Allah ! ni dai tun da nake arayuwata ban tab'a ganin miskilin mutum irin Yarima ba, ko d'an yana tak'ama da mulki da kud'i ne oho".
A cikin raina nake ta zancen ni kad'ai, Saima naga ta matsa tahau jere masa abin kari kala-kala ni wani girkinma ko ganin irinsa ban tab'ayiba bare ince na ci.
Da katar da ita yayi da hannu ba tare da yayi magana ba.
Ina ganin haka 'ya'yan hanjina suka kad'a tsoro ya kamani ko wani laifin muka sakeyi.
"Kira Jakadiyya".
Abin da kawai ya furta kenan ya cigaba da aikin sa ko ince sana'ar tasa.
Da rawar jiki na fice na tafi neman Jakadiyya, wata mata Ladidi na tambaya tasanar min tana b'an garen Fulani Sokoto ai kuwa can d'in na nufa.
Ina shiga na zube na kwashi gaisuwa wajen Fulani Sokoto, wani kallo ta watsomin kafin tace da Jadiyya.
"Wannan kuma fa?".
"D'aya ce daga cikin ma aikatan Yarima".
"Cikinsu har da yarinya irin wannan ?".
"Ehh Yarinyarce suna fama da gararin talauci ne, tazo aikine domin su dunga samun abin da zasu ci".
Sai naga Fulani Sokoto tayi murmushin da bansan ko na mene neba, araina ina tunanin meye yasa zatayi wannan maganar akaina?.
"Meke tafe dake?".
Maganar Jakadiyya ta katse n i daga tunanin da nake, na bata amsa da fad'in.
"Yarima keson ganinki da gaggawa".
Ta mik'e tana yiwa Fulani Sokoto sallama nima nabiyo bayanta, a hanyarmu ta zuwa b'angarensu Yarima ta dube ni tana fad'in.
"Ki iya takunki da kowa a gidan nan, ki kame kanki kada ki soma shiga abin da ba ruwanki, sannan kiyi taka tsan-tsan da al'amuran b'angaren Fulani Sokoto".
Ni dai har tagama bayaninta ban fahimci komai ba, sabida tunani na yagama bani yau korata z'ayi kawai tuni na fara matsar kwalla.
Muna shiga ta zube a gabansa nima haka, Saima kuwa dama tana inda nabarta illa gani da nayi ta zubawa Yarima ido kamar zata cinyeshi
Bai ko kalli inda mukeba ya fara magana.
"Gaskiya wa 'yannan basu san aikin su ba, in da dama acanja wasu".
Jakadiyya ta russuna tana fad'in.
"Sunyi laifi ne ranka dad'e?".
Ya tsuna fuska yayi kafin ya bud'e baki a hankali yana magana.
"Ya za'a ajiyemin breakfast ba tare da anshare ba?".
"Ayi afuwa Magajin gobe, Kai kace a cire mutum d'aya, to laifi nawane aga farceni ban sanarwa Aynu gyaren falo ya dawo gare ta ba na mance ne wallahi".
Kai kawai ya gyad'a alamun ya gamsu, yamik'e ya fice daga d'akin ya barmu nan zaune, Jakadiyya ta dubeni.
"Aikin kine Aynu share falon nan ki goge sosai kisa turare domin Yarima ma'abocin son k'amshi ne, ki kiyaye da kyau".
"To ba damuwa".
Haka kawai nace, domin ko bata gayamin ba na fahimci irin so da k'aunar da yakewa dangin turare, ta mik'e ta fice daga d'akin ta barmu ni da Saima, ita ma Saiman bayan ta gama kwashe kwanukan abincin tafice abinta tana fad'in.
"Idan kin gama zaki iya zuwa ki juye abincin nan nakine, domin kece kalar yunwa".
Ta fice abinta nabi bayanta da kallo araina ina mai-maita kalmar.
"Kalar yunw? Kalar yunw?, Ehh gaskiya ni kalar yunwace kowa ya ganni zai san haka, to amma mai yasa zatacemin haka?, na d'auka duk wanda yazo aiki yazone domin nemana abin da zai ci ne ko?, ko kuma akwai masu zuwa aiki ne domin ra'ayi kawai?".
Ganin bani da amsa dukkan tambayoyi na, kuma babu mai amsamin yasa na hak'ura nahau yin aikin dake gabana, duk k'ok'arina yau in koma gida da wuri domin inje islamiyya.
"Mama kina nufin Yarima Fudhal zaki nema wa auren Gimbiya Safiyya?".
Cewar Jalil kenan dake zaune gefan mahaifiyyar tasa, murmushi tayi kafin ta bashi amsa.
"Ehh mana haka nake ganin shine mafita, bayan auren zan sanar maka shiri na na gaba".
"Amma fa ni nake son tafa kin sani Mama!".
"Kai fa sha-shane wallahi mutumin da ake nema masa hanyar sarauta mai zai yi da wata soyayya?".
"Nasani Mama amma gaskiya banjin zan iya hak'uri da sonta".
Murmushi tayi akaro na biyu kafin ta dube shi da takaici.
"Na zaci ko sanin kana sonta Gimbiya batayi ba?".
"Ehh amma aike nake nufi ki gayawa Mai Martaba anema min aurenta".
Fulani Sokoto dariya tayi mai sauti awan nan lokacin tana mai yiwa d'an nata kallon soko baka san abin da kake yi ba, amma a fili kuma cewa tayi.
"Amma kai dai baka da tunani ko kad'an Jalil taya Mai Martaba zaiyi maka aure ga yayan ka bai ko kawo maganar auren ba !, ka dai sake tunani amma ni maganata na gama".
Jalil yayi shiru yana duban Mahaifiyar tasa batare daya sake furta ko mai ba itama haka.
Yarima Jalil suna matuk'ar kama da Yarima Fudhal ban-ban cinsu kawai shekaru da kuma k'asumbar fuska, Yarima Jalil shekararsa ashirin da bakwai kuma shi baya tara k'asumba a fuskarsa illa siririn sajen da yayuwa fuskarsa k'awanya, yayin da Yarima Fudhal ke da shekaru talatin aduniya ma'abocin tara suma ne ta kai da kuma fuska da suke shan gyara ko yaushe wanda hakan bak'aramin kyau yake k'ara masa ba.
Mik'ewa yayi zai fice bata dubeshi ba take fad'in.
"Ka kiramin Ladidi".
"To".
Kawai yace ya fice daga d'akin, a hanyarsa ta zuwa b'angaren sane ya gamu da Ladidin ya bata umarnin taje mahaifiyarsa na kiranta, shi kuma ya shige b'angarensu.
Fitowa ta kenan daga falon Yarima na gama gyarawa zan tafi mukayi karo da shi yana shirin shiga d'akinsa, durk'usawa nayi na gaishe shi bai amsaba sai k'uramin ido da yayi yana bina da kallo, na mik'e na wuce abina domin tunanina shima miskilin ne irin Yarima Fudhal.
Har sai da nak'ule ya daina ganina sannan ya shige d'akin nasa yana sosa k'ewa fuskarsa cike da murmushi kona menene ? oho.
Yau ban jira Zainab ba sabida saurin da nake, naje na juye abincin da Yarima ya bari acikin Viva nayiwa Jakadiyya sallama na tafi gida.
[09/07, 00:23] Nana Sales Aliyu Fbk Mai Quratu Group: *YARIMA FUDHAL*
NAGARTA WRITERS ASSOCIATION®
FIRDAUSI S.A (QURRATUL-AYN)©
06
Yauma kamar kullum haka na tadda shi kwance bisa katifarsa mai kama da gado ya lullub'e jikinsa da bargo mai taushi, hannunsa dake rik'e da waya kawai sune a waje yana danne-dannansa.
Naje na gaishe shi duk da baya amsawa amma hakan bai sa na dai na gaidashi ba sabida gudun yin laifi, na mik'e na wanke toilet na fito na sanar masa na gama.
Ya ziro k'afafuwansa ya saka takalmimsa yashige toilet batare daya kalli inda nake ba, ni kuwa na mik'e na kad'e ko ina na share na goge , na kalli agogo naga kusan awa guda kenan, araina nace.
"Wannan wane irin wanka ne?, mutum yayi awa guda a toilet kamar mai canja fata?".
A fili kuwa na furta.
"Ko da yake komai na masu sarauta da ban ne".
Jin motsin fitowarsa da nayi ne yasa na d'ebi tsin tsiya da abin mooping nayi falo, na cigaba da gyaran falon, na kusa gamawa sannan sai ga Saima ta shigo hannunta rik'e da tire bata ko kalli inda nake ba ta wuce inda Yarima ke cin abinci ta fara jere masa, ni kuwa na gaggauta tsaftace falon sabida kada ya fito yaga ban gamaba.
Allah kuwa ya taimakeni bai fito ba sai da na gama na d'auke komai sannan ya fito, shigar coat yayi fara har zuwa wando da agogon hannunsa da takalmi duk farare ne na fahimci dai baya son manyan kaya domin tun dawowarsa banga ya saka kayan nan k'asar ba.
Yaje ya zauna yana wani shan k'amshi, Saima ta jere masa dukkan nin abin da tasan zai buk'ata ta koma gefe ta zauna tana kallonsa, ni dai kaina ak'asa yake addu'a nake Allah ya rabamu dashi lafiya yau.
Cokali d'aya yayi na ruwan tea wayarsa dake hannunta tahau ringing ya d'aga yana mai sata free, domin duk muna jin abin da ake cewa a waya r sai dai bana fahimtar abin da suke fad'i domin yaren turanci naji sunayi ni kuwa kun dai san banko k'arasa primari ba bare ince zan ji turanci, Saima ce dai naga tana ta murmushi kamar tana fahimtar wani abu da yake fad'a a wayar.
Yana kashe wayar yamik'e ya fice, Saima ta tattara kayan da sauri ta fice da su tabarni zaune a falon nayi ta gumi ina wani tunani na da ban, sai kawai ji nayi andafa ni ta baya firgigit na juya domin ganin waye?, domin tunanina ya bani Zainab ce.
Ina juyawa sai naga sab'anin tunani na a she Yarima Jalil ne, na durk'usa da sauri na gaishe shi duk da fad'uwar gaban da nake fuskanta awannan lokaci.
Amsawa yayi yana mai cigaba da kallo na, ni kuwa kaina na k'asa cike da tsoro na furta .
"Ko kana buk'atar wani abu ne?".
Kai kawai ya girgiza alamun a'a yana mai neman guri ya zauna yana fad'in.
"Ku nawa kuke yiwa Yarima aiki?".
"Mu biyu".
Na bashi amsa a gag-gauce, yad'an tab'e baki a hankali kafin yace.
"Kina jin dad'in aiki anan kuwa?".
"Ehh".
Na kuma bashi amsa.
Shiru ya gauraye d'akin na wani lokaci, nidai kaina yana k'asa Allah Allah nake insamu in fice daga d'akin, dan haka kawai nidai hankalina bai kwanta da al'amarin Yarima Jalil ba, ina cikin tunanin yanda zansamu in fice daga d'akin sai kawo jin hucin numfashinsa nayi a fuskata naja baya da sauri, bina yayi da kallo kafin yayi murmushi kawai ya fice daga d'akin, ajiyar zuciya na saki kafin in mik'e da sauri nima na fice daga d'akin har ina tun-tub'e.
A hanyata ta zuwa inda sauran ma'aikatan gidan ke zama insungama aiki naci karo da Zainab taa ganni duk a wani tsorace, jana tayi wani b'angare na gidan da ban tab'a sanin da shiba domin Zainab tasan ko ina a cikin gidan kuma kowa ya san ta.
Muka zauna ta rik'o hannunta tana tambayata.
"Lafiya Aynu?".
Nayi shiru nad'an lokaci ina kallon wani gefe na wajen, kafin na dawo da kallona kanta na fara bata labarin abin da yafaru.
Zainab ta zaro ido waje tana fad'in.
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, sai kinyi taka tsan-tsan da Yarima Jalil sosai wallahi".
"Kamar yaya?".
"Nasan baki san waye Yarima Jalil bako Aynu?".
Tad'an rage muryarta k'asa-k'asa.
"To Yarima Jalil ya wuce dukkan tunaninki, ya ksance mashayin giya kuma manemin mata a cikin gidan nan duk wacce aka kawo aiki indai ta burgeshi to wallahi duk hanyar da zai bi sai yabi domin ta zama yarinyarsa, ma aikata uku aka zubarwa cikinsa, kuma aka kulle bakinsu da kud'i kada su fad'a babu wanda yasan haka sai mahaifiyarsa sai kuma Jakadiyya, domin ita ce ma take sanarwa Babah Tasallah lokacin dana fara aiki a gidan nan, ko Mai Martaba kansa bai san muna nan halin Yarima Jalil ba".
Gumi ne ya ketomin ta gefan fuskata jin wannan bayani na Zainab nayi maza na goge ina fad'in.
"Ina hakan ma ba zata tab'a faruwa ba, babu dole sai in hak'ura da aikin".
Dariya Zainab tayi kafin tace.
"Kina hauka kenan?, ai barin aikin ki bai ta soba domin ko kinbar aikin sai ya binciko inda kike kuma sai ya biki".
"Wayyo Allah na to yanzu ya zanyi?".
Nace da Zainab cike da tsoro, domin kunsan halina akwai tsoro kamar farar kura.
Zainab tayi shiru kafin tace.
"Ki kwantar da hankalinki ko Ummanki kada ki fad'awa, tun da Allah yasa ba aikin dare kike ba, ko kad'an kada ki bashi fuska iya kaci gaisuwa bazai tab'a saki wani aiki ba tunda yasan ba b'angarensu ki kewa aiki ba kawai dai ki iya takun ki a gidan nan".
Shiru nayi ina duban Zainab kafin ince.
"Au dama akwai masu aikin dare ne?".
"Ehh akwai koni da farkon zuwana aikin dare na farayi sai da Jakadiyya tayi magana na dawo safe".
Aynu tayi ajiyar zuciya domin kalaman Zainab ya kwantar mata da hankali ya kuma bata kwarin gwiwa, har dai da taji batun bazai tab'a umartatta da wani aiki ba tunda ba'a b'angarensu take aiki ba taji dad'i sosai.
Nan sukayi ta hirarsu har Zainabu take sanarwa Aynu taji Yarima Fudhal yana fad'in zai fita shida abokansa sun shirya masa party na murnar kammala karatunsa lafiya.
Aynu tace "kaji illar wasu masu kud'inba, idan har murnar za'ayi da gaske mai zai hana ayi saukar al'qur'ani da walima".
"Kema dai kya fad'a kinsan bakowa yake son abin da za'a fad'i abin da Allah da Manzonsa suka ce ba, al'amuran yahudawa yafi rinjaye a zukatan yawancin mutanen mu nayanzu, duk da cewa ba duka aka taru aka zama d'aya ba".
"Haka ne, Allah dai yasa mu dace".
"Amin ya Allah".
Suka amsa baki d'ayansu da haka har lokacin ta shinsu yayi kowacce taje ta d'auki abincinta suka tafi gida.
*** ***
Filin wajen cike yake mak'il da jama'a maza da mata kowanne yana ji da kansa, domin kowa ka kalla a wajen za kasan kud'i ya zauna sabida daga d'an Alhaji da Hajiya sai d'an menister wane 'yayan 'yan kasuwanni da 'yan siyasa sune suka cika wajen bakajin komai sai tashin kid'an turawa kala-kala da wannan ya katse sa kaji wannan ya d'ora, dare ne amma tamkar rana haka wajen yake sabida hasken daya haske wajen wanda shine ya basu kwarin gwiwar yin harkokinsu hankalinsu kwance.
Filin wajen kansa abin mamaki ne banda irin cikar da yayi, jerin motoci goma ne sukai layi a harabar wajen duka bak'ak'e ta tsakiya ce kawai fara, jikin lambar motar kowacce anrubuta Emirs 1 har zuwa 10.
Baki d'aya gurin yarud'e da ihun kiran sunan YARIMA FUDHAL.
Cikin takun k'asaita yafito kamar bazai iya taka k'asa ba yana wani shan k'amshi yayi shiga irin tasu ta sarauta kowa ya ganshi yasan Yarima ne wanda akeji da shi a gida da kuma waje, sauran abokansa suka take masa baya.
Waje na musamman aka ware masa shi da abokansa, hankalin 'yan matan gurin nan kaf yayi kansa kowacce burinta tasamu shiga wajensa.
Bayan kowa ya natsa kuma aka buk'aci Yarima Fudhal yayanka cake, yamik'e fuskarsa cike da murmushi ya d'auki wuk'ar zai yanka, aka fara irga.
"One....two.....thr..".
K'arar motar dake shirin yin parking a wajence ta katse kowa, dukkan hankulan jama'ar gurin ya koma kan motar.
Domin mota ce da duk wajen babu wand ya halarci gurin da ita mota ce k'irar Perrari mota mafi kyau da tsada.
Kowa burinsa a wajen yaga waye ma mallakin wannan motar?.
A hankali ta ziro shantaleliyar k'afarta da tasha dogon takalmi mai tsini yana da igiyoye wanda sune suka taimaka wajen rik'e k'afa fuwanta, shigar dake jikinta kuwa guwn ce pink da tabi dukkan jikinta ta d'ame, daga gaban rigar har zuwa k'asa yasha adon stone blue dark tayi rolling da mayafi k'arami shima blue.
Wayar dake hannunta ta d'orata bisa cinyarta X ce itama kalar takalminta blue, duk wannan bayanin da akefa bata fito da dukkan jikinta ba bare har mukai da ganin duskarta.
Ta shafe mintuna kusan biyar a haka kafin ta fito zuwa waje, anan ne fa dukkan nin mumfashin mutanen dake wajen ya kusa d'aukewa sabida kyakykyawar halittar da idanuwansu yayi tozali da ita, duk da bak'im glass d'in dake fuskarta daya rufe kusan rabin fuskarta, amma hakan bai hana ganin tsan-tsan kyawun halittar dake tattare da ita ba.
Cike da murmushi ta doso inda Yarima yake tana wani taku tare da rangaji kamar bishiyar da iska ke kad'awa.
Nidai tunani na banyi zaton zata iya taku da takalmin dake k'afar taba, amma sai naga tana tafiya kamar wadda tasanya silifas .
Bata tsaya ba sai da taje dai-dai inda Yarima Fudhal yake tsaye rik'e da wuk'ar yanka cake sannan ta tsaya jikinsu har yana gogar juna ta juyo tana k'arewa sauran mutanan wajen kallo kafin ta saka hannu ta cire glass d'in da yayiwa kusan rabin fuskarta k'awajen.
A fili na furta "SAIMA!".
[10/07, 20:09] Nana Sales Aliyu Fbk Mai Quratu Group: *YARIMA FUDHAL*
NWA®
FIRDAUSI S.A(QURRATUL-AYN)
07
A fili na furta "Saima !".
