COMPILED BY
ESHATT SMILER HOM OF HAUSA N ENGLISH NOVELS DOCUMNTSS
@WASAPP 08066360176 MORE
馃挆馃挐馃挐馃挆
*BUGUN ZUCIYA*
( _Heartbeat_)
馃挀馃挐馃挆
馃挆
馃挀馃挐馃挆
*By*
馃挆
_*Fadeela Lamido*_
1鈨� to 3鈨�
*Dasunan Allah Mai Rahama maijin kyai*
馃摍 Dada! Dada!! Wata matashiyar yariya ce ke rangadawa tsohuwar kakanta kira"
Fitowa tsohowar tayi tana kokarin gyara daurin zaninta take fadin, nashige su nikam wannan irin kira haka?"
Turbune fuska yariyar tayi lokacin da sukayi ido biyu da kakar tata tana fadin ayya dada danma kinsamu ina murnan ganinki shine zakice wani kin shigesu?, juyawa tayi da nufin komawa, cikin sauri dada ta jawota cikin fara'a tace dawo2 ai ban dauki murya ba, maraba lale lale takwara, karashewa tayi tare da jawota jikinta ta rungume"
Daidai lokacin wani farin dattiju ya shigo tare da sallama, yana ganin su haka yasaki murmushi"
Cikin sauri yariyar ta kwace daga rukon dada ta nufi cikin dakin, tabarma ta dauko ta shinfida wa mahaifinta ya zauna tana jin sun shiga gaisawa da dada ta koma dakin dada"
Gyarawa tashigayi duk da cewa dakin agyare yake dan dada macece me matukar tsafta, gadon ta lokuikuye yayi tsaf kaman baza ahauba sannan ta dau tsintsiya tahau shara"
Bayan ta gama ne ta dauko dan kaskon turaren wuta ta nufin dan karamin kitchen din dada dake tsakar gida"
Tagabansu dada tazo zata wuce dan haka duk suka juyo suna kallonta harta kusa isa kitchen din dada tace"
Aiko takwara bazaki samu rushi a kitchen dinnan ba, dan yanzun baban ninki sun hanani amfani da murhu"
Juyowa tayi ahankali tace to yanzun baki kunne turaran rushi kenan?
Gurin tabawa nake samowa"
Cikin rawar jiki ta nufi kofar gida tana fadin bari naje na samo"
Lokacin da dada ta komar da kallonta ga dannata gani tayi yayi shiru kanshi akasa, gyaran murya tayi sannan tace girman dan mutum babu wuya yanzun dan Allah kalli yadda takwara ta girma ko yanzun aka mata aure saita xauna"
Da sauri ya dago kai, yace dada kin sosamin inda ke min kyaikayi, hankalina ya fara tashi ayau tum muna hanya zuciyata ta fara tsinkewa"
Cikin kulawa tace kakwatar da hankalin ka insha Allahu Allah zai tsare babu abin da zai faru, kuma ma ai takwarar tawa Allahamdulillahi natse take tsaf ga kunya ga tsafta"
Hmmm dada akwai wani hali dana kula tanashi wadda har yanzun banji kowa ya furta ba, ban saniba koni kadai nake gani?
Kaga, banason jajibe2 karkace komai tunda ta gama secondary data same miji amata aure, idan ma kana da burin tayi karatu ne idan tayi aure tayishi can dakin mijinta"
Nisawa yayi daidai lokacin ta shigo da sauri tashige dakin dada cikin kankanin lokaci kamshi ya cikka gidan"
Dada ko hira sukaci gaba da danta zuwa can ya dauki mukullin motar sa dake kan tabarma yayiwa dada sallama ya fice"
Mikewa dada tayi ta nufi daki tana fadin takwara maza ki fito kutafi kisan abbanki besan jira"
Aguje ta fito ranta bace ta kalli kakar tata tace kai dada memakon kice mishi yabarni anan, ninafi son zamagurin ki kuma, shiru tayi kawai ta nufu kofa cikin zubura baki"
Binta da kallo dada tayi harta kule, sannan ta sauke idananunta tare da fadin duk sanki da gidan nan *Asma'u* dole ki hakura dan babanninki ba yadda zasuyi ba"
Ko da suka kama hanya babu abinda take banda zunbura baki, abbanta na kula da ita saidai ya dauke idon daga kallon ta dan ya fahimce manufarta"
Suna isa gida ta nufin dakin mahaifiyarta ranta bace, tare da matso hawaye"
*Ma'u* ya, kin fita da farinciki kuma kin dawo min da kuka, menene ya faru?
Turo baki ta karayi cikin kuka tace mama nifah banason gidan nan nafison gidan dada, kuma aidama keda abba kuncemin idan na kare secondary zan koma can"
Shiru mama tayi tana nazari kafin ta dago kai abba yayi sallama ya shigo ganin su haka yasashi hade fuska tare da fadin yaya ne?
Mikewa mama tayi tare da fadin alhaji ai kafi kowa sanin halinta gatanan wai ita gidan hajiya takeson zama"
Bazaiyuwu ba mamana, idan kikayi wasa konan da kofar gida zan hanaki fita, kinga yau kika dawo daga makaranta karki yadda wani abu ya hadani dake ban ce bazaki koma gurin dada ba, amman sai naga yanayin natsuwar ki, yana gama fadin haka ya fice abinsa ko waiwaye babu"
Washegari
*Asma'u* ce tsaye gaban mama cikin shirinta na tafiya islamiyya jan wando farar riga tare da jan hijjabi kudin break mama ta miko mata sannan ta mata sallam ta fice"
Gidan kawarta Zainab ta nufa cikin sauri dan karta wuce ta barta"
Tana kokarin shiga gidan zainab na fitowa cikin farin ciki suka rungumi juna cikin dauki zaina ke tambayan ta yaushe kika dawo?
Jiya abba ya dauko ni, jawo hannunta tayi tana fadin zo mutafi idan mundawo mayi hirar danni tsoron bulalan baba idi nake"
Mike layin sukayi har sun kusa isa makarantar zainab tajawo hannun *Ma'u* tanufi wani dan lungu"
Cijewa *ma'u* tayi tare da fadin me zamuyi alungu kuma?
Cikin rawar jiki tace *ma'u* taho dan Allah kinga waccen, na zaune din cen, dan daba ne idan yana zaune agurin ko maza basa wucewa, kizo mu wuce tunkan ya hangu mu"
Hannu *ma'u* ta daga ta nunashi tare da ya tsuna baki tana fadin waccen din?
Bege hannunta xainab tayi tace ke *ma'u* wlh idan yaga kina nunashi munshiga uku, gudun tsiya ne dashi kuma jikin shi duk wukake ne, ranan fa muna aji muna karatu saiga baba idi aguje, sai haki yake wai duna ne ya biyoshi"
Tintsirewa *ma'u* tayi da dariya hartana rike ciki, ganin haka yasa Zainab ta sake ta arude takoma jikin wani gida ta labe"
Tsagaitawa tayi da dariyar sannan tabi bayan zainab kallonta tayi tace gaskiya ke muguwar matsoraciya ce nikam bebani tsoro ba, dan haka wlh ta gabanshi zan wuce, ai layin bana ubanshi bane dazai hana mutane wucewa dallah fito mutafi"
Fitowa zainab tayi daga mabuyarta tana share zufah, dariya *ma'u* ta kara tutsirewa dashi sannan ta kama hannun zainab tana fadin to meyasa akecemishi *Duna* kuma gashi ba baki bane?
Oho nima haka naji anacemai *Shamsu duna* tafiya suka fara dan haka kowaccen su ta tsuke bakinta"
Lokacin dasuka isa dafdashi zainab ta sunkuyar da kanta kasa tare da sauri, itako *ma'u* kur tamai da ido tana karemai kallo,
dan haka zainab ta
Wuce tabarta agurin"
Zaune yake idon shi akasa yana wasa wuka, dogo ne kakkaura bashi da haske kuma baza akirashi baki ba, gabobinshi abon tsoro ne duk sunbi sun murmurde xaikai kimanin shekara 33 zuwa da 35, tabone ajikin shi kaca2 gani tayi yana kokarin dagowa dan haka ta fara kokarin dauke kanta dai batakai ga dauke kan nataba suyi ido 4"
Tsoro ne ya kamata sosai cikin sauri ta kalli kofar makarantar gani tayi har ankulle wani sabon tsoron ne ya sake kamata, batai aune ba saiganin *Duna* tayi agabanta"
Kerma ta fara dare da kara kallon wukar dake hannunta sai kyalli take, ahankali taxame tasa gwuiwanta akasa cikin rawan baki tace * yaya shamsuddeen inakwana?
Hadiye wulakancin daya tanazo yayi tare da tsareta da ido"
Cikin daure fuska yace mike"
Da saurinta ta mike tana kokarin wucewa"
Zonan taji ya fada dawowa tayi ta tsaya tare da runtse ido dan tunda ya matso kusa da ita tagane jikinshi abun tsoro ne gashi babu rigar kirki ajikin shi"
Ta dade ahaka ganin da tayi baya da niyan mgn yasata bude idonta, mamaki ne ya kamata dumin hangoshi tayi ya koma gurin zaman shi idon shi lumshe kaman me bacci
Aguje ta karasa makaranta jikinta sai rawa yake, abakin gert din ta tsaya ta saita kanta sannan ta karasa cikin mkrntr, office din baba idi ta kalla tare da addu'a Allah yasa baya ciki dan tana masifan tsoron dorinar shi, tsuguna wa tayi ta cire takalmanta ta fara takawa ahankali sadaf2 harta wuce office din tashege ajinsu"
Saidai duk abinda take baba idi nadaga can gefe yana kallon ta hannun shi rike da buta dan yagama alwala kenan ya mike ya hangota tana sanda"
Kai ya girgiza sannan ya shiga tunani yariyar nan batajin mgn duk da cewa mahaifinta namatukar kokari wajen bata tarbiya, dukanta yaso yi sai dai yasan halin *Asma'u* da tsoron duka dan ta makalkaleshi bawani abu bane awajenta, dan haka gara kawai ya barta"
Karfe 11:30am aka tashesu sai dai ana buga kararrawan baba idin ya aiko akira masa *ma'u*
Hankalinta be tashiba kawayenta taja su uku suka isa gurin baba idi"
Hango fuskanshi kawai sukayi su kasan lallai babu wasa dan haka duk suka doje"
Haushi sosai *ma'u* taji ahankali ta fara takawa harta isa gabanshi"
Cikin girmamawa ta gaidashi sannan ta sunkuyar da kanta kasa"
Ke *Asma'u* karfe nawa kikazo makaranta?
yau?
Kinci gidan Ku, ai Ina kallon ki sanda kikazo, meya yahana ki zowa makaranta akan lokaci?
Um um baba wlh daman yaune abban mu ya daukoni daga makaranta yanzun fah ko gida banje ba......
Sakin baki baba idi yayi yana kallota yarasa ma me zaice mata shiru yayi yana kallon kasa zuwa can ya dago yace"
*Asma'u* yau yaushe?
Alhamis"
Cikin ido baba idi ya kalleta
Ganin haka *ma'u* ta fara girgiza jiki alman tsoro, runtse ido baba idi yayi domin gani yayi kirjinta na tsalle, addi'oi neman tsari yayi sannan ya bude ido yace"
*Asma'u* ? Ki kace yau alhamis?
Shiru tayi dan haka ya girgizakai sannan yace Allah ya shirye ki"
Harta fara tafiya taji muryan shi yana cewa, ai zanga baban naki"
Tsurrr cikinta ya kada, cikin sauri ta juyo ta tsuguna tare da fadin me kace?
Jeki kawai ba dake nake ba"
Marai2 cewa tayi idonta cike da hawaye tace baba dan Allah karka gayawa abba wlh daga yau nabari"
Shiru kawai yayi yana kallonta dan becika son yin dogowar magana da itaba duk da yariya ce karama tana matukar birge shi saboda saurin kadaukan karatu da anbiya data dauke shi, kiriniyarta kawai ke hada shi da da ita domin duk fadin makaranta bawanda besan da zaman *ma'u* ba sabo da tsokanar tsiya"
Kara daure fuska yayi sannan yace naji tafi"
Jikinta asanyaye ta isa gurin kawayen ta dasukayi tsaye bakin mkrntr suna jiran ta, dan duk daliban sun wuce suka dai suka rage"
Tana shiga cikin su ta manta da zancen wani baba idi, lbrn haduwanta da *Duna* ta fara basu"
Rahama da faty ne sukaita kwasan dariya dasukaji *ma'u* ta tsugu ta gaida *Duna* itako zainab kara rudewa tayi cikin sauri ta nufa lungun da taso bi dazon tana fadin nidai saikun taho"
Basu hanataba tafiya suka fara suna cigaba da zancen *Duna*"
Rahama wai meyasa ake cemishi *Duna*?, ni naga beyi bakin da za'ace mishi haka ba, ni fuskar shi wlh kyau tamin jikinshi ne kawai yabani tsoro"
Au ke har kallon faskan tashi kikayi ni bantaba mai kallon kurullah ba dan baya son a kalleshi, amman naji mutane na cewa wai *karan* shi ne bakinkirin shiyasa ake kiransa *Shamsu duna*"
Hannun Rahama ta rike sannan tace toh wai meyasa baya son akalleshi?
Oho nima bansani ba"
Faty ce takalli *ma'u* tace kefa kin cika tambayan tsiya idan kin matso kije ki tambaye shi"
Murmushi kawai *ma'u* tayi, shiru sukayi harsuka isa gurin da ta ganshi daxun sai dai yanxun babu kowa agurin, raba ido *ma'u* tafara duk ta waiga babu alamansa, cizon yatsa tayi sannan tacigaba da tafiya
sun wuce gurin da kadan suka hango shi jingine jikin wani gida ya rufe fuskan shi da hula, da alama bacci yake"
Cikin sandan suka wuce shi, ja *ma'u* tayi da baya tare da fadin kash馃槵 na manta xobe na aji kuxo ku rakani na dauko"
Faty ce ta bata fuska sannan tace gsky kibari da yamma kyaduba"
Sakin hannun Rahama *ma'u* tayi sannan tace kuje sai nazo dan bazan iya zuwa gida babushi ba, abba na ne fah ya sayomin shi a Dubai"
Da haka tamusu wayo ta koma baya sai da ta bari su Rahama suka bace da ganin ta sannan ta tsuna ta debi dutsinan ta madaidaita guda 3 a hankali take takawa jikin gidan dake kallon shi ta nufa ta shige dan wani lungu dake tsakanin gidajen guda 2 ta labe, dutsen ta daya ta dauka sannan tayi saitin *Duna*
_Heartbeat_
*Mmn Yazeed Ce*
[22:49, 12/19/2017] 鈥�+234 806 858 0203鈥�: 馃挆馃挐馃挐馃挆
鈥�*BUGUN ZUCIYA*鈥�
( 鈥婬eartbeat鈥�)
馃挀馃挐馃挆
馃挆
馃挀馃挐馃挆
鈥婤y鈥�
馃挆
鈥嬧€�*Fadeela Lamido*
4鈨� to 6鈨�
馃摀 Bakaramin firgita ma'u tayi ba lokacin da taga duna ya bude hannun shi ya cabe dutsen, cikin sauri ta sunkuyar da kanta dan gudun kar ya hangota"
Shiru taji dan haka ta sake lekawa, baccinshi taga yaci gaba kamar ma bashi aka jefa ba, tintserewa ma'u tayi da dariya tare da fadin ashema magagi yake, katon banza baccin rana harda magagi, dariya ta kara sannan ta sake daukan wani ta jefa mishi"
Wannan karon ahancin shi ya sauka amman ko motsawa beyi ba"
Bakaramin dariya ma'u ke kwasa ba saida tayi me isarta sannan tace kash馃槵 ina ma na taho da waya dana mai photo nakaiwa su zee suga mutumin da sukejin tsoron sa ashema nauyin bacci gare sa harda su magagi"
Wani dutsen ta sake dagawa, jin kiran sallah yasata zabura ta yarda dutse ta fito cikin takun kasaita ta wuce deeni tana kwambare kafada"
Sai karfe 1:15 ma'u ta shiga gida, da fada mamata taryeta tana fadin"
Asma'u wanne irin kunne gareki dazun2 nan abban Ki yace kidaina biyawa gidan dada amman dayake kunnen ki na kashi ne saida kikaje ko?
Muryanta dauke da shagwaba tace, mama nifa bacan naje ba, tun dazun fah muna makaranta baba idi ne yasamu sharan masallaci"
Fuskan mama dauke da rashin yadda tace sharan masallaci? Tsohowa bansan karya inace maza keyi?
Tun yaushe aka daina basu, ai basu iyaba duk ranan da maxa sukayi baya sharuwa muko namu yayi kyau sosai malamai nata samana albarkan Allah ya bamu miji nagari"
'Da da mahaifi sai Allah, nan danan mama ta saki murmushi tana ameen tsohowa Allah ya mike albarka"
Cikin kunya tace amin sannan ta nufi dakinta"
Kai tsaye toilet ta shige, wanka tayi sannan ta fito rike da kayan da ta cire tana kwalah kira goggo tani2
Da saurinta ta shigo dakin tare da fadin Asmau lfy kuwa?
Kayan ta mika mata tana fadin lfy lau goggo kayan mkrnt na zaki wanke min"
Toh kuma gashi yanzun bani nake wanki ba, bala ne keyi amman bari nakai masa"
Yar karamar riga ta saka tare da siket daidai guiwar ta, fitowa tayi tana tafe tana raira karatun al Qur'ani, afalo ta samu mama, cak ta tsaya lokacin da ta hango kayan makarantar ta agefen mama"
Agogo ta daga kai ta kalla 2:10pm cikin fushi tace mama kinga goggo tani nabata kayan.....
Dakatar da ita mama tayi da fadin nina hanata takaiwa bala kayan, goggon sa'arki ce ita dazaki dinga kwala mata kira kina danga daki, saikace sabowar mejego?
Shiru tayi tana cigaba da zonburo baki"
Mama taci gaba da cewa toh maza ki dauki kayanki kije ki wanke dan goggo tunda tayi ciwon hannu abban ki ya hanata wanki, bala ne keyi, kuma ma bandan rashin hankali irin naki ya zaki hado harda bra dinki kice wai akwaiwa bala, yanzun ke bazaki iya wankewa ba acikin toilet"
Mama nifa wlh abani duk wani aiki amman banda wanki" ni ban ma iya ba wlh"
Toh aiko zaki koya maza ki kwashe kayan ki kije ki wanke babu me wanke miki agidan nan"
Buga kafa ta fara akasa tare da kara kallon agogo cikin kuka tace"
Mama nifah inason ne naje mkrntn yamma Kuma gashi yanzun lokaci ya kure, kuma idan banje yau ba duka na za'yi gobe"
Karfe nawa kika shigo gidan nan?, ai suma malaman sunsan yau bazaku samu zuwa ba, tun da su suka saku aiki"
Juyawa kawai tayi ta koma daki, dan bata da bakin mgn, kan gadonta ta fada, murmushi ta sake lokacin da ta tuna baccin duna, tare da wassafa fuskanshi a idon ta, mutun ne kyakyawa sai dai yaya akayi ya saka kanshi adaba, gashi duk anji mishi ciwo ajiki, da alama ma bashi da karfi tunda yake bari na jimai ciwo, tsaki taja tare da fadin katon banza kana Yawo da wukake amman kana bacci atiti badole ayanyanke ka ba"
Washegari tun karfe 7:30 ta nufi mkrnt bata biyawa zainab ba dan tasan bazata barta tai abinda tayi niyya yadda ya kamata ba"
Tafe take cikin kayan mkrnt idan ka ganta gwanin ban sha'awa, ita ba dugowa ba ita ba gajera ba, fara ce tas, ga wani siririn hanci da bakin ta madaidai ci shekarunta basu wuce 16 zuwa 17 ba amman kirjinta cike yake kai kace wata cikkakiya budurwa ce"
Lokacin da ta isa kofar gidan da taga duna dubawa tayi ko ina babushi babu alamar sa, azuciyar ta taji babu dadi dan taso ace ta ganshi"
Kad'a kai tayi ta wuce mkrt har aka tashi bata cikin natsuwar ta, Allah2 take atashi tabi hanya"
Tana ganin akusan tashi ta tsiri rubutu, dan haka su rahama basu tsaya jiranta ba sukayi
tafiyan su"
Saida ta dainajin hayaniyan yan mkrntr sannan ta dauki littafinta ta fito"
Dakalin ta da ta ganshi akai jiya yauma yauma kwace yake agurin ya daura kafarsa daya kan daya, ya daura hula kan fuskar"
Babu kowa alayin dan unguwa ce ta masu hali kowa yana cikin gidan sa babu ruwan wani da wani, hakan ne yaba ma'u daman isa gaban duna cikin sanda"
Cikin siririyar muryanta ta rangada sallama taji shiru babu amsa dan haka ta gara matsawa daf dashi tare da tabbacin yauma baccin shi yayi nisa kaman jiya, ahankali ta daga hannuta ta dafa hular dake kanshi, jitayi be motsaba dan haka ta daga hular fuskan ta bai yana"
Idon shi rufe dan haka ma'u ta bude baki da hanci tana karemai kallo"
Deeni wankan tarwada ne dan baza akirashi baki ba yana da duguwar fuska tare da dogon hanci daidai gwargwado, sakko da idonta tayi kan kirjishi da tat bai su kai kaca kaca dashi, yatsa ta cija sannan tace afili, meyasa kake bacci atiti bayan kuma ka sani sarai nauyin baccin gare ka, koni danake mace zan iya kashe ka ma ba jimaka ciwo ba, kallo ta kara masa sannan ta saka hannu ajakar makaranta ta dau waya ta daukeshi hoto har guda biyar sannan ta kwashe da dariya tare da fadin kai gskiya ni jaruma ce, agogo cikin wayar ta duba sannan ta nufi gida cikin sauri"
Washegari ko ta nuna ma kawayen ta hotunan duna kaman yadda tayi niyya, mamaki ne ya kamasu tun daga ranan zee bata kara yadda ta jera da ma'u ba, dasu rahama take jerawa su jirata daga can gefe ta gama tsokanan duna tazo su tafi suna kyalkyalketa dariya"
Ahankali wannan dabi'a tazama jiki agun ma'u kullum idan aka tashi mkrnt saita sameshi agurin yana bacci, haka zata gama surutun ta akan duna ta wuce gida"
Haka har aka samu tsawon wata biyu ,wannan lokacin ma'u intaje gaban deeni bata sanda ko mgn ahankali dan tasan idan har yayi bacci idan kaso zaka iya daukan shi ka gudu"
Abu ya zaman ma ma'u jiki harta kai alhamis da juma'a da babu makaran ta tana shiga damuwa dan haka yau juma'a da wuri ta isa dakin abban ta"
Bayan ta gaida shi ta zauna daf dashi"
Kallonta yayi da murmushi akan fuskanshi yace mamana ya akayi? duk yadda akayi akwai abin da kike so"
Cikin shagwa ba tace abba na tuna Dada ne"
Dada tana nan lfy mamana kulum tana cewa nagaishe mata da takwararta, ba inagaya miki ba?
Eh abba amman ni inason ne naje naganta"
Shiru yayi zuwa can ya dago yana share zufa yace, to naji amman kibari nasamu lokaci zan kaiki da kaina"
Shiru tayi badan ranta yaso ba, tana fitowa ta fara matso hawaye, karo sukaci da mama zata shiga dakin, ganin ma'u cikin hawaye yasa tabita da kallo"
Alhaji yau kuma fada kukayi kaida maman taka?, naga ta fita tana share hawaye"
Au kuka takeyi? Allah sarki, wlh ina matukar jin dadin yadda Asmau take nuna soyayyarta ga dada, amman kash bazan iya barinta ta zauna acan ba, sabo da gudun kar abinda ya faru shekarun baya yasa ke faruwa, shi yasa bana son na nuna mata gida biyu, kuma nacewa dada ta dawo ta zauna tare damu tace a,a bazan iya bari Asmau ta dinga zirga zirga atiti ba yau tana gida gobe tana gidan dada, dan gudun haduwa da gurba tattun samari"
Mamace ta dago da kanta bayan ta gama sauraren shi ahankali tace alhaji Allah ne fah yake tsarewa, kuma ai be kamata ace anhanata zuwa gidan dada ba itama dadan ai bazataji dadi ba"
Mikewa yayi fuskan shi babu annuri yana kokarin fita yace kice mata idan shirye take ta fito na sauke ta"
Dagudu ma'u ta fito fuskanta cike da fara'a ta shiga motar ta zauna har suka isa bece mata komai ba"
Akofar gidan ya sauketa sannan yace ki jirani idan nata so zanzo na dauke ki, ranta be soba, amsawa tayi ta shige gidan"
Bakaramin dadi dada tajiba dataga ma'u, aikace2 gidan sukayi tare sannan suka zauna suna hira, suna cikin haka dada ta fara gyangyadi, ma'u naganin haka ta kalli agogo 11:15 tagani, zama tayi har taga 11:20 dan haka ta mike ta dauki bakin gyalenta agefen gadon dada sadaf2 ta fice"
Da sauri take ta fiya dan taje ta dawo kafin dada ta tashi, tun daga nesa ta gane baya nan, dan gurin da yake kwanciya babu komai awajen, ja tayi ta tsaya domin taso ace ta ganshi"
Gajiya tayi da tsayowa dan haka ta juya ta fara tafiya da nufin komawa gida, kaman ance ta juya ta hango shi kwace, kai yaya akayi haka? Ma'u ta tambayi zuciyarta, juyawa tayi cikin sauri ta isa gurin tare da sallama, jin babu amsa ya tabbatar mata da bacci ya wuce dashi daf dashi taje ta cire hular dake fuskanshi, idonshi rufe yake kamar kulum, fuskanta takai saitin tashi sannan ta huramai iska ahankali"
Wani gwaron ajiyan zuciya ya Saki, da sauri ma,u taja baya"
Ganin yaci gaba da baccin yasa ta sake matsawa ta bude baki ta sake hura mai fuska akaro na biyu, karaf taji anrike ahannunta"
Subuhanallah yau nashiga uku na lalace, wayyo abba na waiyo dadata kuzo ku ceceni, dan Allah kayi hakuri
wlh takalmi nane ya tsinke na tsuguna zan dauka bansan akwai mutum agurin ba
Heartbeat
Mmn Yazeed馃崄鈥�
[22:49, 12/19/2017] 鈥�+234 806 858 0203鈥�: 馃挆馃挐馃挐馃挆
鈥�*BUGUN ZUCIYA*鈥�
( 鈥婬eartbeat鈥�)
馃挀馃挐馃挆
馃挆
馃挀馃挐馃挆
鈥婤y鈥�
馃挆
鈥嬧€�*Fadeela Lamido*
7鈨� to 9鈨�
馃摎 Murmushi yayi kadan batare da yace komai ba, binta da wani mayan kallo kawai yake"
Ma'u ko duk ta firgice tana rokon shi ya sakar mata hannu"
Mikewa yayi tsaye batare da ya saki hannun ba, kuma har yanzun idonshi na kanta wani maya tatcen kallo yake mata"
Cikin wata irin murya da bazata iya tattance yanayin sa ba yace"
Ke baby natsu, bason gaddama, kishiga hankalin ki, kinji ko?
Hannunta tasa duk 2 ta rufe bakinta tana daga kai alamar eh, acikin zuciyarta ko fadi take tawa ta kare"
Menene sunan ki?
Cikin rawar baki tace Asmau"
Lumshe ido yayi sannan yasa ke cewa menene ya fito dake yau bayan babu mkrnt?
Dan Allah dan darajan annabi kayi hakuri wlh daga gidan kakata nake, nasan yanzu tanacen tana nema na"
Cikin wata irin murya yace baruwa na da wata kakarki ni ke kadai nasan.....
Kukane ya kwace mata, cikin kukan tace to aini ban sanka ba wlh tsautsayi ne kawai ya kawoni nan, wlh da nasan haka ne da banzo ba"
Murmushi ya sakeyi ahankali ya kara runtse hannuta cikin nashi, tare da lumshi ido"
Zuwa can ya bude yace inace kinzo gadi nane?, dan kada abokan gaba su kawamin farmaki, dan kinsan nifa nauyin bacci gare ni, ke fah?
馃槴 Nima inada shi wlh, narantse inada shi"
Wannan karan saida yadan dara sannan ya dan jawota jikin shi tare da fadin baby ki kwantar da hankalin ki, bazan miki komai ba, jarumtar ki ta birgeni, ni jarumi ne dan haka inason naga mace jaruma, kin yi kokari sosai dakika tunkare ni, amman meya hana kika kasa hakuri zuwa gobe asabar kika fito yau?
Ainace maka gidan kakata naje yanzun ma tsautsayi ne ya fito dani"
Hmmm kawai yace sannan yaja hannuta zuwa gurin kwanciyar shi ya zaunar da ida"
**
Aban garen dada kuwa da misalin 12:09 sallama alhaji ne ya tasheta daga bacci"
Afirgece ta tashi tana fadin takwara shine baki tasheni baccin ba bayan kinsa ina tafiya masallacin juma,a da wuri"
Gaba dayan su wurga ido suke suga ta ina ma'u zata bullo daga abba har dada"
Jin shiru yasa dada ta shiga kwala mata kira taji shiru, mikewa tayi azabure tana fadin zoka zauna inaga ta shiga gidan tabawa bari nakirata"
Zama yayi kamar yadda dada tace sannan ya cire hular kansa ya aje agefe, tare da fadin Hmmm Allah ya kyauta"
Lokacin da dada ta shiga gidan ta bawa cemata tayi ko kallita bata gani ba, dan haka tayo waje hartana tuntube"
Azauren suka hadu da dan tabawa yana kokarin shiga gidan, kallon shi dada tayi tace kai iro baka gamin Asmau ba?
Aiko dazun naganta nan wajen hanyar mkrtnr su......
Bata bari ya rufe baki ba tabi hanya tana gudu2 sauri2"
Kalu innalillahi wa Inna ilaihir raju'un ta fada lokacin da ta hango ma'u rike hannun Duna"
Jikintane ya fara rawa bata San sanda ta kwasa aguje ta nufi gida ba"
Ganin dada agoje abin yabawa iro daya biyo bayan mamaki, shan gabanta yayi dan gudun karta tuntsura, riketa yayi tare da fadin dada lfy menene ya faru?
Ajiyan zuciya ta fara bata iya cewa komai ba saijan hannun iro take"
Daga nesa tamai nuni dasu, lokacin suna zaune ita da Duna"
Salati yayi sannan yace dada, ki tsaya inwuce saiki kwala mata kira tunda ke tsohowa ce kila bazai miki komai ba, amman ni idan ya ganni akwai matsala dada, tunda shi fadan shi baya wucewa inda kikasan shedan haka yake, cikin sauri iro yabar wajan yana me Kara karfafawa dada guiwa da hannun shi"
Tashin hankali ne sosai azuciyar Dada, kafafuwanta banda rawa babu abinda suke, kallo ma'u tayi tana mamakin yaya akayi ma'u tasan deeni harta bari suka zauna guri daya , kuma da alama ba tursasata yayi ba, kawar da tunanin tayi sannan ta daga murya ta kwalawa ma'u Kira"
Tana hango dada ta mike azabure, ta nufota aguje, ganin haka duna ya mike ya biyo bayanta"
Takaici ne ya kama dada dan haka ma'u na isowa ta daga hannu ta sharara mata mari, hannu ta sake dagawa zata kara mata, taji andaka mata tsawa cikin wata irin murya ta kyauraye"
Ke ! Ke!! Yasin yasin kika sake hannunki ya kara kaiwa jikinta sena sassara ki, Allah wlh *gunduwa gunduwa* zanyi dake, yasin hannunki ya kara kaiwa jikin ta kigani"
Suman tsaye dada tayi, fita tayi daga hayyacin ta, lokacin da network dinta ya dawo gani tayi suna tafe ita da ma,u sai janta take, tana kara fadin dada taho mana"
Bata iyace mata komai ba illah binta da take da kallo, sai dai akwai tashin hankali karara a idon ma,u"
Sauri ta kara dan sai yanzun ta tuna abban Asma'u yana gida yanajiran su, jitayi kaman lema ajikinta dan haka takai idonta kan zaninta jike yake sharkaf nan ta tabbatar fitsari ne"
Suna karya kwanan layin, ma'u ta hango abbanta sai zagaye yake akofar gidan dada, gefen shi iro ne azaune ya rafka uban tagumi"
Hunnun dada ta matse tare da fadin wayyo Allah na, nashiga uku"
Kallota kawai dada tayi ta tabe baki tare da fadin Hmmm"
Jikin ma'u ban da rawa ba abinda yake, cikin mtsanan cin tashin hankali ta taja ta tsaya tana me tsiyayar da hawaye dan ta tabbatar yau kashinta ya gama bushewa"
Ganin abba na tahowa yasa ta faraja da baya ahankali, tana kokarin rike Dada"
Yana isowa yasa hannun shi ya rabata da jikin dada ya zaf ga mata mari har saida ta fadi kasa, cikin karaji yace daga gidan uban wa kike?, jin da yayi babu amsa yasa ya daga kafa ya nufi cikinta yana kokarin tokarin ta aciki, tare da fadin badake nake mgn ba?
Cikin matsanan cin firgici dada ta rike Abba da wani irin karfi da batasan tana dashi ba, tana fadin kasheta zakayi ne?, toh bismillah nunamin yarka ce, nace kanuna min ka haifa kuma ni mahaifiyar ka ban isa na aiki yar ka ba"
Sanyi jikin Abba yayi, cikin natsuwa ya shiga bata hakuri, badan ya yarda cewa dadan ce ta aiketa ba"
Haka dada taita fada abba nabata, hakuri da karshe da kanta tasa ma,u amota abban ta, tana cigaba da fada"
Dada na tsaye akofar gida har motan abba ta bace, ajiyan zuciya ta sauke sannan ta juya ta shiga gida tana mamakin inda ma,u tasan deeni"
Kulle gidan tayi da sakata domin ita har yanzun gani take kamar duna zai shigo mata gida dan ba karamin tsorata tayi ba, wanka tayi ta gyara jikinta sannan ta wanke kayan da ta cire ta shanya, aranan dada bata runtsaba data rufe ido duna take gane"
Asmau kuwa suna isa gida ta sauka aguje tayi cikin gida"
Binta da kallo Abba yayi tsananta me tsanani yaji acikin ransa dan haka bayan ya shiga falon ya zauna, ma'u daga daki taji yana waya yana fadi"
*Usman* na gari ne?, toro mun shi yanzu yanzun nan, akwai matsala"
Faduwa ma'u tayi daga kan gadon dan ta tabbatar yau sai dai buzun ta indai ta bari har ya usman ya riketa"
*WAIWAYE*
Alhaji sani haifaffen jahar Kano ne, su 2 iyayen su suka haifa, daga shi sai yayan shi Alhaji musa, alhaji sani shine mahaifin Asmau, su uku suka haifa, tare da matar sa Fatima, usman shine babban, sannan fiddausi sai yar auta asmau wacce taci sunan kakanta"
Shiko alhaji musa Saida ya shikara 15 be samu haihuwa ba, dan haka kaninsa alhaji sani ya bashi danshi usman alokacin yana da shekara 5"
Usman ya taso cikin gata gidan alhaji musa tamkar dan da suka haifa da cikin su, yayin da alhaji sani yaci gaba da kula da fiddausi wadda take yar shekara 2"
Alharji sani da yayan sa ma,aikatan gwamnati ne, kuma suna samu daidai gwargwado dan a unguwar su idan xa ai lissafin masu hali baxa a kirga 5 babu su aciki ba"
Fiddausi nada shekara 10 aka haifin Asmau, tun daga kan asmau basu sake samun haihuwa ba"
Bayan shekara 8 fiddausi ta zama cikakkiyar budurwa meji da kanta duk abin da take so shi ake mata, saidai abu daya abban su baya barin yawo indai ba gidan dada tace zataba ba a barinta zuwa ko ina, dan haka lokacin da ta kare secondary ta samu daman tafiya jami'a ta balle bishashanta acan, ahankali fiddausi ta zama bata da abokai sai maza, haka zaka ganta tsakiyar maza ita kadai mace"
Babu wadda keda lbrn halin da fiddausi take ciki amakaranta, dan da antashi gida take yowa dan tasan ko minti 10 takara sai ance inata tsaya"
Ana haka maza suka fara canzawa fiddausi tunani domin ko duk abokanta kusan su 7 babu wadda baya lalubeta da sunan wasa, dan haka ta farajin babu abin da take so illah taga ta kadai ce da namiji"
Duk abinda suke sauran dalubai na kula dasu, yayin da wasu daga cikin matan suke tur da halin fiddausi, ita kenan yau ka ganta manne jikin wancen gobe jikin waccen"
Yauma kamar kullum tana cikin motar wani abokinta KB suna manne da juna ita da kanta ta lalubo bakin shi ta cusa nata ta, saida suka gama shagala, sanna ta gabatar mai da kudurinta"
Murmushi KB yayi dan yasan za'ai haka, yayi mamaki ma da har aka kawo yanzun bata bada kai ba, sabo da salon da suke mata"
Kwantar dakai KB yayi tare da fadin babu damuwa, amman fa saidai kizo muje Ki tayani kwana"
Zaro ido tayi dan tasan zancen shi bamai yuwuwa bane, tace KB ? Kana son Abbana ya kasheni ne?
Tsaki yaja sannan yace haba meyasa kike abu kamar wadda bata waye ba, ai dibara zaki masa"
Bayan kwana 2 fiddausi ta kasa hakuri dan haka ta shirya tayi sallama akan zata gidan dada ta kwana"
Gidansu KB ta wuce wadda har ya kaita da kwana adakin kb kuma har komai ya kasan ce, karfe 7:09am ta isa gidan dada da kayanta ajaka kamar yadda ta shiryu, ganin inda take tattale kafa yasa dada fadin ke lfy meya sameki kike wani tafiya saikace agwagwa"
Akafa fah na taho dada wlh gajiya nayi"
Ruwan wankan dada ta juye tayi wanka tare da gasa jikinta, ko karyawa bata tsaya yi ba, ta haye gado sai bacci domin KB be bari ta runtsa ba"
Damisalin karfe 8 alhaji sani ya iso gidan ganin fiddausi agado hankalin shi ya kwanta"
Tun daga ranan wannan dabi'a ta zaman mata jiki har saida ya kasance gaba dayan su 7 sun gama sanin wacece fiddausi"
Ankwashi tsayon watanni ana haka kullum fiddausi tana hanya wata rana takan kwana gidan dada amman sauda yawa dakin samarinta take wucewa idan ko har ta kwana gidan dada toh safiya nayi zata wuce gurin samarinta, babu wadda ya lura da halin da fiddausi take ciki har saida fiddausi ta fara rashin lfy, ana zuwa asibiti gwajin farko aka shaida musu tana dauke da ciki Wata 2"
Mummunan tashin hankali suka shiga ba kadan ba, wadda da takai har abba ya kwanta asibiti saka mukon hawan jini daya kamashi,
Duk abinda ake usman bashi da lbr dan lokacin yana mkrnt yana kokarin karasa karatun shi na soja"
Bayan abba ya samu sauki ne suka zauna da yayan shi alhaji musa tare da sanya fiddausi agaba ta fada musu wadda ya mata ciki"
Tashin hankali ba'a sa maka rana nan idon fiddausi ya raina fata damin kuwa acikin abokanta guda 7 babu wadda baya kusanta ta dan haka batasan sunan Wa zata kira ba
Heartbeat
Mmn Yazeed馃崄鈥�
[22:49, 12/19/2017] 鈥�+234 806 858 0203鈥�: 馃挆馃挐馃挐馃挆
鈥�*BUGUN ZUCIYA*鈥�
( 鈥婬eartbeat鈥�)
馃挀馃挐馃挆
馃挆
馃挀馃挐馃挆
鈥婤y鈥�
馃挆
鈥嬧€�*Fadeela Lamido*
馃敓 to 1鈨�1鈨�
馃摀 Nadama ce me tsanani ta shigeta cikin kuka ta furta KB, koda alhaji musa yasa aka binciko masa KB nunawa yayi ai bashi kadai ke nemanta ba dan ko satin daya wuce a dakin abokin sa ballo ta kwana, dan haka babu wadda ya isa yace ciki nasa ne"
*Bugawa* zuciyar abba tayi jin yarshi tana kwana dakin maza, duk irin tsaron da yake bata, hawaye masu dumi suka fara zubo masa"
Ganin inda abba ke zubar da hawaye hankalin fiddausi yayi mummunan tashi, acin kuka tace abba dan Allah kayi hakuri ka yafemin"
Mikewa KB yayi yana fadin ni kar a kara kirana akan wannan xancen danni tun farko ita ta nemeni gatanan ku tambayeta cewa tayi intaima keta"
Fashewa abba yayi da kuka kaman karamin yaro, alhaji musa ne yace bazaibar xancen ba, yan sanda yasa suka kama KB, cikin bin ciken su suka kama mutun 7 da fiddausi take kwana dakin su"
Lokacin da abba yaga tika2 maxan da fiddausi ke kwana agurin su abin ya bashi tsoro kuma gashi kamar hadin baki dan kowanne cikin su cewa yake ita tace ya taimaketa"
Nan take abba ya fara aman jini, asibiti aka nufa dashi kai tsaye, satin shi 2 asibiti ya fara samun sauki"
Aban garen fidausi kuwa tunda tasamu lbr rashi lfyn abba kulum cikin kuka take, figewa tayi ta lalace gawani uban baki da tayi"
Kwata2 mama bata mata mgn , ko gaidata ma da takeyi cewa tayi idan ta Kara mata mgn Allah ya isa"
Rayuwa tayiwa fiddausi zafi haka zataita kwara amai mama naji amman ko kallota batayi adaki take zama tace kukunta takoshi, hakika fiddausi tasan ita ta basu KB dama amman ai su sukasa hartakai wannan matakin saboda irin wassannin da suke mata, kuka taci sosai tundaga ranan ta kama rashin lfy"
Satin ta daya adaki bata ko iya tashi, goggo tani ce tashiga dakin dan taji shirun fiddausi yayi yawa, samunta tayi duk ta rame ta tsutse gashinta baje akan gado bakinta ya bushi yayi wani bawo2"
Furgita sosai goggo tayi tana xare ido tace ke kina cin abinci kuwa?
Ruwa ruwa kawai fiddausi take fadi"
Tashin hankali sosai abba ya shiga lokacin da dada takai mai lbr"
Hakika yana matukar son firdausi saidai wannan Abu data aikata yana sosa masa zuciya"
Firdausi naganin abba ta fara rokonshi da girman Allah ya yafe mata tari ne ya kwace mata, babu kyaukyautawa dan haka hankalin kowa ya koma kanta"
Zuwa can jini ne ya fara fita ta baki ta hanci, cikin rudu abba ya wuce ya tallabeta tare da fadin firdausi na yafe miki, kuma zanci gaba da addu'a duk wadda ya lalata miki rayuwa uban giji Allah ya saka mike"
Murmushi tayi kadan sannan ta jawo hannun mama ta rike acikin nata, ta karyan da kai alaman roko"
Mama ta fahimce ta, itama karya kai tayi hawaye na sauka afuskanta tace na yafe miki duniya da lahira"
Murmushi tayi sannan ta daga hannu tanawa su dada bye bye鉁嬸煆�"
Abba ne yace ya kamata mutafi asibiti dan naga jikin ya matsa mata"
Murmushi firdausi tayi tare da girgiza kai tana mutsa baki"
Ahaka abba da alhaji musa suka dauketa suka nufi asibiti, banda murmushi babu abin da take"
Emergency aka shiga da ita, yayin dasu abba sukai cirko2, zuwa can likintan ya fito yana share zufa tare da fadin alhaji saidai kui hakuri dan *zuciyar* yariyar yariga ya *buga*"
Mekake nufi? abba ya tambaya yana me kallon cikin idon likitan"
Cikin sanyin jiki yace ta rasu"
Innalillahi wa inna ilaihir raju,un shine abin da kuwa yake cewa agurin"
Lokacin da abba ya tsaya akan gawan Fardausi, Hawaye ne sosai yake fita a idon shi kanta ya dafa yace Allah yajikan ki Allah yasa mutuwa ta xame muki hutu, kukane yaci karfin sa dan haka alhaji Musa ya kamashi yayi waje dashi"
Bayan ankwai Firdausi gidanta nagaskiya ne alhaji musa ya tura adauko usman"
Bayan isowan usman ya shiga munmunan tashin hankali, kuma yaci alwashin daukan fansa agun su KB"
Abba cewa yayi babu wani fansa daza,a dauka duniya ce wadda bezoba ma jiransa take dan haka abar ma Allah"
usman ya koma makaranta bayan sadakar 7 mama da Abba kuwa sunfi shekara 1 suna cikin jimamin Abba yau ciwo gobe lfy"
Wannan dalilin yasa abba ke matukar sawa ma,u ido tare dayin kaffa2 da ita"
Ayanxun usman ya gama karatun shi ya zama cikken soja kuma yayi aure shekara 1 data wuce
itako ma'u awannan watan ta kare secondary dan haka yanzun islamiya kawai take zuwa"
*CIGABAN LABARI*
Dakin baccin mama ta nufa aguje tana fadin mama dan Allah karki bari yaya usman ya dakeni wlh dada ce ta aikeni.....
Fita kiban guri cewa mama dake nunawa ma'u hanya"
Kuka ta fara tana rokon mama tsayowar mota taji dan haka ta ruga dakinta"
Usman ne ya shigo falon tare da matarsa Fa'iza, bayan ta gaida abba ta fita ta basu guri"
Abba ne ya kwashe duk abin da ya sani ya fada ma usman, shiru yayi zuwa can ya mike yace abba bari naganta"
Kofar dakin ya tura ya shiga, ma'u na tsugune agefen gado idon nan zuro2"
Zama yayi agefen gado sannan yace ke zonan"
Bata iya mikewa ba da rarrafe ta matso, jikinta sai kerma yake"
Ina kikaje?
Toshe bakinta tayi da hannunta hawaye na zobowa afuskanta tace"
Yaya narantse dada ce ta aikeni, kuma ka tambayeta ka......
Wani uban tsawa usaman ya buga mata wadda yai matukar razanata, sannan yace"
Wasa nake dake?, zaki gayamin inda kikaje kosaina karya ki tukuna?
Mikewa tayi arude tana fadin yaya dan Allah karka karyani wlh dada ce ta aikeni "
Mikewa taga usman yayi yana nan nade hannun rigar sa, uhu ta bara lokacin da taga yana kokarin kwance ma dauri wandon sa"
Batai aune ba ta farajin saukan duka, yana dukanta ne yana gara tambayanta inda taje amman har yamzun mgn daya take maimai tawa dada ce ta aiketa, dan haka usman be dena dukanta ba har saida yaga ta kasa tashi, ihunta ma ya daina fita sannan ya tsagaita"
Bakin gadon ya koma ya zauna sannan yace kince dada ce ta aike ki dan haka inason ki gayamin inda ta aike ki"
Tsintan kanta tayi tana fadin carbin ta ne ya tsinke tace nakai mata gyara"
Carbi? Jitayi yasake hada mata mari akumatunta duka guda biyu, bata kara sanin inda take ba"
Zuwa can ta bude ido taga matar yaya usman zaune agefenta tana mata fifita"
Muryanta adashe tace anty zainab kina gidan nan kikabar yaya yana neman kashe ni?
Rufe mata baki tayi idonta cike da kwallah tare da fadin Asmau naso na shigo mama ce ta hanani"
Kuka ma,u taitayi Anty zainab na lallashinta"
Washegari da safe ma,u ta tashi jikinta ya mata tsami ga fuskanta duk ya kunbura, jin muryan dada afalo yasata farin ciki , tashi tayi tana takawa ahankali ta fito falo"
Salati dada tasa lokacin da idonta ya sauka afuskan asmau sannan ta juya ta kalli abba tace"
Au yanzun nan saida ka duki yariyar nan?, aida kasani ka hada haddani tunda nice babban me laifi, amma ba komai Allah ya baka hakuri, juyawa tayi zata fita ranta bace"
Hakuri abba yaita bawa dada, daker ta yadda ta dawo, rike asmau tayi suka shige daki, bayan sun zauna ne dada ta kalli asmau cikin tohuma tace"
Toh asmau mgn nazo muyi me mahimmanci, kuma inason kisa aranki wannan mgn tsakanin ni dake ne babu mejinta"
Gyada kai ma,u tayi tana share ragowan hawayen dake fuskanta"
Asmau menene tsakanin ki da wannan ibbilishin yaro?
Shiru tayi tana kallon kafar ta, tare da zubo da wasu sabbin hawaye"
Takwara badake nake mgn ba?
Cikin kuka tace dada ni wlh babu komai tsakanina dashi ahankali takwashe duk yadda akayi ta gaya mata"
Shiru dada tayi tana mamakin hali irin na asmau, ace yariya ba'abin da tasa agaba sai tsokana, zuwacan ta kalli ma,u sannan tace"
Karki kara irin wannan rashin hankalin, ban da kuruciya me ya dameki dashi? Mutumin da manya ma gudunshi suke, shine ke zakina shige mishi?, kinatsu sosai kisan me kike keba karamar yariya bace, koko so kike kisa ubanki atashin hankali?
Girgiza kai tayi sannan tace aina bari baza sake kulashi ba kuma dan Allah idan yaya usman ya tambaye kice kika aikeni"
Hmmm takwara kenan, naji kuma zan fada amman saikin min alkawarin baxaki sake kula wannan shaidanin yaron ba"
Har cikin zuciyarta batajin dadin sunan da Dada take kiran deeni, dan haka saida ta runtse ido sannan tace, nayi alkawari"
Bayan kwana biyu jikin ma,u yayi sauki saidai har yanzun akwai shaidan duka ajikinta kuma fuskanta be gama sabewa ba"
Shiryawa tayi cikin kayan mkrnt sannan tayiwa mama sallama ta wuce"
Wata zuciyar ce tace kibi ta gurin mana ko hangoshi ne kyayi daga nesa, a'a nayiwa dada alkawari ta fada afili, koda takai daidai lungun fasa bi tayi dan jitake idan bata gansa ba kaman wani abu zai faru"
Tunkafin ta isa gurin ta hangoshi sai waige2 yake kamar dai yana neman wani, zuwa can ya juyo da kallon sa, gurinta, wani munafukin murmushi ya sake sannan ya fara tahowa"
Kaucewa ma,u take, tare da kara sauri, amman duna sai dad'a binta yake"
Ganin haka ma,u tasa kuka, tare da tsayawa cak"
Wani irin kallo yake mata, tare dason kallon kwayar idonta, zuwa can ya mika hannun sa ya shafi kuma tunta shedan yatsu ya gani kwance"
Nan danan idonshi ya rikice ya kuma jawur, sannan ya karkata kai yace"
Shedan hannun waye afuskan ki?? uban waye ya dake ki??
Jikin asma'u banda kerma ba abin da yake, agigice ta kauce tana kokarin guduwa"
Damkanta yayi tare da fadin ina wasa dake ne? Ashe yau unguwar nan babu zaman lfy indai baki fadamin wadda ya bata miki fuska ba ton wlh duk wadda nagani sara ne"
Rudewa asma'u tayi cikin kuka tace a'a wlh yaya nane"
Yayan ki?, toh wlh sainaci uwassa, zai shaida cewa bakin rijiya bawajen wasa makaho bane, yasin saina canza mai halitta
*Mmn Yaxeed*馃崄鈥�
[22:50, 12/19/2017] 鈥�+234 806 858 0203鈥�: 馃挆馃挐馃挐馃挆
鈥�*BUGUN ZUCIYA*鈥�
( 鈥婬eartbeat鈥�)
馃挀馃挐馃挆
馃挆
馃挀馃挐馃挆
鈥婤y鈥�
馃挆
鈥嬧€�*Fadeela Lamido*
*@AM拢拢NCI WRITER'S ASSOCIATION馃*
1鈨�2鈨� to 1鈨�4鈨�
馃摉 Hannu asmau ta daura akai 馃檰馃徏馃檰馃徏 domin kalaman deeni sun tsuratata tsugunawa tayi sannan tace dan Allah kayi hakuri karka masa komai yaya na ne, kuma abba nane yasa shi ya dake....
Bata kaiga karasawa ba taji andauketa cak ana tafiya da ita"
Wuntsula kafa take tare da kara me tsanani"
Tana kallo ya shiga da ita wani gida wadda kusan shine gida na marusu karfi agunwar"
Wata dattijuwar mata ce ta fito aguje tare da fadin auta yau lfyr ka kuwa?
Bece komai ba kokarin shegewa dakinsa da ma'u kawai yake, ganin haka mahaifiyar tashi ta sake shan gaban shi tare da cikuikuye hijjabin ma'u tace haba auta bansan ka da wannan dabi'a ba, ka dubeta dakyau mana islamiyya zata, idan ma wani abu ta maka toh kayi hakuri kaji?
Idonshi ya dago ya daura akan na mahaifiyar shi sannan yace ummi ba abinda tamin, kawai naga tsohunta bashi sonta ne"
Hmmm auta kataba ganin Mutun ya haifi da yace baya so?, yanzun dai sauketa sai muyi mgn"
Ummi da inason ne nasata akatifa tayi bacci"
Sai wannan lokacin ma'u ta samu bakin mgn cikin kuka tace wlh ni banajin bacci mkrnt zani"
Sai kinyi bacci wannan dole ne"
Daker da sidin goshi deeni ya sauke ma'u amman duk da haka hannunta na cikin nashi"
Kujera ummi ta aje guda 2, kan daya ya zaunar da ma,u sannan yaja dayan ya zauna, cikin Wata irin murya yace ummi kawo mata kokona tasha dan da ganinta bata karya ba"
Zare ido ma'u tayi domin ita bata iya shan kokoba baya ga hakama ai makaranta zata, gashi lokaci na kurewa, hawaye kawai taji yana zobo bata acikin zuciyarta tace meyasa ban kyauce ma hanyar da zamu hadu da deeni ba? Waini me yake shirin faruwa dani?, Allah ina rokonka karkasa nazama sanadin BUGAWAR ZUCIYAN Abbana"
Daidai lokacin ummi ta ajiye babban kofi cike da koko, sannan ta mikawa ma'u ludayi"
Girgiza kai tayi tare da fadin ummi wlh ni akoshi nake nakarya kafin na fito, mikewa ta fara sannan ta sake cewa inason zan wuce mkrnt dan abbana bayanson ina tsayawa ko ina"
Fincikota deeni yayi ya maidata kan kujera sannan ya dauki kofin kokon Yasa ludayi ya deba ya nufi bakinta, yace bude"
Girgiza kai tayi sannan tayi raurau da ido tace nifa wlh akoshe nake"
kibude nace ko dan ni babu ruwana da koshin ki"
Babu yadda ta iya dole ta bude baki deeni yaita dura mata koko tasha kusan rabi amai ya kece mata, daga deeni har ummi suna tsaye akanta hartayi ta gama"
Deeni na rike da hannun asmau yana mata sannu, kan kujerar ya maidata sannan ya dauki ragowan kokon nan yacigaba da bata"
Tanashan kokon tana kuka samuda tsabar bakin ciki"
Duk abinda suke ummin deeni dake wanke2 agefe tana satan kallon su, ganin inda ma,u take hawaye yasata fadin haba auta ka kyale yariyar nan haka indai baso kake ta amaye yanhajinta ba"
Ummi nifa so nake nakoya mata sha saboda gaba"
Hmmm auta Allah ya shiryamin kai"
Saida tashanye kokon tas sannan ya juya yace ummi sammana goro"
Kallon shi tayi sannan tayi murmushi, mikewa tayi ta nufi daki tana kara binshi da kallo"
Zuwacan ta dawo dauke da roban da take jika goro ta ajiye agaban su"
Hannu deeni ya saka ya zabe fararen ciki ya mikawa asmau haka taita karba tanaci badan ranta naso ba"
Ummice ta gama wanke2 tamike ta dauki kayan zatakai kitchen kallonta ne yakai kan deeni daketa dirkawa ma'u goro tace"
Kai jama'a auta waikai meyasa baka da kan gado ne, ya zaka dauki goro kaita dirkawa yar mutane, kai komai bakayin shi ahankali saidai da karfin tsiya, kitchen ta shige tana cigaba da korafi"
Mayar da goron dake hannun shi yayi cikin ruwan sannan ya juya ya kalleta yace toh yanzun inna zan rakaki makaranta ko gida?
Ahankali tace karfe nawa ne yanzun?
11:15am ya fada yana kallon cikin idonta"
馃槼 Nashiga uku ni gida zani"
Daidai lokacin ummi tayi kiran deeni, dan haka ya mike yana fadin barin dawo"
Asmau bayan shi tabi da kallo tana ganin shiganshi ta ta mike ta kwashe takalminta ahannu ta fara ta fiya cikin sanda"
Ahankali ta bude kofar gidan ta fallah aguje"
Karan kofar gidan ne ya fito da ummi da deeni daga cikin kitchen din"
Ahanzar ce ya nufi kofar gida, hango ma,u yayi tana falla uban gudu dan haka abin yai matukar bashi dariya"
Dariya yake sosai besan cewa yayi nisa adariyar ba saida yaji muryuyin yan mkrntr su ma,u , cikin sauri ya murtuke fuska sannan ya nufi gida"
Kujerar da ma,u ta tashi yaje ya zauna sannan ya dauke alaiyahun da ummi take tsinkewa ya fara tayata"
Dagowa tayi fuskarta dauke da murmushi tace"
Auta wannan yariyar a ina ka samota?
murmushi yayi kadan sannan yace nan nake ganinta idan zata mkrnt"
Itama murmushi tayi tana kallo cikin idon deeni sannan tace auta da alama dai ka fada soyayya"
Murmushi yayi kadan sannan ya dan basar yace a'a ummi"
Fuskanta kara fadada tayi da murmushi tare da kara kallon cikin idonshi tace toh idan warin ya bunkasa ai zamuji, amman dai akwai shawaran da zan baka"
Kai ya daga ya kalleta sannan yace inajin ki ummi"
Auta ba atura soyayya da karfin tsiya, ita mace yar lallashi ce, idan har kana son tasoka toh ka daina ta kura mata in banda karfin hali irin naka da baka son azauna lfy ya zaka takura yariya dole saita sha koko"
Ummi jinayi kawai inason tasha"
Toh daga yau idan ka bata wani abu tace bataci karka matsa mata"
Zan bari ummi amman ni basonta nake ba, kawai jarumtar ta ke burge ni"
Hmmm kawai ummi tace sannan taci gaba da kallon sa"
Itako ma,u saida ta ganta aharaban gidan su ta tsaya tsayawa tayi numfashin ta ya dawo daidai sannan ta shiga gida"
Ranan wuni ma,u tayi tana tunanin duna, ita dai batasan abinda ke damunta ba hakanan takeson ganin sa, duk da cewa yau ya firgita ta besa taji tana kinsa ba"
Shima deeni adaren ranan be runtsaba tunu ma,u kawai yake yana kyalkyata dariya hakika dabi'unta na matukar birgeshi, kosawa yayi gari ya waye haka ya kwaanaa babu bacci"
Washegari ma,u ta shirya zuwa makaranta kamar yadda ta saba, dakin mama ta nufa ta duba bata ciki dan haka ta nufi dakin abba"
Atsorace take dan tunda abin ya faru abba baya amsa gaisuwanta"
Tsugunawa tayi sannan ta gaida su babu laifi yau abba ya amsa gaisuwanta cikin sakin fuska, sallama ta musu tana kokarin mikewa abba ya dakatar da ita"
Hannu ya mika mata dan haka ta matsa ta mika nata"
Ahankali yace mamana idan na tambaye ki zaki gayamin gskiya?
Eh ta fada jikinta asanyaye"
Asmau ni mahaifin kine karkice zaki boye min wani abu, kinason namiki aure yauzun?
Zaro ido tayi馃槼 tare da fadin aure abba ai nayi kankanta kuma ma ai duk acikin kawaye na babu wacce akama aure"
Bakiyi kankanta ba mamana, dan da ace kin jawomin abin mgn gara namiki aure, nasan kina da lbrn abin da ya faru da yar uwar ki, banason makamancin hakan ya faru akanki"
Wasa ma,u ta farayi da zuben dake hannunta, hawaye na zuba aidonta tace"
Abba dan Allah karkamin aure wlh ni bana kula kowa, Abba nifa ko saurayi bani dashi kum.....
Abba ne ya dakatar da ita da fadin ya isa mamana, nikaina inason ace kinyi sauka sannan namiki aure, Amman al' amarinki ya fara bani tsoro"
Rushewa ta karayi da kuka tana fadin nashiga uku abba ka yadda dani wlh wlh bana sauraran Kowa....
Dakatar da ita abban ya sakeyi akaro na biyu sannan yace naji na amince dake amman inason kimin alkawarin rike mutuncin ki amatsayin ki na 'ya mace, karki yadda wani ya keta miki hijjabin ki, idan kikamin haka kin gama min komai duniya da lahira"
Nayi alkarin abba"
Murmushi abba yayi sanna ya sake cewa mamana duk lokacin da kikaji kinason aure ki sana da mahaifiyar ki ko Dada, nikuma in Allah ya yarda acikin satin zanmiki aure"
Dahaka ma,u tayi sallama da iyenta ta nufi makaranta, ko ahanya hawaye be daina zubo mata ba ba komai ke firgitataba sai furucin abba wai zai mata aure, tunda take bata taba kawo tunanin wani aure, kallo jikinta tayi sanna tace ko kallon namiji bazan kara ba, balle ace za,amin aure"
Yau ma'u canza hanya tayi ta lungun nan taabi dan ma karta hadu da deeni"
Koda ta isa makarata batada walwala kaman da , baayan antashi ma ta lungun ta saake bi, dan haaka yau basu ahadu da duna ba"
Tundaaga ranan ma'u takebin logu har satin ya kare"
Abangaren deeni kuwa. Kullum yana zamaan jiiran wucewa asmau amman har satin ya wuce babu itaa dan haka ya fara tsinta kanshi ciki damuwa"
Yau ta kama asabar tun safe ummi kejiran fitowa deeni amman shiru dan haka ta nufi dakin"
Tura kofar take tana fadin auta wai kwana 2 meke damunka ne? Nifa kwana 2 naga ko mgn bakaso"
Hangoshi tayi nannade abargo dan haka ta tsaya sororo zuwa can tace auta ban saba ganin ka cikin wannan halin ba, tunda kazo duniya nasan jarumi na Haifa, dafashi tayi sannan ta sake cewa auta nasan kaiba rago bane gayamin meke damun ka?
Tashi yayi ya zauna ya jingina bayanshi da jikin bango, sannan ya rufe ido"
Girgizashi ummi tayi tare da fadin auta yazun ni har kana da wani sirri daza boyemin?
Bude idon shi yayi dasuka rune suka zama jawur yace ummi yariyar nan ce yau sati 1 kenan ban ganta ba"
Kwashewa ummi tayi da dariya daman tuni ta dagoshi cikin dariya tace au daman saboda asmau kayi yajin cin abinci? lallai auta kana da aiki, toh meya hana ka kabita gidan su?
Cikin kosawa yace toni nasan gidan su ne??
Kallon shi ummi tayi sannan ta kauda kai, damuwa tagani karara a idon shi , tunani ta shiga yi wacce hanya zatabi ta gano ainihin abinda ke damun sa"
Bakin katifan ta zauna sannan ta jawoshi jikinta ta kwatar"
Hannu ta tura cikin gashin kansa tana shafawa take fadin auta ka daina boye min, nariga na fahimci son Asmau kakeyi, mu aje wannan agefe yanzun Meye yake damun ka har ka kasa dannewa?
Ajiyan zuciya ya sauke sannan yace ummi tunani nake ko wanne hali yariyar take ciki, dan naga alaman ba'asonta agidan su, ranan gabana wata munafukar kakata ta mareta, kuma ranan da nashigo da ita gidan nan wani yayanta ya daketa duk ya lalata mata fiska, ranan naso nasa *Caka* ya kawomin *Duna* ya bashi misali, amman sainaga yariyar ta tsorata tana zubar da hawayenta"
Nisawa yayi sannan ya kalli ummi data dukar da kanta kasa yace ummi kinajina narantse da sarkin dake busan numfashi duk wadda ya kara daura hannun shi akan yariyar nan da sunan duka ko mace ko namiji ko yaro ko babba ko tsoho ko tsohuwa kai gemunshi najan kasa ne saidai uwassa ta haifi wani, kai inbansa *Duna* yamin dambu da namansa ba shege nake"
Mikewa ummi tayi ciki matsanancin tashin hankali tabbas duk abinda ya fada zai iya aikatawa, amman wani hali zasu shiga idan ya aikata irin wanna aiki acikin wannan uguwar da mutanan cikinsa ke kemar dabi,un autan ta"
Kulum mutanen cikin unguwan kuka suke da halinshi wasuma cewa suke karya bata musu tarbiyan yara"
Wannan tunani yasata fadin haba auta ai idan kayi haka ita Asmaun taka bazata soba, banda abinka kuma kana son yariya kuma ka daki yayanta? Ko kana son su hanaka aurenta ne?
Hmmm Ummi kina nufin ko yariyar nasona yan uwata zasu iya hani aurenta?
Kwarai kuwa auta kasan mutanen garin nan sunsha babban da mutanen garin *Jaguma*"
Murmushi yayi Me kama da yake sannan yace ummi ashe za,a zubda *Jini*, be jira me zata ce ba ya mike ya fice"
Itama ummi jiki babu kwari ta fito ta kama aikace aikacenta"
Yauma kamar kullum 11:30am aka tashi su ma,u amakaranta, ita da zainab suka jera, ta lungu sukabi jefijefi suna taba hira har suka iso gida"
Aharabar gidan taga motan yaya usman saida gabanta ya fadi dan dama can bashiri sukeyi ba"
Tanashiga ta wuce dakinta saidai ko adakinta tanajin sautin muryan shi dan shi baya mgn ahankali muryan nan kamar ana buka ganga"
Kosawa tayi ya gama abinda yake ya wuce dan hankalinta ya kasa kwanciya"
Kwanciya tayi gefen gadonta ko kayan makarantan ta kasa cirewa saboda tsabar tsoron yaya usman datake, bacci ne ya fara dibanta acikin baccin taji muryan yaya usman yana kwala mata kira"
Asittin tamike ta nufi dakin mama tana matsa ido"
Atsaye ta samu yaya usman cikin kakin sojuji da alma tafiya yake shirinyi"
Ke dan ubanki kin dawo makarata bazakizo kice kin dawoba zaki wuce daki ki kwanta?
Kwalkwal tayi da ido kaman zatayi kuka"
Jin shiru yasa yasake cewa shegiya makaryaciya dallah zoki kwashe ledojin nan ki kaisu kitchen"
Jikinta har rawa yake wajan daukan ledan, bata san cewa ledan da nauyiba saida ta aje a kitchen taji hannuta ya rike"
Guri ta samu ta zauna saida taji tashin motar shi ta miki tana kokarin fita sukaci karo da mama"
Murmushi mama ta mata sannan tace Asmau je kicire kayan makarantar kizo kitayani aiki"
Mama aiki kuma, bayan naga goggo tani ta gama girkin"
Eh wannan na yayanki ne ya kawo amai zaiyi baki"
Baki? toh mama matarsa fah?
Akaikaice mama ta kalleta sannan tace idan bazakiyi ba ki bari"
Daki ta wuce ta canza kaya sannan ta koma kitchen ta samu mama da goggo tani sun kacame da aiki, itama wani aikin ta kama nan danan sukaci rabin aikin"
Mama na tsaye tana karasa soyan kaji asmau ta matso tace mama kawo na karasa, cikin sauri ta mikamata ta matsa gurin tani, zuwa can asmau tace caf mama bakin na yaya harsu nawa ne dazai basu wannan uban naman?