Amma Yarima Fudhal kuwa tsaya wa yayi yana dubanta cike da mamaki tare da tunanin inda ya tab'a ganin fuskarta.
A hankali ta dawo da kallonta kan fuskar Yarima da ya tsare ta da shanyayyun idanuwansa yana nazari a kanta sosai, tunaninsa ya tsaya adai-dai lokacin daya tuna yatab'a ganin mai kama da ita awani guri.
Idan zai iya tunawa lokacin daya ba da umarinin a kira wo masa Jakadiyya ranar da ba'ashare falo ba, a lokacin bai zaci da mutum zaune ba yad'auka dukansu suka fita yana ta danne-dannan wayarsa ya d'ago kai bai zata ba suka had'a ido tayi saurin sauke kanta k'asa shine ganin da zaice yayiwa mai kama da ita.
"Wacece ke!".
Bai san sanda ya samu kansa da jefa mata tambayar ba, bata bashi amsaba illa rik'o hannunsa dake rik'e da wuk'ar yan kan cake d'in da tayi ta fara irga, sai kawai gani yayi ta yanko cake ta nufi bakinsa da shi kau da kansa yayi gefe yana mai komawa inda yake a zaune ya zauna.
A dai-dai lokacin da aka k'ara sakin kid'a ana ciye-ciye da shaye-shaye, Saima ta koma kusa da shi ta zauna tana dubansa tare da zuk'ar lemon da ke rik'e hannunta, ta d'an basar kamar yanda taga yayi mata amma ta kasa jure shirun nasa ta gyara zama tana fad'in.
"Suna na Saima 'yar gidan Alhaji Buba 'yarsa tilo guda d'aya da akeji da ita tamkar kwai, nice first kuma nice last a gidanmu, bawai nazo wajen nan dan wani abu ba, nazone intayaka murnar dawowarka k'asarka lafiya sanna in sanar maka irin son da nake maka, sauran bayani zan baka numberta sai muyi magana a waya".
Duk zubar datake ko kallon inda take bai yi ba, shidai burinsa kawai ya fita daga kokwanton da zuciyarsa takeyi masa, aransa yana fad'in.
"To idan wannan 'yar gidan Alhaji Buban dana sani ce waccan kuma da take min aiki wacece?".
Babu amsa domin maganar aransa yake yinta bai ko yi k'ok'arin tambayarta ba, sai ji yayi ta zare wayarsa dake rik'e a hannunsa binta kawai yayi da kallo kafin ya mai da kansa kan al'ummar wajen, sai da ta sanya numberta a wayarsa ta d'auki tasa a tata wayar sannan ta ajiye masa wayar a gabansa ta mik'e ta shiga filin rawa.
'Yam matan dake wajen baki d'aya sun raina kansu, da had'uwa da kud'i irin na Saima, samari kuwa tuni sukayi ca a kanta kowa yana zuba mata kud'i, domin su sami shiga a wajen ta duk da sun saddak'ar ita d'in ta Yarima Fudhal ce.
Shidai Yarima bai ko taka inda ake rawar ba, har suka gama aka hau d'auke d'auken hotuna kuma.
11:30pm
Sai sha d'aya na dare aka tashi kowa ya nufi hanyar gidansu, Yarima ya dawo a gajiye wanka kawai yayi da sallah ya nemi makwancinsa ya kwanta, yana Allah Allah gari ya waye ya warwarewa zuciyarsa wasi-wasin da take ciki.
*** ** ***
7:30am.
Muryar Aynu ita ce tayi sanadiyyar ta shinsa daga dad-da d'an baccin da yake, domin da k'yar dama ya samu yayi sallar asuba ya koma, domin shi mutum ne da baya wasa da sallah ko kad'an, mik'a yayi tare da salati ya mik'e ya nufi toilet ba tare daya kula da gaishe shin da take ba, domin inda sabo yaci ace ta saba da halin Yarima.
Nan d nan sai gashi yafito falo Aynu ta cika da mamakin shirya warsa da wuri haka yau, lokacin Saima na zaune ta gama jere masa abincin, zama yayi yana mai k'urawa Saima ido, sai dai wani abu daya rud'ar da shi akan Saiman jiya da wadda take masa aiki shine.
Wan nan bak'ace waccen kuwa farace sol kamar a tab'a fatarta jini ya zubo duk da manyan idanuwansu yazo d'aya, sannan kuma ta jiya tana da hip sab'anin wannan siririya.
"Ke ! mik'e tsaye".
Sukaji saukar muryarsa akunnu wansu da sauri suka mik'e duka, sai kuma ya tuna ai ta jiya ta sanya dogon takalmi ne bazai iya tan-tance tsayunsu ba.
"Mene sunanki?".
"Ay....".
Aynu tabud'e baki zatayi magana yakatseta da fad'in.
"Ba ke ba ".
Ba tare daya dubeta ba, domin idonsa na kafe kan Saima kawai.
Tayi shiru abinta tana kallon ikon Allah yau.
"Saima ".
Ta bashi amsa, sai yaji muryar Saiman jiya tafi siririya akan ta wannan, kai ya girgiza yana fad'in
"Sunan ne yazo d'aya tare da kama kenan?".
A fili yayi maganar yayin da Saima da Aynu suka dubi juna, Saima ta jefawa Aynu wata muguwar harara, Aynu kuwa ta mayar mata da murmushi.
Mik'ewa yayi ya fice ba tare daya bi takan abincin nasa bama.
Kai tsaye shashin mahaifiyarsa ya nufa, ya sameta tana bada umarnin wasu abubuwa a gidan neman guri yayi ya zauna yana mai gaishe da mahaifiyyar tasa yayin da ma aikanta suka gaishe da shi, bai amsa ba suka mik'e duk suka fice.
Sai yayi shiru kuma yana jujjuya wayarsa a hannunsa, kallonsa Fulani Bingel ta tsayayi tana karantar yanayinsa.
"Lafiya Magaji?".
A jiyar zuciya yayi kafin ya fara magana.
"Hajiya dama a kwai mutanen da zakiga basu san junaba basu had'a wani relation ba amma kuma kiga suna kama sosai?".
Fulani Bingel tad'anyi dariya tana fad'in.
"Magaji kenan ! to ai ko wanne mutum da kagani akwai copy d'insa bakwai a duniya, wani abune ya faru kake wan nan tambayar?".
"A'a babu komai".
Abin da yace kenan bai sake magana ba, yamik'e ya shiga b'an garen Kakarsa Mai Babban d'aki, anan yayi breakfast d'insa bai bar wajen taba sai k'arfe biyu da aka kira sallar azahar ya fito ya tafi masallaci, kafin ya dawo su Aynu tuni sun gama aikinsu sun nufi gida, ya shige d'akinsa ya kwanta abinsa.
***
BAYAN SATI GUDA !.
Sati guda kenan da had'uwar Saima da Yarima Fudhal kullum tana zuba ido taga kiransa a wayarta, amma girman kai da jiji da kai ya hana ta nemeshi ita, yayin da shi kuma yama mance da al'amuranta domin shi mutum ne da baya son sanya abu aransa domim yan zunnan sai abin ya nemi ya zame masa matsala tunda ya samu Mahaifiyarsa tayi masa bayanin ana samun copy d'in mutum bakwai aduniya shikenan domin dama kokwan tonsa ko ta zo aiki gidanne sabida wani nufi nata amma yanzu zuciyarsa ta bashi waccen Saiman daban wadda ke masa aiki daban.
B'angare guda kuma kwana uku kenan Aynu batazo aiki ba sabida Ummanta dake kwance babu lafiya, sai dai ta fad'awa Zainab ta sanar a gidan sarki kada aga bata zuwa, Jakadiyya tace babu komai taje ta sanarwa Yarima shima cewa yayi ba damuwa sannan ya ciro dubu biyar yace a bata su sai magani Jakadiyy da kanta ta kai musu gida domin macace mai kirki da rik'on gaskiya da amana.
A rana ta biyar ne Aynu taga jikin Mahaifiyar tata yayi sauk'i ta shirya tace zata koma aiki ta yima Ummanta sallama da Babanta ta tafi.
7:30am.
Bakwai da rabi na safe kamar yanda ta saba ta isa gidan, bayan taje ta gaishe da Jakadiyya ta gaida Fulani Bingel kai tsaye kuma b'angarensu Yarima ta nufa.
Tana shiga taga Naja ta fito daga d'akin Yarima Jalil da alamun rashin gaskiya a fuskarta, Aynu tayi kaman bata ganta ba ta wuce d'akin Yarima.
Kamar yanda ta saba batayi tunanin komai ba tasa kai cikin d'akin, yanda ta ganshi ne ya sata zubewa bisa gwiyoyinta ta runtse idonta k'am jikinta na faman b'ari kamar mazari.
Ta mudubi ya ga shigowarta a fili ya furta.
"Ohhh my God !".
Yana mai dafe goshinsa.
[17/07, 16:25] Nana Sales Aliyu Fbk Mai Quratu Group: *YARIMA FUDHAL*
NAGARTA WRITERS ASSOCIATION®
FIRDAUSI S.A (QURRATUL-AYN).
SADAUKARWA:- Namesy ta Pheerdauceey Jeebour.
Amma wannan page naki ne SAFIYYA GALADANCHI Allah yabar zumunci.
08
"Ohhh my God !".
Ya fad'a yana mai dafe goshinsa.
Aynu kuwa tuni hawaye ya fara zarya a kan kuncinta harta saddak'ar yau aikinta yak'are a gidan.
"Wanne kuskure tayi da har ta shigo ta taddashi a wannan yanayin?".
Tayi tambayar cikin ranta.
"Sallama !, Ita ce kuskuren da nayi da a ce nayi sallama da ban shigo na same shi a haka ba, da yayi k'ok'arin kintsawa kafin shigo wata, ko ya da katar dani harya suturce jikinsa".
"Wayyo Allah na !".
Ta fad'a a fili kuma da k'arfi wanda har sai da Yarima Fudhal dake k'ok'arin suturce jikinsa ya juyo yana dubanta, wannan shine karo na farko da Yarima ya tab'a duban fuskar Aynu tun zuwanta gidan aiki, gabansa ya buga dammm, yayi saurin d'auke kai yana mai ci gaba da sanya rigarsa tare da tunanin yanda a kaima tazo ta taddashi a haka, aransa ya furta.
"Kuskure na ne !".
MINTUNA TALATIN DA SUKA WUCE
Kasancewar Aynu ta daina zuwa aiki kwana biyu sabida jinyar Ummanta, sai aikin wankin toilet da shara ya koma hannun Saima duka.
Yau ya tashi yajishi a gajiye ga kuma gumi da yaji yanayi duk da sanyin AC da ke d'akin amma hakan bai hana shi jin zafi ba, ha kan ne yasa ya nufi toilet domin watsa ruwa.
Sai dai Yarima nada wata al'ada guda d'aya, kasan cewarsa mai tsafta da kuma kyankyami shiyasa ko kad'an baya iya barin abu jik'ak'k'ema ajikinsa yana fitowa daga toilet yake wurgi da towel d'insa sannan ya nemi wani ya d'aura ko ya bari ya gama shafa mai da koma kafin ya suturce jikinsa, sabida ya san babu mai shigo masa d'aki sai da izininsa hakan ya kuma zame masa jiki sosai, to yauma a hakan ne Aynu ta shigo ta tadda shi.
Yana gama sanya rigar ya sake dawo da dubansa kan Aynu da jikinta ke ta tsuma tana jiran saukar duka ko wani mugun hukunci daga Yarima.
Zama yayi gefan katifarsa yana fad'in.
"Ke !, zo nan".
Aynu ta rarrafa da jan gwiwa ta k'arasa inda ta jiyo muryarsa idonta har lokacin a kulle bata bud'e ba, cike da tsoro ta haufad'in.
"Kayi hak'uri ka gafarce ni dan Allah !, wallahi tallahi banyi zaton zan tadda kai a haka ba Allah, dan Allah kada ka kore ni da wannan aikin muka dogara nasha wuya kafin in same shi amma....!".
Kuka ne yaci k'arfinta ba tare da ta iya k'arasa mganarba ta mak'ale a mak'oshinta.
Yarima kuwa murmushi yayi yana mai k'arewa halittarta kallo yayin da yakeji bugun zuciyarsa na k'aruwa sosai amma yana jin da d'in kallon nata sosai, musamman yanda take sarrafa leb'anta wajen magana, sai zara-zaran gashin idonta da suka jik'e da hawaye duk da bai ga idon nata ba.
"Bud'e idonki babu abin da zanyi miki".
Yayi maganar yana mai kafe idanuwansa bisa nata.
Aynu ta hau bud'e idonta kad'an-kad'an wai dan kada ta kuma ganinsa a yanda ta ganshi d'azu, tana gama bud'ewa sukayi ido biyu da shi, tayi saurin sauke idonta tana mai rissi nawa da fad'in
"Nagode sosai, Allah yak'ara girma".
"Amin".
Da sauri ta d'ago kai ta dubeshi sabida mamakin yau karo na farko tayi magana ya mayar mata, murmushi kawai ta ga yayi mata, ta d'auke kanta tana mai shigewa toilet din domin wankewa.
Mintuna kad'an ta fito ta taddashi a inda tabarshi illa wayarsa dake hannu yana daddan nawa, yanaji ta fito ya d'aga kai yana binta da kallo har ta zo ta durk'usa tana sanar masa ta gama.
Mik'ewa yayi ya fice bai ce da ita komai ba, yana fita Aynu tayi ajiyar zuciya domin ita kanta kallon da yake mata ya fara bata tsoro sosai, ji take aranta kamar hukuncin da zai yi mata yake shiryawa.
Ta gama komai ta fito falo ta taddashi zaune, amma wannan karan ya akiye wayar gefansa yana kallon ball a TV, gefe guda kuma Saima ce zaune Aynu na fitowa ta hau aika mata sak'on harara ita kuwa bama tasan tanayi ba, ta fara k'ok'arin gyara falon duk abin da ta keyi idon Yarima akanta shi kansa bai san dalilin da yasa yau d'aya yanajin dad'in kallon yarinyar sosai, komai takeyi a nutse cikin sanyi kuma hakan na burgeshi sosai.
Sai da ta gama komai yau duk yana zaune, sannan Saima tazo ta jere masa kayan Breakfast d'insa, yana ci yana faman kallom Aynu yayi mamakin irin abincin da yaci yau sosai, ya gama Saima takwashe kwanukan ta fice tabar Aynu nan zaune.
Zaman duk ya gun dureta ga kallon da Yarima Fudhal keta jifanta dashi domin lokaci-lokaci data d'ago kai sai sun had'a ido baki d'aya jinta take yau duk a takure sai take tayin data sanin zuwanta aikin ma yau baki d'aya.
"Mene sunanki?".
Taji tambayarsa ta jefi kunnuwanta, ta d'an gyara zama tana fad'in.
"AYNU".
"Aynu kuma?, ci kakken sunanki nakeson ji".
Ajiyar zuciya tad'anyi kafin ta bashi amsa.
"AYNUL-HAYAT".
Ta fad'a tana mai gyara zamanta da kyau domin ji tayi k'afafuwanta duk sunja jini sunyi wani iri babu dad'i sabida zaman d'urk'ushen da tayi.
"Aynul-hayat !".
Taji ya mai-maita cikin wata irin murya da ta sanya tsigar jikinta tashi, ta d'ago kai akaro na biyu ta dube shi shima ita d'in ya kafe da idanuwa ya jefe ta da murmushi kafin yace.
"Nice Name".
Tayi saurin sauke idonta yayin da bugun zuciyarta ya cigaba da k'aruwa, aranta tana fad'in.
"To me ya zauna yi yau ayanda nasan shi da yana gama cin abinci yake ficewa zuwa wajen Kakarsa ko Babarsu amma yau ya wani zauna ya tsare mutane".
A fili kuwa ita ma murmushin ta d'anyi duk da bai kai zuci ba.
"Beautiful smile".
Taji yak'ara fad'a ita ta d'auka ma waya yake da turawa dan bata fahimci mai yake fad'i ba.
Mik'ewa yayi ya shige bedroom d'insa mintuna kad'an sai gashi ya fito sanye da jeans bak'i da T.sheet blue yayi kyau sosai, yazo yad'an rage tsayinta akanta yana fad'in.
"Aynul-hayat !".
Taji gabanta ya fad'i, ta d'ago kai ba tare data amsa ba, shima bai da muba ya cigaba da fad'in.
"Yaushe kuke tafiya gida?".
"K'arfe biyu ko biyu da rabi".
"Ok".
Abin da yace kenan ya kama hanya ya fice ya barta nan zaune tana tunanin abubuwan da suke faruwa da ita yau.
"AYNU".
Ta sake jin muryarsa ta daki kunnuwanta ta juyo da sauri sai taga ashe Yarima Jalil ne tsaye bakin k'ofa ya nad'e hannuwansa bisa k'irjinsa yana jifanta da wani mugun murmushi.
Gaishe shi tayi ya amsa yana fad'in
"Mai yasa bakyason sakin jiki da ni, da zaran kin ganni sai kin tsora ta?".
"Babu komai".
"Da wani abu mana fad'i gaskiya dai?".
Ji yayi andafa kafad'arsa ta baya ya juya da sauri sai yaga ashe Yarima Fudhal ne ya kuwa had'e girar sama data k'asa, ya dubi Aynu yana fad'in.
"Ke...!, tashi ki fita".
Sum-sum Aynu ta fice dama neman hanyar fita ta keyi, Yarima Jalil kwafa yayi yana cijen lab'e yabar k'ofar d'akin, domin yasan yanzu kome zai yi Yarima Fudhal bazai kulashi ba kuma ba zai tsaya suyi maganar arzik'iba tunda ya d'aure fuska.
Assalamu alaikum
Nagode sosai 'yan uwa da abokan arzik'i abisa addu'arku agareni Allah yabani lafiya sosai, masu inbox zuwa call da message ina godiya Ubangiji Allah yasaka da alkhairi amin.
Zaku cigaba da jina insha Allahu kamar ko yaushe.
[18/07, 18:08] Nana Sales Aliyu Fbk Mai Quratu Group: *YARIMA FUDHAL*
Na
FIRDAUSI S.A (QURRATUL-AYN).
NAGARTA WRITERS ASSOCIATION®
SADAUKARWA:-Namesy ta Pheerdauceey Jeebour.
Wannan page naki ne Tawan ta hannun damana HAFSAT M. ki morewa abinki.
09
Aynu na fita can baya taje ta samu waje babu kowa ta zauna abinta tana nazari a kan abubuwan da suka faru, a haka Zainab ta tadda ita.
Neman guri tayi kusa da Aynu ta zauna tana tambayarta "lafiya kuwa?".
Aynu bata ji komai ba ta kwashe dukkan abin da ya faru ta sanar da ita sai dai ta b'oye abu guda bata fad'a mata ba, wato ganin da ta yiwa Yarima wanda aganinta bai dace ta fad'awa kowa ba.
Zainab tace.
"Haba Aynu wannan d'an abin shine kuma abin da zai ta da hankalinki, ki kwantar da hankalinki wallahi babu abin da zai faru insha Allahu".
Nan dai tayi ta jan Aynu da hira har ta samu ta war-ware daga damuwar da take ciki, kafin su mik'e su koma ciki domin k'arasa ayyukansu, Zainabu tayi b'an garen Fulani Bingel ita kuma ta nufi b'an garensu Yarima.
***
"Ni kuwa mai Martaba dama akwai wata shawara da nakeson baka akan Magaji !".
Mai Martaba dake kishin gid'e kan kusun ya d'an sake gyara kwanciyarsa, Fulani Sokoto ta mik'o masa yan kakken tufa d'in da yake ci yakarb'a ya kai bakinsa yana fad'in.
"Ina jinki, wacce shawara ce wannan?".
"Kan batun auren Magaji da kake taso yayi shi kuma kaga har yanzu baice komai ba, wata k'ila baiga wacce yake so ba, shi ne nace mai zai hana anema masa auren Gimbiya Safiyya !".
Mai Martaba yayi shiru yana duban Fulani Sokoto cike fa nazari bisa maganar da tayi yanzu can ya gyad'a kai yana fad'in.
"Shawara mai kyau Safiyya 'yar Sarki Maina yarinyace mai tarbiya ai babu wanda zai ganta yace batayi masaba, gaskiya naji dad'i sosai akan wannan zab'in da kika yiwa d'an namu".
"Mai Martaba kenan ai nima d'ane a wajena inda abin da yafi hakama zanyi masa".
"Gaskiya ne aikuwa zamuje nema masa aurenta batare da b'ata lokaci ba".
Tuni wani sanyin dad'i ya ziyarci zuciyar Fulani Sokoto domin tarkonta ya kama, addu'arta d'aya Allah yasa kada ta samu matsala da Yarima Fudhal kuma?.
***
Kwance yake falo kan d'aya daga cikin kusun d'in dake falon rawar sanyi yake sosai amma ya kasa tashi ya nufi d'aki ko ya nemi abin da zai rufa dashi gashi wayarsa ma tana cikin d'akin, bai jin zai iya d'aga ko da dai-dai da yatsansa d'aya bare ya bud'e baki yayi magana.
A haka Aynu tayi sallama cikin falon ta taddashi, k'ara sawa tayi da zauri zuwa inda yake tana tambayarsa lafiya? ganin da tayi jikinsa sai rawa yake yasa ta fahimci cewa sanyi yakeji.
Mik'ewa tayi ta nufi d'aki ta d'auko masa k'aton bargon da yake rufa dashi ta zo ta rufa masa sannan ta koma ta fara aikin ta mintuna kad'an da gama wankin toilet tana gyara cikin d'akin ta dinga jiyo kakarin amansa, ta fito zuwa falo taga yayi aman bisa carpet ne kawai amma ban da jikinsa .
"Ko inkirawo maka Yarima Jalil ne?".
Kai ya girgiza mata alamun a'a, Aynu tayi shiru tana dubansa shima ita d'in yake kallo.
"Ko a kira Hajiya?".
"Bana buk'atar kowa".
Abin da yace da ita kenan kawai, tayi shiru na tsawon lokaci kafin ta sake fad'in.
"To koma d'aki in gyara falon".
Dubanta ya tsayayi yana k'ok'arin bud'e bakinsa domin yin magana amma kuma maganar tak'i fita, a hankali ya dafa bango ya mik'e yana tafiya har ya isa d'akin toilet ya wuce ya watsa ruwa a daddafe tare da wanke baki ya fito ya sanya jallabiya ya kwanta.
Aynu ta gyare falon tas tasanya turare aranta tana jin tausayin Yarima domin tasan bak'aramin ciwo ne zai kwantar dashi har haka ba.
Lokaci-lokaci takan lek'a tayi masa sannu ta dawo ta cigaba da aikinta, sai da ta gama komai sannan ta koma ta tambayeshi koyana buk'atar wani abune?, Ruwan tea kawai ya buk'ata ta kawo masa.
Lokacin k'arfe bakwai da mintuna arba'in da yake tazo da wuri yau burinta bai wuce ta samu ta koma gida da wuriba sabida wani dalili nata.
Kitchent ta nufa ta sanar da buk'atar Yarima nan da nan aka mik'o mata flast da cofuna da sauran tarkacen kayan tea.
A gabansa ta ajiye ta zuba masa ruwan tea d'in kawai da sugar domin yace baya buk'atar komai da k'yar yamik'e ya karb'i tea d'in yana sha, ita kuma ta fice daga d'akin ta nufi wajen Fulani Bingel wato mahaifiyarsa domin ta sanar da ita halin da yake ciki.
Tare suka tawo da ita da sauran ma'aikatanta, sukayi masa sannu suka fice ni dama falo nayi zamana muna shigowa, Yarima Jalil ne ya shiga yayi masa sannu shima ya fito ya koma d'akinsa, cikin k'ank'anin lokaci ciwon Yarima Fudhal ya bazu ko ina sai faman dubiya ake zuwa abin har ya bani mamaki, sai na tuna da ni kaina idan zamuyi wata nawa muna ciwo sai wanda ya zama dole yake zuwa dubamu, Allah sarki arayuwa idan a kace kud'i da mulki angama komai.
Fulani Bingel ta jima a tare da shi komai ta tambayeshi yana so sai yace A'a daga k'arshema cewa yayi baya buk'atar masu zuwa duba shi suna k'ara masa ciwo ne, mu dai muna zaune falo munyi jugum, can sai ga Fulani sokoto tazo duba shi sai da tak'are mana kallo tana wani yatsina sannan ta wuce ciki.
Tare suka fito da Fulani Bingel tana fad'in.
"Aynu ki kula dashi yace baya buk'atar kowa likita zai zo nan da anjima ya dubashi ".
"To angama Fulani".
Abin da nace kenan na koma na zauna, Fulani Sokoto ta bini da wani mugun kallo tana mai ficewa, suma sauran ma'aikatan suka takewa Fulani Bilgel baya suka fice, suka barni ni kad'ai zaune falo kamar wata mayya.
Har doctor yazo ya dubashi yayi masa allurai sannan ya kirani yayimin bayanin magun-gunansa da yanda za'a dinga bashi ya tafi, na nemi guri na zauna ina kallon yanda yake fitar da numfashi da kyar hucin zafin jikinsa kuwa ina daga inda nake ina jiyo zafin.
Ganin alamun yana magana nayi na k'arasa da sauri zuwa dai-dai kansa domin idan ba haka kayi ba ba zakaji mai yake cewa ba, sai ji nayi ya kamo hannuna yarik'e kam ya had'a da hannusa, har sai da naji zafin rik'on ga kuma zafin jikinsa, a haka na zauna ina kallon ikon Allah domin da nayi k'ok'arin janyewa zai hud'e ido yana girgiza kai alamun kar incire, araina nace.
"Sai kace wani k'aramin yaro, kome yake damunsa ma oho?".
A haka har bacci mai nauyi ya d'aukeshi sabida allurar da akai masa na samu na cire hannuna na dawo falo na zauna ina kallom TV films d'in india ne ake duk da bana fahimtar abin da suke cewa amma kallon yana min dad'i sosai, na jima a zaune sai ga Yarima Jalil ya shigo ya zauna na gaishe shi yana tambayar mai jiki nace.
"Yayi bacci ma".
Da haka yayi ta jana da hira jefi-jefi har na mance a tare da waye nake ga Yarima Jalil akwai ban dariya tuni na ware yana bani labaran abin dariya ina dariya, abin da yake burgeni dashi kenan ba ruwansa da girman kai illa abu biyun da sukaiwa rayuwarsa illa ban dasu na fahimci Yarima Jalil na da kirki sosai har yafi Yarima Fudhal ma anawa ganin kenan.
Ya gama bani wani labari ina cikin dariya sai ganin mutum kawai mukayi a kanmu kamar mala'ikan mutuwa haka muganshi a tsaye.
Yarima Jalil ya washe baki yana fad'in.
"Sannu broda ka tashi kenan, ya k'arfin jikin?".
Idan TV d'in dake d'akin tayi magana to shima yayi magana, nima na durk'usa inayi masa sannu wani kallo ya watsomin daya sanya hanjin cikina k'ullewa ba k'aramin k'ok'ari nayi ba wajen rik'e fitsarin da yayi shirin zubomin a wando.
[19/07, 17:42] Nana Sales Aliyu Fbk Mai Quratu Group: *YARIMA FUDHAL*
Na
FIRDAUSI S.A(QURRATUL-AYN).
NAGARTA WRITERS ASSOCIATION®
SADAUKARWA:- Namesy Pheerdauceey Jeeebour
Wannan page d'in naki ne FIRDAUSI SODANGI A cigaba da suburbud'a mana cakwakiyar KWAD'AYI MABUD'IN WAHALA muna tare da ke har zuwa inda al'kalamin ki zai tsaya.
10
Na mik'e tsam na koma waje guda na zauna ina jiran umarninsa.
"Sannu Broda Allah yak'ara lafiya".
Cewar Yarima Jalil kenan yana mai ficewa daga d'akin.
"Ke zo nan".
Na mik'e da sauri na k'arasa wajensa ya kafeni da sexy eyes d'insa da bana iya juran kallonsu, ya jima a haka kafin ya bud'e baki ya fara magana.
"Kada insake ganin ki tare da Jalil".
"To".
Na sake mik'ewa na nufi cikin d'akinsa na d'auko magun-gunansa na d'auko ruwa a robar faro na kawo na ajiye, ina mai b'alli maganin na mik'a masa ya karb'a yasha ya jawo kusun ya koma ya kwanta, sai lokacin na lura k'arfe biyu tayi ashe dubansa nayi ina fad'in.
"Zan iya tafiya?".
Bak'aramin k'arfin hali nayi ba wajen tambayarsa domin bansan amsan da zai bani ba.
Kai kawai ya d'agamin alamun ehh, na mik'e da sauri ina k'ara yi masa Allah sauwak'e na fice daga d'akin duk da ban juya ba amma nasan ni yake kallo.
Kitchen na nufa kai tsaye naje na juye abincin nayiwa Jakadiyya sallama na tafi gida, araina ina tunanin rashin zuwan Saima yau.
"Ko da yake jiki da jini a kace".
***
5:00pm
"Assalamu alaikum wai Aynu tazo".
Aynu dake shara tsakar gidan ta ajiye tsin-tsiyar tana tambayar.
"Waye ya aiko ka Mallam?".
"Ya Sayyadi ne fa na Islamiyya !".
"Au kace ina zuwa".
Yaron da ta kira da Mallam ya fice domin isar da sak'onta.
Aynu ta shige d'aki ta d'auko hijab d'in islamiyyarta tana mai duban Ummanta.
"Umma bari inje wai Ya Sayyadinmu ke kira na".
"To sai kin dawo a kula dai da kyau".
"To Ummata".
Aynu ta sanya ta mutsats-tsan silifas d'inta ta fice.
Yana tsaye jikin bishiyar darbejiyar k'ofar gidan, fari ne d'an siriri mai doguwar fuska sai saje bak'i da yayiwa fuskarsa k'awanya da ka ganshi ka ga tsan-tsan bafulatani, yana sanye da jallabiya fara har k'asa da hula fara da ake kira tashi ka fiye naci.
Aynu ta k'arasa wajensa fuskarta cike da fara'a kamar yanda tasa take, ta d'an rissina ta gai dashi ya amsa yana fad'in.
"Malama Aynu kwana biyu na jiki shiru bakya zuwa makaranta?".
Aynu ta d'anyi murmushi tana mai gyara tsayuwarta tare da fad'in.
"Wallahi Ya Sayyadi aikin dana samu ne sai a hankali, ban cika da wowa gida da wuri ba".
"To ikon Allah adinga dai daurewa ana zuwa".
"Insha Allahu kuwa".
Zuwan Babanta dake shirin shiga gidan ya ka tsesu daga tattau nawar da suke, Ya Sayyadi ya durk'usa ya gaishe da Babanta cikin girmamawa, shima ya amsa fuskarsa fal farin ciki ya wuce ya barsu nan, yana shiga gida Ya Sayyadi yayi mata sallama ya tafi ita kuma ta koma cikin gidan.
Tana shiga taji Ummanta da Baban nata suna tattaunawa akan Ya Sayyadin ita dai bata tsaya taji mai suke fad'iba ta cigaba da aikinta ganin babu wanda ya sakota a zancen.
*** *** ***
Yaune ta kama ranar da za'a fara biyan su Aynu albashi, tun asuba ta tashi zuciyarta fes cike da nishad'i, nan da nan ta kammala komai nata na gidan kafin k'arfe bakwai da yake Zainab ta bata wani k'aramin agogo da shi take amfani, bakwai nayi taci abinci tayi komai ta kama hanyar zuwa gidansu Zainab domin su tafi tare.
Tana isa ta tadda itama ta gama shiryawa suka kama hanya.
Yau dai ta tadda Yarima Fudhal ya war-ware tsaf har ya tashi yayi wanka ya shirya yana zaune gefan katifarsa ta taddashi, ta durk'usa ta gaishe da shi ya amsa fuskarsa cike da fara'a, ta mik'e ta nufi toilet ta kama aikinta.
Tana fitowa ta cigaba da sauran gyare-gyarenta k'arfe takwas akai kiransu za'a bawa kowa kud'insa na aiki.
Su nasu b'an garen har k'ari suka samu daga dubu goma sha biyar zuwa a shirin ba k'aramin dad'ine ya rufe Aynu ba sosai tana tafe tana lissafin abubuwan da zasu siya sai ji tayi taci karo da mutum taja baya da sauri tare da d'ago kai sai taga ashe Yarima Fudhal ne, ya kuwa had'e fuska kamar bashi ne ta ganshi d'azu cikin fara'a ba.
"Bani kud'in !".
Yayi maganar babu alamun sassauci, jiki na b'ari ta mik'a masa yasake kallonta yana fad'in.
"Jeki kawomin breakfast".
Ba musu ta juya ta nufi kitchent domin cika umarninsa.
Haka tayi ta zaryar shirya masa breakfast sai da ta gama ta had'a mai komai ta mik'a masa sannan ta koma gefe tana jira ya gama, komai baya wuce cokali d'aya zuwa biyu yake ci ya gama ta kwashe kwanukan ta mayar ta dawo ta zauna kenan yace taje ta kawo masa fruit, haka ta sake mik'ewa taje ta kawo, ta kuma zauna a gefansa yana daga kishingid'e tana yankawa tana mik'a masa yana sha, musamman apple ta fahimci yana cinsa sosai.
Sai da ya gama ta kwashe ta mayar ta dawo ta zauna ta jira taji yace ga kud'inta ta tafi, amma taji shiru gashi tana jin nauyin tambayarsa sai dai ta dubeshi kaman zatai magana sai taji ta kasa.
Sun jima a haka kafin yamik'e ya shige cikin d'akinsa, ya barta nan zaune tana tufka da war-wara.
"Aynul-hayat !".
Taji ya kira sunanta ta amsa a hankali tana mai nufar d'akin nasa da sallamarta ta sanya kai d'akin.
"Zo nan".
Ya kuma kiranta ta k'arasa inda yake a zaune gefan katifa ta durk'usa tana kallon ikon Allah.
Kud'ine dank'am a gabansa tun daga dollar zuwa dubu-dubu d'ari biyar-biyar 'yan d'ari biyu har zuwa kan naira biyar kowanne bandir-bandir.
"D'ebi duk yanda ki keso".
Aynu ta saki baki tana dubansa, sai take ganin abin kamarma wasa yake mata.
"D'ebi mana".
Ta kai hannu kan 'yan goma ta d'auka, dariya ya d'anyi yana fad'in.
"Sarkin tsoro".
Karb'a yayi ya d'auki bandir d'in 'yan dubu ya mik'a mata, girgiza kai tayi alamu a'a, shiru yayi Yarima yana dubanta cike da mamaki fal cikin ransa.
"Kyauta tace a gareki karb'i".
"A'a nidai ka bani kad'an, sunmin yawa wad'annan".
Jujjuya kud'in yayi tayi na wani lokaci kafin yayi murmushi yace.
"To idan na k'ara miki goma akan naki zaki karb'a?".
Shiru tayi ba tare da ta ce dashi komai ba, ya irgo dubu talatin ya mik'a mata ta k'i karb'a.
"Idan baki karb'i wannan ba sai dai ki rasa kud'in naki duka".
Aynu ta dube shi da sauri ya gyad'a kai alamun da gaske yake, hannu biyu ta sanya ta karb'a tana yi masa godiya, yace baya buk'atar godiya nan da nan taja bakinta ta tsuke.
***
Aynu ce zaune gaban Ummanta tana faman lissafin abin da ya kamata su saya, Ummanta ta murmushi tayi tana fad'in.
"Aynu kenan !, to ai duk lissafin da kike kud'in ba zasu kai ba sai dai asayi abin da ya samu kawai".
"To Umma amma dai ya kamata musayi atamfa ko ta dubu d'aya da d'ari biyu ce, sai a asiyawa Baba yadi shi kuma ya d'inka, sauran sai mu sayi takalma da ta barma ko?".
"Uhmmm yanzu dai d'auki dubu biyu ki kaiwa mai shagon da muke karb'o sabulu, ki bashi dubu kud'insa ne da yake binmu, dubu d'ayan kuma ki siyo silifas ki sayo mana sabulun wanka da wanki tare da makilin".
"To Ummata".
Ta fad'a tana mai mik'ewa tare da d'aukan kud'in ta fice.
A hanya ta gamu da Ya Sayyadi suka gaisa yana fad'in.
"Ina zaki haka da rana tsaka?".
"Ummata ce ta aikeni".
"To masha Allahu muje in taka maki".
Haka suka tafi suna hira jefi-jefi har zuwa shagon tayo siyayyar suka dawo tare har k'ofar gida ya rakota sukai sallama ya tafi.
A ranar dai aka siyawa Aynu sabon hijab da atamfa Daviva guda biyu suka sayi sabuwar tabarma da 'yan kwanuka da cofuna domin nasun duk sun lalace.
Aynu sai jinta take kamar sun shiga wata sabuwar rayuwa, jinta take kamar ba ita ba yau ita ce da sabon d'inki abin da sai dai abata kwance yau kuwa gashi ta d'inka da guminta.
"Alhamdulillahi, Alhamdulillahi ala kulli halin !".
Abin da take ta faman mai-mai tawa kenan cikin ranta cike da nishad'i da jin dad'i.