Oh asmau, ni dai mutun daya yace min, yanata min kwatancen shima bangane shi ba, sunan da naji yana kiran shi *MANGA* yasa na gane mahaifinshi *Alhaji Buba Manga* mutumin babaku ne sosai kafin ya koma Abuja"
Shima Soja ne?
Eh mama ta bata amsa cikin kosawa
Toh wai meyasa bekaima momy shi ta dafamai ba?
Dariya mama tayi sannan tace aikinsan hajiya amina bazata shiga kitchen ba, masu aiki zataba, shikuma kisanshi da iyayi"
Dakuma shegen fadinrai ta fada azuciyarta, take zacen deeni ya fado mata wai saiyaci uwar yaya usman, tunawa tayi da yadda yake ciccijewa yana karkata hanci da baki sainaci uwassa!! kyalkyalewa tayi da dariya dan tayi nisa atunani tama manta ba ita kadai bace agurin"
Dariya take babu kaukautawa ta kurawa guri daya ido"
Daga mama har tani mikewa sukayi suna binta da kallo, afirgece mamata tace ke asmau menene haka?
Batasan sunayiba kuma har yanzun dariyar take, takawa mama tayi da sauri ta girgizata cikin sauri ma,u ta hadiye dariyarta"
Asmau kinyi gamo ne? Cewar mama tana zare ido"
a,a mama wani abu na tuna jaye hannuta tayi tare da fadin barin nayi sallah na tafi makaranta"
Tundaga lokacin jikin mama ya mutu murus har lokacin da mau taxo mata sallama xata wuce"
Ahanyama babu abinda take sai tunanin deeni dan haka yau tanajin bata iya hakuri idan bata ganshi ba"
Bata biyawa zainab ba dan yau bazatabi ta lungu ba"
Sai dai har takai kofar gidansu deeni bata ganshii ba dan haka wata zuciyar tace kii shiga gidan mana"
Takawa tayi ahankali harta isa kofar gidan idonta tasa asakon kofar ta leka babu kowa sai ummi datai zaune kan kujera ta rafka tagumi"
Gabantane
yayi mugun faduwa sakamakon jin kokan katan kare abayanta, afirgice ta juyo sukai ido 4 da karan, baki ne mummuna bashi da kyan fasali ko kadan"
Tsugawa taga karan yayi zuwa can ya dago da karfii kaman zai yago mata fuska ganin haka ma,u ta saka uhu tare da neman hanyan guduwa"
Duk inda tabi shima be yake tare da kokarin yago hajjabinta ganin haka mau ta cire hijjabin tayi titi aguje"
Jitayi anjawota atsorace ta waigo deeni ne tsaye, gawani mutun mummuna agefen shi bayanta ta waiga ta hango karan aguje dauke da hijjabinta a bakin shi"
Ai batasan lokacin da ta kadandane deeni ba tana tsala uban uhu"
Kokarin rabata da jikinshi yake yana fadin Ohh sorry gaisuwa ce fah, *Duna* kenan meyasa kin cika tsoro.......
Heart beat
*Mmn Yazeed*鈥�
[22:50, 12/19/2017] 鈥�+234 806 858 0203鈥�: 馃挆馃挐馃挐馃挆
鈥�*BUGUN ZUCIYA*鈥�
( 鈥婬eartbeat鈥�)
馃挀馃挐馃挆
馃挆
馃挀馃挐馃挆
鈥婤y鈥�
馃挆
鈥嬧€�*Fadeela Lamido*
*@AM拢拢NCI WRITER'S ASSOCIATION馃*
*Na sadaukar da wannan shafin gareki馃憞*
馃憫Queen馃憫馃槝
*Nima ILove u wojuga wojuga wlh馃槏*馃嵀
1鈨�5鈨� to 1鈨�6鈨�
馃搾 Jin ya ambaci gaisuwa ce yasata jan jikinta ta koma gefe, tare da karabin karan da kallo"
Haryanzun hijjabinta na bakin shi, matsowa yayi ya ajiye hijjabin akasa sannan ya koma kusa da deeni yana goga kanshi ajikin deeni"
Sai alokacin ma'u ta tuna jikinta babu hijjabi hannu tasa ta rufe kirjinta, sannan ta matsa ta dauki hijabinta ta saka"
Karan tabi da kallo har yanzun Yana gaban deeni sai shafamai kai yake alman lallashi"
Tsaki taja azuciyarta sannan tace wannan bakin karan ne duna, ganin inda yake lallashin karan abin yai matukar bata haushi, hawaye ta fara matsowa acikin zuciyarta tace yanzun akwai miyon wannan mumman karan ahijjabi na wlh Allah ya isa, bata san cewa mgnr ta fito fili ba saiji tayi deen na fadin wa kikeyiwa Allah ya isa.....
Atsora ce tace ni bada kai nake ba, da wannan mummunan karan naka nake"
Ke *duna* kike kiran mummuna kinyi na farko yariya karki kara, idan kuma kika kara zan barki dashi"
Kallo kawai ta bishi dashi har yanxun lailaya kan Karen yake, harga Allah haushi yake bata dan me xaisa hannun sa yaita shafa kare batasan lokacin da tace toh kadaina shafashi haka mana"
Inaruwan ki ko kanki nake shafawa?
Kasa tayi dakai tana cigaba da kunkun"
Tunda ta fara motsa bakinta deen
yake kallon bakin amman ya kasa gane kalma daya da take Dada dan haka yace banajin abinda kikecewa"
Turo baki tayi sannan tace ai badakai neke ba"
OK da *Duna* kike kenan?
Shiru tayi batare da tace komai ba dan haka deen yayiwa caka mgn da hannusa gani tayi ya matsa can gefe ya tsaya atsakiyan hanya"
Kallonta ta mayar kan deeni gani tayi ya dago kan *Duna* yana mai mgn da ido aguje yayo kanta tare da haushi irin na mahaukatan karnuka"
Cikin gidan su deen tashiga aguje ummi na zaune tana wanke2 tayi fatali da ruwan cikin jikita ta shige ta kwakumeta"
Kobata tambaya ba tasan karen deen ne ya biyota dan tun dazun takejin haukan sa, rungumeta tayi ajikinta tare da fadin uban gidan nasa baya wajen ne ya bari yana tsorata Ki?
Sai alokacin kuka ya kwace mata cikin kukan tace ai shine yace mai ya biyoni"
Daidai lokacin deen ya shigo yana murmushi harara ummi a zubamai sannan tace nadai hanaka shigowa da karan nan uguwar nan kaki bari ko?
Ummi nakawoshi ne yagaida wannan yariyan ita kuma sai zaginshi take"
Ai dole ta xageshi auta tunda bata saba ba ita gani take tsoratata yake, yanxun zoka rakata ta shiga makaranta"
Makaranta ? Yau bazata makaranta ba lokacima ya kure"
Bude baki ummi tayi xatayi mgn amman deen sai ya mata wani irin siririn fito tare da kada mata hannu nan danan taja bakinta ta tsuke , shiko deen dakin sa ya shiga"
Daga ma,u har ummi tsaye suke saidai jikin ummi asanyaye yake kamar tana cikin damuwa"
Zuwa can ta waigo tace Asmau dan Allah ga abincin auta nan a kitchen taimaka ki kai masa rabon sa da abinci ya dade basan me yake damunsa ba"
Shiru ma,u tayi kanta akasa acikin zuciyarta tace toh meyasa bayacin abinci? Afili ko cewa tayi ummi wlh tsoron shi nakeji"
Murmushi ummi tayi sannan tace a'a karkicemin kinajin tsoron sa keda mutumin ki kuma? bubu abinda zaiyi miki tashi maza kije"
Jikinta babu kwari ta nufi dakin da taga deeni ya shiga sallama tayi abakin kofar bayan ya amsa tashiga"
Dakine dan karami daga can gefe akwai yar karamar katifa gefen katifan ko wukakene an jigine su a jikin bango"
Gyare dakin yake tsaf ahankali ta karasa gaban katifan ta aje kwanan tana kokarin mikewa ya rike hannun cikin sauri ta dago ta kalleshi"
Ido suka tsurawa juna natsayon wanni lokaci take ma,u taji tsigan jikinta na tashi nan danan idonta yacika da kwalla amman takasa dauke idonta akanshi"
Shiko deen wani irin farin ciki yakeji wadda betabajin irinsa ba har yanajin inama su kwana ahaka"
Murmushi yasaki wadda yai matukar dacewa da fuskanshi azuciyar ma,u cewa tayi inama ace haka fiskarshi take kullum"
Kasa ta sauke idonta tare da sauke ajiyan zuciya, haka shima deeni ajiyan zuciya ya sauki sannan yasa hannun shi ya sake dago fuskanta"
Runtse idonta tayi cikin wata dashashshiyar murya taji yace *Asmau* bude idonki ki kalleni"
Koro na farko da deeni ya kira sunanta agabanta dan haka taji yafi kowa iya kiran sunanta"
Bude idon tayi saidai baxata iya kallon sa ba kamar yadda yace dan haka ta durkusan da kanta kasa"
Jawota yayi daf dashi ya zaunar sannan yace meyasa kwana 2 baki zuwa makaranta?
Ina xuwa ta fada atakaice"
A'a karya ne bayan kullum inajiran ki akofar gida amman ban ganin wucewan ki"
Wlh kullum ina zuwa bandai wucewa ta nan ne "
Me yasa ?
Shiru tayi tana tunanin tagayamai abbanta yace zaiyi mata aure ne ko karta gayamai, idan bata gayamai ba toh mezata cemai?
Tunanin me kikeyi?
Bakomai "
Shiru yayi xuwa can yasake dagowa yace yau kinji ganina kenan shine kikazo kina leka mana gida"
Turo baki tayi kaman zatai kuka zuwa can taji ya sake cewa wadda ya dauki ki a mota ranan shine babanki?
Eh tace tare da kurawa kirjin shi ido"
Shiru yayi yana kallonta zuwa can yace me kike kallo?
Kai tsaye ta nunamai sarkan dake wuyan sa"
Kina sone?
Tana wasa da yatsunta take fadin a'a kacire ne beyi maka kyauba"
Dariya yayi sosai har hakoran shi suka baiyana zuwa can yace naji tunda bakison ganina da sarka saikizo kicire da kanki"
Tana cigaba da wasa da hannunta tace kacire da kan ka ai babu kyau mace ta dinga taba namiji"
Axuciyar shi yace kina da wayo babu kaifi afili kuwa cewa yayi toh bakison nadaina sawa kenan?
Mikewa tayi tare da fadin nixan tafi kar atashi amakarata bansani ba"
Daure fuska yayi sannan yace dawo ki zauna, idan lokaci yayi zan fada miki"
Zama tayi nesa dashi badan ranta yaso ba, kanshi ya turo mata ahankali ta fara warware sarkan duguwa ce sosai, kallon sarkan take tana mamakin wai mutum da hankalin sa ya dauki wannan karfen yasa ajikin sa"
Shiko deeni kallonta yake yana murmushi yana da tabbacin yadda *ZUCIYAR* shi ke buguwa haka ta ma'u ma take bugawa, xuben da ke karamin yatsan shi yacire ya kamo hannun ma'u ya zura mata"
Harcikin zuciyarta taji dadi kallon zuben tayi sannan tace nagode"
Murmushi yayi sannan yace toni me xaki bani?
Tsintan kanta tayi da cewa me kakeso na baka?
Duk abinda kika bani zanyi farin ciki dashi"
Cikin sauri ta ciro xoben da abban ta ya saya mata ta mikamai"
Nuke kafada yayi kaman yadda yara keyi yace bazan karba ba, ni ai saka miki nayi dan me xaki bani ahannu"
Shiru tayi cikin rashin jin dadi zuwa can tace ka karba ai be dace bane ina mace kuma.. ..
Kasa karasawa taayi dan haka deen yaja tsaki ya kwatar da kanshi akan katifan"
Ganin haka yasa ma'u taji babu dadi dan haka ta kamo hannun saidai duk yatsan da ta nufa zuben baya shi, daker ya shiga karamin yatsan shi, shima be gama shewa ba"
Tagama sawa tana kokarin mikewa ya mirginota jikinsa ya rungumeta tsam ajikin shi, tare da sunbata goshinta kumatunta zuwa kan lebenta, neman rikicewa yake, dan haka ma'u tafara kokari kwace kanta take mgnr abbanta ya fado mata, hawaye taji yana zubu mata"
Daidai lokacin ummi ta dago labulen cikin sauri deen ya mirgina ma'u gefe sannan ya cigaba da sauke ajiyan *ZUCIYA*"
Cikin sauri ma'u tamike tana gyara hijjabinta"
Itako ummi kallon deen take cikin bacirai zuwa can tace auta har ka manta alkawarin dakamin?
Be iya cewa komai ba dan koya bude baki besan me zaice ba"
Yana kwance yanajiyo fadan ummi, dakanta ta rike ma'u tayo waje da ita"
Jin asmau zata tafi yasashi mikewa dasauri ya fito samu yayi daidai ummi ta budewa ma'u kafar cikin sauri ya rike hannuta tare da zuba mata jajayen idon shi sannan yace gobe zaki zo ?
Tana share hawaye tace eh"
Murmushi yayi kadan sannan ya karkata kai"
*****
Tafe take tana kuka dan daganin yanayin garin andade da tashi makaranta"
Ta saka wannan ta kwance wancen tana tunanin wata karyan zata shirya"
Taci rabin ta fiya taga motar yaya usman ta wuceta"
Innalillahi ta fada azuciyarta Allah yasa be ganeni ba"
Hango motar tayi ta tsaya tana dawowa da baya"
Jitayi 'ya'yan hanjinta na motsawa daidai saitinta yaya usman ya tsaya ya zubo mata idonta shi sannan yace ke sai yanzun kike dawowa daga makarantar?
Mutumin dake zaune agefen shi ta kure da ido, gani take kaman kunki ne domin kwata2 baya motsi, jarida ce bude ahannun shi idonshi sanye da farin glass"
Yaya usman ne yace kagamin shegiyar yariya ina mata mgn tana kallon wani guri"
Zabura tayi ta dawo cikin hankalinta ta kara matso kuka tace"
Yaya wlh kare ne ya tareni ahanya ya hanani wucewa.....
Kutumar ubanki shigiya yar iska, ni xaki rainawa hankali duk cikin daluban be tare kowa ba saiki ? A ina kika tsaya?
Cikin kuka ta tattaro hijjabinta tace wlh yaya da gsk ne kagama yadda karan ya lalatamin hijjabi"
Takaici ne ya kama usman dan haka yace Allah ya kara, dayasani ma ya ciccije ki dan ubanki, kin tsaya shashanci duk dalubai sun wuce sun barki dallah dobeki saikace doluwa, ni shiga mota mutafi"
Tashiga mota? mutumin dake kusa da yaya usman ya tambaya batare da ya waigo ya kalleta ba har yanzun idonshi nakan jaridan"
Waigawa usman yayi ya kalleshi sannan yace wannan itace kanwata *Asma'u* danake baka lbr, wlh kwata2 yariyar nan batajin mgn"
Idonshi akan jaridan yace aina ganeta, kanta na rawa, naji kaman kana cewa ta hau mota, ai kamata yayi ta isa gida kafin mu isa"
Kumafa hakane usman ya fada yana kallon ma,u zuwa can yace asmau kafin mu isa gida nasameki acan, idan har kika bari na rigaki isa gida kashinki ya bushe"
Arude tace yaya amota kake fa ?
Muryan bakon taji yace ke!!, dakaran ya yabiyoki bakiyi gudu ba?
Idonshi nakan jaridan dan haka ta murguda baki tace nayi?
Toh irinshi zakiyi, idan kuma kikabari har mukaje gida bakizo ba, zan kirga mintocin da kika kara duk minti 5 yana da bulala 15, be jira mezatace ba yace usman muje"
Figar motan sukayi kankace me suyi nisa sai kellin motar take hangowa"
Cije lebe tayi sannan tace lallai abokin yayan nan bakin mugune har yafi yaya mugunta idan ba samun guri ba daga zuwanka bakunta zakace zaka dake ni ko gidan ma bakaje ba?
Cafdin ta fada afili wlh bazan tsaya ka dakeni ba idan ko ya dakeni da abba zan hada su"
Juyawa tayi ta fara tafiya lokacin data shiga gida ana kiran mangariba"
Aharaban gidan taci karo dasu zasu masallaci"
Abokin yaya taga ya kalli agogon dake daure ahannu shi sannan yaci gaba da tafiya batare daya kalleta ba"
Koda ta shiga gida mama bata nuna fushinta ba"
Dakinta ta wuce tayi wanka sannan ta dauro alwala Riga da siket ta saka na atamfa sannan ta saka babban hijjabi. ta tada sallah"
Bayan ta idar ta wuce dakin mama"
Tana shiga mamata tace ke kuma garinyaya kare ya tareki kinason kizama ballagaza ko?
Shiru tayi dan haka mama taja tsaki sannan tace wuce Ki dauki abinci ki kai falon abban ku"
Bata kawo komai a xuciyarta ba, ganinta abba zata ajewa abinci kafin ya shigo dan haka da karfinta ta shiga falon"
Turus tayi lokacin da taga abokin yaya zaune akan doguwan kujera ya miki kafa fuwan shi"
Cikin sauri ta aje abincin ta juya zata fita taji muryan yaya usman yace"
Ke zonan?
Dawowa tayi ta tsaya tana kokarin matso hawaye".
Jitayi ya sake cewa *JAMAL* gata"
Kaman jira yake ya juyo ya sakko da kafan shi kasa sannan yace kina da bulala 30"
Kallon su kawai take dan ita gani take wasa suke zuwa can taga wadda yaya usman ya kira da suna *JAMAL* ya mike sannan ya saka hannu a aljihun gaban gaban wandon shi daidai guiwa ya ciro wata zafgegiyar bulala sannan yace daga zanin Ki.....
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
.鈥�
[22:50, 12/19/2017] 鈥�+234 806 858 0203鈥�: 馃挆馃挐馃挐馃挆
鈥�*BUGUN ZUCIYA*鈥�
( 鈥婬eartbeat鈥�)
馃挀馃挐馃挆
馃挆
馃挀馃挐馃挆
鈥婤y鈥�
馃挆
鈥嬧€�*Fadeela Lamido*
*@AM拢拢NCI WRITER'S ASSOCIATION馃*
1鈨�7鈨� to 1鈨�8鈨�
馃摍 Na daga zani ? Lailai wannan dan rainin hankali ne aiko yaya betaba cewa na daga zanina ba, bare wani katon banza"
Muryan yaya usman taji yana cewa wai bada ke ake mgn ba?
Karya murya tayi sannan tace ai ba zani bane siket ne"
Abokin yaya taji yace koma menene ki dageshi sama"
Cikin sauri ta kalleshi saidai shi ba ita yake kallo ba"
Mikewa yaya usman yayi ya fice dan haka Asmau taita zubawa abokin shi harara"
Zuwa can taga ya fara tahowa yanazuwa daidai inda take yasa kafa ya kwasheta"
Ganinta kawai tayi akasa cikin sauri ta fara kokarin mikewa amma ina jitayi kwankwasonta ya rike"
Daker ta iya dago kanta ta kalleshi daidai lokacin daya dago hannu ya sauke mata mari"
Innalillahi wa inna ilaihir rajun'un ta fada da karfin saboda zafin marin ya shigeta, zaki daga ko bazaki dagaba?
Wlh zan daga arude ta Kwaye zanin har zuwa guiwa, tare da tsiyayar da hawaye"
Bulalan ya daga sannan yace idan kinga dama ki kirga, dan ni ba kirgawa zanyi ba, kuma idan kika sosa bandashi alissafi"
Fukanta cike da hawaye ta kalleshi acikin zuciyanta tace lallai wannan bakin mugune so yake yaga karshena, nan danan taji wata dakiya tazo mata, dan haka ta tsaya cak"
Kin shirya?
Eh tafada tana kauda idonta gefe"
Bulalan ya daga yaita zula mata tuntana daurewa harta kasa taita zuba uhu"
Shiko *JAMAL* kaman kara zugashi take har wani tsalle yake yi"
Goggo tani ce tajiyo uhunta tundaga cikin gida harda gudunta ta nufi idan take jiyo sautin kukan daker ta kwaci ma,u ahannun sa"
Hargun mama goggo tani takai ma'u tanaci gaba da korafin cewa adaina mata irin wannan dukan haka kwanaki usman ya mata dan banzan duka kartaxo ta saba da duka"
Mama batace komai ba mikewa kawai tayi tabar dakin"
Nan ma,u ta kwanta tanajawowa *Jamal* Allah ya isa acikin zuciyarta"
Ko ina ajikin ma,u ciwo yake dan yau abin ya mata yawa ga wahalan da *Duna* ya bata gana wannan dan iskan abokin yayan"
*****
Washegari ma haka ta tashi batajin kwarin jikinta dan haka batace zata makaranta ba"
Misalin 11 tayi wanka ta danji dadin jikinta, falon Abba ta wuce acan ta samu mama"
Gaban abba ta zauna ta tankwashe kafa sannan ta fashe da kuka"
Nan danan hankalin Abba ya tashi, zaman shi ya gyara tare da kura mata ido sannan yace"
Mamana waye ya taba ki?
Cikn kukan tace ba yaya usman bane yacewa abokinshi wai banajin, shikuma kawai sai ya ciro bulala ya hau dokana"
Abokin nasa?
Eh Abba"
Duka fa kika ce mamana?
Xanin ta ta fara dagawa tare da fadin eh abba kagama gurin"
Babban mgn Abba ya fada bayan yaga inda jikin ma'u yai rudu2"
Mikewa yayi sosai sannnan ya daga waya ya kira usman"
Cikin Monti 15 suka iso, dukka su jallabiya ce ajikin su fara kar"
Tunkafin su zauna abbba yake fadin a'a wanake gani kaman *Jamal*"
Mumurshi kamal din ya saki yana shafa keya yake fadin nine abbba"
Bayan sun gaida abbba hira suka hauyi, dan haka ma'u ta Kule"
Mikewa tayi tana kokarin tafiya Abba ya dakatar da ita sannnan yace"
Mamana kinga wannnan sunan shi Jamal yayanki ne shima, nida mahaifin shi tare mukayi wasa, dan haka yadda usman yake da daman hukuntaki shima yana da dama kijji ko"
Tana barin falon ta fara kunkunai kai tsaye ta wuce dakin mama dan daman tuni ta bar musu falon, zama tayi tare da share guntun hawayenta sannan taci gaba da kunkunan ta"
Mama na gefe tanajinta jefi jefi tana tsintan abinda take cewa, zuwa can tace"
Kee!!!! Tashi kibani guri, haka kurun zakizo kisani agaba kinamin mita toh me kikeso nayi rama miki zanyi kome?, yariya banda fitsara ba abinda kikasa agaba ke wacece da baza'a dakeki ba?, to kici gaba kece zakisha wahala"
Dahaka mama ta fice tabarta adakin"
Itama mikewa tayi tabar dakin"
Tundaga ranan asmau bata sake zuwa makaranta ba har wani satin ya zagayo, gashi kewan deen ya dameta, dan tasan yanzun har ya gaji da zuba ido"
***
Yau ta kama asabar dan haka tunda wuri ma'u tayi sallama ta fito"
Saidai tana fitowa taci karo dasu yaya suna kokarin shigowa"
Dauke Kai tayi taja gefe sanan tace ina kwanan Ku murya ciki2"
Yaya usman ne kawai ya amsa amman jamal gaba yayi, harta kusa fita taji jamal na cewa usman, kunabin bayan yariyar nan Kuwa....
Daidai lokacin suka sha kwana dan haka bataji amsan da yaya usman ya bashi ba"
Tana tafiya tana waige dan gani take kaman Jamal zai biyo ta"
Hango deen akofar gida shine yasata ta manta komai tundaga nesa ya sakar mata murmushi itama mayar mai tayi tare da sunkuyar da kanta kasa"
Tana isa gaban shi taja ta tsaya tare da kara sunkuyar da kanta kasa"
Babu abinda deen yake banda kallonta acin tuhuma ya dago fuskanta sannan yace"
Me yasame ki kwana 2 ?
Shiru tayi tana kara tsurawa kafarta ido"
Girgiza kai yayi sannan ya cije lebensa na kasa Yasa ke daga ido ya kalleta cikin bacin rai yace"
Yayan kin yasake dukan ki ne?
Kanta na kasa ta girgixa kai"
Kanshi ya daga ya kalli sama sannan yace yasin zanyi rashin mutunci wlh, fuskanki ya nunamin an cuceki kuma kina cikin bacin rai wai wanene wannan yayan naki? a ina zan sameshi ?
Nan danan hawaye ya fara zubo mata dan bakaramin takaici takeji ba, haka kurun daga zuwan shi zaisa bulala ya zane ni"
Murya kasa2 tace ba yayana bane, abokin shi ne"
Abokin sa ? Idon shi daya ya rufe sannan ya karkata dayan yace dukan ki yayi?
Hannu tasa ta share hawayen daya zubo mata sannan tace eh"
Uban wanene ya bashi iznin ya dake ki?
Bata iya cewa komai ba illah kukanta daya karu"
OK shikenan dena kuka kingane?, ban ni dashi zan nuna masa daya tabaki gara yaje ya tari babban mota, haduwan mu bazaiyi kyauba naratse sai uwassa ta kasa gane shi"
Yana mgnr ne yana daga hannuwan shi tare da karkace baki"
Ganin inda yake fada yana tiriri yasa ma'u jin dadi ko banza tasamu wadda zai kwatan mata enci, amma tafison deen yayi abin cikin sirri ba baro baro ba dan batason kowa yasan shi arayuwar ta"
Dago kanta tayi sannan tace bari na shiga makaranta idan antashi zan shigo nagaida ummi....
Batajira me zaice ba ta fara tafiya tana jiyo muryan shi yana cigaba da babatu"
Ko a makaranta batayi karatun kirki ba, kawai tunanin hanyan daukan fansa take"
Zuwa can tunanin duna ya fado mata, tabas duna kadai ya ishi jamal amman idan deen ne duka zasu masa dan suma suna takama da karfi, karshema kila su kamashi, amman duna zai iya basu whl batare da sun san waye ya turoshi ba"
Kwashewa tayi da dariya sannan tace inama ina gurin inga ya zasu yi?
Takarda ta samu ta fara rubuta yadda takeson abin ya kasan ce, tana cikin rubutun aka tashi tsayawa tayi ta karasa sannan ta fito"
Lokacin da tafito babu sauran dalubi amakaranta duk sun fita"
Gabanta ne yayi mummunan faduwa sakamakon hango Jamal tsaye shida baba idi"
Batasan me suke cewa ba, tana kokarin fita taga jamal ya wuceta"
Abakin makarantar taga motar yaya usman, budewa Jamal yayi ya shiga, har sun tada mutar yaya usman yace shigo mutafi"
Wani haushi ne ya kamata, tasan duk shirin jamal ne, bayan ta zauna suka fara tafiya banda masifa babu abinda yaya usman ke yi, Jamal ko kauda kansa gefe yayi ya bude jarida"
Ma,u ko hankalinta yana kan dakalin da deen yake zama, yana nan zaune sai raba ido yake"
Suna zuwa daidai inda deen yake ta saka hannuta ta widow motar sannan ta wurgawa deen takardan data rubuta"
Akan jikin shi ya fada, tana kallon deen ya dauka sannan yabi motar da kallo"
Sun gota gurin kadan taga Jamal ya rufe jaridar hannun shi ya aje agefe, sannan ya cire glass din dake idon sa"
Waigowa yayi ya kalleta cikin ido sannan yace"
Usman koma baya....
Heart Beat
*Mmn Yazeed*鈥�
[22:51, 12/19/2017] 鈥�+234 806 858 0203鈥�: 馃挆馃挐馃挐馃挆
鈥�*BUGUN ZUCIYA*鈥�
( 鈥婬eartbeat鈥�)
馃挀馃挐馃挆
馃挆
馃挀馃挐馃挆
鈥婤y鈥�
馃挆
鈥嬧€�*Fadeela Lamido*
*@AM拢拢NCI WRITER'S ASSOCIATION馃*
1鈨�9鈨� to 2鈨�1鈨�
馃摍馃摍 Ahankali usman ya koma baya, kusa da dakalin deeni Jamal yace yayi"
Hannu ya mika ya dauki glass din shi ya maida a idonshi sannan yace"
Ke! Sauka ki karbo dakardan da kikajefa"
Idanuwa ta fito dasu waje zufa taji yana karyo mata, kallo gurin tayi taga deen ya daga bakin shi sama yana fito"
Jamal ya sake cewa ko bakiji abinda nace ba?
Jikinta har rawa yake ta bude motar ta sauka, daga gefen dakalin duna ta hango wata takarda ko kallon inda deen yake batai ba ta tsuguna ta dauka, harta shiga motar tanajin fiton deeni"
Usman ne ya karbe ta kardan ya bude babu komai aciki, tsaki yaja sannan yace kai manga kana da matsala wlh"
Ko kallon shi beyi ba yace kaidai muje kawai, kaima ai matsalan gareka"
Itako ma',u tunda ta dauko tasan ba ita bace, har suka isa gida babu wadda yace uffan"
***
Da yamma tana zaune adakinta tunani ta shigayi ta yaya zata bullowa al amuranta"
Hakika deeni yana matukar burgeta kuma da bi'un shi suna sata nishadi, amman idan ta tuna abbanta gabanta na faduwa"
Koda atunanin ta bason deeni take ba, amman tana tsoron ranan da abba xaisan tana mgn da deen harma tana shiga gidan su, alhanin ya gargadeta daga makaranta ko gidan dada be amince taje ba"
Hawaye taji yana zubo mata hakika batason bacin ran abbanta kuma tanason ta masa biyayya amman kuma tanajin deen ajikinta kuma tanaso kasancewa dashi akoda yaushe, har tanaji inama su zauna gida daya taita kallon shi harta gaji"
Murmushi tayi lokaci da ta tuna yadda deen yayi data gaya mishi an begeta, tabas da zatabawa deeni dama da yayi banna komai girman mutum dan ya duramai zagi bawani abu bane, ji inda ya takarkare agabana yana cewa zaici uwar yaya, wata kila ya manta cewa uwarmu daya"
Wata zuciyar ce tace ke ba mantawa yayi ba yana sane ko kin manta yadda yayiwa dada?
Kwashewa tayi da dariya har tana rike ciki kai gsky dada matsuraciya ce, dagajin zance sara ta ware kafa amman da anyi mgn tace kafanta na ciwo*
Dariya take sosai har da hawaye, da karfi taji anturo kofar, mama ce kallo tabi ma'u dashi sannan tace toh wai kodai mahaukacin kare ya cijeki ne?, mutum shi kadai yaita dariya adaki"
Gintse dariyarta tayi sannan tace mama dada fah na tuna"
Dada ? Ke banason shashanci kinji ko, kiyi hankali da kanki ba kowa bane keson dariya dallah ni tashi ki kaiwa su yayki abinci'
Hade rai tayii sannnan tace mama ni gaskiya nagaji da ganin su agidan nan waishi yaya meyasa baazai kaishi gidan shiba??
Ke tashi kiji bansoo. Surutun banza
Mikewa tayi ta fara tafiya tana. tana mgn ahankali"
Binta da kallo. Mma
Sannan tace me kike cewa?
A,a mama daman cewa nayi kodai Anty fa'iza tayi yaji ne?
Cikin takaici mama tace bani da lbr amman idan kije kina iya tambayo shi"
Bata sake cewa komai ba ta juya ta fita dan tasan mama gatse ta mata"
Kwance ta same su afalon abba sunyi wani shabe shabe dasu, duk su biyun jikin su babu babu riga dan haka batace zata tsawaita kallon su ba"
Jarida ce ahannun Jamal kaman yadda ya saba yayin da usman ke rike da waya yana dannawa"
Ajiye abincin tayi ta juya zata tafi taji waya na kara
Harta kai bakin kofa taji Jamal yace Haba Momy kiyi hakuri wlh wani abu ne ya tsaidani, amman gobe da wuri zan taho"
Yadda Jamal ya kashe murya yana shagwaba abun yayi matukar bata mamaki dan haka taja ta tsaya tana jiran taji me zai sake cewa"
Muryan yaya usman taji yace ke me kike jira"
Azubure ta fice adakin"
Koda ta koma daki addu,a taitayi Allah yasa momyn shi ta matsamai ya tafi gobe, dan wannan bakon gundura ne"
Washegari da safe bayan tayi shirin makaranta ta fito ta samu mama sai hada wasu kaya take"
Cike da zumudi tace mama wannan kayan fa?
Idon mama akan kayan tace wlh Jamal ne be tashi gayamin zaitafi gida ba saiyau da safen nan, shine zan bashi turaren nan ko kyauta yayi dashi"
Kasa boye murnanta tayi tace ai gara ya tafi"
Mama batace mata kala ba harta fice"
Cikin farin ciki ta nufi mkrnt tanaji azuciyarta daga yau zaman kunci ya yaye"
Tana daf da isa kofar gidan su deeni ta hango karnuka guda 3 sai shawagi suke"
Ja tayi ta tsaya tare da dafa kirji, ido ta sake zuba musu manya2 karnuka ne amman duna duk ya fisu girma"
Ahankali ta fara takawa ta koma lungun da kawarta zainab take bi dan bakaramin tsoron duna take ba"
***
Shiko Jamal karfe 10:45 ya mike yacewa usman bari naje wani guri na dawo"
Cikin mamaki usman yace kadai CE natashi muje"
A'a bana bukatan rakiyan kowa, ni daya zani"
Mamaki ne yasake kama usman dan tunda yazo garin nan kusan satin shi 2 be taba cewa zai fita shi kadai ba sai yau"
Murmushi Usman yayi sannan yace toh adawo lfy Allah ya tsare, key din motar sa ya mika masa amman sai yaki karba yace da kafa zashi"
Makarantar su ma'u ya nufa yana tafe yana shirya muguntan dazai mata indai ya sameta da laifi"
Koda ya hango karnnuka na shawagi be kawo komai azuciyan shi ba, dan ya saba ganin karnuka iri2, dan haka kanshi tsaye yake tafeya tare da neman inda zai labe yaga wucewan ma'u idan ma wani abu take shiryawa yau zai gani"
Shiko deeni yana zaune kan dakalin da ya saba zama ya rufe ido tare da dage hanci sama"
Kan Jamal tsaye ya nufi bita tsakiyan karnukan yana daf da shiga cikin su yaga sun haukace kaman suna fada da junan su, duk idan yaso be ya wuce nan suke dawowa suna kawai junan su rikici"
Jamal be tsorata ba acikin zuciyan shi yace wadan nan wasu irin yan iskan karnuka ne"
Daure fuka yayi sosai yayi kansu gadan kadan tare da niyan idan suka kawo mai wargi zai kai masu duka"
Wata muyar yaji daga gefen tana cewa dan durin uwar mutun ya tabamin kayana yagani"
Juyawa yayi ya kalli gurin da yaji mgn mutun ne zaune kato meji da karfe Kuma daganin shi bayaji dan almun rashin ji sun bayana agareshi haka ne ya nunawa jamal shine mamallakin karnukan amman saidai kaman bashi ne yayi mgnr ba dan idon shi rufe yake"
Karnukan ya kara kallo har yanzun sunan a inda suke dan haka ya daga murya yace "
Ai sai kazo ka tattara kayan naka dan inason zan wuce"
Baki deeni yasake dagewa sama yafara fito" dan haka Jamal yasa kafar yayi ball da daya daga cikin karnukan"
Akuje duna ya taso ya yi kan jamal yana kaimai cizo tare da yakushi, saidai baya kawaiwa jikin Jamal din domin fada da kare ba sabon abo bene awajen shi, da duna ya kawo mai cizo yake kaimai duka"
Ana haka aka tashi yan mkrnt, suna ganin abinda ke faruwa suka watse wasun su sunbi lugu wasuko makarantar suka koma, mau ko wani logu ta rabe tana lekowa tana komawa acikin zuciyanta tace kai Jamal akwai maye"
Jikinta ne yayi sanyi lokacin da ta hango yadda jamal ke kaiwa duna duka, ga deen zaune ya rufe ido kaman me bacci hawaye taji yana zubu mata shikenan Jamal zai gama da duna ya dawo kan deeni tunda ciwon baccin shi ya motsa, jitayi kaman ta tashe shi dan tasan babu yadda za'ai idon shi 2 ya bari ana jamgar masa duna"
Kuka take sosai hawaye shabe2 zuwa yanzun ta fara tausayawa duna itace tajamai gashi Jamal zai kashe abanza"
Wani irin kuka duna ya fara almar yana shan wahala, yana fara kukan taji deeni yayi wani irin fito me kama da mgn, nan danan duna ya haukaci tare da wani irin haushi me firgitarwa yayi kan jamal akan damtsen shi ya kafa bakin shi saiga jini yana zuba"
Hannu Jamal yasa ya danne gurin hakan yaba duna daman cigaba da cizon Jamal akafan shi dole tasa Jamal ya sake uhun da be shirya ba, tare da kokarin guduwa"
Daidai lokacin ummi ta dawo daga cefane afirgece ta saki kanyan miyan sannan tayi kan duna tana kai! Kai!! Ja baya duna yayi amman har yanzun yana gurnani tare da kunbura wuya"
Ma,u ko banda dariya babu abinda take saidai taso ace duna yabi Jamal aguje"
Tana cikin wannan tunanin taji duna ya sakeyin fito aguje taga duna ya wuce sauran karnukan nabin shi abaya "
Sai alokacin mutanan unguwan suka fara fitowa, deen ko mikewa yayi ya shige gida"
Allah wadai mutane suketayi da halin deeni yayin da wasu daga ciki suka rufan ma ummi da hayaniya cewa tajawa danta kunne"
Wasu dadtawa ne su 2 suka saka Jamal amota suka nufi asibiti dashi"
Cikin gida ummi ta nufa tana share hawaye, hakika babu dade ace danka bayaji tabbas ta sani duk unguwannan babu me irin dabi,un deeni kuma tasani kuskure ne da tayishi tun abaya ta manta cewa ice tun
yana danye ake tankwara shi, afili tace babu komai zanci gaba da addu'a Allah ya shirya min shi"
Koda tashiga gida batawa deen mgn ba wuceshi tayi tana cigaba da share hawaye"
Kallonta kawai yayi ya kyauda ido, daidai lokacin Asmau ta shigo fuskanta dauke da murmushi"
Shima murmushi yayi sannan yace zoki zauna"
Girgixa kai tayi tace sauri nake amman yaya akayi kasan Jamal?
Murmusawa yayi sannan yace ai jiya daku ka wuce na kare musu kallo na gane yayaki ne ta kama dake dana gani"
Shiru sukayi zuwa can tace yaya shamsundeen wai dan Allah meyasa kake bacci akofar gida?
Murmushi ya sakeyi sannan yace sabo da bana samon bacci da dadaddare"
Cikin mamaki tace toh meyake hanaka baccin?
Cikin sauri ya jawo hannunta ya hada da nashi sanan ya kafeta da ido yace tunanin Ki ke hanani sukuni harna kasa bacci
Tunani na kuma馃檮?, dama kaima kana tunani na?
Kema kina yin nawa ne?
Cikin sauri ta girgiza kai, tare da fadin a'a"
Karya kikeyi Asmau kinayi na tabbatar abinda nakeji kema kinaji"
Hannuta ta janye sannan tace zan tafi, kar aga na Dade"
Karajan hannuta yayi sannan yace toh wani tukuici zakibawa duna"
Shiru tayi zuwa can tace to ka fadamin abin da yake ci gobe na kawo masa"
A'a bayason abinci, goben idan kinzo zan nuna miki yadda zaki masa"
Aranan saida deeni ya rakota har kusa da gida, suna tafe suna hira , yau ma'u jitake kaman karsu rabo da deeni, koda suka rabo sai waiwayen shi take"
Shima kasa tafiya yayi yana jira wai sai ta shiga gida" darker suka hakura da kallon junan su"
Tana shiga gida tasamu mama hankalinta tashe ko tambayan ina ta tsaya batayi ba tace"
Asmau Jamal ne ya buguwa usman waya wai yayi hatsari tun dazun fah, gashi har yanzun basu dawo ba"
Cikinta cike da dariya tace hatsari kuma??
Kafin mama ta bude Baku suji tsayowan mota arude ummi tayi waje, yayin da asmau ta shige daki dan tasa bazata iya boye dariyarta ba"
*Mmn Yazeed*鈥�
[22:51, 12/19/2017] 鈥�+234 806 858 0203鈥�: 馃挆馃挐馃挐馃挆
鈥�*BUGUN ZUCIYA*鈥�
( 鈥婬eartbeat鈥�)
馃挀馃挐馃挆
馃挆
馃挀馃挐馃挆
鈥婤y鈥�
馃挆
鈥嬧€�*Fadeela Lamido*
*@AM拢拢NCI WRITER'S ASSOCIATION馃*
Dedication 馃憞馃徎
*Firdausi Sodangi*馃槝
2鈨�2鈨� to 2鈨�4鈨�
馃挐馃挆 Tana shiga daki ta fashe da dariya bakin window taje ta tsaya tana kallon yadda Usman ke kokari tallafu Jamal"
Gajeren wando ne kawai ajikin Sa, kafan shi duk 2 nade suke da bandeji haka damtsen hannun shi na dama"
Saida taga shigowan su sannan ta koma bakin gado ta zauna taci gaba da dariya tare da share hawayen mugunta"
Bayan usman ya kwantar da jamal akan gadon dake dakin dake kusa dana abba, gefe gadon ya koma ya zauna sannan yace manga yaya akayi ka tsaya kare yacije ka?
Ido ya runtse dan babu halin bude jarida"
Binshi da kallo usman yayi sannan yace ina mgn kayi shiru"
Cikin fada yace dallah Malam karka dame ni"
Shiru usman yayi yana tunani zuwa can yace to kodai Karen daya tsare asmau ne ranan ?
Bansani ba, nace maka kabar mgn sai wani nanatawa kake kare2 salon wani yazo yaji kuma"
Toh meye idan anji uban waye yace ka tsaya kare ya cijeka, wlh ka bani mamaki Dan Allah ji inda ya maka kaca2"
Kaga usman banaso ka rabu dani kawai"
Mikewa usman yayi ya fice dan abin takaici yake bashi"
Mama ko tayi tayi da asmau taje ta gaishe da Jamal taki zuwa, tanajin yadda mama ta takarkare tana gayawa Abba wai yau Jamal ya auna arziki"
Dariya ce ta kwace mata taita tuntsurawa dan haka daga mama har Abba suka juyo suna kallon ta"
Cikin fada Abba yace wanne irin iskanci ne wannan?
Nan dan ta daure fuska tare da sukuyar da kanta kasa"
Abba ne yaci kaba da cewa kina hauka ne, yaya ana mgn Mutun yayi hatsari Ki kama dariya"
Mamace tace ai yanzun dabi'a data fara kenan ita kadai ma saikaga tana dariya, narasa gane kanta, Jamal ko Daman ta tsane shi wlh ina kula da ita tunda nace mata yayi hatsari annashuwa ta cika fuskanta"
Fada yaita mata tun yanayi cikin fada har ya dawo nasiha akarshe ya kara da lallashi"
Kwana 2 jamal ya fara samun sauki, dan haka yau Usman gida yake shirin tafiya dan matar sa ta dawa ta dawo tun ranan da abin ya faru"
Jamal na zaune akan kujera yayin da usman ke zaune agefen shi"
Usman ne ya kalli damtsen hannun jamal yace kai amman gsky karan nan ya iya tsiya toh wai ta bayanka ya biyo ?
Kwashe duk yadda akayi yayi ya gayawa usman sanna ya kara da cewa kasan Allah saina naga uban da ya tsayawa mishi"
Usman ne yace kana nufin karan yafi irin karnukan mu horo"
Guntun tsaki Jamal yaja sannan yace wannan fa umarni ake bashi kuma ni tunda nake bantaba ganin kare me zafi kalan shi ba, amman na dakeshi sosai na tabbatar inda nai jiya shima saiyayi jiya dan dukan dana mushi banzaci zai iya tashi ba bare har yamin wani abu, kuma ni fa bawai nabar mgn bane"
Aidama ko kanarta ni bazan bari ba abinda yasa ban daga mgn ba sabo da naga baka son asani"
Eh banaso"
Towai saboda me?
Haba usman ina Sonja aga kare yamin haka?
To ai tsautsayi ne ko?
Shiru yayi zuwa can yace nifa sabo da wannan yariyan ne banason asani, kartazo ta raina muta ne
Kallon shi usman yayi sannan yace au wai Asma'u?
Ita, kasan yariyar ba kunya kareta ba kuma akwai wani abu da nake nazari idan na tabbatar zan gaya maka"
***
Washegari ta kama alhamis dan haka yau babu makaranta ma'u na daki tana ninke kaya taji kiran mama"
Bayan taje mama fada taita mata akan kin zowa gaida Jamal datayi, haba asma'u wanne irin zuciya gareki ace mutun agidan ku yayi hadari Ki kasa zuwa ki gaida shi, haba asma'u ke bakiji dadi bama daya nuna yadamu da lamarin ki ?
Nan danan ta fara matso hawaye tare da fadin mama hakanan fah ya zanene saboda tsabar cin zalli wlh na tsane shi kuma idan Allah ya yarda bazai gama da duniya lfy ba"
Ah, ah ah babban mgn Asma'u kanki daya kuwa? Toh idan kece uwarshi saiki hanashi gamawa da duniyan lfy"
Wucewa mama tayi ta barta aguri, zama tayi taita kuka domin ita harga Allah bata kyaunar ganin Jamal, bata tabajin ta tsani wani ba kaman yadda ta tsaneshi"
Har yamma mama bata sake mata mgn ba koma ta mata bata amsawa
Ganin haka Yasa ta mike ta nufi dakin da Jamal yake tayi sallama"
Daker ya amsa bayan ta shiga ta dan rage tsayonta sannan tace sannu ya jiki?
Banza yayi da ita harta gaji da durkuson ta fara kokarin mikewa"
Haka ake gaisuwa sannan saiyau kikasan bani da lfy ?
Shiru tayi tare da turo baki"
Shiru shiru zuwa can ta waiga daga yana bacci , zabura tayi ta mike harta taba kofa yasake cewa idan kika fita ranki zai baci tambaya nayi kuma inason kibani amsa"
Shiru tayi taki mgn shikuma ya dage dole tayi mgn, ahaka Usman ya shigo ya same su"
Murmushi usman yayi sannan yace kona koma ne?
Hararan shi yayi sannan yace shigo mana"
Bayan usman ya zauna Jamal ya kalleshi yace wai yariyar nan ajinta nawa?
Usman ne ya waigo yace ke ajikin Ki nawa ?
5 tafada batare da ta kallesu ba
sauraki shekara daya kenan?
Eh ta fada tana share guntun hawaye"
Ganin inda take nuna alaman gajiya Yasa Jamal yace tashi ki tafi , wawiya dake kawai"
Tana fita Jamal yabi bayanta da kallo sannan ya juya yacewa usman usman wannan yariyar yaushe zaku mata Aure?
Shiru usman yayi yana nazari, zuwa can ya hada fuska sannna yace"
Munyi mgn da Abba kwanaki yace data yi sauka zaiyi mata Aure, kaga kenan bazai wuce nan da shekara 1 ba"
Kuna nufin bazata karasa karutunta na ban garen boko ba?
Eh gsky kozata karasa sai adakin mijinta, saboda wannan dalili dana gaya maka"
Shiru Jamal yayi zuwa can yace amman da kun bari ta karasa saboda yanzun zamani ya canza kuma bakowanne namiji bane zai yadda matarshi ta tafi makaranta, kaga kamarni bani da ra'ayin mace tana gida na kuma tanazuwa makaranta, saboda na sani inada kishi sosai"
Girgiza kai usman yayi sannan yace ina aiko ni bana goyon bayan Asma'u taje Jami'a idan mijin da zata aure be amince ba shikenan wadda ta samu Allah ya amfana"
Shiru Jamal yayi tare da rufe ido, ganin haka usman ma ya kwanta agefe, sun kwashe kusan minti 30 ahaka, Jamal ne ya kira usman batare da ya bude ido ba"
Waigawa usman yayi yayi ya kalleshi sannan yace yaya akayi ?
Daman tambayan ka zanyi kun mata miji ne?
Wani haushi ne ya kama usman nandanan ya hade rai sannan yace Eh ammata wani abu ne"
A'a tambaya ce kawai, jamal ya fada yana kokarin tashi, akwatin shi ya dauko ya fara hada kayan shi yana zuba kayan yana fadin gida zani gobe"
Gobe kabari mana sai ka kara warwarewa"
A'a ni gida zani mezan zauna nayi?
Dacan me kakeyi?
Cikin fada yace dalla gafara Malam karka dameni, ubana ne kai daxaka tareni da tambayoyi?
Mamaki ne ya kama usman, cikin shi cike da dariya yace Allah ya baka hakuri"
Jamal bece komai ba yaci gaba da hada kayan shi"
****
Washegari Jamal yayiwa su mama sallama, Abba yaso ya kara kwana biyu amman Jamal ya dage"
Tare da usman suka fito har sun shiga mota usman na kokarin tayarwa Jamal yace usman dan Tsaya...
Tsayawa usman yayi yana kallon jamal"
Basarwa Jamal din yayi sannan yace ko kuma muje kawai"
Usman bece komai ba ya tada motar har ya fara tafiya Jamal ya ja tsaki sannan yace wai *Husna* batanan ne ?
Sarai Usman ya gane wayake nufi amman saiyace wacece *Husna* kuma?
Cikin dakewa yace *Asma'u* nake nufi"
OK kasan dayake babu me kiranta da *Husna* sainaji abin yamin banbarakwai yana mgnr ne yana kara waya akunne, zuwa can yace mama dan Allah turo mana *Asma'u*"
Usman na sauke waya ya juya ya kalli jamal, sai wani daurewa yake yana wani basarwa, dariya ce taso kama usman Amman saiya cije yace ga *Husnar* nan zuwa"
OK Toh daman inaso ne nadan ja kunnen ta"
Daidai lokacin Asmau ta fito dan haka usman ya bude motar yana kokarin fita yace eh gsky haka yana dakyau"
Heart Beat
*Mmn Yazeed*鈥�
[22:51, 12/19/2017] 鈥�+234 806 858 0203鈥�: 馃挆馃挐馃挐馃挆
鈥�*BUGUN ZUCIYA*鈥�
( 鈥婬eartbeat鈥�)
馃挀馃挐馃挆
馃挆
馃挀馃挐馃挆
鈥婤y鈥�
馃挆
鈥嬧€�*Fadeela Lamido*
*@AM拢拢NCI WRITER'S ASSOCIATION馃*
2鈨�5鈨� to 2鈨�7鈨�
馃挒馃挐 Gefe ya koma ya zauna, yana mamakin halin jamal
Itako Asamau fuskan nan murtuk ta tsaya agefen da jamal ke ciki sannan ta turo baki tace gani "
Daure fuska yayi murtuk kaman be taba dariya ba sannan yace ni sa'an wasanki ne zaki tsaya daga nesa kina cemin wani gaki ?
Bata rai tayi kamar zatai kuka sanna ta matsa kusa da widow motar tana cigaba da turo baki"
Fuskar shi adaurai yace nayi ciwo harman warke bakizo kika duba ni ba, yanzun gashi zan tafi bakizo muyi sallama ba ko?
Rasa inda mgnr shi ta nufa tayi dan haka tamai shiru tana wasa da hannunta"
Ajikinta taji kallonta yake cikin sauri ta dago ta kalle shi"
Sauri yayi ya dauke idon shi sannan yace *Husna* bazaki min mgn ba ?
Batace kala ba , ganin lokaci na tafiya Yasa Jamal yace shikenan nizan tafi gida ki kula da kanki, kuma ki rage son wasa, kinji ko?
Kai kawai ta daga mai"
Hannu yasa aljihun gaban rikar shi ya Ciro kudi ya kirga 20k ya mika mata"
Hannu buyu tasa ta karba dan ta kosa tabar wajen, juyawa tayi da nufin tafiya taji yace *Husna* nacewa Momy na kina gaisheta ?
Kaita sake dagawa sannan ta juya da sauri dan ta kosa ta daina jin muryan shi"
Usman na Ganin wucewan asmau yatashi ya koma, aguje ya tashi motar yabar gidan"
Asmau ko tana shiga gida ta mikawa mama kudin tace gashi nan yace nakawo miki"
Tunkafin ta rufe baki mama tace karya kikeyi aini yabani nawa".
Mama to nima na baki, ni banason komai nashi wlh yadda na tsaneshi haka na tsani duk wani abu daya shafe shi"
Kai asmau nikam al'amarin ki yana bani tsoro, kin fiye naci da mitan tsiya, dan Allah kiyi hakuri kibar mgn yanzun dauki kudinki ki wuce ina ce dazun kikace nabaki 3k ?
Em mama kibani amman ni wlh bazan bazanyi amfani da kudin shi ba"
Mikewa mama tayi tare da fadin Allah ya shirye ki"
***
Tunda Jamal ya tafi ma'u ta saki jikinta kulum da wuri take zuwa mkrnt , sai ta fara biyawa gidan su deeni sannan ta wuce makaranta"
Kuma da antashi break take kumawa sai kuma taji anbuga kararrawa sannan ta koma mkrnt"
Shakuwa sosai sukayi da deeni, baya zuwa ko ina sai ya jira anta she su akamakarata, zuwa wannan lokacin kawayen ta rahama da zainab sun fahimci halin da suke ciki tsakaninta da deeni, dan haka dukkan su tsoron mu'ammala suke da ita, duk da cewa basu taba taranta akan mgnr ba amman sun san soyayya suke yi"
Ahaka har suka kwashe tsoyon wata 8 zuwa wannan lokacin ma'u ta fahimci son deeni,
Take Dan haka shima deeni soyayyan asma'u yakeji sosai azuciyar shi, saidai babu fargaban komai azuciyan shi dan gani yake ko za azubar da jini saiya Aure asmau"
Itako asmau anata bangaren tana fargaban kaimai deeni a matsayin mijin da zata aure domin tasan mawuyacin Abu ne Abba ya yadda da zabin ta, dan haka ta fara shiga damuwa"
**
Abba ne zaune cikin mota akan hanyar su ta zuwa gidan dada"
Kallon asma' u yayi sosai yace mamana wai meke damunki kwana 2 ?
Karya ta shirya ahankali tace babu komai abba kawai karatu nake dan munkusa fara jarabawa ga kuma saukan mu na tahowa"
Har cikin zuciyan shi yaji dadi, fuskan shi dauke da murmushi yace"
Allah ya taimaka mamana, saura wata 2 ko?
Eh abba"
Murmushi yayi sannan yace kinga dakin gama sai Aure ko ??
Zuciyarta taji ta bugu cikin sanyin jiki tace um um Abba ba yanzun ba"
Kul mamana kar muyi haka dake, isha Allahu bazaki kara wata uku agida ba, Aure zakiyi mamana, meye amfanin zaman"
Nan danan idonta ya ciko da ruwa bawai auren bane bataso deeni ne bata shirya kaishi gida ba"
Baitai aune ba taji hawaye na zubu mata, hannu tasa ta sharewa Abba ne ya juyo ya kalleta sannan yace"
Mamana kina kuka ne ?
Shiru tayi tare da daura hannuwanta dukka biyu afuskanta"
Kallonta abba ya sake yi sannan yace Asmau Ki kwantar da hankalin ki, karkiga wai dan har yanzun baki kawo kowa amatsayi wadda zaki aura ba, zaisa namiki auren dole, bani da niyar na aurar dake ga wadda bakiso, dan haka Ki kwantar da hankalin ki kinji ko?
Sosai taji dadin mgnr Abba acikin zuciyarta tace haka na nufin duk wanda nake so Abba zai amince dashi, yanzun idan nakai mai deeni zai barni na Aure shi?
Dahaka suka isa gidan dada, harta sauka ta shiga ciki Abba sai kallonta yake yana murmushi tare da godewa Allah da bashi yariya kimtsatsiya"
***
Jikinta babu kwari ta shiga gidan dada, idonta har sun fara tasawa almar tayi koka"
Atsakar gida ta samu dada tana shara kai tsaye ta wuce daki"
Bayanta dada tabi da kallo daidai lokaci da Abba ya shigo dada take fadin ita kuma wannan meya same ta"?
Abba ne yace rabu da ita dada shirman miyace"
Tabarma ya nufa ya zauna sannan suka shiga gaisawa da Dada, sun dan taba hira har ya bada lbrn yadda sukayi da Asmau "
Cikin dariya ta mike tace inazuwa barin ganta"
Kan gado ta sameta ta kwanta ta kifa ciki' ahankali dada ta Saka hannunta ta dagota sannan tace ke kanki daya kuwa ?
Shiru tayi dan haka dada tace" to shike nan tashi Ki gayamin meye matsalan ?
Tashi tayi da sauri ta zauna sannan tace dada idan na gaya miki zaki tai make ni?
Me zai hana takwara?
Dada ?, idan na fada miki bazaki fadawa Abba ba?
Nan danan jikin dada ya haurawa ba komai ta tuna ba , sai Firdausi mgn da ma' u tayi yasa ta fara tunani ko itama ta kwaso abin mgn ne, dan haka batasan lokacin da tace babu meji takwara ina jinki"
Hawaye ne ya zubo mata tasa hannu ta share sannan tace"
Dada dan Allah ko abinda zan fada be miki ba, ki tai make ni kirufa min asiri"
Naji naji Asma'u menene kike ta maimaita zance daya"
Dada nifa deeni nake so"
Tsaki dada taja sannan tace to dan wanan kiketa kunbiya2, wanene deeni?
Dada baki ganeshi ba ? Shamsu fah na kayin makarantar m...
Zaro ido dada ta yi tare da dafa kirji arikece tace kar dai kice min wannan tambadaden yaron?
Cikin sauri Asma'u ta diro ta Saka hannuta duk biyun ta rufe bakin dada"
Dada ko banda rawa babu abinda jikinta keyi salati take kokarin yi amman saboda rawan jiki fadi take"
Kalu lahaula innalillahi La,ila ha'illahu......
Asmau kara rudewa tayi ta manta tsoron dada shiya harta fada mata"
Tsugunawa tayi ta rike hannu dada tace dada dan Allah kiyi shiru haka ya isa"
Ina rawa kawai jikin dada yake gaf2 idonta na kifkifyawa"
Cikin matsan cin kuka tace dada yau dan nagaya miki damuwata shine kika rikece, dada idan ban gaya miki ba wa zan gayawa, kefa kika ce duk abinda ya dame ni na fada miki"
Arikece Dada ta bige hannun asma'u tare da fadi ke dallah can rabo dani neman tsari nake"
Toh dada ai ba daidai kikeyi ba kibari karkizo kiyi sabo"
Kallonta dada tayi sannan ta saki salatin ta fara fadin"
Summassabila yassara....
Kara danne bakin dada asmau tayi cikin rude tace dada dan Allah kiyi hakuri kar Abba yaji"
Ina dada bata san tanayi ba cigaba tayi da addu,ai ta batare da tasan metake fada ba"
Itama asmau rudewa tayi tare da kirgixa dada daker ta samu dada ta dawo cikin hayyacin ta"
Kallo dada ta bita dashi tana share zufa zuwa can dada ta dage ta kwasa mata mari"
Hannu tasa ta dafe gurin tare da runtse ido"
Mikewa dada tayi sannan tace duk yadda akayi kinada wani ciwo acikin kanki, idan ma mafarki kike to maza ki farka, dan bazai taba tabbata ba"
Cikin kuka asma'u takalli kofa sannan tace dada to kiyi shiru kar abbba yaji"
Dallah can rufemin baki fitsarariya tir da halin ki, waye zaiso ya hada zuriya da irin jaraba inbada ke shasha"
Ta inda dada take shiga batanan take fita ba, ma'u ko kuka take yi, tare da data sanin fadinwa dada"
Dada ko rufe ido tayi taita masifa daga karshe ta kara fasa kuka"
Saida sukayi me isan su sannan dada tace Asma,u kiyiwa girman Allah ki fita harkan Yaron nan, ni daman tunda na ganku tare kwanaki hankali na be kwanta ba, na firgita da ganin ku tare, wlh takwara ina gargadin ki karki yadda abbanki yaji wannan mgnr, kisan ba lafiyayye bane tun tuni akace zuciyar shi tana daf da bugawa"
Kudundune kai asma,u tayi tana kuka ciki2, zuwa can ta dago kai tace shikenan dada naji nahakura, idan Allah yaso zan cireshi azuciyata, sannan dada dan Allah karki gayawa kowa"
Cikin fada dada tace bazanyi shiruba asmau , idan nayi shiru na zuba ido wani abu kuma ya faru fah"
Dada babu abinda zai faru namiki alkawari dada daga yau bazan sake kulashi ba"
Yadda asmau ta marairaice ne tabawa dada tausayi, dan haka ta shiga mata nasiha"
Da gsk jikin ma'u yayi sanyi dada ta kula da haka, dan haka bayan ta gama ita da kanta ta daga ma'u sannan ta share mata hawaye tace muje kar abban Ki ya gaji da jira"
Tsaye suka samu Abba ganin fitowan su yasa shi fadin da zanje na dawo ne"
A'a karka batta tasata agaba ku tafi gida"
Sallama yayi ya fice ma'u nabin shi abaya"
Har suka isa gida tana share hawaye abba na kula da ita amman yayi kaman be ganta ba, a tunanin shi mgnr auren da yayi mata ne"
Ranan ma'u bata runtsaba tunani yadda zatayi ta rabo da deeni take, amman duk inda ta juya saitaga bazata iya rabuwa dashi ba"
Washegari ma babu mkrnt wuni tayi da tunanin deeni acikin zuciyan ta ta yanke shawaran gayawa deeni ya nemo masu mafita"
Washegari ta kama asabar dan haka karfe 7:30 tayi sallama ta wuce mkrnt"
Tundaga nesa take kallon gurin zaman deeni abin mamaki yau babushi aguri, mamaki abin ya bata dan kullum gurin take samun shi"
Koda takai kofar gidan gurin ta tsaya ta kallah sosai sannan ta shiga cikin gidan"
Ummi ta gani zaune ita da wata mata sai kuka take matan na lallashin ta"
Arude tace ummi lafiya ?
Ummi tana kuka tace Asma'u ankama auta, suntafi dashi"
Ankama deeni ? Ummi waye ya kamashi? kuma me yayi?
Share hawaye ummi tayi sannan tace"
Asma,u bansan me yayi musu ba, muna cikin bacci mukaji sojoji cike da gida, kafin infito ma sunsa deeni amota, wasun su suna kaimai duka"
Tsugunawa ma'u tayi ta fara kuka saida tayi me isarta sannan tace ummi babu wadda yabi bayan su?
Sojuji ne fa asmau, kisan ba hankali suka cika ba kuma da alama badaga nan garin suke ba"
Zama tayi dirshen taita kuka ranan bata iya zuwa makaranta ba, tana ganin lokacin tashi yayi ta wuce gida tana tafe tana kuka,
Akofar gida sukaci karo da abba kallonta yayi yaga idonta jawur yace lfy?
Abba cikina ne yake min ciwo"
Cikin tausayawa Abba yace toh sannu maza ki shiga gida"
Kaitsaye dakin mama ta shiga domin yau ta rasa inda zata tsoma ranta jikin mama ta fada sannan ta saki kuka meban tausayi"
Jikin mama sanyi yayi dan bata taba ganin ma'u nayin irin wannan kukan ba, cike da damuwa tace asmau daina kuka ki gayamin me yayi zafi ?
Cikin muryan kukan tace mama bani da lfy"
Jawota mama tayi ta rungume dan yanayinta ya fara bawa mama tsoro, tana kwance ajikin ta tace menene yake miki ciwo?
Bansani ba mama, wlh bansan abinda ke min ciwo ba"
Shiru mama tayi tana kallon ma'u zuwa can tace"
Asma'u idan akwai abinda ke damun ki kifada karkice zaki boye mana damuwar ki"
Shiru tayi bata sake cewa komai ba tai kwance jikin mama jefi2 kana jin ajiyan zuciyarta"
Ganin ta samu natsuwa yasa mama ta kalleta sannan ta jawo Wata leda akusa da ita ta daura mata ajiki"
Duk da tana cikin damuwa da zumudin ta ta fara bude ledan, da kwalin waya ta faracin karo, jikinta babu kwari ta bude kwalin sannan ta ciro wayar, waya ce lafiyayya dadi taji sosai ajiye wayan tayi ta kara leka ledan takalma ne kafa 3 masu kyan gaske tare da turare masu tsada"
Kallon mama tayi tace mama wannan kayan fah ?
Naki ne yayanki ne ya kawo miki, yace agaidaki sauri yake aiki ne yakawoshi
Yayana ? Mama wanene yaya na?
鈥�
💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
Na sadaukar da wannan shafin ga masoya *BUGUN ZUCIYA* aduk inda suke 👌🏻💝😘
2⃣8⃣ to 3⃣0⃣
🏀 Yayan ki *Jamal*
Mikewa ma'u tayi da sauri sannan tayi jifa da ledan " bantawa tayi tacire wayar acikin kwali dan haka ta dauki kwalin ta buga da kasa" sai lokacin ta kula dan haka ta dauki wayar ta makawa bango"
Ji kake tassss"
Da gudu ta fita ta nufi dakinta ta fada gado tare da saka sabon kuka"
Wato Jamal ne yaje har gida ya kama deeni ? Ko tantama batayi Jamal ne wani sabon tsanan shi taji axuciyarta ji take kamar ta kashe shi"
Tashi tayi ta zauna yanzun meye abinyi ?
Yaya zanyi inkubutar da deeni daga hannun Jamal
Mama ko mamakin hali irin na ma'u tayi sannan ta juya ta kalli bannan da tayi ta girgiza kai, cike da takaici ta fita adakin"
Da misalin karfe biyu da rabi ma'u ta fito cikin shirin tafiya mkrnt yamma, kallonta mama tayi taga idonta duk sun kumbura cikin idonta jawur sun kankance, da alamar ma ko cire kayan makaratar batayi ba tunsafe, dauke idol tayi akanta domin al'amarinta ya fara bawa mama haushi"
Saida ta turu baki tace natafi"
Ko kallonta mama batayi ba tace adawo lfy"
Kaitsaye gidan su deeni ta shiga, ummi nazaune ta tasa abinci agaba ta kasa ci"
Gabata ma'u ta zauna ta bude sabon kuka, hankalin ummi kara tashi yayi, rufe abincin tayi sannan tace ki daina kuka Asma'u bakiga inda fuskan ki ta kunbure ba, mutaru miyi hakuri inada tabbacin auta na zai dawo gida domin nasan shiba rago bane, wannan tashin hakalin da kika ganni ci narashin tabbacin inda yake ne da rashin sanin halin dayake ciki amman da yardan Allah auta zai dawo"
Dahaka ummi ta samu ta shawo kan ma'u, ta wuce makaranta"
Da daddare Asma'u na kwance afalo tana cigaba da tunanin deeni badan tana tunanin kar asirinta ya tonu ba data ansa no Jamal agun yaya usman ta bashi hakuri ya sakar mata deeni"
Tana cikin wannan tunanin taji sallaman yaya usman rufe ido tayi kaman me bacci, Allah2 take ya wuce amman saitaji ya zauna akujeran dake kallon nata"
Zuwacan mama ta fito tana fadin ka iso?