7:40am
Yau dai Saima ta rigata zuwa gidan, sabida yau ta makara sosai ko da ta gaishe da Yarika k'in amsawa yayi bata damu ba domin tasan halin sa, tayi dukkan abin da ta saba ta gama ta nemi guri ta zauna, har lokacin ko kallonta bai yiba gefe guda kuma ga Saima sai faman wani ciccika take tana batsewa da zaran sun had'a ido da Aynu ta jefe ta da harara.
"Zaku iya tafiya".
Suka ji muryarsa yana basu umarni, ko wacce tamik'e ta fice daga d'akin a hanyane Aynu ta dubi Saima tana fad'in.
"Kwana biyu bakya zuwa har anyi albashi....".
Bata k'arasa maganar ba Saima ta katseta da fad'in.
"Ke kud'in ya dama".
Ta wuce ta barta nan tsaye tana searching d'in maganar Saima.
"Me take nufi da ni kud'i ya dama?".
Kafin ta kai da bai wa kanta amsa sai ganin Yarima Jalil tayi a gabanta fuskarsa fal murmushi yake fad'in.
"Beauty kin b'uya !? ko da yake naga Yayan namu baya buk'atar ganinmu tare".
Aynu ta tsaya tana nubanshi dan ko kad'an bata fahimci inda maganarsa ta dosa ba.
"Zauna nan magana za muyi da ke".
Yayi mata nuni bisa d'an da kalin dake kusa da su, Aynu ta zauna shima ya zauna gefe da ita kad'an.
"Kin san wani abu?".
"A'a sai ka fad'a".
"Wai me yasa Yarima baya son gani na da ke ne?".
"Nima ban sani ba gaskiya".
"Ok".
Shiru ne ya biyo baya na d'an wani lokaci, kafin yasake dubanta yana fad'in.
"D'an juyo nan".
Aynu ta zuyo tana dubansa, ya kai hannu gefan fuskarta yana fad'in.
"Wani abu ya b'ata beauty face d'inki bari in goge miki".
"Jalil.....!".
Suka ji muryar Yarima Fudhal akansu, Yarima Jalil ya sauke hannunsa yana fad'in.
"Sannu da fitowa Broda".
Bai ko dubeshi ba, illa kafe idanuwansa da suka fara rinewa daga fari zuwa ja akan Aynu da yayi, a hankali ya furta.
"Jeki k'arasa aikin ki".
Sum-sum Aynu ta wuce zuwa falon Yarima ita dai tasan ta gama aikin ta, may be wani aikin zai saka ta abin da ta raya aranta kenan.
Mintuna kad'an da zamanta ya shigo fuskarnan babu annuri neman guri yayi ya zauna yana fad'in.
"Had'amin tea".
Da rawar jiki ta mik'e ta zuba masa tea d'in tafa shashshe sosai, yace ka da ta sanya komai illa sugar nan da nan ta had'a ta mik'a masa yasa hannu ya karb'a, tana shirin mik'ewa taji ya jawo hannunta kafin ta ankara sai jin rad'ad'i da azabar zafin ruwan tea d'in tayi bisa hannunta wanda ya ratsa har cikin kwakwalwar kanta.
[20/07, 14:40] Nana Sales Aliyu Fbk Mai Quratu Group: *YARIMA FUDHAL*
Na
FIRDAUSI S.A(QURRATUL-AYN).
NAGARTA WRITERS ASSOCIATION®
SADAUKARWA :-Namesy Pheerdauceey Jeebour.
(RAZ) ku matso kusa wannan page d'in nakune AMRAH, ZAHRA, RABI'ATU....Allah yabar manaku ya k'ara donk'on zumunci da k'aunar juna Inayin ku irin sosai d'innan (Raz).
11
Har cikin kwakwalwar kanta ta jiyo rad'ad'i da zafi na ruwan tea d'in, ta kafe Yarima da idanuwa cike da kallon mamaki mai d'auke da tambayar me nayi maka?.
Shima Yarim ita ya kafe da idanuwa yana karantar yanayinta can ya kau da fuska gefe yana mai naushin hannunsa na hagu da hannun da mansa game da furzar da iska daga bakinsa mai zafi.
Aynu kuwa ta kasa magana illa hawaye dake zarya bisa kuncinta kawai tarik'e hannun da d'ayan da babu k'unar.
Yarima yayi k'asa da kansa ya dafe da hannu na d'an wani lokaci, kafin ya d'ago ya sake kafeta da ido a karo na biyu, tsaki ya d'anja kad'an yana mai sanya hannunsa ya kamo nata daya k'ona ya dubi hannun tare da duban fuskarta.
"Am so sorry...nayi hakanne domin ki fahimci irin k'unar da na keji a duk lokacin dana ganki da Jalil, why me yasa kika kasa fahimta har na kai da yi miki wannan hukuncin?".
Ita dai Aynu kallonsa kawai take domin ko kad'an bama ta fahimtar me yake fad'i, azaba ta isheta hawaye kawai take fitarwa domin kuka mai sauti ma k'in fita yayi daga bakin ta a wannan lokaci.
Kai hannu yayi kan fuskarta da niyan share mata hawayen sai kuma ya fasa, ya dubeta yana fad'in.
"Da zafi sosai ne?".
Kai ta kyad'a masa alamun ehh.
"Sannu yi hak'uri !".
Abin da yace da ita kenan yaja hannunta suka fito zuwa waje, haka yayi ta janta har suka isa b'angaren Fulani Bingel duk inda suka wuce sai a bisu da kallo amma kasancewar Yarima Fudhal ne kowa yasan babu wasa da sun had'a ido da mutum zaiyi k'asa da kansa yana gaishe shi.
Shi kuwa Yarima bai cika niba har sai da muka isa cikin falon mahaifiyarsa, Fulani Bingel na ganinmu ta mik'e tsaye tare da fad'in.
"Lafiya Magaji?".
"Hajiya kira doctor d'inki ".
Fulani Bingel ta bishi da kallon mamaki cike da tambaya.
"Mai ya faru da ita?".
Yarima neman guri yayi ya zauna ya dubi sauran masu aikin dake d'akin.
"Ku bamu waje".
Sum-sum ko wacce ta fice ya rage daga ni sai Yarima da Hajiyarsu.
Fulani dai ta kafeshi da idanuwa tana jiran amsar sa.
Yarima yad'an yatsina fuska kafin ya bata amsa da fad'in.
"K'onata nayi".
"Subhanallah ! garin yaya?".
Cewar Fulani kenan tana mai k'arasowa wajena, taga hannuna yayi jawur ta mai da dubanta kan Yarima.
"Akan me ka aikata wannan d'an yan aikin?".
"Hajiya ita ta jama kanta fa !, na gaya mata bana son ganinta da Jalil ba ta ji ne yarinyar !".
"To dan baka son ganin ta da Jalil sai kayi mata wannan mugun hukuncin ?, mai yasa bazaka fad'amin ba ko kayi mata hukunci dai-dai misali".
"Abin da nake ji araina ne !, shine na gwada mata taji yanda nakeji ko tafi fahimta".
Fulani Bingel sakar baki tayi tana duban sa cike da mamaki ko mamakin me take yi oho?, sai dai ta kalleni ta kalleshi.
Ajiyar zuciya tayi tana fad'in.
"Mai zai hana ka kira likitanka?".
"Haba dai Hajiya Namiji ne fa?".
"Dan namiji ne bazai duba taba".
"Ina ! A'a gaskiya ki taimake ni dai ki kira likitarki dan Allah Hajiya kinji?".
Ya k'arashe maganar kamar zaiyi kuka, ni dai ina zaune ina jin ikon Allah tun da nake da Yarima yaune karo na farko da yayi doguwar magana kuma duk a kaina, ga shi kuma babu ko kunya ko nauyi ko shakka bare jin tsoro yana sanarwa mahaifiyarsa da kansa ya k'ona ni !, nidai sai na nemi hawaye na rasa tsabar mamaki da al'amarin Yarima Fudhal.
Hajiyarsa girgiza kai kawai tayi tana dubana ta d'auki waya bugu d'aya tayiwa likitan bayanin abin da yake faruwa, muna ji likitan ta amsa da cewar ga tanan zuwa da yake wayar a free ta sanya ta.
Hajiya ta ajiye wayar tana kallon Yarima da yayi ta gumi yana kallonta, ta jima tana nazarin Yarima Fudhal ba tare da tace komai ba, haka shima bai kuma fad'in komai ba, baka jin k'arar komai a d'akin sai k'arar A.C da ajiyar zuciyata jefi-jefi sabida kukan da nayi.
Muna haka har Doctor Hafsat ta shigo ta tadda mu, ta gaishe da Hajiya da Yarima Hajiya tayi mata bayanin nice na k'one da ruwan zafi, nan da nan tayimin allura tare da bani magani domin k'unar bata tashi ba bare ace za'a wanke, tayiwa Hajiya sallama ta tafi domin tana bakin aiki ne ta tawo.
Tana fita Hajiya tace.
"Ka da ka sake mai-maita hakan kana jina?".
"Insha Allah".
Abin da yace da ita kenan, yana mai kwanciya kan kusun, Hajiya tace.
"Mai yake shirin faruwa tsakaninka da yarinyar nan?".
Yarima ya mik'e ya zauna tare da dubana yana fad'in.
"D'an bamu waje".
Na mik'e na fice abina dama duk a takure nake jina.
"Ka da dai kacemin sonta ka ke?".
Murmushi Yarima yayi yana sosa k'eyar kansa jin tambayar da Hajiyan tasa take yi masa.
Fulani Bingel tayi ajiyar zuciya domin ta fahimci komai tun farkon tattauna warsu.
"Ka da kamance 'yar aikin kace, 'yar aiki kuwa a gidan nan tamkar bayi ne ko ka mance ne?".
"A'a".
"Kasan ko Mai Martaba bazai tab'a yarda ba idan ni na amince !".
Dammm gaban Yarima ya buga amma ya dake ba tare da yace komai ba, Fulani ta cigaba da fad'in.
"Duk bama wannan ba, kasan cewa ana nema maka auren Gimbiya Safiyya kuwa?".
A firgice Yarima ya dubi Fulani.
"Safiyya kuma ni nace ina sonta ne har da za'a nema min aurenta?".
"A'a zab'in mahaifinka ne, to ita wannan d'in tasan kana son tane?".
"A'a amma ai zan fad'a mata lokaci nake jira, amma Hajiya da gaske kike akan maganar Safiyya?".
"Na tab'a yi maka wasa ne ?".
Yarima ya girgiza kai alamun a'a, yayin da kuma zuciyarsa ke ta aikin bugawa da sauri da sauri hankalinsa idan yayi dubu ya tashi, har sai da Fulani Bingel ta fahimci haka ta dafa kafad'arsa tana fad'in.
"Kada ka d'aga hankalinka Magaji ka nemi zab'in Allah kawai, domin kafi kowa sanin waye Mai Martaba".
"Amma Hajiya ki fahimtar dashi mana nifa gaskiya bana sonta".
"Kai mai zai hana ka sanar dashi, zaifi fahintar maganarka akan tawa ma".
Yarima ya dubi Mahaifiyartasa kafin ya kau da kai gefe zuciyarsa na cigaba da k'una, gefe guda kuma yana tunanin mafita akan wannan batun.
***
Aynu kuwa na fita inda ta saba zama taje ta zauna ta had'a kai da gwiwa tana kuka, ji tayi an dafa kafad'arta ta baya ta d'ago da sauri dan ganin waye?.
Zainab ce ta zagayo ta zauna tana fad'in.
"Subhanallahi !, Aynu mai ya faru kike kuka ya akayi kika k'one ke da ba a kitchen kike aiki ba?".
"Yarima ne Zainab, Yarima ne !".
Aynu ta sake fashewa da kuka tana mai d'ora kanta kan cinyar Zainab, Zainab ta d'an bubbuga bayanta alamun rarrashi tana fad'in.
"Mai kikayi masa?".
"Wai akan Yarima Jalil...".
Nan dai ta kwashe dukkan abin da yafaru ta sanar mata, Zainab tayi ajiyar zuciya tana fad'in.
"Kece bakyaji ai na gaya miki waye Jalil kin k'i yarda, amma abin tambaya kenan Yarima Fudhal yana kishin ganinki da Yarima Jalil?, Idan har kishi yake kenan sonki yake ko?".
"Oho nima nasani jeki tambayeshi".
Zainab dariya tayi domin wasu lokutan tasan Aynu 'yar rigimace ta k'arshe, a fili kuwa cewa tayi.
"A'a mai da wuk'ar bani nakar zomon ba ratayarma ban d'auka ba".
Aynu tad'an kaiwa Zainab dukan wasa, tana fad'in.
"Ni ko sona yake Allah bazan soshi ba mugune wallahi na k'arshe".
Zainab tayi murmushi tana fad'in.
"Ki godewa Allah Aynu samun irin su Yarima Fudhal wuya garesu a yanzu, wallahi nayi miki murna sosai Allah tabbatar mana da alkhairi, ni yanayin soyayyar tashi ne ma ta fara burgeni !".
Wani kallo Aynu ta jefi Zainab da shi mai dauke da harara.
"Wai ke waya gaya miki sona yake ?, nifa bai fad'amin ba".
"Daga jin yanda labarin ya fara kowa kika sanarwa Allah yasan al'amarin so ne yaja hakan, domin idan ba so ba mata nawa ne suke harka da Yarima Jalil a gidan nan amma bai da muba sai a kanki, nasan wata rana zai fad'a miki yana sonki".
"Tab..Allah ma ya kiyaye, dubi fa hannu na wanda yayi maka haka kuma yazo yace yana sonka?".
Cewar Aynu kenan tana mai k'arewa hannunta kallo cike da takaici, ba tayi aune ba sai ji tayi ruwan hawaye na bin fuskarta.
Nan sai suka Zauna Zainab na k'ok'arin ganar da ita amma ita tana faman botsewa da haka har k'arfe biyu tayi basu sani ba, a gurguje suka had'a inasu inasu sukayi gida, dan Aynu ko part d'in Yarima k'in komawa tayi dan kada wani abun ya sake faruwa.
Yarima na dawowa sallah yahau nemanta amma sama ko k'asa ya rasa ta sai Jakadiyya ke sanar dashi sun tafi gida, kwafa yayi yana duban maganinta da aka bata yana tunanin yanda za'ai ta sha domin kada k'unar ta tashi kafin gobe, hankalinsa idan yayi dubu ya tashi, sai dabara tazo masa ya baiwa Jakadiyya ta kai mata domin yaga ta san ta, ba musu Jakadiyya ta karb'a ta nufi gidan su Aynu domin kai mata maganin lokacin kuwa daf da maghriba ne.
***
Ko da Aynu ta koma gida k'in sanarwa Ummanta abin da ya faru tayi, duk da cewar Umman taji muryarta ta canja tayi tambayar duniya akan meya sata kuka?, Aynu tace .
"Babu komai Umma kawai tari na d'anyi".
Nan dai ta k'ok'arta tayi dukkan abin da zata iya ta nufi Islamiyya dawo warta kenan ta shiga d'aki ta cire hijab taji sallama, ta fito domin ganin waye sai taga ashe Jakadiyya ce har Umma ta bata gurin zama.
Aynu ta fito suka gaisa tamik'awa Umma ledar maganin tana fad'in.
"Gashi Aynu maganin naki, Yarima duk ya tashi hankalinsa yace kisha kafin ki kwanta, Allah ya k'ara sauk'i ni zan koma".
"To mungode Allah saka da alkhairi ki gaida gida a yiwa Yarima godiya sosai abisa d'awainiya".
Cewar Umma kenan dake zaune gefen tabarmar da Jakadiyya ta zauna.
Jakadiyya tayi musu sallama ta tafi, Aynu dai mutuwar tsaye tayi tana jira taji mai Umman zata ce da ita.
"Zo nan Aynu".
Taji muryar Ummanta Aynu ta k'arasa kusa da ita ta zauna tana fad'in .
"Gani Umma".
"Fad'amin gaskiya mai ya faru?".
"Dama....dama fa...dama Umma ruwan zafi ne ya zubomin a hannu".
"Amma shine zaki min k'arya kice ba komai tari ki kai".
"A'a Umma kawai banaso hankalinki ya tashi ne ".
Murmushi Umman tayi tana fad'in.
"Aynu kenan, bani hannun inyi miki tofi".
Aynu ta mik'a mata hannun, Ummanta ta kama tayi mata addu'a kafin ta saki hannun tana fad'in.
"Da ace kina k'onewa ansamu gasarar koko anzuba akai ba zata tashi ba, domin k'una sanyi take so, da zarar ansanya gasarar iska na kad'awa har ta bushe shikenan ba zata tashi ba".
"Umma ai yanzuma bata tashi ba kawai dai ja hannun nawa yayi".
"To Allah sauwak'e ya kiyaye gaba ki dinga lura da kyau dai".
"To ummata".
[22/07, 20:22] Nana Sales Aliyu Fbk Mai Quratu Group: *YARIMA FUDHAL*
Na
FIRDAUSI S.A (QURRATUL-AYN)
SADAUKARWA:-Namesy Phirdauceey Jeebour.
NAGARTA WRITERS ASSOCIATION®
12
Washe gari wayar gari akai Mai Babban d'aki wato Mahaifiyyar Mai martaba babu lafiya, baki d'aya hankalin kowa ya tashi da ka shiga gidan zaka san babu lafiya musamman Yarima Fudhal da Mai Martaba sunfi kowa shiga damuwa da ciwon Mai Baban d'aki.
Ciwo anwayi gari da shi rana d'aya amma kai kace tayi shekara tana yi, tuni aka d'ebeta sai asibiti likitoci uku ne akanta amma sun kasa gano musabbabin ciwon nata bare har asan abin da za'ayi akai.
Ni dai tun da muka doshi gidan ni da Zainab mukasan babu lafiya agidan, muna shiga kuwa muka samu bayanin Babar Mai martaba ce ba lafiya tana asibiti, Yarima ma nacan hospital d'in Zainab ce ta tayani gyara b'angaren Yarima sabida k'unar dake hannuna muna gamawa na nufi gida kuwa domin Saima ma da tazo ta tadda abin da yake faruwa bata zauna ba ta koma gida abinta.
***
Daf da maghriba kuwa Hajiyar Mai Martaba tace ga garin kunan, ba Sarkin ba duk wanda yaji mutuwar baiwar Allahn nan dole yayi kuka mace kamila mai hak'uri da dattako mai son addini da son iyalinta ga uwa uba barkwanci da faram-faram.
Gaskiya bak'aramin rashi su Yarima sukayi ba gari ya d'auka kaf da rasuwar baiwar Allahn nan, ni dai ina zaune a gida najiyo a babban masallacin unguwarmu ana sanarwa cewa za'ayi jana'izar ta da safe idan Allah ya tashemu da rai da lafiya, ba wani shak'uwa mukai da ita ba amma naji mutuwarta sosai babu abin da yafara fad'omin arai irin so da shak'uwa dake tsakaninta da Yarima fudhal koya zaiji aransa oho?
"Allah sarki Yarima Allah baku hak'uri da dangana !".
Abin da nace kenan ina yankewa Ummata farce ta amsa min da.
"amin Aynu mutuwa ai dole ce sai dai in lokaci baiyi ba duk kuwa irin so da shak'uwar da kukai da mutum dole wataran zaka barshi".
Jikina yayi sanyi da kalaman Ummata sai naji hawaye nabin gefan fuskata har dai da na tuna Ummata da Baba na su kad'aine duniyata sune farin cikina su kad'ai na sani sune nake kalla inji dad'i, yanzu dole watara zan barsu ko su barni, duniya kenan babu matabbata Ubangiji Allah kasa mu dace ka kashemu da imaninmu amin.
***
Ka sancewar rasuwar da akai nasan kuma cin koso da jama'a yanzu sun cike gidan hakan ya saka nak'i zuwa washe garin da akai rasuwar, nayi zamana agida amma wunin ranar nayi shine cike da tunanin gidan.
washe gari kuma ranar biyu da rasuwar nayi niyar zuwa kodan inyi gaisuwa sai dai na tashi da wani irin matsanancin ciwon kai, Zainab data biyomin mu tafi har da ita asa bakin inyi zama duk da cewar naso zuwa amma Umma da Zainab suka kafe kan in zauna har zuwa gobe inga yanda jikin nawa zaiyi.
"Haba Fudhal kayi hak'uri kad'au dan gana abisa rashin Hajiya da mukayu mutuwa kasan dole ce amma sai da hak'uri, muma da muke mata munyi hak'uri bare kai namiji ?".
Cewar Yayarsu Aunty Sadiya kenan data iske Yarima d'akinsa shi kad'ai kwance kamar wani mara lafiya.
Falonsa abokansa ne cike amma shi ya wuce bedroom ya kwanta kamar mai bacci amma azahiri ba baccin yake ba domin duk abin da ake yana ji.
Ta gaji da magana amma ko d'ago kai baiyi ya kalleta ba, ta tashi ta fice daga d'akin ta koma wajen mahaifiyyarsu Fulani Bingel tana sanar mata.
Fulani tasan Yarima ya shak'u da Hajiya sosai amma tasan akwai wani abu daban da yake damunsa domin tasan waye Yarima tasan halayyarsa sarai, hakan yasa tayi murmushi kawai ta dubi Aunty Sadiya tana fad'in.
"Rabu dashi kawai akwai abin da dai yake damunsa, kar ki damu".
"Kamar ya ! Wanne abune yake damunsa haka?".
"Zanyi miki bayani wani lokacin".
Fulani Bingel ta wuce ta koma falo inda tabar jama'arta ke jiranta, ta bar Aunty Sadiya nan d'akin tana tunanin me yake damun d'an k'anin nata?.
Yarima kuwa gani yayi kwanciyar babu abin da zata haifa masa illa tarin damuwa mai yawa, hakan yasa shi mik'ewa ya fito harabar gidan yana dube-dube kome yake nema oho?.
Duk inda ya wuce sai gai dashi ake wani ya amsa wani ya wuce kawai da haka ya isa har filin shamaki inda bayi da ma'aikatan gidan ke zaune, suka durk'usa baki d'aya suna gai dashi ya amsa tare da k'urawa Zainab ido, yana tunanin indai bai mance ba tare yafi ganinsu da Aynu may be zata iya sanin wani information akanta.
"Ke zo nan".
Yayi nuni da Zainab ta mik'e da sauri tabi bayansa domin har ya bada baya ya tafi.
Wani guri yaja ya tsaya inda babu mutane yayi shiru kansa a k'asa bai ce da ita komai ba, har Zainab ta gaji da tsaiwa taji kaman zata fad'i, amma babu daman zama can ya d'anyi ajiyar zuciya ba tare daya d'ago kai ba yake fad'in.
"Ke kinsan Aynul-hayat ko?".
"Ehh Yallab'ai?".
"Ok mai yasa 2days bata zoba, ko gaisuwa ma tak'i zuwa ?".
"Ba tajin dad'i ne".
Yarima Fudhal ya d'ago kai da sauri yana dubanta, jin maganar da ta doki kunnensa.
"Me yake damunta?".
"Tace dai ciwon kai ne".
A jiyar zuciya ya saki mai k'arfi wadda har sai da Zainab ta dubeshi, ya cigaba da fad'in.
"Bani address d'inta".
Nan da nan Zainab ta bashi bayanin gidansu Aynu, tana gamawa ya juya ya tafi ya barta nan tsaye babu ko godiya Zainab tabi bayansa da kallo aranta tana fad'in.
"Ikon Allah maganar minti biyar amma ashafe awa guda da wani abu anayi, lallai Yarima na musam-manne Matarsa na da aiki kuwa".
Ta juya abinta itama tabar wajen ta koma inda ta taso.
•••
Aynu dai bata samu ciwon kan ya lafa mata ba sai dare wajen k'arfe takwas bayan sallar isha'i kenan, ta tashi tayo alwala ta hau gabatar da sallolin da bata samu ta iyayi ba, ta idar kenan tana addu'o'in data saba ko yaushe sukaji sallamar Yaro a tsakar gidansu.
Umma dake zaune gefe daga inda Aynu take sallah ta amsawa Yaron Sallama, ya gaishe da Umma yana fad'in.
"Wai ana kiran Aynu a waje".
"Aynu kuma da daren nan?".
"Ehh haka yace min Aynu yake nema".
Aynu ta sallame addu'ar tana fad'in.
"Kace ina zuwa".
Yaron ya fice Aynu ta dubi Ummanta tace.
"Yanzu haka Ya Sayyadi ne dan yaga yau banje Islamiyya ba".
"Ehh nima nayi tunanin hakan !, tashi kije kada ki jima dan kinga dare yayi".
"To Umma ni dama bana jin dad'i, tsayuwarma bazan iya ba muna gaisawa zan dawo".
Aynu tasa takalminta ta fice.
Dake dare ne kuma unguwar duhu basu da wadatar nepa, hakan yasa bata iya shaida kowane ba, yana tsaye jikin darbejiyar k'ofar gidan cikin k'ananun kaya daya tabbatarwa da Aynu ba ya sayyadi bane domin ta sanshi gwanine wajen shigar jallabiyya yau kuwa taga sab'anin haka, ta waiga bata ga kowa ba illa dai wanda ke tsaye jikin bishiyar.
Dake wa tayi tare da k'arawasa sai dai tun kan takai da isa wajen zuciyarta tahau bugun uku-uku ga kuma k'amshin turarensa daya doki hancinta wanda bata iya manceshi ko a wane yanayi taji shi zata gane nasa ne.
Shi kuwa tun fitowarta ya kafeta da idanuwa yayin da wani sanyin dad'i ya mamaye zuciyarsa, har yanaji aransa kamar yaje ya d'aukota don hutar da ita daga tafiyar da take.
Ta k'arasa wajen da sallam cikin siririyar muryarta ya masa mata ta d'an rissina ta gaisheshi tare da fad'in.
"Kayi hak'uri ban d'auka kai bane...".
Sai kuma tayi shiru, shima baice komai ba yayi shiru tare da nad'e hannunsa bisa k'irjinsa, a hankali ta d'ago kai duk da a duhu ne amma ta fahimci kallonta yake.
"Ya k'arin hak'uri kuma?, Allah yaji k'anta ya gafarta mata".
"Amin nagode sosai".
"Mai ya hanaki zuwa kwana biyu?".
Aynu ta gyara tsayuwarta sosai tana wasa da yatsun hannunta, ta bud'e baki ta bashi amsa.
"Banajin dad'ine".
"Shine dalilin da yasa kika k'i zuwa?".
"Ehh".
"Ko dai kinajin haushi nane akan k'onakin da nayi".
"A'a wallahi bani da lafiya sosai musamman yau yanzune ma nad'anji sauk'i".
"Ok".
Ya fad'a yana mai mik'o mata ledar dake ajiye gefansa Aynu ma ko lura da ita batayi ba.
Batayi magana ba haka kuma bata karb'a ba, shima kuma baice komai ba illa kafeta da idanuwa da yayi.
"Dole fa ki dinga karb'an kome na baki banason gaddama kamar yanda banaso inyi kyauta adawomin da ita".
Aynu tasa hannu ta karb'a tare da fad'in.
"Nagode sosai Allah k'ara girma da arzik'i yaji k'an hajiya".
Murmushi ne ya kufce masa wanda yasa fararen hak'oransa baiyana waje sosai yaji dad'in addu'ar Aynu agareshi, kamar yanda yake jin dad'in sautin muryarta akunnensa yana kuma jin dad'in kasan cewarta atare da shi ko da ba zaice da ita komai ba yanaso ya dinga kallon beauty face d'inta any time.
Aynu tsayuwar tafara isarta har k'afafunta na kakkarwa, amma ta gaza iya furta masa zata shiga gida.
"Kije gida sai da safe".
Taji muryarsa ta doki kunnenta, domin batayi tsammanin zai sallame ta ba a yanzu.
"To nagode sosai, a gaida su Hajiyarku".
Ta juya ta tafi domin tasan ba lallai ya amsa ba, shi kuwa bin bayanta da kallo yayi har ta shige cikin gidan nasu ya jima anan tsaye kafin ya nufi wajen da yayi parking motarsa ya shige ciki ya zauna yana tunanin da baisan kona mene ba haka kawai yaji zuciyarsa tab'aci duk da baya raba d'ayan biyun tafiyar Aynu ce taja masa hakan.
Aynu nashiga gida samun guri tayi kusa da Ummanta ta zauna tana fad'in.
"Ashe Yarima ne ba Ya Sayyadi ba".
"Yarima kuma Allah sa lafiya dai?".
"Lafiya k'alau Umma wai yazone yaji lafiya ko k'unarce take damuna banjeba kwana biyu".
"Allah sarki yaron na da kirki kuwa".
Aynu ita dai ajiyar zuciya tayi ranta tana fad'in.
"Dan bakisan waye shi bane kikace haka Umma".
A fili kuwa cewa tayi.
"Kin ga harda kaya yazomin da shi kona mene oho, bari in duba ingani".
Ta fad'a tana mai jawo ledar ta bud'e magunguna tana gani aciki sai kayan snack a ciki da juice gefe guda kuma taga wata guntuwar ta kadda ta bud'e aranta tana fad'in.
"Ko mene a ciki?".
"Kisha kowanne da k'aidarsa maganin ciwon kannaki ne".
Aynu tayi shiru tana sake karanta takaddar tare da tunanin inda yasan kanta na ciwao sai kace aljani?.
Ta fad'a aranta.
"Umma magani ne ashe tare dasu snack !".
"Allah sarki sai kisha maganin to, kyasamu sauk'in ciwon angode masa sosai Allah saka masa da alkhairi".
*YARIMA FUDHAL*
Na
FIRDAUSI S.A (QURRATUL-AYN).
NAGARTA WRITERS ASSOCIATION®
SADAUKARA:-Namesy Phirdauceey Jeebour.
Ina kike ne? Miemie Bashir (Queen) matso kusa wannan page d'in naki ne domin jin dad'inki kawai.
13
***
WASHE GARI
Cikin ikon Allah Aynu ta wayi gari lafiya k'alau kamar ba tayi ciwo ba.
"Umma gaskiya maganin nan yana da kyau kinga k'unar hannun sab'a takeyi har ta warke kenan?".
"To masha Allah haka ake so ai, Allah ya k'ara lafiya".
"Amin Ummata".
Sallamar Babanta ce ta katse su daga hiran da suke ya shigo ya nemi waje ya zauna, Aynu tayi masa sannu da zuwa tana mai mik'ewa domin kawo masa kunu da k'osansa na karyawa, taje ta d'auko ta ajiye a gabansa ya bud'e kwanun ya kurb'i kunun kafin ya dubi Aynu yana fad'in.
"Ya k'arfin jikin naki?".
"Naji sauk'i sosai Baba".
"Allah k'ara lafiya, haka akeson ji dama".
"Amin Baba".
"Yau ba zaki je gidan Sarkin ba ne?".
Ummanta ta fad'a tana mai duban gefan da Aynu ke zaune, Aynu ta d'an yatsina fuska kafin tace.
"Ban jin fita wallahi yau Umma ki bari har gobe naje".
Babanta yayi murmushi yana fad'in.
"Kiyi zamanki ki huta 'yar gidan Umma ki k'ara samun sauk'i sai kije".
"To Baba".
Baban nata ya sake dubanta karo na biyu fuskarsa fal murmushi yana yinsa da komai Aynu ta d'auko kama ce kawai ta d'auko ta Ummanta kamar antsaga kara.
"Ina Umar Faruq kuwa Aynu?".
"Ohh Baba Ya Sayyadi Umar wai? yana nan".
"Yaron na da kirki sosai kullum ya ganni har k'asa yake gaishe ni yauma fitar nan da nayi kinga naira d'ari biyar ya bani wai ayi cefane, nayi-nayi ya barta amma yak'i dole na karb'a".
Aynu tad'anyi murmushi tana wasa da yatsun hannunta take fad'in.
"Ai yana da kirki sosai akwai shi da kyauta ko a islamiyya".
"Bashi ne nake gaya maka yazo har gidan nan wancen satin ya gaishe ni ba".
Umma ta fad'a tana mai wasa da sandar hannunta.
"Ai inaji araina kamar akwai wani abu da yaron yake b'oyewa".
Cewar Baba kenan yana mai kallon fuskar Aynu cike da murmushi, itama murmushin take duk da kuwa fad'uwar gaban da taji ya tsanan ta a cikin zuciyarta, haka kawai taji hiran ta fara gundurarta tamik'e tsaye tana fad'in.
"Bari ingyara d'aki Umma".
Ta wuce ta barsunan suna ta tattaunawa, daga k'arshe sukabar hiran Ya Sayyadi Umar aka koma ta Yarima, Aynu duk tana jinsu tayi luf a d'aki domin duk cikin su babu wanda take ji hirarsa nayi mata dad'i, sun jima suna hirar kafin Baba yamik'e ya fita waje yabar Umma nan zaune.
Sai sannan Aynu ta fito domin sama musu abin da zasuci da rana kuma.
°°°
Yarima kuwa ranar wuni yayi yana zuba idon ganin Aynu amma har dare shiru, haka ya wuni kamar mara lafiya jama'a da dama suna d'auka alhinin rasuwa ne, amma anashi b'angaren abun da yakeji aransa game da Aynu shiyafi komai d'aga masa hankali da kuma mamaki.
Har ya yanke shawaran zuwa k'ara dubota domin ya zaci ko ciwon ne har yanzu ya hanata zuwa, amma sai dai ya share domin bayaso zak'ewarsa tayi yawa ta rai na shi.
Hakan na d'aya daga cikin abin da yasa Yarima k'in yin soyayya duk cikin shekarun da suka wuce, domin shi mutum ne mai son girma mai son a girmama shi baya son raini ko kad'an, a ganinsa da zaran ya furtawa budurwa yana sonta to raini zai iya shiga ciki shiyasa yake kau da kansa akan duk wata 'ya mace.
Amma kuma abin mamaki sai gashi rana guda ya kamu da son 'yar aikinsa kuma 'yar miskinai so mai tsanani kuwa, duk da yasan abune mawuyaci Aynu ta rainashi domin yarinyar nada tsoro sosai duk da k'arancin shekarunta ya fahimci yarinyar nada hankali da nutsuwa da sanin ya kamata, uwa uba kuma ya yaba da tarbiyarta, ba kamar sauran 'yan matan da suke son saba.
Murmushi yayi yana mai dafe kansa da yaji yana masa ciwo kad'an-kad'an, ya san hakan na faruwane sabida rashin ishash-shan bacci da kuma hayaniya domin shi baya son hayaniya ko kad'an shine dalilin da ya sama yake wuni a d'aki abinsa.
Maganin da ke aje gefan katifarsa ya d'auka yana mai bud'e robar faron da ya aje gabansa yasha maganin ya koma ya kwanta nan da nan kuwa bacci yayi awon gaba dashi. (ASUBA TA GARI YARIMA).
***
Washe gari tun da wuri kaman yanda ta saba tayi dukkan abin da ya kamata ace tayi kafin ta tafi, tayiwa iyayenta sallama ta kama hanya domin yau alhamis suna azumine bata tsaya bata lokacin neman abincin safe ba.
Ko da ta biyawa Zainab harta tafi sai sannan taga lokaci ashe har takwas ta kusa setting agogonta ya goce kenan? ta gaida Babah Tasallah ta fito a gurguje ta nufi gidan domin bata son yin late ko kad'an.
Bata tsaya ko ina ba sai cikin falon Yarima Fudhal tayi mamakin ganin falon fes dashi kamar jama'a basu zaunaba kai tsaye cikin d'akinsa ta nufa da sallamarta ta tura k'ofar d'akin tasa kai.
Yana kwance abinsa lullub'e da bargo ya takure waje guda kaman mai jin sanyi hakan yasa ta kashe AC dake ta famanyi ita kad'ai a d'akin har lokacin baccinsa ya ke hankalinsa kwance bai ma san ta shigo ba, ta wuce toilet tahau aikinta har ta gama bai farkaba ta fito tashare d'akin ta goge amma bai ta shiba ta wuce falon ta sake sharewa ta goge, ta lek'a d'akin taga baccinsa yake har lokacin ta dawo falo ta zauna, ganin baccin nashi bamai k'arewa bane yasa ta fito daga part d'insu zuwa cikin gidan.
Taje tayiwa Jakadiyya gaisuwa tare da Uwar soro, sannan ta wuce wajen Fulani Sokoto tana shiga cikin falon ta tadda Fulani zaune tare da Yarima Jalil da Jalila suna ta hiransu ta durk'usa ta gaishe su tare da yi musu gaisuwa, shi kuwa Yarima Jalil tun da tashiga ya kafeta da idanuwa ko k'iftawa ba yayi, ciki-ciki Fulani ta amsa ki dan taga ba 'yar aikin wajenta bace? Oho.
Aynu ta mik'e ta fito daga b'angaren ta nufi wajen Fulani Bingel itama falon cike ta taddashi tayi musu gaisuwa suka amsa Fulani na fad'in.
"Kwana uku kenan ban ganki ba, ko k'unarce ta dameki?".
"A'a k'una ta warke ma banajin dad'i ne dai, sai yau naji dama-dama".
"Allah k'ara afuwa".
"Amin".
'Yan d'akin suka amsa banda Aunty Sa'ida da take ta faman banka mata harara ita dai Aynu kanta na k'asa batama san tanayi ba.
Aunty Sadiya ta dubi Fulani da murmushi tana fad'in.
"Wannan ce Aynul-hayat d'in?".
"Ehh ".
Fulani ta bata amsa, murmushi ta ya fad'ad'a a fuskarta tace.