Eh naje gidan momy yanzun tacemin kina nema"
Zama tayi sannan tace eh Daman Asma'u ce gatanan narasa gane mata, kwashe duk yadda akayi tayi ta gaya masa"
Sannan ta nuna masa yadda tayiwa wayar da Jamal ya kawo mata"
Cike da baccin rai yace mama bawani abinda yake damunta banda iskanci da sangarta, bataga ba,a dukanta ba kuma ai ba wuce dukan tayi ba, dan ubanta Jamal din sa'anta ne
Usman na tsaka da fada Abba ya shigo, daga mama har usman sannu suke mai" amman abban yaki amsawa fadin yake ina Asma'u
Toh fah mama ta fada azuciyarta domin indai taji alhaji ya kira ma'u da sunan ta toh akwai mgn"
Itako ma,u tanaji Abba ya kira sunanta ta bude ido tare da sakkowa akan kujeran azuciyarta tace shikenan dada ta fadawa abba"
Kusa da ita abba ya zauna sannan ya rike hannunta guda daya"
Jikinta gaba daya rawa yakeyi"
Abba ko ido ya kureta dashi zuwa can yace, yau naje gidan malam idris na tuntubeshi game dake, ya nunamin komai lfy kuma kina karatu sosai yadda ya kamata, amman abinda ya bani mama cewa da yayi wai baki zuwa makaranta akan lokaci, bayan nikuma nasan kina fita gida da wuri"
Shiru Abba yayi yana jiran yaji me zata ce"
Jita shiru yasa yace badake nake mgn ba"
Kanta akasa tace Abba wlh ni babu inda nake zuwa"
Amman kinsan malam idris bazaimin karya ba ko?
Nasani abba, amman ni daga nafita wlh tallahi banazuwa ko ina sai makaranta, sai dai idan kafin naje lokaci yake kure ....
Cikin ido abba ya kalleta sannan yace bari rantsuwa, ai bacewa nayi ki rantse ba, bakomai daga yau drive zai dinga kaiki makaranta, idan lokacin tashi yayi zai dawa ya daukeki, haka yayi ko ?
Daga kai tayi badan ranta yaso ba"
Juyawa abba yayi ya kalli usman sannan yace kaikuma me kazoyi da daddaren nan ?
Cikin natsuwa ya fara fada mishi komai kamar yadda mama tafada mai, sannan ya kara da cewa abba ya kamata adauki mataki akanta be kamata azuba mata ido tanayin abinda taga dama ba"
Shiru falon yayi zuwa can abba ya nisa sannan yace...
Ke !! Asma'u wani abu na damun ki ne?
Cikin sauri ta girgiza kai tare da fadin a'a"
Akwai wani abunda kikeson ne ko kike son a saya miki ?
Nan ma a,a ta sake cewa"
Shiru abba yayi sannan yace....
Ninasan abinda ke damun ki, Aure ne baki so, kuma bazai yiyoba, tun ranan dana miki mgnr aure kika fara koke2 ita kuma dada ta biye miki har tana taya Ki, bazan kara kaiki gidan ba bare ki kara sata kuka"
Juyawa yayi ya kalli mama sannan yace wlh tun ranan danakaita gidan, dada na nan babu lfy, yanzun jiya nakaita asibiti sunce jininta ya fara hawa"
Juyawa yayi ya kara kallon asma,u sannan yace ki shirya gobe zakiyi bako, ni ba nufina namiki auren dule ba, a'a zaizo ne ya ganki, kema ki ganshi, idan kun daidaita shikenan, idan kuma baku daidaita ba zan sake turo wani, bana bukatar kice wai saikinsa halinshi, duk wandan
kikaga na turo miki na yadda da inganshi tare da mutuncin iyayen sa, dan haka kwana 2 kawai na baku, ganin inda tayi shiru yasa abba fadin kinajina ko ?
Kai kawai ta iya dagawa sannan tasa hannunta ta share hawaye"
Tattaunawa suka fara tsakanin mama da abba tare da yaya usman, haka ne yabata daman tashi tabar musu falon"
****
Washegari ma'u ta tashi da matsanan cin ciwon kai, saka makon rashin baccin da batasamu, taso taki zuwa mkrnt amman kuma tanason taga halin da ummi take ciki, dan haka ta mike tahau shiri"
Drive ne ya kaita har bakin mkrntr sannan ya juya, dan kaka bata samu daman zuwa gidan su deeni ba saida aka tashi break"
Xama sukayi jugum ita da ummi kamar masu zaman makoki"
Bayan antashi makaranta abba da kanshi yazo ya dauketa"
Koda ta shiga gida a kitchen ta samu mama tanata soye2 sai alokacin ta tona da bakon da abba yace zaizo"
Yatsuna baki tayi sannan ta juya ta shige daki, wanka tayi tai sallah sannan ta tsaya tai addu'a sosai Allah ya kubutar da deeni daga hannun Jamal"
Tana zaune kan sallayan mama tashigo tana fadin Asma'u maza ki fito bakonki ya iso"
Gabanta taji ya fadi, kanta ta daga ta kalli mama sannan tace...
Mama dan Allah kice bacci nake, nifa bansan mezance mai ba"
Shiru mamatayi zuwa can tace, kinga, Asma'u banason shirme maza ki fito ko na kira abbanki na gayamai"
Cikin sauri ta mike tana matso hawaye ta nufi hanyan kofa"
Ke !! Zonan mama ta fada tana kare mata kallo"
Bayan ta juyo tace nufinki ahaka zaki tafi fuska saikace tsowar me takaba"
Bakinta agaba tace to ai yanzun nan fah nayi wanka"
Mama batace komai ba ta juya ta fara ciro mata kaya, mika mata tayi ta Saka sannan ta zaunar da ita dakanta ta mata kwalliya bawata me hayaniya ba"
Madaidaicin gyale ta mika mata dasukai matukar dacewa da kayan datasa, kallo ta kare mata sannan tace toh maza ga kayan motsa baki can na hada ki dauka ki tafi dashi"
Jikinta babu kwari ta nufa kitchen tare da nazarin abinda zata ma bakon ta kuntuka mishi haushi"
Ahankali ta tura kofar falon abba tare da sallama cikin siririyar muryanta, cikin ido ta kalli bakon nata farine babu laifi yana da kyau daidai misali, saidai daganin shi yana da iyali, duk da cewa bawani babba bane amman daganin shi yana da iyali, sauke idonta tayi akanshi sannan ta karasa shiga falon tare da neman yadda zata mishi"
Kayan motsa bakin ta ajeye agefen shi sannan ta koma tsakiyan falon ta tsuna, cikin ladabi tace...
Inakwana daddy, ina gajiya, bata jira ya amsa ba taci gaba da cewa gashi kazo kuma abban bayanan ya tafi Office amman idan ya dawo zan fadamishi kazo"
Cikin mamaki yake kallonta aranshi yace lallai wannan yariya da hikima take, idan na fahimceta tana nufin namata tsufa, gyaran murya yayi sannan yayi murmushi yace, toh shikenan asma'u idan ya dawo din ki gaya mishi, amman wa zaki ce masa?
Rasa abun cewa tayi zuwa can tace zance masa bayan fitanshi wani yazo neman shi"
Murmushi ya sake zaiso kasancewa da wannan yariyar, kallonta yayi ya girgiza kai sannan yace kinada abin dariya, ni sunana Jafar inada mata 1 da yara na guda 2 nine bakon da mahaifi ki ya sanar dake zuwan Sa, duk da nasan kinsan koni waye"
Ko kallon gafen shi batayi ba acikin zuciyarta tace wato abba neman kai yake dani, ya rasa wadda zai turomin sai me mata, dumi taji akumatun ta tana shafowa taji hawaye"
Duk abin da take bakonta na kallonta dan haka ya mike yace nizan tafi sai ince ki gaida mutanen gida"
Bata ce komai ba yasa hannu ya ciro kudi aljihu ya aje agefen kujera yayi waje dan yaga bata da niyar kula shi"
Itama ficewa tayi batare da ta dau kudin da ya ajiye mata ba, bare kayan motsa bakin datakai mai"
Afalo ta wuce mama ta shige dakinta, zama tayi tare da addu'a Allah yasa abban ya janye wannan kudirin nashi"
Washegari da safe ta shirya tsaf domin zuwa mkrnt falon abba ta fara shiga, bayan ta gaisheshi ta mike zata wuce abba ya dakatar da ita"
Komawa tayi ta zau tare da sauke kanta akasa"
Kallonta abba yayi sosai sannan yace bakon ki yazo jiya ko?
Kanta akasa tace eh"
Shiru ne ya ziyarci falon zuwa can abba ya sake cewa...
To me kika ce ? Ya miki ?
Shiru tayi bata ce komai ba, zuwa can abba ya sake cewa....
Karmuyi haka dake mamana, banason na takuraki saboda kin min biyayya saboda haka nakeson na saka miki, wadda kike so shi zan baki bazan miki auren dole ba da iznin Allah, inason nasan meye azuciyar ki game da jafar ?
Motsa baki tai tayi daker ta iya bude baki tace Abba ni banason shi"
Saboda me ? abba ya tambaya
Abba tsoho ne fah kuma yana da mata"
Murmushi Abba yayi kadan sannan yace ashe jafar ya cinka daidai, toh bakomai amman nayi miki sha,wan shi, dan yaro ne me mutunci da sanin ya kamata, haka iyayen shi mutane ne masu karamci, kuma bawani babba bane mamana, ko zai girmin usman bazai wuce shekara daya ba, amman ba komai tunda kince haka, gabe wani zaizo ki ganshi, kinji ko?
Saida gabanta ya fadi wato abba bazai bar mgn haka ba, da wannan tunanin ta tafi mkrnt ko wa Abba zai sake turo mata oho?
***
Akofar gidan su deeni ta hango samari cike, da alama yaran duna ne kome suke agurin oho, acikin su caka kawai ta sheda yanata fada yana daga hannu saidai har motan su ta wuce bata tsinci abinda suke cewa ba"
Ko a aji batai karatun kirki ba Allah2 take atashi break taje taga me akeyi"
Kawayen ta kallonta kawai sukeyi, domin sun kula akwai abun da ke damunta"
Ana buga kararrawa ta fito ta nufi gidan su deeni saidai yazun babu kowa akofar gidan"
Cikin gidan ta nufa tana tura kofar sukayi ido 4 da deeni, zaune yake kan kujera ummi tsugune agefen shi tana tsuma tsunma aruwa zafi tana dannan me ajikin shi"
Hunnu tasa ta mumtsuke idonta sannan ta sake sauke shi akan deeni, aguje tayi kansu, jinta kawai tayi jikin deeni ya rungume ta yana sumbatan ta"
Cikin sauri ummi ta dauke bokitin ruwan zafinta ta basu guri, jefe2 tana satan kallon su"
Sun dan juma ahaka ahankali asma'u ta zame ta koma gefe sannan ta zubawa deeni ido"
Shedan bulala ne ajikin shi rudu2 wasu guraren hadda ciwo, hawaye taji ya cika mata ido, nan danan suka fara zubowa acikin kuka tace nina jawo maka nasan bakowa bane yayi maka haka sai Jamal dan Allah ka yafe min"
Hannuta ya jawo ya riketa dakyau sannan yace....
Shine Asma'u amman karki damu yanaso ne wai ya nunamin shi Soja ne amman ba jarumi ba, wanna abin daya aikata ya nunamin be kai ba"
Kara karkace baki yayi sama sannan yace.....
Ai nagaya masa dan *uwas* data haife shi, idan yana jin yakai shege, ya goyo *uwassa* abaya, ya fadi ina zamu hadu, daban daban zasu koma gida"
Heart beat
*Mmn Yazeed*
Yayan ki *Jamal*
Mikewa ma'u tayi da sauri sannan tayi jifa da ledan " bantawa tayi tacire wayar acikin kwali dan haka ta dauki kwalin ta buga da kasa" sai lokacin ta kula dan haka ta dauki wayar ta makawa bango"
Ji kake tassss"
Da gudu ta fita ta nufi dakinta ta fada gado tare da saka sabon kuka"
Wato Jamal ne yaje har gida ya kama deeni ? Ko tantama batayi Jamal ne wani sabon tsanan shi taji axuciyarta ji take kamar ta kashe shi"
Tashi tayi ta zauna yanzun meye abinyi ?
Yaya zanyi inkubutar da deeni daga hannun Jamal
Mama ko mamakin hali irin na ma'u tayi sannan ta juya ta kalli bannan da tayi ta girgiza kai, cike da takaici ta fita adakin"
Da misalin karfe biyu da rabi ma'u ta fito cikin shirin tafiya mkrnt yamma, kallonta mama tayi taga idonta duk sun kumbura cikin idonta jawur sun kankance, da alamar ma ko cire kayan makaratar batayi ba tunsafe, dauke idol tayi akanta domin al'amarinta ya fara bawa mama haushi"
Saida ta turu baki tace natafi"
Ko kallonta mama batayi ba tace adawo lfy"
Kaitsaye gidan su deeni ta shiga, ummi nazaune ta tasa abinci agaba ta kasa ci"
Gabata ma'u ta zauna ta bude sabon kuka, hankalin ummi kara tashi yayi, rufe abincin tayi sannan tace ki daina kuka Asma'u bakiga inda fuskan ki ta kunbure ba, mutaru miyi hakuri inada tabbacin auta na zai dawo gida domin nasan shiba rago bane, wannan tashin hakalin da kika ganni ci narashin tabbacin inda yake ne da rashin sanin halin dayake ciki amman da yardan Allah auta zai dawo"
Dahaka ummi ta samu ta shawo kan ma'u, ta wuce makaranta"
Da daddare Asma'u na kwance afalo tana cigaba da tunanin deeni badan tana tunanin kar asirinta ya tonu ba data ansa no Jamal agun yaya usman ta bashi hakuri ya sakar mata deeni"
Tana cikin wannan tunanin taji sallaman yaya usman rufe ido tayi kaman me bacci, Allah2 take ya wuce amman saitaji ya zauna akujeran dake kallon nata"
Zuwacan mama ta fito tana fadin ka iso?
Eh naje gidan momy yanzun tacemin kina nema"
Zama tayi sannan tace eh Daman Asma'u ce gatanan narasa gane mata, kwashe duk yadda akayi tayi ta gaya masa"
Sannan ta nuna masa yadda tayiwa wayar da Jamal ya kawo mata"
Cike da baccin rai yace mama bawani abinda yake damunta banda iskanci da sangarta, bataga ba,a dukanta ba kuma ai ba wuce dukan tayi ba, dan ubanta Jamal din sa'anta ne
Usman na tsaka da fada Abba ya shigo, daga mama har usman sannu suke mai" amman abban yaki amsawa fadin yake ina Asma'u
Toh fah mama ta fada azuciyarta domin indai taji alhaji ya kira ma'u da sunan ta toh akwai mgn"
Itako ma,u tanaji Abba ya kira sunanta ta bude ido tare da sakkowa akan kujeran azuciyarta tace shikenan dada ta fadawa abba"
Kusa da ita abba ya zauna sannan ya rike hannunta guda daya"
Jikinta gaba daya rawa yakeyi"
Abba ko ido ya kureta dashi zuwa can yace, yau naje gidan malam idris na tuntubeshi game dake, ya nunamin komai lfy kuma kina karatu sosai yadda ya kamata, amman abinda ya bani mama cewa da yayi wai baki zuwa makaranta akan lokaci, bayan nikuma nasan kina fita gida da wuri"
Shiru Abba yayi yana jiran yaji me zata ce"
Jita shiru yasa yace badake nake mgn ba"
Kanta akasa tace Abba wlh ni babu inda nake zuwa"
Amman kinsan malam idris bazaimin karya ba ko?
Nasani abba, amman ni daga nafita wlh tallahi banazuwa ko ina sai makaranta, sai dai idan kafin naje lokaci yake kure ....
Cikin ido abba ya kalleta sannan yace bari rantsuwa, ai bacewa nayi ki rantse ba, bakomai daga yau drive zai dinga kaiki makaranta, idan lokacin tashi yayi zai dawa ya daukeki, haka yayi ko ?
Daga kai tayi badan ranta yaso ba"
Juyawa abba yayi ya kalli usman sannan yace kaikuma me kazoyi da daddaren nan ?
Cikin natsuwa ya fara fada mishi komai kamar yadda mama tafada mai, sannan ya kara da cewa abba ya kamata adauki mataki akanta be kamata azuba mata ido tanayin abinda taga dama ba"
Shiru falon yayi zuwa can abba ya nisa sannan yace...
Ke !! Asma'u wani abu na damun ki ne?
Cikin sauri ta girgiza kai tare da fadin a'a"
Akwai wani abunda kikeson ne ko kike son a saya miki ?
Nan ma a,a ta sake cewa"
Shiru abba yayi sannan yace....
Ninasan abinda ke damun ki, Aure ne baki so, kuma bazai yiyoba, tun ranan dana miki mgnr aure kika fara koke2 ita kuma dada ta biye miki har tana taya Ki, bazan kara kaiki gidan ba bare ki kara sata kuka"
Juyawa yayi ya kalli mama sannan yace wlh tun ranan danakaita gidan, dada na nan babu lfy, yanzun jiya nakaita asibiti sunce jininta ya fara hawa"
Juyawa yayi ya kara kallon asma,u sannan yace ki shirya gobe zakiyi bako, ni ba nufina namiki auren dule ba, a'a zaizo ne ya ganki, kema ki ganshi, idan kun daidaita shikenan, idan kuma baku daidaita ba zan sake turo wani, bana bukatar kice wai saikinsa halinshi, duk wandan
kikaga na turo miki na yadda da inganshi tare da mutuncin iyayen sa, dan haka kwana 2 kawai na baku, ganin inda tayi shiru yasa abba fadin kinajina ko ?
Kai kawai ta iya dagawa sannan tasa hannunta ta share hawaye"
Tattaunawa suka fara tsakanin mama da abba tare da yaya usman, haka ne yabata daman tashi tabar musu falon"
****
Washegari ma'u ta tashi da matsanan cin ciwon kai, saka makon rashin baccin da batasamu, taso taki zuwa mkrnt amman kuma tanason taga halin da ummi take ciki, dan haka ta mike tahau shiri"
Drive ne ya kaita har bakin mkrntr sannan ya juya, dan kaka bata samu daman zuwa gidan su deeni ba saida aka tashi break"
Xama sukayi jugum ita da ummi kamar masu zaman makoki"
Bayan antashi makaranta abba da kanshi yazo ya dauketa"
Koda ta shiga gida a kitchen ta samu mama tanata soye2 sai alokacin ta tona da bakon da abba yace zaizo"
Yatsuna baki tayi sannan ta juya ta shige daki, wanka tayi tai sallah sannan ta tsaya tai addu'a sosai Allah ya kubutar da deeni daga hannun Jamal"
Tana zaune kan sallayan mama tashigo tana fadin Asma'u maza ki fito bakonki ya iso"
Gabanta taji ya fadi, kanta ta daga ta kalli mama sannan tace...
Mama dan Allah kice bacci nake, nifa bansan mezance mai ba"
Shiru mamatayi zuwa can tace, kinga, Asma'u banason shirme maza ki fito ko na kira abbanki na gayamai"
Cikin sauri ta mike tana matso hawaye ta nufi hanyan kofa"
Ke !! Zonan mama ta fada tana kare mata kallo"
Bayan ta juyo tace nufinki ahaka zaki tafi fuska saikace tsowar me takaba"
Bakinta agaba tace to ai yanzun nan fah nayi wanka"
Mama batace komai ba ta juya ta fara ciro mata kaya, mika mata tayi ta Saka sannan ta zaunar da ita dakanta ta mata kwalliya bawata me hayaniya ba"
Madaidaicin gyale ta mika mata dasukai matukar dacewa da kayan datasa, kallo ta kare mata sannan tace toh maza ga kayan motsa baki can na hada ki dauka ki tafi dashi"
Jikinta babu kwari ta nufa kitchen tare da nazarin abinda zata ma bakon ta kuntuka mishi haushi"
Ahankali ta tura kofar falon abba tare da sallama cikin siririyar muryanta, cikin ido ta kalli bakon nata farine babu laifi yana da kyau daidai misali, saidai daganin shi yana da iyali, duk da cewa bawani babba bane amman daganin shi yana da iyali, sauke idonta tayi akanshi sannan ta karasa shiga falon tare da neman yadda zata mishi"
Kayan motsa bakin ta ajeye agefen shi sannan ta koma tsakiyan falon ta tsuna, cikin ladabi tace...
Inakwana daddy, ina gajiya, bata jira ya amsa ba taci gaba da cewa gashi kazo kuma abban bayanan ya tafi Office amman idan ya dawo zan fadamishi kazo"
Cikin mamaki yake kallonta aranshi yace lallai wannan yariya da hikima take, idan na fahimceta tana nufin namata tsufa, gyaran murya yayi sannan yayi murmushi yace, toh shikenan asma'u idan ya dawo din ki gaya mishi, amman wa zaki ce masa?
Rasa abun cewa tayi zuwa can tace zance masa bayan fitanshi wani yazo neman shi"
Murmushi ya sake zaiso kasancewa da wannan yariyar, kallonta yayi ya girgiza kai sannan yace kinada abin dariya, ni sunana Jafar inada mata 1 da yara na guda 2 nine bakon da mahaifi ki ya sanar dake zuwan Sa, duk da nasan kinsan koni waye"
Ko kallon gafen shi batayi ba acikin zuciyarta tace wato abba neman kai yake dani, ya rasa wadda zai turomin sai me mata, dumi taji akumatun ta tana shafowa taji hawaye"
Duk abin da take bakonta na kallonta dan haka ya mike yace nizan tafi sai ince ki gaida mutanen gida"
Bata ce komai ba yasa hannu ya ciro kudi aljihu ya aje agefen kujera yayi waje dan yaga bata da niyar kula shi"
Itama ficewa tayi batare da ta dau kudin da ya ajiye mata ba, bare kayan motsa bakin datakai mai"
Afalo ta wuce mama ta shige dakinta, zama tayi tare da addu'a Allah yasa abban ya janye wannan kudirin nashi"
Washegari da safe ta shirya tsaf domin zuwa mkrnt falon abba ta fara shiga, bayan ta gaisheshi ta mike zata wuce abba ya dakatar da ita"
Komawa tayi ta zau tare da sauke kanta akasa"
Kallonta abba yayi sosai sannan yace bakon ki yazo jiya ko?
Kanta akasa tace eh"
Shiru ne ya ziyarci falon zuwa can abba ya sake cewa...
To me kika ce ? Ya miki ?
Shiru tayi bata ce komai ba, zuwa can abba ya sake cewa....
Karmuyi haka dake mamana, banason na takuraki saboda kin min biyayya saboda haka nakeson na saka miki, wadda kike so shi zan baki bazan miki auren dole ba da iznin Allah, inason nasan meye azuciyar ki game da jafar ?
Motsa baki tai tayi daker ta iya bude baki tace Abba ni banason shi"
Saboda me ? abba ya tambaya
Abba tsoho ne fah kuma yana da mata"
Murmushi Abba yayi kadan sannan yace ashe jafar ya cinka daidai, toh bakomai amman nayi miki sha,wan shi, dan yaro ne me mutunci da sanin ya kamata, haka iyayen shi mutane ne masu karamci, kuma bawani babba bane mamana, ko zai girmin usman bazai wuce shekara daya ba, amman ba komai tunda kince haka, gabe wani zaizo ki ganshi, kinji ko?
Saida gabanta ya fadi wato abba bazai bar mgn haka ba, da wannan tunanin ta tafi mkrnt ko wa Abba zai sake turo mata oho?
***
Akofar gidan su deeni ta hango samari cike, da alama yaran duna ne kome suke agurin oho, acikin su caka kawai ta sheda yanata fada yana daga hannu saidai har motan su ta wuce bata tsinci abinda suke cewa ba"
Ko a aji batai karatun kirki ba Allah2 take atashi break taje taga me akeyi"
Kawayen ta kallonta kawai sukeyi, domin sun kula akwai abun da ke damunta"
Ana buga kararrawa ta fito ta nufi gidan su deeni saidai yazun babu kowa akofar gidan"
Cikin gidan ta nufa tana tura kofar sukayi ido 4 da deeni, zaune yake kan kujera ummi tsugune agefen shi tana tsuma tsunma aruwa zafi tana dannan me ajikin shi"
Hunnu tasa ta mumtsuke idonta sannan ta sake sauke shi akan deeni, aguje tayi kansu, jinta kawai tayi jikin deeni ya rungume ta yana sumbatan ta"
Cikin sauri ummi ta dauke bokitin ruwan zafinta ta basu guri, jefe2 tana satan kallon su"
Sun dan juma ahaka ahankali asma'u ta zame ta koma gefe sannan ta zubawa deeni ido"
Shedan bulala ne ajikin shi rudu2 wasu guraren hadda ciwo, hawaye taji ya cika mata ido, nan danan suka fara zubowa acikin kuka tace nina jawo maka nasan bakowa bane yayi maka haka sai Jamal dan Allah ka yafe min"
Hannuta ya jawo ya riketa dakyau sannan yace....
Shine Asma'u amman karki damu yanaso ne wai ya nunamin shi Soja ne amman ba jarumi ba, wanna abin daya aikata ya nunamin be kai ba"
Kara karkace baki yayi sama sannan yace.....
Ai nagaya masa dan *uwas* data haife shi, idan yana jin yakai shege, ya goyo *uwassa* abaya, ya fadi ina zamu hadu, daban daban zasu koma gida"
Heart beat
*Mmn Yazeed*
Heart Beat
*Mmn Yazeed*鈥�
[22:51, 12/19/2017] 鈥�+234 806 858 0203鈥�: 馃挆馃挐馃挐馃挆
鈥�*BUGUN ZUCIYA*鈥�
( 鈥婬eartbeat鈥�)
馃挀馃挐馃挆
馃挆
馃挀馃挐馃挆
鈥婤y鈥�
馃挆
鈥嬧€�*Fadeela Lamido*
*@AM拢拢NCI WRITER'S ASSOCIATION馃*
Dedicated 馃憞馃徎
*Sa'adatu Lamido馃憣馃徎*
3鈨�1鈨� to 3鈨�2鈨�
馃檳馃檳 Hannu shi yasa yana share mata hawaye, yana cigaba da fadin.....
Ki daina zubar da hawayen Ki abanza ni be tsoratani ba kuma banyi nadamar hadashi da duna ba, kisan menene, tuhumata yakeyi akan ki"
Ido ta zare akaina kuma?
Eh dan ya nemi nabashi takardan da kika wurgu min da ita"
Tashin hankali bai yane afuskan ta tace... Kabashi ne?
A'a na nunamai bansan wannan zancen ba, amman sai naga yayi dariya, na lura kanshi na aiki sosai, murmushi deeni yayi kadan sannan yace.....
Asma'u da kika samu lbrn Sojoji sun tafi dani ya kikaji?
Wani sabo hawaye ne ya fara zobo mata cikin kuka tace....
Komawa nayi tamkar marainiya, kullum cikin kuka nake, gashi ranan na taho da matsalata, domin mune mi mafuta, wlh ranan jinayi kaman bani da lfy, kuma bansan abinda kemin ciwo ba, tun daga ranan hankali na bekara kwanciya ba, kum.....
Deeni ne ya matse hannun ta, dan haka ta kasa karasa abin da tayi niyya, sannan ta daga ido ta kalleshi"
Shima ita yake kallo sannan yace.....
Inason nasan wacce matsala ce kikazo da ita ranan?
Shiru tayi zuwa can tace abbana ne yace.....
Inayin sauka zai min aure, kuma gashi saura sati 6, yace bazan wuce wata 3 agida ba, shine hankali na ya tashi sosai"
Hannunta ya kara runtsewa sannan yace.....
Toh menene abin damuwa anan Asma'u ?, ko bakison muyi aure ne ?
Shiru tayi tana kallon kasa, zuwacan taji ya sake cewa....
Gayamin meye matsalan ?
Kanta akasa tace inajin tsoron gayawa abbana kai nake so"
Matse hannunta yayi da karfi harsai da tayi kara, cikin yanayi irin na mejin zafi tace.....
Wayyo, hannuna dan Allah kabari da
Zafi fah"
Me yasa kike tsoro? taji ya fadi fuskan shi murtuk"
Saboda ina tunanin bazai yadda ba"
Bangane bazai yadda ba, shi zai zauna miki da miji ?
A'a ba haka bane, ta fada tare da kautar da idanta gefe, haka nan taji bata ji dadin furucin ba, sai take ga kamar da raini aciki"
Shiko ido ya kura mata zuwa can yace.... Inajin ki"
Idan ta kwal2 yayi kaman zatai kuka tace....
Yaya deeni ni. nasan waye abba na, mawuyacin abu ne ya amince dakai, ko hankan zata kasan ce ko, to saida sa hannun kakata, kuma nafara mata zancen duk tabi ta firgice, saboda ta tsorata dakai, gashi abbana jiya ya turo min wani mutumi wai mu daidaita, karashe mgnr tayi tana zubar da hawaye"
Tana rufe baki deeni ya zabura ya mike tsaye, kashi ya daga sama yana kallon sararin samaniya tare da fadin..... Kikace baban ki ya turo miki wani ?
Kaita daga alamar eh"
Kuma wadda aka turo din yaxo ?
Eh tasake cewa tanabin kanshi daya dage sama da kallo"
Shiru yayi, zuwa can yace..... Kinyi mai dariya ne?
A'a"
Mgn fah ?
Ahankali ta shiga fada mishi yadda sukayi da jafar"
Ajiyan zuciya ya sauke sannan ya sakko da kan shi ya kalleta, hannushi Yasa ya dagota sannan ya saki murmushi tare da fadin, na yadda kina sona, kuma duk wadda ya sake turo miki karki yadda ki kulashi bare har kimai dariya, ke bama haka ba, ko fuskanki karki yadda wani ya gani"
Shiru yayi ya kura mata ido sannan yace kince babanki dan rayi ne ko?
Shiru tayi ta kasa bashi amsa, dan tasan darajan abban ta, tsoro take kar yazo ya fadin mata wata mummunan kalma akan abbanta"
Shiru yaji dan haka deeni ya sake cewa.... Kakar nan taki mamanki ta haifa ko babanki ?
Jimmm ma'u tayi sannan tace abbana"
A haf, a gurita ya dauko, dan kakar nan taki, lutiyar munafuka ce, amman bakomai Wata rana zamu hadu"
Mamaki furucin deeni bawa ma'u, nan take ta fara hawaye wannan ai zagi ne, yana nufin abbanta ma munafuki ne kenan, cikin matsanan cin kuka ta mike tare da kwace hannunta daga rukon daya mata"
kofar gidan ta nufa, cikin sauri ya mike yabi bayanta , tana daf da fita ya riketa, ganin inda take hawaye yasashi fadin menene ?, na miki wani abune ?
Wani sabon haushi ne ya sake kamata dan haka kukanta yaki tsayawa"
Ganin inda take kuka ya sashi ya kwalawa ummi kira"
Bayan ta iso yace ummi kinga yariyar nan munacikin mgn ta rikece min da kuka"
Hannuta ummi ta rike suka shiga daki, deeni yaso shiga Amman ummi tace yajira su awaje"
Zuwa can suka fito ummi rike da hannun ma'u tana kara rarrashinta tare da share mata hawaye"
Ummi me tace miki? Deeni ne ya tambaya tare da tsare su da ido"
Auta ina yawan gaya maka karinka gyara kalamin ka, iyaye fah ba,abin wasa bane"
Nan take ya fahimci laifin shi dan haka bejira ummi ta gama mgn ba yaja hannu ma'u yayo waje da ita"
Akofar gida yaja ya tsaya sannan ya kalleta yace..... Allah ya huci zuciyar ki, basan mgnr zata baki haushi ba, lallai kinason abban nan naki, gashi shi kuma ko kadan be damu dake ba, ganin inda ta daure fuska yasashi ya kama kunnen shi duk 2 sannan yace na tuba"
Be barta ta tafi ba harsai da yaga ta saki jikinta, tana dariya"
****
Washegari da misalin karfe 5:00pm bakon Asma,u na 2 ya iso"
Tafiya take jiki babu kwari domin isa falon da abba ya ke sauke baki, zuciyarta cike da tunanin deeni dan komai takeyi jitake kamar ana kara mata sonshi"
Tana shiga falon da kujeran data fara cin karo ta zauna sannan ta juya mai baya"
Bata ce kala ba shima bece komai ba, sun kwashi kusan minti 15 ahaka, sannan taji wata siririyar murya tace..... hajiya ba mgn ne?
Yi tayi kamar bata jishi ba, dan haka ya miki ya dawo kujeran dake kallon tata, cikin sauri ta sake juyawa ta kalli ban garen daya baro, kafarta daya ta daura akan daya tana dan girgizawa"
Jitayi yana fadin OK nine bazaki kalla ba kenan, toh idan ke bazaki kalleni ba ni kibari nagan ki"
Nan ma shiru yaji kada kafa kawai take"
Zuwa can ya sake cewa Asma'u ni akan hanya nake, ya kamata ki juyo muyi mgn yamma nayi"
Batace kala ba dan haka ya mike yana fadin OK shikenan, na fahimta, bekara cewa komai ba yayi waje"
Koda ta shiga gida bata tayar da hankalin taba harkokin ta ta shiga yi, dan idan ta tuna abba yace bazai mata auren dole ba hankalinta na kwanciya"
Washegari da safe abba ya aiko kiranta, hijabi ta dauka dogo har kasa ta saka sannan ta nufi falon abba"
Tun abakin kofar taji wata murya kaman ta *Jamal* suna gaisawa da abba"
Gabanta taji ya fadi tare da tunani yaushe yashigo gidan nan da sanyi safiyar nan yazu musu gida?
Tana shiga suka hada ido da *Jamal* yana zaune cikin kakin sa, agaban abba ya zauna ya cire hular shi, tare da tankwashe kafa, kamar wani me daukan karatu"
Yana ganinta ya dauke idon shi, tsunawa tayi ta gaida Abba sannan ta juya ta gaida Jamal"
Ciki2 ya amsa, kamar wanda be iya mgn"
Abba ko daure fuska yayi sannan ya dawo da hankali shi gareta, acikin bacin rai yace.....
Mamana kin fara bata min rai fah, ya zan turo miki bako kimai shiru?, towai tukuna ma, me kike nufi ne ?, nakula lamarin ki akwai abin dubawa aciki, toh bari nagaya miki niba mutumin banza bane, bazan dauki iskanci ba, duk yadda akayi acikin 2 za,a samu daya kodai wani ke hure miki kunne, ko kuma kinason kita zama agida har ki tsofe, amman banda iskanci ya zan turo miki bako ki banza dashi??
Asma'u kuka kawai take harda shashsheka, zuwa can taji muryan Jamal yana cewa....
Abba tunda bata so abarta mana, ai naga bawani girma tayi ba"
Au, au haka zakace, eh dole kace haka tunda kaima auren ba damun ka yayi ba, Abba ya fada sannan ya koma kan ma'u yace zan turo miki bako na karshe acikinsu, su 3 nan dole ki dauki daya, idan kuma kinada wani boyayye ne wadda kike so to kidaina wahalar dani"
Kuka ma'u tai tayi agaban Abba zuwa can taga ya juya gurin Jamal sun cigaba da hira, mikewa tayi tana kokarin fita taji Jamal nawa Abba sallama"
Da sarauri yake tafiya dan haka yacin mata, angajeta yayi kadan sannan ya juya ya kalleta yace..... toh ballagaza saboda rashin hankali kina kallo na kuma kika bege ni"
Cikin murya irinta wadda yaci kuka ya koshi tace ai kaine ka begeni bani ba"
Hannu ya mika ya murde mata kunne, batasan sannan da ta kwallah kara ba"
Mama ce tafito da sauri tana fadin menene ya faru?
Tseye ta same su ganin mama yasa shi ya saki kunnen, yana fadin mama wlh yariyar nan bata da kunya, tana ganina fa amman saita ture ni"
Juyawa mama tayi tana fadin wlh kabata kashi, batabari mama ta wuce ba tabi bayanta da gudu tana mamakin halin Jamal, wato banda mugunta kuma harda sharri?
Tundaga ranan abba be sake mata zancen aure ba, har ranan saukan su tazo, anyi sauka nagani na fada, abba yayi farin ciki sosai ganin inda ma'u take raira karatu hawaye yaji yana zubo mishi saboda tsabar farin ciki, addu'a ya fara Allah ya nuna mishi ranan aureta haka, itama ma,u farin ciki tayi sosai ganin dangi duk sun hallara kuma duk dominta"
Deeni ne kawai babu agurin tayi2 yasa manyan kaya yazo, amman yace shi bazai saka ba dan tunda yake betaba saka manyan kaya ba, dan haka tayi fushi tace karyazo"
Sun yi sauka da kwana 2 Abba ya aiko kiranta, mgnr dai daya ce gobe bakonta zaizo"
Kin tashi tayi tai zaune ta fara kuka, banza abba yayi da ita ya juya yaci gaba da rubuce2"
Suna haka alhaji musa ya shigo, ganin ta haka yasashi tambayan lfy?
Abba ne ya gayamai duk halin da ake ciki, shiru yayi zuwa can ya juya ya kallai ta yace"
Asma'u duba, ai shi aure dole ne, dan haka idan Allah yaso, nan da sati 2 kina dakin mijin ki, ko akwai wadda kike so ne?
Motsa baki ta fara amman ta kasa bude baki"
Alhaji musa ya sake cewa inajin ki, nakula bakin ki akwai mgn
Dago kata tayi ta kale abba sanna ta sake maida kanta kasa hawaye na zubowa tare da majina"
Abba ne yace ni Ki daina kallo na, ki fadi abin da ke bakin Ki"
Alhaji musa cikin tohoma yake kallon ta sannan yace....
Kina da wadda kike so ne?
Ahankali ta daga kai, saika kula sosai zaka gane"
Abba tashi yayi ya zauna sosai sannan yace waye shi?
Alhaji musa ne yayi murmushi sannan ya a,a bahaka za'ayi ba, ta turo mana shi kawai, ai daman mu bamu da burin yi miki auren dole, dan haka ki gaya masa munason ganin shi"
Ciki2 tace abba iyayen shi ne zasu zo, ko shi?
Girgiza kai Abba yayi cikin takaici, alhaji musa ne yace shi dai muke son gani kafin ajega mgnr iyayen sa, ai kisan aure yana son bincike ko ?
Heart Beat
*Mmn Yazeed*鈥�
[22:52, 12/19/2017] 鈥�+234 806 858 0203鈥�: 馃挆馃挐馃挐馃挆
鈥�*BUGUN ZUCIYA*鈥�
( 鈥婬eartbeat鈥�)
馃挀馃挐馃挆
馃挆
馃挀馃挐馃挆
鈥婤y鈥�
馃挆
鈥嬧€�*Fadeela Lamido*
*@AM拢拢NCI WRITER'S ASSOCIATION馃*
鈥�
Dedicated 馃憞馃徎
*Firdausi Sodangi Aisha Aliyu Garkuwa & Deeje Waziri*馃槏馃槏
3鈨�3鈨o3鈨�5鈨�
馃枻 Tashin hankali ma'u ta shiga tunkafi tabar falon, mikewa tayi jiki babu kwari ta koma dakin ta"
Ko acan din ma tunani ta shigayi, ta yaya zata kawo deeni gidan su, anya idan abba yaga deeni bazata fuskanci tashin hankali ba kuwa?
Hakika da ace zan iya hakura da deeni, da komai yazo min da sauke saidai bazan iya ba, yanzun ne ma nakejin son shi acikin zuciyata"
Shiru tayi tana tunanin hanyar da zatabi su hadu da deeni ayau"
Tana cikin wannan tunanin taga abba ya turo kofa, idonshi jawur har sun dan tasa"
Bakin gadon yazo ya zauna, yayi jugun yana kallan kasa"
Tsoro ne ya kama ma'u, kodai abba dokana yazo yi, wannan tunanin yasa ta fara ja da baya harta sauka agadon ta tsuna akasa"
Kallonta abba ya sake yi, sannan ya maida idon shi kasa, yayi haka kusan su uku sannan ya mike tsaye ya goya hannushi abaya, cikin wata irin murya wadda batasan Abba na da itaba taji yace.... Asma'u kin munafunce ni, tuntuni naso na miki aure amman sai kika nunamin ke ba yanzun ba, sai ayanzun naga laifina dana biye miki, shiru yayi zuwa can yace a ina kuka hadu dashi?
Cikin dasheshshiyar murya tace layin makarantar mu"
Juyowa yayi da sauri ya kalleta, akwai alaman tsoro a jdon shi, yace Allah yasa baki watsar da mutunciki ba ?
Karuwa kukanta yayi, cikin kuka tace... Wlh bakomai Abba"
Tsayawa yayi ya gama kare mata kallo, sannan yajuya ya fara tafiya tare da cewa daga yau karki sake fita ko haraban gidan nan bance kije ba,
Juyawa yayi ya fice abinshi"
Ma'u ko kuka taita yi, tana share hawayen"
Da daddare mama ta shigo dakin ma'u ranta abace, ganin haka yasa ta takara shiga cikin hankalinta"
Mama kasa mgn tayi illa kallo kawai data bita dashi, bayan ta gama kare mata kallo, ta juya ta fita batare da tace komai ba"
Washegari ma'u tanason ta sanar da deeni, ta rasa ya zatayi, gashi abba ya hata fita, kuma gashi bata taba karban no deeni ba, dan haka ta yanke shawaran ta rubuta taba drive ya kai mai"
Bayan ta gama rubutawa, ta miki tana tunani yama zatayi tabawa drive, bayan abba yace ko haraban gidan be amince taje ba"
Goggo tani ce ta fado mata, dan haka taje ta sameta, cikin ladabi tace mata goggo daman sani nake son nabawa sako, kuma gashi Abba ya hanani fita"
Mikewa tayi tana fadi.... to bari nayo miki kiran sa, hala laifi kikayi"
Sani drive nazuwa ta bashi takardan sannan tamai kwatan cen gidan, ya wuce"
馃挐馃挐馃挐
*Wanene *Jamal* ?
*Jamal* shine d'a name farko agun alhaji inuwa manga, mahaifiyar shi hajiya Sadiya bafulata ce ta usuli, bayan haihuwan Jamal suka samu sabani wadda harta kaisu da rabuwa"
Bayan rabuwan su ne ya aure hajiya asabe wadda ta haifan yarta guda daya Aisha, ran hajiya asabe besoba, taso ace namiji ta haifa, dan haka ta dauki tsana ta daurawa Jamal, Jamal yasha matukar wahala agun hajiya asabe wadda suke kiranta da mami"
Tun daga kan Aisha bata sake samon haihuwa ba, dan haka tsanan Jamal yake kara ruruwa acikin zuciyarta, jitake tamkar ta kashe shi"
Jamal yasha wahala bakadan ba, duk da cewa mahaifin shi attajiri ne, amman mama taki bari yaji dadi, ta kanainaye komai"
Dan haka tun yana karamin ya taso dason ya zama soja, saboda yawan zaman kunci dayake, ya saba da zaman shiru, zama shi kadai be dameshi ba, kulum yana daki saboda mami bata barin shi ya sake, kullun ida ya tafi makaranta tun safe sai 6, daya dawo zai shige dakin sa, haka yasa bashi da abokin hira sai karan ce karan ce, aban garen addini ma ba,abarshi abaya ba kullum da subahi yakan karanta Qur'ani, dan haka tun yana karami yake da kaifin basira"
Har tasowan shi karatun shi kawai yasa agaba, bayan ya kammala karatu ne hankalin Alhaji inuwa ya fara dawowa kanshi,
Kuma lukacin ne ya lura dabi,un shi, sun canja, baya son yawan mgn, dan haka ya fara janshi ajikin shi, itama mami lokaci da ta fahimci yanzun ya mallaki hankalin shi saita fara sakar mai fuska, agaban idon shi"
Itako momyn jamal bayan rabuwanta da alhaji inuwa ta aure wani attajiri har suka haifi 'yarsu 1 Nafisa, sheran Nafisa 14 mahaifinta ya rasu dan haka bayan Momy ta gama takama ta dawo gidan alhaji inuwa, ayanzun haka shekaranta 2 da dawowa gurin daddy Jamal, tare da 'yarta Nafisa,
Bayan Jamal ya fara aiki ne akafara mai zancen aure, amman ko kunya bayaji yake cewa Allah ya kyauta nine Zanyi aure, 'yar karamar yariya ta rainani, ni ba auren da zanyi"
Lokacin daya fara fadin haka, daga Momy har daddy dariya suka yi, tare da ganin wauta ce ta mai yawa, hartakai duk abokan shi sunyi aure, amman shi ko abokin shine zaiyi aure daga gun daurin auren ya keyin sallama acewan shi bazaije gun taron mata ba haka kurum su raina shi, dan haka lokacin da usman ya matsawa Jamal ya kawo musu ziyara, yace zaixo amman fah bazai sauka gidan shiba sabo da kar matar shi ta raina shi"
Dariya kawai usman yayi sannan yace toh kazo saika sauka gidan abba, haka tasa dole yayi karyan matar sa tayi tafiya"
Acikin abokan Jamal babu wadda besan halinsa ba nashegen son girma"
Momy da daddy suyi mgn har sun gaji akan yayi Aure amman killum mgnr daya ce, shifa bazaiyi Aure ba dan kada yariya tace zata raina shi"
Tun daddy da momy nawa abin dariya, har yazo ya fara basu haushi"
Ranan daya dawo daga gidan su ma'u kuwa kasa zama yayi, bashi falo bashi dakin momy, hakanan yaji zancen auren ma'u ya dame shi"
Momy ce ta lura zirga zirgan shi yayi yawa dan haka ta bishi da kallo tare da fadin kai lafiyan ka ?
Kusa da Momy yaje ya zauna sannan yace Momy wata 'yar tatsiyar yariya ce wai za,a mata aure, idan kika ganta kamar 'yar tsana"
Tsaki momy taja tare da fadin kaifah baka da kan gado, na kula adawa kake da aure"
Momy wlh yariyar da kadan tafi Nafisa"
Hmmm Jamal kenan toh ai ko Nafisan ana iya mata aure, lallai ma Jamal kaman Nafisan kake kira 'yar tsana, Allah ya shirye ka"
Haka ya kwana bayajin dadin, gashi ya rasa me yake damun Sa, dan haka washegari ya tashi bayajin karfin jikin sa"
Gajiya yayi da kwanciya adaki karfe 11:30 ya tashi ya zauna abakin gadon, azuciyar shi yace waini meke damu na ne? Husna yaji wani bangare na zuciyan shi na fadi"
Tsaki yaja afili yace.... Babu wata *Husna* kawai ban da lfy ne, ji yayi kaman yanajin sanyi gashi har yanzun beji natsuwa tazo masa ba, dan haka yajawo bargon daya rufa dashi ya rufe jikinshi ruf, kanshi kawai kake hangowa ya nufi part din momy"
itako momy tana zaune afalo, Nafisa kwance ajikinta tana kuka ahankali"
Cikin tausayawa mama take cewa haba nafisa ki dinga hakuri mana, yakamata ace yanzun kin saba tunda duk Wata haka yake miki"
Daidai lokacin mama ta hango Jamal yana tahowa ya kudundune cikin bargo"
Da mamaki take kallon shi, harya karaso daf da ita ya zauna bata daina kallon shi ba"
Menene haka kuma Jamal?
Momy wlh bani da lfy"
Allah na gode maka, meke damun ka?
Yana kara lullube jikin shi yace... Inaji dai kaman zazzabi ne"
Toh Allah ya sauwake, ka tashi ka koma daki kasha magani, kaga Nafisa ma tun safe mata jin dadi"
Kallonta yayi sosai sannan yace.... Nakoma daki fah kikace, nace miki bani da lfy kuma kice na koma daki na zauna ni daya?
Hmmm Jamal kenan, toh idan ka zauna anan ni me zan maka, kaga amfanin iyali kenan"
Shiru yayi yana girgiza kai, zuwa can yace..... Momy nida Nafisa akwai banbaci kenan tunda gashi kin dauki nafisa kin daura ajikin Ki, nikuma kince nakoma daki,nayi jinyan kaina"
Tunawa momy tayi da kishi irin na jamal dan haka ta fara kokarin daga Nafisa tana fadin zo ka hau"
Mikewa yayi cikin sauri yana kokarin fita yana fadi, ai kince na koma daki idan na mutu shi kenan"
Yana wucewa momy tace Ja'iri duk yadda akayi zama shi daya ne ya soma damun shi, bari dai daddyn sa ya dawo asan abinyi"
****
KANO
Tun da sani ya tafi ma'u ta koma dakinta tana zaman jiran dawowan sani tare da addu'an Allah yasa komai ya tafi daidai 馃檹馃徎"
Lokacin da sani drive ya isa gidan da asma'u ta kwatan ta mai fitowa yayi yai sallama akofar gidan"
Ummi ce ta leko bayan sun gaisa yace.... Shamsuddeeni yake yake son gani"
Kaman daman jira yake, ya fito yana mazurai, jada baya sani yayi domin tsorata da yayi da ganin deeni"
Cikin mazurai deeni yace..... Kai!! Menene lfy?
Jikin sani na rawa ya ciro takaddan ya mika mashi,tare da fadin asma'u ce tace nakawo maka"
Murmushi ne ya baiyana afuskan deeni nan take ya warware takardan ya fara karantawa, bayani tamai akan kiran da abbanta yake mai, dadi yaji ba kadan ba, idon shi ya dago ya kalli sani sannan yace shikenan kace mata ina gaisheta, Jim yadanyi sannan ya juya zai shiga yana fadin inzuwa"
Sani ya dade tsaye akofar gida yana jiran deeni, zuwa can saiga gashi ya fito, takarda ya mika masa sannan ya nuna masa hanya tare da fadin ware"
Ahanya babu abunda sani yake banda tunani, tun da yake betaba tsam manin asma'u zata saurari mutum irin deeni ba, duba fah wai ni yake nunawa hanya saikace bani na kawo kaina ba, irin su abu kadan zaka musu su rufeka da duka, addu'a ya fara yi azuciyar shi Allah yasa kar akara aiko shi"
**
Deeni yau ji yake babu ishi, wani mugun farin ciki ne yaji ya kamashi, ummi ma taji dadin lbrn saidai ta wani bangaren gabanta na faduwa, dan ayadda taga ma'u tasan cewa iyayenta bazasu so dabi'un autan ta ba, dan haka daga deeni har asma'u tana tausaya musu, dan itace sheda tafi kowa sanin inda suke son junan su"
Zama tayi ta zuba uban tagumi tana bin deeni da kallo sai murmushi yake yi, hakan nan taji yana bata tausayi"
Gyaran murya ummi tayi sannan tace.... toh auta goben kai kai kadai zaka ?
Toh ummi nidawa zani, saidai idan idan caka zan kira, kai ninafison na tafi ni 1 "
Da Sauri ummi tace eh gare katafi kai kadai, kuma dan Allah kayi shiga na mutunci karkai irin shigar nan taka, ni kaga asubanci zanyi domin inason nayi mgn da yaya larai"
Bece mata komai ba ya mike ya shige dakin Sa"
Itako ma,u tunda sani drive ya kawa mata sakon deeni karantawa take tana sake maimaitawa, dadi taji dataga no banshi aciki dan haka bata bata lokaci ba wajen kiran shi"
Da wayar mama ta kirashi dan ita har yanzun ba,a bata damar rike waya ba"
Hira sukasha sosai sannan ta gaya mishi lokacin da abba yake gida"
Goggo tani ta samu ta roketa dan Allah ta gayawa mama bakon nata zaizo gobe da misalin 11:30am"
Dan haka washegari ta tashi da tunani guda 2, ko nasara ko akasin haka"
Aban garen deeni ko, shiri yake tayi domin zuwa ganawa da sirikin shi, tun da duku2 ummi ta wuce dan haka shikadai ne agidan"
Bayan yayi wanka ya gama kintsa jikin sa, karamar riga ya dauko hannunta iya daidai kafada, sannan yasaka wandon shi ya dan wuce guiwa da kadan, turare ya dauka yana fesawa ajikin shi, sai alokacin mgnr ummi ta fado mishi, da take cewa... idan ka tashi tafiya kasa kayan mutunci, kallon kayan ya kara yi sannan ya kalli gurin dayake ajiye kaya, gani yayi duk acikin kayan wannan ne me dama dama, dan haka ya saki fito tare da dage kansa sama"
Fitowa yayi ya rufe gidan ya fara tafiya, ji yayi kaman akwai abinda ya manta agida, jayayi ya tsaya tare da shafa wuyan shi, sai lokacin ya tuna
ya bawa ma'u sarkan shi, da yanzun ita zatamai rakiya yana tafiya tana kara, tare da tashi sama, tsaki yaja afili yace.... Ina bazai yuyoba tafiya babu sarka kuma babu duna ai sai na dade banje ba"
Hannu yasa aljihun shi ya ciro waya sannan ya karata akunnesa
yana fadin...... Caka kawomin Duna da matar sa zasumin rakiya"
Cikin kankanin lokaci Caka ya kawa su kamar yadda ya bukata"
Cikin wani irin taku ya fara tafiya duna da matar sa nabin shi abaya suna mishi haushi duk inda aka kan shi kyaucewa ake abashi hanya.....
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
[22:52, 12/19/2017] 鈥�+234 806 858 0203鈥�: 馃挆馃挐馃挐馃挆
鈥�*BUGUN ZUCIYA*鈥�
( 鈥婬eartbeat鈥�)
馃挀馃挐馃挆
馃挆
馃挀馃挐馃挆
鈥婤y鈥�
馃挆
鈥嬧€�*Fadeela Lamido*
*@AM拢拢NCI WRITER'S ASSOCIATION馃*
鈥�
*馃挐馃挐馃挐 Salam masoya BUGUN ZUCIYA, hakika kun nunawa wannan book kauna, tare da ni kaina, farin cikina bashi missaltuwa, sai dai nace muku nagode2 Irin sosai!!! din nan, kuma ina fatan kun fara fahimtan darasin dake ciki馃挐馃挐馃槝馃槝*
*SADAU馃憞馃徎KARWA*
*Masoya BUGUN ZUCIYA aduk inda suke*馃槏馃槝
3鈨�6鈨o3鈨�7鈨�
馃悤馃悤馃悤 Cikin wannan yanayi deeni ya isa kofar gidan su ma'u"
Yana kokarin taba get din sani drive na fitowa"
Wani mugun faduwan gaba yaji dan haka besan sadda ya kauce ya bashi hanya ba"
Mannewa yayi ajikin bango tare da bin karnukan da kallo, har suka shige cikin haraban gidan"
Suna shiga gidan karnukan suka daina haushi sakamakon hannu da deeni yasa yana shafa musu kai"
Zuwa can deeni ya dago ya kalli sani cikin daure fuska yace..... Gaya mata na iso"
Jikin sani na rawa ya nufi cikin gidan, mama ya samu afalo jikin shi na rawa yace wai bakon Asma'u ya iso"
Tabe baki mama tayi sannan tace toh ka bude masa falon alhaji"
Juyawa sani yayi badan ransa yaso ba"
Sani nagaba deeni nabinsa abaya, har suka isa, kofar ya bude, tare da fadin bismillah"
Shigewa deeni yayi, su duna na take mushi baya' tsaye yayi yana karewa falon kallo, tare da fadi azuciyar shi, lallai mahaifin ma'u me kudi"
Waiwaigawa yayi ya zabi kujeran dayaga tamishi ya zauna"
Yayin da karnukan shi suka kwanta agefe"
***
Ma'u tunda taji sani yana gayawa mama ta shiga damuwa tare da addu'an Allah yasa deeni manyan kaya ya saka, kuma Allah yasa ummi ta gargade shi ya gyara harcen sa"
Addu'oi da tai tayi kenan, har zuwa lokacin da taji fitowan abba da baba"
Cikinta taji ya kada dan haka ta tashi ta shiga bayi"
Alhaji musa ne agaba abba na binsa abaya dan haka alhaji musa na tura kofar yayi to zali da duna"
Tsayawa yayi cak sannan ya juya ya kalli abba tare da tambayan shi, Gamo nayi ne?
Atare suka maida idon su cikin falon, tare da karasa shiga ciki, ko wanne su bakin shi dauke da addu'oi a bakin shi"
Wani irin BUGAWA ZUCIYOYIN su yayi atare ganin matashin saurayi zaune, karnuka kewaye dashi, cikin bin bango abba ke kokarin shiga ciki hannun shi daya dafe da saitin ZUCIYAR shi"
Alhaji musa ne yayi karfin halin karasawa gaban deeni tare da fadin.... Daga ina?
Deeni cike da kwarin guiwa yace nine bakon da Asma'u ta sanar muku da zuwan shi"
Runtse Ido alhaji musa yayi tare da dafe kirjin sa yana sauke wani irin nufashi, ja yayi da baya ya nemi wata kujera ya zauna"
Abba kuwa yana rike da kirji shi acikin zuciyar shi ko fadi yake Allah Yasa yazamto mafarki ne"
Ganin inda Abba ya sandare aguri guda, yasa alhaji musa dakewa, ya fara kwalawa Asma'u kira"
Tunda asma'u ta jiyo irin kiran da baba yake kwalawa tasan akwai Marsala, dan haka jikinta narawa tafi falon abba"
Tagaban Abba ta wuce haryanzun yana nan a inda yake"
Gabantane yai wani mummunan faduwa ganin duna kwance atsakiyan falon mahaifinta"
Ganinta kawai tayi ta daura hannuwanta 2 aka, tare da zubar da hawaye"
Sauke hannun ki taji Abba yace, bashiri ta sauke su kasa sannan tabi Abba da baba da kallo"
Deeni ko ma'u yake kallo fuskan shi dauke da murmushi"
Ahankali Abba ya nemi guri ya zauna, alhaji Musa ko, kallo yake bin ma'u da deeni dashi"
Abba ne ya kalleta sosai sannan yace.... Asma'u wannan shine yaron da kikace kina so ?
Eh, tace batare dajin kunya ba, dan ita ganinta wannan itace daman ta na karshe"
Girgiza kai Abba yayi tare da fadin yayi kyau, shiru yayi zuwa can ya sake cewa.......Asma'u kikace wannan shine wadda kika amince ya zama uban 'ya'yan ki ?
Kasa mgn tayi hawaye na zuba a idon ta"
Shiko deeni, wani irin kallo yake yi Wa abba dan ya rasa inda mgnr abba ta nufa be amince bane, koko so yake ya tabbatar?
Inajin Ki abban ya sake fada"
Ahankali ta daga kai alamar eh"
Abba komawa yayi ya kwanta ajikin kujera"
Alhaji Musa ne yayi ajiyan zuciya sannan ya juya ya kalli deeni yace......... To kai Yaro bamu gaisa ba bare musan sunan ka"
Cikin murya nan da kukasan deeni da ita ya karkace baki yace..... Sannu ku dai, ina kwanan ku?
Alhaji musa ne kurun ya amsa Abba ko inbanda binshi da kallo ba abin daya ke"
Cigaba yayi da fadin...... Ni sunana shamsundeeni amman anfi sanina da shamsun duna"
Yayi kyau alhaji musa ya fada, sannan ya kara da cewa...... Kai dan gidan waye ?
Murmushi deeni yayi sannan yace...... Ni jikan isa kaka ne"
Isa kaka ? Abba ya fada yana zare ido"
Eh, deeni ya fada"
Isa kaka ai 'ya daya ya haifa, kananufin kai dan saratu ne?
Eh deeni ya sake fadi"
Toh, toh, abu yayi na fahimta, cewar abba yana kokari mikewa tsaye, kanshi ya daga sama sannan yacewa alhaji musa shike nan, sallame shi"
Ma'u alhaji musa ya kallah, sannan ya kalli deeni yace...... Shikenan kaje zamu neme ka"
Mikewa deeni yayi yanabin ma'u da kallo ya fice waje, yan rakiyan shi nabin shi abaya"
Mikewa asma'u tayi zata fita, alhaji Musa yace koma ki zauna"
Jikinta na bari ta zauna, abban najin fitan deeni ya kalli ma'u idon shi jawur yace..... tirrrrrr Asmu'u, kinyi asara, dan yatsan shi daya ya daga sama sannan yace wlh wlh Asma'u ko zaki mutu asma,u bazaki aure yaron nan ba"
Alhaji musa ma mikewa yayi cikin tuhuma yace...... Asma'u kisan waye shi?, kinsan waye ubanshi?,
meye abin sha,awa?, me kika gani ?, meye ya rudeki ?
Kan asama'u akasa kuka kawai take, kaman ranta zai fita, tasani dabi'un deeni basu da kyau amman tamai fatan shiriya, dan haka acikin zuciyarta take addu'an Allah ya karkato da hankalin su abba su bata zabin ranta"
Muryan Abba taji ashake yana cewa..... Sabo da wannan abon kika kora mutane masu mutunci ?, Atunanin ki nizan daukeki inbawa wannan katon Dan iskan ? Wlh kinyi kuskure, baki isaba kinyi kadan, wato ina nan ina tufka wani na warware min" wan nan yaron da kike gani daga uwar shi har uban shi ba mutanen kirki bane"
Yadda abba ke daga murya yasa mama shigowa tsaye tayi tana sauraran su, harta fahimce akan abun da suke mgn"
Ma'u tabi da kallo hawaye ciki da idonta, Abba ko banda tsiyaya fada babu abinda yakeyi"
Alhaji musa ne ya tsaidashi ta hanyar fadin......barta haka, yanzun mgn ta kare, bazamu zuba mata ido ta zubar mana da mutunci ba, ko kina so ko baki so da yardan Allah bazaki wuce sati 2 agidanan ba, za'a daura miki aure da duk wadda Allah yasa shine Mijin ki"
Rikecewa ma'u tayi da kuka harta fara fita cikin hayacin ta, cikin kuka tace baba, dan Allah kumin rai, wlh Abba shi nake so, idan ban aureshi ba mutuwa zanyi, dan Allah karku rabani dashi, Allah ne ya dauramin sonshi bani nadaurawa kaina ba"
Hawayen takaici ne suka fara zobowa a idon Abba, mikewa tsaye yayi azafafe ya fara takowa gabanta tare da fadin zakiyi fito nafito da ni ne ? yau zan gani tsakanin ni dake waye ya haifi wani, duka ya rufeta dashi kan kace me abba ya kece da amai"
Alhaji musa arude ya nufeshi ya rike shi, amman duk da haka abba dukan ma'u yake tare da wani irin tari sai lokacin Alhaji musa ya lura kanin nasa aman jini yake"
Daker ya rabashi da jikin ma'u duk jikinta jinin abba ne, haka yasa hankalin shi ya kara tashi"
No Usman alhaji musa ya kira, ya gayamishi halin da ake ciki"
Da taimakon Sani drive suka saka Abba amota suka nufi asibiti dashi"
Shiko usman lokacin da akirashi suna tare da Jamal a Abuja, suna tsakiyar aiki"
Ganin inda hankalin shi ya tashi yasa Jamal be bashshi ya taho shi kadai ba"
Sun iso Kano dafda magariba, kai tsaye asibitin suka wuce"
Lokacin da sukazo abba baya cikin Hankalin sa, kwance kawai yake, komai na jikin shi baya motse, bakin shine kawai yake motsawa, ahankali yakai kanshi saitin bakin abba, jiyayi yana fadin Asma'u, fadi yake baya kyaukyautawa, dan haka ahargitse ya kalli mama tare da fadin duk yadda akayi asma'u ce sanadin ciyon nan na Abba, bakin shi sunanta kawai yake kira"
Sallaman dada ne ya katse musu hanzari, arikece ta wuce usman tana leka fuskan abban, ganin shi haka yasa ta fara tofamai addu,io"
Usman ne yaci gaba da tambayan mama ma'u tayi wani abu ne ?
Mamatana share hawaye take gaya musu halin da ake ciki, ai ganin dada kawai sukayi ta zame kasa, tare da fadin yanzun nan yariyar nan bata bar mgnr yaron nan ba?
Duk abinda suke Jamal na gefe yana kallon su, rungume hannun shi yayi akirji tare da lumshe ido kamar besan me ake cewa ba"
Nan danan jikin dada ya rikice, haki ta fara babu kyau2 tawa dan haka usman yaje ya kira likita, cikin mintocin da basu wuce 7 ba, dada ta fita cikin hayyacinta dole tasa aka bata gado"
Mama da momy ne suka kwana akan dada yayin da Alhaji Musa da su Jamal suka kwana akan abba, babu bacci dan Abba sai kusan asuba ya samu bacci"
*****
Washegari Abba ya tashi jikinshi yayi dama dama bakaman jiya ba, saidai jikin dada sai kara rikicewa yake"
Da misalin karfe 1:23pm Alhaji inuwa manga ya iso duba jikin abokin shi"
Bayan gaishe2 tsanin alhaji inuwa manga da alhaji musa, matsawa yayi gurin Abba"
Mgn suke ahankali abba da kanshi yabawa alhaji inuwa lbrn halin da ake ciki"
Nasiha yamai tare da tare da kara bashi shawar wari, nan Abba yadan ji sanyi aranshi"
Zuwa can abba yaji bacin rai ya sake taso mai, dan haka ya kira jamal da usman yace musu..... Maza kuje gida kutaru Ku karya min asma'u"
Kaman jira suke suka fita cikin sauri, Alhaji inuwa nakiran su ina, sun riga sun fice"
Bayan fitan su alhaji inuwa yakalli alhaji musa yace inason ganin ka"
Waje suka fita sun dan juma sannnan suka dawo fuskan su dauke da murmushi"
Abba kallo ya bisu dashi, koda besan me suka tattauna ba, ya san magana ce me mahimmanci"
Ganin inda yake kallon su, yasa alhaji musa cewa......rana ita yau za,a daura auren *Asma,u* da *Jamal* mahaifin shi ya neman mai aureta aguri na kuma na bashi"
Cikin farin ciki Abba yace Allah ya nuna mana"
*****
Ma'u ko yadda taga rana haka taga dare ba abun da yake damunta ban da tunanin abban ta, kasa komai tayi nan danan ta rame tai zuro2 goggo tani ce taita lallashin ta ruwa kawai take iya sha"
Misalin karfe 3:00 goggo ta matsa mata tai wanka, dan haka ta mike ajikinta babu kwari tacire kaya ta dauko towel ta daura, toilet ta shiga harta tube ta murza kunfa, tafarajin ana kwala mata kira, cikin hargagi, muryan yaya usman ta gane aciki, hayaniya irin nasu na sojoji"
Arikece ta mike ta dauki towel dinta ta daura, daidai lokacin taji an banko kofar daki"
Saida ya kira sunanta so uku ajere sannan asma'u ta amsa adabur ce"
Fito dan uban ki"
Cikin rawan murya tace yaya wanka nake yi"
Idan kika bari nashigo bazan miki da wasa ba"
Kara rikicewa asma,u tayi, sannan ta rushe da kuka, batai aune ba taga yaya usman acikin bayin, mari ya wanka mata, kafin ta ankara take karajin saukan wani, dan haka ta riki ce tayi waje rike da towel dinta dake kokarin warwarewa"
Mutum take gani dishishi kamar yaya Jamal zaune agefen gadonta cikin kakin sa, yana danna waya"
Gani tayi ya rabun mata kashi2 duk inda ta waiga shi take gani, daga can ta hango yaya usman yayo kanta, Dan haka aguje ta tayi kan abin da take ganin shi kaman gizon yaya jamal
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
[22:53, 12/19/2017] 鈥�+234 806 858 0203鈥�: 馃挆馃挐馃挐馃挆
鈥�*BUGUN ZUCIYA*鈥�
( 鈥婬eartbeat鈥�)
馃挀馃挐馃挆
馃挆
馃挀馃挐馃挆
鈥婤y鈥�
馃挆
鈥嬧€�*Fadeela Lamido*
*@AM拢拢NCI WRITER'S ASSOCIATION馃*
鈥�
Dedicated馃憞馃徎
*Miss xoxo*
I love u, so much馃槝
*Kaunarki gareni daga Allah ne*
3鈨�8鈨o4鈨�0鈨�
馃ず馃ず馃ず
馃ず Duk da cewa Jamal yayi kaman beganta amman yana ganin inda ta nufoshi gadan2 yasa ya ajiye wayar shi agefe sannan ya miki cikin sauri"
Itako asma'u tanazuwa ta fada jikin shi ko da tajita jikin shi ma, bata tsaya ba, kara kadandane shi take dan tasan idan tayi haka dole yaya usman yabarta, dan haka hannunta tasa guda 1 ta bayan sa yayin da dayan ta danne towel dinta dashi"
Ganin haka hankalin Jamal yayi mummanan tashi kokarin rabata da jikin shi yake tare dasa hannushi ya rike mata towel din kamar yadda yaga tayi, saboda gudun kartayi tsirara, cikin tsawa yake fadin usman bari, bari, menene haka ?"