"Kai amma taci sunan nata wallahi Hajiya".
Ita ma Fulani murmushi tayi tana fad'in.
"Sosai kuwa".
Aynu ta mik'e tana fad'in.
"Zan koma aiki".
Ta fice daga d'akin suka bita da kallo, Aunty Sa'ida taja tsaki.
"Kai wallahi Aunty Sadiya da kayan haushi ki ke !, meye wani abin kyau anan yarinya bak'auya yar talakawa".
"Ke ! banson jin wannan sha shancin anan kinji ko ina ruwanki to".
Aunty Sa'ida taja tsaki, tare da cizon leb'e.
Fulani tace "Allah ya shiryeki Sa'ida meye wani abu ajikin talaka da har zai zama abin k'i, ka da insake jin wannan maganar abakin ki".
Tafiya take kanta ak'asa tana wasa da yatsun hannunta sai ji tayi anjata gefe guda ta d'ago kai da sauri domin ganin waye?, ajiyar zuciya tayi tare fad'in.
"Zainab kin ban tsoro wallahi !".
Zainab tayi murmushi taja hannunta gefe guda suka zauna tana fad'in.
"Ke kinsan abin da yafaru kuwa?".
"A'a sai kin fad'a !".
Aynu ta bata amsa, Zainab ta cigaba da fad'in.
"Gaskiya Aynu Yarima na sonki sosai, bakiga yanda hankalinsa ya tashi ba kwana biyu da baki zoba".
Tsaki Aynu taja kad'an tare da fad'in.
"Amma ke kam kin fiye zato wallahi !, daga kinga ya shiga damuwa sai ki ce akai nane, mutuwafa akai musu kuma kinsan yanda suka shak'u da ita fa?".
Zainab abin ya bata dariya sosai ta kanne tana fad'in.
"Ba wani wallahi, shifa ya nemeni na bashi kwatancen gidanku, kuma wallahi bakiga yanda hankalinsa ya tashi ba sanda nace masa baki da lafiya, sai da yaji ciwon kai kike sannan naga hankalinsa ya d'an kwanta ko bai zo gidan naku ba ne?".
Aynu shiru tayi tana duban Zainab har sai da Zainab tad'an zungureta sannan ta dawo daga tuanin da take.
"Dama a wajenki yasan ciwon kai nake?".
"Ehh mana, yazo gidan naku kenan?".
"Ehh yazo da dare har da magun guna da kayan snack ya kawomin".
Zainab ta fad'ad'a murmushinta cike da sonjin bayani .
"To mai yace da ke?, fad'amin dan Allah yace yana sonki ko?, ki ke wani b'oyemin !".
"Sai kiyi kuma !, ke kam kina da matsala wallahi, ke nifa ko yace yana sona banjin zanso mutum irin sa".
"Sabida me?".
"Haka kawai".
"Aynu kenan ke kam baky fahimta wallahi".
"Ehh naji kinga mubar wannan maganar, kinsan kuwa Ya Sayyadi Umar sai faman zarya yake a gidanmu nifa har ya fara bani tsoro".
"Meye na tsoro kuma?, ta tsuniyar gizo dai bata wuce k'ok'i, amma nidai nafi sonki da Yarima !".
Zainab takai maganar tana dariya, Aynu ta mik'e tana turo baki wai ita adole fushi tayi ta wuce tabar Zainab nan zaune, ganin da Zainab tayi da gaske tafiya za tayi shine yasa ta mik'e itama ta bi bayanta da sauri tana kiran sunanta, amma Aynu ta toshe kunnuwanta tayi tafiyarta.
Ko da ta koma d'akin ya farka daga baccin yana zaune gefan katifarsa ya had'a kai da gwiwa, da sallama ta shiga d'akin ya d'ago da sauri yana dubanta, sai kuma ya kau da kai gefe guda kamar bayason ganinta a can k'asan zuciyarsa kuwa farin cikin ganinta ne fal ransa.
Har gabansa tazo ta durk'usa tana gaisha shi ya amsa can k'asan mak'oshi, Aynu ta d'an gyara zamanta sosai tana fad'in.
"Ya k'arin hak'uri kuma?, nagode sosa da kulawa, nazo na tadda kana bacci ne shine nak'i tashinka fatan banyi laifi ba?".
Bai ko kalle taba bare ya nuna mata ya san dashi take magana, bata damu ba ta cigaba da fad'in.
"Ko kana buk'atar wani abu ne?".
Shiru yayi na wani lokaci kafin yabud'e baki a hankali ya fara magana kamar wanda ake yiwa dole.
"Kije falo".
Aynu tamik'e ta fito falo ta zauna tana jiran fitowarsa, ya shafe kusan mintuna talatin kafin ya fito falon sai faman tashin k'amshi yake cikin wani farin yadi mai shara-shara ana iya hango singlete d'insa ta ciki baisa hulaba illa taje sumarsa da yayi takwanta luf yaune karo na farko data ganshi cikin kayan hausawa tun dawowarsa.
Ya zauna gefan kusun yana duban Aynu, can ya kau da kansa ya mai dashi kan screeng d'in wayarsa da ke ringing.
SAIMA DARLING
Yagani bisa screeng d'in wayar tasa yasa hannu ya d'aga ahankali tare da sanyata a headfree.
Daga can b'an garen tanaji ya d'aga tahau fad'in.
"Haba Yarima !, ashe yanda na d'auke ka baka d'aukeniba!, mai yasa kake wulak'anta mai son kane?".
"Sabida banayin abu a rufe".
Ya bata amsa, cikin d'aga murya kad'an tace.
"Kamar ya kenan?".
"Kamar yanda ki kaji na fad'a".
"Ok amma mai yasa tun ran birthday d'inka baka nemeni ba, ni ina nan ina zaman jiran kiranka".
"Na manta ne".
Daga can b'arin Saima ajiyar zuciya tayi, domin ba kad'an takejin ciwon maganar da Yarima keyi mata ba duk da tanajin dad'in sautin muryarsa, ya katseta da fad'in.
"In kin gaji zan aje wayar?".
"A'a kawai banajin dad'in reply d'in kane".
"Time d'in breakfast d'ina yayi zaki iya kira anjima?".
Ya kashe wayar ya ajiye gefe, duk maganar da yake idonsa na kan Aynu yana karantar yanayinra, ita kuwa kanta na k'asa tana wasa da wani d'an k'aramin zobe kod'ad'd'e dake hannunta.
Duk tanajin maganganun da suke amsar k'arshe daya bayar da kuma kashe wayar shi yafi komai bata mamaki da Yarima, amma data tuna waye shi?, sai mamakinta ya kau domin tasan zaiyi fiye da abin da yafi haka indai Yarima ne, b'an garan jiji da kai, girman kai da d'agawa ga shegen miskilanci da wulak'anci tun da take bata tab'a ganin mutum irin yarima ba abin nasa yayi yawa.
Ya katseta da fad'in.
"Yau wannan banjin zata zo?, inaga zan koreta aiki ne kawai !, jeki kawomin breakfast ".
*YARIMA FUDHAL*
Na
FIRSAUSI S.A(QURRATUL-AYN).
NAGARTA WRITES ASSOCIATION®
SADAUKARWA:-Namesy Phirdauceey Jeebour.
Wannan page d'in naki ne *Ashnurpyar* Nagartacciya Allah yabar zumunci amin.
14
BAYAN KWANA BIYAR
Zaune take can gefe daga inda yake yanata aikin danne dannan wayarsa, tafiya take sonyi amma ya hanata ko da fita cikin gidan ne.
"Zo nan Aynu".
Taji muryarsa yana kiranta tamik'e ta k'arasa wajen da yake zaune nesa da shi kad'an.
"Matso mana".
Ta d'an kuma matsawa kad'an, murmushi yayi yaga alamun bata da niyan zuwa kusa dashi mik'ewa yayi yazo daf da ita ya mik'a mata wayar hannunsa yana fad'in.
"Kalli ki gani".
Aynu takai dubanta bisa screeng d'in wayarsa wata farar mace ta gani kyakykyawa ajin farko tana sanye cikin alkyabba pink data k'ara bayyanar da kyanta.
"Gimbiya Safiyya kenan".
Ya fad'a yana mai duban fuskarta.
Murmushi tayi Aynu tare da furta.
"Amma ta had'u sosai tayi kyau wallahi".
Yarima Fudhal ya kafeta da idanuwa yana dubanta kafin yad'anyi murmushi kad'an.
"Ita ce ake son had'ani aure da ita !, nan da 3days zatazo gidan nan, amma ni gaskiya bana sonta !".
"To amma kuma kake ajiye hotonta?".
"Meye ra'ayinki akanta?".
Ya tambayeta ba tare daya bata amsar tambayar ta ba, Aynu ta dube shi da murmushi saman fuskarta.
"Ta dace da kai sosai kuwa".
"Uhmmm haka ki kace?".
"Ehh mana".
"Wannan zab'in iyayena ne, amma ni bata daga cikin zab'ina".
"Sai kabi zab'in iyayen naka ai, domin nasan basuyi maka zab'in tumun dare ba".
Tsaki Yarima Fudhal yaja yana mai duban Aynu cike da takaicin amsar da take bashi, dubanta ya sakeyi a karo na biyu yana fad'in.
"Bawai na nuna miki bane domin ki bani shawara akan zab'in da zanbi, na nuna miki ne domin.......".
Sai kuma yayi shiru maganar ta tsaya a mak'okwaronsa, dai-dai da shi gowar Saima ya d'auke dubansa daga kan Aynu ya karb'i wayarsa tare da fad'in.
"Tashi kije".
Aynu ta mik'e da sauri ta fice dama ta takura da al'amarin Yarima sosai, Saima ta bi bayanta da kallon tuhuma, har sai da Aynu ta fice sannan ta dawo da kallonta kan Yarima tana fad'in
"Kana buk'atar wani abu ne?".
"A'a jeki kawai".
Ya bata amsa batare daya dubeta ba.
DARE
8:20PM
Da dare misalin k'arfe takwas da mintuna ashirin Aynu na zaune bisa tabarmar da tayi sallah gama cin abincinta kenan akai sallama tare da fad'in.
"Wai Aynu tazo inji Yarima".
Dammm gabanta ya buga har sai da tad'an lumshe ido tare da karanto addu'a cikin ranta afili kuwa ta furta.
"Yarima kuma !, me zaiyimin da daren nan?".
"A'a tashi kiji tunda kiga mutum ya tako har inda kike yazo yana da abun da yakawo shi mai muhimmanci ne musamman manyan mutane ai sai da babban dalili suke zuwa wajen mutum".
Umma ta fad'a tana mai duban inda 'yar tata take zaune duk da ba gani take ba.
Aynu tayi ajiyar zuciya gami da tashi daga cin abincin dama ta gama ta wanko hannu ta zari hijabi ta fice.
Yana tsaye jikin katangar gidan nasu hannunsa rik'e da wayarsa yana dannawa d'aya hannun kuma na cikin aljihun wandon jeans d'insa, aranta ta furta.
"Ko ina dai ba'a gajiya da sana'ar".
Da sallama ta k'arasa wajensa Yarima ya amsa tare da fad'a d'a murmushinsa yana duban ta, Aynu tayi saurin yin k'asa da kanta sabida irin kallon da Yarima Fudhal yake ji fanta dashi idanuwanta bazasu iya d'auka ba.
Shiru ne ya ziyarci wajen kafin Yarima yayi k'arfin halin katse shirun da fad'in.
"Ke na keson aura Aynu !, zuciyata tafi aminta dake akan wacce iyayena suka zab'amin amma...".
Sai kuma yayi shiru yana mai haska fuskarta da hasken wayarsa domin ganin yanayin ta, Aynu dai kanta yana k'asa amma zuciyarta na bugun uku-uku wanda ta rasa dalilin faruwar haka.
"Ko bakya so na?".
Taji saukar muryarsa akaro na biyu yana tambayarta, maimakon ta bashi amsa kawai juya wa tayi tabar wajen ta shige gida ta barshi nan tsaye.
Yarima yabi bayanta da kallo ba tare da yayi yunk'urin da katar da ita ba yanaji zuciyarsa nayi masa zafi, tare da jin haushin abin da tayi masa.
***
Kwance yake bisa lallausar katifarsa sai faman juyi yake yana son yin bacci amma hakan ya gagare shi, tunanin abin da Aynu tayi masa d'azu shine yake damunsa, amma babban abin da yafi damunsa bai wuce jin tsoron kada Aynu tace bata son saba.
Lokacin ya jawo wayarsa ya duba agogo k'arfe biyu da kusan rabi, ya d'an ja tsaki tare da cigaba da danna wayar da alamu akwai abin da yake nema.
Can ya danna wata number tare da karawa akunnensa, sai da wayar ta kusa tsinkewa sannan aka d'aga tsaki Yarima yaja tare da fad'in.
"Kai fa d'an rainin wayo ne Anwar !, mai kake nufi ?, da ba zakayi picking bane?".
Cikin muryar bacci Anwar ya amsa da fad'in.
"Kai fa prince kafi kowa matsala wallahi ban da ni wa zaka kira da tsakad daren nan ya d'aga".
Yarima Fudhal yaja dogon tsaki kamar ya yanke wayar sai kuma ya fasa yana fad'in.
"Kaga malam maganace mai muhimmanci ka tashi daga baccin".
"Akan me?, fad'i maganarka kawai ina jinka".
"Mene ma'anar idan ka furtawa mace kan sonta tayi tafiyarta batare data baka amsa ba?".
Daga can b'angaren Anwar dariyace ta kwace masa har da rik'e ciki, ba k'aramin k'ok'ari yayi ba wajen saita kansa domin tambayar tazo masa a bazata da kuka mamakin wanda yayi tambayar, bai kai da baiwa Yarima amsa ba yaji ya katse wayar yasan dama za'ayi hakan, kira ya sakeyi harta katse Yarika yak'i dagawa sai da ya kira sau uku sannan ya d'aga batare da yayi magana ba.
Anwar cikin dariya ciki-ciki yahau fad'in.
"Am sorry Prince kawai naji mamakin tambayar da kayi min ne wallahi, da gaske soyayya kake son sanar dani ka fara ko kuwa me?".
"A'a kawai inason jin amsar ne".
Anwar yayi murmushi tare da fad'in.
"To kabari har gobe mayi magana mana".
"A'a yanzu nake so shiyasama na kiraka ai, da naso har gobe ai sai goben zan neme ka".
"Hakane, amma gaskiya a gani na duk macen da kace kana so tayi tafiyarta ta barka nan batare da amsa ba to d'ayan biyu ne ko kunyar baka amsa take ji ko kuma bata son ka...".
Kafin ya kai da k'arasa maganar Yarima Fudhal ya katse wayar ya wullata can k'arshen katifarsa tare da yin tsaki, sai kuma yamik'e ya zauna maganar Anwar nayi masa yawo akai.
"Aynu kunyata take ji, ko kuma so nane batayi ?".
Kai ya girgiza yayin da zuciyarsa ta tsinke tsoro ya ziyarce shi, sai ya samu kansa da fad'in.
"Allah yasa kunyace ta hana ta bani reply !".
Hhhhhhh to fa !, su Yarima Fudhal anshiga taskun soyayya, to amma aganinku Aynu zata so Yarima Fudhal kuwa?.
Nabar muku wannan amsar Reader.
Kuyu hkr da wannan page d'in babu yawa, nagode sosai masoyana kuna raina koyaushe.
*YARIMA FUDHAL*
Na
FIRDAUSI S.A (QURRATUL-AYN).
NAGARTA WRITERS ASSOCIATIONS®
15
8:00am
Zaune Anwar yake gefen kusun yana duban Yarima Fudhal cike da tsokana yake fad'in.
"Amma dai kowa ya ganka yaga wanda yajik'e da mayen so, amma kace min kai ba soyayya kake ba?".
Yarima dake kwance gefe ya dora hannunsa na dama bisa fuskarsa kamar bacci ko motsi baiyi ba, bare ya kula da maganar da Anwar yake masa.
Aynu ce ta fito daga cikin bedroom hannunta rik'e da moopa ta d'an risina tana fad'in.
"Na gama zan gyara nan".
Yarima ya mik'e ba tare daya dubeta ba ya wuce cikin d'akin yana fad'in.
"Sai ka ta so ko".
Anwar yabi Yarima da kallo kafin ya dawo da dubansa kan Aynu yana fad'in.
"Mene sunanki".
"AYNU".
Ta bashi amsa kai ya gyad'a tare dayin murmushi yana fad'in.
"Nice name, a wacce unguwa kike?".
Yarima ne ya banko labulan d'akin ya fito cike da b'acin rai, kallon daya watsawa Aynu shine yasa ta shan jinin jikinta tayi k'asa da kai ba tare data baiwa Anwar amsa ba.
Anwar ya sanya dariya mai sauti tare da mik'ewa yabi bayan Yarima cikin d'akin yana fad'in.
"Abin da nayi zato ya tabbata Prince, wai me yasa kake b'oyemin ne?, tun da nazo nake karantar yanayin ka akan yarinyar nan".
"Sabida kamai da zancena gist mana !, kasan ni bana wasa a cikin al'amura na".
"Ehh to zancen wasa ya wuce, amma ka da dai kacemin wannan Yarinyar kake so?, domin naga kishinta k'arar bisa fuskarka".
"Ehh ita nake so !, wani abun ne?".
"A'a amma fa yarinyar tayi wallahi, duk da dai kanta ba'awaye yake ba".
"Ehh naji koma dai mene, amma kasan wani abu ?".
"Menene fad'amin inajinka".
Saima ce ta shigo da Sallama tare da fad'in.
"Breakfast d'inka yayi ready".
"Ok ina zuwa".
Ta juya tafice, Anwar ya dubi Yarima tare da fad'in.
"Ina jinka".
"So nake kajawo hankalin wata yarinya, ma'ana kayi soyayya da ita".
"Ban fahimce kaba?".
"Ok abin da nake nufi, inaso kasa wata yarinya ta soka, ni so nake hankalinta ya tashi daga kaina ya koma kanka, Yarinyar tana so nane hakan na neman jawomin matsala ".
"Wacce matsala kenan?, amma kuma wacce yarinya ce?".
Yarima Fudhal yayi murmushi tare da kau da kansa gefe.
"SAIMA 'yar gidan Alhaji Buba, ita nake so kayi soyayya da ita, so nake kamar yanda ta furta tana sona inaso ta furta da bakinta bata so na !".
"Amma mai yasa ka yanke wannan hukuncin, Yarinya kamar Saima mai tsada tace tana sonka amma kace a'a?".
"Yes bana ra'ayin 'yan mata irin tane, jiya da Yamma Mai martaba ya kira ni ya sanarmin Baban ta Alhaji Buba da kansa yazo nan wajen Mai Martaba akan yana so ya had'a zuri'a da mu, wato dai yana so ya auramin 'yarsa, bayan kuma anmin zab'in Safiyya, amma kasan amsar da Mai Martaba ya bawa mahaifinta?".
"A'a sa ka fad'a".
"Cewa yayi ai namiji mijin mata hud'u ne, babu komai sai a had'amin mata biyu in aura aini Yarima ne kuma magajin gobe, wannan dalilin yasa na kasa daure zuciyata har sai da naje na furtawa Aynu ina sonta, sai dai bata bani amsa ba har yanzu, hakan namin ciwo sosai jiya ko bacci kasa yi nayi".
"To ka had'asu duka ukun mana".
"Bana ra'ayin hakan, kawai ka yimin abin da nagaya maka".
"To amma idan Saima ta dawo kaina, ita Safiyyan ya zakayi da ita?".
"Banyi tunani akan taba, sai na gama da wannan".
"Amma kuma idan ta furta bata sonka ni take so, rabuwa zanyi da ita kome?, dan nima gaskiya ba lallai ya kasance in so ta ba".
"Wannan ya rage naka karabu da ita ko ka aure ta, inkaso zaka iya son ta bai dame ni ba, amma nidai buk'ata ta tace bata so na".
Anwar ajiyar zuciya yasaki mai k'arfi yana mai kallon Yarima cike da tunanin al'amarinsa, shikam yasan tun yana yaro tare suka taso da Yarima amma har yanzu ya gaza fahimtar halayyar Yarima, shi wani irin murd'ad'd'an mutum ne, sai ka kasa gane inda yasanya gaba.
"Kayi shiru ko kana buk'atar lokaci ne?".
"A'a zanyi yanda kace, amma kana ganin ita wannan Yarinyar zata so ka?".
"Ban dai sani ba?, amma shirun ta na bani tsoro".
Anwar ya girgiza kai da murmushi saman fuskarsa yana fad'in.
"Babu komai Allah ya shige mana gaba".
"Amin".
Suka mik'e suka fito zuwa falon, komai ready kai tsaye wajen abinci suka nufa sukayi breakfast, suna ci suna tattaunawa domin falon babu kowa sai su kad'ai.
Zaune take bisa da kalin dake farfajiyar Shamaki babu kowa wajen sai ita, tayi zurfi cikin tunani domin ba tasan ma Yarima Fudhal na tsaye bisa kanta ba, ya kira sunanta yafi sau a k'irga amma bata amsa ba.
Hakan ya sashi zama kusa da ita tare da sanya hannu yad'an girgiza kafad'arta, firgigit ta farka tare da mik'ewa da sauri tana duban Yarima, Yarima Fudhal murmushi yayi mata yace.
"Zauna mana".
Aynu ta koma ta zauna amma duk ata kure take jinta.
"Me kike tunani?".
Ya tambayeta Aynu tayi k'asa da kanta tana duban tafin hannunta.
"Babu komai".
Ta bashi amsa, girgiza kai yayi alamun bai yadda ba.
"Bana son k'arya kodai tunani na kike?".
"A'a !".
Ta kuma bashi amsa, Yarima yayi ajiyar zuciya tare da kafeta da idanuwa har lokacin murmushin fuskarsa bai d'aukeba.
"Aynul-hayat !".
Ya kira sunanta da wata irin murya wadda tasanya tsigar jikin Aynu tashi, har tad'an rintse ido kad'an, hannunsa ya sanya bisa tafin hannunta yarik'e, ya cigaba da fad'in.
"Ki fad'amin mana, ko kunyata kike ji?".
Aynu ta girgiza kai, tana mai k'ok'arin janye hannunta amma yarik'e kam.
"Bafa zan cika ki ba, har sai kin bani amsar tambayar da nake miki".
Aynu dai tayi shiru sai motsa bakinta take amma kuma maganar tak'i fitowa, su Zainab ta hango suna nufo wajen kusan su biyar da dukkan alamu sungama aikin sune sunzo su huta domim duk a wajen suke hutawa.
Ta kafe su da idanuwa tsoro ya k'ara kama ta, jikinta har wani rawa yake Yarima ya juya yana duban inda take kallo murmushi yayi yana fad'in.
"Indai baki bani amsa ba sai dai su taddamu ahaka, danni kinsan babu ruwana !".
Aynu tahau girgiza kai kawai, bai zata ba sai jin saukar ruwa yayi akan hannunsa ya kalleta da sauri yana mai sanya hannu ya d'ago fusakarta, afili ya furta.
"Kuka kuma?, Yi hak'uri share hawayen kada suzo su gani wasa nake maki fa n".
Ya cika mata hannun yana murmushi, ya mik'e tsaye ya zuba hannuwansa cikin aljihun wandonsa yana kallon yanda taketa k'ok'arin share hawayen amma wasu na zubowa, sosai abin yake burgeshi sai yaji dama su dauwama haka yana kallonta.
K'arasowar su Zainab ce tasan yashi barin wajen yana fad'in.
"Zaki zo kisame ni ne".
Zainab tak'arasa wajen Aynu tana fad'in.
"Lafiya Aynu?".
Harara ta sakar mata tare da juyar da kai gefe, sosai take jin zafin rik'e hannunta da Yarima yayi.
"Wai ke mene yake damunki ne?".
"Babu komai".
Ta bawa Zainab amsa, Zainab tace.
"A'a wallahi nasan da wani abun, yanzufa naga Yarima yabar wajen nan, wannan ruwan hawayen kuma fa?".
Tsaki Aynu taja tana fad'in.
"Ke kam kin shiga uku da tambaya".
"Ehhh naji, ai ni dake iya wuya muna tare".
Aynu tayi murmushi ta juyo ta kalli Zainab tana mai bata labarin abin da ya faru, ajiyar zuciya Zainab tayi tare da fad'in.
"To ke mene ra'ayinki akan Yarima Fudhal, son shi ne ba kyayi ?".
*YARIMA FUDHAL*
Na
FIRDAUSI S.A (QURRATUL-AYN).
NAGARTA WRITERS ASSOCIATION®
16
Hello makaranta
Hope na sameku lafiya?
Ya komai, ya kowa?
Kuyi hak'uri dan Allah zaku dinga ganin post d'ina ko yaushe insha Allah amma ban da ranar Friday sabida wani dalili.
Nagode sosai da sosai.
"wai ni ya zanyi ne Zainab !, Yarima ya matsamin akan lallai sai yaji ina sonsa ko bana sonsa?".
"To wai ke mene ra'ayinki akansa ne !, nima kaina na kasa gane maki ko son sane bakyayi?".
Aynu ta girgiza kai cike da jimami.
"Nima har yanzu nakasa tan-tancewa ina sonsa ko bana sonsa, abin da kawai nasani ina jin tsoro ne sosai?".
"Tsoson me kuma?".
"Yarima yafi k'arfina Zainab !, mai Yarima zaiyi da ni?, 'yar miskinai kuma baiwarsa niba 'yar kowa bace Zainab !, Yarima yana tak'ama da kud'i da mulki mafiya yawan al'ummarmu na yanzu musamman masu kud'i da masu mulki sunfi son AURE KWARYA TABI KWARYA, ina jin tsoron abin da zaije ya dawo ne".
Zainab dogon tsaki taja cike da takaicin maganganun da Aynu ta fad'a.
"Toke mene zai dame ki, bafa ke kika ce kina son saba shine yace yana sonki, ni dai shawarata agare ki kada ki bari damarki ta wuce ki, kiyi 'kok'arin yin amfani da damarki, ki sanarwa Yarima kina sonsa, sauran lamarin ki barwa Allah komai kiyi ta addu'a da yardar Allah komai zaizo cikin sauk'i".
Zainab ta nisa tana mai kallon Aynu dake share kwallar dake k'ok'arin zubo mata bisa fuskarta ta cigaba da fad'in.
"Aynu kina son Yarima !, ki yarda da hakan kuma, kawai tsoro da fargaba ne sukafi tasiri a zuciyarki shiyasa kika kasa fahimtar cewa kina son sa !".
Aynu murmushi tayi tana mai duban Zainab, Zainab kai ta gyad'a mata itama fuskarta d'auke da murmushi ta dafa kafad'ar Aynu tana fad'in.
"Zan tayaki da addu'a sosai, amma kada ki bari Yarima ya sub'uce miki, domin ke kikafi dacewa da Yarima Fudhal".
Sosai Aynu taji dad'in shawaran Zainab agareta, rik'o hannun Zainab tayi tana fad'in.
"Nagode ! Nagode !! Nagode !!! Zainab Allah yabar mutare".
"Amin".
Shela aka hauyi a cikin gidan na cewar tawagar Gimbiya Safiya ta sauka aje a tarbota.
Da sauri su Aynu suka mik'e suka nufi waje.
Jerin motoci goma ne sukai parking a k'ofar gidan, wani dogari ya taka da gudu yaje ya bud'e k'ofar motar, cike da tak'ama da izza Gimbiya Safiyya ta sako k'afa ta fito, mace doguwa fara kyakykyawa ajin farko tana sanye da farar alkyabba wacce ta rufe dukkan jikinta, inbanda hannunta da k'afarta sune kawai a waje, takalimin k'afarta mai gashine shima fari iya had'uwa ta had'u k'arshe.
Aynu sai taga tafi kyau afili ma fiye da a hoto data ganta, take taji wani abu ya ziyarci zuciyarta taji ta raina kanta sosai domin babu abin da zata nunawa Gimbiya Safiyya indai kyaune zai sa aso mutum to tabbas da Yarima baice yana sonta ba, domin Gimbiya Safiyya kyakykyawace ta k'arshe.
Tana fitowa aka hau yi mata ruwan fure tare da tawagarta bayi mata biyar ke biye da ita, kai tsaye wajen Mai Martaba dake tsaye ta nufa tayi gaisuwa, sannan muka rufa mata baya zuwa cikin gidan.
Kai tsaye muka nufi b'angaren Fulani Sokoto da ita, tana tafe anayi mata ruwan fure tare da kirari har zuwa cikin falon Fulani Sokoto.
Yarima Jalil da Jalila duk suna zaune falon tare d ma'aikatan Fulani, muna shiga Fulani ta fito daga cikin d'akinta tana yiwa Gimbiya Safiyya sannu da zuwa, rungumeta Gimbiya Safiyya tayi tare da yinn kiss d'in kuncinta tana fad'in.
" I Miss u my Mom !".
Ta juya kan Yarima Jalil shima abin da tayiwa Fulani haka tayi masa, sannan ta juya kan Jalila itama haka tayi mata, mudai sakar baki mukayi muna kallon ikon Allah dan wannan ya zame mana saban al'amari aganinmu idan zata rungumi Fulani da Jalila ai bai kamata ta rungumi Yarima Jalil ba?.
Neman guri tayi ta zauna tana fad'in.
"Ku bamu waje ko?".
Duk kanmu muka mik'e muka fito zuwa waje, kowa ya kama gabansa, ni da Zainab neman waje mukayi muka zauna muna hira, bamu jima ba akayi kiran Zainab a b'angaren Fulani Bingel, ta barni nan zaune gashi ni inba Zainab ba bana shiga harkar kowa nan nayi ta zaune har zaman ya isheni na mik'e nima na nufi b'angaren Fulani Bingel tunanina inje intaya Zainab aikin da take, ko ba komai yafi zaman da nake ni kad'ai.
Ina tafe ina 'yan wak'e-wak'ena sai ji nayi anjawo hannuna cike da tsoro na bud'e baki zanyi ihu yasa hannunsa ya rufan bakin yana fad'in.
"Sarkin tsoro !".
Fuskarsa d'auke da murmushi, ajiyar zuciya na saki tare dayin k'asa da kaina, Yarima Fudhal ya tsareta da idanuwa yana fad'in.
"Yau dai kinga kishiyarki ko?".
Aynu batasan sanda ta jefeshi da wat uwar harara ba, Yarima yayi murmushi yana mai cigaba da fad'in.
"Mene na kishi a kaina kuma?, bayan bakya sona?".
Sai lokacin Aynu ta lura da abin da tayi kunya ta rufeta sosai, murmushi yayi mai sauti.
"To yau dai sai kin fad'amin kina sona ko bakya so na?".
Aynu tayi shiru tana wasa da yatsun hannunta.
"Baki ce komai ba?, ko bakya so na?".
Ta girgiza kai alamun a'a.
"To kina so na?".
Ta gyad'a kai alamun ehhh, tana mai rufe fuskarta da tafin hannunta, murmushin dake kan fuskar Yarima ya sake fad'ad'a, sosai yake jin wani sanyin dad'i na ratsa dukkan sassan jikinsa, har yanajin kamar ya rungumeta tsabar farin ciki.
"AYNU...!".
Ya kira sunanta da wata irin murya, bata d'ago kanta ba illa amsawa da tayi kawai tana jiran taji mai zai ce.
BAN HAK'URI
Ku k'ara hak'uri dani dai, naso nayi muku typng mai yawa sakamakon jiya banyi muku post ba, sai dai Allah bai yarjemin ba wlh bbu chaji awayana yanzu kuma kunata jirana shiyasa na k'ok'arta nayi muku wannan zuwa anjima insha Allahu indai na samu chaji zaku sake jina nagode sosai da kulawa.
*YARIMA FUDHAL*
Na
FIRDAUSI S.A(QURRATUL-AYN).
NAGARTA WRITERS ASSOCIATION®
SADAUKARWA:-Namesy Phirdauceey Jeebour.
17
Ya cigaba da fad'in.
"Tabbas naji dad'i sosai da jin amsar data fito daga bakin ki, yau rana ce ta musamman agare ni da bazan tab'a mancewa da ita".
Yayi shiru yana mai cigaba da kallonta, har lokacin Aynu bata iya d'ago kanta ba, sanya hannu yayi ya d'ago kan nata yana mai duban fuskarta cike da so da k'auna, Aynu ta rintse ido domin bata iya juran kallonsa, sakin fuskarta yayi ya ce.
"Hak'ik'a kin bani farin ciki wanda nake fatan d'orewarsa har aba da !".
"Bari inje Mai Martaba na kira na, zan zo yau da dare gidan ku !".
Kai kawai Aynu ta gyad'a masa ya tsaya yana kallonta kamar kada ya tafi, da k'yar dai ya juya yabar wajen.
Aynu tabi bayansa da kallo tafiyarsa kanta abar burgewa domim Yarima idan yana tafiya da gaba d'ayan jikinsa yake tafiya, gyaran muryar da ta jine ya sanyata juyawa da sauri domim ganin waye?.
Yarima Jalil ne tsaye yana binta da kallo ya nad'e hannunsa ak'irjinsa fuskarsa babu yabo babu fallasa.
Aynu tad'an risina ta gaishe shi, ya amsa tare da fad'in.
"Ya had'u ko Yayan nawa?".
Yayi maganar yana mai d'aga mata gira, murmushi Aynu tayi ba tare data iya cewa dashi komai ba.
"Anyi masa mata to !, dama kin barshi kindawo wajena Beauty".
Aynu dai batace komai ba, ya d'an matso kad'an zuwa wajenta adai-dai kunnenta ya rad'a mata.
"Dani kika fi dacewa, nine zan baki dukkan k'auna !, duk naji abin da yake fad'a miki ki watsar da batunsa, ki fuskanci batuna domin dai ga matar da zai aura nan, bayan ita kuma akwai wacce akayi magana su biyu zai aura ya angwance !".
Ya k'arashe maganar cikin dariya ciki-ciki.
Aynu da sauri ta dubeshi da kallon tuhuma tana son tabbatar da maganarsa, gira ya d'aga mata tare da wani guntun murmushi a saman fuskarsa.
"Ko baki yarda dani bani?".
"A'a na yarda mana, amma ni nace maka akwai wani abu atsakanin mune ?".
"Baki fad'aba amma idanuwanku sun shaida hakan, kiyi tunani sosai akan Fudhal dani Jalil waye zaifi dacewa da rayuwarki ?, indai har zaki yarda da soyayyata zanbar dukkan wani abu mai muni da nake aikatawa kuma zan rayu dake ke d'aya babu wata ".
Yayi shiru yana karantar yanayinta kafin yad'an cije leb'e ya cigaba da magana.
"Shin aganinki wanda zai auri mace kamar Safiyya zaiyi tunanin kuma auren wata 'ya mace ne, ki tuna bayan ita akwai wata, itama kuma ba baya ba wajen kyau da kud'i da komai n".
"Zan barki kiyi tunani akan hakan duk shawaran da kika yanke zaki iya fad'amin".
Ya juya yabar Aynu da jijiyoyin jikinta baki d'aya sun tsinke tsoro ya ziyarci zuciyarta sosai, take taji zuciyarta nayi mata zafi wajen Zainab d'in da bataje ba kenan tayi tafiyarya gida aganinta zatafi samun nutusuwa da kwanciyar hankali idan ta koma gidan.
Sai dai ba anan gizo yake sak'arba ko da ta koma gida kasa aikata komai tayi inbanda aikin tunani babu abin da take yi, aranta tanaji Yarima Fudhal ya cuceta, duk da k'asan zuciyarta ya kasa gasgata hakan.
Ummanta tayi tambayar duniya ko akwai abin da yake damunta amma Aynu tace babu komai, daga k'arshe da taga Umman ta damu sai tace kanta ne yake ciwo tasha magani tayi kwanciyarta.
***
Haka Aynu ta kwana bacci sai dai b'arawo, amma a cikin daren sai da tasamawa kanta mafita, duk da wani b'angaren na zuciyarta ya kasa yarda da hukuncin data yankewa kanta.
Washe gari kuwa ko da takoma aiki abin da ya kaita kawai tayi, kuma daman ta tarad su Yarima sun fita tun asuba hakan ba k'aramin dad'i yayi mata ba, amma tana gama aikin da zatayi neman guri tayi falo ta zauna tare da fuskantar wani k'aton frame na hoton Yarima Fudhal da aka d'aukeshi gaba d'ayansa yana sanye da farar coat da wando fari hatta takalmi da agogon hannunsa fari ne, sosa Aynu takeson hoton tun ba yanzuba haka kawai takanji dad'in ta zauna tana kallon hoton domin kamar kace Yarima ya amsa hoton ya d'auku sosai.
11:30am.
Basu dawo ba sai k'arfe sha d'aya da mintuna ya turo k'ofar d'akin ya shigo cike da sallama, Aynu bama tasan ya shigo ba domin tayi zurfi cikin tunani, wani dad'i yaji alokacin da idonsa yakai inda Aynu take kallo murmushi yad'anyi tare da k'arasawa wajen da take zaune ya dafa kafad'arta.
A firgice ta d'ago kai sai kuma ta saki ajiyar zuciya ganin Yarima.
Turo k'ofar da akaine ya sasu juyawa baki d'ayansu, Gimbiya Safiyya ce ta shigo cikin takun k'asaitar nata tabisu da wani kallo wanda Aynu takasa tan-tance kona menene?.