Usman natada jijjiyan wuya yake fadin..... kasan Allah wlh saina sumar da yariyar nan"
Shima cikin tsawa yace naji ko ka shetama zakayi zaka iya amman ka bari tasa kaya ajikin ta"
Usman fah ranshi ya riga ya bacci banda jijiyoyi kan shi baka hango komai, dan haka jamal ya dauketa cak ya nufi toilet da ita, tare da kare dukan da usman yake kaimata"
Ciki ya sakata sannan ya jawo kofan tare da tsawa abikin toilet din dan usman har yanzun be hakura ba"
Kallo Jamal yabi usman dashi sannan yace dallah jin inda kake tada jijiyan wuya, mace ce fah, macen ma yar ficiciya"
Juyawa usman yayi yana huci, ya fice"
Usman na fita jamal yaja tsaki sannan yace ke kuma dallah karki cikawa mutane kune da kuka, nan dan ma'u ta kunshe bakin ta"
Zuwa can ya sake cewa fito ki saka kaya, ki fito falo ki same ni"
Sai da taji ta dainajin motsen sa sannan ta fito, tayi zuro2 da ita"
Saboda tsabar rudewa riga daban siket daban ta Saka, sannan ta daura Karamin hijjabi akai"
Afalo ta same su, Usman har yanzun bebar huci ba, Jamal ko kallo ya bita dashi, Sannan yace tsuguna kisa guiwar ki akasa"
Tsugunawa tayi kamar yadda yace tare da sunkuyar da kanta kasa"
Daga hannun ki sama sannan ki rufe idon ki"
Innalillahi, ta fada sanan ta miki tana dan bubbuga kafa alamar tsoro"
Mekewa jamal yayi tare da fadin eh lallai baki dakuba, rawa ma kike min ?
Cikin kuka ta tsuguna tana fadin wlh na daku, hannu nama ciwo yake min dan Allah kuyi hakuri"
Usman ne yace nagaya maka duka ne ya dace da yariyar nan, kace ba haka ba, mikewa yake kokarin yi Jamal ya tare shi tare da fadin banni da ita, karyan rashin kunya take"
Dasauri ma'u ta tsuguna tayi kamar yadda yace, idonta arufe amman hawaye na zuba a idonta, bayan kusan minti 30 taji daya daga cikin su ya fita, saidai bata san ko wanene ba"
Gaba daya jijjiyoyin hannunta ya sake, kuma hakan takejin kamar kallonta ake dan haka tayi saurin bude ido"
Jamal ta gani ya ya kurawa guri daya ido, bin inda yake kallo tayi da idonta, nan ta gane ashe sanadin daga hannunta sama rigarta ta daga dan haka cibiyanta baiyane yake, kuma indai idonta ba kizo ya mata ba' Jamal gurin yake kallo"
Cikin sauri tasa hannunta ta jawo siket dinta sama, zabura Jamal yayi tare da fadin ke!! Waye yace ki bude idonki"
Mayarwa tayi ta kulle, tare da kara tsanan Jamal, tsine mishi taitayi azuciyanta tare da mai fatan bala'i kala2, bata san abin da yasa ba, duk abin da yaya usman zai mata kadan yake bata haushi, amman na jamal yana mata kuna"
Saida Jamal yaga tana tangadi kamar zata fadi sannan yace zauna"
Zama tayi tana share hawaye da hijjabinta, idon nan luhu2
Wuce kiban waje kuma duk ranan da kika sake Tayar da zancen me kare sai kinci kaniyar ki"
Tafiya ma'u tayi harta shege daki tana jerawa jamal Allah ya isa, tare da addu'an Allah yasa yana fita mota ta begeshi ya mutu"
Har Washegari su mama basu dawo ba, dan haka taji bazata iya hakuri ba, Sani ta samu ya dauketa suka tafi"
Tunda sani ya sauketa gabanta ke faduwa ba komai ke damunta ba sai haduwanta da Abba da mama, tasan suna fushi da ita"
Tana tura kofar dakin sukai idon 4 da mama, daga can gefen gadon ko, wani Mutun ne, me tsananin kama da Jamal sosai kamar harta baci"
Mama na ganin ma'u ta mike tana fadin.....
Me kikazo yi ?, menene ya kawo ki?, kinzo ki karasa su ne ?....
Sakin kofar ma'u taso yi, karafff taji anriketa, wannan mutumin ne me kama da yaya Jamal"
Hannnuta ya ruko suka shigo cikin dakin, sannan ya kureta da ido, zuwa can yace a shema yariya ce karama, rashin wayo ne yake damunta, kallonta ya karayi sannan yace..... Yi shiru kinji 'yata? Ki daina kuka"
Ta gaban mama ya wuce da ma'u agaban gadon da abba yake ya saketa sannan yace...maza ki tsuguna kibawa mahauifiki hakuri, nasan kinje makaranta kuma kinsan girman iyaye agare ki, daga yau kar akara ce miki ga abinda zakiyi, kice a'a, domin duk abin da babba ya hango yaro ko rimi yahau bazai iya hangowa ba, kuma wani lokacin zuciyarmu nason abu, wata kila ba alheri bane, dan haka kiyiwa iyayenki biyayya, ko kinason wani abu ya samu mahaifin ki ta dalilin Ki,?
Gargiza kai ma'u tayi hawaye na sauka aidonta"
Toh ki maida hankali Ki, gatan da uba zaiyiwa yarsa shine aure, kuma wada duk ya rasa wadda zai masa fada yayi asara"
Sosai maganga nun suka shiga jikin ma'u, cikin kuka tafara rokon Abba gafara, tare da nuna masa yayi yadda ya gadama da ita"
Koda abba bece mata kallah ba Amman yaji dadin kalamanta"
Alhaji inuwa kan mama ya juya yaita nuna mata mahimmanci jawo 'ya'ya ajiki, tare da nuna mata ta daina kyaran ma'u"
Bayan ya gama da mama ya sake jawo hannnun ma'u ya kaita har dakin da dada take, saidai dada naganin ma'u ta fara fadin Innahu Sulaimana Wa innahu Bismillahir Rahimu, Kalu lahaula, Lahaula wala kuwata, kufita min da ita , gata nan, gata nan"
Momy ce ta rike dada tana fadin dada Asma'u ce fah, takwaranr ki, ki kwantar da hankali ki mana"
Karasawa daddyn Jamal yayi ya kamo hannun dada ya hada dana ma'u, sannan yace mata ta bata hakuri"
Cikin kuka ma'u ta rike dada tace dada kiyi hakuri dan Allah nina bari bazan kara ba"
Arikece dada tace kikace kin bari, kin hakura dame karan?
Kai ma'u ta gyada mata"
Ke takwara da gsk kincire me karan azuciyar ki?, nidai indai kinsan baki hakura ba' to ki fada min, dan nasa amai dani mahaifata"
Hannu tasa ta share hawaye sannan tace nahakura dada"
To ko kefa, yanzun kinga ran juma'a za'a daura miki Aure"
Gabanta taji ya fadi rasss, sakamakon jin zancen dauren aure, amman yaya zata yi indai tana son zaman lfy, dole tabi umarnin iyayenta"
*****
Kwanan su uku a asibiti suka dawo gida, Allhamdulillahi jiki yayi kyau sosai, kuma aranan abba ya sanar da ita ranan juma'a zai mata aure"
Tadade zaune agaban abba tana kuka, ganin inda take kuka ya hana ya gaya mata waye mijin nata"
*Abuja*
*Jamal* ne zaune agaban daddyn sa, gefensa momy ce, duk kansu fuskan su babu wasa, hakan ne ya tabbatar masa mgn ce me mahimmanci daddy ya kira sa akai"
Rubuce rubuce daddyn keyi akan wasu takardu, zuwa cen daddy yayi gyaran murya yace Jamal yau yaushe ?
Tuesday ya fada yana kallon fuskan daddy"
Batare daya kalleshi ba, daddy ya sake cewa toh ran Friday za'a daura maka aure"
Azabure yace Aure kuma daddy? aini nace muku bazanyi aure ba"
Bazaiyiwo ba Jamal Aure ibada ne, Allah Ta鈥檃la da ya tashi ni鈥檌mtar da bayinsa daga rahamarsa, sai ya ni鈥檌mtar dasu da Aure, domin aure daya ne daga cikin ni鈥檌momin Allah, wanda Allah ya ni鈥檌mtar dashi akan bayinsa gaba daya'
Kuma Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yace鈥� Idan bawa yayi aure, hakika ya cika rabin Addinin sa, sai yaji tsoran Allah asauran rabin,
Kuma ya kara cewa鈥� Duniya rayuwa ce mafi alkhairin rayuwar duniya mace tagari
Jamal ka duba mafi yawa daga cikin wadan da basuyi aure ba, kuma suna da ikon yin auren, zaka ga tunanin su gaba daya kan Zina yake, kuma zina tana nisantar da mutum a yanke daga imani"
Shiru Jamal yayi domin bashi da bakin mgn"
Zuwa can daddy yace..... Jamal baka ce komai ba"
Shiru yayi kaman bazaiyi mgn ba, zuwa can ya bude baki cikin fushi yace... daddy nifa raini ne bana bana so"
Murmushi daddy yayi kadan, sannan yace..... kana bani dariya Jamal, ai ba kanka aka fara ba, bakuma kanka za'a kare ba"
Shiru yayi zuwa can ya miki zuciyar shi cike da tunani kala2, babu abin da yake bashi takaici irin ace wai shine zaije yanawa yariyar daya girma karamar murya"
Muryan Abba yaji yace baka tambaye ni amaryan taka, ko kunyi mgnr da usman ne?
Cike da mamaki yace daddy usman yasanta ne?
Murmushi abba yayi, sannan yace kanwar sa ce, Asma'u
Afirgice Jamal ya daura 馃檰馃徏鈥嶁檪 tare da fadin haba daddy ya zakamin haka, sabo da Allah, daddy karasa yariyar da zaka hadani da ita sai asma'u, yariyar da bata da kunya, kuma ma ai ma ba tsarata bace, shekara ta 30 harda wani abu, ita kuma 10 da wani dan kwayoyi, haba daddy me zan da ita, inbanda ta raina ni.....
Gani daddy yayi bashi da niyar shiru kamar ma sambatu yake, dan haka ya mike sannan yace..... nidai nagaya maka, idan ka gaji da surutun ka bari"
*Kano*
Tunda ma'u ta dan saki ranta, mama take dan sakan mata fuska, dan haka yau ma'u ta mamayi mama ta dauki wayarta"
Dakinta ta shiga ta kulle ko ina, sannan ta fara shigar da no deeni"
Kaman jira ya ke ya daga tare da fadin haba asma'u
Yazaki share ni kunsan kwana nawa kinsan halin dana shiga kuwa ?
Kuka ne ya kwace cikin sauri tasa hannuta ta rufe bakinta dan gudun kar yaji kukanta"
Marairaicewa ya sakeyi yana fadin asma,u bari na kwatanta miki yadda nakeji"
Asma' na kasance tamkar kifi a cikin ruwa, idan nayi gabas sai kuma na dawo nayi yamma, idan nayi kudu, sai kuma na dawo nayi arewa"
Shiru yaji, dan haka ya sake cewa asma'u me yasa kikai shiru ?
Hannun ma'u dafe da bakinta, ta kasa cewa komai, tausayin deeni, tare da tsananin kyaunan sa takiji acikin jikin ta, hawaye da majina ne suka hade afuskanta"
Shiru yayi zuwa can ya sake cewa..... Asma'u nasan kinaji na, yau kuma wani sabon salo kika fito dashi?
Shiru ya sakeyi zuwa can yaji shirun yayi yawa, dan haka yace....
Tattausan lafazin ki nake saurare yake abin kyaunata, komai naki daban dana sauran 'yan mata, da zan kwana ina misalta kyawun halittar ki, ba zan iya kaiwa karshe ba, koda kuwa zan wanzu ina yi har karshen rayuwata"
Kasa danne kukanta tayi, cikin kukan ta bude bakinta, domin ta faranta mishi rai, tana sheshshekan kuka take cewa.....
Akwai matsala deeni"
Wani irin nufashi yake fitarwa, kasa yayi da murya sannan yace..... wacce irin matsala kuma asma'u ? bakya so nane?
Hannu tasa ta share hawaye da majinan dasuka dame afuskanta, sannan tace......
Ina sonka tamkar yadda ba zan iya bayyana maka ba, ina sonka tamkar yadda baza ka iya kirga adadin ruwan sama ba, kada ka zubar da hawayenka, yayin da wani ya bata maka rai, tuna da wacce kake so, ka ke kauna, sai zuciyarka tayi fari, ina sonka abin kaunata, na kasance a cikin matsin kasa bacci yayin da dare ya tsala, bani da komai sai tunaninka har wani lokacin gari kan waye ban iya runtsawa ba, nasan wannan yana faruwa ne saboda irin tsantsar soyayyar da nake maka, Shin ko kaima haka ne?
Karashe mgnr tayi cikin matsanancin kuka"
Dan haka hankalin deeni ya tashi, idonshi ya kankance, karkace baki yayi sannan ya bude wannan muryan tasa yace wanne d'an ta shekiyan ne ya bata miki rai har kike kuka?
Sau sauta kukan tayi sannan tace deeni ranan juma'a za,amin aure"
Diffff yayi, zuwa can yace...... Yaseeeen karya ne, Asma'u ko sama da kasa zata hade hakan bazai faru ba"
Itadai ma'u kuka kawai take"
Jitayi ya sake cewa dawa za,ayi miki auren"
Nima bansani ba amman ina zaton Jafar ne"
Kai!!! Ina, yaseeen karya ne"
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
[22:53, 12/19/2017] 鈥�+234 806 858 0203鈥�: 馃挆馃挐馃挐馃挆
鈥�*BUGUN ZUCIYA*鈥�
( 鈥婬eartbeat鈥�)
馃挀馃挐馃挆
馃挆
馃挀馃挐馃挆
鈥婤y鈥�
馃挆
鈥嬧€�*Fadeela Lamido*
*@AM拢拢NCI WRITER'S ASSOCIATION馃*
Dedicated馃憞馃徎
Faty Afreen馃拫馃こ馃徎
4鈨�1鈨o4鈨�3鈨�
馃挄馃挊馃挒馃挄鈥�
Asma'u idan kika ga na barki agidan wani to ki tabbatar bana numfashi"
Zan dauki mataki agun duk wadda ya nemi ya rabani dake, ke tawa ce danni aka halicce ki"
Nisawa yayi yana huci, yaci gaba da cewa karki yadda da duk Wanda za,abaki, dan wlh zan kashe mutun"
Shi tsohon naki bashi da anhali ne, zan batar dashi yaseeen'
Kukanta ne ya Karu, cikin kuka tace......
kayi hakuri banason abin da zai taba abba na, duk abinda ka mishi ni kamawa, kuka ta tsaya tayi sosai, deeni yana sauraran ta, zuwa can tace.......
Deeeni muhakura kawai"
Diffff, yayi zuwa can yace...... Asma'u ni kike cewa muhakura? Kin manta kalaman da kika gayamin yanzu, daman yaudarata kikeyi ?
A'a ba haka bane deeni, tunanin abbana nake, banason nasa shi awani hali, tunda ya nuna baya so, dole na hakura koda haka zai zama sanadin ajali na"
Girgiza kai deeni yayi kaman yana gabanta sannan yace........
haka kika ce ko ?, tabbas zan kashe Jafar"
Iya abin da ma'u taji kenan ta kashe wayan, tare da fashewa da kuka, acikin zuciyanta tace wlh wlh duk wadda ya aure ne ya daukan ma kasan wahala, dan bazai taba samun inda yake so ba"
Kuka tayi sosai sannan ta goge no deeni, toilet ta shiga ta wanke idonta sannan ta nufi dakin mama domin ta mayar mata da wayarta"
Tana shiga mama tace idan kin gama da wayar bani "
Bata nuna tsoro ba, cikin dakewa ta mika mata tare da cewa......
Muyi hira da zainab ne, dan mun dade bamu hadu ba"
Hmmm kawai mama tace, Sanan ta karbe wayar ta tare da fadin ga zuma nan a cup zauna ki shanye shi, ki bani cup din"
Bata kawo komai azuciyarta ba ta zauna ta dauko kofin, rabon da tasa wani abu abakinta ta dade, deba tayi ta kai bakinta, wani irin bauri taji, dan haka ta mike aguje tayi toilet"
Binta da kallo mama tayi, tanajin ta tana kwara amai, zuwa can ma'u ta fito tare da fadin mama, menene wannan kika bani ?
Zoki zauna mama ta fada tana nuna mata wajen zama"
Zuwa tayi ta zau sannan mama ta dauki cup tace bude bakin ki, wannan abun da kike gani yana da muhimmaci sosai, kuma kinsan bazan baki abinda zai cutar dake ba"
Bude baki asma'u tayi tare da rufe ido mama taita dura mata zubar abaki, bayan ta gama mama ta kalleta, sannan tace..... Yanaga idonki sun kara tasawa? asma'u kodai har yanzun jikan kakan nanan zaciyan Ki ne?
Shiru tayi, mama nabinta ta kallo zuwa can tace niba tunanin sa nake ba"
Toh tunanin me kikayi asma' u kinga yadda kika rame kuwa, kinyi wani zuro2 dake, jifa inda wuyan riganki ke fadowa"
Kallon wuyata tayi sannan tace......
Mama toh daza'a dan daga auren ne tunda yanzun banda lfy"
Hmmm asma'u kenan, ai idan ma kina tunanin za'a daga auren nan gara ki bari"
Shiru tayi zuwa can tace mama abba fah yamin alkawarin bazai min auren dole ba, kuma gashi zaimin."
Ke kikajawa kanki asma'u ban da rashi tunani meya kaiki soyayya da d'an daba, duk wadda kika ganshi awannan harkan bayajin tsoron iyayen sa, dan duk iyaye na gari bazasu so ganin dansu cikin irin wannan harka ba"
Shiru sukayi zuwa can ma'u ta kalli mama tace......
Wlh mama deeni yanada kirki, kuma inaji ajikina idan na aure shi zai bari, cikin rawan murya ta karasa dan haka mama ta bita da kallo sanan tace........
Zuciyan Ki bata gaya miki gaskiya asma'u, ki daina asaran hawayen ki"
Shiru asmau tayi bata sake cewa komai ba, saidai lokaci zuwa lokaci tana Saka hannunta ta share hawaye"
Jamal kuwa tunda tunda yaji lbrn auren shi da asma'u ya rage walwala, baya wa kowa magana sai yaita mazurai yana cicin magani"
Yau alhamis Jamal na zaune adakin sa yana aikin da ya saba wato karatun jarida"
Ji yayi ana buga kofar, saida ya hada rai sannan yace waye?
Nafisa dake tsaye abakin kofa tace... Nice"
Shiko ya fada tare da maida kanshi kan jaridan"
Shigowa tayi sumi2 harta nufi bakin gadon, ta tuna yaya Jamal baya son ahaumai gado, dan akwai Wata rana data zauna abakin godon yaita masifa, wai dan tsabar rashin kunya zata zauna mai agado, saida Momy tasa baki sannan yabar mgn, dan haka yau ta tsaya atsaye"
Yaya Jamal ina kwana"
'Dagowa yayi fuskan shi adaure ya kalleta, wanne irin iskanci ne zakizo kimin tsaye aka"
Cikin sauri ta nufi kujeran ta zauna sannan tace, daman Momy ce tace naxo na dubaka ko lfy, wai taga tun safe baka fito ba, kuma abba na kiran ka"
Toh naji, wuce kiban waje"
Jifa yayi da jaridan hannu shi sannan ya miki yabi bayanta"
Har cikin dakin daddy ya shiga, daga nesa dashi ya zauna ya mika gai suwa"
Bayan daddy ya amsa sukayi shiru na dan wani lokaci, zuwa can yace......
Jamal jibi fah daurin aure banga gana shiri ba"
Daker ya bude baki yace.......
nasani ai daddy ni babu wani abu da zanyi ne"
Toh ai ko bazaka yi komai ba Jamal ka gayawa abokan ka, ko baka son suzo maka daurin aure ?
Shiru yayi bece komai ba"
Kallon shi daddy yayi sosai yace.... Kuma gashi har yanzun bakaje gurin yariyar ba, domin kaji bukatun ta"
Cafff ya fada azuciyan shi, afili kuwa sai yace, sai dai nayi aike daddy, dan inada aiki gobe"
A'a, ai zuwa dakai yafi sako kadaure dai kaje din kaji ko"
Toh kawai yace tare da mikewa yana kokarin fita, axuciyan shi yace.....
yaya ma za'ayi nayi zaman aure da *Husna* ai ni koda anyi aure sai dai na aure wacce ta girme ni"
***
Deeni ko tunda suka gama waya da asma'u ya shiga cikin wani hali, haka kurum yaji hawaye na zubo mai, tunda yake beta neman wani abu ya rasa ba, duk abin da yake so shi ake mishi, amman yau yaga ma'u na shirin subuce mishi"
Cikin wannan halin ummi tacimai afirgice tace.....
Auta menene haka? Meya maka zafi har kake tsiyayar da hawaye?
Hannun yasa ya share hawayen sannan yace ummi zan kashe baban Asma'u, dan naga nema yake ya rabani da ita"
Kul auta na karka soma, kana son ka tura mata kiyayyan ka ne ?, mundin ka kashe babanta toh duk son da take maka juyawa zaiyi ya koma kiyayya, kuma ina gargadin ka da kadaina kuka idan Allah ya yarda zaka Aure asma'u"
Hannusa ya shafo hawayen ya kallah ummi wlh in masifar son asma'u"
.Nasani auta tun da gashi naga kana zubar da hawaye rabonda naga hawayen ka tun kana goye"
Ummi bakomai ke ta damin hankali ba, ummi sai kalman asma'u wai ta hakura dani sabo da bata son bacin ran abbanta, ummi to idan nakashe Mijin fah"
Karka kashe kowa auta idan Allah yaso dakai za,ayi"
****
Yau ta kama alhamis, dan haka baki sun fara sauka agidan su ma'u"
Tunda ma'u taga 'yan uwan sun fara zuwa hankalinta ya tashi, tunanin ta gobe iyanzun tana matsayen matar wani, ba deeni ba" kuka take son yi amman hawayen yaki zuwa, rasa inda zata saka kanta tayi"
Da misalin karfe 11:00am yaya usman ya shigo har dakin ma'u, fuskan shi daure yace ke dauko gyalen ki kisame ni amota"
Mikewa tayi cikin sauri ta fito, ganin Anty fa'iza acikin motan yasa taji sanyi"
Tunkafin ta karaso anty fa'iza ke mata murmushi, shiga tayi ta zauna, har sukai nisa babu Wanda yace uffam"
Sunyi tafiya me nisa, sannan Anty tace, asma'u lalle zamu da gyaran kai kinga gobe dauren aure ko?
Dauke kai ma'u tayi tare da matso hawaye, wani kululun abu taji ya tsaya mata awuya"
Bata sake cewa kala ba, har sukaje akayi komai aka gama, ko ruwa aka bata bata sha"
Bakaramin kyau ma'u tayi ba, lallai ne dan uban su, dan haka tai kaman ba itaba, sai dai raman da tayi yasa idonta duk ya zurzurma"
Sun kusa isa gida wayar yaya usman ta fara kara, dauka yayi ya kara akunne sannan yace ka iso ne?, OK toh kashiga ciki mana, shiru yayi zuwa can yasake cewa toh kama ka zasuyi?, tsaki yaja sannan ya kashe wayan"
Karfe 5 da wani abu suka dawo, tun kafin ta fito ta hago yaya Jamal tsaye ajikin wata mota, gani tayi kaman ya kara tsayo dauke kanta daga kallon shi tayi, aranta take cewa shikuma wannan mugun meya kawo shi" wata zuciyar tace kika sani ko an gaiya to shine idan kinyi gaddama yaci uban ki"
Batace zata jira anty ba tayi gaba abinta, koda taje gaban Jamal bata kalli inda yake ba, harta wuce Taji yaya usman na cewa ke zonan"
Juyowa tayi afirgice tazo gaban su ta tsaya"
Zakice bakiga Jamal bane koko gaidashi ne bazakiyi ba?
Ban kula dashi bane, ma'u ta fada sannan tace ina wuni?
Juyowa Jamal yayi ya kalleta, sannan ya tabe baki tare da daga hannu shi, ya mata alma wai tatafi"
Koda tashiga gidan, kowa fadi yake tayi kyau, azuciyar ma'u fadi take da kusan abinda nakeji da bazakumin mgn ba"
Zuwa can Anty ta shigo, fuskanta dauke da dariya ke kuma haka akeyi, kina ganin mijinki saiki wani dauke kai"
Dasauri ta kalli Anty sannan tace waye mijin nawa ni ba wanda nagani"
Hmmm Asma,u bayan tun muna cikin mota naga kin kalle shi"
Mikewa tsaye tayi da sauri sannan ta koma ta manne da bango, hannunta dafe da kirjinta Anty kina nufin *Jamal*? Jamal ? shi abba ya hadani dashi?
Mikewa anty tayi cikin sanyin jiki tace, daman baki sani ba?
Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, wlh bana son shi, bazan aure shiba, dana Aure shi gara na kashe kaina"
Kafin anty tayi yinkurin cewa wani abu, ma'u tafita da gudu, cikin kuka tashiga dakin mama, idonta arufe ta fada jikinta tana kuka kaman ranta zai fita tace mama dagaske wai da yaya Jamal za'amin aure ?
Kai tsaye mama tace, eh, daman abban Ki be gaya miki ba?
Bana son shi mama, wlh na tsane shi, dan Allah karku hadani dashi, mugune mama, kuma azzalumi ne"
Bakin alkalami yariga ya bushe asma'u, dama ki daina bata bakin ki"
jikin bango ta koma ta dunkule hannu tare da fadin, mama wlh idan aka hadani dashi zan kashe shi, zan kashe mama"
Batasan cewa yaya usman na dakin ba, saiji tayi yace" idan har zaki iya to ki kashe shi"
Bataji tsoro ba, dan yanzu jitake zuciyarta ta bushe, da za'aita dukanta har akasheta dataji dadi"
Dakinta ta koma ta zauna tare da zubawa guri daya ido, deeni ne ya fado mata arai, inama zabar ta ta aure deeni, dataji dadin arayuwan ta, Amman me ake da wani jamal, tsaki taja sannan tace afili , wlh idan har akayi kukkuren yimin Aure da jamal dagani harshi haka zamu kare rayuwan mu cikin bakin ciki"
Tana cikin wannan tunanin taji ana kiran sallahn mangariba, mikewa tayi ta dauko dogon hijjabi har kasa ta saka"
Lekawa falo tayi taga babu kowa duk sun shiga sallah, dan haka tacire ta kalminta tarike ahannu sadaf2 ta fice agidan"
Gidan su deeni ta nufa tana tafe tana waige, harta isa gidan, akofar gidan ta tsaya ta kurawa dutsen da tasaba ganin deeni akai ido, hawaye taji yana zubo mata, ahaka ta shiga gidan, deeni na zaune atsakar gida ya zuba uban tagumi"
Tsugunawa tayi agaban shi, ahankali ya dago ya kalleta"
Mamaki baiyane afuskasa yace asma'u kece?
Cikin kuka tace nice deeni"
Yaya akayi kika fito da daddarenan ina nan ina shirya kayan yakin da zan fito dasu gobe, ina tabbatar miki gobe babu tsoho babu Yaro shara ne kawai"
Hannu tasa ta rufe mai baki sannan tace, bazaka iyaba deeni, kasan dawa za'amin aure ?
Gargiza kai yayi tare da kura mata ido"
Jamal, tafada tana share hawaye"
Wata irin muguwar dariya yayi sannan yace, jamal"?
Eh Jamal, ka kwatar da hankalin ka, bazan taba zama da jamal ba, na yake shawara adaren da aka kaini aranan zan kasheshi, karkace zaka dauki wani bataki, ka bari harsai nakasa"
A'a asma'u bazaki iya ba, insha Allahu bazakije kidan saba, ke macece bawani karfi gareki ba, ni kuma *na dad'e ina dama furata bazan so wani ya shanye min ba,* abin da yafi kawai kije gida da asuba kisan yadda zakiyi ki fito zanzo na daukeki mugudu"
Shiru tayi zuwa can tace......
Deeni wacce fura ce wannan?
Kau da idon shi yaye gafe, tare da fadin bazaki gane ba"
Cikin sauri tace nagane deeni, ummi na nan ne ?
Daker iya cewa taje anso min magani"
Shiru ta sake yi zuwa can ta kalle shi tace toh me zai hana kashanye furan taka yanzun"馃檰馃徏
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
[22:54, 12/19/2017] 鈥�+234 806 858 0203鈥�: 馃挆馃挐馃挐馃挆
鈥�*BUGUN ZUCIYA*鈥�
( 鈥婬eartbeat鈥�)
馃挀馃挐馃挆
馃挆
馃挀馃挐馃挆
鈥婤y鈥�
馃挆
鈥嬧€�*Fadeela Lamido*
*@AM拢拢NCI WRITER'S ASSOCIATION馃*
鈥�
Dedicated馃憞馃徎
*Firdausi Sodangi*馃拫
4鈨�4鈨o4鈨�6鈨�
馃殧馃殧馃殧
Da saurin shi ya mika hannun shi kan kafadan ta, ido ya zoba mata, itama kallon shi take cikin ido"
Sun kwashi tsoyon lokaci ahaka, zuwa can ya sake shigota"
Asma'u nasha kika ce?
Kai ta gyada masa sannan tace indai hakan zaisa ka yadda dani.....
Bata gama rufe baki ba, ya rarumo bakinta, sunbatan ta yake kaman zai cinye ta"
Sun dauki tsayon lokaci haka, deeni duk ya fita ahaiyacin shi"
Acikin wannan hali ummi ta riske su, babu abin da take ban da salati"
Cikin sauri ma'u taja jikinta, deeni ko ya kasa sakinta sai kara binta yake yana rokota"
Hannu ummi tasa ta rike ma'u, tare da fadin ke asma'u meya fito dake da tsohon daren nan"
Ma'u bata iya cewa komai ba, kanta ta sunkuyar akasa"
Kanta ta maida kan deeni daya rike hannun ma'u daya da kyau"
Ta dade tana kallon cikin idon shi sannan tace, auta haka mukayi dakai"
Jan ma'u ya fara, yana kokarin shiga dakinsa da ita, batare dayace wa ummi komai ba"
Dan haka ummi tabi su, fadin take kai auta kana hauka be?, saketa mana"
Ummi ina zuwa mana, akwai sakon da zan bata"
Runtse ido tayi tana fadin bana so auta, kasake yariyan muta ne, ta wuce gida karka jawo mana abin mgn"
Daramm gaban ma'u ya fadi, muryan Abba taji yana mata Yawo aka, lokacin da yake cewa.... da kijwo mana abin mgn gara namiki aure, cikin sauri ta zame hannunta ta fara kokarin tafiya"
Binta deeni yayi ya sake jawo hannun ta, sannan ya matsa daf da ita, hannu yasa aljihu ya ciro wata yar karamar wuka acikin dan gidanta, ya mika mata, cikin rada yace ki rike wannan koda anyi nasaran kaiki gidan wannan danta shegiyan, inason ta zama filonki, ma'ana akarkashin filonki, kara cije baki yayi, ya dage shi sama, sannan yace, daya neme karban wani abu awajen ki, ki kaddamar mass"
Kuma kisan yadda zakiyi kifito daga gidan tun kafin akiran asuba"
Idan ban ganki ba zansan baki zamu daman fitowa bane, kuma washeri za'a daura miki aure, idan haka ta faru Asma'u, banason ki wuce kwana 3 banji lbrn mutuwan Jamal ba, idan kuma kin kasa kina da no zamuyi waya"
Kuskus sukai mgnr dan haka babu mejinsu"
Ummi ce tarako asma,u, tame cigaba da mata fadan ditowa da daddare"
Tana isa kofar gidan ta cire takalminta ta rike ahannu, bakinta dauke da addu,ai"
Allah ya tai make ta me gadin benan, hakane ya bata daman shiga gidan cikin sauki"
Harta shiga bayi tai wanka ta fito tai sallah babu wadda ya nemeta"
Dan haka tai zaune ta fara aikin nata wato kuka"
Hayaniyan mutane taketaji cikin raha suna wasa da dariya, azuiyarta tace dafa haka kawai ne da yanzun ina cikin su ina kasan dariya"
Zuwa can tafarajin ana cewa wai ina amaryan ne ya kamata asata alallai dare nayi"
Cikin sauri ta juya ta haye gado ta kudunne kanta"
Wata kanwar mama ce ta shigo ta yaye bargon ta fesheta da turare, sannan ta rangada guda"
Ba ma'u kadai cikinta ya karta ba harda na jamal, jin wannan gud'a ya tabbatar mai auren nan babu fashi"
Dare ya tsala kowa yayi shirin bacci amman banda ma'u, zau ne tayi ta rafka uban dagumi"
Da misalin karfe 4:30am ta fara jin wani dan siririn fito, haka ya tabbatar mata deeni ne, dan haka tafara kokari meman yadda zatayi ta fice"
Waigawa tayi ta kalli Anty fa'iza dake kwance akan gadonta, tare da yariyar kanwar mama Khadija, bacci su suke kashir ban, dan haka ta mike, daman hijjabin ta, na jikinta ahankali ta bude kofofin tayi waje, a harabaan gidan taji gabanta na faduwa dalilin tunawa datayi, ai get din kwado ake samishi yanzun yaya kenan?, dan dakatawa tayi, zuwa can Wata zuciyar tace mata maza kisan duk yadda zakiyi kibar gidan nan, idan ba haka ba gobe Aure za,amiki da jamal"
Guiwanta taji ya kara kwari dan tana ganin duk duniya babu wadda yakaita tsanan jamal"
Karasawa tayi bakin get din, abin da yayi matukar bata mamaki, abude gidan yake, ahankali ta bude karamar kofan ta fita"
Cikin Sauri deeni ya karasu ya riketa da duk hannun wanshi guda biyu ido ya zuba mata zuwa can yace muje ko?
Jikinta taji yayi sanyi ko wani hali Abba da mama zasu shiga idan suka wayi gari basu ganta ba, amman kuma bazata iya tsayawa ba, haka kurum ahadata da Jamal, dan haka ta gyada masa kai, tafiya suka fara amman ma'u saitaji kaman anfito daga cikin gidan"
Waigawa tayi ta kalli get din, bataga komai ba, saboda duhu, dan haka ta juya sukaci haba da tafiya"
Sunyi kaman taku 5 sukaga andallare su da filan mota mai tsananin haske"
Gaba dayan su suka juya, ganin Abba tsaye abun yayi matukar razanata ahankali ta zame kasa tare da daura hannuwan ta aka, tana fadi na shiga uku na"
Deeni ko fadi yake tashi muje asma,u karki yadda suyi nasara akan mu bazan iya rayuwa babu ke ba, kinsa ni ina tsananin sonki"
Karasuwa Abba yayi cikin tsananin tashin hankali yace"
Asma'u tashi Ki bishi, ai bansan cewa ni ban isa dake ba sai yau, dan haka bazan hanaki Ki bishi ba, amman kisani idan kika Saka kafa kika wuce nan wajen Allah ya isa takanina dake, sai yanzun nake dana sanin saka miki sunan mahaifiyata danayi, baki cancanci sunan nan ba"
Deeni ne ya karkace baki shi sama sanan yace toh saika goge sunan, maza sa ruwa ka goge sunan sunan tsuhuwar taka"
Zare ido ma'u tayi abba ko kokarin karasawa gaban deeni yake, saida yaje dafda shi sannan ya bigi karjin deeni tare da fadin zakamin rashin kunya ne ai daman na sani kai d'in fitsararre ne"
Murmushi deeni yayi sannan ya kalli ma'u yace tashi muje"
Kuje Abba ya fada yana nunawa ma'u hanya tare da fadin tarihi ne zai maimaita kan shi, kallon deeni yayi cikin ido, sannan ya cigaba da cewa haka ubanka yayi Wa uwarka"
Dan zaro ido deeni yayi tare da zuba su akan abba"
Dan haka Abba yace, eh kaje ka tambayi uwarka saratu, ta gaya maka yadda tayi ta zame ka"
Runtse ido deeni yayi tare da dunkule hannuwa"
Abba ko juyawa yayi ya nufi gida, yana kaiwa saitin motan yace"
Jamal sakko ka rufemin gidana"
Ganin haka yasa ma'u ta mike tabi bayan abba aguje yana Saka kafa acikin gidan tana saka tata, kafafuwan shi ta rike tana kuka take fadin Abba ka yafe min"
Hannu Yasa ya begeta tare da fadin na tsane Ki asma'u kin siremi, kwata2 Allah yacire min ke azuciya ta, tashi ki bani guri bana son ganin ki"
Yana mgnr ne hannun shi dafe da kirjin shi"
Muryan Jamal taji yana cewa, yi hakuri abba, ka yafe mata"
Jamal baka ganin inda take neman tozarta ni bataga darajata ba bare da tausaya min, duk irin adalcin dana mata arayuwa, wlh 'ya'ya mata fitina ne, sun azaftar dani"
Cikin sanyin jiki Jamal yace abba hakuri zaka yi jarabawa ce"
Juyawa Abba yayi ya shige gida batare da yace komai ba"
Dan haka Jamal ya juya ya kalli ma'u yace"
Ke kuma tashi kiban guri tunkafin na hadaki da bango"
Bata bari ya rufe baki ba, tamiki da sauri ta shige gida".
*****
Deeni tsayawa yayi kaman gunki, mgnr abba ce ke mishi yawo akai, *kaje ka tambayi uwarka saratu, ta gaya maka yadda tayi ta same ka*"
Jijiyon kan shi ne suka fito rudu rudu, idon shi yayi jawur kaman gar washi, acikin wannan halin ya isa gida, lokacin anfara kiran assalatu"
A kitchen yaji motsin ummi dan haka ya manne ajikin bango"
Besan abun da zaiyi ba damuwan ta mishi yawa, zuwa can ummi ta fito dauke da butu ahannun ta"
Ganin deeni tsaye jikin kofa yasa ta fadin Auta menene haka? Karka yadda son asma'u yasa ka zama rago, dan naga yana shirin zauta ka"
Ummi inason nasan yadda kikayi kika same ni"
Dafa kirji ummi tayi tare da fadin kaman ya?, ban gane ba?
Ummi inason nasani wanene ubana, kuma yaya akayi aka same ni?
Ajiye butan ummi tayi, cikin faduwan gaba ta matsa daf dashi tace"
Auta wani yace maka baka da baba ne?, ai kai kasan uban ka, ahannun shi ka taso"
Kara kankance wa idon deeni yayi, tare da fadin ummi ki fadamin kawai, kar kice zaki boye min wani abu, nafara mugun tunani akan ki, mahaifin asma'u yace nazo na tambaye ki yadda kikayi kika same in"
Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, zamewa tayi ta zauna akasa duk da cewa garin akwai sanyi amman ummi zafi takeji"
Idon ummi gulu2 tace auta tashi muyi sallan saina kaya maka"
Bazanyi ba yaseeen, idan kikaga nabar nan nasan matsaya ta"
Binshi da kallo ummi tayi, tare dajin nadaama irin wacce bata taba ji ba"
Tana matsanancin kuka tace"
Auta akwai kuskuren babban Dana ai kata abaya"
Nakasan ce ni daya iyayrna suka haifa, dan Haka na tashi cikin gata, duk da cewa iyayena bawani karfi garesu ba"
Mahaifina yana kokarin bani tarbiya daidai gwargwado harnakai munzalin Aure"
Dan haka yamin baiko da yakubu Dan kanin sa, ana saura wata 2 aurena da ya kubu, wani bakon matashin saurayi ya sauka agidan mu"
Ina daki naji baba na ya shigo dashi yana cewa ummata ga boko nan munyi, matafiye ne, yana neman masauki daga garin baguma can wani kyauye kafin akai Niger"
Da hannu 2 mahaifiyata ta karbe shi"
Baya Wata 1 shakuwa me karfi ta shiga tsakani na dashi, har takai idan yakubu yazu banason zuwa wajen shi"
Dan haka yakubu ya farajin haushin bashir"
Dahaka soyya me karfi ta kama mu nida bashir wato mahaifin ka"
Shirye shiryen baki naga anatayi agidan mu, dan kaha naje nasamu baba, nace mishi nifah yanzun bashir nake so"
Nuna min yayi baxai yuyo ba, dan yariga yaba yakubu ni, tun ina karama, sannan yakara da cewa ban da abinki saratu, shi bashir ina mukasan asalin shi, bako ne fah?
Haka na dage nifa bashir nake so, har ana saura kwana 3 ban daina cewa inason bashir ba"
Bashirma kullum kara huremin kunne yake tare damin wasu abubuwa wadda basu dace ba, ana jibi bikina mahaifina yazo ya samemu cikin irin wannan hali, ranshi ya baci sosai dan haka ya kori bashir"
Nikuma yayi fushi dani"
Da misalin karfe 8:00 na daren ranan maman yakubu ta shigo da gudu tace ga yakubu can duk an yanke shi"
Dan haka duk suka bita aka barni ni kaidai agidan"
Bayan fitan su babu dadewa bashir ya shigo arude hado kayan ki muje"
Bayiwa bashir musuba na hada kayana nabi bashi"
Wanan tafiya tawa ita ta haddasar da halin da mike ciki ayanzun"
Natafi batare da sanin halin da iyena zasu shiga ba"
Bayan mun isa garin baguma tun kafin mu isa gidan su bashir, nafara ganin al'dar su tasha babban da tamu, kusan kowa ka gani da makami ahannun shi, muna isa kofar gidan bashir yaja ya tsaya tare da kallo na, sannan yace"
Idan muka shiga gida zance ke matata ce, dan haka duk irin tanbayan da za'a miki kar bari musaba baki"
Bayan mun shiga gidan sun karbeni hannu biyu, koda suka tanbaye shi ni, cewa yayi matar sa ce ni"
Daki aka bamu ni da bashir, cikin kankanin lokaci Akasamu cikin ka"馃槶
Sai alokacin nafara tunanin halin da iyaye na suke ciki, amman bashir akulum lallashi na yake, tare da bani duk wani abu da nake so"
Dan haka na acire Kowa azuciyata naci gaba da zama harna haife ka"
Sosai Bashir da mahaifin sa suke nuna maka kyauna basu barin kowa ya dake ka, koda nikai nace"
Tun kana dan shekara goma kakanka ke tafiya farauta dakai, bashir ko akulum cikin koya maka fada yake, dan haka na matsa asaka amakaranta, bayan ka fara zuwa makaranta saina kula bakason karatu ko kaje makarantar ma, daga ace kayi fada da wannan, sai ace kayi da wancan"
Idan ankawo karanka gida kuwa, bashir dariya yake tare da cewa, shi yasan danshi jarumi ne, idan kuna iyawa kuje kurama ma dan Ku"
Komai girman Mutun baya kada ka afada, idai da wuka ne saidai ayanke juna, akarshe kuma kaine me nasara"
Duk abinda kayi daidai ne awajan bashir, nikaina bani da bakin mgn"
Har zuwa lokacin da kacika shekara 25, lokacin ne duk ka addabi mutanen garin"
Nasan yana nan a idon ka, baka manta ba, kuma alukacin ne aka nemin baban ka aka rasa, wanda hakan yayi sanadiyan dawowan mu nan"
Kuka deeni Yake sosai, take yaji ya tsani ummi, yana kukan yake fadin gsky kuncuce ni Ashe duk abinda ya faru dani kune sila, ku kuka jefani cikin halin da nake ciki, Ashe shiyasa danaje daukan Asma'u mu gudu abbanta yace tarihi zai maimaita kanshi?
Tuni idon ummi suka kankance saboda tsabar kuka, auta karka sake ka raba asma'u da gidan iyayenta, dan shine abun daya zama min babban kuskure arayuwa ta, naiwa iyayena laifi babba, lokacin dana dawo na neme gafaran su, akace min shekaran su 2 da rasuwa, sai filin gidan gashi kana gani, da hannuta take nunamai tsakar gidan da suke zaune aciki, tare da kara rushewa da kuka"
Shima deeni kai ya hade da guiwa yayi kuka me isar Sa"
Rawan sanyi ummi ta fara deeni na kallo amman saboda tsabar jin zafita daya ke, yaki kulata"
Zuwacan ya miki tsaye ya daga kanshi kasama tare da karkace baki, dan ya riga ya zaman mai jiki, guri daya ya kurawa ido sannan yace"
Na rantse da sarkin dake busan numfashi saina auri Asma'u, babu uban da zambarwa, inanan inakan bakata, ko ana muxuru ana shaho saita dawo gareni"
****
Ma'u ko sanda ta shiga gida samu tayi kowa yana tsaye duk suntashi, kallonta kowa keyi dan haka ta gane sunji abin da yake faruwa"
Koda ta shiga daki babu wadda ya biyuta, har misalin 12 na rana tana kwance"
Haniyan mutanen da taji ya kara yawa haka ya tabbatar mata zancen auren nanan babu fashi"
Zuwa can ta farajin karan motoci, mikewa tayi ta kama labulen window ta leka"
Manyan mutane taga suna futowa mahaifin Jamal kawai ta shaida"
Komawa tayi ta zauna ta daura tagumi, zuwacan ta sakejin wasu motocin nashigowa tare da hayaniya"
Agogo ta kallah 2:30pm arikice ta miki afili tace yanzun dan Allah har 2 tayi, nashiga uku na"
Gaban window ta tafi ta leka, Sojoji ne gungu2 hannun su rike da manyan bindigogi, wurin yacika makil da jama'a daga can ta hango Jamal sanye cikin shadda fara karrr, atsakiyan abukan shi yake, kowanne fuskan shi dauke da murmushi amman tashi kamar amai mutuwa"
Bakin gadon ta koma ta zauna, zuwa can taji maruki na fadin Alhamdulillahi andaura auren *Jamaludeeni* da *Asma'u*
Jitayi kaman ansoka mata kibiya akirji, hawaye taso matsowa Amman sunki zobuwa, gefen gadon ta koma ta makure"
Zuwa can taji anbude kofar ahankali ta dago kanta, momyn yaya usman ce, hannuta rike da kaya, abakin gadon ta ajiye kayan, sannan ta shiga toilet, zuwa can ta fito tace to taso maza yamma nayi"
Kaman za'a kamata haka take tafiya' bayan tayi wanka ta fito momy ta mika mata kayan ta sanya zuruf suka shige, saboda tsabar raman da tayi"
Komawa tayi ta zauna, tana haki, gyale momy ta yafa mata sannan tace tashi muje ke kadai ake jira"
Wayyo momy馃檰馃徏 wlh nagaji, waida zan dan huta ne"
Me kika yi? Maza taso muje"
Haka taitabin bayan Momy kaman me koyon tafiya, har suka isa falon Abba"
Zaunar da ita tayi sanna itama ta zauna tace toh Alhaji ga Asma'u nakawota tayi sallama, tare da neman gafarar ka zamu rakata dakin mijinta"
Dauke kai abba yayi can gefe sannan yace kuje kawai Amina"
Mutumin dake gefesa ne yace a,a bazayi haka ba, ya kamata kace wani abu"
Kwantawa Abba yayi ajikin kujera ya rufe ido, dan haka mutumin yajuya ya kalli Asma'u
Yace barin ara bakinsa naci masa albasa, Allah yasa kije asa'a kinji ko?, Allah ya miki Albarka"
Kuma Dan Allah kiyiwa mijinki biyayya, yi nayi bari na bari"
Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yace"
Da zan umarci wani da ya yi wa wani sujada, da na umarci mace tayima mujinta sujada"
Manzon Allah ya kara cewa"
Baya halatta ga matar aure tayi azumi kuma mujinta bayayi, face sai da izininsa, ba tada ikon zartar da wani Abu sai da izinin sa"
Haka yaita mata nasiha amman agurin ma'u shiga yake yana fita domin ku fadi take azuciyata, Allah ya kyauta nawa Jamal biyayya"
Har akasata amota kuka take, tare da kankame karamar jakanta ahannu"
Ahaka suka nufi Abuja, gabanta na dukan uku uku, tare da addu,a insha Allahu jibi iwar haka zata sake biyo wannan hanyan"
*Abuja*
Sun shigo karfe tara da rabi na dare kai tsaye gidan Jamal suka nufa"
Agaban wani tankasheshen gida sukaga drive ya tsaya, gida ne me dan karan kyau get din aka bude musu dan haka drive yasaka hancin motan cikin gidan, tun acikin mayafi ma'u ta hango haske kaman rana, ahankali ta dan daga gyalen ta tana kallon Gidan, amma me? Wasu sojoji tahango sunfi 10 suna shawagi haraban agidan tare da manyan bindigogi, kuma da alma agidan suke, cikinta taji ya karta, cikin sauri ta rike momy tare da fadi Momy wadannan agidan suke?
Kallo momy tabi gurin da ma'u take kallo dashi sannan tace"
Eh masu gadi ne?
Innalillahi wa inna laihir raju,un nashiga uku na"
Momy na kokarin lallashin ma'u wayarta tai kara, dauka tayi tasa akunneta batace komai ba ta cire wayar akunneta ta mikawa ma'u tanacewa ansa Jamal zaiyi mgn dake"
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
[20:21, 12/14/2017] +234 813 679 9888: 💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
4⃣7⃣ to 5⃣0⃣
🐕🐕🐕
Amsa wayar tayi badan ranta yaso ba, daga cikin wayar taji muryan Jamal yana cewa"
Kafin ki shiga gidana ki ajiye Duk wani iskanci naki, akofar gida, karki shigan min dashi gida, dan bazan dauki rashin kunyar ki ba,"
Bejara mezata ce ba ya kashe wayar"
Guntun tsaki ma'u taja sannan ta mikawa momy wayarta, sake gyara mata gyale Momy tayi, sannan taja hannunta suka shi cikin Gidan, tare da ayarin mutanen da sukazo dasu"
Suna shiga falon tasa hannunta ta bude idonta, dan ita bataga dalilin daza'a rufe mata ido ba"
Idonta kiri kiri take kallon gidan, eh Gidan ya had'u kuma anzuba kayan daya dace aciki, amman ita basu bane agabanta, Allah ya sani tana masifar son deeni"
Haka nan taji damuwan ta ya ragu sosai, dan haka ta shiga cikin su Anty fa'iza da Khadija da suke hira adakin daya ke matsayin dakin baccin ma,u"
Su uku ne kadai adakin, manya suna falo suna kallo, dan haka anty fa'iza tayi amfani da daman tana bata shawara"
Asma'u kinga jamal yana da kirki sosai, dan Allah ki bishi sauda kafa, ku zauna lfy, kuma ki guje duk abinda baya so"
Toh kawai asma'u take cewa, Ganin haka Anty fa'iza ta ciro wani littafi ajakarta ta mika mata"
Ranan kusan kwanan zaune sukayi, sunsha fira ammam hirar tafi karkata tsakanin Anty da khadija"
Washegari suka tashi da shirin komawa gida dan haka hankalin ma'u ya tashi "
Damisalin karfe 2 na rana suka fito domin kai asma'u gida momyn Jamal, su kuma su wuce gida"
Motoci aka kawo wadatattu"
Bayan sun isa a gaban momy suka ajeta"
.
Momy da yau ne ganin ma'u nafarko, ta taso da sauri ta kamata, kan cinyan ta, tasata tare da leka fuskan ma'u"
Masha Allah, ta fada afili, sannan taci gaba da cewa Allah ya zaunar daku lfy"
Daga nan su Momy suka yi sallama suka fice da nufin daddare Jamal zai mayar da ma'u
Tun da suka fita ma'u najikin momy tana kuka, Nafisa ko na zaune agefe fuskan ta dauke da dariya"
Bakomai ke bata dariyan ba kuwa illa, tunawa da tayi yaya Jamal baya son ahau gadon sa, kuma yau gashi da mata"
Har gurin karfe Goma, ma'u na gidan Momy, tana jaran Jamal har bacci ya fara deeban ta"
Ganin ma'u na bacci Momy ta shiga kiran jamal awaya yana dauka tace"
Jamal kana ina ?
Ina gida mana momy"
Gida ? toh ina Asma'un ?
Cike da kwarin guiwa yace gata akusa dani"
Mamaki ne, ya kama momy, juyawa tayi ta kalli inda ma'u ke kwance sannan ta maida hankalin ta cikin wayar tare da fadin, kaniyar ka Jamal, abinda zakayi kenan?
Me kuma nayi momy?
Takaici ne ya kama momy harta rasa abin cewa, zuwa can tace kazo yanzun nan inason ganin ka"
Cikin kankanin lokaci ya iso kai tsaye dakin momy ya shiga"
Yan mata guda 2 ya gani suna bacci dan haka ya bisu sa Ido, ya shaida nafisa amman dayar ya kasa tantaceta"
Damamaki yace momy wacce wacece ?
Uwarka ce, waikai sai yaushe zakai hankali, kirikiri ince maka ina Asma'u kace min wai gata, bayan tun da 'yan uwata zasu tafi suka kawo ta, toh inason insan abin da kake nufi?
Jikin shi asanyaye yace toh momy Allah ya huci zuciyar ki"
Mikewa momy tayi tana kokarin fita adakin take fadin, gatanan ta riga tayi bacci, sai kasan yadda zakayi, ficewa tayi abinta"
Bin bayan momy yayi da kallo sannan ya juya ya kalli inda ma'u ke kwance ahankali ya matsa gurin cikin siririyar muryan shi yace ke, *Husna*, Husna, ganin ya kirata su biyu bata tashi ba, yasa ya tsaya yana tunanin yadda zaiyi"
Zuwa can ya matsa kusa da nafisa, hannu yasa yadan dake kafanta nan danan ta mike, sannan yace zoki tasa min Husna"
Da saurinta ta taso, tana tashin asma'u, tashi tayi ta zauna tana mutsutsu ke ido"
Lallan hannunta yabi da kallo, har ya kasa dauke idon sa ahankali yace tashi muje"
Kuka ma'u ta fara tare da fadin nidai aban ni anan dan Allah"
Harga Allah tabashi tausayi amman saiya mika hannu yana fadin zo muje dare yayi fah"
Ganin bata da niyar tashi, yasa ya fita, afalo ya samu Momy dan haka yace,
Momy taki zowa fah"
Harara momy tamai sannan ta nufi dakin zuwa cen ta fito rike da ma'u, kuka take sosai momy na lallashin ta, kiyi hakuri kinji idan ankwana biyu zanzo, in duba ki, idan naga bakijin dadi zaman sai kudawo nan, bayan momy ta zaunar da asma'u amota ta juya ta kalli Jamal tace kaikuma kaji tsoron Allah"
Suna isa gida ta bude motan da sauka, shima saukowa yayi, Amman sai taga ya nufi wani bangare daban, ido kawai ta zuba mai acikin zuciyanta tace yana nufin ni kadai zan kwana awancen part din"
Ahakali ta fara takawa harta shiga ciki, agogo ta kalla taga karfe goma sha biyu"
Tagume tayi, tare da tausayin kanta, karamar jakanta ta dauka ta Bude' ahakali ta jawo sarkan deeni, kura mata ido tayi, hawaye taji yana sakko mata na takaice, rungume sarkan tayi tare da tunani yau wane hali deeeni zai shi?
Ahaka ma'u ta kwana rungume da sarkan deeeni lolaci2 tana sunbatar ta"
Washegari kuwa ko kyalin Jamal bata ganin ba, haka ta kwashe sati biyu bataga Jamal ba" dan haka tunanin ta ya fara canjawa, gashi babu waya ahannuta bare ta kira deeni taji wani wani hali yake ciki"
Kara ramewa tayi tai baki, tai zuro2 da ita, domin babu me matsa mata data ci abinci, sai dai intaji cikinta na kugi ta shiga kitchen ta girka"
*****
Yauma kamar kullum tana zaune afalo taji ana kokarin bode kofar"
Kofar tabi da kallo Jamal ta gani ya kara wani haske tare da murjewan fata"
Zama yayi akujeran dake kallon tata, ya kura mata ido"
Zuwa can yace *Husna* babu ko gaisuwa?
Shiru tayi tana kallon gefe, domin idan taganshi jitake kama ta kashe shi"
Husna ina mgn kin min shiru"
Shirun dai ta sakeyi ganin haka ya mike tare da fadin haryanzun dai baki gama yin taushi ba"
Ganin yana shirin ficewa yasa ta mike tana binshi abaya"
Ja yayi ya tsaya tare da fadin ina zaki?
Cikin kuka tace ni wlh nagaji nagaji da zama anan"
Idon ya zuba mata tare da jin tausayin ta axuciyan shi"
Idon shi akan karjin ta yace, toh yanzun yaya za'ayi kenan"
Sunkuyar da kai tayi tare da wasa da hannuta"
Inajinki menene matsalan"
Ni gaskiya bana son gidan nan"
Shiru yayi ya zuba mata ido, zuwa can yace, zanso kiso gidan nan Husna, garama Ki cire kinsa azuciyar ki, dan ko zaki fita gidan nan toh bayanzun ba"
Kara matso wasu hawayen tayi, dan haka Jamal ya tsinta kanshi da kasa tafiya"
Tsayawa yayi ya tsare ta da ido, harta tsargu da kallon da yake mata"
Zuwa can yace Husna kukan me kike yi?
Uffam batace ba, hawaye ne kawai ke zuba kaman anbude famfu"
Ahankali ya sake kiran sunanta, dago jajayen idonta tayi ta kalle shi tare dajan majina"
Inason ki gaya min abin da yake damun ki, banason yawan koke koke, ke kuma naga dabi'arki kenan, ki gayamin meke damun Ki,
kidauka da usman kike mgn, dan nida usman bamu da banbanci, na amince da aureki ne dan na gyara miki zama, bawai dan zan iya rayuwar Aure dake ba, danni kinmin kankanta, kina fara hankali zan sallame ki, dan haka ki natsu zaman ki agidan nan na wani dan lokaci ne"
Har ga Allah taji dadin mgnr shi, dan haka tasa hannu ta fara share hawaye"
Dariya taso ba Jamal amman sai ya dake tare da juyawa ya fice"
Kan kujara ma'u ta koma ta zauna, tare da tunanin hanyar da zata billowa Jamal bataso ace har yanzun tana garin nan ba, kuma yanzu dataji kalaman Jamal tafara canza shawara, ayanzun deeni ne kawai zai iya nemo masu mafuta, dan haka ta fara neman inda zata samu waya"
Acikin zuciyanta tace wannan wata irin rayuwa ce, duk abi antsane ni, kowa baya sona, idan ba deeni ba babu me nunamin kulawa"
Haka ta wuni tana tunani tare da zubar da hawaye"
Tunda Jamal ya fita be sake shigowa ba har washegari"
Damisalin karfe tara, tana kwance adakinta taji ana sallama afalo"
Mikewa tayi, jiki babu kwari ta fito, Momy tagani ita da nafisa, dan haka ta fara murmushi batare datasa sanda ya fitoba"
Cikin sauri momy ta taho ta rike Asma'u, tajata kan kujera tare da mannata ajikinta"
Duku da kanta tayi saitin na ma'u, gani tayi hawaye na zobowa a idon ta, hannu tasa ta fara share mata, sannan ta dagota tace"
Asma'u me yake faruwa?, wani abu na damunki ne?
Kukane ya kwace ma asma'u harda shashsheka, dan haka jikin momy yayi sanyi, waya ta daga ta kira Jamal, cikin kankanin lokaci ya iso"
Har lokacin asma'u kuka take, dan haka ya tsaya ya tsareta da ido"
Momy ma kallo ta bishi dashi, sannan tace, Jamal me yasa kake haka, dan Allah ka duba yariyar nan sati 2 kawai ji inda ta dawo?
Momy to ai itace taki kwantar da hankalinta, kulum bata da aiki sai kuka, ni nagaji da koke2 haushi ma take ban"
Jamal da kaga tana kukan ka tambayeta abinda yake damunta?
Ai ni bata min mgn"
Shiru momy tayi zuwa can tace, Jamal haka ake aure?, dahar zaka kalli tsabar idona kacemin wai batamaka mgn"
Jamal bece komai ba, shiru falon yayi nadan wani lokaci, zuwa can momy ta sake cewa"
Toh shikenan tunda abi haka ne, zantafi da ita gida, ku zauna abangaran ka"
Dago kai Jamal yayi tare da fadin, a'a momy, daddy ma yace haka, amman nacemai ni nafison na zauna anan"
Aiko daddyn naka idan yaga yadda yariyar nan ta fige bazai yadda da zaman ku anan ba, domin alamu sun nuna baka kula da ita, dan wannan kukan da take yi inda kana kula da ita bazata yishi ba"
Juyawa momy tayi, kalli nafisa sannan tace Nafisa hadu mata kayanta"
Shiru Jamal yayi yana karabin ma'u da kallo, aranshi beson su koma gida dan kwai abubuwa da dama daya shirya"
Ma'u na jikin momy har suka bar gidan"
Bayan sun isa gida haka momy taitajan ma'u ajikinta harta fara sakin jikinta"
Damisalin karfe 7:30 na dare ma'u ta samu daman karban wayan nafisa, tashi tayi ta shige toilet"
Shigar da no deeni tayi, cikin kankanin kokaci ya dauka tare da fadin Asma'u ? meyasa zakimin haka?
Ajiyan zuciya tayi sannan tace deeni ? Yaya akayi kasan nice?
Ajikina naji, asma'u nashiga cikin wani hali, ina tsananin bukatan ki akusa dani, Asma'u bani da gata, bani da kowa saike, me kikeyi har yanzun baki dawo ba?
Cikin kuka tace na kasa, deeni bansan yadda zanyi ba"
Shima hawaye ya share sannan yace Allah yasa baki bari ya shanyemin Furata ba"
Kukan ma'u karuwa yayi, cikin muryanta da ta kasa fita sabo da kuka tace"
A'a naka ne kai kadai, Yaya Jamal be isa yashata ba, dan yafi karfin sa"
Ajiyan zuciya ya sauke, sannan yace kin tabbata?
Eh ta fada cike da karfin guiwa"
Shiru sukayi na wani lokaci, zuwa can, yace awacce uguwa kuke?
Bansan sunan unguwan ba deeni, tunda nazo ko kofar gida ban fitaba, nan ta kwashe duk yadda sukayi da Jamal ta fadawa deeni"
Shuru yayi, zuwa can yace, Asma'u karki yadda da duk abinda Jamal zaice miki, karya yake, yana sonki, wlh muna fuki ne, nafahimci sonki yake, tun lokacin dayazo har gida shi da mutanen sa suka tafi dani, yace ki natsu ne dan ya samu hanyar da zai cusa miki soyayyar shi, bawani rabuwa da zaiyi dake karya yake yi"
Hawaye ma'u ta share sannan tace toh yanzun yaya za,ayi?
Karki sake kimai biyayya, duk abin da kika lura baya so shi zakiyi, karkiji tsoron sa ko kadan, na kula dan zafin kai ne, inaga yin hakan zai tunzura shi ya sake ki, sannan kiyi kokari ki binciko min sunan unguwan, tare da no wayar Jamal"
Amsawa tayi cike da kwarin guiwa, dahaka ta kashe wayar badan tagaji dajin muryan deeni ba"
Wanke fuskanta tayi sannan ta fito, babuwa adakin dan haka ta nufi falo"
Fuskan momy dauke da murmushi take kallon ma'u, cike da kulawa tace, daman yanzun zan sa Nafisa ta kiraki, dan mijiki ya shigo tun d'azun"
Daramm taji gaban ta ya fadi, sabo da yadda momy takira Jamal da sunan mijinta"
Kira Momy ta kwalawa Nafisa, bayan ta iso tace rakata part din jamal"
Jitayi cikinta na kugi anya kuwa zata iya yin abin da deeni yace"
Data tuna fuskan Jamal takejin gabanta ya fadi, gsky tana shakkar sa, dan fuskan shi babu wasa"
Suna cikin tafiya, ma'u ta juya ta kalli nafisa tace"
Nifisa tsoron yaya Jamal nake, ban son zuwa kusa dashi"
Da sauri nafisa ta kalleta tare da fadin kema?
Fuskan ma'u dauke da mamaki tace, au kema yana miki masifa"
Baki nafisa ta kama, tare da fadin ke ai wlh yaya jamal mugun masiffe ne, masifa ta masa yawa amman ai ke kila bazai miki ba?
Shiru kawai ma'u ta mata, dan taga sun isa bakin kofar, suna taba kofar sukajita abude, dan haka suka shiga bakin su dauke da sallama"
Yana zaune akan kujera yana yin abin da ya saba wato karatun jarida"
Matsawa Nafisa tayi tabawa ma'u hanya ta shige sannan ta juya tare da fadin saida safe"
Ke zonan"
Da sauri Nafisa ta juyo ta kalle shi"
Me kuka zo yi?
Momy ce tace na rako Anty Asma'u"
Ki rakota? tamin me?
Kaji yaya jamal din nan da wata mgn, nafisa ta fada azuciyanta, afili kuwa cewa tayi"
Bansan me zata maka ba, nima momy ce tace na rakota"
Kan shi ya maida kan jaridan, ganin haka nafisa ta fice"
Ma'u kujera ta samu daga gefen shi ta zauna"
Ko kallon inda take beyi ba, sun dauki tsayon lokaci ahaka"
Zuwa can ya waigo ya kalleta a hankali yace"
Husna inajin bacci, zanje na kwanta, ke a ina zaki kwanta?
Haushi tambayan ya bata dan haka tace duk inda kace"
Kallonta yayi sannan ya sake cewa, OK toh ki kwanta afalo, akafin gobe agyara miki dakin ki, ni gadona kananan yara basa hawa, dana barmiki, yana mgnr ne yana tafiya"
Innalillahi wa inna ilaihir raju'un ta fada tare da bin bayan shi da kallo"
Haba tayaya zan kwana afalo bayan tunda uwata ta haifeni bantaba kwana afalo ba, wannan wanni irin wulakacin ne zaice wani wai na kwana afalo, aiko bako ne yazo aka barshi, ya kwana afalo an wulakanta shi"
Tunanin da taitayi kenan har gurin 12 tana xaune, zuwa can ta mike ta nufi bishi, dan ita bazata iya bacci afalo ba, kofar da taga yabi, ta tura, kofufi guda uku ta gani ajere, na farkon ta tura"
Daki ne lafiyayya babu Kowa aciki, yana zuba uban kamshi"
Ajiyan zuciya ta sauke sannan ta shiga, nan taga jirin akwatunan ta dasuka taho dasu dazon, watoh jamal saboda tsabar mugunta ya barni na kwana afalo, dayake beda imani ko tausayi na, bayaji"
Washegari da safe ta fitoh da nufin zuwa part din momy"
Ta kusa isa ta hango megadin gidan yana zaune da redio sa ahannu, azuciyarta tace"
Barinje in tambaye shi, wacce unguwa muke, karasawa tayi tanayi tana wai wayen bayanta"
Takusa isa taji muryan jamal, Ke Husna"
Afirgice ta waigo tana kallon shi"
Ina zaki ?