"Wace wannan?".
Ta jefawa Yarima tambaya, Yarima Fudhal ya nemi guri ya zauna batare daya bata amsaba, sai ma fad'i daya hauyi.
'kawomin breakfast Aynu".
"A'a ta barshi ai tafe muke da shi, Larai...!".
Gimbiya Safiyya ta kira wata mai aiki dake bakin k'ofa, Larai ta shigo hannunta d'auke da tire ta ajiye gaban Gimbiya Safiyya data nemi waje kusa da Yarima Fudhal ta zauna.
Larai ta juya ta fice, Gimbiya Safiyya ta d'auki Apple ta kai masa baki Yarima ya kau da kansa gefe yana fad'in.
"Tea nake buk'ata Aynu zoki zuba min".
Gimbiya Safiyya ta kaiwa Aynu wani kallon wulak'anci tana fad'in.
"Au dama baki fita ba, fita ki bamu waje !".
"Babu inda zata domin kafin zuwanki ita ke ci da ni".
"To yanzu tun da nazo ba sai ta huta ba?".
Takai maganar tana hararar Aynu, Aynu tayi k'asa da kanta ba tare da tace komai ba.
"Zo ki serving d'ina".
Ya sakewa Aynu magana, Aynu tamik'e tazo tayi serving komai ta koma gefe ta zauna.
Gimbiya Safiyya tad'auki kofin tea d'in takai masa bakin wai zata ci da shi ya d'auke kansa tare da fad'in.
"Na gaya miki bana buk'ata".
"Amma kasan aure zamuyi?, mene danna ci da kai tun yanzu ai treaning nake yi".
Yarima tsaki yaja yana mai kau da kansa gefe cike da takaici, Gimbiya Safiyya ta sake duban Aynu cike da masifa tana fad'in.
"Wai ke wacce irin macace akace ki fita ko?".
Aynu tamik'e ta fice aranta tana jin zafin wulak'ancin da Gimbiya ke yi mata, amma ak'asan zuciyarta sai taji babu komai domin ita 'yar aiki ce kuma baiwa ita kuwa 'ya ce ga Sarki guda.
Yarima Fudhal bai yi magana ba har Aynu ta fice tana goge kwallar dake gefan idonta, ransa idan yayi dubu yab'aci take yamik'e ya fito shima yabar mata d'akin.
Ran Gimbiya yab'aci sosai ta fito itama ta nufi b'angaren Fulani Sokoto tana kuka wai Yarima Fudhal yafifita Baiwa akanta ?.
Rarrashinta Fulani tayi tare da fad'in.
"Ki kwantar da hankalinki zan san abinyi dani yake zancen !".
Jalila dake zaune gefe tsaki taja tace.
"Kema dai Aunty Safiyya kin manta waye Fudhal ne?, tun da kin taka kinje wajensa ai kuwa sai abin da kika gani !, shi Allah na tuba baka shiga harkarsa ba ma ya wulak'anta ka bare kuma ka shiga....!".
"Ke gidanku nace !, rufemin baki dan taje wajensa meye a ciki?, ina nan da kwanaki kad'an mijin tane?".
Cewar Fulani kenan cike da fad'a, Jalila tsaki taja tana k'uk'uni.
"Nifa Momy ba haka nake nufi ba, Allah ya baku hak'uri".
Ta fad'a tana mai mik'ewa ta fice daga cikin d'akin.
Yarima Fudhal na fitowa neman Aynu yahauyi lungu-lungu amma bai ganta ba, sai da ya gaji da nema ya tsaya jikin windown wani d'aki sai yadinga jiyo shash-shek'ar kuka bayan d'akin, zaga yawa yayi domin ganin waye yake kukan?, Aynu ya gani ta had'a kai da gwiwa a hankali ya taka zuwa wajen tare da kiran sunanta yana mai kama kafad'unta ya d'ago ta, fuskarnan shab'e-shab'e da hawaye hannu yasa yahau share mata yana fad'in.
"Yi hak'uri kinji !, mene abin kuka kuma?".
Aynu ta janye jikinta daga nasa tana yi masa wani mugun kallo ta juya masa baya, k'ara juyo da ita yayi ta kuma juyawa masa baya ganin da yayi tana k'ok'arin barin wajen ne yasa shi shan gabanta yana fad'in.
"Wai lafiya kuwa?".
Tsaki tad'anja tana mai ratsewa ta gefansa tabarshi nan tsaye bin bayanta yayi da kallo, zuciyarsa na k'una akan abin da tayi masa yaso binta amma kuma sai ya fasa.
D'aki ya koma ya kwanta yana tunanin laifin da yayi mata har tayi fushi dashi, jiya dai sun rabu lafiya amma kuma yau tana fushi dashi kodan yace zaije bai jeba?.
Sai kuma tunanin abin da yafaru d'azu ya fad'o masa arai.
"Safiyya ce tajawo komai kenan?".
Ya fad'a cikin ransa mik'ewa yayi zaune tare da fad'in.
"May be kishi ne !, zanyi k'ok'arin shawo kanta".
Abin da yafurta afili kenan ya mik'e ya fito daga d'akin zuwa waje, ya sake dubawa amma bai gantaba daga k'arshe ya tambayi Jakadiyya tace masa ta tafi gida tun d'azu, tsaki yaja aransa ya nufi b'angaren Mahaifiyarsa.
Wunin ranar haka Yarima yayi shi sukuku da shi, b'angaren Aynu ma haka abin yake.
Ya so ya bari har dare yaje wajenta ko yasamu nutsuwa cikin ransa, amma kuma ya kasa daurewa zuciyarsa nata faman azalzalarsa k'arfe hud'u da mintuna a shirin yayi parking motarsa bakin layin gidansu Aynu.
Ya fito ya kulle motar ya taka har zuwa k'ofar gidan tun kafin ya k'arasa ya hango ta tsaye da wani zuciyarsa sai da ta buga yayi k'arfin halin k'arasawa ya tsaya nesa dasu kad'an.
Yan da suke hiran Aynu na d'an murnushi abin sosai yake sosa ran Yarima, ji yayi kaman yaje ya shak'e wanda suke tare, amma dai ya daure ya cigaba da tsaiwa har sai da wani yaro yazo wucewa yace masa ya kirawo masa Aynu.
Aynu na sane dashi tunfarkon shigowarsa layin ta ganshi amma ta kau da kai suka cigaba da hirar da suke da Yasayyadi Umar.
"Aynu kije inji wancan mutumin".
Yaron ya fad'a yana mai nuna Yarima Fudhal.
Tare suka d'ago ita da Yasayyadi suka dubi inda Yarima yake tsaye ya had'e girar sama data k'asa.
"Waye wancan d'in?".
Ya Sayyadi ya jefa mata tambayar yana mai kallonta, Aynu ta k'ak'alo murmushi tana fad'in.
"Shine wanda nake yiwa aiki ai !, Yarima Fudhal ne".
Kai kawai Ya Sayyadi ya gyad'a yana fad'in.
"Jeki dawo to zan jiraki domin akwai maganar da zamuyi".
"To".
Abin da tace kenan, ta taka zuwa wajen Yarima wanda tun tawowarta ya kafeta da idanuwa yana kallonta, da sallama tak'arasa wajen tana mai kau da kanta gefe, mai makon ya amsa sallamar sai cewa yayi.
"Waye wancan?".
"Ya Sayyadi Umar kenan, malamin islamiyyar mune".
Ta bashi amsa, Yarima ya cize leb'ansa na k'asa yana mai cigaba da fad'in.
"Anan ma Islamiyyar kuke kenan?".
"A'a yazo duba Ummata ne".
"Dubiyar anan waje ake yinta?".
"A'a rakoshi nayi zuwa waje".
"Kinsan tsayin lokacin danayi anan, nasan kuma kafin zuwana may be kun jima tsaye".
"Ehh nasan kazo mana !".
Da sauri Yarima Fudhal ya dubeta jin amsar k'arshe data bashi, cikin kasa lallliyar murya ya furta.
"Meke faruwa ne Aynu?".
"Babu komai n, yi hak'uri na barshi tsaye bari inkoma".
Bata jira mai zai ce ba ta juya kawai ta barshi nan tsaye, Yarima binta yayi da kallo yama rasa mai ya kamata yayi.
Ya bita ko ya rabu da ita ne????.
Hello makaranta
Sai dai fa kuyi hak'uri dani domin alk'alamina bazai iya zayyane muku irin son da Yarima Fudhal ke yiwa Aynul-hayat ba, kamar yanda girman kai da jiji da kai ba zasu bar Yarima Baiyyanawa Aynu irin son da yake yi mata.
Kawai sai dai ku ayyana irin son a cikin ranku....!.
ASHA KARATU LAFIYA.
*YARIMA FUDHAL*
Na
FIRDAUSI S.A(QURRATUL-AYN).
NAGARTA WRITERS ASSOCIATION®
SADAUKARWA:-Namesy Phirdauceey Jibour.
18
Yana cikin wannan tunanin wayarsa dake hannunsa tayi ringing, ya d'aga yakara a kunnensa ba tare daya duba yaga waye mai kiran ba.
"Haba My...! Abbana yazo har gida anyi magana fa !, amma ko ka kirani mu tattauna batun auren mu...!".
Cire wayar yayi daga kunnensa ya duba screen d'in wayar sunan Saima ne d'od'ar bisa screen d'in, guntun tsaki yaja tare da mai da wayar kunnansa, ta cigaba da fad'in.
"Duk da ance mu biyu zaka had'amu zan amince ne kawai sabida son da nake maka.... !".
Cikin b'acin rai ya katse ta yana yana fad'in.
"Duk naji amma ki sani duka ku biyun babu wacce nakeso aciki, zaki iya kashe wayar !".
Ya fad'a yana mai kashe wayar ya jefata cikin aljihun wandonsa, ya mai da kallonsa kansu Aynu dake tsaye har lokacin suna hira.
Tsaki yaja ya juya kawai ya bar wajen zuciyarsa cike da sak'e-sak'e da kokwanto kala-kala, tare da dumbin tunanin nemawa kansa mafita tunkafin lokaci yak'ure masa.
Saima kuwa yana kashe wayar hawaye ya fara zarya bisa kuncinta zuciyarta na zafi da k'una, a haka Momynta tazo ta tadda ita, dafa kafad'arta tayi tana fad'in.
"Haba Saima !, har zuwa yaushe ne zaki samawa kanki mafita abisa muguwar damuwar dakika d'orawa kanki !, nad'auka damuwarki ta kau tunda har iyaye sunyi magana ?".
Saima ta fad'a bisa cinyar Momynta da ta zauna kusa da ita cikin kuka ta hau fad'in.
"Momy Yarima Fudhal ne !".
Tsaki Momyn tayi tana fad'in.
"Me kuma yayi miki yanzu?".
"Yace duka mu biyun wai baya sonmu !, Momy ji nake kamar zan iya mutuwa wallahi indai har na rasa Fudhal arayuwata !".
A jiyar zuciya Momyn tayi tana mai d'ago da 'yar tata zaune, ta kalli fuskarta sosai.
"Haba Saima kamar ba 'ya mace ba, kamarki ki zauna kinayi namiji kuka !, ni anawa ganin tun da har ya furta baya sonku ki hak'ura da auren sa kawai, ki danne zuciyarki akan Yarima ki barshi bari na har abada !".
"Momy taya hakan zai yiyu?, ina son Yarima sosai wallahi Momy ki taimake ni dan Allah !".
"Bani da wani taimako da zan iya yi miki wanda ya wuce addu'a, sannan zan sanar dake wani abu da baki saniba arayuwa, Saima..! akan ki auri namijin da baya sonki ke kike sonshi, gara ki auri wanda yake sonki ko da bakya sonsa, domin shi zai iya jure dukkan abin da zakiyi masa na b'acin rai, sab'anin wanda kike so, kuma ba lallai auren yaje ko inaba kuskure kad'an zaki zai iya rabuwa dake rabuwa ta har aba da !".
Saima zaune tayi tana sauraren Momynta kawai, lokaci-lokaci tana share hawayen fuskarta, wayarta dake kusa da Momyn tayi ringin Momy ta d'auka ta kara a kunnensa sabida ganin number da tayi babu suna, daga can b'arin aka hau fad'in.
"Please Saima gani nan tsaye cikin gidanku !, dan Allah yau dai kifito ko gaisawa muyi kada ki shanyani kamar ko yaushe".
Momy ta kashe wayar tana mai kallon Saima tare da mik'a mata wayar tana tambayarta.
"Waye wannan?".
Saima ta b'ata rai kafin ta bata amsa.
"Momy wanine wallahi duk yabi ya takuramin".
"Har tsawon wane lokaci ya d'auka yana zuwa gidan nan?".
"Inajin dai zuwansa uku".
"Amma shine kike wulak'anta mutum Saima !, duk wanda yace yana sonka arayuwa ya gama maka komai fa !, tashi ki fita".
"Momy nidai ki rabu da shi dan Allah".
Tayi maganar cikin shagwab'a har ragowan hawayen fuskarta na fitowa.
"Ki tashi kije nace !, tum kafin ranki ya b'aci, bana son musu kin sani ".
Saima ta mik'e cike da k'uk'uni ta shige toilet ta wanko fuskarta ta fito, dama doguwar rigace a jikinta ta janyo wani yalolon mayafi ta yafa akanta ta fice.
Momy ta bita da kallo tana fad'in.
"Saura kuma inji kin wulak'antashi ".
Yana tsaye jikin motarsa cikin wata sky blue d'in shadda wanda tasha d'inki d'an ubansu, hular kansa da takalminsa duk iri d'ayane farare, kansa na kan wayarsa dake hannunsa yana daddan nawa, iya had'uwa ya had'u son kowa k'in wadda ta rasa lol.
Saima tun da ta fito take binsa da kallo aranta taji ya burgeta sosai, yanayin tsayuwarsa da sajen fuskarta tamkar na Yarima, ba da ban zuciyarta ta tsumu da soyayyar Yarima ba da babu abin da zai hanata aminta da wannan gayen, abin da ta aiyana aranta kenan.
Da sallama ta isa wajen ya d'ago kai cike da murmushi yana amsa mata tare da fad'in.
"Yau wace rana ce?, rana mafi sa'a agareni...ranar da bazan mance da ita ba....domin nayi to zali da mafi haske a cikin mata.....yau ta amsa sallamar d'an talikin da baya da zuciya akanta ko yaushe !".
Saima bata san sanda murmushi ya sub'ucewa fuskarta ba, dubansa tayi akaro na biyu kamar zatayi magana sai kuma ta kau da kai gefe.
"Yi hak'uri Madam kada dai incikaki da surutu, sunana ANWAR SALISU MAI KUD'I, nasan zaki iya sanin mahaifina ko kiji sunansa?".
Kai Saima ta gyad'a tana fad'in.
"Ehh na sanshi kace kai na gida ne ma, ai mahaifinka abokin Abbana ne".
Murmushi Anwar yayi yace.
"Nima nasan da hakan !, na d'auka ke baki san hakan bane?".
"Na sani ! ".
Ta bashi amsa a tak'ai ce, shiru ne ya biyo baya kafin ya katse shirun da fad'in.
"Saima a gaskiya bazan b'oye miki, gaskiya tun sanda na ganki a wajen birthday d'in Yarima kika kwantamin arai, sai dai naso dannewa sabida tsoron irin tarbar da zan samu daga gareki, amma zuciyata ta gaza samun nutsuwa da hak'urin da nake bata ako da yaushe".
Sosai k'irjin Saima ya buga jin ya ambaci sunan Yarima, sai dai tayi k'ok'arin danne zuciyarta, tare da k'ak'alo murmushin dole, ya cigaba da fad'in.
"Ina fatan zaki karb'i k'ok'on bara na Saima?".
"Kar ka damu zanyi shawara akan hakan".
"Ok sai dai ina neman wata alfarma?".
"Alfarmar me kuma?, fad'i ina jinka".
"Kimin alk'awarin zaki dinga d'aukan kirana dan Allah".
Saima tayi shiru na d'an wani lokaci kafin ta ce .
"To babu damuwa Allah ya bani ikon cikawa !".
"Amin".
"Ni zan koma, sai yaushe zan dawo kenan?".
Sosai Saima ta farajin hiran na gundurarta cikin sauri ta bashi amsa.
"Ko yaushe ma".
"Nagode sosai, sai kinjini a waya".
"To".
Ta juya kawai tabar wajen, ba tare datayi tunanin komai ba, domin ta kasa daurewa zuciyarta da tsayuwar da takeyi da shi.
Anwar yabi bayanta da kallo yana dariya cikin ransa.
***
Ta sowarsu kenan daga islamiyya suna tafe suna hira jefi-jefi Zainab ce ma ginshik'in hiran, can tayi shiru ta dubi Aynu da fad'in.
"Kamar fa kina cikin damuwa Aynu?".
Aynu tayi yak'e tare da duban Zainab tace.
"Wallahi abubuwa ne sunk'ullemin kai sosai, kinsan Yarima Fudhal yana sona to gefe guda kuma Yarima Jalil shima yace yana sona har yana fad'in inrabu da Yarima Fudhal indawo wajensa, ta d'aya gefan kuma Ya sayyaadi Umar".
"Dama na sani ai !, inkaga kare na shin-shinar takalmi to d'auka zaiyi, nidai kinsan daman na gaya miki na fisonn ki da Yarima Fudhal wallahi Aynu?".
"Ni kuma kinga Ya sayyadi yafi kwantamin arai domin shine dai-dai ni, shi yafi dacewa dani da rayuwata".
Zainab taja dogon tsaki.
"Ke kam bakya fahimta wallahi !, yauwa ni kuwa mai ya had'aku da Yarima Fudhal ne?".
"Mai kika gani?".
"Babu komai, naga dai kamar bakwa shiri kamar da".
"Ehh to gaskiyar daya b'oyemin akansa ne ta fito fili".
"Kamar ta me fa?".
Nan Aynu ta kwashe dukkan abin da yafaru tsakaninta da Yarima Jalil ta sanarwa Zainab.
"Ni na yanke shawaran barin Yarima Fudhal kawai?".
Cike da fushi Zainab ta hau fad'in.
"Zancen banza !, wai ke haryanzu baki san waye Yarima Jalil ba ko?, lallai da sauran ki Aynu to Jalil ya wuce dukkan tunaninki da har zaki d'auki maganarsa gaskiya wallahi zai kai ki yabaroki ne kawai".
"Nifa gani nayi gaskiya ya fa'amin ai".
"Gaskiyarsa d'in banza !, baki d'auki shawaran da nabaki ba ko?, shikenan kinga tafiyata ni".
Zainab ta wuce tabar Aynu nan tsaye tana ta kwala mata kira amma tayi banza da ita.
Download Yarima Fudhal Littafi Na Daya Complete
1 Comments
Yarima fudhal compelet
ReplyDeleteThank you for this comment