Dawowa tayi da baya tana kokarin shga part din Momy, amman saitaji jamal yace karki shiga, wa kika tambaya kafin kiki fito?
Ahankali ta dawo baya, tana zuwa daidai gurin shi, yasa hannu ya matse kunneta tare da fadin, ke wai wacce irin yariya ce? me kikaje yi kuma gurin me gadi? sai kace wata ballah gaza"
Zafin da taji shi yasata ta fitar da Wata yar kara, tare da kama hannun nashi tana kokarin cirewa akunneta"
Yarrrr yaji ajikin shi, sanadiyan kama mai hannu da tayi, nan danan jikin shi ya mace, daker ya iya bude baki yace"
Kina ganin kaman zaki iya kwatan kanki ahannu nane?, ko wannan dan iskan saurayin naki idan na rikeshi bazai iya kwatan kashi ahannuna ba, bare ke, kuma bazan sake ki ba harsai kin gaya min me kikaje yi agurin"
Saboda tsananin azaban da take ji batasan sanda tace, rake fah nake son sha, shine naje na bashi ya sayo min"
Tirrrrr, rake? natsani naga mace nashan rake, amman nasan..... Kome ya tuna kuma sai yayi mormushi sannan yace, ina kudin ?
Tsuro tsuro tayi ganin haka ya sake yin murmushi, sannan ya saki kunnen ta yace"
OK, rake zakisha ko? barin naje na nemo miki"
Juyawa yayi ya fita, zuwa can ya dawo ya mika mata ledan hannun shi, tare da fadin daga yanzun duk abin da kike so, kimin mgn zan kawo miki"
Gefe ya koma ya zauna, duk da cewa bawai son raken take ba, amman da ta tuna yace beson yaga mace nashan rake, yasa ta dauko ta fara sha"
Shiko jamal yadda ta daddage take shan raken abin yaso bashi dariya, hakanan yaji tana burge shi"
Tas ta shanye raken, sannan ta mike tana kwashe bawon"
Cikin shi cike da dariya yake satan kallonta, harta shige daki yana bin bayanta da kallo"
11:41pm Jamal kwace akan gado, bacci yaki zuwa duk inda ya juya Husna yake gani lokacin da take shan rake, dariya yayi kadan, sannan ya dada gyara kwanciyan shi, ji yayi kaman gadon yamai fadi dan haka ya jawo folo ya rungu me
Itako ma'u ganin Jamal be nuna fushin shi ba, yasa ta daukan alkawarin sashi yin fushi, dan haka ta tashi ta nufi dakin jamal"
Kayan bacci ne ajikinta dan haka ta dauki hijjabi ta daura kai"
Ahakali take buga kofan"
Waye ? taji ya fada"
Murya kasa kasa tace nice"
Saukowa ya fara yi, tare da fadin menene ?
Daidai lokacin daya bude kofar ya kura mata ido"
Turu baki tayi kadan tare dayin kwalkwal da ido, sannan tace"
Rake zan sha"
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
[22:19, 12/15/2017] +234 813 272 6929: 💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
5⃣1⃣to5⃣3⃣
Rake ? Banda wadda kikasha d'azon?
Kai ta daga tare da sunkuyar da kanta kasa"
Kallonta yayi daga sama har kasa sannan yace"
Da tsakar daren nan ne zakice min zaki sha rake, banson iskancin banza fah"
Duk da cewa yadda yayi mgnr ya firgitata amman saita dake ta turo baki, cikin shagwaba tace toh ai kaine kace duk abin da nake so nagaya maka"
Yana binta da idon yace, dan nace miki haka kuma sai kizo ki hanani bacci, da daddren nan, ina zan samo rake yanzun"
Hawaye ta matso ya zobo akan kuma tunta"
Ganin haka jamal ya fara fadin kin fara ko?, to yanzun me kike nufi?
kukanta kawai take yi, batare da ta sake kallon sa ba, zuwa can yace"
Duba, husna yi hakuri kije ki kwanta, gobe da safe zanje in nemo miki, kinji"
Wani haushi ne ya kamata, dan ba haka ranta yaso ba, dan haka taki wucewa"
Kallonta kawai yake yana rike da kofar, yana karewa santalin kafa fuwanta kallo, dan rigar bata kai mata kasa ba, zuwa can yayi ajiyan zuciya sannan yace"
Kisan Allah, idan baki wuce ba ranki zai bacci, karki nemi ki raina ni, idan baki hankali ba cikin daren nan saina tayar miki da jiki, karki wuce kiban guri ki gani, kofar ya maida ya rufe sannan ya koma gado ya kwanta"
Itama ma'u karamin tsaki taja tare da fadin maye kawai, juyawa tayi ta shige daki zuciyarta cike da haushin shi"
Hijjabinta ta cire sannan ta haye gado, karaman jakanta ta rarumo ta rungume babu dadewa bacci ya dauketa"
Shiko Jamal bacci gagaran shi yayi, ji yake da akwai inda zaisamo ya bata adaren daya je, ko dan ta daina kukan"
Kasa hakuri yayi dan haka wata zuciyan tace je ka duba mana ko tayi shiru"
Tashi yayi ya nufi dakin ma'u ahankali ya tura kofar, hangota yayi tayi daidai agado tana bacci, haka ne ya bashi daman karasawa ciki"
Ahakali yake tafiya dan beson tasan da shigowan shi"
Tsaye yayi akanta yana karewa ahalitta ta kallo, karo na farko a rayuwan shi dayaji yana son ya kai hannushi jikin mace, saidai bazaitaba bari hankan ta kasance ba"
Ganin kanta babu dan kwali yasa ya tsuna agaban gadon, wani karamin gyale ya gani agefe, ahankali ya dauko ya nannade kan dashi sannan ya kawoshi gaban kan ya daure, shida kanshi daya kalla yasan ba haka ake ba, dan ya tabbarar har gari ya waye bazai kwance ba"
Addu'oi ya tofah mata sannan ya jayo bargo ya rufeta, kula yayi da jakar dake hannunta, ahankali yasa hannun shi ya zare jakan, mikewa yayi ya fara tafi, har yakai tsakiyan falon ya tsaya tare da waiwayawa ya kalle ta, wata zuciyan ce tace danje ka sunbaceta, afilin yace tirrr Allah ya kiyaye"
Dakinsa ya koma ya zauna abakin gado sannan ya bude jakar"
Da sarkan deeni ya fara cin karo, hannu yasa ya zarota, dogowa ce sosai, ga uban nauyi, agefe ya ajiyeta, sannan ya kara saka hannun shi, wani dan dogon Abu yaji me karfi, fitowa yayi dashi, nan ya fahimci wuka ce"
Zarota yayi acikin dan gidanta sannan ya kureta da ido"
Babu abinda wukar take banda sheki dagani bakaramin kaifi gareta ba"
Mamaki ne ya kama jamal, nan take ya shaida daga inda suka fito"
Amman meyasa deeni zaibawa Husna waka? me zatayi dashi? Idan ya bata sarka saboda soyayya ? Toh wukar ta menene?
Take Wata zuciyan tace soka maka za,ayi?
Mikewa tsaye yayi tare da fadin lallai akwai aiki agabana dan husna nema take ta zama yar daba"
Afili yace waishin soyayya hauka ce? Yar karamar yariya duk tabi ta haukace a soyayya ? Idonta ya rufe babu gani babu ji?
Tunanin abban asma,u ne ya fado mai arai, hakika yana tsananin tausayin Sa, yanzun inda wani guri tayi aure za a iya sakin ta ayau, dan babu wadda zayi aure yaga matar da wuka beji tsoron zama da itaba, kuma za,azagi iyayenta"
Dan haka yaci alwashin shima bazai gayawa iyayen saba, dan yasan idan suka sani duk yadda suke Santa saita sure musu"
Ranan Jamal be iya runtsawa ba, tunani kawai yake tare da tsananin mamaki dan abin ya wuce tunanin shi"
Yasan cewa babanta yayi iya kukarin shi akanta, amman shi yana gani akwa wani abu da iyaye basa bashi mahimman ci"
Idan kakai danka makaranta, ba komawa zakayi ka nade hannu ba, yana da kyau ka dinga kai mishi ziyaran bazata, akai akai, kaman duk kwana 3 ko 4, sanan jawo yaro ajiki yana da matukar mahimman ci, dan zai saki jiki dakai, bazai dinga boye maka abuba, haka zai baka daman dakatar da abin tunkan yayi nisa"
Tunanin da Jamal yaitayi kenan, be fargaba saijin kiran sallah yayi"
Boye jakar yayi da kyau, sannan ya shige toilet ya dauro alwala ya wuce masallaci"
Itako ma'u tana tashi taji kanta daure tamau"
Hannu tasa ta shafa cike da mamaki tace menene kuma haka? Kokarin kwancewa take ta kasa, gaban madubi taje ta kallah"
Afirgice ta cire hannuta kai, dan ganin tayi kaman andaure kaya"
Toh waye yamin wannan daurin? Wata zuciyar tace jamal, da sauri ta girgiza kai tare da fadin yaya jamal bazai dauramin dan kwali ba, kodai aljanune, wannan tunanin yasa ta firgice, tayi dakin Jamal aguje, saidai tana shiga taga babu kowa dan lokacin Jamal yana masallaci"
Kara firgicewa tayi ta ranta aguje,ta nufi fita daga bangaren su...
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
5⃣4⃣to5⃣6⃣
Jin tayi tayi karo da wani abu, gamshin turaren da taji shiya tabbatar mata Jamal ne, hannu yasa ya dogota daga jikin shi tare da daure fuska yace"
Menene haka, ina zaki ahaka?
Adaburce tace gurin momy zani"
Me zakije yi gurinta?
Tana waiwayen bayanta take fadin nifah wlh tsoro nakeji bazan iya zaman nan ba"
Tsaki yaja tare da kokarin tafiya, afirgice ta kama rigarshi, kallon da ya watsa mata yasa ta sake shi da sauri tare da fadin yaya wlh tsoro nakeji, karka tafi kabarni
Tsaki ya sake ja yayi gaba abinshi, aguje tabi bayan shi tsagal tsagal daga ita sai rigan bacci"
Yana kokarin shiga dakin itama tana kokarin shiga tare da zare ido, ganin tana kokarin bangaje shi yasa ya matsa ya bata guri ta shige"
Kan kujera taje ta rakube, Jamal ko ido ya zuba mata yana kallo kaman ya samu TV"
Zuwa can ya sake jan tsaki tare da dauke kanshi daga kallon ta, sannan ya wuceta yana kokari balle botirin hannun rigar sa"
Waigowa yayi ya kalleta sannan ya daure fuska tare da fadi.....
Toh yanzun yaya zamuyi?, inason zanyi wanka"
Idonta tsuru2 tace toh dan Allah karaka ni gurin nafisa, nibazan iya xama anan ni kadai ba"
Dauke kai yayi sannan yace ai ko zaki iya ma bazan barki ba, dan inason na sake adaki na, maza ki tashi ki wuce naki dakin"
Dan Allah kayi hakuri wlh tsoro nakeji, aljanu ne adakin"
Aljanu?, baki yi addu'a idan zaki kwanta ko?
Cikin sanyi murya tace inayi jiyane na manta banyi ba"
Toh yayi miki kyau gare da suka firgita Ki, gobe kya kuma"
Hawaye ta matsu sannan tace nifah ba firgita ni sukai ba, jifah inda aka daure min kai kuma na kasa kwancewa"
Akaikai ce ya kalleta sannan yace waya ya daure miki kan ?
Nima ban sani ba kawai bacci nayi, ina tashi naga kaina a haka"
Dariya taso bashi dan haka yai kasa dakai, saida ya saita kanshi sannan ya dago kanshi ya kalleta tare da fadin ai kice bakijin mgn gashi suma mutanen boye hankalin su ya dawo gareki, kinatsu kinki natsuwa, saikace me kunnen kashi toh aigashi nan kinsamu daidai dake"
Kuka ma,u ta fara harga Allah ta yadda da mgnn Jamal, hango Jamal na shirin shiga toilet yasa ma'u mikewa tayi kan Jamal cikuikuye shi tayi sosai ta shige jikinshi
Cikin sauri ya dage hannuwan shi sama tare da fadin tsaya2, sakeni inkwance miki dan kwalin, daker ya samo ya rabata da jikin shi, sannan ya mika hannu ya fara kwance mata, daf da juna suke dan haka kowanne najin domin daya, Jamal ji yayi yanayin jikinshi ya fara canzawa, duk lokaci daya da canzawan tunanin shi, Kai *Husna* ta hadu komai nata me kyau ne, lebenta ya kallah sannan ya sakko kan kirjinta, cikin sauri ya runtse ido dan kawar da tunanin, itako ma'u idonta na kasa dan haka batasan bakin daya yake ba"
Shima ganin idonta akasa yasashi maida idon shi kan kirjinta, kasa dauke ido yayi, ya dauki tsayon lokaci ahaka, zuwa can ma'u ta dago kai, cikin sauri ya kawar da kansa gefe, daker ya iya hada kalman zomoje narakaki gurin momy"
Lokacin da suka isa part din momy tana daki bata fito ba, kai tsaye dakin ya shiga ma'u nabinsa abaya"
Ganin momy kwance tana bacci yasadhi juyawa dakin nafisa ya nufah, itama kwace take tana bacci' juyawa yayi ya kalli ma'u yace toh matsoraciya saikije ki kwanta"
Juyawa yayi ya fice har ya gota dakin momy ya ja yatsaya, juyawa yayi ya koma dakin, tananan kwance inda take"
Ahankali ya karasa gaban gadon ya zauna sannan ya mika hannu ya fara tashin momy"
Ganin Jamal adakinta da safen nan abin ya bata mamaki dan haka ta tashi atsora ce ta zauna tare da fadin Jamal lfy ?
Kasa yayi dakai sannan ya karyar Sakai kaman karamin yaro yace"
Momy daman ...... Shiru yayi ya kasa karasawa"
Kallo Momy ta bishi dashi ahankali tace"
Jamal gaya min menene ya faru? Ko wani abo na damun ka ne?
Cije lebe yayi kadan sannan yace momy daman inaso ne nayi Aure"
Aure kuma? Wanne irin aurene kuma Jamal? Duka2 kwanan ka nawa dayin auren?
Kasa ya karayi da idonshi sannan yace momy ai wannan ba Aure bane, *Husna* fa kanwata ce, nida usman duk daya ne, babu wani babbaci, daukata nake kaman nafisa, dan haka Momy ni inason nai aure yanzun"
Wani kallo Momy tamai mekama da harara sannan tace"
Amman dai Jamal wautanka yawa gareta, inna fahimceka kana nufin bazaka iya rayuwan Aure da Asma'u ba"
Shiru yayi bece komai ba, dan haka Momy ta sake cewa toh shikenan Jamal tunda bazaka iya zama da itaba ai saika sallameta, dan za man beda amfani"
Shiru yayi zuwa can ya daga jajayen idon shi yace"
Momy nifa cewa nayi zan kara aure bawai wani abuba"
Eh ainaji zaka iyayin aurenka ammafa idan ka sallameta, dan baza,a tauyewa yariya rayuwa ba"
Mikewa yayi fuuuu ya fice"
Binshi da kallo Momy tayi afili tace wawa kawai, yana girma yana cin kasa"
*****
Allah sarki deeni bawan Allah,
Deeni ne zaune atsakar gida, ya rame yayi duhu, gefen shi ummi ce kwance kan tabarma, tun daga ranan dauren auren ma'u bata sake samun lfy ba, deeni ko baya iya tabuka mata komai, shima kaman mara lfy yake domin yau sati kenan, beji muryan ma'u ba"
Zaune kawai yake hawaye na zobo mai, hannu yake sawa yana sharewa, jifi jifi yanawa ummi kallon tsana"
Suna haka suka farajin haushin duna, cikin sauri deeni yayi waje"
Caka ya samu tsaye akofar gida, cikin fada yace"
Caka me yasa zaka kawo min shi, ayanzun bani da bukatan duna, katafi dashi bana son ganin kowa, idona asma'u kawai yake son gani, caka bani da kowa, kuma bani da gata, duk abin da ya sameni laifin ummi ne, itace tajamin narasa asma'u, inaji ajikina indan bansamu asma'u ba zuciyata zata Buga, wlh ina masifar son asma'u, hannun caka ya kama ya daura akan kirjishi tare da fadin taba kaji inda zuciyata take yi inaji kaman numfashina zai dauke"
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
*Slm inaba masoya BUGUN ZUCIYA hakuri sakamakon jina shiru kwana 2 da kuka yi, haka ya faru sakamakon wani uzuri nawa, ifatan zaku fahimce ni, kumin uzuri, insha Allahu zan dinga yi, ko babu yawa, wadanda sukamin mgn prvt sukaji shiru suyi hakuri pls🙏🏻 sakon yamin yawa sosai, masu son group ma suyi hakuri pls🙏🏻 insha Allahu page nagaba zan bada no dazuyi mgn asaka Ku*
5⃣7⃣to5⃣9⃣
Haka deeni yaita sambatu, batare daya san me yake cewa ba"
Sosai caka ya tausayawa deeni, bayan ta fiyan caka deeni ya shige gida, samun ummi yayi tanata nunfarfashi, kallonta yayi, kamar bazaije ba, sai kuma ya fara takawa harya je gabanta saida ya share hawayen fuskan sa sannan yace"
Ummi jikin ne?
Hannu ta fara miko mishi dan haka ya tsuna agabata tare da mika mata hannun shi"
Rike hannun tayi da kyau, hawaye na zuba a idonta cikin murya irinta wadda take jin jiki tace"
Auta dan Allah kayi hakuri naga har yanzun fushi kake dani, inacikin wani hali auta, zuciya namin kuna ina takaicin rayuwata, har inajin inama ba,a halittoni ba, duk bawani abu bane ya jawo min illah bin zuciya, gashi yanzun nazo ina dana sani, babu wadda yafi bani mamaki irin baban ka, tunda yasa kafa yabar gari har yau ban sakijin duriyar saba, juyawa tayi ta kalli deeni dayai kasake yana yana sauraronta tace auta kana jina?
Kai ya gyada mata sannan ya kauda kansa gefe"
Ummi taci gaba da cewa, auta babban burina ayanzun shine inga mahaifin ka, inason inganshi kafin ta Allah ta kasance akai na" banason na mutu nabarka babu dangin uwa babu na uba, auta nasan cewa ka girma amman nasan baka iya zama da mutane ba, sai yanzun nake wani tunani, auta da ace kai natsatsene ko na mutu nabarka makota zasu taimake ka, kuma zasu tausaya maka"
Hawaye deeni ya share sannan ya Kali ummi, tausayinta yaji ya kamashi, hawaye ya fara share mata yana fadin bayanzun zaki mutuba ummi, kuma kicire tunanin wannan tsohon a zuciyan ki, ni banason ganin shi natsane shi, kuma duk ranan dana ganshi idona dana shi, wlh wlh na rantse da sarkin dake busan numfashi sai yayi daya sanin kawoni duniya, bana sonshi sam, kuma duk randa na ganshi idona dashi saina mai SAKK"
Girgixamai kai ummi take ahankali take cewa karkayi haka auta"
Cikin sauri ya mike tsaye haba ummi ina tsananin son asma'u Amman gashi tana neman tseremin yau kusan sati 2 kenan banji muryanta ba, ummi inason asma'u kuma inason na aureta, dan haka nifah saina aureta, kuma wlh idan jamal ya kuskura ya tabamin kayana sai na masa CAN CANTA
Hmmm auta taya zaka aureta bayan tana gidan wani, zansu ka cireta azuciyar ka, ka daina kiran matar wani da kayan ka, dan musamu mu fuskanci gaba"
A,a ummi saina aureta, daga baya ma fuskanci gaban"
Toh auta karinka hadawa da insha Allahu, kuma kayi addu'a Allah ya baiyana Mahaifin ka"
Girgiza kai yayi tare da mikewa tsaye, kallon ummi ya sakeyi sannan ya kada kai yayi waje"
****
Shiko Jamal bayan yabar part din momy bangaren su ya koma, afalo ya zauna sannan yasa hannun shi duk 2 ya dafe kai, zuwa can ya cire hannun nashi sannan ya daura tagumi, neman hanyan dazai bi yake, dan gaskiya ayanzun yana bukatar mace akusa dashi, amman fa yana son wadda zai aura ta kasan ce ta girme shi, ko kuma suzo sa annan juna, daker ya iya tashi ya shirya cikin kakin Sa ya fice"
Momy ko batasan da shigowan ma'u sai kusan 12 na rana"
Dakin nafisa ta shi tana fadin nafisa zoki kiramin asma'u"
Turusss tayi ganin asma'u kwance ta kifa kanta akan gado"
A,a ke kuma yaushe kika shigo?
Nafisa ce tace momy ai tunda asuba, yaya Jamal ya rakota, kuma tun lokacin take kuka"
Tahowa Momy tayi tare da fadin kukan lfy, zama tayi abakin gadon sannan ta daga hannu ta jawota tare da halan wani abu Jamal din ya miki?
Shiru batace komai ba, dan haka Momy ta sake cewa asma'u waini me kika daukeni?, nace miki idan kina da matsala ki dinga samu na kina gayamin, ko menene kiji ko"
Murya kasa kasa tace momy inaso nakoma gida bazan iya za agarin nan b....
Sabo da me? Cewar momy tana tsare ma'u da ido"
Tsoro nakeji momy bazan iya zama abangaren yaya ba akwai aljanu aciki"
Aljanu? Inji Jamal din ne ya fada miki?
A,a momy jiya ne na kwanta bacci ban daura dan kwali ba amman dana tashi sai naga andaura min dan kwali"
Murmushi momy tayi kadan sannan ta kauda kanta gefe tare da fadin to banda abin ki, Asma,u ai bake kadai bace adaki, yanzun haka Jamal ne"
Jin ta kawai tayi tace bashi bane momy, shi ai baya ma shigowa dakina"
Shiru momy tayi zuwa can ta waiga ta kalli nafisa sannan tace"
Nafisa kira min umma me lalle"
Mikewa nafisa tayi ta zura hijjabi sannan ta kama hanya"
Cikin kan kanin lokaci nafisa ta dawo da me lalle"
Bayan sun gaisa Momy ta nuna ma'u tace kitso zaki mata da lalle"
Cikin kankanin lokaci ma'u ta fito ras, yamma likiss jamal ya dawo lokacin ma'u na zaune afalon Momy"
Sallama yayi sannan ya nemi guri ya zauna"
Idon shine ya sauka akan lallen hannun ma'u, ya ilahi ya fada azuciyan shi, cikaba yayi da cewa tunda nake ban taba ganin irin wannan lalle ba, gani yayi fuskan ma'u ta kara wani irin kyau, dan haka ya sakankance yana kallonta"
Zuwa can yaga tana kokarin dago kai cikin sauri ya maida kanshi kasa tare da saka hannu aljihu ya Ciro wayar shi"
Daga ta yayi ya kare fuskan shi, zuwa can yaga bazai iya hakuri ba, kautar da wayar yayi daidai lokacin da ma'u ta dago idonta dan haka cikin sauri ya maida wayar"
Camera ya shiga yayi saitin ma'u sosai, ya kura mata ido, har ya shagala da kallonta"
Gyara zaman shiyayi, harda kishin gid'a, yana kara mata kallo babu wadda ya lura dashi"
Momy kallon Jamal take ajikin zuciyanta tace wannan kwai miskilin jaraba, wato ko kallota bama bazaiyi ba, harda wani tare fuska da waya"
momy harara kawai take jefawa Jamal, dan babu namijin da zai kalli ma'u beso ya kara kallonta ba sai Jamal"
Shiko Jamal tuni kwakwalwar shi ta nitsa cikin kogin tunani, kallon ma'u yake yayin tunanin shi ke kimanta masa wani sura tata"
Be Ankara ba yaga ma'u ta mike tana kokarin barin wajen"
Aranshi yaji beji dadin tashinta ba dan haka yaja tsaki ya sauke wayan"
Wani haushi ne ya sake kama ummi wato, saida yaga asma,u ta tashi sannan ya aje wayan, itace beson ya kallah kenan"
Ummi ce ta juya tace Jamal ka tashi ka tafi part din ku, ga asma'u can ta wuce, kuma dan Allah karkai nisa da ita, dan naga tana da tsoro"
Mikewa kawai yayi, saida ya fara tafiya sannan yace saida safe"
Allah ya tashemu lfy momy ta fada, cikin sauri ya nufi part din dan ya kosa Yasa ma'u a idon Sa"
Adakinta ya sameta sai dube2 take, abakin gadonta ya zauna sannan ya bita da ido"
Daker ya iya furta me kike nema ne?
Kuka ta fara matsuwa tare da fadin jakatace bangani ba"
Jaka ? Kuma ? Menene ajikin jakar"
Rasa abincewa tayj dan haka taca kayan kwalliya ne aciki"
OK indai kayan kwalliya ne karki damu zan saya miki
Ko inda yake bata kalla ba, taci gaba da neme2 ta, shima bekara bin ta kanta ba, waya ya sake cirowa ya kare fuskan shi, hotuna ya fara daukan ta, duk inda tabi saitin ta yake bi"
Lokaci lokaci ma,u na waigowa ta kalle shi acin ranta take cewa shi kuma wannan me yakeyi anan bayan ba shigowa yake ba"
Gajiya tayi dan haka ta koma gefe ta zauna, ko banza sarkan deeni tana debe mata kewa, idan ta kalli sarkan har kanshin deeni takeji, hawaye taji yana zubo mata, tasa hannunta ta share, sannan ta fara neman hanyar da Jamal zai bata aron wayar shi"
Kara karfin kukanta tayi, ahankali ya juyo ya kalleta, kewai baki gajiya da kuka ne?, kulum kuka, kullum kuka, yanzun kukan kayan kwalliyan kike?
Dago kanta tayi ahankali ta kalleshi, cikin sanyin murya tace inaso ne, nayi waya da mutanen gidan mu"
Murmushi yayi kadan, sannan ya dannan wayar ya mika mata"
Gani tayi har ya danna kira, Abba ta gani akan wayar cikinta ne ya duri ruwa domin ita deeni taso kira"
Muryan Abba ce ta katse mata tunani, cikin karsashin shi yake cewa, Jamal ya Kuke, yagida"
Rasa abin cewa tayi, zuwa can Abba ya sake cewa Jamal kanajina kuwa?
Cikin kuka tace Abba bashi bane ni ce"
Jim abba yayi zuwa can yace"
Yaya aka yi?, shiru yaji dan haka yacigaba ta cewa"
Kinanan da halin naki ko kuma ya dan lafa?, ki kula kisan abin kike idan kinason kiga fara'a ta kaman da, to kiyiwa mijinki biyayya, ki kwantar da hankalin ki kikautawa mijin ki, kinji ko?
Hankali tace toh abba"
Sosai abba yaji dadin inda ta amsa, dan haka ya mikawa mama wayar"
Itama nasiha ta mata sosai, sannan sukayi sallama"
Jamal ta juya ta kallah zuciyanta cike da haushin shi, tabas Jamal be da makusa, ya hadu sosai, kuma ya iya daukan wanka, sabanin deeni da kullum yana nan dai cikin kananun riguna kusan kullum jikin shi abude yake, dan wandonan shi da wuya su wuce guiwa"
Tunawa tayi da yadda batan Jamal take sheki luf luf, sannan ta hango ta deeni data baci da sara kaca kaca"
Juyawa ta sakeyi ta kalli Jamal, sannan ta kyauda idonta gefe, acikinranta tace ni babu ruwana da wai kyan ka, duk da haka nidai deeni nake so"
****
Tundaga ranan haka Jamal yake lalacewa wajen kallon lallen ,ma,u ko gaban Momy da daddy ko haka zaiyi saitin da wayar shi,
Har aka kwashe tsayon sati 2 zuwa wannan lokacin lallain ma'u ya fita dan haka ya farajin babu dadi, besan yana son lalle ba sai wannan lokaci"
Ranan da ta cika sati uku momy ta sake kiran me lallai, Momy cewa tayi wannan karon kiyi mata na gargajiya"
Juyawa Momy tayi ta nufi dakinta, afili take fadin nikam narasa gane kan Jamal, wannan wacce rayuwa ce?, nidai nasan babu namijin da zai kalli ma'u yace beso, amman al'amarin Jamal ya fara bata tsoro, ko kallo ma'u bata isheba"
Jamal be kula ma'u tayi lallai ba sai washegari nan ya lalace gurin kallo har ya makara fita gurin aiki"
Koda yajema haka yake lalacewa gurin kallon hotonan ma'u
Har lallen ma'u ya fita Jamal be nuna yana so ba ko sha awan shi ba, dan haka momy bata sake kiran me lallai ba, aramta ta fara tunani kila ba lafiyaye bani, ganin tun tasowan shi bashi da budurwa, duk da cewa yan mata da yawa suna cewa suna sanshi amman saiya ce wai sun rainashi ne"
Tunanin hajiya asabe ne ya fado mata, kodai tayiwa Jamal wani abu ne dan ta cerai mai sha'war mace, dan ta kula kiyayyan da hjy asabe take nunawa Jamal tayi yawa"
*****
Ran da lallen ma'u yayi sati 1 da fita Jamal ya gaji da jiran ganin sabon lalli, dan haka daya shirya tafiya ya fito afalo ya samu ma'u"
Bayan ta gaidashi yasa hannun a aljihu yaciro, dubo 20 yaje agefen ta, tare da fadin gashinan kiyi lalle da kitso"
Dasauri ma'u ta kalleshi sannan tace, aini daman momy ce take cewa ayimin, bani nake zuwa ba"
Shiru yayi zuwa can yace toh Ki rike kudin saikije kicewa momy kinason amiki lalle"
Turo baki tayi kamar me shirin kuka tace nifah daman bason nake ba, dan dai momy ce kawai nake tsayawa"
Wani haushi ne ya kamashi cikin fada yace"
OK rashin kunya zakimin kenan ?
Ganin ta sunkuyar da kanta kasa yasa ya fice, yana kada kai"
Bayan kwana biyo yaga bazai iya hakuri ba, dan idan yana kallon lalle wani irin nishadi yakeji part din Momy ya nufa yana sanye da jallabiya"
Momy da daddy ya samu afalon nafisa na kwance jikin momy,"
Bayan ya gaida su ya kalli nafisa yace"
Ke bannan?
Mikewa tayi ta fice"
Motse ya fara da bakin shi, ya rasa ta ina, zai fara zancen yana son husna tayi lalle, ai wani ma sai yace sonta nake"
Wata zuciyar ce tace, to meye dan motum yace yana son kawar sa tai lalle"
Daddy ne yace jamal kaman bakin ka da mgn"
A'a daddy ba komai"
Shiru sukayi zuwa can Jamal ya mike ya nufi fita har yakai tsakiyan falon ya tsaya, tare da Fadin momy ina son na ganki.....
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
6⃣0⃣to6⃣3⃣
🤳🏻🤳🏻🤳🏻 Yana gama fadin haka ya shige dakin momy"
Mikewa tayi tabi bayan sa, yayin da daddy ya bisu da kallo"
Bayan momy ta zauna ta kalli Jamal tace ina jika yaya aka yi?
Dariricewa yayi yarasa mema zan ce, zuwa can ya dan sosa keya sannan yace"
Yariyar can ne naga kafarta kaman na maza, ko dan irin kunshin nan babu"
Cikin mamaki Momy tace wacce yariya kenan?
Husna, ya fada atakai ce"
Hmmm Jamal Kenan, ka manta kanwar ka ce?
Dukar dakai yayi kasa sannan yace ban manta ba momy, ai bawani abu bane dan nace kanwata tayi kunshi ko?
Murmushi Momy tayi sannan tace"
Eh bawani abu bane, amman ina baka shawara tun wuri ka sauke girman kan nan naka, ka daina yaudaran kan ka"
Kanshi akasa yace momy ban gane yaudaran kaina ba?
Tsaki Momy taja tare da mikewa tsaye tana fadi, ni wlh bana son munafunci mutun naso yana kaiwa kasowa"
Har momy ta fice Jamal binta da kallo yake, sannan ya jigina kanshi jikin gado, runtse ido yayi idan na fahimci momy nufinta son husna nake, eh nasani tunda na daura husna a idona ban tajin wai basonta ba, inason ta amman bada Aure, sosai nakejin ta acikin zuciyata, dan haka nashige cikin lamarinta"
Haka yaita tunani daka karshe ya tashi ya bar gidan"
Momy ko koda ta koma gurin daddy mamakin halin Jamal taitayi, ita bataga amfanin mutum nason abu ba amman yaita wani kyauce kyauce, kwashe yadda sukayi da Jamal tayi ta fadawa daddy"
Dariya daddy yayi sosai tare da fadin tunda yana son kunshi daya fita kisa amata sabon design"
Itama momyn dariya ta sake yi, sannan tace"
Ni wlh mamaki ma abin yake bani, kofa kallonta baya yayi, amman kaji ashe idon sa ya gano masa kunshin ta"
Bayan fitan daddy momy kiran ma'u tayi, tace nafisa ta tsefe maki kai, anjima umma zata zo ta miki kitso"
Mgnr Jamal ce ta fado mata, take taji batason yin, kumshi kwata2, kanta tasa akasa sannan tace"
Momy abari sai gobe ne dan kaina yau ciwo yake min"
Shiru ummi tayi zuwa can tace toh Allah ya kaimo goben lfy, kin sha mgn ko?
Eh kawai tace, sannan ta mike zata fice"
Ahankali momy takira sunanta bayan ta dawa ta mika kofin dake gefenta tare da fadin shanye kiban kofin"
Karba tayi tana kara bin cikin kofin da kallo, ko ba'afada ba tasan maganin mata ne aciki, Karba tayi ta shanye azuciyanta tanajin ana gyarawa deeni ne"
Da yamma Jamal ya dawo gida jikin shi babu kwari, kallo daya yayi wa ma'u ya kyauda kai tare da Jan tsaki"
Kallon shi momy tayi tare da fadin lfyr ka?
Lfy lau yace ataika ce sannan ya mike ya fice"
Binshi da kallo momy tayi sannan ta juya ta kalli ma'u tace tashi ki wuce part din Ku"
Afalo ta wuce Jamal yana zaune ya zuba uban tagumi, kallon shi tayi alalace tashige daki"
Harta kwanta bacci bata sakejin motsin Jamal ba"
Shiko Jamal lokacin dayayi nufin zuwa daki ya kwanta kasa wucewa yayi, saida ya tura kofar ma'u ya gama lekenta sannan ya wuce"
*****
Washegari
8:00am Jamal ya fito cikin shirin tafiya aiki, falon daddy sa ya nufa, bayan ya zauna ya mika gaisuwa gurin daddy da momy"
Cikin natsowa yace fara gayawa iyayen sa antura shi kasar Somalia, sati me zuwa zasu wuce, karashe magar yayi cikin yanayin damuwa"
Addi'oi daddy da momy suka masa sosai"
Amsa musu kawai yake da ameen amman zuciyar shi babu dadi"
Daddy ne ya kula da sanyin jikin jamal dan haka yabishi da kallo sannan yace"
Jamal yadai ? naga kamar bakason tafiyan nan, tun da kake tafiya bantaba ganin jikin ka yayi sanyi haka ba"
Ya ke, yayi sannan yace a,a bakomai daddy kainane yake dan min ciwo"
Toh kasha magani ko?
Mikewa yayi tare da fadin idan nafita zan nemi magani"
Dahaka yayi sallama da iyayen Sa ya nufin office"
****
Deeni zaune agaban ummi nasiha take mai akan ya hakura da ma'u, amman ya dage yace inna sam asma'u kayan shi ce"
Dan haka wata dibara ta fado mata, tari tayi sannan ta juya tace"
Auta gawata jaka can kaje ka dauko min"
Mikewa yayi babu musu , bayan ya dako ya mika Mata"
Bude jakar tayi ta ciro kudi masu yawa ta mikawa deeni, sannan tace"
Kaga wannan kudin nabaka ne kayi kudin mota kaje garin baguma kaji ko suna da lbrn mahaifin ka"
Wani kallo deeni ya watsawa ummi sannan ya karkace baki yace"
Ummi aina gaya miki idona idonshi za'yi batacciya Allah wlh"
A'a auta koma me kakeji kayi hakuri, inason naganshi akwai maganar dazan gayamai, kuma kagani bani da lfy bazan iya zirga zirga amota ba"
Daker da sudin goshi deeni ya yadda zai tafi baguma"
Haka ko, washegari ta asubahi ya dauki hanya"
Da daddare ya isa kyauyen su, dan haka ba kowa ne yasan da zuwan nashi ba"
Tsofaffen kakannin shi yasamu kwance tsakar gida suna shan iska"
Sallamar shi yasa tshowa duduwa karo fitilan kwan dake gefenta"
Shima tsoho carbin shi ya rarumo yana fadin wanakeji kaman Shamsudeeni"
Shine ya fada atakaice"
Arude tsofaffin biyu sukayo kashi suna haska shi da fitila"
Tabass shamsudeeni ne murnace ta kamasu gaba dayan su"
Bayan sun natsu suka kawo masa abinci, yanacin abincin yana gaya musu yadda ya baro jikin ummi, tare da gaya musu dalilin zuwan nashi"
Duduwa ce tace muko muke da lbrn bashir, dan bashir ya dawo tuntuni, kuma yayi bakincin rashin samun ku anan"
Shiru duduwa tayi na dan wani lokaci dan haka deeni yace toh yanzun yana ina kenan"
Nigeria wani gari wai Abuja, bashir yayi kodi sosai bayan komawan shi Nigeria, tunda Allah ya hadasu da dan yayata Alhaji Muhammad Inuwa......
Deeni bebari ta karasa ba yace"
Ashe arziki ya tafi nema mu kuma ya bazatar damu, ya tafi yabar ummi cikin tashin hankali, ya manta da ita bare ma ya tuna dani, aina zan ganshi?
Ai ka baroshi abaya, mikewa tayi tare da fadin inzuwa"
Bata jima ba ta dawo ta mikamai wata takarda, Karba yayi ya duba address ne ajikin ta"
Dubawa yayi sannan ya mike tare da fadin zan koma, zanje innemeshi duk inda yake"
Be samu mota adaren ba dole tasa ya kwana atasha, da misalin karfe 6;00am motar su ta tashi,
Sai washegari ya iso Abuja cikin ikon Allah ya isa kofar gidan kaman
yadda adireshin ya nuna"
Saidai ganin gidan ya tsorata shi, sabo da tsaruwan sa, harya fara tunanin anya kuwa gidan ne, dan yafi kama da gida jen turawa"
Lokacin daya nufi shiga gidan fir megadi ya hanashi shiga, acewar sa ai ba'a sanar cewa wani bako zaizo ba"
Dakarfin tsiya deeni ya tura megadin ya shige tare da fadin ubanka yaci uwatarrr"
Megadi bekara cewa zai tare deeni ba dan ya gano kalla, uhu ya fara yana fadin ranka ya dade akwai Matsala"
Wani farin Alhaji ne ya fito cike da zafi, bayan shi wasu maza ne, da alama abokanshi ne"
Ganin deeni cikin sauri alhaji ya fara tako matakalar benen"
Tsayawa deeni yayi aharabar gidan yanawa alhaji wani mugun kallo"
Cikin sauri ya karaso ya kama kafadar sa, tare da fadin shamsudeeni kai ne"
Be tanka ba kuma har yanzun wani kallo yake watsa mishi"
Hannun shi alhaji bashir ya faraja yayi cikin gidan da shi"
Afalo yaga wata yariya zaune ta hakimce gefenta yara ne guda biyu suna wasa"
Harara ya watsa mata kardai wannan yariyar baban nasa ya aura"
Dakin baccin sa yakai deeni, cikin sauri ya jawo akwatin kayan sa ya aje agaban deeni, tare da fadin"
Shamsudeen ka bude akwatin nan ka zabi kaya, ka sauya, bana son abokai na suganka cikin wannan shigan, zaka bani kunya, zaka zubarmin da mutunci, inason kasan wani abu yanzun bada bane, mutane namin kallon mutunci bazan su ka zubar min da mutunci ba"
Bakin gadon deeni yaje ya zauna ya daura kafa daya kan daya yana fito"
Sororo alhaji bashir yayi yana kallon deeni, nadama ce ta shigeshi me tsanani"
Hannu yasa Aljihu ya ciro waya, ya danna sannan ya kara akunne, zuwa can ya fara fadin Alhaji inuwa yau Allah ya kawo shamsudeen har gida, gashi agabana sai dai yana nan da halin nan nasa wadda nagaya maka, ka......
Shiru yaji baban nasa yayi yana saurara, zuwa can ya miko ma deeni wayar tare da fadin ku gaisa da baban ka"
Tunda suka gaisa da deeni da alhaji inuwa suka shiga zuciyoyi junan su,"
Daga karshe alhaji inuwa yacewa deeni karyaje ko kofar insha Allahu jibi zaizo ya dauke su"
****
Abangaren deeni kuwa yau tafiyan shi saura kwana biyu duk yabi ya kara rikicewa, dan haka da safe dayaje gaida momy harya mike zai fice ta dakatar dashi"
Jamal wai meke damun ka ? Ko tafiyar ce baka so?
A'a momy nima bansan me yake damuna ba, haka nan dai nakejin babu dadi"
Shiru momy tayi zuwa can ta sake cewa, Jamal naga dai ba yau ka fara tafiya ba, ban taba ganin ka daga hankalin ka kaman wannan ba"
Shiru yayi tare da sunkuyar da kanshi kasa"
Kallon shi Momy tayi sannan ta sake cewa"
Jamal kodai kana son katafi da matarka ne?
Kanshi akasa yace a'a bahaka bane"
Kollonshi kawai Momy tayi ta tabe baki"
Da daddare bayan yayi shirin kwanciya ya nufi dakin ma'u"
Tana kwance, ta kurawa sama ido, har ya zauna kusa da ita bata sani ba"
Tsintan kan shi yayi da hura mata ido"
Cikin sauri ta lumshe idonta sannan ta bude su akan Jamal"
Husna tunanin me kike?
Bakomai ta fada atakaice"
Shiru yayi zuwa can ya sake cewa momy ta gaya miki Zanyi tafiya jibi"
Eh ta fada atakai ce"
Shiru yayi tare da lunshe ido zuwa can ya sake cewa idan na tafi zanyi wata 7 ko sama da haka, ban yadda kije ko kofar gida ba, ki natsu ki tsare mutuncin kanki, karkimin wasa da aurena, ki sani duk abin da zakiyi idan ni bana ganin ki Allah na gani"
'Dauke kai tayi tare da turo baki"
Kyau yaga tamasa dan haka ya zuba mata idanuwa, zuwa can yasake cewa"
Idan akwai abinda kike so ki fada ko kirubuta kobe ki bani, hannu yasa a aljihu ya ciro wata waya ya mika mata tare da fadin gashi nasa miki no duk wadda ya gamata aciki, bayan su ban yadda kiyi waya da kowa ba idan kikayi Allah na kallon ki kuma ban yafe ba"
Kara turo baki tayi tare da dan murgudawa"
Murmushi yayi kadan sannan yace gashi har zan tafi baki sake min kunshi ba, ko baki son na gani ne"
Saida ta murguda baki sannan tace ninace banaso dan Momy tace zata kirata nace a'a
Abun mamaki Jamal beji haushi ba, murmushi ya sakeyi sannan yace toh dan Allah gobe Ki daure kiyi, kinga jibi zan tafi"
Kara bata rai tayi sannan ta jawo bargo ta rufe kanta' ganin haka yasa ya mike ya fita"
Washegari Jamal ya samu daddy da momy afalo"
Zama yayi nesa dasu, cikin nishadin daddy ya juya ya kalli momy sannan yace"
Kinko gaya masa anga shamsudeen?
Ziro ido Momy tayi tare da fadin na manta ko"
Shiko Jamal fadi yake waye haka?
Dan wajen kanina alhaji bashir dana baka lbr, tun muna yara mukayi alkawari idan muka haifi 'ya'ya maza zamusa musu shamsudeen da jamaludeen, kuma gashi Allah ya cika mana burin mu" gobe zan dauko shi ya zaauna tare damu, kai kuma gashi gobe zaka tafi"
Eh daddy ma gaisa ta waya daya iso akirani awaya
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
*Sadaukarwa*
*Faty Afreen Firdausi Sodangi Miss xoxo Zeenaseer, Deeja Wazari, Aisha Ali Garkuwa, Safiya Galadanchi Cwtjiddah Hamagee*
6⃣4⃣to6⃣6⃣
Naso ace kana nan dan zaifi jin dadin zama agidan"
Yake Jamal yayi kandan"
Daddy ma gyara zama yayi sannan yace"
Daman akwai mgnr da zan maka" kaga iyalin ka ya kamata ta koma makaranta sabo da yamzun zamani ya canza idan babu ilmi kana ji kana gani za,a barka abaya, dan haka kafin kadawo zaka samu ta koma makaranta"
Jamal ji yayi gaban shi yayi mummunan faduwa, tare da tashin hankali me tsanani"
Daddy ya kula da haka dan haka ya tsare shi da ido, tare da fadin Jamal ko baka son taci gaba da karatun ne?
Cikin sanyi jiki
yace gsky daddy abari saina dawo"
Me zakayi idan kana nan din, ai duk daya ne, kaga nafisa takusa karasa nata gara ta fara tun nafisa nacen ko?
Gyada kai kawai yayi badan ransa yaso ba, amman hankalin shi tashe yake"
Tashi yayi yabar falon, part din su ya nufa, nan falon ya kwanta, rufe ido yayi kaman me bacci, zuwa can ya bude, wayar shi ya jawo ya danna sannan ya karata akunne"
Zuwa can yace Usman ya gida"
Daga can cikin wayar usman yace lfy lau manga ya iyali"
Tsaki Jamal yaja kadan sannan yace lfy, gobe ne fa tafiyan mu"
Eh ai ina lissafe Allah yasa kuje lfy kudawo lfy"
Ameen yace ahankali sannan yaja wani gwaron ajiyan zuciya"
Ya dai ? Naga kamar bakajin dadi ne?
Wlh usman banaji dadi narasa meke damu na, kwata2 bana son tafiyan nan"
Dan murmushi usman yayi sannan yace haba Jamal kayi tunani dole zaka san abin da yake damun ka"
Shiru yayi zuwa can yaja tsaki yace"
Nasan dai banason barin Husna gida"
Kecewa da dariya usman yayi, saida yayi me isarsa sannan ya sarara, tare da fadi"
Me zai hana kasata ajaka"
Tsaki Jamal yaja sannan yace usman bafa wasa nake ba, dagaske nakeyi da akwai yadda zanyi afasa tafiyan dana yi"
Sabo da Asma'u ?
Kin amsawa Jamal yayi, shiru sukayi nadan wani lokaci, zuwa can, Jamal yace"
Usman duk da baka nan garin nabaka amanar husna, akwai waya ahannunta yazun zan turo maka no ta ka kirata ka mata nasiha ta kulamin da aure na"
Shiru usman yayi yana sauraron shi, lallai Jamal soyayya ta mika harda sambatu, dahaka sukayi sallama"
Jamal tashi yayi ya zauna hannun shi duk biyun yasa ya dafe kanshi, ya dade ahaka zuwa can ya mike ya nufi gurin Momy"
Tana zaune kan kujera yaje ya zauna kusa da ita sannan ya kwantar da kanshi akan cinyanta"
Hannunta ta dauka ta daura akanshi tare da fadin Jamal wai meyasa kanada damuwa amman ka kasa fadamin, Jamal jikina yayi sanyi akan yadda kake yi"
Kamar bazai yi mgn ba, zuwa can yace, momy idan zai yuyo abar mgn maranta husna harsai na dawo"
Shiru momy tayi zuwa can tace Jamal wai me zai hana ka tarkata husnan ka tafi da ita tunda naga hankalin ka yaki natsuwa"
Momy muna da yawa zamuyi tafiyan nan, bamusan taka memen gurin da zamu zauna ba, kinga bazai yiyu intafi da ita ba"
Toh jamal ka kwatar da hankalin ka kuma ai ba ita kadai bace agidan"
Ajiyan zuciya yayi sannan ya mike ya sake komawa part din su"
Afolo ya samu ma'u tana zaune kanta babu dan Kwali"
Saida ya tsaya ya gama kare mata kallo, sannan ya karasa daf da ita ya zauna"
Cikin sauri ma'u ta matsa dan saitaga abin ya mata ban barakwai"
Kallo yabita dashi sannan ya kara matsawa tare da sa hannun sa yajawota jikin shi"
Kokarin kwacewa take Amman ta kasa duk da cewa hannu daya yasa amman saida yayi nasaran kwatar da ita akan cinyan shi, tare da zuba Mata jajayen idon shi"
Cin wata irin murya yace husna gobe zan tafi, inajin wani iri ajikina"
Cikin tsiwa tace toh ni ina ruwana dan Allah ka sake ni"
Idon shi ya kara zuba mata tare da fadin husna kallah"
Idonta ta bude akan nashi, gani tayi idonshi yayi jawur kaman garwashi gefen kanshi ko wasu jijiyoyi ne rudu2, jikin shi ko banda rawa babu abin da yake, taso ta danji tausayin shi Amman saita kawar da idonta daga kallon shi Cikin san yin jiki tace yaya Jamal sake ni"
Bazan sake kiba husna inason kafin na tafi na neme gafaran ki dan nasan ni me laifi ne awajen ki, duk da cewa duk abinda na miki gata ne Amman nasan bazaki fahimci haka ba sainan gaba"
Batare da tayi tunanin komai ba tace nayafe maka toh sakeni"
Rangwanta rokon da yayi mata yayi sannan yace husna bakijin wani irin?
Kokarin kwace kanta take tare da fadin ni ba abun da nakej.....
Bata ankaraba taji hannun Jamal acikin rigarta, kallon shi tayi tare da zaro ido tunda take bata kawowa azuciyarta haka zata faru tsakaninta da Jamal ba, nan danan jikinta ya dauki rawa, tare da tsirarowan hawaye"
Hannun shi daya yasa ya dafe kanta yana lashe hawayen yayin da hannun shi daya yake saman kirjinta🙈"
Saida yaga hawayen ya daina zuba sannan ya sauke bakinshi kan nata"
Wani abu ma'u taji tun daga tsakiyan kanta har zuwa babban dan yatsanta, kokarin kwace kanta take Amman ta kasa gaba daya Jamal ya gama kashi mata jiki"
Tafi tafi Jamal ya cire riga sannan ya zage zip din rigar ma'u, duk da zulzullewar ma'u be hana Jamal sarrafa asma'u ba yadda ransa keso"
Kiran sallah mangariba yasa shi sakinta tare da maida nunfashi, sai lokacin na kula da bra din ma'u dake yashe atsakiyan falon"
Itako ma'u tashi tayi ta zauna tare da juyawa Jamal baya hawaye na zuba a idonta, kokarin maida zip dinta take sai lokacin ta lura zip din yariga fice"
Tsugunawa Jamal yayi agabanta tare da fadin yi hakuri kitashi kinga lokacin sallah yayi"
Mikewa tayi cikin fushi batare da tabari sun hada ido ba ta shige daki"
Murmushi yabita dashi sannan ya miki ya dauki rigarshi tare da bra dinta"
Dakinta ya shiga aje mata bra din abakin gado sannan ya shige nasa dakin"
Wanka yayi ya nufi masallaci, saida yayi ishsha'i sannan ya nufi gida"
Bayan ya dawo dakin ma,u ya sake komawa, samunta yayi tanata raira kuka, tana ganin shigowan shi ta dauke kai"
Zama yayi nesa da ita ahankali yace"
Husna menene abin kuka kuma?, nifa mijin kine, kuma nasan kinsan hakkina akan ki"
Bata ce kalaba dan haka shima yaja bakin shi yayi shiru bata kara bari sun hada ido ba"
Acikin zuciyarta ko mamaki take wai yau Jamal ne ya aje girman shi agefe, ita kunya ma abin yake bata ko son tinawa batayi, saidai har yanzun tanajin jikinta ba daidai ba, tun da deeni yake tabata bata tabajin yadda taji yau ba"
Muryan Jamal ne ya katse Mata tunani"
Husna me zai hana yau ki tayani kwana?
Make kafada tayi batare da ta waigo ta kalleshi ba"
Cikin kwantar da murya ya sake cewa haba husna baki son na tafi ina farin ciki ne?, jiya fah narokeki kiyi kunshi kika ki, yanzun kuma nace kitayani kwana zakice a'a"
Kara dauke kanta tayi tare da zunburo baki"
Damuwa ne ya bayyana karara afuskan shi"
Zuwa can ya mike ya fice adakin"
Ma'u na ganin fitan shi ta mike ta haye gado, tare da fadi azuciyar ta, haka kawai ni zakama wayo"
Shiko Jamal koda ya koma dakinsa kasa kwanciya yayi, gani yake kamar wannan ne daranshi nakarshi aduniya, dan haka ya mike ya koma dakin ma'u"
Itako lokacin tayi nisa abacci, gadon ya hau ya kwanta sannan ya jawota jikin shi ya rungume tare da sun batan ta"
Bebarta haka ba kara turmutsa hannun shi yake, cikin jikinta"
Cikin baccinta taji hannuwa na yawo ajikinta, cikin sauri ta rike hannun tare da zillewa"
Kara kankameta yayi ajikin shi ya shiga sarrafata san ransa"
Sun kwashe tsayon lokaci ahaka, Jamal duk ya daririce yafita hayyacin sa, ma'u tayi tayi takwace kanta ta kasa"
Ganin Jamal na kokarin maidata mace jikinta ya hau rawa fadi take"
Dan darajan iyayen ka, dan kalmar la'ilaha illalahu, karka min haka"
Be saurareta ba ganin haka yasa tacigaba da rokon sa, da duk wata kalma da tazo bakin shi"
Duk da cewa yakai kololuwa be hanashi tausayinta ba, sai dai ya kasa sakinta, tana manne ajikin shi, yace haba husna ya kamata ki duba halin da nake ciki, ki tausaya min"
Jikinta na karma tace dan Allah dai kayi hakuri"
Sunbatan ta yayi sannan ya zuba mata jajayen idonshi tare da fadin nayi, nayi hakurin Husna, idan ban yi hakurin ba ya zanyi dake, duk da nasan hakki nane, amman bazanso inkwace shi da karfi ba"
Daker ya iya tashi ya zauna tare da jawo bargo ya rufe jikin Sa, zuwa can ya dauki rigan shi ya maida sannan ya fice adakin"
Ma'u tashi tayi ta zauna, tausayin Jamal taji ya kamata, gaskiya ya bata tausayi kuma yanzun ne ta fara sanin yana da kirki, sai dai bazata iya bashi kanta ba, domin ta rigada tama deeni alkawari"
Amman kuma ta tabbatar da Jamal beji tausayinta ba bazata iya kwatan kanta ahannun shi ba, koma ba kowa bane zai samu wannan damar ya bari ta subuce mai, gsky Jamal yana da kirki kuma komai nashi daban ne"
Haka ta kwana ta tausayin Jamal azuciyanta"
******
Washegari karfe 8:00am Jamal ya fito cikin shirin tafiya"
Kaki ne ajikin sa fuskan shi daure tam kamar be taba dariya ba, bindigogi ne ajikin sa ta ko ina"
Falo ya sameta tana kwance tana danna waya"
Ajiye wayar tayi sannan ta gaidashi batare da ta daga ido ta kalleshi ba"
Daker ya amsan sannan ya zauna nesa da ita tare da fadin tashi ki zauna"
Zama tayi kamar yadda yace sai dai taki yadda su hada ido"
Meyasa bakison daura dan kwali?
Shiru tamai dan haka yaci gaba da cewa, ki dinga kokari kina daurawa sannan idan zaki kwanta bacci kidinka kokari kinayin addi'oi, sai Abu nakarshe da zan rokeki karki min wasa da aure, nasan kinsan akwai igiyoyina uku akan ki, bana wasa dasu, kena karkiyi wasa dasu, nasan kinje makaranta kuma na san angaya muku girman aure, karki yadda son zuciya yasa idon ki ya rufe ki take sani"
Shiru yayi nadan wani lokaci sannan yaja tsaki yace"
Idan namiki wani abu ki yafemin, nima na yafe miki wadda kika min abaya har zuwa yau, amma bazan yafe wadda kikayi bayan bananan ba"
Jitayi jikinta yayi sanyi, take taji kwallah tacika mata ido, cikin rawar murya tace bazaka dawo bani"
Hmmm zan dawo insha Allahu, kisan idan mutun zai yi tafiya yana da kyau ya neme gafara"
Mikewa yayi yace ni dai zan shiga gurin Momy bazan dawo tanan ba zan wuce, ki dinga barin wayar ki akunne"
Jamal na fita hawayen da take makalewa suka zubu, tashi tayi ta daga labulen window har ya shiga part din momy tana kallon shi tana hawaye"
Duk da cewa jira take Jamal yabar kasan takira deeni awaya amman yanzun sai taji kwata2 batason tafiyan shi, ko banza yanzun Jamal ya zama dan uwanta batajin kin shi kaman da"
Bayan yayi sallama da iyayen sa aka fitarmai da akwatin shi"
Harya mike Momy tace toh ina asma'u fa, nafisa jeki kirata"
Sai da ta goge fuskanta sosai sannan ta fito, duk afalo ta same su"
Momy da daddy fita sukayi suka tsaya agaban motar suna kallon yadda ake zuba kayan Jamal aciki"
Jamal ma hannu ma'u ya roko suna daf da fita ya lura kuka takeyi, ajikin bango ya mannata sannan ya fara share mata hawaye rungumeta yayi tsam ajikin shi, tare da zura bakin shi cikin nata"
Angama loda kayan Jamal amman har yanzun basu fito ba, dan haka momy ta nufi komawa ta dubo su"
Tana tura kofar tasakai, juyowa naga Momy tayi da sauri har tana tuntube"
Karan kofar ne yasa Jamal ya saki ma'u, cikin sauri ya fito daga falon ya nufi mota yayin da ma'u kebin bayan shi, tana tafiya ahankali tare da kallon kasa"
Tana zuwa gurin da momy take ta tsaya har yanzun idonta na kasa"
Cikin motar ya shiga ya zauna daddy ne zaija motar yayin da Jamal ke zaune agefen sa"
Har daddy ya tada motar Momy ta daga hannu tanawa jamal bye bye, idonta cike da kalla, juyawa tayi takali asma'u hawaye tagani yana malaluwa daga idonta"
Hannun asma'u ta jawo takaita saiti window da Jamal ke zaune"
Ido ya zuba mata sannan ya girgiza mata kai, wani hawayen ne ya sake zubowa wadda ita kanta tarasa na menene"
Hannun shi ya miko ya rike nata sannan yasa dayan hannun ya share mata hawaye, fuskan shi dauke da murmushi"
Daddy ne yayi gyaran murya sannan yace, asma'u koma gida kiji ko"
Ahankali jamal ya saketa tajuya ta nufi gida"
Daddy ne yakalli momy sannan yace toh kema wuce kuje Ku daura wa shamsudeen girki, yan zunan zan dawo"
Karfe 11:30am jirgin su jamal ya lula sararin samaniya"✋🏻
Gidan Alhaji bashir daddy ya nufa"
Aharaban Gidan yaga wani gafjejen saurayi, cikin kananan kaya masu tsadan gasky, takalmin dake kafar sa ma abin kallo ne, yana ganin shi ya shai da shine shamsudeen, idon shi sanyi da bakin Glass kwaftarere"
Alama yamai da hannu yazo cikin sauri ya bude motar ya shiga, har suka kusa gidan deeni be juya ya gaida daddy ba, bare ya gaida shi"
Dan haka daddy jefi jefi yake juyawa ya kalli deeni yayi mormushi"
Shiko deeni yama manta inda yake yayi nesa atunanin asma'u ji yake yanzun Jamal babu abin da zai nuna mishi, ko yaki ko yaso dole ya bashi ma'u, jira yake kawai ya huta yaje nemanta"
Suna isa suka sakko sannan daddy ya rike hannun deeni suka nufi cikin gida"
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
*SADAUKARWA👇🏻*
*AMINCI WRITER'S*👍🏻💋💋
*GAISUWA TA MUSAMMAN GARE KU👇🏻*
*Fadeela Lamido Fans group*
*Bugun Zuciya fans 1 2 & 3*
6⃣7⃣to7⃣0⃣
🤳🏻 Ma'u na kwance dakin nafisa taji uhun nafisan tana murnan ganin shamsudeeni"
Tsaki taja sannan ta dada gyara kwanciyarta dan yau jinta take kamar wata mara lfy, ga waya ahannunta amman ta kasa kiran deeni"
Momy ko tunda taga shamsudeen ya shiga ranta, sai dai ta kula akwai karancin tarbiya atare dashi, dan tunda ya shigo babu wadda ya gaida, kujera ya samu ya daura kafa daya kan daya"
Nafisa ko kur tamai da ido, hakanan taji yana birgeta"
Bayan sun hallara akan tebirin cin abici suna tsaka da cin abincin, daddy ya kalli deeni yace" shamsudeen baka iya gaisuwa bane?
'Dagowa yayi ya kalli daddy sanna ya maida kansa kasa yace"
Sassanun ku, ya gari yajin dadi?
Mormushi daddy yayi tare da bin deeni da kallo, zuwa can yace"
Shamsudeeni haka ake gaisuwa? Karna karajin kayi irin wannan gaisuwan bata mutanen kirki bace kaji ko?, yana da kyau idan ka samu dan uwanka musulmi kamai sallama, sannan ka gaida shi inakwana ina gajiya"
Ahankali deeni yace toh"
Daddy yaci gaba da cewa kuma irin wannan kayan dake jikin ka karka kara saka su, gobe zan baka kudi ka shiga kasuwa ka samo kaya na mutunci, gashi jamaludeen baya gari da kunje tare amman ba komai saina hadaka da drive"
Tsagal nafisa tace daddy zan rakashi"
Wani harara deeni ya waigo ya zafga mata, wadda saida yasa nafisa ta dukar dakai"
Shiko daddy fadi yake yauwa ga kanwar ka nan zata raka ka"
Bayan sun kammala ne, momy tasa Nafisa ta nunawa deeni dakin da zai zauna, tana gaba deeni nabinta abaya"
Koda suka shiga dakin wuceta yayi tare da fadin fice kiban guri shegiya munafuka"
Da mamaki ta kalleshi sannan ta juya ta fice guiwanta babu kwari"
Itako ma'u duk abinda ake tanaji, jin muryan bakon take kamar na deeni dan haka taji tunanin shi ya bijiru mata kewanshi ya dameta"
Tashi tayi ta zauna sannan tace afili Allah meyasa ka dauramin son abin da bazan samu ba, ina tsananin son deeni, inason nayi rayuwata dashi, nakuma kare dashi, bana gajiya da kallon sa, bana gajiya da sauraron muryan Sa, hawaye ne sosai yake zubowa a idon ta"
Nafisa ce ta shigo da gudu ta fada gado, tare da fashewa da kuka"
Hannu ma'u tasa ta goge hawayen dake fuskanta sannan ta juya ta kalli nafisa tace"
Nafisa menene?
Kaman jira take ta juyo ta kalli ma,u tace"
Anty Asma'u kina ganin waccan bakon daga zuwan shi ya fara duramin zagi"
Zagi? Kuma kika tsaya kina kallon shi?
Toh yazanyi babba ne fah"
Tabe baki ma'u tayi sannan tace hakane fah babu inda zakiyi nima da haka yaya Jamal yamin idan yaje gidan mu har bulala yake sawa ya dakeni"
Da gaske? Nafisa ta tambaya"
Kai ma'u ta gyada mata kawai domin kiran sunan jamal yasa tunanin sa ya dawo mata"
Har dare ma'u ta kasa kiran deeni, ga waya ahannunta amman zuciyarta babu sukuni, tunin jamal kawai take, lallai mutum rahama ne, Ashe ko gilmawan shi ma arziki ne"
Haka ta kwana da tunanin mutun 2 azuciyarta deeni da Jamal"
Washegari ma kasa kiran deenin tayi, ta rasa menene dalili, gashi dai azuciyarta tana masifan son jin muryan sa kuma tanason tasa wani hali yake ciki"
Tana daga cikin Daki taji fitan nafisa da bakon su, dan haka ta mike ta fito falo"
Kallon ta Momy tayi sannan tayi murmushi kadan tace"
Ai na dauka bacci kike, yanzun su nafisa suka fita, dakin bisu kema kiga gari"
Yake tayi kadan sannan ta dukar da kanta kasa"
Ganin haka yasa momy ta sake cewa ko Jamal yace karkije ko ina ne?
Kai ta girgiza tare da fadin a'a"
Shiru sukayi na d'an wani lokaci zuwa can, momy ta sake cewa"
Kunyi waya da jamal kuwa?
A'a ta fada tare da dago kai ta kalli momy, tambayan ta take son yi ita ya kirata ne, amman ta kasa"
Jugum sukayi kowanne da tunanin sa, Nafisa ce ta katsa musu tunanin da tashigo cikin kuka"
Jikin momy ta fada tare da fasa wani sabon kuka, arude momy ke tambayanta lfy ?
Cikin kuka tace yaya shamsudeen ne yaita zagina ahanya sannan yacewa drive ya tsaya na sauka"
Tabe baki momy tayi sannan tace toh yanzun ina samsudeen din?
Saukeni sukayi suka wuce, da kafa na dawo, kuma saida ya bari anyi nisa"
Hararanta momy tayi tare da fadi, maganin Ki kenan, daga ganin mutum sai shigemai kike, yanzun ai kya kiyaye shi"
***
Kwanan deeni uku agidan suka tafi kano shida alhaji bashir domin dauko ummi"
Bayan sun iso sun sameta jiki ya dada rikecewa, ko hutawa basuyi ba suka nufi asibiti da ita, kwananta uku sa samu sauki dan haka suka koma gida"
Washegari Alhaji bashir yace ta hada kayanta dan tafiya zasuyi da ita amman tace sam bazata ba, dagewa yayi itama ta dage, dole ya hakura, juyawa yayi yacewa deeni tashi mutafi"
Nan fah hankalin alhaji bashir ya Kara tashi domin cewa deeni yayi jeka kawai ina gurin ummina"
Shiru Alhaji bashir yayi zuwa can alhaji bashir ya kalli deeni tare da fadin bamu guri muyi mgn"
Mikewa yayi yana waiwayen ummi sa"
Ya kwashe kusan minti 30 sannan yaji Alhaji bashir ya kirashi"
Yi alwala muje masallaci, alhaji bashir ya fada tare da kwance agogon hannun shi"
Bata rai deeni yayi sannan yace"
Nifah banazuwa masallaci ad'aki nakeyin kayana, dan 'yan unguwar nan gaba dayan su munafukai ne"
Daker suka shawo kanshi ya yadda zashi masallaci, bayan ankidar ne yaji ance kowa ya zauna akwai daurin aure"
Mamaki ne ya kamashi lokacin dayaji ana daura auren ummin sa da alhaji bashir, ji yayi kaman acire masa wani gungumemen dutse ajikin sa"
Suna komawa gidan ummi suka hau shiri, duk da cewa alhaji bashir yace karsu dauki komai amman deeni saida ya kwashe wukaken shi tas"
Cikin takaice tare da dana sani alhaji bashir ya kalli deeni sannan yace"
Me kuma zakayi da wukake haka, bafa nason wannan dabi'ar yanzun ba da bane"
Ummi ce tace auta kabarsu anan karka tafi dashi"
A'a ummi akwai abin da zanyi dashi ummi, kisan zama be ganni ba, bazan barwa Jamal asma'u ba, dole zan nemesa duk inda yake, yabani kayata, wlh wlh ummi matsawar inna nunfashi bazan barwa Jamal asma'u ba' daga
ranan da nasamu nasara asma'u ta dawo gareni zan aje makami na"
Sakatoto Alhaji Bashir yayi da baki yana kallon deeni zuwa can yace"
Saratu wacece Asma'u?
Ahankali ummi ta warwarewa masa komai"
Shiru yayi na wasu lokaci zuwa can ya dafa deeni tare da fadin"
Ka kwantar da hankalin ka, indai kudi na magani zaka Aure asma'u ka neme shi, ko nawa yake so zan bashi, bukatata kawai ya saketa"
Take wani dadi ya ziyarci zuciyan deeni, bakin abban sa dayake gani ya goge tas"
Karfe goma da rabi na dare suka isa Abuja, saida suka sauke deeni agidan daddy sannan suka wuce giida"
Tunda deeni ya dawo kullum saiya fita neman ma'u, yayi dakon jiran kiranta harya gaji"
Damuwa ya fara shiga, Allah yasa Asma'u lfy take, dan yasan inda lfy take bazata bari har akwashe kwanakin nan bata kirashi ba"
Babu laifi yanzun deeni ya natsu, kulum da safe yake zuwa ya gaida daddy da momy"
Nafisa ko bata gajiya da kallon deeni, akulum tana cikin satan kallon shi"
Duk da cewa daya kalleta yake galla mata harara"
Yauma kamar kullum, deeni na zaune afalo shida daddy da nafisa"
Babu abin da deeni ke yi banda tunanin ma'u, yana takaicin wai kamar asma,u ace babu waya ahannunta, tsaki yaja kadan sannan ya dauko wayar shi"
No da ma'u ta kirashi kwanaki ya gani, ji yayi kamar ya kira, sai kuma ya tuna tace mishi na kanwar Jamal ne karya kira"
Gani yayi bazai iya hakuri ba dan wannan ce damar data rage mai danna no yayi tare da karawa akunen sa"
Dai dai lokacin wayar nafisa dake gefe ta fara kuka"
Daukan wayar tayi ta danna tare da fadin hello"
Cikin sauri deeni ya kashe wayar tare da kallon nafisa"
Itama sauke wayar tayi tare da jan tsaki"
Kara duba no deeni yayi, tabass itace dan yariga ma ya haddace no din"
Kira ya kara dannawa, wayar nafisa ta sake kara
Cikin mamaki deeni yake kallon nafisa yaya akayi haka"
Tunawa yayi da lokacin da daddy yace gashi jamaludeeni bayanan da kunje tare, take wani gumi ya fara karyo mai"
Mikewa yayi tsaye cikin matsanancin tashin hankali, juyawa yayi ya kalli daddy yace"
Daddy jamaludeen yana da mata ne?
Cikin murmushi daddy yace kardai kace min baku taba gaisawa da asma'u?
Wani irin mummunan faduwa gaban deeni yayi, take idon shi ya kada yayi jawur, wasu jijiyoyi ne suka tasomai kamar zasu tsintsinke, jikin shi na wani irin rawa"
Daddy ne ya kalle shi yace yadai?
Ajiyan zuciya ya sauke sannan ya daki bango tare da fadin, ina, billahillazi la'ila ha'illahuwa bazata sabo ba"
Daga daddy har nafisa mikewa sukayi, daddy ne ya karaso ya dafah kafadar deeni tare da fadin menene ya faru?
Babu komai ya fada yana kokarin fita afalon"
Koda ya koma dakinsa bangon ya sake duka, zuwa can ya share gumin da ya karyo mai sannan yace"
Wannan dama ce babba nasamu, da wannan damar zanyi amfani innunawa Jamal kuskuren Sa, da wannan damar ne zan turamai takaicin da sanda ma zai saketa be sani ba"
Kwashewa yayi da dariya saida yayi me isarsa sannan ya sarara"
Gurin megadi ya nufa domin yanason yasan unguwar da gidan Jamal yake"
Mamaki yayi sosai dayaji cewa wai asma'u anan cikin gidan take, dan haka ya yake shawaran da dare zaikai mata ziyara"
1:32am Nafisa da Asma'u ne kwance akan gadon dakin nafisa"
Gaba dayan su bacci suke duk su bararraje"
Ahankali deeni ya turo kofar ya shigo dagashi sai gajeren wando"
Kallon yabi gadon dashi, daga can gefe ya hango ma'u"
Takawa yayi yakai saitinta sannan ya tsaya, kurama mata idon yayi na wasu lukuta, ahankali ya aje ajiyen zuciya sannan ya tsuguna agabanta"
Gani yayi tayi fari tare da kiba kadan, ahankali yace Allah yasa baki bashi furata ba"
Murmushi yayi kadan daya tuna yadda ma'u take nonamai kyauna"
Ahankali yasa bakin shi saitin fuskanta yana hura mata isa"
Kara runtse idonta tayi sannan ta dada gyara kwanciyan ta"
Ahankali yasa dan yatsan shi awuyanta ya fara mata tafiyan tsutsa......
Heat Beat
*Mmn Yazeed*
💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
Dedicated👇🏻
*Beebee Isa*
7⃣1⃣to7⃣3⃣
Cikin bacci taji taji kamar wani abu na mata yawo ajiki"
Hannu ta fara mikewa ta shafa gurin"
Jitayi kamar ta rike hannun mutum, ahankali ta fara bude idanuwanta"
Fuskan deeni ta gani yana mata murmushi, kara mutsuke idonta tayi, sannan tasa hannu ta murza idon ta sake budewa"
Yana nan dai ayadda taganshi dazun, dan haka afirgice ta fara kokararin tashi, tare da mika hannun domin tashi nafisa"
Hannun ya daga mata alamar kul, cikin sauri ta janye hannunta tare da kara tsareshi da ido"
Da hannun ya sake mata alama ta sakko"
Batai musu ba, dan tarasa metakeyi mafarki ne, ko da gske ne"
Ahankali ta sakko deeni yana gaba tana binshi abaya, har zuka fita dakin
Jatayi ta tsaya bakinta ya kasa furta komai"
Zuwa can tayi ta mazata tace deeni kai ne? Ko kuma mafarki nake yi"
Ni ne asma,u, nine ba mafarki kikeyi ba"
Kara zero ido tayi sannan tace, yaya akayi kazo nan, deeni ta ina kashigo, dan Allah dan darajan annabi ka rufamin asiri ka tafi, dasafe zan kiraka awaya zamuyi mgn"
Ganin inda jikinta ke rawa yasa yayi dariya sannan ya fara takowa ya dafa kafadarta tare da fadin ki kwantar da hankalin ki, nasan kina da lbrn bakon da kukayi agidan nan, bakowa bane nine shamsudeen"
Cikin mamaki tare da zubuwar hawaye tace"
Yaya akayi haka ta faru"
Ahankali ya shiga warware mata komai"
Cikin sanyi taja da baya ta manne ajikin bango, tare da fadin, ina lillahi wa inna ilaihir raju,un"
Hannun deeni yasaKe dagawa yakai bakinshi, ya mata nuni datai shiru tare da waigawa ya kalli bayan shi sannan ya matsa ya dafa kafadanta"
Da saurinta tasa hannu ta zame hannun deeni daga jikinta"
Hannun da ma'u ta sauke ya kallah sannan ya daga idon sa ya kalle ta yace"
Asma'u nine fah?
Sunkuyar da kanta tayi kasa ahankali tace nasani deeni"
Hunnuwanta ya sake jawowa ya fara tafiya da ita zuwa dakin sa"
Deeni ina zaka kaini?
Dakina, akwai mgnr da zamuyi domin mu samar ma kanmu mafita"
Cikin sauri ta girgiza kai sannan tace"
Haba deeni baka tunanin wani ya ganmu, akwai fa Aure akaina, duk wadda ya ganmu tare da wannan lokacin bazai mana uzuri ba, karashi mgnr tayi cikin zubowan hawaye"
Ido deeni ya zuba mata tare da fadin me kike nufi da wannan maganar ?
Shiru tayi zuwa can tace ina nufin ka bari da safe zan kiraka awaya saimu yi mgnr"
Kallo ya sake binta dashi cikin jajayen idon sa da suka kuma jawur yace"
Asma,u kardai kice min kin fara son jamal idan kikamin haka nima bazan miki uzuri ba, wani abo ya shiga tsakanin ku ne?
Girgiza kai tayi batare da ta dago kai ta kalleshi ba"
Hannun shi yasa ya dago kanta sannan yace"
Gaya min meye matsayi na azuciyar ki?
Cikin rada tace deen kana nan a inda kake, babu abin da ya canza"
Karya ne, ada bakimin musu, yau ko nagani acikin idon ki, kina nema ne kimin taurin kai"
Bata bari ya rufe baki ba' tace yanzun da daba daya bane deen, yanzun fah agidan mijina na nake, kuma ina tare da iya.....
Batakai ga karasawa ba taji deen ya make mata baki, cikin sauri tasa hannunta ta dafe bakin, sabo da tsabar zafi sai takeji kamar hakurinta ya zubo"
Cikin fada tare da daga muryan shi sama yace"
Ni kike cewa agidan Mijin ki kike, kinsan yadda nake jin sonki acikin zuciyata kuwa? Da kin sani bazaki furta gidan mijinki agabana ba"
Ganin inda ta dafe bakinta yasashi saurin kai hannun fuskanta tare da fadin Allah yasa banji miki ciwoba, yi hakuri raina ne ya bacci, bazan iya juran ganin ki kina taraya dawani namiji bani ba, jeki ki kwanta, amman gobe da safe ki fito falo inason ganin ki ko bazamu yi mgn ba"
Har bakin dakin nafisa ya rakata sanna ya juya yana waigenta, jiyake kamar ya makaleta ajikin shi ta tayashi kwana"
Ya wuce tsakiyan falo yana daf da fita momy tafito"
Daidai lokacin da deeni ya taba kofar zai fita"
Shamsudeen Momy ta fada cikin matsanancin mamakin ganin shi wannan lokacin"
Cikin dakiya yace na'am momy sannan ya waigo yana kallonta"
Agogo ta kallah karfe 3:34am dan haka ta juyo takalshi tace"
Shamsundeen me kakeyi cikin daren nan afalo tun dazon nakejin motsi"
Murmushi yayi tare da shafa keya sannan yace"
Momy waya nayi"
Oh tafada sannan tayi murmushi ta juya daki"
Ma'u ko tana shiga daki ta samo nafisa zaune abakin gado, jitayi gaban ta ya fadi"
Wani irin kallo nafisa ta mata sannan tace ina kikaje kuma?
Toilet ta fada tana kokarin hawa gado"
Cikin mamaki nafisa ta bita da kallo, zuwa can tace Amman ga toilet adaki me zaikai ki waje?
Jawo bargo tayi tare da fadin kofar ce taki buduwa"
Nafisa batakara cewa komai ba ta haye gado ta kwanta"
Ma,u ko bata iya runtsawa ba tunaninta ta wacce hanya zata bollowa lamuran ta, hakika ayanzun tana neman shawara sai dai babu wadda zata iya tunkara da wannan zancen"
Kuma tana tunanin kar mutuncinta ya zube a idon duniya, tasani deeni ba abun kunya bane awajen shi, dan angan su tare, amman ita tasani ganin su tare masifa zai janyo mata babba tare da bakin fetin da batasan ranar fitanshi ba, wata kila abba da mama su tsine min duniya ma zata zageni, da auren wani akaina kuma ina sauraran wani, babu wadda zai fahimce ni, koda bawani abu muke aikatawa"
Cikin hawaye cabe cabe take,cikin zuciyarta tace Allah ka kawo min mafita, Allah kasa nafi karfin zuciyata, inason deen kuma akwai aure akaina"
Washegari tashi tayi bakinta ya kunbura, saboda dukan da deeni yayiwa bakinta, idonta maha sakamakon kukan da takwana yi"
Nafisa ko kallon ma'u kawai take amman acikin zuciyarta bata yarda da zancen ma'u ba, gashi yadda taga fuskanta ya nuna mata akwai matsala, dan haka tunda safe taje ta kira momy"
Yadda momy taga fuskan ma'u abin ya bata tsoro, dagota tayi tana kara kallon fuskanta"
Asma'u menene ya sameki abaki?
Bugewa nayi cikin dare na tashi zani bayi shine ban sani ba nabige"
Shiru momy tayi tana kallon asma'u zuwa can tace toh idonki fah?, naga duk kinci kuka ga dukkan alama bakiyi bacci ba, kuma begewa ai bazaisa ki kuka haka ba, wani abu na damun ki ne?
A'a
Toh ko kina tunanin mijinki ne?
A'a ta sake fada da saurinta"
Toh ki gayamin abun da ke damun ki idan ba hakaba to tunanin Jamal kike"
Shiru tayi kanta akasa domin bazata iya gayawa momy abonda ke damunta ba gara aje atunanin Jamal din take"
Momy bata kara cewa komai ba kallon ma'u kawai take tana girgiza kai, zuwa can tace"
Asma'u ki kwantar da hankalin ki kamar yau ne zakigan shi ya dawo, kodan kinga har yanzun be kira bane hankalin ki ya tashi?, nima da hankali na ya tashi amman daga baya daddyn ku yaje Office dinsu dakenan Abuja antabatar mai suna nan lfy gurin da suke ne babu service"
Duk da ba haka bane azuciyar ma'u taji daddin jin lbrn Jamal yana lfy"
Haka momy taita lallashin ma'u hartaga kaman hankalinta ya kwanta sannan ta tafi"
Momy na fita nafisa ta fara dariya saida tayi me isarta sannan tace"
Ashe dai yaya jamal nada matsaye, amman kuke nuna kamar baku damu da junan ku ba"
Mikewa ma'u tayi ta nufi toilet batare da ta kalli inda Nafisa take ba"
Wunin ranan ma'u ta kasa fita falo, dan gudun kar wani ya fahinta dan tasan halin deeni"
Shiko deeni afalo ya yuwuni, sallah kadai ke fiddashi, har momy ta fahinci kamar akwai abin da yake jira dan motsi kadan yake jan tsaki tare da kallon hanya"
7:30pm ma'u na zaune daki ta takure guri guda, ga abinci da nafisa ta kawo mata agefe ta kasa ci, hawaye ne yake zubo mata ta gefen idonta, bakomai ke tada mata hankali ba illah gudun bacin sunanta ta tabbata deeni zai iya dawowa adaren yau, dan haka dole ta nemi mafita"
Nafisa ce ta shigo ta tabi ma'u da kallo tare da fadin"
Lallai abin naki babba ne, saboda tunanin yaya kike kin cin abinci"
Tsaki taja kadan sannan tace"
Wai nafisa meyasa ba'a rufe dakin nan?, nifa gaskiya tsoro nakeji"
Mikewa nafisa tayi tare da fashewa da dariya sannan tace"
Bana kullewa, kuma ni ba yaya bane bare kimin shagwaba"
Fita tayi tabar ma'u dabin bayanta da kallo, sanna ta share hawayen da ya gangaro ma"
Nisa tayi da tunani zuwa can ta yake shawaran kiran deeni domin tasan indai bata kirashi ba, babu abinda zai hanashi dawowa yau"
Bugu 2 ya dauka tare da fadin"
Asma'u sai yanzun kikaga damar kira na?
Cikin sanyin jiki tace yau banajin dadi ne"
Meke damunki? Koda yake ma barshi Anjima zanzo indubaki tunda kinki zuwa na ganki.....
A,a deeni dan Allah karkazo, koma meye kabari sai yaya jamal ya dawo, tunda yace bazai zauna dani ba, dan Allah deeni kayi hakuri nasan bakaji dadin mgnta ba, kafin yaya Jamal ya tafi yamin gargadi sosai tare da nunamin karnamai wasa da Aure"
Wani kara ma'u taji alamun deeni ya daki wani abu, cikin fada yace"
Ni kike gayawa Jamal ya baki umarni?, atunanin ki ni zan saurari umarnin sa ? Yaci uwassa dan uban sa, me kike nufi kina nufin kinason Jamal yanzun kuma zakibi umarnin sa?
Hawaye ta share sannan tace"
Bahaka bane deeni, narasa inda zansa kaina, inajin tsoron fushin uban gijina, wannan mgnr da mukeyi yanzun haramun ne, deeni kar akamani da wani laifi ayanzun abba zai tsine min duniya zata kalleni abaibai, dan Allah kayi hakuri mubi komai ahankali"
Asma'u kin daina sona ne?
A'a haryanzu kana nan inda kake amman kabari mubi komai ahankali"
Ajiyan zuciya yayi sannan yace"
Asma'u dan Allah karki gujeni idan kika gujeni bansan inda zan saka kaina ba, sonki acikin jinina yake, daga ranan da kika gujeni zuciyata zata iya bugawa, wata kila na rasa rayuwata, asma'u duk abinda kikaga nayi ba laifina bane laifin son da nake miki ne, sonki ya shigeni batare da yayi shawara dani ba"
Ahankali tace deeni?
Na'am asma'u
Nace mezai hana muruki Allah idan alheri ne atsakanin mu ya kawo mana mafuta, idan ba alheri ya canza mana da mafi alheri"
Jiya yayi gaban shi ya buga, cikin fada yace karke sake min irin wannan mgnr, ya zaki dinga mana muguwar addu'a idan bazaki iya furta alheri ba kiyi shiru kawai, kuma bari kiji ni bazanbi umarnin Jamal ba, idan har bakison nabiyoki dakin Nafisa to ki koma part din Jamal gobe"
Amsawa kawai tayi batare da tayi tunanin komai ba, da haka sukayi sallama"
Kara kudundune manta tayi, tana zubar da hawaye tare da rokon Allah ya kawo mata agaji"
Kira ta sakeji ya shigo cikin waryarta azabure ta mike dan atunaninta deeni ne"
Bakuwar no ta gani cikin sauri ta dauka tare da sallama"
Muyar Jamal taji cikin sanyi murya yana amsawa"
Shiru sukayi gaba dayan su, zuwa can Jamal yayi ajiyan zuciya sannan yace"
*Husna* ya gida?
Lfy lau ta fada ahanlkali"
Shiru ya sakeyi hartayi tunanin koya kashene"
Gyaran murya yayi sannan yace"
Momy tacemin kin bige baki, garin yaya?
Shiru tayi harya gaji da jira, jiyayi shirun yayi yawa dan haka yace"
Bazakiyi mgn ba?, to shigenan ki dinga tafiya ahankali Allah ya sauwake, kuma ki daina yawan tunani, muyi waya da usman yanan zuwa acikin satin nan shida dada"
Dadi taji ba kadan ba cikin murna tace Allah ya kawo su lfy"
Shiru suka sakeyi zuwa can Jamal yace"
*Husna* kinajin sanyi kuwa?
Da saurinta tace a'a"
Ajiyan zuciya ya sauke sannan yace"
Niko sanyi na yawan damuna kibani shawara ya zanyi ne?
Rasa inda mgnr shi ta nufa tayi dan haka tamai shiru"
*Husna* ya kikayi shiru?
Ahankali tace toh ka rufa mana....
*Husna* kona rufa jinake kamar ana karamin, tunda nake bantajin abin da nakeji yanzon ba"
Toh kaje asubiti abaka magani mana"
Ganin bata gane inda ya nufaba yasashi fadin to shikena zanje idan bemin ba saiki bani wata shawaran sallam sukayi harta kashe ta sake ganin wani kiran ya shigo"
Dauka tayi taji Jamal na fadin mantawa nayi bacce kimana addu,ar samun nasara ba, kuma idan namiki wani abu ki yafimin"
Tabude baki zatayi mgn taji ya kashewayar hakanan taji gabanta ya fadi, sake kiran no tayi amman yaki tafiya, tsin tan kanta tayi da addu'an Allah ya dawo dasu cikin kushin lfy"
******
Washegari da yamma deeni ya sake kiran ma'u tare da jajjada mata idan bata koma part din Jamal ba babu abinda zai hanashi zuwa anjima"
Cikin kuka take cemai Jamal ne yace ta zauna anan
gurin momy"
Dagewa yayi tare da nuna mata akwai mgnr da zasu yi me mahim manci, kuma aranan ne zasu nema ma kansu mafuta"
Hankalin ma'u rabuwa yayi kashi biyu, wata zuciyar na cewa taje wata na cewa a'a" kai wata ma zuciyar cewa take kodai zaki gaya momy ne"
Mikewa tayi ta fito falo, momy ta gani zaune tare da deeni, wani irin kallo ya mata, sannan ya mata alama ta gyawa momy zata koma part din Jamal"
Babu abunda gabanta keyi sai duka tara tara ahakali ta bude baki tace......
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
7⃣4⃣to7⃣7⃣
💐💐💐 Momy ni yau adakin ki zan kwana"
Da mamaki momy ta kalleta sannan ta danyi murmushi kadan tace"
Halan Nafisa na takura miki da shegen surutunta?
Kin kallon inda deeni yake tayi tace a'a bahaka bane, akwana biyu inayin mafarkai idan na farka ina kasa bacci tare da tsoron dakin"
Shiru momy tayi zuwa can tace"
Asma'u kinayin addu'oi kuwa?
Inayi momy"
Tsakin da deen yaja ne yasa duk suka kalleshi"
Momy ce ta lura harara yake zafgawa ma'u, dan haka ta kira sunan shi sannan ta nuna ma'u tare da fadi"
Wannan itace Asma'u matar jamaludeen dan uwan ka, nasan baku san juna ba ko?
Wani haushi ne ya kama Jamal wadda yasashi mikewa batare da yasan lokacin ba"
Kallon shi momy tayi tace wani abu ne? Naga inakan maka mgn ka mike"
Daker ya iya sarrafa kanshi ya koma ya zauna sannan ya hura iskan dake bakin sa yace"
Naganta momy gsky yayi dacen mata kuma sunan ya dace da ita"
Murmushi momy tayi tare da fadin wlh kuwa nima ina farin ciki da kasancewan ta matar jamal, kaima Allah ya baka yariya me hankali kamarta"
Ma'u banda dukan uku uku babu abunda kirjinta kemata, duk atsorace take, kin yadda tayi su hada ido da deeni duk da ta lura abun da yake so kenan"
Muryan shi taji yana cewa ameen momy amman nima inada yariyar da nakeso itama sonanta Asma'u tana da kyau sosai kamar waccen Asma'u"
Ma'u jitayi hanjin cikinta na tsintsinkewa addu'oi take karantowa acikin zuciyarta, tare da kerman jiki"
Itama momy haka kawai taji bataji dadin zancen deeni ba, amman dama tuni ta lura lamarin shi akwai gyra, juyawa tayi tace asma'u shiga dakina ina zuwa"
Mikewa tayi badan ranta yaso ba dan batason tabar deeni da momy dan tana gudun karyaje ya fadi wata mgnr da zata jawo illah arayuwarta"
Tana daf dashiga dakin taji muryan deeni yana cewa"
Allah yasa yadda kuke sonta itama tana sonku haka"
Wani irin kallo momy ta masa sannan tace"
Meyasa kace haka?
A'a na fadane kawai momy, momy kinsan menene?
Saika fada"
Kwantar da kanshi yayi ajikin kujera sannan yace"
Yariyar da nakesonta take sona babanta baya kyaunata yaki bani ita sannan ya gayamin wasu kalamai da suka girgizani, duk da cewa duk abin da ya fadin haka ne, amman naji zafin sa sosai soboda kalmar da yayi ammafani da ita wajen mgnr sa"
Nisawa yayi kadan Momy na sauraron sa, sannan yace gaba da cewa"
Wlh tsohon nan kawai yaci darajan son 'yarsa da nake amman wlh dasai na zubar masa da hakora"
Baki momy ta rike tare da fadin shamsudeen abin naka har yakai haka"
Wani irin bazawaran murmushi deeni yayi sannan yace Momy kenan, wlh ina tsananin son 'yarsa banajin zan iya barinta jinina da nata gauraye yake, banzan iya barinta ba momy rasata na nufin tsayawar numfashina
Duk abinda deeni ke fada ma'u na makale tanaji innalillahi wa inna ilaihir raju'un kawai take ambata tare da fadin wacce irin masifa ce wannan Allah ka kawo min mafuta"
Muyar Momy ta tsinkaya tana cewa Shamsundeen inason na fahimtar dakai wani abu guda daya, ka dauka kamar kana mgn ne da mahaifiyar ka wacce ta tsuna ta haifeka"
Maida hankali deeni yayi gurin Momy"
Tana kallon cikin idon shi tace Shamsudeen waye ya gaya maka anaja da iyaye? tunda mahaifinta yace bazai bakaba toh kayi hakuri kabar masa 'yarsa"
Cikin sauri yace momy bashi da wani dalili, bakinciki kawai yake min, ya dauki laifin da banawa ba ya daura min, momy daman laifin wani nashafar wani?
Tuni momy ta dago inda zancen deeni ya nufa, dan haka taji tausayin sa ya kamata"
Shima nan danan idon shi ya kankanci ranshi ya dada baci jikin shi har wani rawa yakeyi"
Mikewa momy tayi ta koma kusa da deeni ta zauna sannan ta jawoshi jikinta kamar yadda takewa jamal idan ta kula yana cikin damuwa"
Shafa kanshi take tare da fadin....
Laifin wani baya shafan wani shamsudeen amman na saratu dana bashir dole ya shafe ka"
Cikin mamaki deeni ya daga kai ya kalli momy"
Nasan komai deeni Saratu da Bashir sun aikata babbab kuskare, Idan su ya rufe sunbar mummunan tarihi, sannan bayan wannan tabo da suka maka aduniya, basu baka tarbiya yadda ya kamata ba"
Kallon deeni tayi da hawaye suka fara zubowa kan kuma tunshi sannan taci gaba da cewa"
Shamsundden bazan boye maka ba, gsky daya ce, duk mutumin da yake da mutunci ba zai haifi 'yarsa ya mata tarbiya maikau sannan ya dauka ya baka ba"
Haryanzun kallon Momy deeni yakeyi hawaye shabebe a idon sa"
Kafadar shi Momy ta kama sannan tasa idonta cikin nashi tace,
Ba'ina gaya maka bane dan nabata maka rai ko kuma na tunzuraka kaji haushin iyayen ka a'a abinda ya faru ya riga ya faru, ina gaya maka ne domin kasan inda zakasa gaba, ma'ana ka gyara halayen ka da kanka"
Yau koda ace kana da cikeken asali amman kana cikin rin wannan rashinji, duk da haka babu wadda zaiso yaba ka yarsa, saboda babu mutum me mutunci dazaiso ka zama sirikin sa"
Da ace kuma bayan haihuwarka iyayen ka sunyi nadama suntsaya sun baka tarbiya tare da ilmin addini tare dana zamani sosai, koda wani zai nemo asalinka wani bazai nemo ba, koda ace anbinciko ma idan wani be maka uzuriba wani zai maka, hawayen dake idonshi ta fara sharemai tare da fadin dan Allah ka gyara dabi'un ka kuma idan yariyar rabon kace zakaga ka sameta"
Gargiza kai yayi tare da fadin indai hakane momy sun cuceni, kuma idan sukai sular rabani da asma'u bazan yafe musu ba har abada"
Karkace haka shamsundeen"
Jikin deeni har rawa yakeyi wajen fadin wlh momy ina masifar sonta, banaso na rasata, wlh momy daga ranan danaga anyi nasara rabani da ita zan kashe Kaina.....
Kaji irinta ko ?, meyasa zaka nuna kai bakasan kaddara ba, Allah yana jarabtan bawan sa ne domin ya gwada imanin Sa.....
Bebari momy ta rufe baki ba yace"
Toni meyasa za'a jarabani ta wannan hanyar yaseeen bazan iya dauka ba......
Cikin sauri Momy tasa hannunta tarike bakin deeni sannan tace toh ya isa haka mubar zance, zan tayaka addu'a idan yariyar alheri ce agareka Allah ya baka, idan....
Taren numbashinta yayi da fadin, momy bar addu'an ki yaka daidai nan"
Kallo kawai momy ta bishi da shi sanna tace Allah ya yaye maka abin da ke damun ka, akwai wani malami daya ke mana karatu da, gobe zai dawo ya fara mana karatu ni dakai"
Kai kawai ya daga sannan ya mike ya fita"
Duk hirar su ma'u taji, tun bata fahimta ba, hartazo ta fahimci inda zancen yasa gaba, daki momy ta shiga ta zauna tare da tsananin tausayin deeni acikin zuciyar ta tace inama zan aure deeni da na mantar dashi bakin cikin dake cikin zuciyar shi"
Share hawaye tayi sannan taci gaba da cewa"
Tayaya hakan zai faru? Yaya zanyi insami deeni? Dakanta taba kanta amsa sai Jamal ya sake ni"
Hawaye ta sake sharewa sannan tace anya kuwa Jamal zai sake ni, wata zuciyar ce tace shifa ya fada, yace bazai iya rayuwar aure dake ba, sannan yace shida yaya bashir basu da babbaci harcewa yayi shi mata basa hawa gadon sa"
Toh meyasa shi yahau naki gadon ? Kuma har yayi wasu abubuwa, wannan yanuna abinda Jamal ya fada ba gsky ba ne, kuma kafin tafiyan shi ya jajjada min karna mai wasa da aure"
Shiru tayi zuwa can tace zaiyi wahala Jamal ya sake ni, hakika da anba mace damar auren maza biyu dasai dai jamal yaji na kara aure da deeni"
Daidai lokacin Momy ta shigo, bin ma'u tayi da kallo sannan tace Asma'u daga yau idan zaki fita falo kisamu karamin hijjabi ko mayafi ki riga sanyawa, dan kinga yanzun gidan bamu kadai bane"
Saida gabanta ya fadi jin kalaman momy, saitake ganin kota fahinci wani abune akalaman jeeni?
Tokawai tace sannan ta dada share hawayen dake makale a idonta"
Adakin momy tai zamanta, momy ma bata kara ce mata komai ba, daddare nafisa ta biyota da abinci, bayan sun gama ci tace toh tashi muje mukwanta"
Kememe taki zuwa nafisa tai nacin ta har tagaji ta fice"
Kashe kawayarta tayi gaba daya dan gudun kar deeni ya kirata"
Ganin yadda ma'u ke firgice daga taji motsi kadan ta kalli kofa dan haka Momy taje ta rufe daki"
*****
Washegari ma batace zata fitaba tana nade adaki"
Dafisalin karfe 1:12pm Momy ta shigo takalli ma'u tace Asma'u taso maza kinyi bako"
Atsora ce ma'u ta mike tare da fadin waye?
Cikin ido momy ta kalleta sannan tace wai Asma'u meke damunki? anya kuwa kinayin addu'oi?
Inayi ma'u ta fada tana kokarin saka hajjabi"
Harta fara tafiya Momy tace bakon yana part din Ku"
Gabanta taji ya fadi sosai, Allah yasa ba deeni bane"
Tana tafe tana addu'oi, tura kofar tayi tare da sallama tana raba ido"
Yaya jamal ta gani zaune cikin kaki, da alama ya dade da zuwa, wani farin cikine ya kamata harta sake murmushi batare da tasan lokacin daya fitoba"
Dama yaya Usman ya damu dani? Daman yaya usman na sona? Hawaye taji ya cika mata ido"
Fuskar usman dauke da murmushi yace karaso ki zauna mana"
Cikin sanyin jiki ta karasa ta zauna, tare da matso hawayen dake makale a idonta"
Bayan hannunta tasa ta share hawayen sannan ta shiga gaida usman tare da tambayan shi mutanen gida"
Cikin sakin fuska ya amsa tare da tambayar lfyr ta"
Kula yayi ma'u kuka take dan haka ya tsareta da ido tare da fadin"
Asma'u yaya haka?, ko bakiyi farinciki da zuwana bane?
Bahaka bane, naga baka taho da dada ba, kuma yace min tare zakuzo?
Murmushi usman yayi kadan sannan yace waye yace miki tare zamuzo"
Idonta akasa tace yaya Jamal"
OK eh da tare zamu taho amman tace bazatazo ba"
Hawaye ne yaki tsayawa a idon ma'u zobowa kawai yake tare da ajiyan zuciya"
Kallon ta Usman yayi acikin zuciyan shi yaji tausayinta dan haka ya daga wayan yana kiran dada"
Mika mata wayar yayi tare da fadin ga dada"
Amsan wayar tayi ta kara akunnenta muryan dada taji tana fadin Usman katafi gidan tame karan ne koko kaima ka fasa"
Dada? Ma'u ta fada ahankali"
Wiiii !! , takwara ce?, kice harya iso"
Hawaye ta share sannan taja majina eh, meyasa kikaki biyo yaya bayan angayamin zakizo kuma harna sarai"
Wa? ni ? Allah sunturu bukui, ai idan kika ganni alahira kaini aka yi, haka kurun, ku hada baki dame kare ku kasheni ? aini har yanzun ban yadda dake ba takwara, saina ganki da tsohon cikin Jamal"
Guntun tsaki ma'u taja sannan ta kara share hawaye tace"
Dada me kika maidani?, dan Allah ki daina irin wannan mgnr ni mahaukaciya ce?
A'a da hankalin ki amman idonki ya rufe baki ganin kowa sai me kare"
Hmmm dada yanzun yashe zakizo?
Sai ranan da kika haihu zanzo namiki wankan jego"
Wani haushi ne ya turnuke ma'u, dan haka tace toh kibarshi karkizo ma, kuma ni kidaina cemin tame kare, ko mun hadu ahanya ma karki nuna kin sanni....
Batajira me dada zatace ba ta kashe wayar sannan ta mikawa usman"
Dariya ce cike da cikin Usman Amman ya dake bakace abin ya bashi dariya ba"
Amsan wayar yayi tare da fadin yau kwanan Jamal nawa da tafiya?
Dogowa tayi ta kalli yaya usman sannan tace,
Zaikai sati 3"
Jinjina kai yayi sannan yace"
So nawa kika kirashi awaya?
Guntun hawayen ta share sannan tace aiko ankira ba samun shi"
Shiru usman yayi zuwa can ya fara mata nasiha cikin kwaciyar hankali"
Jikin Asma'u yayi sanyi sosai sabo da yadda usman yake xayyano mata girman miji agun matar sa, duk da duk abinda ya fadi ta sansu amman ya kara farkar da ita"
Babu abin da take tunawa sai yadda Jamal yaita mata magiya adaren da zai tafi, yanzun kenan mala'ikun Allah sun tsine min?
Hawaye ne suketa zubomata babu kyaukyautawa"
Bayan usman ya sarara sai ya shiga neman layin jamal"
Saidai babu sa'a domin wayar sa kashe take dan haka ya fara neman dayan layin"
Saida ta kusan katsewa sannan ya dauka, cikin dariya taji suna gaisawa sannan ya gayamai gashi agidan su"
Gani kawai tayi usman ya miko mata waya, dan haka adaburce ta karba tasa akunnenta"
Gaidashi tayi saida ya dade kafin ya amsa sannan yace ya bakin, kiji sauki?
Eh kawai tace idonta akasa"
Shiru sukayi dukkan su zuwa can Jamal yace *Husna* ?
Saida Asma'u ta lumshe idon saboda muryar da Jamal yayi amfani da ita wajen kiran sunan ta"
Daker ta iya amsawa sabo da yadda muryansa ya kashe mata jiki"
Ahakali yace sanyin nan fa har yanzun inajin shi, wanne shawara zaki sake bani?
Kasa mgn tayi dan haka ta kashe wayar, Cikin sauri ta mikawa usman, saidai kafin wayar taje hannunsa Jamal ya sake kira"
Janye hanunsa yayi dan haka ta maida wayar kunnenta"
Husna meyasa zaki kashemin waya?, ko kina kunyar usman ne? Idan kunyarsa kikeji tashi ki koma daki"
Kallon inda usman yake tayi ganin tayi hamkalin shi nakan wayar da take hannusa, dan haka tacewa Jamal a'a
Toh kina jina nacemiki sanyi na damuna, da daddare bana iya bacci sosai sai naji gadon yamin fadi, wani lokacin saina rungumi filo nakejin dadi"
Sai yanzun ta fqra dago inda yasa gaba, shiru tamai dan batasan mezatace ba"
Husna ya kikayi shiru?, wlh na kosa na dawo, Husna anya kuwa bazan ajiye aikin nan ba"
Shiru yaji dan haka yasashi fadin Husna kinajina kuwa"
Ummm ta fada tare da kallon yaya usman"
Jamal ne yace meye ummm?, to shikenan tunda bazaki min mgn ba sai an jima, amman ki shirya idan na dawo akirjin Ki zan rinka kwana"
Cikin sauri ta kashe wayar domi mgnr Jamal ta girmi kunnuwanta, wai meyasa maza basu da kunya?
Da misalin karfe 4:34pm usman yayi sallama fitowa yayi nafisa da asmau nabinshi abaya rike da kayan da momy ta hada akaiwa mama"
Daidai lokacin Deeni ya fito ya wuce su ma'u ya angaje Usman"
Saura kadan usman yakai kasa cikin zafin nama ya jawo wuyan rigar deeni tare da shake shi da ita"
Kallon shi yayi sai ya ga kamar ya taba ganin wanna fuskan amman ya rasa ina ya santa"
Cikin fada usman yace waye kai?
Wata irin dariya deeni yayi , nafisa ce ta ruga cikin gida ta kira momy, itako ma'u tuni cikinta ya burga"
Cikin wata irin murya deeni yace sakarni"
Daidai lokaci Momy ta fito aguje deeni tarike tare da fadin haba shamsundeen menene haka?, sirikin ka ne fah yayan matar jamal y kawo mana ziyara"
Tsaki yaja sannan ya fincike rigarshi ya fita"
Hakuri momy ta bawa usman cikin bacin rai yabar gidan"
Har yayi nisa atafiya ya tsaya ya fara neman no Jamal domin yaji wanne dan rainin hakali ne agidan su"
Ya dade yana gwada duk layikan shi amman duk akulle suke, haka ya hakura"
Tundaga ranan deeni ya daina ko kallon inda ma'u take, amman kullum fuskan shi murtuk"
Wani lokacin d'aki yake shiga yaci kukan shi ya kushi domin zuciyar shi na gayamai Asma'u amanar shi zataci"
Akwai wani abu da ya kudura aranshi dan haka yabarta ta gama haukanta"
Dama kawai yake nema domin ya nunawa asma'u ba'a hada soyayyan shi data kowa"
Ganin yadda deeni keyi ya fara tsorata ma'u ayanzun babu wadda take son gani banda yaya jamal, dan haka ta yanke shawaran kiranshi ta gayamai, ko zata samu saukin halin da take ciki"
Tun safe take neman no Jamal har dare bata shiga ba"
Tsayon sati biyu kenan kulum saita neme no Jamal Amman bata samun shi kullum dakin Momy take kwana bata iya sakewa acikin gidan gada daya atakure take"
Ranan da Jamal yacika wata biyu da tafiya , abun ya fara damun ma'u tun daga ranan da yaya usman yazo bata kara samun no Jamal ba, dan haka yau ta yanke shawaran samun momy da zancen"
Afalo ta same momy ta rafka uban ta gumi gefen idonta hawaye ne kwance"
Zama ma'u tayi jikinta asanyaye tare da fadin momy lfy kuwa?
Zabura momy tayi domin ita batasan da shigowar ma'u ba nan danan ta kakaro murmushi tare da fadin lfy lau asma'u"
Shiru tayi zuwa can, tace momy kulum na kira wayar yaya Jamal bana samun sa"
Adaburce momy tace wata kila network ne amman ni kullum muna waya, akwai abinda kike sone?
Girgiza kai tayi tare da fadin nagadai kwana biyu be kira bane"
Gefe ta koma ta takure gsky tanaso jin muryan Jamal sannan ta gayamai deeni nacikin gidan su" tasan kome yake har yaji deeni na gidan nan zai bari ya dawo"
Tanacikin wannan tunanin wayarta tayi kara, no usman ta gani cikin sauri ta dauka"
Tana dauka taji usman na fadin Asma'u Jamal ya canja no ne?, wadda nake dashi yafi wata akashe"
Take taji gabanta ya yaken ya fadi kafafuwanta rawa kawai su, muryanta na rawa tace"
Yaya nima rabon da muyi waya tun randa kazo"
Me ?, Taji ya fada atsorace, tare da kashe wayarsa"
Hakanan taji hawaya na zubo mata, anya kuwa lfy amman momy tace yana kiranta, shiru tayi zuwa can tace"
To meyasa naga momy na share hawaye kai Jamal babu lfy"
Mikewa tayi ta shiga cikin dakin momy, agado ta sameta tana zaune sai share hawaye take idonta jawor"
Ji tayi kafafuwanta sun kasa daukanta zamewa tayi tai zaman dirshan akasa daidai lokacin nafisa ta shigo itama idonta jawur, dan haka ma'u ta fashe da kuka"
Daga momy har nafisa kan ma'u sukayo tare da kokarin boye hawayen su"
Cikin kuka tace momy ku gayamin abin da yake faruwa ku cireni aduhu, ina yaya Jamal yake ? Idan wani abu ne ya sameshi agayamin "
Jawota momy tayi ta rungume sannan tace, Jamal na nan lfy lau....
Umm umm momy ba lfyrsa lau ba wayar sa tafi wata bata aiki"
Waye ya gaya miki, ki kwantar da hankalin ki, yanzun inda suke ne babu daman waya, kuma ai wata 7 yace zaiyi dukka fa wata 2 kenan da tafiyar sa memene abin damuwa?
Daidai lokacin daddy ta alhaji bashir suka shigo ko wanne hankalin shi atashe"
Ganin momy rungume da ma'u daddy yace yaya aka yi?
Yake momy tayi sannan tace tafara damuwa darashin kiran mijinta ne"
Shima yake yayi sannan yace ai yanan lfy, Meye abun damuwa, juyawa sukayi suka fita cikin sauri momy ta zame ma'u tabi bayan su"
Ma'u naganin fitan momy ta bude jajayen idonta ta kalli nafisa sannan ta riketa katam tace"
Hardake ake boyemin ko?, dan Allah ki gayamin gsky menene ya same shi?
Bakomai nafisa ta fada tana kallon cikin wayarta"
Cikin kuka ma'u tace shikenan amman nasan ba gaskiya kuka fada ba, bayan naga momy tana kuka kema kina kuka.....
Wayarta ce tayi kara tana kallah taga yaya usman cikin sauri ta dauka"
Ba momy wayar abinda yaya usman yace kenan, cikin sanyin jiki ta nufi hayar falon kamar me koyon tafiya
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
[22:52, 1/2/2018] +234 806 744 6138: 💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
7⃣8⃣to8⃣0⃣
💘💘💘 Tun kafin ta karasa takejin muryoyin su daddy, amman suna ganinta sukai shiru"
Cikinta babu kwari ta mikawa momy tare da cewa yaya usman zaiyi mgn dake"
Bayan momy ta amsa wayar ma'u gefe ta tsaya kirjinta na dakan uku uku"
Da ido taga daddy ya kalli momy cikin sauri ta mike ta shiga part din daddy"
Bayan momy tabi da kallo sannan sannan ta juya ta kalli daddy idonta kwalkwal kamar zatai kuka"
Daddy yi yayi kamar be ganta ba, ta dadde tsaye momy bata fito ba dan haka ta juya ta koma daki"
Nafisa na zaune ta tallabe kumatunta da duk hannuwanta biyu, ga wayarta agefe tanata tsuwa"
Karasa tayi ta dauki wayar ta mika mata tare da fadin idan kin gama tunanin ana kiranki awaya"
Azabure nafisa ta dauki wayar, harara ma'u ta bita dashi sannan ta koma gefe tayi tagumi"
Tundaga ranar gidan ya zama kowa babu walwala, bama kamar momy da take wuni dakin daddy, tsakanin nafisa da ma'u ko zaman jigun suke"
Usman be sake kiran ma'u ba amman tana yawan jin suna waya da momy"
Ahaka har aka kwashe wata hudu da tafiyan Jamal"
Zuwa wannan lokacin hakali Momy yafi na barawo tashi, harta fara tunani danme za'a boyewa ma'u daddy ne me karfin halin cewa kar agaya mata bari insha Allahu zai dawo"
Deeni ko besan biken da ake ba duk da cewa yanzun yana yawan ganin babanshi na zuwa gidan amma besan meke kawoshi ba"
Burin shi be wuce yaga samu damar da yake jira ba, yasan daga ranan da yasamu damar shikenan ma'u ta zama mallakin sa, Dan haka ya barta ta gama guje gujenta, ko Jamal dawowa yayi baxai hanashi abin da yayi niyya ba"
Duk da dabi'un shi sun fara canzawa amman sonta na nan makale azuciyan shi, kuma yasa ma'u ma tana kyaunar sa so take kawai ta tursasa kanta wajen yiwa mahaifinta biyayya, amma bawai son Jamal take ba"
Itako ma'u abin duniya ya isheta, tarasa dalilin damuwan ta
Hakanan takejin ta kosa tasan wani hali Jamal ke ciki, tare da tsananin son ganin sa, meyasa nakejin haka ?ma'u ta tambayi kanta, meyasa na damu da rashin jinsa?, haka na nufin inason Jamal kenan?
Girgiza kai tayi tare da fadin ba sonshi nakeba, jimamin sa kawai nake amatsayin sa na dan uwa musulmi kuma aminin yaya usman"
Amman meyasa yanzun nabar tunanin deeni, ko haduwa dashi bana fata, ayanzun Jamal kawai idona keson gani"
Tana cikin wannan halin taji hayaniyan mutane afalon cikin sauri ta fito"
Wata dattijuwar mata ce tare da wata yariya budurwa zatakai sa'ar nafisa, daidai lokacin data shigo falon taji matar na fadin Allah ya bayyana shi"
Runtse idonta tayi tare da fadin nashiga uku"
Ganin inda ma'u ta runtse ido yasa momy ta washe fuska tare da fadin"
Wannan itace Asma'u matar Jamal tunda akayi biki baku haduba shikuma be kawo miki itaba"
Wani irin kallo matar tawa ma'u, muryan momy taji tana fadin asma'u wannan itace abokiyar zamana, sannan ta sake nuna budurwan dake kusa da ita tace wannan kuma kanwar Jamal ce"
Hakanan ma'u taji kwata kwata basu mata ba, tunda tazo gidan bata taba ganin suba saiyau"
Gefe ta nufi zama cikin sauri momy ta mike ta jata daki, dan batason ta fahimci halin da ake ciki"
Kallon momy kawai take amman tasan dole akwai abin da ya faru, ta kula ita kadai ne abason ta sani, hawaye ne suka zubo mata tasa hannunta ta share sannan ta kalli hawayenta dake hannunta tace"
Sai yaushe zan daina kuka? Sai yashe hankali na zai kwanta?
Wata zuciyar ce tace sai ranan da Jamal ya dawo, idan kuma mutuwa yayi fah?
Cikin sauri ta girgirza kai tare da fashewa da kuka, tana kukan take fadin Allah karka nufeni da ganin wannan ranan, inason nasake ganin Jamal a idona, inason nasakejin muryan sa tare da kamshin turaren sa"
Daidai momy tayi ma hajiya asabe rakiya tana shigowa taji sautin kukan Asma'u"
Aguje ta karasa ta kalli asma'u tare da fadin meye kuma?
Cikin kuka tace momy idan wani abu ya sameshi ne ki gayamin dan Allah"
Shiru momy tayi na wani lokaci zuwa can tace"
Kinga ki kwantar da hankalin ki idan Allah ya yarda lfy kyalau zai dawo"
Kallon Momy kawai tayi acikin zuciyarta tunani kala2"
Cikin dare kwata kwata ta kasa bacci burinta kawai tasan wani hali yake ciki, tashi tayi ta zauna, sai lokacin ta kula momy ma bata dakin, mikewa tayi ta nufi falo, wannan lokacin babu tsoro ko fargaba azuciyanta"
Momy tagani ita da nafisa sai sallah suke, cikin sauri ta juya daki agogo takallah karfe 2:08am, jitayi bazata iya hakuri ba dole ta kira yaya usman adaren nan wata kila bazai boye mata ba"
Tana dannan no aka dauka kamar daman jira ake Asma'u? Taji yaya usman ya fada"
Cikin dakushshayar muyar ta amsa"
Shiru yayi kaman ruwa yacishi, zuwa can yace Asma'u me kikeyi har yanzun bakiyi bacci ba?
Kuka ne ya kubuce mata cikin kukan tace bakomai"
Shiru ya sakeyi sarai ya gane kuka take dan haka ya rasa mezaice mata"
Itama rasa ta ina zata fara tayi, zuwa can yaya usman yace"
Duba asma'u ki kwanta kiyi bacci da safe zan kiraki"
Haka ta hakura badan ranta yasoba, alwala taje tayi sannan tazo ta tada sallah, tanayi kwalla nasauka idonta"
Har aka kira sallahn asuba tana azaune bayan ta ida sallah tasake kiran no yaya usman, tare da alwashin zata cire kunya ta tambaye shi Jamal"
Yana dauka yace Asma'u kinyi bacci kuwa?
Rasa abincewa tayi tare da rikecewa"
Shiru na wani lokaci sannan yaya usman yace"
Menene ke damunki ?
Tsintan kanta tayi da fadin babu komai inason ne nayi mgn da anty fa'iza"
Toh ina zuwa, ya fada sannan ya kashe wayar"
Ba adaukin lokaci ba kiran yaya ya shigo cikin sauri ta dauka"
Gaisawa sukayi a gajarce sannan ma'u ta fara kuka"
Shiru fa,iza tayi tana sauraranta domin kota bude baki batasan me zatace ba"
Zuwa can ma'u ta tsagaita da kukan sanan tace"
Anty fa'iza meye nufin ku na boyemin halin da ake ciki, sabo dame za'a boye min, idan wani abu ne ya sameshi ku gayamin, kara tsananta kukanta yayi amman a haka tace anty ko ya mutu ne?
Muryan usman taji yana fadin"
Ke, be mutuba yanan da ransa, menene kikeyi haka? tun dare kike faman koke koke, Ku daman mata haka Kuke duk kubi ku dama mutum lissafi, yanzun ki bari yau zanshigo Abuja"
Babu laifi ta dan samu natsuwa, saidai yau ta lura gidan yafi kullum rikecewa dan yau ko abun kare ba'adaura ba domin babu masuci"
Da misalin karfe 2 Usman ya iso"
Asma'u na zaune idonta duk sun kode sunyi suntum nafisa ta shigo tace tazo daddy na kira"
Afalon ta same yaya usman da alhaji bashir, momy ma na zaune agefe"
Karasawa tayi ta zauna akasa, acikin dashshiyar muryanta ta gaida su"
Fuskan daddy atunkushe ya kira sunanta, sannan yaci gaba dacewa"
Akwai abun da banso ki sani ba, Amman ba yadda zanyi, ya zama dole kisani, domin abun ya wuce tunanina, tunda jamal ya tafi yau wata uku kenan babu lbr, tun bayan ta fiyanshi da wata daya be sake kiran kowaba kuma ko ankira ba'a samunshi"
Wannan dalili yasa muka fara tsorata kuma tundaga lokaci muke zuwa ofishin su, saidai suma Kansu basu da wani lbr akansu, kullum hakuri suke bamu, tare da nuna mana sunakan meman inda suke ne, amman yanzun mun yanke shawara Usman da shamsudeen zasubi bayan sa"
Tukafin daddy ya karasa ma'u ta fashe da kuka, sai yanzo ne takeji son Jamal me tsanani azuciyarta, fuskan shi ta hango a idonta tare da dogon hancin sa, baya murmushi amman duk sanda yayi abin sha'wa ne, cikin kuka tare da jan majina tace daddy zan bisu"
Kafin daddy yayi mgn deeni ya shigo cikin shirin tafiya tare da wata jaka rataye abayan sa....
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
[22:52, 1/2/2018] +234 806 744 6138: 💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
8⃣1⃣to8⃣3⃣
Wani kallo deeni ya watsa mata sannan ya dauke kanshi"
Cikin tausayawa daddy ya kalli ma'u sannan yace,....
Ki kwantar da hankalin ki asma'u ke macece babu abin da zaki iya illa ki kara musu aiki"
Zaman ki agida shi yafi ki zauna kiyiwa mijin ki addu'a"
Kuka ta kara fashewa dashi, Usman ne yacire tagumin sa yace....
Ke karki kawo mana hauka, yaza tasa mutane agaba keta mana kuka, meye amfanin kukan?
Tsagaitawa tayi da kukan tare da to she bakinta"
Ciga usman yayi da fada har sai da daddy yace ya isa haka usman ka mata ahankali, kasan mata da miji sai Allah
Wani haushi ne ya sake kama deeni, cikin shi yaji yayi sanyi aranshi yace wannan kukan da asma'u keyi na meye, anya ba babu soyayyar Jamal azuciyarta, dan yaga ko kallon inda yake batayi"
Ji yayi kamar yace bazashi ba ya zauna yaga iya gudun ruwanta amman bazai iya ba soboda ayanzun yana Ganin Momy ne tamkar ummin Sa dan haka bazai zauna ba agidaba bayan yana Ganin hankalin ta atashe"
Shiko usma sosai asma'u take bashi mamaki wai ita da take ikirarin zata kashe jamal saigata wujuga wujuga tana kukan rashin sa, kara kallonta yayi yaga idonta duk sun kunbura"
Juyawa Usman yayi ya kalli daddy yace"
Daddy ni zan wuce basai natafi da wani ba, nikadai ma zan iya"
A'a usman zanfi son ku tafi ku biyu zaifi"
Ba yadda usman ya iya dole tasa zai tafi da deeni badan ransa yaso ba"
Koda suka mike suna sallama ma'u kuka kawai take"
Bayan fitan su momy taita lallashim ma'u, tare da nuna mata ta rage damuwa karya jawo mata ciyo"
Bayan tafiyan su da kwana biyu usman yayiwa daddy waya amman batasan abinda suka tattauna ba, dan haka da daddare tacewa momy abata no da yaya usman ya kira dashi"
Momy bata mata musuba dakanta tasa mata no din"
Acikin daren ma'u takira no saidai usman naji muryanta ya kashe"
Washegari duk suna zaune afalo, kowa babu bakin mgn, zuwa wannan lokacin kuka ya daina zuwa ma'u saidai kunan zuciya wani irin zafi takeji akirjinta ji take kamar tayi tsuntsu ta ganta agaban Jamal, idan ma mutuwan ne ta daukesu tare"
Mikewa tayi ta fita daga falon"
Momy da nafisa ne suka bita da kallo"
Ankwashi kusan minti 15 ma'u bata dawoba dan haka Momy ta kalli kofar tace"
Nafisa dobumin Asma'u kigani waje ta zauna?
Dasauri nafisa ta fita zuwa can ta dawo tace momy bafata waje"
Bata waje ? Amman nan naga tayi, kota dawo ne ta wuce ne bamu kulaba, duba ciki"
Dawowa nafisa tayi tace momy saidai ko toilet ta Shiga amman bata daki"
Zama sukayi suna jiran fitowanta, har aka kwashe minti 30 dan haka momy ta mike gaba daya part din saida ta duba toilet din amman babu ma'u dan haka ta fito afirgice tana fadin nafisa asma'u fa bata gidan nan"
Gaba dayan su waje suka nufu, suna isa gurin me gadin suka hada baki wajen fadi"
Asma'u ta fita ne?
Gargiza kai megadin yayi tare da aje radion shi agefe sannan yace tun fitan Alhaji nake zaune gurin nan banga fitan kowa ba"
Shiru momy tayi zuwa can tace anya baba kodai bacci ya debeka ta wuce baka gantaba"
Girgiza kai yayi tare da fadin idona biyu hajiya babu wadda ya wuce"
Cikin sauri momy ta nufi part din Jamal nafisa nabinta abaya, tun kafin ta karasa tahango alamar kofar abude take"
Da saurinta tashiga cikin falan babu kowa dan haka kai tsaye ta nufi dakin ma'u, saidai abinda ya bata mamaki ma'u bata dakin, dan haka arude momy ta fito tana fadin nagaya muku asma'u bata gidan nan, har momy ta kama kofa zata fita Wata zuciyar tace baki duba dakin Jamal ba"
Cikin sauri ta juya hartana hadawa da gudu nafisa ma ba'abarta abaya ba"
Suna shiga dakin suka hango ma'u kwance akan gadon Jamal"
Bacci take idon ta duk shedan hawaye ya bushe, hannunta daya dauke da glass din Jamal yayin da dayan yake rike da jaridan Sa"
Kara matsawa momy tayi har bakin gadon ta kurawa ma'u ido, bacci take sosai, hannuwan ma'u tasake kallo take taji kwallah tacika mata ido, domin ita kanta hango Jamal tayi zaune sanye da gilashin sa, hannun shi dauke da jarida kamar yadda ya saba"
Kuka ne ya kubuce mata cikin sauri tasa hannunta ta toshe bakinta dan karta tashi ma'u
Nafisa ma kuka take tare dabin dakin da kallo"
Ahankali momy tace Allah ina rokonka dan tsarkin mulkin ka Kadawo da jamalumdeen gurin iyalan sa, muna tsananin bukatar sa"
Haka momy taita addu'oi me kama da sambatu, daga karshe ta jawowa ma'u kofar suka fita"
Sai yamma likis ma'u ta shigo, babu wadda yace mata kalla harta nemi guri ta zauna"
Zuwa can momy ta kalleta tace kinyi sallah?
Eh kawai tace sannan tasa kanta akasa"
Abinci nafisa ta dauko ta aje agaban ma'u sannan ta zauna tace muci"
Wani haushi ne ya kama ma'u dan haka tasa hannu ta ture abinci tare da fadin banci "
Momy ce ta kalle su sannan tace wanni irin bakici ina kula dake yau kusan kwana nawa? bakicin abinci, kina nufin rayuwa zata yiwo ahaka?
Kamar me shirin kuka tace momy konaci awuya yake tsayamin wlh baya wucewa"
Haka nan zaki daure Asma'u nikaina idan inacin abinci ji nake kamar inacin magani"
Momy wlh bazan iya ba yanzun ma kirjina zafi yake min ji nake kamar nufashina zai dauke"
🙆🏼Kinga?, Asma'u ki rage tunani karki jawowa kanki ciyo"
Washegari da safe ma'u taji wayarta na kara, tana dubawa taga Abba ne, duk da tana cikin wani hali saida taji farinci, dan ta dade tanason kiran Abba da mama tsoro ne yake hanata"
Cikin siriyar muryarta tayi sallama, Abba ya amsa sannan ta gaida shi"
Ya amsa babu yabo babu fallasa, nasiha ya shiga mata tare da nuna mata komai mukkadari ne daga Allah kuma babu wadda ya isa ya canja yin Allah"
Wanna mgn ta Abba ya kara tayarwa ma'u hankali saitake ganin kamar Jamal ya mutu ne, dan haka ta kara rikicewa da kuka tare da fadin abba ya mutu ne?
A'a waye yace miki ya mutu?
Toh abba naji kana min nasiha ne"
Jim, yayi zuwa can yace yanzun asma'u sai jamal ya mutune zanmiki nasiha?, toh yanzun wannan kuka da kikeyi meye amfanin sa?, kinfi iyayensa son sa ne?
ance baki cin abinci, rashin cin abincin shine zai dawo dashi?, ki natsu kimai addu'a shi yafi bukata ayanzun, kuka da rashin cin abinci bazaiyi magani ba, irin wannan nasiha daddy yaita mata harta sarara da kukan sannan yaba momy wayar, itama nasiha taita mata daga karshe sukayi sallama"
Ma'u bata daina zuwa dakin Jamal ba, kulum can take bacci rana, domin da dare bata iya bacci adakin nasa ma, wani abunsa take dauka ta rungume, bacci ne yake daukanta batare da sanin lokacin ba"
****
*Somalia*
Tunda Usman da deeni suka taho magana bata hada suba ko kallon juna basu yi"
Yau kwanan su biyo agarin, gida daya suke kwana kowa da barayin shi"
Hakanan usman yaji be yadda da deeni ba dan haka yake kulle dakin daya yake"
Shiko deeni yarasa wacce hanya zaibi dan yaga jamal dan yana son ya ganshi kafin kowa ya ganshi"
Ranan da suka cika kwana uku agarin deeni zaune wani soja ya shigo yace Oga yace ka fiti idan kashirya idan baka shirya ba xai wuce"
Tashi yayi cikin sauri domin aganin shi yafi kowa son ganin Jamal dan haka duk wulakancin da usman zai mai zai jure"
Amota daya suka tafi, wani katon waje yaga anshiga wadda yayi ma deeni kama da gidan sojoji"
Suna tsayawa Uman ya fita ya fara tafiya cikin hanzari irin naso na sojoji"
Ko ina ka kallah sojoji ne ke shawagi"
Gadan gadan usman ya nufi shiga cikin sauri sojojin dake wajen suka dakatar dashi"
Hannun Yasa yaciro idcard dinshi ya nuna musu, cikin sauri suka saramai tare da bashi hanya"
Ko waiwaye usman beyi ba ya shige, deeni ko basu barshi wucewa ba dan haka yacika kamar zai fashe
Heat beat
*Mmn Yazeed*
[22:52, 1/2/2018] +234 806 744 6138: 💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
*SADAUKARWA GA*
*Masoya BUGUN ZUCIYA*👍🏻👍🏻👍🏻💋💘💘
8⃣4⃣to8⃣6⃣
Wani guri deeni ya nufa ya zauna, abin duniya ya dameshi, yana kallon yadda sojojin ke kaiwa suna dawowa, dan zaman shi gurin ya fahimci suna girmama manyan su, koda kuwa sun wuce su ashekaru"
Dan ko usman da suka sara masa, da yawa daga ciki sun girmeshi, wani tunani ne ya fadon masa acikin rana waishi yana ina ne lokacin da wadannan yan fici ficin yaran sukai karatu?, me nakeyi agida? Har waddan da aka haifesu abayana suka zama wani abu ni ina zaune?
Yanzun gashi ina kallo akabar waccen me kama da lagwanin ya wuce, ni aka hanami, duk su ummi ne suka jamin, gaskiyan momy ne su ummi basu daurani hanya mekyau ba"
Tunawa yayi da malamin da ummi ta turo masa shima dukka bazai wuce 22 ba, amma gashi har na kiranshi malam, karatu abakin shi kamar me, shiru yayi na dan wani lokaci zuwa can yace"
Yanzun idan nace zanyi karatu ta ina zan fara?, ko secondary ban gama ba taya zan zama kaman wadancen"
Hawaye yaji yana zubomai hakika su ummi basumai adalci ba, kusan ma su suka kashemai rayuwa, ayanzun ya fahimci ilmi shine gaba yanzun gashi yana da lfy yana da karfi amman ya zama dan kallo"
Share hawaye yake yanayi yana basarwa dan kar wani ya fahimci halin da yake ciki"
Saida usman ya kwashe kusan awa biyu sannan suka fito, su da yawa ya gani, yayin da wani ya taho da gudu ya bude musu mota suka shiga"
Itakanta motar daka ganta saika tsorata domin fentinta kallar kakin su"
Yana kallo motar ta tashi yayin da wasu motocin suka rufa musu baya"
Shiko deeni yanan zaune agurin babu wadda ya sake bin ta kansa"
Misalin karfe 9:38 sanyin gurin ya fara damun sa, zucigarshi babu dadi wani irin radadin yake ji azuciyan shi, nisawa yayi, zuwa can yaji wayarsa tayi kara daddy ne"
Bayan sun gaisa ya tambayeshi halin da ake ciki"
Beji kunyan cewa babu abinda ya sani ba, kwashe duk halin da ake ciki yayi ya gayawa daddy"
Jamm, daddy yayi sanan yace toh bari nakira usman din yasa akaika masauki, idan babu dama ma kai ka dawo gida"
Basufi Monti 5 da aje wayaba wani yazo yacewa deeni ya taso yakaisa gida"
Tunda ga ranan be sake Saka usman a idonshi ba har tsayon sati biyu, amman idan sunyi waya da daddy yana ce masa yanzon suka gama waya da usman kuma babu wani lbr"
Ranan da suka cika sati 2, da rana deeni na zaune yana tunanin ma'u aharabar gidan"
Ganinta yayi acikin idonsa ranan da ya fara sakata a idonshi"
Tsugunawa tayi har kasa tace ina wuni yaya shamsudeen, tun lokacin yaji ta shiga ransa"
Dan kaha yake mata bakam ta gama budurinta aka shi, kuma lokacin ne ta gama shiga zuciyan shi, murmushi ya sakeyi tare da fadin Asma'u yariya ce me shiga zuciya, inama farincikin da muka samu afarkon haduwan mu ya daure har yanzun" duk da naga asma'u na kokarin tura son Jamal acikin zuciyanta kamar yadda nima nekeyi ayanzu, amman azahiri banason Jamal natsane Sa, bantabajin na tsani wani ba kamar yadda na tsane sa, nasani Malam ya gayamin ciwa babu kyau gaba, amman nakasa cire kiyayyan Jamal acikin zuciyata, cire kiyayyan sa ko nanufin nabar basa Asma'u, nikuma bazan iyaba, *Na dad'e ina dama furata bazan yadda haka nan wani ya shanye min ba*
Karan motocin dayaji ne ya tsayar mai da tunanin"
Usman yagani ya dakko daga mota duk yayi furu furu ya fita hankalin sa"
Suna saukeshi suka juya suka fita daga gidan, part dinshi ya shige batare daya kalli inda deeni yake ba"
Tashi deeni yayi yabishi yana daba kofar yajita kulle, dan haka ya koma gefenshi ya zauna zuciyan shi cike da tunani barkatai"
Washegari karfe 7:00am daddy ya kira deeni"
Cikin sanyin jiki suka gaisa da daddy sannan yace"
Shamsundeen ya kamata muhakura haka, dan atunanina Jamal baya raye, duk inda ake tunanin ganin su anje babu shi amman ansame gawan wasu daga cikin su, shima Jamal din ansame jakar sa tare da wayoyin Sa, amman shi babu shi cikin kuka daddy ya karasa mgnr"
Shiko deeni yarasa abin da yakeji yayi, farin cikine ko bakin ciki be sani ba"
Daddy ne yaci gaba da cewa ka hada kayanka yau zaka dawo, usman yace akwai abun da zai yi bayanzun zai dawo ba"
Koda suka aje waya deeni cewa aidaman nasan asma'u tawace"
Deeni besake ganin usman ba sai afilin jirgin sama, gani yayi ya rame idonshi jawur kamar garwashi, jakar dake hannunshi ya mikawa deeni yace kabawa daddy jakar Jamal ce"
Har jirgin ya tashi usman natsaye ya rungume hannun akirji"
*Abuja*
Koda deeni ya isa gida samun kofargidan yayi cike anata zuwa wa daddy jaje, abban ma'u ya hango zaune kusa da daddy dan haka yayi maza yabi ta baya dan bayanson ya ganshi agidan nan"
Daddy ko yaga wucewan deeni dan haka ya tashi yabi bayansa"
Zuwa can ya fito dauke da da jakar Jamal ahannun shi sannan ya kira Abba da alhaji bashir suka shiga cikin gida"
Falon ma cike yake da yan jaje cikin harda da momyn usman, tare da anty fa'iza"
Atsakiyar falon daddy ya tsaya yace inna asma'u?
Tana dakin nafisa"
Kai tasaye suka nufi dakin momy ma bayan su tabi"
Ma'u na zaune tayi tagumi taga abbanta ya shigo dan bata san da zuwan su ba"
Afirgice ta mike tare da dafa bango dan tasan hakanan abba bazaizo ba, idan ma yazo toh bazai shigo har daki ba"
Kamata momy tayi suka koma suka zauna, suma su daddy zama sukayi sannan suka fara mata nasiha daga karshe ya fada musu halin da ake ciki tare da ajiye jakar Jamal atsakiya"
Fashewa Momy tayi da wani irin kuka, me tsuma rai sannan tace ban yadda ba, alhaji be mutuba, idan kuma ya mutu babu abin da na isa nayi amman kubani gawan sa"
Ma'u ko batace kala ba, kuma batai kuka ba, asalima gutun murmushi ne akan idonta"
Wani irin mikewa tayi, cike da karfin guiwa ta tsuguna agaban jakar"
Ahankali ta zage zip din ta zazzage kanyan ciki akasa, Abba ne yayi yinkurin hanata amman daddy yace abarta"
barbaza kayan ta farayi nan taci karo da hotona ahankali ta zaro daya, kara zaro ido tayi ganin pic dinta, akofar gidan su deeni lokacin da taje ana gobe dauri auren su, ajiyewa tayi agefe sannan ta kara dauko wani, shima natane lokaci da yayi zuwa nafarko zai tafi bata manta ba lokacin ne yake ce mata yayi ciwo harya warke batamai sannu ba"
Haka taita fitowa dashi, duk natane alokuta daban daban, mamakine ya kamata dawani lokaci yake daukata hoto batare da ta sani ba, zabura tayi ta watsar da huton sannan ta rarumo wayar sa"
Kunnawa tayi, pic din tane ya bayana akan fuskan wayar tana zaune afalo hannnuta zane da lalle, daga cen gefen pic din an rubuta My Queen"
Tundaga lokacin wuta ya daukewa ma'u, ta kame kam, kwata kwata bata motsi illah hawaye dake diga ta gefe idota"
Momy na kuka tazo ta girgiza ta amman babu motsi kuma hawayen be daina sakkowa ba"
Ihu momy tasa haka ya jawo hankalin mutanen dake falon"
Da taimakon su aka aka daura ma'u agado sannan daddy ya fita domin ya dauko wayar sa ya kira family doctor"
Ta kofar baya ya fita dan haka dan haka yana fita sukaci karo da deeni"
Ganin daddy arude yasashi tambayan daddy fly?
Shima arude yace babu lfy, yariyan nan asma'u ta kwallafa rai akan mijinta, gashi yana nema ya zaman mata matsala, yanzun tana ganin jakarshi ta suma"
Daddy be jira jin abin da deeni zaice ba ya wuce"
Deeni ko jikin bango ya manne tare da fadin suma? da gaske asma'u daman son Jamal take? dagaske ba dan antursasata bane take zaune? Wata zuciyarce tace da gaske ne mana lokacin da ta
rasaka ai bata suma ba, jiyaye kamar numfashin sa zai dauke, wani irin kara yakeji daga kasan zuciyan shi, nan ya manne ajikin bango tare da fitar da wani iron numfashi
Bayan doctor yazu ya gama aune aunen sa, ya tabbatar ma'u ta kamu da ciwon zuciya, wadda yace idan ba ai hankali ba zuciyarta zata bugu"
Lokaci da doctor kewa daddy mabayani, deeni naji dan hanka hakalin sa ya kara tashi, kafuwan sa banda rawa babu abinda suke"
Awannan halin daddy ya fito yasamu deeni dan haka yace kai kuma meke damun ka"
Be iya amsawa ba, kira daddy ya fara kwalawa Dr tare da tafiya yana fadin zo ka dubamin shi"
Deeni najin haka yaja jiki yana matsanancin haki yabi ta wani logu yabar gidan dan ya tabbarar idan aka gwadashi za,ace zuciyar shi ta wargatse"
Koda suka dawo babu kowa gurin dan haka daddy yace yaje zai kawo sa"
****
Tsayon kwana 3 ma'u ta fara motsawa, amman babu baki kuma hawayen nan makale agefen idonta bata rabo dashi"
Haka kuma batacin abinci koda yaushe ruwa, dan haka momy take dama mata koko datace ruwa saita zuba ruwa akai ta mika mata"
Aranan su abba suka tafi gaba daya bayam sun mata nasiha sosai, sunso su tafi da ita amma ta nuna bazata ba"
Deeni ko kokari boye damuwan shi yake amman ji yake zuciyar shi tafi garwashi zafi"
Tsayon sati daya da tafiyan su abba amman bar yanzun ma'u bata magana ta rame ko cikakiyar mikewa bata iyawa, farau faraun ma yanzun sai anyi da gaske takesha wanna wadda tarage shi momy ke kurbewa"
Damisalin 12:31am kowa ya kwanta ammam babu wadda ya runtsa"
Dagacan suka farajin kara motaci tare da hayaniya"
Cikin sauri daddy ya tashi ya zauna yana tunanin anguwar lfy kuwa? yana yinkurin sauka agadon wayar sa tai kara, be duba no ba ya dauka tare da mikewa tsaye"
Muryan usman yaji yana fadin daddy abude mana Get"
Fitowa daddy yayi yana tsakiyar falon ya daga murya yace usman kana nufin kana kofar Gidan nan?
Wannan mgn ta daddy babu wada bejitaba dan duk Gidan basu runta ba"
Daidai lokacin da daddy ke fadin baba megadi bude get, a guje ma'u ta duro daga gado, tana fitowa falo ta fadi kasa......
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
.💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
8⃣7⃣to8⃣9⃣
Ma'u na kwance akasa taga wucewan momy da nafisa aguje dan haka tafara kokarin mikewa amman jiri sai maita yake"
Daga can ta farajin karan momtoci suna shigowa gidan tare da hayaniyan mutane"
Ai ganinta kawai tayi ta mike, tana daf da isa gurin taji momy na fadin....
Usman ?, ansame Jamal din ne?
Bataji amsan da usman yaba momy ba tasakejin daddy yace yana raye?
Aguje ta kwasa ganinta kawai tayi atsakiyan sojoji, kutsawa taitayi har ta isa gaban motar da taga sunzagaye"
Anan taga suna ciki cikin fito da Jamal daga cikin motar"
Daga momy har abba rigegen kallon Jamal suke, dan haka gaba daya sunkewaye gurin"
Momy fadi take Jamal? Kaine Jamal?
Ahakali yace nine momy"
Ina ka shiga jamal kabarmu cikin wani hali?
Cikin yanayi irin na mejin jiki yace kuyi hakuri"
Itako ma'u har yanzun raba ido take takalli deeni, domin kafarshi kawai take iya gani mutane duk suntare mata ganin sa"
Wani daga cikin sojojin ne yace.....
Alhaji yakamata akaishi ciki domin yana bugatan hutu"
Cak suka daukeshi suka nufi part din daddy, kan gadon daddy suka kwantar dashi, sannan suka juya usman kadai ya zauna"
Duk suna tsaye akan jamal daddy Momy, nafisa ma tana tsaye agefe"
Jamal suke kare ma kallo yadda aka daure cinyan shi duk biyun, gashi yayi wani irin baki ya rame, tare da tarin uban kasunba"
Bayan daddy ya gama karewa Jamal kallo ya kalli usman yace"
Wai karayace har cinya biyu?
Girgiza kai Jamal yayi tare da fadin harbi ne aduk kafa fuwan, kuma ya shiga naman sa sosai, dan haka akace karya taka kafan harsai wajen ya warke"
Jimami sukaitayi akan jamal, shidai yana kwance idonshi rufe shi kadai yasan me yakeji"
Sai lokacin Momy ta juya ta kalli dakin tare da fadin a'a ina asma'u?
Gaba dayansu waigowa sukayi suna kallon dakin arude sukayo waje"
Itako ma'u kunya ce ta kamata tana kutsawa momy da abba suna kutsawa dan haka ta zauna afalo tare da hada kai da guiwa domin ta kusa tasa Jamal a idon ta, amman saidai shi kanshima Jamal din kunyan hada ido take dashi"
Suna fitowa suka ganta zaune tayi tagumi"
Daddy ne yace ke meyasa zaki zauna Anan ?, tashi maza"
Kanta akasa ta fara kokarin mikewa Momy ce ta taimaka mata ta mike sannan ta riketa har suka shiga dakin"
Abakin gadon ta zaunar da ita sannan ta juya ta fita badan tagaji da kallon Jamal ba saidan ta kula kamar kunya ma'u takeji"
Shima Jamal din yanajin fitan momy ya bude ido da sauri ya sauke kan ma'u, cikin sauri ya fara kokarin jawo jikin shi kusa da ita tare da miko hannu"
Usman deke zaune agefe ya dago kai ya kalli ma'u gani yayi har yanzun bata daga kai ta kalli Jamal ba, dan haka ya mike ya fice"
Kaman jira ma'u take ta juya ta kalli Jamal tare da fadawa kan kirjin shi, fashewa tayi da wani irin kuka har su momyn dake falo suna jinta"
Hannun shi yasa guda daya ya kara danna kanta akirjin shi, ji yayi zuciyar shi fari kar domin kukan ma'u ya tabbatar mai tayi missing dinshi"
Dan kwalin dake kanta ya zame sannan ya tura hannun shi cikin gashin kanta, zuwa can ya fara sunbatanta tun daga gashin kanta har zuwa wuyanta"
Kara karfin kukanta tayi tare dasa hannunta tana cakumo mai gaban riga kamadai me shirin fada"
Tsayawa yayi cak yan kallonta zuwa can ya rike hannunta muryan shi can kasa yace husna menene haka?
abin kuma fada ne?
Tsayawa tayi cak tana sauraran muryan shi, jin abin take kamar mafarki Dan haka ta dago kai ta kalleshi, kur sukawa juna, zuwa can ta bude baki cikin kuka tace
Yaya Jamal kai ne???
Nine husna"
Hannun ta kara kaiwa kan kirjin shi tare da fadin, Allah yasa ba gizo idona kemin ba"
Kara shafu gashinta yayi tare da kura mata ido, muyar kasa kasa yace.....
Husna ba gizo idonki ke miki ba nine da kaina"
Kusan minti 5 suna kallon junan su zuwa can ma'u ta cire idonta tare da wasa da yatsanta"
Jamal ko ci gaba yayi da kallonta tundaga fuska har zuwa hannun da take wasa dashi"
Kara jawoyo jiki yayi ya rike hannun"
Cikin sauri tayi yinkurin kwace hannunta tare da matsawa can bakin gadon"
Jamal ma kara jawo jiki yayi ya iso bakin gado yana kokarin mika hannun shi ya kamo na ma'u ta mike da sauri ta fita"
Lebe Jamal ya cija sannan ya fara kwalawa usman kira"
Daman usman naganin wucewan ma'u ya mike tare da bin bayan ta da kallo, acikin zuciyar shi yace munafukar yariya"
Yanajin muyar Jamal ya nufi dakin da sauri"
Samunshi yayi ya dawo bakin gado dan haka yace menene haka Jamal?, yaya akayi ka dawo nan?
Kawar da zancen yayi da fadin wai husna tayi ciwo ne naga duk ta rame?
Bazan usman yayi dashi sannan ya gyara mai kwanciya, juyawa yayi yana fadin duk dai abinda zakayi kayi ahankali, kasan dai abinda likita yace"
Shima share zancen yayi bece komai ba"
Washegari gidan cika yayi da baki, cikin harda abba da mama"
Ma'u kasa hada ido tayi dasu abba wani irin kunya takeji idan ta tuna yadda taita kuka akan Jamal"
Tun daren da Jamal ya dawo deeni ya sani Amman yanata kaucewa haduwa dashi"
Kwanan su Abba 1 suka koma, kuma aranan ne alhaji bashir ya kawo ummi deeni"
Bayan tayiwa momy Allah ya kyauta gaba, suka rankaya harda dakin Jamal"
Jamal naganin ummi gaban sa ya fadi domin bazai taba manta wannan fuskar ba"
Saidai abin da ya basa mamaki menene ya kawota gidan su"
Adaddafe suka gaisa, sannan Jamal ya kureta da ido"
Bayan tafiyanta Jamal
yasa usman
ya kira masa momy"
Zama momy tayi kusa da Jamal sannan tace gani yaya akayi?
Idonshi kur awaje daya yace, momy wannan matar da kuka shigo tare wacece?
Kanta tsaye tace matar babanka ce alhaji bashir, itace babar shamsuddeen"
Shamsuddeeni ? Jamal ya maimaita sannan yayi shiru, zuwa can yace Momy kina nufin itace mahaifiyar shamsuddenin da daddy yake gayamin?
Cikin fara'a momy tace itace, ai shamsuddeenin ma yana nan gidan, kasan wani irine shi shiyasa baku haduba, saidai mutaro mumai addu'a Allah ya shirye shi"
Gaban Jamal sake bugawa yayi, Allah Allah yake Momy ta fita ya kira ma'u dan ita kadai take da amsan tambayen shi"
Ji yayi hankalin shi ya tashi idonshi ya rufe mamaki ne yasa ya rasa mezai yi yaji daddi, gashi babu damar tafiya"
Bayan momy ta fita usman ya dawo tun kafin ya zauna jamal yace....
Usman dan Allah kiramin Husna"
Wani irin kollo usman ya masa sannan yace wannan ne kuma baka isa ba wlh, komenene xanyi maka amman ka daina min zancen asma'u bare ma har kace nakira maka ita"
Shiru yayi zuwa can yace toh bani aron wayarka nakira"
Mikamai yayi sannan ya mike ya fita, yana zaune afalo ma'u tazo tashiga dakin da Jamal yake"
Acikin zuciyar shi
Yace wannan ba girmana bane, ya kamata nabar gidan nan"
Ma'u nashiga Jamal ya mata wani irin kallo, tunda take bata taba ganin ya mata irin kallon ba"
Tsayawa tayi tana kallon shi"
Fuskanshi dauke da bacin rai yace"
Husna ke munafuka ce ko? Dake da deeni kuka kulla wannan munafuncin ko, tayaya za,ace deeni dan uwanane? Sai yanzun nasan kunnen kashi gareki, wato kin kawoshi har cikin gidan ubana kuci amanata?
Tuni ma'u fara kuka tare da fadin yaya Jamal bari kaji, dan Allah ka tsaya kaji"
Be saurareta ba daga murya yake cikin fada yana cewa.....
Husna ni kika munafunta ashe duk kukan da akace kinyi na rashina muna funcin ne? shikenan nagaji da halin ki hakurina ya kare, husna inada tsananin kishi akan abin da nake so, zan hakura dake dan nasan yanzun kinbashi kanki"
Cikin kuka take girgiza kai tare da fadin wlh a'a yaya Jamal ka tsaya kaji, wlh bansan komai ba game da zuwan deeni gidan nan, nikaina dana ganshi nayi mamaki, wlh yaya Jamal ban kulashi ba, kuma babu wani abu daya shiga tsakanina dashi"
Cikin tsawa yace karya ne, karya kikeyi, tun kina gidan iyayenki kikai niyar basa kanki, nasan komai"
Dam taji gabanta ya buga take hawaye suka fara zubowa kamar anbude famfo"
Cikin kukan tace yaya Jamal karka yanke hukunci cikin fushi, wlh wlh banci amanarka ba, dan Allah ka natsu karka batamin suna, yaya Jamal karkai sanadin da iyayena zasu tsine min, idan kayi haka ka zalinceni,😭 zanta kuka har karshen rayuta, dan Allah kamin adalci🙏🏻
Wata muguwar tsawa ya daka mata tare da fadin fita kibani guri"
Aguje ta fita tana sheshshekar kuka, cikin mamaki usman ya shiga cikin dakin"
Samun Jamal yayi fuskan shi murtuk idonshi jawur"
Yaya dai ? Usman ya tambaya yana kokarin zama"
Tsaki jamal yaja sannan ya kyauda kai tare da fadin babu komai"
Shima usman tsaki yaja sannan sannan yace wlh kaji kunya akan asma'u zaka dinga bata ranka har kana daga murya tun daga falo nakejin hargagin ka"
Tsaki Jamal yasake ja sannan yace.....
Sanda zaka tafi nemana ance kaida dan gidan baba bashir kuka tafi, amman meyasa baka gayamin deeni bane saurayin husna?
Deeni? Kana nufin shamsundden shine deeni?
Au zakacemin baka gane bane?
Dafashi usman yayi sannan yace yace, aini bawani sanin sa nayiba ina kamar so daya na taba ganinsa, dan bezama dole nagane shiba, amman kai me kake tunani akan hakan?
Kanshi tsaye yace akwai wani abu ban yadda da wannan Al'amarin ba"
Wani iri usman yaji cikin sauri yace jamal zan baka shawara badan asma'u tana kanwata ba, dan Allah ka aje kishinka agefe kayi bincike"
*****
Haka suka kwashe sati tsakanin ma'u da Jamal ba wadda yake runtawa saboda damuwa, hakama usman da tausayin abban sa ya damesa"
Kuma sosai yaji zafin kalaman Jamal amman babu yadda zaiyi dole ya daure"
Yauma kamar kulum jamal na zaune akan gado yana aikin tunani yaga daddy ya turo kofar rike da hannun deeni"
Mantawa yayi da ciwon dake kafarsa daddy be ankaraba yaga Jamal shakure da wuyan deeeni"
Arude daddy ya rike Jamal din tare da fadin yaya haka Jamal? innalilahi wa inna ilaihir raju'un, kasa kwatan deeni yayi"
Shiko deeni beyi yunkurin kwatan kanshiba, gutun murmushi ne akan fuskan shi, tare da tarin wahala"
Salatin Abba ne yajawo hankalin duk mutanen gidan ciki harda ma'u
Daker usman ya kwaci deeni ahannun jamal , Jamal cigaba yayi da fadin wlh koni ko kai, yariya ma tayi aure bazaka barta ba? tana gidan mijinta kana bibiyanta?
Sororo su momy sukayi, har ya gaba bambamin sa ya juya ya kalli ma'u dake tsaye cikin dogowar riga kanta babu dan kwali"
Hannun shi ya kada yana nuna ma'u tare da fadin.....
Eh tunda kin ganshi ai dole ki fito tsirara, juyawa yayi yana dingishi sannan ya koma bakin gado ya zauna"
Ya bude baki zaiyi mgn momy tazo da sauri ta matsamai baki, tare da fadin Jamal? Wasu irin maganganu kakeyi haka? Kwakwalwarka ta samu matsala ne"
Daddy ko tunda yaji kalaman Jamal ya dago kan zancen, dan abban ma'u be rufemai komai ba"
Kallon deeni yayi ya kalli Jamal sannan yace duk kuzauna, Malam Jamal ai abin bekai haka ba"
Kai deeni daman kaine wadda ka taba neman asma'u shine baka taba gayamin ba?
Shiru yayi tare da sosa kai, ke kuma asma'u meyasa baki nuna kisan shamsudeen ba"
Sukuyar dakai tayi tare da share hawaye"
Cikin sauri Jamal yace ai munafukai ne, bazasu fada ba"
Momy ce ta kara dakatar dashi tare da fadin kul Jamal bari zargin matar ka idan ba hakaba zaka lalata auren ka' kuma nikaina shaida ce, tun ranan haduwan su da shamsudeen asma'u ta rikece tazama firgitattaciya kwanciya dakin nafisa ya gagareta, daga karshema tacemin ita adakina zatana kwana, wlh dataji kara take tsorata, dole tasa nake rufe kofa, ko falo bata fitowa"
Wani sanyi Jamal yaji azuciyan shi, daddy ne yace"
Jamal shamsudeen dan uwanka ne, da wacce ta haifeni da wacce ta haifi baban sa uwa daya uba daya suke, dan haka babu fada, kada nasakejin Wata mgn, wannan ma ai zancen baza ne kakeyi asma'u ai matar Aure ce, wani kishin banza zaka nuna mana?
Shiru Jamal yayi tare dasa hannun shi yasafu fuskan shi"
Shiko deeni kyauda kai yake tare dajin wani iri acikin zuciyar Sa"
Daddy ne ya juya ya kalli deeni sannan yace"
Kai kuma Shamsudeen kayi hakuri, kadauka dama can asma'u ba rabonka bace, Kuma ba laifin mahaifinta bane, kasa azuciyar ka Allah ne me badawa kuma me hanawa karfin mutum da dukiyar sa baza su iya bada abinda Allah be yadda dashi ba, haka kuma inda Allah ya nufa asma'u matar kace Duk kin da mahaifinta yayi saika aureta, dan haka ina dada baka hakuri, Sannan nabaka dama kaje ka nemi yariyar da kakeso ko yar gidan waye zan tsaya maka, amman ka gyara halinka, nasani ka rage wasu abubuwa amman inason cigaban yafi haka, Allah ya muku Albar ka🙏🏻🙏🏻
Deeni bece komai ba kuma be daga kai ya kalli kowaba ya tashi ya fita"
Cikin sauri daddy yabi bayan shi, momy ma mikewa tayi sannan ta mikawa asma'u hannu suka fice"
Daga Jamal sai usman suka rage adakin, Jamal sai kyauda kai yake' sai yanzun yakejin kunyan usman"
. Da daddare Jamal ya dami Momy da waya, saidai daya kira kusan sau 6 kuma data dauka saiyace ya manta ne, ba ita zai kira ba"
No ma'u tun rana yake kira amman ba'a dauka"
Momy yasake kira bayan ta dauka yasake Jan tsaki yace wai no nan rikina ni take"
Gutum murmushi momy tayi sannan tace....
Anya jamal mantuwa ce ? kodai asma'u....
Bejira me momy zatace ba yayi maza ya kashe wayar"
Befi da minti goma ma'u ta shigo, fuskanta turbune, kamar zatai kuka, can nesa dashi ta tsaya sannan ta sunkuyar da kanta tare da fadin gani"
Kallonta yayi sosai sannan ya nuna mata gefen shi tare da fadin zokizauna"
Karasa tayi ta zauna inda ya nuna mata, cikin zafin nama ya jawota jikin shi ya rungume"
Sun dadde ahaka, dumin jikinta ya gama daburta shi, wani tunani ya fara kawowa, zaiso hakan ya kasan ce ayau, amman kuma likita yace karna ataka kafar bare asa masu ruwa, wanka ma da dabara usman ke masa"
Wata zuciyar ce ta tambayeshi bazaka iya bane? Zan iya ya bata amsa, haka zuciyar shi taci gaba da bashi karfin guiwa dan haka yasa hannun shi ya yaye hijjabin dake jikinta ya ajeshi agefe"
Arude ma'u tace dan Allah kabari yaya usman fah yana falo"
Cikin Wata kasalalliyar murya yace bazan iyaba inason Zumata ayau.....
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
9⃣0⃣to9⃣2⃣
eyi yinkurin hanawa ba, cikin sauri ya saketa tare da kauda kansa gefe"
Bakin gadon ta zauna jikinta asanyaye, waigowa Jamal yayi ya kalli ma'u sannan yace.....
Oya tashi ki tafi, tunda nikikewa rowa, ina matsayin mijin ki amman na nemi hakki na aki bani, ni daman nasan ba sona kike ba, ai waccen katon dan isanka kin bashi dama sobo dashi kina son shi"
Da sauri ta waiga ta kalleshi tare da fadin yaya Jamal ni ka dani gayamin irin wannan mgr.....
Bazan bariba baki bashi dama bane? Duk hiranku kedashi inasa ne da ita niba jahili bane da ilmina karkiga kamar bansan abun da nake ba, da kunnena naji bawani bane ya gayamin, na dade ina dama furata bazan bari wani daga sama ya shanye min ba, zaki iya tuna amsan da kika bashi alokacin?
Idan bazaki iyaba barin tuna miki"
Kuka ne yaci karfin ma'u tare da wani irin nadama, fada ta farawa kanta da kanta meyasa bataji mgr Abba ba tun farko gashi abin na neman zama mata matsala agidan aurenta"
Girgiza kai tayi tare da fadin yaya Jamal nace maka kabar irin wannan maganganun, dan Allah ka bari"
Jajayen idonshi ya sauke akanta sannan yace....
Bazan bariba Husna, aduk lokacin dana nemin wani abugurin ki kika hanani abinda nake tunuwa kenan, fita kiban waje"
Mikewa tayi cikin fushi ta fita, usman ne ya kula cikin fushi take dan haka ya tsaidata tare da fadin yaya akayi?
Hawaye ta share tare da saukar da kanta kasa, zuwa can ta bude baki zatai mgn yaya usman ya tsaidata"
Ido ya zuba mata yana kallon yadda take share hawaye zuwa can yace....
Ki koma ki bashi hakuri"
Ido ta daga ta kalli usman da niyar mgn ya sake tsaidata tare da fadin nace miki kibashi hakuri ko?
Juyawa tayi ta koma ta sameshi idon shi kamar me bacci, cikin siririyar muryanta tace....
Yaya Jamal kayi hakuri bazan sake maka musuba"
Saida ta maimaita sannan ya bude ido tare da miko hannun Sa"
Karasawa tayi da saurinta dan gudun karta kara laifi"
Sosai ya shige jikinta, dada jawota yake kamar wadda yayi wanka da ruwan sanyi alokacin sanyi"
Ma'u arude take amman babu yadda zatayi dole tasa ta rufe idonta tanajin yadda hannun Jamal yake Yawo ajikinta"
Jikinta banda rawa babu abunda yake sai yazon ne tasan me aure yake nufi da batasan menene Aure ba, ko lokacin da ta bamawa deeni dama bata kawo ya zataji ajikinta ba, itadai kawai tanason taga deeni yayi farin ciki"
Yanzun ne wannan tunanin ya fado mata, yanzun ne take tuna lallai idan tabar Jamal zai gana mata azaba, amman bata isa tace komai ba idan ba haka ba yanzun nan Jamal zai burkitata"
Haka tanaji tana gani Jamal ya fara rabata da kayan jikinta, yadda yakeyi bazaki ce akwai ciwo ajikin saba ya manta da cewo sha'anin sa kawai yake "
Ganin haka abin ya farabawa ma'u tsoro da mamaki yanzun yaya Jamal ne yakemin haka mutum me jijji dakai tare dashariya"
Abu ya dada kankama ma'u dukta firgita da sallon Jamal, kuka tasa tare da rike hannunsa"
Jaye hannun sa yayi yaci gaba da abin da yakeyi, tare da tushe mata baki da nasa"
Ganin inda Jamal ya rikice ya makale ma'u yasa nayi saurin barin dakin😜
Jikin kofar na makale daga can naji ma'u tayi wata yar kara, shiko Jamal wani irin nishi yake kamar wadda ya shanye robar yaji"
Zuwa can naji yana cewa....
Tsarki ya tabbata ga ubangijin daya kago wannan halittan, Allah ya miki Albarka, Husna dame zan kwatantaki, idan nace miki zuma ma na maidaki baya, husna barin takaice miki, duk duniya babu wani abu me dadin dazan kwatantaki dashi, shiru naji, zuwa can ya sake cewa Husna dadinki yafi dadi dadi, kin sani farin ciki mara misaltuwa Allah ya miki albarka"
Kuka kawai ma'u ke yi, saboda irin radadin da takeji ta kasan ta, hawaye ya fara share mata, zuwa can ya wawusheta yayi toilet da ita"
Gasata yayi tsaf, duk da cewa bata son haka amman ba yadda zatayi dole ta daure"
A toilet din ya baro ta ya fito ya canza zanin gadon sannan ya boye wadda ya cire"
Daidai lokacin asma,u ta fito, tana kanin Jamal ta rufe ido"
Kamota yayi ya zaunar da ita abakin gadon fuskan sa dauke da farin ciki, yace.....
Bude idonki mana"
Kin budewa yayi dan haka yace....
OK to shikenan amman inason kimin wani abu dan Allah kijirani naje nayi wanka kinga idan usman yaga Zanyi wanka bazai barni ba"
Komai batace ba ya juya fita, taganin shiganshi ta mike ta maida kayanta sannan ta maida hijjabinta ta zauna"
Be Wani dade ba ya fito yana dingishi tare da runtse idonshi guda daya"
Cikin sauri ya maida kayanshi sannan ya hau gadon ya kwanta"
Jawota yaso yi jikinshi cikin sauri ta mike tana dingisawa"
Gani tayi usman be wajen dan haka tawuce batare da wani ya gantaba"
Bayan nafisa ta kwanta idonta be daina zubar da ruwaba kamar yadda jikin ta be daina mata zugiba"
Can cikin dare zazzabi ya rufeta, rawan sanyinta ne ya tashi nafisa"
Ganin halin da take ciki Yasa ta kira momy"
P.c.m momy ta bata sannan ta rufeta da katon barko kafin da same akira likita"
Kusan kwana Jamal yayi yana kiran wayar ma'u amman taki dagawa"
Yau tsayon sati daya kenan ma'u bata daukan kiran Jamal, sannan kullum saiya aiko nafisa kiranta saitaki zuwa"
Momy ma hartayi mgn ta gaji, kirikiri take kin zuwa"
Ranan doctor dayake duba kafar Jamal yazo yana warware ciwon yace kash amman nace muku kar abari ruwa ya taba gurin"
Cikin sauri usman ya eh doctor ai munabin doka"
Girgiza kai yayi tare da fadin wannan kamar ansa musu ruwa sosai ma kuwa"
Usman ne ya kalli deeni yace kasa ruwa ne ?
Kyauda kai Jamal yayayi tare da fadin ni? Idan ma ruwan ne saidai idan kai kazuba"
Tsaki likitan yaja sannan ya fara wanke ciwon tare da kwaso ruwan daya shiga cikin ramin"
Bayan ya kama nadee kafar yayi tare da fadin ku kula sosai dan Allah kuma karya taka kafar koda yaushe ta kasance amike, idan ba hakaba gurin bazai warke yadda ya kamata ba naman wajen zai iya tattatewa"
Doctor na fita momy tacewa usman ko za'abar wankan ne?
Eh momy gara abarshi"
Momy najuyawa zata fita jamal yace usman dan rakani dakin nafisa"
Waigowa momy tayi sannan tace...
Kanajin dai abinda likita yace ko?, usman karka kulashi"
Mikewa yayi tare da fadin aini momy yau fitama zanyi basai ya ganni ba"
Kaitaye momy dakin nafisa ta nufa, hannun ma'u ta kamo bata saketa ba saida ta kaita gaban Jamal, sannan ta juya ta fita"
Murmushi ya sakar mata sannnan yace....
Husna wani irin huro ne wannan? Kodan kinga bani da kafa? Haba husna anya kina tausayamin kuwa ?
Muryanta kasa kasa ta fara gaidashi"
Make kafada yayi tare da fadin bazan amsaba, banason irin wannan gaisuwan"
Ahankali ta sake cewa wacce iri kake so?
Matso in nuna miki"
Saida gaban ta ya fadi, domin yanzun muryan Jamal kadai fadar mata da gaba take"
Ahankali ta karasa hannunsa ya ware, ta shige ciki"
Yauma Jamal be kyale ma'uba abinda ya nema rannan yauma shiyasa ke nema, harma yafi ranan nan zakiwa, tundaga ranan Jamal ya maida abin alada kullum sai yayi, tare da wujjugata sosai"
Ahaka har aka samu sati 2, dataje gaida shi usman yake fita falo, da wannan damar Jamal yake amfani yayi abin dayaso"
Wani fari yayi yai jawur, har usman na tsokanar shi dacewa lallai na iya jinya wannan irin murjewa haka"
Dariya kawai jamal keyi"
Domin shikadai yasan me yakeji"
****
Yau tunda ma'u ta tashi takejin miyau abakinta, ta rasa meke damunta"
Bata kawo tunanin komai azuciyarta ba, itadai kawai tunaninta bakinta ya bacci da kwadayi"
Zama tayi tana tunanin abinda zata saka abakinta domin miyoun ya daina zubowa"
Zuwa can tunaninta ya fada mata kan gwaiba, juyawa tayi tace nafisa nikam inasoncin gwaiba ina zan samu"
Tafff ai yanzun ba lokacinta bace"
Miyau ne cike da bakinta ta mike taje ta zubar tundaga ranan ma'u bata sakejin dadin jikinta ba"
Yauma kamar kullum ma'u taje gaida Jamal ta samu usman sai fifita yakemai, ya hada uban zufah"
Tsaye tayi agefe dan ko gaisuwan data mai ya kasa amsawa"
Zuwa can momy tashigo abincin dake gefe ta bude tare fadin....
Jamal daure katashi kaci abincin kafin likitan yazo"
Kallon abincin kawai ma'u tayi ta fara kakarin amai, da gudu ta nufi toilet, duk abinda ke cikinta saida ta amayar dashi"
Bayan ma'u ta fito wani irin kallo momy ta bita dashi me cike da tuhuma"
Gani tayi ma'u ta dashe tayi fari fat,
Acikin zuciyarta tace bazata sobo ba, dole nasa agwada min yariyar nan kamar ciki gareta daman Jamal ya fada akwai wata alaka tsakanin shamsudeen da asma'u na karyata shi, ga gaskiya na shirin bayyana
Heart beat
*Mmn Yazeed*
💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
9⃣3⃣to9⃣5⃣
Jamal ne ya bude idonshi tare da fadin momy daman bata da lfy ne?
Kunyan idon usman yasa momy ta amsa amman zuciyarta cike yake da bacin rai"
Daker ta iya cewa eh duk da bata fada ba Amman nakula kwana biyu batajin dadi"
Ido ya sake rufewa"
Momy juya tayi zata fita tare da fadin Asma'u zo"
Abaya tabi momy har cikin dakinta, nafisa ce zaune aciki tana nuke kaya, juyawa momy tayi ta kalleta tace....
Nafisa bamu guri"
Ajiye kayan take hannunta tayi ta fice"
Wani kallo momy tama ma'u sannan tace... .
Asma'u wannan watan kinyi al'ada?
Idonta tasa akasa sannan tace momy ai lokaci beyi ba"
Shiru momy tayi zuwa can tace....
Amman wancan watan daya wuce kinyi?
Eh"
Gaban ma'u banda faduwa babu abinda yake"
Sallaman doctor ne yasa momi mikewa ta fice"
Zuwa can momy ta dawo tace zo asma'u
Suna zuwa momy tace Dr gata"
Kallo kawai tabi momy dashi har aka debi jininta bata daina kallon momy ba"
Itama momyn kauda kai take tare da cin magani, cikin daure fuska tace doctor kaje ka gwada min yanzun dan Allah hankalina bazai kwanta ba har sai naga saka makon"
Hankalin ma'u Kara tashi yayi, kafa fowanta babu kwari"
Dakin Jamal suka koma yayin da momy ta zauna ta hakince ko fara'a bata yi"
Itama ma'u ta kurewa tayi saboda ganin fuskan momy babu annuri"
Saida Dr ya kwashe kusan awa 2 ya dawo"
Hannu ya mikawa usman suka gaisa sannan ya mikawa Jamal, tare da tambayan ya kafa?
Sannan ya juya gurin momy ya mika mata farar takarda tare da fadin Congratulation tana dauke da ciki na sati 2"
Yake Momy tayi sannan ta mike tare da fadin nawane kudin ka?
Adadin kudin ya gaya mata ta biya sannan ya juya ya tafi"
Shiko usman tunda yaji abinda likita yace ya kurama Jamal ido, so yake yasan me zaice amman Jamal yaki bude ido"
Itama ma'u kasa tayi da idonta tare da zallar tashin hankali"
Takardan momy ta jefawa ma'u tare da fadin Asma'u ina kika samo ciki?, bayan mijin ki na kwance ko bayi zashi saida dibara, yau satin shi 5 agidan nan, aina aka samu cikin sati 2?
Cikin sauri Jamal ya bude idonshi tare da kallon ma'u"
Kokarin tashi yake ya zauna dan haka usman ya taimaka mishi"
Hankalin usman tashe yake, ya rasama me zaice"
Momy ta sake cewa ba dake nake mgn ba"
Kuka ma'u ta fara harda shashsheka, domin ita yanzun batasan me zatace ba, domin ko a film bata taba ganin inda uwar miji ta tare matar danta da wannan tambayan ba"
Zaune Jamal yayi yana neman ta ina zai fara mgn mezaice? Ince cikina ne? Kai gaskiya inajin kunyan momy sosai bazan iyaba, acikin zuciyarshi yace Allah yasa husna tace cikina ne, nikuma idan antabaye ni nace eh kawai"
Daidai lokacin usman ya matsa kusa da ma'u yace dan ubanki badake ake mgn ba?
Idonta ta daga ta kalli jamal alma ya mata da hannu tace shine, kyauda idonta tayi tare da tsananin jin zafinshi aranta"
Gadan kadan usman ya nufi ma'u harya kai mata duka ta guce, ta nufi bayan Momy"
Cikin sauri momy ta matsa tabawa usman hanya"
Usman karka daketa, nawane cewar jamal
Cikin sauri momy ta matsa bakin gadon tace naka? Kana hauka ko? A yadda kake dinnan inakai ina kula mace, mezaka iya kafafuwa a daure kana tafiya daker, daidai da bayi sai an raka ka"
Shiru yayi yana sosa kai yazama dole ya bude baki yai mgn idan bahaka ba momy zata sheganta masa ciki"
Sosakai yayi tare da kauda kai gefe yace momy nidai kibar mgnn nan nawane wlh"
Tsakanin Jamal da momy kallon juna suyi inda momy take ganin ko ganin usman ne yasa yace nasa ne"
Jamal karka maidani mahaukaciya bawasa nake dakai ba,
Kara sunkuyar dakai yayi"
Karemai kallo momy tayi, sannan ta juya ta fita cikin tsananin tashin hankali, ma'u ma bayanta tabi"
Usman ne ya karasa bakin gadon yace jamal kaina ya kulle, tayaya asma'u zata samu cikin sati 2, dana Wata 5 akace zan yadda, kaida ke kwance tare fah muke kwana, har Bayi ni nake karaka ka"
Kanshi akasa yace.....
Wlh usman kuna bani mamaki kuntaba ganin inda ake tare matar aure da mijinta ace waye ya mata ciki?
Cikin ido usman ya kalli Jamal yace....
Me kake nufi da wannan mgnr?, kafito fili kamin dallah dallah"
Tsaki Jamal yaja sannan yace, dallah mlm karka dame ni, inace fa'iza tsohon ciki gareta, na taba tirkeka nace maka wayayi mata?
Cike da mamaki usman ya kalli Jamal sannan yace....
Kana nufin kaikayi kenan?
Dagowa Jamal yayi ya kalli usman sannan yace eh ninayi"
Kaika yi?
Eh, ya fada tare da jawo bargo ya rufe kansa"
Girgiza kai yayi tare da fadin gaskiya Jamal basan baka da hankaliba saiyau, banga amfanin zamana agidan nan ba wlh, yau yau zanbar garin nan, nakashe komai nawa nabaro aikina da iyalina dan nayi jinyanka amman kun maidani hoto, ni dan iskane haka kawai zakasa yariya ta rainani, Ashe shiyasa kwanaki da doctor yace ansawa kafa ruwa, dagewa kayi kai baka saba har kanacewa wai nina zuba maka, narantse da Allah dakai karamin yaro ne saina maka matsiyacin duka zanbar garin nan"
Bude fuska Jamal yayi sannan ya kalli usman yace....
Haba usman yazaka tasani agaba kaitamin fada, Husna fa matata ce, ba zina nayi ba"
Ai bance ba matarka mace amman ai anabarin halas kodan kunya sannan ga ciyon dake jikin ka, baka tunanin gurin ya samu matsala ko fah taka kafar ance karkayi"
Nifah usman bantaba karanta aya ko hadisi daya fadi haka ba, kuma ni wannan ciwon be isa ya kashemin rayuwa ba"
OK toh shikenan, azuciye usman ya fita"
Daddare ma'u na zaune momy ta shiko tace biyoni"
Hijjabinta tasa tabita abaya, dakin da Jamal yake ta nufa dan haka tabi bayan Sa"
Ma'u na shiga taga daddy adakin dan haka hankalinta ya kara tashi"
Tunkafin momy ta zauna daddy yace....
Asma'u taho nan Ki zauna"
Inda ya nuna mata ta zauna tare da matso hawaye"
Ahankali daddy yace.....
Jamal ance matarka nada cikin sati 2, shine nake son sanin ko naka ne?
Muyar kasa kasa yace eh"
Shiru daddy yayi sannan yace toh nakane dai kace ko?
Eh yasake fada ahankali"
Shiru daddy yayi zuwa can yace....
Toh Alhamdulillah Allah ya rabasu lfy, daman bawani abu bane yasa na tambaya saidan naga baka lfy, kuma matsalar acinya take, shiru ya sake yi sannan ya sake cewa toh shikenan babu koma, jiya usman yace ka kwana kafa na damun ka, dan haka yanzun likita zaizo ya dubaka"
Momy ko babu abunda take banda hararan Jamal ammam saiyaki kallonta"
Karfe 8:00pm likita ya shigo kwance kafar yayi yana mamakin yadda akayi gurin ya rarike haka"
Ganin inda doctor yake kallon gurin yasa daddy da momy lekawa, sosai gurin ya zurma, juwa yayi ya kalli Jamal yace kafannan anasa mata ruwa meyasa bazaka taimaki kanka ba, kaifa ba karamin yaro bane, meyasa zakana mayar mana da aiki baya"
Haka Dr yaita fada daga karshe ya wanke wajen sannan ya kara ja musu kunne"
Likitan na fita momy ta rufe Jamal da fada, ta inda take shiga ba tanan take fitaba"
Daidai lokacin usman ya shigo nan momy ta kwashe yadda sukayi da dr ta gayamai, sannan ta kara da cewa ashe Jamal da kanshi yake shekawa kansa ruwa saboda rashin hakuri irin nashi, wai ahaka dinnan ya danne yariya ya dirka mata ciki"
Daddy ne ya fara dakawa momy tsawa tare da fadin wai menene haka?
Itama cikin takaici tace barni alhaji abin ne yake bani takaici wlh, ji inda usman ya kashe komai nasa ya zauna dan yaga kasamu lfy"
Jamal ji yayi kamar ya nutse saboda tsabar kunya"
muyar usman game yana cewa.....
Aini momy gobe da sassafe zanbar garin nan, Asma'un tayi jinyar shi"
Kwama cala kenan, usman babu inda zaka, dan wlh idan akabar Jamal da asma'u adakin nan kafar Jamal rubewa zatayi"
Daddy kallo yabi Momy dashi sannan ya girgizakai ya fice domin kalamanta kunya take bashi agaban yara"
Momy naganin fitan dadddy tace....
Gobe idan Allah ya kaimo dakaina zankai Asma'u Kano taje taji da abinda ke cikinta, badan bazan iya jinyarta ba, saidan dan wannnan me wutan cikin....
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
Dedicated
*Sadnaf*👍🏻💋
9⃣6⃣to9⃣8⃣
Jamal be sake kallon inda suke ba, itako ma'u tana takure agefe"
Tattaunawa suka cigaba tsakanin momy da usman daga karshe momy taja ma'u suka wuce"
Adakinta ma'u ta kwana motsi kadan momy taji ma'u tayi zatace me kike so?
Washegari da safe momy da kanta ta hadawa ma'u kayanta sannan tace tayi wanka su tafi"
Wankan taje tayi saidai jikinta babu dadi hakama zuciyarta, azahiri batason Tafiyan tafison ta zauna gurin mijinta"
Bayan ta gama shiryawa ta zauna momy kadai take jira, tsintan kanta tayi da rafka uban tagumi"
Ahaka Momy ta sameta, dan haka ta tsaya cak tanabin ta da kallo sannan ta karasa kusa da ita tare da kiran sunan ta"
Ma'asawa tayi tare da kallon momy"
Ahankali momy tace.....
Asma'u anya kuwa kinason tafiyan nan?, kodai za'abar tafiyan ne?
Cikin sauri ta girgizakai tare da fadin inaso"
A'a asma'u bayan gashi naga duk kin shiga damuwa, ni asma'u bawai inason na rabaki da Jamal bane, wlh ciwon shine yake tayar min da hankali, kuma shi duk abinda likita yafada beji, idan wani abu ya faru Mu zai bari da wahala"
Nisawa tayi sannnan taci gaba da cewa kiyi hakuri nasani daga ke har Jamal bazakuji dadin hukunci na ba amman nan gaba zaku gane gata ake muku"
Tashi sukayi da nafisa kadai sukai sallama suka dauki hanya"
Karfe 2:38pm suka isa Kano suna isa gidan ma'u taga komai ya canja, kamar bata taba rayuwa agidan ba"
Mehadin ne yafara shiga da akwatin ma'u anan ne mama tagane sunyi baki"
Har sukashi falon momy na rike da hannun ma'u"
Da fara'a mama ta tarbe su, nan tashiga hidima dasu, bayan sun natsa ma'u tashi ta basu guri"
Dakinta na da ta shiga nan abubuwa da dama suka dawo mata, kwallace tacika mata ido, rayuwan su da deeni ne ya fara fado mata, dan haka batasan sanda ta fara hawaye ba"
Anan bacci ya kwasheta batare da tasan lokacin ba"
Ta dauki dogon lokaci tana bacci sai can kusan yamma ta farka"
Tana tashi taga wayarta tare da kudin masu yawa agefenta, kwasan kudin tayi ta nufi falo"
Babu kowa afalon dan haka ta nufi kitchen acan ta samu mama tana aikace2"
Mama na kallonta tayi murmushi tare da fadin Asma'u kin tashi?
Cikinjin kunya tace natashi mama ina momy"
Ai tuni ta wuce"
Mun shigo kina bacci tace abarki kar atashe Ki"
Wani iri taji azuciyarta, amman taki bari mama ta gane"
Tare da ma'u suka karasa aikin, bayan sungama tacewa mama zata gidan yaya usman"
Shiru mama tayi zuwa can tace......
Kin ganki, daga zuwanki zaki fara yawace yawace"
Turbune fuska ma'u tayi sannan tace.....
Mama gidan yaya usman din ne yawo? ni idan na tafima sai gobe zan dawo"
Tabe baki mama tayi sannan tace toh ai saiki bugawa mijinki waya idan ya amince drive ya sauke ki"
Da saurinta ta juya daki gyalenta ta dauka ta saka sannan ta fito ta samu mama zaune agefen kujera"
Kallonta tayi tace kinmai wayan ko?
Eh kawai tace tare da gyara gyalenta"
Sosai fa'iza tayi murnan ganin ma'u suna rungume da juna, zuwa can ta kalli ma'u ta sheke da dariya"
Dariya taitayi harda rike ciki, ma'u ta tsaya sororo tana kallonta"
Zuwa can fa'iza ta sarara da dariyan sannan ta kalli ma'u tace.....
Asma'u kenan, jiya keda mijin ki kuncikawa yayan ki ciki, ashe Jamal dan duniya ne ban sani ba?
Tsaki ma'u taja sannan ta daure fuska tare da fadin anty dan duniya fa kika ce?, kina nufin dan iska ne?
Cikin sauri fa'iza tasa hannunta abaki tare da fadin alallai, ni karkimin fassara bahaka nake nufi ba, kallon ma'u ta karayi har yanzun ranta abace yake, cikin ido ta kalli ma'u tace sai yau na yadda kiyayya tana komawa soyayya, kuma na yadda duk abinda babba ya hango yaro ko yahau rimi bazai gano shiba"
Saboda me kika ce haka?
Murmushi fa'iza tayi sannan tace.......
Na tuna lokacin da kike cewa ke bakison jamal kin tsane sa, ke har cewa kikayi idan aka aura miki shi saikin kasheshi, sai gashi yanzun kin fada kyaunar Jamal dumu dumu, lokacin da Jamal ya bace kika zama kamar zararriya, da ace har yanzun ba'aga Jamal ba wata kila dakin zare"
Shiru ma'u tayi tana nazari, zuwa can tace Anty?, wlh da kwata kwata bani da hankali, idan na zauna ina tunani sainace da wani hauka ne ya shigeni, dan rashin hankali na zauna naita musu dasu Abba, yana cewa ga abinda zanyi inacewa ga wadda nake so, sai yanzun naki ganin illar sarashin jin maganar iyaye, ba dama nayiwa yaya jamal wani dan abu nan danan saiya hassala yaita fada, dan haka yanzun duk abinda yace banamai musu inba haka ba saiyace ai lokacin deeni kaza, akwai wata mgn da mukayi nida deeni bakaramin mamaki nayi da naji abakin yaya Jamal ba, nan ta kwashe komai tagayawa fa'iza"
Jinjina kai fa'iza tayi tare da fadin gsky kuruciyar ki kinyi hauka da yawa, to yanzun gayamin matsayin deeni azuciyar Ki"
Cikin sauri tace....
Deeni?, wlh bana son ganin deeni domin idan naganshi tausayin shi yana kamani, Anty bazan boye miki ba, ayanzun inajin son Jamal kuma bana neman abun da zai rabani dashi, zama na dashi yasa na fahimci halin shi, halayen shi masu kyaune, dabi,un shi suna burgeni, anty yaya Jamal be faye son mgn ba duk abin da zai fito bakinsa me mahimmanci ne, sannan nakula yana tsananin sona dukda yana boyewa bayason nagane ko wani ya gane haka"
Nisawa tayi sannan taci gaba da cewa anty yaya jamal ya dade yana sona amman be bari kowa ya saniba yaita dannewa, kuma koda naje gidansu amatsayin matar sa ko kallo na bayayi, yana nuna bana gaban shi, Amman bayan bacewan shi da aka gano jakarshi nagono sirrikan shi da dama, hutonane bila adadin awayar yaya Jamal wadda bansan sanda ya dauke su ba, sannan hutonane akan wayar Sa, tun alokacin naji sonshi ya ratsa ko ina ajikina"
Dariya fa'iza tayi sannan tace Jamal dai yaci gari kenan?, ya ture gwamnatin deeni"
Girgiza kai tayi tare da fadin to anty idan ma inasonshi yaya zanyi?, da dai ammana umarni da auren maza 2 to wlh dana kara da deeni dan wlh tausayin deeni ya hanani nayi walwala, ina tananin tausayin sa, kuma inaso rayuwar sa ta inganta, wani lokacin inaganin laifin zuciyata data fada son jamal"
Hirar tasu bata kare bace, dan haka sukayi shirin zuwa gidan dada"
Tafe suke suna cigaba da hirarsu, acikin su babu wadda ta tambayi mijinta"
Sun kusa isa gidan ma'u ta tsaya tana waige"
Kallonta fa'iza tayi tare da fadin menene?
Ma'u na wage2 take fadin akwai abinda dada tamin kwanaki dan haka wlh yau saina tsoratata"
Tsaki fa'iza taja sannan taja hannun ma'u suka nufi gidan"
*****
*Abuja*
Momy zaune ita da deeni jefi2 suna hira"
Zuwa can deeni ya kalli momy yace momy yau ke kadaice agidan naji shiru ne?
Murmushi tayi sanna tace wlh dagani sai jamal Nafisa sun fita ita da usman, Asma'u kuma tana Kano"
Kano? Kano kuma? Meyasa zata tafi gano bayan mijinta bashi da lafiya"
Cikin takaici Momy tace, to ai ita ba jinyarshi zata iya ba, itama yanzun tana neman me kula da itane tunda karamin jiki gareta"
Cikin sauri ya runtse ido tare da fadin.......
Ciki? Ciki kuma? Haba wannan ma ai ba mgnr dazata sabo bane"
Kallonshi momy tayi da sauri, tare da fadin meka ce?
Mikewa yayi tare da fadin babu komai' ina zuwa"
Wucewa yayi cikin sauri yana shiga dakinsa ya dungule hannun ya Saki wani kara, jikin bango ya manne sannan ya zame kasa tare da fashewa da kuka, kuka yake kaman karamin yaro, hawaye ne shame2 a idonshi, yanzun asma'un shi tabari Jamal kusanceta anya kuwa zai iya rayuwa, fashewa yasa keyi da kura tare da gwara kansa da bango, wani irin tsananin kishine ya taso masa wadda yakeji bashi iya sarrafa kansa wani irin hawaye ne masu danko suke zubo masa, tare dajin kirjin shi kamar ana sukamai kibiya.......
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
Dedicated
*Meelat Musa*
9⃣9⃣to 1⃣0⃣0⃣
Kwanciya yayi akasa banda numfarfashi babu abin da yake"
Haka ya kwana cikin tsananin damuwa da bacin rai, wadda tunda yazo duniya be taba jin irinsa ba"
Kwace kawai yake hawaye na malalowa ta gefen idon shi"
Babu wadda yasan halin da yake ciki, acikin zuciyar shi yake addu'an Allah ya dauki ranshi, domin yana bakin cikin yaga ma'u da cikin wani bashi ba"
****
Itako ma'u azauren gidan dada ta tsaida anty fa'iza daker ta yadda ta tsaya, cikin gidan ta leka ta hango dada na wanke kayan miya"
Kara lekawa tayi sannan ta gyara murya tare da magewa tace......
Wai ana sallama da Dada"
Batare da dada ta waigo ba tace....
Kaji wata fitina da yamman nan, koma wanene ce mishi ya shigo"
Murmushi ma'u tayi sannan ta kara make murya tace......
Tsohuwa shamsun duna ne fah, kuma tare yake da gayyan kar......
Ai dada bata bari taji karshen zancen ba ta tuntsurar da kayan miyar, ya watse akasa sannan tabi takai a guje"
Dakinta ta shige ta maida sakata"
Fitowa ma'u tayi tana tuntsira dariya, fa'izama dariyar take, tare da nuna ma'u da yatsa tana fadin ke ko?
Abakin kofar suka tsaya fa'iza ce taita kwalawa dada kira tare da fadin kibude dada nice Fa'iza"
Ta fadi haka,yakai so uku dada bata amsa ba"
Zuwacan fa'iza ta sake cewa dada?
Na'am ta fada ahankali"
Nace ki bude"
Ahankali tace bakiga wani dan daba anan gidan ba?
Babu kowa dada Asma'u ce fah take tsorata ki"
Ahankali ta sake cewa ina asma'un take?
Gatanan muna tare"
Bude kofar dada tayi ahankali ta leko da idonta guda daya, ganin su tsaye yasa ta karasa bude kofar tare da fadin......
Kinci jakar ubanki, kinga min fitsararriyar yarinya, shikenan kuma na zama matoni"
Wuceta ma'u tayi ta shige dakin ta haye gadon dada me runfa ta kwanta"
Suma shigowa sukayi dada nacigaba da fada"
Baza ma'u tayi da ita hartayi ta gama sannan ta leko da kanta ta kalli dada tace.......
Ai ni munsa kafar wando daya dake dada tunda kikace wai idan kikazo gurina zamu hada baki dame kare mu kashe ki"
Murmushi dada tayi kadan, sannan ta nemi guri ta zauna tare da fadin"
Aini zolayarki nake takwara mutuwa ai ita muke jira, ina me gidan naki tare kuke?
Me kare?, ma'u ta tambaya idonta kan dada"
Kai, kai, asma'u
wai meyasa kike fadar min da gaba ne?,
Sanin kankine bana sonjin sunan wannan ibilishin yaron, wlh kika sake zan kira ubanki nagaya mai"
Daga ma'u har fa'iza dariya suka Saka, ganin inda idon dada yayi wuki2
Tare da fa'iza suka karasa aikin gidan yayin da ma'u ke kwance tana kwasan bacci"
Sai kusan sallar mangariba ta tashi lokaci sungama hada abincin dare"
Tuwon shin kafa ne miyar ganye, kallon miyar kawai ma'u tayi ta fara sheka amai"
Bayan ya lafa mata Anty fa'iza ta dawo da ita dakin dada, ma'u rike hancinta tayi da hannunta guda 2
kukarin kuka ta fara tare da fadin anty ni kizo muje gida wlh gidan wani iri wari yake yi mara dadi"
Wani irin kallo dada tawa ma'u sannan ta kalli fa'iza tace......
Wannan yariyar ko ita kadai ce?
Cikin sauri asma'u ta mike ta figi gyalenta tayi waje"
Dadama tashi tayi tana fadin ke takwara dawo kici tuwo"
Ina lokacin ma'u harta bar kofar gidan"
Gidan abbanta ta nufa tana tafe tana hada hanya"
Afalo ta samu daddy sunacin abinci shida mama"
Zama tayi fuskarta dauke da fara'a, nan ta shiga gaida abba"
Wani irin fara'a tagani kwace afuskan abba rabon da taga irinsa afuskar abba ta dade"
Amsawa yayi sannan ya tambayeta jikinta tare da jikin yaya jamal"
Cikin jin kunya ta amsa sannan yashiga samata albarka"
Dadi taji sosai ganin abba yabar fushi da ita"
Zuwa can taji yace matso muci abinci"
Karasawa tayi ta dauki cukali ta faraci, badan ranta nasoba saidan tayin da abba ya mata"
Sosai taci abincin jifi jefi abba najanta da hira, zuwa can taji amai na taso mata daurewa taso yi saidai hakan ya gagara, ji tayi zai kwace mata dan haka ta tashi aguje ta nufi toilet"
Kallonta abba yayi itama mama cikin sauri ta aje cukalin dake hannunta tare dabin bayan ma'u"
Sousai ma'u tabawa mama tausayi, wani irin wunkuri take kamar hanjinta zai fita"
Daker aman ya tsaya sannan mama ta wanke mata jiki ta fito da ita"
Daki taso wucewa da ita amman abba yace abarta afalo tasha iska"
Wani irin kunya ma'u takeji, takasa hada ido da abba, sun sunne kai take taki yadda su hada ido da abba"
Tana cikin wannan halin taji muryan abba yana cewa.....
Mamana me kike son ci?
Bakomai abba banjin yinwa"
Mikewa Abba yayi tare da fadin a'a mamana kiyi tunani bazaki rasa abinda kike so ba"
Shiru tayi tana dad'a boye fuska"
Ganin haka Abba yayi murmushi ya juya ya fita"
Bayan fitan abba ma'u ta mike ta shige daki ta kwanta, ba dadewa bacci ya dauketa"
Cikin baccinta taji wani irin kamshi na addabarta, jitayi koma menene tana sonci, dan haka ta tashi da sauri tana baza hanci taji ta ina kamshin ke tasowa"
Daga can gefe ta hango wasu manyan ledoji sunkai 4, saukowa tayi ta fara budewa"
Kayan kwalama ne cike adayan ledan, dayan ko kajine manya manya guda 2, nan ma'u ta shaida sune suke wannan kamshin, bata tsaya duba sauran ba tahau ci"
Ci tayi tai kat, nan bacci ya sureta"
Misalin 11:00pm mama tashigo, bakaramin dadi tajiba dataga ma'u taci naman sosai"
Kwashe sauran kayan tayi ko wanne ta ajeshi a inda ya dace sannan ta tashi asma'u tace tashi Ki koma gado"
*****
Jamal ne kwance agado sai juyi yake ma'u yake son agani, raboshi da ita tun shekaran jiya da suka fita tare da momy"
Yana cikin wannan tunani usman ya shigo, cikin fara ya zauna akusa da Jamal tare da fadin.....
Yazun muka rabo da bello, yashigo gari jiya da daddare"
Tsaki Jamal yaja, sannan yace, wai yaushe zaka wuce ne?, nifa ka takuramin wlh"
Wata yar karamar dariya usman yayi tare da daukan wayarsa yana dannawa"
Tsaki Jamal ya sake ja sannan yace.....
Haka kurum mutum da matar sa ahanashi ganinta"
Eh kuma dole mutum ya hakura ko yaki ko yaso nima matata nabaro da tsohon ciki"
Gyara kwanciya Jamal yayi sannan yace.....
Nina kiraka?, kaikaga zaka iya, ni da karfina babu abin da bazan iyaba wlh, dan Allah ka tafi wajen matar ka, banason jiyar na warke"
Wani irin kallo usman yayiwa Jamal sannan yace waikai wani irin mutum ne?, nifa sirikin ka ne amman kake gayamin irin wannan mgnr"
Jan jiki Jamal yayi ya zauna sannan ya kalli usman yace......
.
Nufin ka naji kunyan ka?, aini bansan kai sirikina bane, da kanayin sirikuta dani da bakazo jinyata ba, har yanzun kai abokina ne"
Mikewa usman yayi tare da fadin shikenan zantafi, tunda kace na takura maka"
Kauda kai yayi usman na daf da fita jamal yace.....
Ka rokar min momy dan Allah ta turomin Husna mugaisa amman dan Allah karka ce injini, cewa zaka yi ya kamata ne"
Waigowa usman yayi yamai wani irin kallo sannan yace......
Wacce Husnar?
Guda nawa ka sani?
Murmushi usman yayi sannan yace ai tunjiya tana Kano"
Azabure yace kano?, mgnr momy ne ya fadomai, jawo kafafuwan shi yayi ya ajiye akasa sannan yace......
Taya momy zatamin haka sabo da Allah?, harta tura Husna Kano batare da amincewata ba"
Jim usman yayi zuwa can yace, to ai laifin ka ne Jamal"
Tayaya ya zama laifina usman? Me nayi? Da sanda naki auren surutu akaita min, yanzun kuma dayin ba'a kyaleni ba, sai surutu akemin salon kananan yara su raina mutum"
Yazun da aka turata kano, can ma yayatani za'yi kenan"
Kalaman jamal basuwa usman dadi ba, cikin bacin rai yace......
Wai meyasa idan ranka ya baci baka tauna lafazin bakin kane?, waye kake cewa wai ana yayata ka, kadai san bani bace na turata ko?
Jamal kasa mgn yayi bayan wasu mintina ya sake cewa......
Toh naji, yanzun abin da za'ayi kaje ka samu momy kawai atura drive ya dawo da ita"
Usman be juyo ba, yace ai kana da kafa kuma kana da baki, ko ba yanzun ka gama cewa babu abin da baza ka iya ba?
Eh amman kasa mgnr da nauyi, bazan iya taren idon momy na fada mata haka ba"
Mikewa usman yayi ya fice abinshi yayin da Jamal yaita sauke ajiyan zuciyan bacin rai"
****
Sai dare momy ta fito falo, zaune tayi tana jiran shigowan Usman tare da deeni, tun safe yau bataji motsin su ba, garama usman dasafe kan ya fita ya shigo har daki sun gaisa"
Amman deeni rabon da ta ganshi tun taren da ta dawo raka ma'u kano"
Shirun taji yayi yawa dan haka ta mike ta nufi dakin Jamal"
Yana zaune ya hada kai da guiwa"
Kai Jamal yau Usman lfy kuwa har yanzun be dawo ba?
Dago jajayen idon sa yayi ya sauke akan momy, tare da fadin nima shinake jira kuma nakira no dinshi kusan so 10 amman be daga ba"
Atsorace momy tafara dannan wayarta tare da fadin to lfy kuwa?
Bata rufe baki ba taji andauki wayar dan haka ta fara fadin usman ina ka shige gashi har dare yayi?
Momy wlh tafiya ce ta taso min dan haka na wuce, yanzun haka ina kano, gobe zamu wuce Sokwato"
Cikin baccin rai momy tace wanni irin tafiya ne zai taso dahar zaka kasa mana sallama haba usman gaskiya baka kyauta ba"
Hakuri yaitaba momy sannan ta mikawa jamal tana fadin ga Jamal"
Saidai usman najin Muryan Jamal ya kashe wayyar"
Juyawa momy tayi hankalinta atashe tana fadin saura deeni barinje na duba ko shima garin ya bari beyi sallama ba"
Wani Irin abu Jamal yaji yana mai yawo akai, wani mummunan tunan tunanni ya ziyarci zuciyar shi, Husna na kano, Deeni ma yabi bayanta......
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
Dedicated
*Rukayya Hassan Osman*😘
1⃣0⃣1⃣
💝💝💝 Cikin tsananin fargaba momy ta tura dakin deeni"
Abude yake saidai babu kowa afalon, cikin dakin ta nufa tana Raba ido"
Akasa ta hango deeni yana numfashi daker, da gudunta ta karasa tace shamsundeeni meya sameka?, baka da lfy ne"
Be iya amsawa ba, kokarin dagashi ta fara amman ta kasa juyawa tayi waje tana kururuwa"
Daddy ne ya fara fitowa sannan nafisa, ganin inda momy tabi yasa sukabi bayanta"
Shima daddy ganin jikin deeni hankalin daddy ya tashi sosai, me gadi yahau kira, juyawa yayi yakalli nafisa da tunda taga deeni ta fara kuka yace"
Kiramin me gadi"
Nafisa ta juya zata fita sukaci karo da Jamal yana dingisa kafa"
Kaikuma meka fito yi ? Ina zaka?
Kallon deeni yayi tare da fadin bakomai"
Toh maza ka koma daki"
Daidai lokacin me gadin ya shigo, acikin kankanin lokaci suka isa asibiti"
Kan gado suka daura deeni sannan suka fara duba shi"
Daga momy har daddy hankalin su atashe yake"
Ba'a dauki lokaci ba likitan ya fito ya nufi office dinshi"
Daddy ne yabi bayan shi
Cikin natsuwa likitan ya gayawa daddy deeni yana dauke da mummunan ciyon zuciya, wadda yayi karfi ajikin shi sosai"
Sannan ya shiga bashi shawaran cewa adaina bata masa rai, ayi kokarin duk abinda ya nuna yana so anemar mai"
Sannan ya kara da cewa zaman shi cikin damuwa na sati biyu zuciyar shi na iya bugawa"
Bayan daddy ya fito ya samu Momy da nafisa tsaye akan deeni, nafisa kuka kawai take"
Cikin tausayawa daddy ya kalli deeni bacci yake daman likitan yace sai safe zai tashi"
Washegari daddy yayiwa alhaji bashir waya ya sanar mai suna asibiti deeni babu lfy"
Cikin kankanin lokaci alhaji bashir ya iso tare da ummi"
Sosai hankalin ummi ya tashi domin ita tasan ciwon deeni be rasa nasaba da asma'u"
Har yanzun bacci yake be tashi ba, dan haka daddy ya kalli alhaji bashir yace.....
Muje gida akwai mgnr da zamuyi"
Nafisa kawai akabari agurin deeni"
****
Bayan sun isa gida afalon daddy suka zauna yayin da Jamal yake daya daga cikin dakunan dan haka duk abin da suke cewa yana jin su"
Daddy ne ya shiga gaya musu abun da likitan yace, sannan ya kara da cewa ya zamar mana dole mu nema mai lfy be kamata mubarshi ya kare rayuwa awahala ba, ina tsananin tausayawa rayuwar Shamsudeen inason ya zama mutum managarci banaso rayuwar shi ta kare ahaka, kuma insha Allahu zanyi korin nema masa abin da ransa ke so"
Cikin kuka ummi tace ninasan abinda yake damun auta, ya dauki son duniya ya daura akan wata yariya, nayi nayi yai hakuri yabar musu Amman yakiji, ubata yai mata aure tuntuni yakuma ce tirrr yaba shi aureta'
Bantaba ganin auta yaso wani Abu aduniya ba kamar yadda yaso asma'u"
Bacin raine kwance akan fuskan alhaji bashir daddy da momy ko hankalin su tashi yayi domin Susan cewa asma'un deeni itace matar jamal
Mikewa alhaji bashir yayi tare da fadin waye uban yariyar"
Shima daddy mikewa yayi tare da goya hannun shi abaya yace zancen waye mahaifin yariyar ai be taso ba, dafa alhaji bashir daddy yayi sannan yaci gaba da cewa....
Bashir kabarmin komai ahannuna nima ai shamsudeen d'ana ne dashi da Jamal duk daya ne, insha Allahu zan nemo mafita"
Duk waddan magan ganun Jamal naji Dan haka hankalin shi ya tashi, kasa zama yayi ya mike tsaye zufa yaji yana karyo mai, tunanin shi yaya zaiyi yaga Husna kusa dashi beso Husna tayi nisa dashi"
Yana cikin wannan tunanin yaji alhaji nashir na fadi"
Inda ace akwai yadda za'ayi musame ita yariyar asma'u ta zauna kusa dashi kona sati 1 ne wata kila ya dawo cikin haiyacin shi"
Cikin sauri momy ta mike tsaye fuskokin su ta kallah sannan ta fita afalon"
Shiko Jamal jiyayi kirjin shi ya buga daramm afili yace matar tawa?
Bazan yadda da wannan shawarar ba, bazata taba yuwuba"
Daha suka tashi kowa zuciyar shi da abinda yake sakawa"
Daddy da alhaji bashir ne suka koma asibiti amman tare da ummi, momy ko cewa tayi anjima zata zo"
Daker momy ta iyayin abinci akakai asibitin, Sanan ta zauna ta rafka tagumi"
Jamal ko ya kasa zaune ya kasa tsaye kano yake son zuwa amman yadda yakejin jikin shi bazai iya fitaba ji yake kamar yana tsami domin rabon shi da wanka tun ana gobe usman zai tafi"
Mikewa yayi ya nufi toilet cikin dibara yayi wankan ya fito"
Gyara jikin shi yaye tare da fesa turare sannan ya dauko manyan kaya ya saka tare da daura hula"
Tafe yake yana dingishi har ya isa dakin momy, ahankali ya tura kofar tare da sallama"
Cire tagumin momy tayi, sannan ta dago ta kalli Jamal"
Kyau taga yayi sosai, mikewa tayi tare da fadi Jamal wanka kayi ne?, meyasa bakajin mgn?
Momy jinayi ina tsami, dama usman ne kemin tun tafiyan shi kwana 2 kenan banyi wanka ba"
Ai da ka kirani namaka, Jamal ka daina wasa da lfyr ka, yanzun kuma da ka kaso kafa ka taho ina zaka"
Kai ya sosa sannan yace, fita zanyi momy, akwai wani aiki ne zan duba ko yana tafiya daidai, yau zan dawo insha Allahu"
Hmmm Jamal wanne aikine? Inace manyan ku sunsan halin da kake ciki?
Eh sun sani momy, wannan aikin idan ban duba ba za'a iya samun matsala ne"
Shiru momy tayi kamar baxatayi mgn ba zuwa can tace.......
Toh shi kenan Allah ya tsare ya dawo dakai lfy"
Ameen yace sannan ya mike ya fara tafiya, harya kai tsakiyan falon Momy tace......
Jamal wanne garine zaka?
Jam yayi kamar bazai yi mgn ba zuwa can yace Kano"
Kano momy ta tambaya sannan tace zonan Jamal"
Cikin sanyin jiki ya dawo ya zauna tare da sauke kansa kasa"
Saida momy ta gama kare mai kallo sannan tace.....
Jamal kace min kawai zaka wajen matar ka, ai bawai rabaku nayi ba, amman tunda hakane ka koma daki zansa dawo da ita"
Jikin shi sanyi yayi bazai iya musawa momy ba, amman hankalin shi nagun husna"
Har daki momy ta raka shi sannan tamai gargadi karya ya sake fitowa"
Momy bata koma asibitiba har dare, tunanin mgnr bashir take, tayaya matar da tai aure za'ace ta zauna gurin balagaggen namiji, hakika tana taya Jamal kishin matar Sa, kuma tana tausawa deeni"
Daddre ma kasa bacci tayi damuwa yayi mata yawa"
10:30pm daddy ya shigo har cikin dakin Momy, nafisa na biye dashi"
Guri ya samu ya zauna nafisa ko gaida Momy tayi sannan ta wuce dakin ta, tare da fadin bari naje nayi wanka"
Amsa mata momy tayi sannan ta maida hankalinta kan daddy"
Hularshi yacire ya aje agefe, sannan ya kalli Momy"
Kauda idonta tayi tare da fadin ya me jikin?
Yaji sauki, ya farka tunda rana, sai dai har yanzun kuka yake yi, kuma ya fada ma abinda ke damun sa yaki fada"
Shiru daddy yayi momy ma mikewa tayi tafara hada kayanta"
Muryan daddy taji yace......
Zauna mana akwai mgnr da zamuyi"
Cikin sauri momy ta aje kayan ta koma ta zauna"
Gyaran murya daddy yayi sannan yace......
Inason ki saurareni da kyau kuma ki fahimceni"
Wani irin kallo momy tamai sannan tace inajin ka"
Akan mgnr shamsudeen ne, nasani kin san cewa asma'u itace yariyar da shamsudeeni ke matukar so"
Cikin ido momy takalli daddy tace....
Ina jinka"
Cigaba daddy yayi da fadin dan haka nake ganin mezai hana shi Jamal ya hakura ya saketa.......
Mikewa momy tayi da sauri tare da fadin Alhaji kasan abin da kake fada kuwa, Asma'u fah matar Jamal ce, kuma ciki gareta, tayaya za'ace ya saketa shamsu ya aura, antaba haka"
Dakewa daddy yayi tare da fadin idan ma ba'ataba za'a fara akan su, dan hakan ne kadai mafita idan ba hakaba za'a iya rasa shamsundeen"
Alhaji wannan mgnr bazai yiwuba sam, dan Jamal nason matar shi, tunda nake da Jamal banta tunanin zaiso wani abuba kamar yadda yake son matar shi"
Gutun murmushi yayi sannan yace nidai abinda nake so dake kiyi addu'a Allah yasa hakan shine mafi alheri"
Nifah alhaji sam ban amince ba, kama aje wanan zancen wlh bazai taba yiyuwa ba"
Daure fuska daddy yayi sannan yace....
Karki nemi yin jayayya dani, daga ke har Jamal akarkashina kuke, babu wadda ya isa nace ga abinda zaiyi yacemin ba haka ba, Jamal dana ne be isa yayi jayayya dani ba"
Mikewa momy tayi tare da ficewa tana fadin wannan ai zalinci ne"
Girgiza kai daddy yayi sannan ya mike ya nufi dakin Jamal"
Gaisar dashi Jamal yayi sannan ya tambaye shi jikin shi"
Shiru dakin yayi zuwa can daddy yace......
Jamal nazo ne muyi wata mgn, kasan cewa dan uwanka yana asibiti ko?
Eh Jamal ya fada ahankali"
Toh abinda nake so dakai, akoda yaushe mutum ya zama me karban kaddara yadda tazo mai, wani alfarma nakeson kamin"
Tashi jamal yayi ya zauna tare da jingina bayanshi da bango"
Daddy yaciga da cewa nasan kana son dan uwanka, dan haka inason ka tausaya masa ka duba halin da yake ciki, ka sakar masa asma'u bayan ta haihu shi ya aureta"
Wani irin firgita Jamal yayi tare da sauke ida nuwan shi akan daddy hannu Yasa ya mustsuke ido sannan yace daddy kaine ko mafarki nake"?
Ba mafarki bane Jamal zahiri ne, inason shamsu yaji daddi rayuwa bana so rayuwar shi ta kare ahaka, rayuwar shi abaibai take"
Jim, Jamal yayi sannan yace daddy ai wannan ba kaddarata bace tashi ce, shiya kamata ya karbeta bani ba"
Cikin ido daddy ya kalli Jamal sannan yace nasan haka Jamal amman ai lalurace ta kawo haka"
Shiru dakin yayi Jamal ji yake kaman anamai daka akirji, daddy ne yagaji da shirun yace.....
Jamal inasauraron ka"
Murya kasa kasa yace banzan iyaba daddy, dan Allah kayi hakuri"
Cikin fusata daddy yace nina rokeka alfarma kace min bazaka iyaba, to bari kaji wannan karon umarni zan baka, kafin nan da wayewar gari ka rubuta ma Asma'u sake"
Afusace ya Mike ya fita, wani irin zugi zuciyar jamal kemai tare da tukukin baccin rai wacce irin rayuwa ce wannan yaushe daddy ya sauya hali da zai zabi deeni akaina"
Inason asma'u banga dalilin dazan saketaba, zanyi koma menene dan nakare martaban aurena, shi wanene dabazaiyi hakuri da kandara ba
Irin tunanin da Jamal ya kwana yi kenan washegari dasafe daddy ya sake duruwa dakin"
Jamal naganin shi gabashi ya fadi, hannu ya mika mishi tare da fadin bani"
Sunkuyar dakai yayi batare dayace komai ba"
Cikin fada daddy yace karka maidani dan iska kanaji ko?
Wani irin mummunan tashin hankali Jamal yaji, tunda yake betaba jayayya da iyayenshi ba, kuma baya so ya fara, aman bazai iya aiwatar da abin da daddy yake soba"
Ahankali Jamal yace daddy dan Allah kayi hakuri wlh baxan iyaba, ba nason jayayya dakai, dan gaskiya inason asma'u bazan iya rabuwa da itaba......
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
1⃣0⃣2⃣
Jamal bana wasa dakai, karkace zakayi jayaya dani, kuma wannan mgnr bana son wani yajita tsakanina ne ni dakai"
Daddy dan Allah ka jayen wannan mgnr, wlh daddy bazan iyaba, bazan iya rabuwa da Husna ba, daddy idan nabarta zan shiga wani hali"
Jamal koma waning hali zaka shiga baxai kai wadda shamsu yake ciki ayanzun ba, bana son nakarajin komai daga gare ka, takarda na nema kuma ita nake son kabani"
Kara dukar dakai Jamal yayi, sun dauki lokaci ahaka sannan daddy yace......
Jamal wlh zan bata maka ranka"
Cikin zuciyar shi yace.....
Raina ya dade da bacci daddy"
Cigaba daddy yayi da cewa, zakai abin da nagaya maka ko kuwa?
Murya kasa kasa yace daddy kayi hakuri🙏🏻
Wlh Jamal zan iya tsine maka"
Kallon daddy yayi da sauri sannan ya maida kanshi kasa yace......
A'a daddy kar kamin haka, dole ce tasa na maka musu daddy ba'a son raina bane, daddy idan na saketa rayuwata zata zama cikin hadari, dan gaskiya inasonta sosai babu rabuwa atsari na, kuma itama tana sona"
Cikin daure fuska daddy yace bantabaye ka wannan ba, kaida shamsu nasan kuna da babbanci kai mutum ne me tawakali da kaddara mekyau ko mara kyau, shamsu bayi dashi, ba'a daura shi akan wannan tarbiyan ba, banaso ya mutu, inaso yayi rayuwa kamar kowa"
Kunya ce ta fita a idon Jamal kwata kwata, tsintan kanshi yayi yana fadin daddy wannan ba kaddarata bace, bazan iya kashe kaina na raya wani ba, Allah ne ya bani Husna, batare da naje neman aurenta ba, duk da cewa na dade ina sonta bantaba nunawa kowaba har usman, kuma ni na sani deeni bawani sonta yake ba, wlh nafishi sonta, yana ikirarin yana sonta ne saboda besan menene so ba"
Itama kanta taso deeni ne cikin yarinta alokacin da batasan me take ba, na tabbata ayanzun Husna bazata so deeni ba"
Daddy idan kace lallai saina saketa bakamin adalci ba, Allah ne ya bani ita batare da yayi shawara da kowa ba, haka kuma Allah ne ya kaddara asma'u ba matar sa bace, dame bazai yi hakuri da hukuncin Allah ba, lallai ne abin da yake so saiya samu?, daddy karku shiga hurumin daba nakuba, deeni ba mutuwa zaiyi ba, darasi ne Allah yake nuna mishi, daddy idan ma muwa zaiyi sakin husnan dakace nayi zai kara mai kwanaki ne? Dan Allah daddy munar Allah yayi hukuncin shi, munemin zabin alheri agurin shi kawai"
Jikin daddy sanyi yayi sosai, shiru yayi na dan wani lokaci zuwa can ya sake cewa.....
Jamal nasani duk abin da ka fada haka ne, shiyasa ako ina nake alfahari dakai, amman kayi yadda nace d'in"
Wani irin yar fa hannun Jamal yayi, sannan ya rungumi hannuwan shi akirji"
Ganin haka daddy yace nakara ma lokaci nanda zuwa gobe ka yanke shawaran, zakamin biyayya ko kuma bijirewa umarni na"
Juyawa daddy yayi da sauri yabar dakin"
Yana fita momy ta fito daga dakin ta bayan daddy tabi da harara sannan taja tsaki ta nufi dakin Jamal"
Tana tura kofar ta hango fuskan Jamal hawaye shabe shabe"
Yana ganinta ya fara sharewa tare da boye idon shi"
Kusa dashi ta zauna sannan ta dago kanshi tace......
Jamal karka tada hankalin ka, bare har ka biyewa zancen mahaifin ka, idan har ka saketa bazan taba yafe maka ba, karka manta, nima ina da hakki akan ka"
Cikin rawar murya yace toh momy ni yanzun yaya zanyi?
Ka dage mishi akan kana son matar ka, ni bantajin inda akayi haka ba, alhaji yana da wani irin son 'yan uwan shi, wadda ya wuce misali"
Jamal be sake cewa komai ba, idonshi ya dauke daga gurin momy ya juyar dashi can gefe, cikin tsananin damuwa"
Momy kokarin kwantar mai da hankali take, amman ta kula hankalinta baya gurin ta, yayi nisa cikin tunani"
Mikewa tayi tai waje tare da fadin Allah ya kyauta"
Jamal naganin fitan ta ya kira wayar ma'u, yauma kashe take kamar kullum, tsaki yaja gashi bashi da no mama"
Wata zuciyar ce tace, ka kira usman, wannan tunani yasashi ya kira layin usman
Zuwa can aka daga usman ne yace gauro ya gari?
Cikin rashin kwarin jiki Jamal yace babban yaya ka huce kenan?
Dariya usman yayi tare da fadin aini daman ba zafi nayi ba"
Kayi fushi mana tinda ka tafi babu sallama, ya gida ya iyali?
Lfy lau suke, karkace min asma'u bata gaya maka fa'iza ta haihu ba"
Yake Jamal yayi kamar yana gaban usman yace da gaske?, me muka samu?
Nana Firdausi, usman ya fada cike da murna"
Allah ubangiji ya albarkanceta acikin addinin musulinci, kace inanan nasake baki nayi 'ya ban sani ba"
Dariya usman yayi tare da fadin wlh jiya da dare ta sauka, na dauka Asma'u zata gayama ne"
Karka karamin haka, ko Husna zata fadamin yana da kyau kaima naji daga gareka, amman bakomai tunda Husna taganta kamar nine"
Hmmm wlh Jamal kana min rashin kunya fah, ya jikinka najika wani iri ne"
Eh wlh bana jin dadi ne, dan hadani da husna mana"
Tsaki usman yaja sannan yace batanan gidan kuma basu dade da tafiya ba ita da mama"
Shiru Jamal yayi zuwacan yace toh sai an jima"
Kashe wayar yayi tare da binta da kallo, lallai yanason suyi waya da husna ayau, dan haka ya yanke shawaran kiran daddy"
Bayan sun gaisa da abba yamai barka samun karuwar da akayi"
Dariya abba yayi tare da fadin toh ai Jamal ku za'aiwa barka, kunji kunya tika tika daku sai yanxun kuka aje daya, daker"
Guntuwar dariya Jamal yayi tare da shafu keyarshi kamar yana gaban abba, acikin zuciyar shi fadi yake abba me kakeci nabaka na zuba"
Jim, sukayi zuwa can Jamal yace.........
Amm abba nakira wayan ta ne akashe, ban saniba ko wayar ta samu matsala ne"
Wai asma'u ?
Eh Jamal ya fada ahankali"
Toh, toh, ina zuwa"
Kashe wayar yaji anyi zuwa can yaji wayar na kara"
No Abba yagani, jikin shi har rawa yakeyi wajen daukan wayan"
Muryan ma'u yaji cikin murna da dauki tana rangada sallama"
Tsintan kanshi yayi da lumshe ido sannan ya amsa mata tare da fadin Husna shine kika yadda kika tafi ko sallama babu ko?
Toh ai momy ce tace haka"
Hmmm Husna toh ya kwana 2?
Lfy lau, ya jiki?
Yayi sauki Husna, yasu mama?
Suna lfy"
Yayi kyau"
Cikin siririyar murya asma'u tace....
Yaya Jamal albishirin ka"
Goro ya fada cike da zumudi dan tunda yake da ma'u bata taba sakar mai jiki kamar yauba"
Yar dariya tayi sannan tace.....
Fari ko jah?
Dariricewa yayi domin bazai ce ga takameme abin da ake cewa ba, tsintan kanshi yayi yana cewa jah"
Kukan shagwaba tasa kamar tana gaban shi, tare da fadin fari fa zakace"
OK toh ya isa kisan ban iya irin wad'an nan abubuwan ba, inajiki toh nace fari"
Cikin murna tace....
Na samu d'iya anty fa'iza ta haihu jiya da dare"
Yi yayi kamar be sani ba, ya lankwasa murya yace......
Dan Allah?
Wlh, yaya bakaga yariyar ba, kamarmu daya"
Har cikin jinin jikin shi yake jin muryanta dan haka ya kara kashe murya yace....
Da gaske?
Hmmm kai dai sai ganta da idon ka, wlh har giran mu iri daya ne"
Zanso inganta kuwa, kishafa min kanta, kice wani babanta na mata barka da zuwa"
Shiru sukayi nadan wani lokaci, zuwa can Jamal yace.....
Husna kina inane yanzun ?
Ina dakina"
Ke dawa?
Ni daya"
OK akwai mgnr da zan gaya miki, akwai wata babban matsala da ta tunkaro mu, daddy ya gindaya min umarni, wadda bazan iya biba, kinsan menene?
Girgiza kai tayi tare da fadin a'a
Ahankali ya fara warware mata abin da ke faruwa"
Kafin ya gama hawaye ya gama wanke mata fuska, cikin kukan tace........
Yaya Jamal nagaji fah, wlh nagaji tunanina bazai iya dauka ba, waini sai yaushe zanji dad'i inama na mutu tun ina kar.......
Wani tsawa Jamal ya buga mata wadda yasata yin shiru batare da ta shirya ba"
Kina hauka ne? Karna sakejin kin fadin irin wannan mgnr, duk inda kika samu kanki ki godewa Allah
Kuka take ahankali"
Shima hawaye ya share tare da ajiyan zuciya yace.....
Husna dan Allah karki yadda arabamu, deeni ba sonki yake ba, sha'awarki kawai yake yi, natabajin shi yana miki karyan banza da wofi, har yana kiran Ki da Furan sa, idan natuna inajin takaici, agidan ubanwa kika zama furan sa? Darajan Ki ta wuce ta fura, babu abinda da za'a kwatantaki dashi, yaudaran ki yaki yake, kuma ni tundaga ranan natsani fura
ko ganinta bana so yi"
Kosawa tayi yabar mgnr, dan tasan yana iya birkice mata, yanzu nan, dan haka tace....
Yaya Jamal kabar wannan mgnr"
Dif, yayi xuwa can yace.....
Husna daddy ya bani daganan zuwa gobe, nakawo mishi sakin ki, dan haka adaren nan zabar garin bazan dawoba sai daddy ya janye kudurin shi akaina, zabar wayata agida dan kada anemeni ke kuma Ki ringa barin wayarki akunne dan zan nemeki, idan na isa inda zan tsaya, sannan aurena nakan ki karki yadda da sako arubuce, ban rubutaba, kuma bazan rubuta ba"
Ban aiko kowa ba, kuma bazan aiko ba, karki yadda da kowa, idan bani kika gani idona da nakiba"
Kuka ta fasa, cikin kukan tace......
Yaya Jamal karka tafi ka barni dan Allah"
Husna nima ba'a son raina zantafi ba"
Cikin matsanan cin kuka tace toh ka tafi dani wlh zan bika.....
Heart beat
*Mmn Yazeed*
h💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
*Masoya BUGUN ZUCIYA kuyi hakuri pls🙏🏻🙈 abubuwa ne sukamin yawa, naso yau nabaku mamaki amman nakasa, gobe insha Allahu page 2 ko 3 zan turo, nagama typing editing ne ya rage, wadan da sukamin mgn ban amsa ba kuyi hakuri pls🙏🏻 sakon ne yamin yawa*
1⃣0⃣3⃣
Indan katafi ka barni zan shiga wani hali bansan inda Zanyi ba"
Husna kiyi hakuri, nima bansan inda zani ba, kinga bekamata na dauki da karamin ciki inkaiki inda xaki wahala ba"
Cikin kuka tace nidai wlh xan bika, duk Inda ka zauna nima zan iya zama, wlh yaya karka tafi ka barni"
OK toh shikenan daina kuka, maza Ki share hawayen ki kuma ki saki ranki"
Make kafada tayi kamar tana gaban Sa, sannan tace a'a saika min alkawarin bazaka gudu ka barni ba"
Namiki husna, ki shirya yau dinnan inanan tafe, amman karki gayawa kowa"
Dahaka sukayi sallama, jikin ma'u sanyi ya kara haka ta takure guri daya taita kuka"
Jamal ko yana gama waya da ma'u ya tashi ya dingisa, mahimman abubuwan shi ya hada guri daya sannan ya sauya kaya"
Awaya ya kira drive bayan ya shigo yace ya dauki jakar yasa amota gashi nan zuwa"
Drive ya fita babu dadewa Jamal ya fito, babu kowa afalon dan haka har ya fita babu wadda ya ganshi"
Hanya suka dauka acikin su babu me cewa kala, yamma likis suka isa Kano"
Sauka Jamal yayi ya nufi cikin gidan cike da zumudin son ganin ma'u
Salama yayi abakin falon, daga ciki mama ta amsa"
Ma'u tunda taji muryan Jamal ta mike tare da ajiyan zuciya"
Cikin ladabi ya shiga falon yana dingisawa tare da sunkuyar da kanahi kasa"
Mama naganin Jamal tace ah'ah Jamal kai da kanka ka kwaso hanya kana fama da kafar ka"
Shafo keyarsa yayi tare da satan kallon ma'u yana murmushi"
Itako ma'u tsaye tai ta kasa cewa komai, kallon Jamal kawai take tare sonjinta jikin shi"
Bayan sun gaisa mama ta shiga kitchen sannan ta kira ma'u"
Bin bayanta yayi da kallo tare da hadiye miyau"
Zuwa can ta dawo dauke da kayan marmari ta aje gaban shi"
Tana kokarin ajewa ya rike hannunta tare da kokarin dagota"
Kan cinyar shi yaso zaunar da ita ta cije tare da fadin ciyon ka fah?
Gefe ya nuna mata tare da fadin daga nan zaki zauna"
Zama tayi sannan ya hada hancin shi da tana tare da fadin kince zaki bini ko?
Kai kawai ta daga almar eh"
Cikin sauri ya wawuro bakinta, nisa yayi sannan ya fara shafa jikinta"
Ummi ce ta sawo kai bakinta dauke da sallama, cikin sauri ta juya tun batakai ga karasawa ba"
Hakan yayi daidai lokacin da suke kokarin rabuwa da juna"
Ganin mama tajuya ya tabbatar musu ta gansu dan haka takaici yasa ma'u ta fara kuka"
Jamal ma kunya ta kamashi, amman fuskan sa na dauke da murmushi yake kallon ma'u, zuwa can yace......
Ke dai kuka be miki wuya, yanzun dan Allah meye abin kuka?
Cikin kukan tace mama fa ta ganmu"
Toh menene husna?, nifa mijin Ki ne bare kice za'amiki fada, dallah ni tashi ki dauko gyalen ki, sai kice ma mama zaki rakani naganu Firdausi"
Wlh yaya bazan iya ba, ni yanzun kunyan hada ido da mama zanji"
Mikewa jamal yayi tare da fadin toh shike nan, ni bari na wuce, dan bani da lokaci'
Rikeshi tayi da sauri, tare da fadin to yaya ai kai ya kamata ka gaya mata"
Shiru yayi yana kallon ta zuwa can yace....
Ok toh yanzun abin da za'yi, kije ki Debi kayan ki kadan kisa amota"
Yana tsaye harta dawo sannan ya matsa kofar mama yace.....
Mama zantafi"
Fuskarta dauki da fara'a tace yau yau din nan ai na dauka kwana zakayi"
Cikin jin kunya yace a'a yau zantafi nazo ganin Firdausi ne"
Murmushi kawai mama tayi dan haka jamal ya sake cewa......
Zamuje da Husna ne ta raka ne"
Adawo lfy Jamal kaida matar ka"
Dan sosa keya yayi sannan yajuya ya kalli ma'u yace dauko gyale"
Basu wani zauna agidan usman ba suka fito bayan Jamal ya gama tofawa yariyar addu'oi"
Tasha Jamal yasa drive yakai su sannan suka sauka tare da kayan su"
Gargadi yawa drive sosai cewa duk wadda ya taban baye shi yace kano ya kawo shi, daganan karya kara komai"
Saida drive ya wuce sannan suka hau motan sokwato"
Drop suka dauka dan haka karfe 10 da wasu mintoci suka shiga cikin garin sokwato, lokacin har Bacci ya kwashe ma'u tana manne ajikin Jamal"
Har suka isa kofar gidan da Jamal yama drive izinin shiga, ma'u bata tashi ba, kallonta Jamal yayi, bacci take kuma dagani tanajin dadin macci"
Kallonta yake vabu kyaukyautawa muryan drive yaje yace oga nagama sauke kayan"
Azabure jamal ya kalleshi sannan yace......
Toh kashi kuma madam tana bacci ni kuma inada matsalan kafa bazan iya daukanta ba"
Cikin sauri drive yace oga tashinta zakayi ai"
A'a bazan tasheta ba, hukuri zakayi har ta tashi ko wani abu ne saina kara maka, dan babu kyau mutum yana bacci atasheshi"
Shiru drive ban yayi acikin zuciyar yace......
Lallai wannan ba karamin so yakewa matar nan tashe ba, ni ina ruwana indai za'abani kudi, Allah yasa ma karka tashi sai gobe"
Jamal babu abinda yake banda kallon ma'u, tun da yake betaba tsayawa ya kallita hankalin shi kwance kamar yau ba"
Tayaya daddy zaice saina sakeki, bayan na farajin dadin aurena, tayaya hakan zai kasan ce, Addu'a yayi azuciyar shi Allah yasa abba ya fahimci gaskiya"
Ma'u ce ta bude idonta tare da fadin nifa nagaji har yanzun bamu kawo ba"
Munkawo husna cewa nayi bazan tasheki ba sai kin gama baccin"
Wani irin kallo tamai tare da mamakin jamal, kwallah taji ya cika mata ido, Ashe Jamal zaisota haka?, lallai ta yadda kiyayya na komawa soyya"
Waigawa tayi ta kalli gidan tare da zare ido, barikine irin na sojuji, ko ina sojujin ne ke zurga zurga, suna fitowa daga cikin motar wani ya taho ya sarawa Jamal sannan ya mika masa key"
Ma'u na manne jikin shi ya bude kofar suka shiga"
Falo ne madaidaici me dauke da daki daya tak da bayi aciki, daga can gefe kuma akwai madaidaicin kitchen"
Bayan ya zaunar da ma'u yace ina zuwa bari nayi sallah ke kuma kibari ki huta"
Kallon shi kawai tayi yana fitowa toilet din ta shege, dan haka tare suka yi sallah"
Bayan sun idar yace bari naje na samo mana abinci"
Be dadeba ya dawo bayan sunci sunsha, ma'u ta fara hamma "
Kallonta Jamal yayi tare da fadin tashi kije Ki kwanta"
Hawa gadon tayi sannan ta kalli shi yana zaune akasa ya mike kafafuwan shi tace......
Yaya gidan nan fah ya mana kadan, yazun kai a inazaka kwanta?
Ban gane a ina zan kwanta ba?
Jan bargo tayi ta rufe idobta sannan tace naga gado daya ne, kai kuma mace bata hawa gadon ka"
Take sanda ya fada mgr ya dawo mai, dan haka yayi dariya sannan yace.....
Ke bakya mantuwa ne?
Bata sake cewa kalla ba ta rufe idotan tai shiru"
Tanajin shi ya mike ya sauya kaya, sannan yahau gadon tare da yaye bargon ya shiga, zuwa can ya mika hannun sa ya rungumota jikin shi"
*Abuja*
Bayan tafiyan jamal, zuwan momy dakin uku bata ganshi ba, lekawa waje tayi nanna megadin yake shaida mata Jamal ya fita tare da drive"
Momy bata tsorata ba, saida taga drive ya dawo babu Jamal"
Tambayan shi tayi ina jamal, kamar yadda Jamal ya fada mai haka ya fada"
Acikin zuciyarta tace wai meyasa Jamal bejin mgn, wannan kafar tashi so yake ta rube, idan ba hakaba me zai kaishi kano"
Da daddare daddy suka dawo tare da deeni da alhaji bashir harda ummi"
Rike daddy yake da deeni yana mai sannu"
Bayan sun zauna momy ta kawo musu abinci"
Daker deeni yaci kadan kallon shi momy tayi taga ya rame"
Shima daddy kallon Sa yayi sannan ya mike cikin sauri ya nufi dakin da Jamal yake"
Alhaji Momy ta kirashi, sannan tace......
Jamal baya nan"
Bayanan?, ina yaje?
Kwashe yadda sukayi da drive tayi ta gayamai"
Shiru daddy yayi na wani lokaci, sannan yace"
Ni Jamal zai watsawa kasa a ido?, shi kenan nasan abin da yake nufi, wayar sa ya dauka ya kira abba"
Bayan sungaisa yace Jamal yazo"
Daga can Abba yace........
Eh haka na samu lbr ance yazo amman ni bangansa ba"
Asma'u fah ?, tananan agida, koya dauketa ne?
Eh mamanta tace sun fita tare, kasan yaran zamani, ita maman tasu dai yace mata gidan usman zasu"
Wani zancen daddy ya dauko sannan sukayi sallama"
Koda ya kashe Wayar alhaji bashir ya kallah cikin tsananin bacin rai yace......
Wlh zan nunawa Jamal nina haifeshi be isa yaja dani ba"
Meyayi ne haka da zafi?, cewar alhaji bashir"
Umarni nabashi shine bazaibiba, yaje ya dauki asma'u ya tafi da ita"
Cikin rashin fahimta alhaji bashir yace.....
Ban game umarni ba?, kuma inda yake kwance beda lfy kamata yayi atausaya masa"
Cikin ido daddy ya kalli alhaji bashir sannan yace.....
Yanzun kaman Jamal bazaiji tausayin d'an uwansa ba, ni dashi nagaya mai halin da shamsu yake ciki, yau zan gaya muku abin da nake ganin shamsu be gaya mukuba, Asma'u yariyar da deeni ke tsananin so itace asma'u matar da Jamal ke aure"
Alhaji bashir da ummi mikewa sukayi ummi harda gutun hawayenta"
Daddy yaci gaba da cewa ganin inda shamsu ke tsananin sonta yasa nace ma Jamal ya saketa bayan ta haihu shamsu ya aura, bantaba ba Jamal Umar yaki biba sai akan mace?
Komawa alhaji bashir yayi ya zauna sannan yace sai kamai uzuri, kaida kanka ka fada wannan ne na farko, kuma aikai ka nemi yama tawaye, tayaya mutum na zaune lfy da matarsa acemai ya saka wani ya aura"
Shiko deeni wani irin kallo yakewa daddy mekama dana Allah ya kiyaye"
Fada daddy yaita yi tare da yin fushi me tsanani da Jamal"
Itama momy hankalinta tashi yayi, ina Jamal zaikai ma'u tana cikin yanayi irin na laulayi, shikuma yana faman dingisa kafa, yaya za'ayi wannan zaman gashi ta kula jamal yacika fitana, baya duba yanayin jikin shi"
Kuka take sosai deeni na kallonta juyawa yayi ya kalli daddy yaga shi sai fada yake, har zuciyan shi so yake d'an shi yasaki mata shi ya aura"
Tunawa yayi da lokacin da alhaji vashir yace idan ansami mutumin daya aura asma'u zai kashe konawa ne dan ya saketa"
Wannan nanufin baba bashir besan kowaba sai ni kenan, daman haka sukemin tun ina Karami abin da nake so shi suke min"
Sun kuyar dakai yayi sannan yace....
Toh shi daddy be kyaunar jamal ne? Nasha jin daddy nawa Jamal fada kota waya ne, niko basu min fada har gara ummi takanyi wani lokaci"
Ahankali deeni yaketa babbacewa tsakanin shi da jamal akwai babbaci, dakanshi ya hango ashe ma idan ka samu wadda zai tsaya ya maka fada kai dan gata ne"
Lallai idan mutum ya rasa me masa fada ya shiga uku, tabbas Jamal bashi da makusa yana yin abubuwan shi kamar daddyn sa"
Duk cikin zuciyar shi yake wannan tunani tare da daukan alwashi insha Allahu zaiyi aure ko bana soyayya ba, dan yaga ya mallaki yara ya basu tarbiya ba irin wacce aka bashiba"
Kallon daddy yayi yace daddy dan Allah kabar fadan nan, ni tun tuni na hakura da asma'u nacireta azuciyata, ba tun yauba, daddy ya zan yi na aure asma'u, bayan d'an uwana na auren ta, daddy kayi kuskuren cewa Jamal yabar min mata, wlh na barta har abada, dan Allah abani no Jamal nakirashi ya dawo gida, zama awani waje be dace dasuba"
Kowa afalon kuka yake yi ba mazan ba ba matan ba"
Daddy ne ya share hawaye sannan yace......
Ai be tafi da waya ba, dan dana kira naji karanta adaki"
Shiru deeni yayi zuwa can yace........ .
Daddy ina son nayi aure, nabaka zabi ka zabar min mata ko ya take indai ka amince da tarbiyan ta, inaso na haifi yara na musu tar biya ba irin wacce akamin ba
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
1⃣0⃣4⃣
Takaici ne ya kama alhaji bashir, tare dajin bakin cikin abin da ya aikata abaya, ga dukkan alma deeni baya al'fahari da zaman su iyaye agare shi"
Itama ummi kuka take tasani tuna baya garesu abin kunya ne, suna da mummunan fenti"
Daddy ne ya share hawaye sannan yace"
Allah ya maka albarka shamsu, naji dadi daka fahimci haka, kuma nima nasan banma Jamal adallaci ba, gani nake kamar bazaka rayuba, rayuwarka taban tausayi, inason nan gaba rayuwar ka tai kyau, atunanina sai ka same asma'u ne zaka tsaya ka gane me rayuwa take ciki, duniya ba wani abubane shamsu inda kasan wasan kwaikwayo haka take, idan ka biyewa son zuciya saikakai kanka ka baro"
Nisawa yayi sannan yaci gaba da cewa.....
Shiyasa Jamal yaban mama ki daya zabi barin gida, hakan dayayi ya nunamin yana son matar shi, matsowa daddy yayi sannan ya dafa kan deeni yace....
Shamsu insha Allah matar da zan zabo maka saikayi mamaki, fatana ka kwantar da hankalin ka, kuma kaci gaba da daukan karatun ka agun malam"
Ana cikin haka momy ta mike ta shige daki bakomai ke damunta ba illah barin Jamal daga gida, ba laifin kowa bane illah na alhaji, idan kafar Jamal ta samu matsala dashi xatayi kuka, inama shika dai ya tafi, da hankalinta bazai tashi sosai ba"
Akacin wannan tunanin ummi ta sameta, dago ido momy tayi ta kalleta ta sake maida kanta"
Saida ummi ta share hawaye sannan tace zamu tafi"
Toh kugaida gida Momy ta fada fukarta daure"
***
Bayan fitan suma momy zama tai taishiru kamar wadda akawa mutuwa"
da dare daddy
ya samu momy adakinta, acikin dibara ya fara sako mata zancen shawaran daya yanke, akan cewa mezai hana ahada shamsu da nafisa"
Cikin sauri momy ta mike tare da fadin Sam alhaji, dan me zakace nafisa ta auri shamsu?, kodan kaga bakai ka haifeta ba?
Wani irin kallo daddy ya mata sannan yace....
Yanzun ne dai zaki nunamin bani na haifeta ba, dan inda ace nina haifi nafisa bazan yi shawara dake ba, tun agurin zance nabashi nafisa, ni yanzun roko nazo dan Allah kicire tunanin komai insha allahu alheri ne"
Nifa alhaji bakin shamsu nake ba, dabi,un shi neke tsoro"
Ai yanzun ya shiryu ke dajin kalaman shi na dazon kisan kura tayi lfy"
Eh tabbas ya gyara abubuwa da dama amman alhaji shamsu fah ko mgnr arziki yake sai karkace baki abin ya riga ya zamar masa jiki, sannan har yanzun inajin kyankyanin rayuwar da iyayen shi sukayi, ina musu kallon tsofaffin banza"
Kul daddy ya fada sannan yaci gaba da cewa.....
Karki zama me roko, komai me wucewa ne"
Hmmm Alhaji idan na yadda aka hada wannan aure na cuci nafisa, kuma ma ai dangin babanta bazasu yaddda ba"
Murmushi daddy yayi kadan sannan yace......
Ai bayan fitana dazon naje wajen wan babanta, mun gama mgn dashi yakuma ce sun bani wuka da nama, na yi komai idan nasa rana na sanar masu"
Shiru momy tayi zuwa can tace kuma ka gaya musu waye shamsu??
Cikin fada daddy yace.....
Nace mishi dan kanina ne, kuma ban amince kije ki gaya musu wata mgn ba, na lura so kike ki tuzarta ni, kamata yayi kiyi addu'a Allah yasa alheri muke shirin kullawa"
Mikewa momy tayi
tana share hawaye tare da fadin shikenan alhaji idan kaga dama ma kayi gunduwa gunduwa da nafisa, amman kafin kayi abinda kaga dama ka nemomin dana ya dawo gida dan baza ahada min zafi 2 ba"
Dariya daddy yayi tare da fadin wannan kicire shi azuciyar Ki, ai shiba mahaukaci bane"
Cikin kuka momy tace nifa idan Jamal be dawo gidaba hankalina bazai kwanta ba"
Tsaki kawai addy yaja sannan ya fice abinshi
Bayan kwana biyu daddy ya shiga har dakin nafisa, kwace take tana latsa wayarta ganin daddy yasata saurin mikewa"
Murmushi daddy yayi sannan yaje bakin gadon ya zauna, sannan ya kira sunanta
Ahankali ta amsa daddy yaci gaba da cewa, nasan zaki mamakin ganina adskin ki ba komai bane ya kawani illah wani alhri da muke shirin kullawa, mum yake shawaran hadaku aure keda shamsu"
Nasani ke yariya ce me biyayya, kuma nasan zaki amince da bukatata, karki yadda momyn ki ta zugaki insha Allahu zamuce gara da akayi"
Kan nafisa akasa wasa take da hannun ta, hakan nan ta tsinci kanta cikin farin ciki saidai fauskan Jamal tana firgitata lamarin shi yana bata tsoro, Allah yasani tun ranan dataga deeni ya kwanta mata arai tsoron fasifar shi yasa tayi nesa dashi"
Mikewa daddy yayi tare da fadin umarni na baki bana neman zabinki, ina fata bazaki ki jin umarnina ba"
Kai da daga ahankali, sosai daddy yaji daddy har yabar dakin yana samata albarka"
Shirye shiryen baki daddy ya hauyi gadan2 komai da ake zubawa yar gata daddy yasa anzuba agidan da yabawa deeni"
Shiko deeni bawani shiri yake ba, domin kokari yake yaga rayuwar sa ta gyaro, bema san wacece amaryar ba, kuma be damu ya sani ba, burinshi kawai yaga ya aje iyali"
Abangaren momy kuwa, kullun fuskarta daure take tam, taki gayawa kowa zancen auren nafisa, dan haka daddy da kanshi ya sanarwa dangita"
Koda yayyata sukazo lallashinta suka yi, akan tayi hakuri insha Allahu auren zai bata mamaki"
Haka shirye shiye ya dada kankama nafisa sai rawar kai take, tare da kawayenta, sosai takebawa momy haushi, saidai batace mata kala, har biki ya rage sati, kuma aranan ne Jamal yacika sati uku da barin gida"
****
Jamal da ma'u nagani agaban doctor, sai ya mutsa fuska take Jamal na tarota"
Bayan Dr ya gama rubuce rubucen sa ya dago ya kalli jamal yace"
Ranka ya dade inaganin abin da yafi kawai, ku raba makwanci har cikin yayi kwari, domin idan har zaku dinga haduwa za'a samu matsala gaskiya"
Shiru Jamal yayi zuwa can ya daure fuska tare da fadin.....
Bakomai insha allahu zan kiyaye, sai mgnr kafata?
A kafar ka Alhamdulillah ta cike saidai ansamu matsala inaganin daga Dr dake wanke maka ciwon ne tun da farko, dan gashi bata warke yadda ya kamata ba, amman bawata matsala"
Godiya Jamal yawa dr sannan ya daga ma'u suka fito"
Biyosu Dr yayi tare da fadin Oga akiyaye fah"
Bayan sun koma gida tarairayan ma'u Jamal keyi sosai baya yadda ta dauki ko kofi abinci ma abaki yake bata, cak yake daukanta ya kaita toilet yai mata wanka, cikin dare ko haka yake rungumeta tsam ajikin shi, kamar dai wani zai kwace masa ita"
Har mamakin Jamal ma'u take wai ayanzun ita Jamal yakewa bauta, duk girman kannan ya ajeshi agefe"
Bayan sati 1
Yau jamal ya tashi da tunanin gida sosai axuciyar shi dan haka yadau waya yasa no momy"
Bugu biyu ta dauka, hayaniyan mutane yaji tare da dallaman Momy"
Ahankali ya amsa"
Arikece momy tace......
Jamal?
Na'am momy kuna lfy?
Kaniyarka Jamal, kai kana da hankali kuwa?, kana inane yanzun?
Momy nakirane naji lfyr ku kuma kusan muna lfy"
Jamal ina Asma'u?
Tana toilet"
Kafarka fah?
Karamar dariya Jamal yayi tare da fadin ta warke mom......
Karya kake Jamal be isa ta warke ba"
Wlh Momy ta warke bari zan turo miki pic dinta kikani"
A'a karka turomin kadawo gida kawai Jamal, hankalina bazai taba kwanciya ba, sainaga ka dawo idan ma kai bazaka dawoba toh katuro Asma'u gida"
Kawar da zancen Jamal yayi tare da fadin momy wai baki gida ne naji hayaniyan mutane ne"
Ina gida Jamal, bikin Nafisa ake yanzun aka daura mata Aure"
Aure kuma Momy?
Fashewa momy tayi da kuka tare da fadin eh Jamal daddy ka ya matsa saiya aurar da ita"
Da sauri Jamal yace dawa?
Da shamsudeeni"
Deeni ?, momy ta yaya zaki bari adaura wa Nafisa aure da deeni?
Jamal kasan halin daddyn ka da kafiya da naso hanawa ma cewa yayi dan naga bashine ya haifeta ba, dan haka nabarshi yayi abin da yaga dama da ita"
Hakuri Jamal ya karabawa momy sannan ya mata alkawarin sunanan dawowa"
Bayan ya aje wayar ya tashi ya shiga dakin baccin su, ma'u na kwance akan gado, hawa yayi ya kwanta, sannan ya jawota jikinshi ya rungume tare da sun batanta ta, acikin kunnenta ya rada mata yau kawarki na Aure"
Zainab ? Ma'u ta tambaya"
A'a Nafisa"
Tashi tayi ta zauna tare da fadin nafisa?, naga yau satin mu 4 anan kuma banji ana mgr aurenta ba"
Eh daga baya ne"
Tabe baki tayi tare da fadin aiko banji dadiba naso ina gida za'ayi, to wa ta aura?
Kauda kai yayi sannan yace deeni"
Deeni? Yaya da gaske???
Zan miki karya ne?, yanzu nakira momy awaya take fadamin"
Guri daya ma'u ta kurawa ido, tare da kokarin danne abinda ke shirin bijuro mata"
Kallonta kawai jamal yayi sannan ya mike ya fita adakin"
Hawaye taji yana zubo mata ahankali ta fara tuno irin rayuwar da sukayi da deeni abaya"
Acikkn xuciyanta take cewa...
Haka Allah ya nufa deeni ba mijina bane bazamu zauna tare ba, duk irin soyayya da mukayi tazama abanxa abubiwan da sukaitayi ne yaita fado mata, zama tayi kamar mahaukaciya wani tai murmushi wani tai hawaye, acan karkashin zuciyanta ko bataso nafisa ta aure deeni ba taso yasamu watacan ya aura"
Tun daga ranan yanayin ma'u ya dan canza haka ma Jamal dayake lora da ita"
***
Deeni ko Sai a Wajen daurin auren yasan nafisa ce amaryan, fuskan shi babu yabo babu fallasa, abokan shi na kano duk sunzo cikin manyan kaya kamar basuba, bayan andaura aure duka suka wace caka ne kawai ya tsaya"
Lokacin da caka zai raka deeni gidan shi saida suka fara biyawa gidan alhaji bashir sosai sukamai fada harsaida abin ya bashi mamaki, bayan sun mike ummi ta kalli caka tace wlh bakuga inda kukayi kyauba, kamar baku ba, wai ya sunanka ne?
Cikin murmushi caka yace ummi sunana *Faisal*
Hannu ummi ta tafa tare da fadin sunanka me dadi ake cemaka wani wai caka, dan ALLAH auta daga yau ka rinka kiranshi da sunan shi"
Addi'oi tayimai sosai sannan suka wuce gidan deeni"
Gidane nagani nafada daddy ya mallakawa deeni tare da mota me zafi, har cikin falon suka shiga har sun nufi cikin dakin deeni ya tuna da karatun malam acikin zuciyan shi yace bazan shiga dawani har cikin dakin mamata ba"
Waigawa yayi ya kalli caka yace faisal zauna anan ina zuwa"
Bakin gado ya samu Nafisa yafe da gyalenta me tsananin shiki, hannu yasa ya yaye gyalen, cikin sauri ta sukuyar da kanta kasa, yana daga tsaye yasa hannu ya dago habarta suna hada ido ta maza ta rufe ido"
Murmushi yayi kadan sannan ya ninke gyalen ya aje agefe sannan yace kisa hijjabi ki sameni falo akwai abokina dazaku gaisa"
Kamar yadda yace haka tayi bayan sungaisa ta koma daki"
Aranan deeni be runtsaba adaren ya dama furanshi kuma yashanye ta tas"
Nafisa ta jigata sosai tayi kuka tayi magiya dan haka dasafe idonta yayi jawur bata san haka haka aure yake ba da bazata taba yadda ba"
Shima deeni tausayinta ya kamashi tsam yasata akirjinshi dare da lalabo duk Wata kallama ta lallashi yana gaya mata"
Ahankali yafarajin sonta na shigarshi, farin cikin yaji ya kamashi sosai tare da godewa Allah daya amsa addu'anshi daman ya shanye furan ne ayau Dan ya yakice burbushin son ma'u azuciyan shi"
Haka suka kwashe tsayon sati uku suna cin soyayyar su, zuwa wannan lokacin sun saki jiki da juna kuma ahankali suna kara shakuwa"
Zuwan su gidan momy 3 amman da daddare suke zuwa itama momy ta fara sakkowa domin ayanxun duk lokacin dazakaga deeni cikin farar jallabiya yake tare da carbi ahannun shi"
Har kasa yake tsugunawa ya gaisheta betaba yadda su hada ido, Nafisa ko cikin manyan hijabai take"
Tayi wani irin kiba naban mamaki"
****
Jamal ko jinyan ma'u yake, tare da kokarin cire mata kowanne irin tunani sosai takejin dadin zama da jamal, dan yi yake tamkar ya maidata ciki"
Dakanshi yake girka mata abincin da zataci, baya barinta tayi ko cangal, anacikin haka ne ya koma aiki dan haka dole yasa ya nemo me aiki"
Bayan sati 2 ma'u tana kwace afalo cikin duguwar riga, sosai cikinta ya turo kaikace cakin wata 7 ne, kyau cikin ya mata tare da Kara fari da sheki"
Daya daga cikin. yaran Jamal taga ya shigo da wusu manyan ledoji guda biyu, cikin sauri ta miki tare da mamakin meyakawo Jamal da rana"
Muryan yaya usman taji yana sallama tare da anty fa'iza"
Batasan sanda ta mike taje gaban fa'iza tana fara'a ba, amsan yariyar tayi sannan ta jawo hannun fa'iza suka zauna yaya usman ta fara gaidawa amman ke madagas yaki amsawa, ganin haka jikinta yayi sanyi gaisawa suka da anty Sannan sukaciga da hira sama sama"
Hannun anty fa'iza ma'u ta dada dagowa tare da fadin zo muje daki"
Bazataba, usman ya fada fukan shi cike da haushinta, cigaba yayi da cewa mara kunya kawai ke me miji ko ?
Kara sukuyar da kanta tayi tare da matso hawaye"
Basu dadde da zama ba taji tsayowar motar jamal tasan gayamai akayi yayi baki"
Yana shigowa ma'u ya fara kallo sannan ya koma gurin da usman ke zaune karasawa Jamal yayi tare da fadin babban yaya daman nasan kaikadai ne matsala ta tunda ka bincikoni akurgumin daji babu a inda bazaka binciko ni ba"
Wani irin kallo usman yamai sannan hace....
Yazun saboda Allah abinda kayi kan kyauta kenan?, kabar momy cikin tashin hankali"
Katseshi yayi tare da fadin haba usman ko kaine bazaka zauna ba hukuncin daddy yayi tsauri da yawa gaskiya inason matata yaya za'ayi ba acemin wani nasaketa "
Juyawa Jamal yayi yaga idon ma'u alamar tai kuka, cikin sauri ya tashi tsam, ya nufi gurinta, ganin tahowanshi yasata mikewa ciki sauri dan tasan riketa zaiyi gaban yaya"
Bayanta yabi tare da fadin.....
tsaya mana, ina daki ta shige Jamal nabin bayanta hannu sa yasa ya tarota sannan yasata ajikin shi tare da fadin usman ne ya bata miki raiko?
Guntun hawaye ta share sannan tace yaya yaushe zamu koma gida?, kaga yaya usman na fushi dani nagaida shi yaki amsawa, ina tsoron kar ace abba ma yayi fushi dani"
A'a Husna Abba bazaiyi fushi dake ba, ni mijin ki ne kuma sun san muna tare, dole ce tasa nai haka bayin kaina bane, dan haka ki daina damun kanki da tunani banza, nasan halin usman ciki dabai, zuwa dare zan kira miki abba Ku gaisa, wata kila hankalin ki zaifi kwanciya"
Sakin ranta tayi kadan, nan Jamal ya barota ya dawo falo yana zama anty fa'iza ta miki dakin ta shiga sosai ma'u taji dadi, nan hira ta barke tsakanin su, lbr yadda abba ya shiga damuwa da daddy ya gaya mushi Jamal yabar gida tabata
Cikin ido ma'u ta kalleta tace kila shima yanzun haushina yakeji?
Bawani haushi, ko jiya da mukaje ya fada mishi ya samu inda kuke cewa yayi agaida ku, kuma usman ya roki Jamal idan cikin ki ya tsufa ya dawo dake gida"
Ajiyan zuciya tayi sannan sukahau hira"
Jamal ma da usman hira sukayi sosai acikin hiran ne usman ya isar da sakon abba"
Difff Jamal yayi xuwa can yace kasan abin da yasa na kasa dawowa wlh banson ganin deeni kullum tsanarshi kaaruwa take axuciyata"
Ai kaji irin ta mutumin da yayi auren shi ina ruwanka dashi, kaifah daman kacika kishin jaraba, shiyanxun ma bata Asma'u yake ba bakaga gadda. Nafisa tai kyauba naji kanmar ma ance ciki gareta, shikanshi deeni idan ba Sanin shi sosai kayiba baka iya shaida shi"
Ker Jamal ya yadda idan cikinta ya tsufa zasu taho, anayin la'asar suka kamo hanya"
Jamal yaciga ba da lallashin ma'u harta saki ranta so daya ya taba kira mata Abba, bayan sungama waya ya kira mata momy, tundaga ranan ya kashe waryarsa"
Bayan 4
Cikin ma'u ya tsufa tafiya daker tashi daker, idan ka ganta saika tausaya mata"
Kuma lokacin ne hankalinta ya tashi sosai, cikin dare bata iya bacci tashi take ta tasa jamal agaba da kuka"
Cikin tsananin damuwa yake tashi ya zauna, tare da fadi husna kiyi hakuri mana kidaina dagawa kanki hankali"
Nina gaji yaya, ciki kusan shekara daya ajikina ni gaskiya daga wannan bazan kara ba"
Kauda fuska Jamal yayi yai dariya sannan ya juyo ya kalleta tare da fadin gobe zamu wuce gida, dan naga nema kike hawan jini ya kamaki, haba ace mutum be gajiya da kuka"
Murna ce ta kama ma'u sauka tayi wai xata hada kaya, jamal ne yahanata shida kanshi ya hada musu kaya"
Dasafe ya kira no Momy, tana dauka tace Jamal wai yaushe raini ya shiga tsakanin mu haka?, bazaka dawo da yar mutane ta haihu agida ba?, cikin watan haihuwanta fa take"
Cikin mamaki Jamal yace momy waya gaya miki?
Uwarka ce, akace maka bansani bane?, ai ina lissafi, ko ta haihu ne ma?
Sosa keya yayi tare da fadin a'a munan isowa yau"
Yauwa Jamal Allah ya maku albarka dan Allah kutaho da wuri"
Toh momy amman kafin mu tahu inason zan shiga kasuwa"
Me zaka saya indai kayan haihuwa ne nariga dana hada komai"
Heart Beat
*Mmn Yazeed*
💗💝💝💗
*BUGUN ZUCIYA*
( Heartbeat)
💓💝💗
💗
💓💝💗
By
💗
*Fadeela Lamido*
*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*
*Sadaukarwa ga duk me karata BUGUN ZUCIYA, nagode da irin soyayyar da kuka nuna min tare da wannan lbr BUGUN HEAT, Allah yabar kyauna💋*
*Sakon gaisuwa da fatan alheri ga marubutan mu, wad'an da suka karamin karfin guiwa wajen rubuta wannan lbr, bani da bakin mgn, hakika kun nunamin kyauna, sai dai nace Allah yabar xumunci🙏🏻*
1⃣0⃣5⃣
✋🏻✋🏻✍🏻 Karfe 3:15pm suka shiga gidan momy murna momy take sosai tana rike da hannun ma'u tare da tsareta da ido, nandan lbrin dawowan su ya zaga ko ina, tsilum saika Nafisa aguje ta shigo da cikinta daya fara tasowa manne ajikinta"
Jikin ma'u taso fadawa, momy ta tareta tare da fadin nafisa lfyr ki lau kuwa? Kewai bakijin nauyin jikin ki ?
Komawa tayi kusa da ma'u ta xauna, sannan ta shiga gaida Jamal wani irin amsawa ya mata batare daya kalleta ba,
'Daga ma'u nafisa tayi sannan ta suka nufi daki, kallon nafisa ma'u take tana mamaki wai yanzun cikin deeni ne jikin nafisa?, Ikon Allah kenan"
Hira suka barke dashi daga falo su momy sunajin dariyar su"
Sai dare deeni yazo daukan nafisa be shigo ba, waya ya mata tafito sutafi sannan tace yana gaida momy"
Daddare momy so tayi ma'u ta kwana gurinta amman taga Jamal sai zarya yake yafita yadawo dan haka tace tashi su tafi"
Dukda kwaciya kawai zasuyi tare yafison haka akan ace sunyi nesa da juna,
Washegari da safe sukaje gaida daddy abinda ya bawa Jamal mamaki daddy be nunafushi ba, sosai farin ciki ya bayyana afuskar shi, koda zasu tashi yaga ma'u na kici kicin tashi, cikin fada daddy yace haba Jamal taimaka mata mana, kunya ce ta kamashi daker ya iya mika hannu ya dagata Albarka daddy yaita samusu tare da addu'ar Allah ya sauketa lfy"
Adaren ranan ciwon nakuda ya tayarwa ma'u tunda momy taga inda take cije baki ta kira jamal, daki ta shiga ta dauko kayan haihuwa tace asibiti zamu"
Karfe 10:39pm ma'u ta haifo zarkada zarkadan 'ya'yanta guda biyu dukkan su maza ne masu kama da Jamal"
Bakaramin maki Jamal yayi ba, tunda suke zuwa asbiti babu wadda yataba cewa yan biyune acikin husnan shi"
Momy ko farin ciki ya hata mgn, adaren suka dawo gida domin ma'u lafiya lau take"
Tun asuba momy ta fara gayawa yan uwa da abokan arziki dan haka tunda safe gidan ya fara cika da baki"
Nafisa ma murna ba'a magana tare da deeni sukazo fuskanshi dauke da murmushi nafisace ta kwaso yaran ta mika mishi kallon yaran yayi gwanin ban sha'awa nan danan idonshi yacika da kwallah yasa hannu ya share tare da fadin nafisa yaran nan sun bani sha'wa inason yara sosai sunbatan yaran yayi tare da fadin Allah yayi muku albarka ya karawa mahaifiyar ku lafy shekara me zuwa ta sake haifo mana kalan ku, yakuma bawa mahaifin ku abinda zai ciyar daku"
Amsawa nafisa tayi da ameen, sannan tace ka manta addu'a daya da bakiyi ba"
Dagowa yayi
ya kalleta, idontshi da ragowan hawaye ga kuma murmushi akan bakin shi yace....
Wacce kenan?
Cikin murmushi tace......
Bakace muma Allah ya bamu irinsu ba"
Murmushi yayi tare da cewa a'a nafisa muruke me albarka kawai, ko mace kona miji ke duk abinda Allah yabani zan karba nayi godiya lokuta da dama abinda mukeso ba alheri bane agare mu"
Dahaka ya mikawa nafisa yaran sanan yace ta gaida asma'u"
Aranan momyn usman ta iso tare da dada"
Tunkafin ta shiga gidan take fadin you alkawari ya cika gani agidan takwara"
Koda suka shiga dakin ma'u daure fuska tayi, tare da kyauda kai, itama dada daure fuska tayi tare da fadin nima ba gurinki nazo ba"
Aranar da daddare hajiya asabe tazo ganin jarirai, farin ciki sosai ta nuna"
Acikin zuciyan Momy tace inma bakin ciki kike ke kika sani, ni baki gabana mantawa ma nake inada kishiya idan yana gidan ki gani nake kamar tafiya yayi"
Awaya deeni ya kira Jamal yamai barka, ana gobe suna ya dauki nafisa suka shiga kasuwa kayan yara yaita kwasa kala kala tare da kayan wasa kai harda keke komai iri daya ne kuma bibbiyu, mota sukaita lodawa, Wata sarka nafisa tagani tace ka saiwa asma'u"
Wani kallo ya watsamata tare da fadin awani dalilin zan saimata ?, kinason mijinta yakaini kutu ko?
Turo baki tayi sannan tace wato ka maida yaya mafadaci ko?
A'a nafisa aiko nine sai inda karfina ya kare"
Washegari akwai suna, anci ansha jama'a ba masaka tsinke da sunan su aka barsu *Hassan da Hussain* aciki waddan da sukazo suna harda zainab kawar ma'u"
Lokacin da yan waliman Jamal suka cika gidan da hayani ma'u ta jawo zainab bakin window da hannu ta mata nuni da deeni"
Tabassa deeni yayi kyau babu wadda zaice yayi rin
rayuwar da yayi abaya, Saika ma zaci yafi su Jamal roko da addini domin su dikine na zamani sanye ajikin su, yayin da deeni yake cikin jallabiya fara karrr hannun sa rike da carbi, gefenshi Faisal ne zaune"
Washegshegari duk yan suna suka watse, sai dada kadai ta rage"
Kulum abba ke kiran dada awaya tare da tambayan jikokin shi, wata rana abba ya kira dada suna cikin mgn ma'u ta kwace wayar tasa akunne tare da fadin abba kulum ni baka tambayata"
Dariya yayi sannan yace......
Asma'u ai muna waya da mijin Ki, nasan lfy lau kike, ya mutanen gidan naku?
Lfy lau"
Toh madallah, Allah ya miki albarka, yadda kika min biyya kema Allah yaba ki masu miki, akullum ina miki addu,a zama lfy tare kwanciyar hankali"
Ameen abba, idon ma'u cika yayi da kwallah, sallama sukayi da abba, hawaye kawai ma'u taji suna Zubo mata daman haka iyaye sukeji idan dan su yai masu biyyaya, lallai naso nayi kuskuren nabi son zuciyata, kome nayiwa iyya na bazan biyasu ba, addu'a ta shiga ma iyayenta Allah ya saka musu da alheri"
Haka dada taciga da kula da yaran ma'u Hassan da Hussain har sukayi arba'in aranan Jamal yakaisu Kano, bayan sati 2 ya koma ya dauko su"
Bayan wata 5
Nafisa ta haifi katon danta, murna gurin deeni ba'a mgn, ya dade rungume da yaron, yana kwalla tare da tufa mishi addu'oi"
Ma'u ma bakinta ya kasa rufuwa, shiryawa sukayi ita da momy zasu tafi, momy na rike da hassan, hussaini a hannun ma'u har sun fito harabar gidan, motan Jamal ya shigo"
Tunkafin ya fito ya daure fuska"
Ma'u ko fara'a take tare da zumudin fadamai nafisa ta haihu"
Cikin basarwa yace naji ai, ina zaki?
Sanyi jikin ma'u yayi, tare da rasa abincewa"
Momy ce ta kalleshi tace.....
Zamuje gano jariri ne"
Da sauri yace amman bada Husna ba"
Daure fuska Momy tayi tare da fadin da Husna kuwa, Jamal wai me kake nufi ne?, kiri kiri ka hana Asma'u zuwa gidan Nafisa, bata taba zuwaba, watanta 6 da haihuwa amman ka hanasu suyi zumunci, wanne irin bakin kishine wannan?
Shiru Jamal yayi tare dasa idon shi akasa"
Cigaba momy tayi da cewa toh abin ya fara damun nafisa, dan harta fara korafi akai, abinda kake nufi baxai yuwuba gara ka canza tunani, jayawa tayi ta kalli asma'u tace wace mutafi"
Acike suka samu falon, ummi na zaune rungume da d'an deeni ahannunta, bayan gaishe gaishe ma'u ta amsa yaron, dakin nafisa ta nufa, tana kokarin shiga dakin sukai karo da deeni yana fitowa"
Cikin sauri ya matsa gefe tare da fadin Ya subuhananlah"
Dago ido ma'u tayi ta kalkeshi, shima idosa nakanta"
Tafiya ta fara tare da gaidashi bayan ya amsa tamai barka sannan ta shiga dakin jikinta asanyaye"
Saida yamma suka koma gida tundaga ranan Jamal be sake barin ma'u tajeba, har ana gobe suna"
Ran momy ya baci sosai dan haka dayazo sallama zai tafi aiki ta rufeshi da fada"
Fadan momy yasa hankalin jamal ya tashi har ya yanke shawaran zuwa ya gano nafisa tare da jaririn da ta haifa"
***
Yana shiga gidan deeni na kokarin fita amman ganin jamal yasa yai saurin fitowa"
Hannu ya bashi suka gaisa fuskan deeni asake yayin da ta jamal take daure"
Har dakin baccin nafisa ya kai Jamal sannan ya juya ya fita"
Bayan sun gaisa ya rungume jaririn ya koma gefe"
Gunshekan kukan nafisa yaji, cikin sauri ya daga kai ya kalleta, sannan yace.....
Ya da kuka kuma?
Yaya Anty asma'u fah bata taba zuwa ba, gashi yanzun ma tunda tazo so daya bata sake zuwa ba"
Shiru yayi yana kallon yadda take share hawaye, zuwa can yace.....
Au saboda haka kike kuka, lallai shagwaba ta miki yawa dallah zoki amsa yaron Ki"
Juyawayi yai ficewan shi"
Daddare nafisa na zaune taji muryan asma'u kasa jira tayi ta shigo"
Cikin fara suka kalli juna sannan nafisa ta karbi yan biyu ahannun ma'u
Bayan sun zauna nafisa take tambayanta halan keda momy?
A'a yaya ne ya saukeni wlh abin yaban mamaki ina zaune yace wai nashirya yakaini Gidan Ki na kwana tunda gobe suna, wlh na dauka sunan ma bazai barni zuwa ba"
Wani farin ciki ne ya kama nafisa, mara misalantuwa"
Washegari yaro yaci suna Mashkur, aranan sunan Faisal yazo, walima sosai deeni yayi"
Washegarin sunan ne daddy ya hada Jamal da deeni, fada ya musu sosai tare da nasiha me shiga ciki, bayan ya gama ne yayiwa deeni albishirin ya budemai manyan rumfuna dazai yi kasunci aciki"
Godiya yayi sosai, nan danan deeni ya zama shararran dan kasuwa"
Tare da faisal suke gudanar da komai cikin Ikon Allah kasuwa saikara burun kasa take"
****
Jamal da deeni zuwan su baguma 3 tare dakai musu niki2 abun arziki"
Yan biyu nada shekara daya ma'u ta sake samun ciki, bayan wata tara ta haifi da namiji wadda aka sawa Aliyu, sosai yan biyu sukayi wayau tafiya suke gwanin sha'awa"
Aliyu nada wata 7 Nafisa ta sake haihuwan Jafar"
Zuwa wannan lokacin Jamal da deeni suna mgn sama sama, yadda yaga deeni na nuna soyayyar nafisa ako ina yasa jamal ya saki jikinshi, kullum cikin kara ririta ma'u yake"
Sosai Abba yakejin daddy idan ya tuna Asma'u na dakin mijinta, Jamal betaba kaimai karanta ba, kullum yaje gaida Abba idan xai tafi ya dinga godiya kenan"
Ita ko ma'u akullum suka hadu da Abba albarka yake saka mata"
Bayan ma'u ta yaye aliyu ne Jamal ya maida ma'u makaranta domin ta cigaba da karatunta"
Manyan hijjabai ya saya mata dakan shi yake kaita indai yana gari"
Bayan shekara 3
Ma'u na daf da karasa karatunta, ta fara laulayin ciki, tashin hakali ta nuna sosai, ganin haka Jamal yaita kwantar mata da hankali tare da nuna mata ai ciki bazai hanata karasa karatu ba"
Lallashinta yaita yi tana dada narkewa ajikinshi tare damai shagwaba iri iri, biye mata yai tayi, har ta saki jikinta"
Itako nafisa cikin na hudu ne ajikin ta, kulawa deeni yake sosai wajen basu tarbiya, baya wasa, beciga son kaisu gidan abbashi bashir ba, daya kaisu aranan yake komawa ya dauko su betaba bari sun kwana agidan ba, duk da yasan cewa komai ya zama daidai amman hankalin shi baya kwanciya"
Gidan momy ko aduk sanda suka samu hutu can yake kaisu har hutun ya kare, dan haka mushkur da yan biyu suka kule, wasa suke sosai"
Cikin ma'u ya tsufa dan haka Jamal ya matsa zai koma gidan shi, momy taso ya bari sai ma'u ta haihu amman ya dage"
Acewar shi tunda da tace tsoro take ji yanzun ai ga yara nan ta samu"
Sun koma da sati 2 ma'u ta haifi 'ya mace"
Kowa ya kalli yariyar cewa yake da ma'u tai kama, amman Jamal dagewa yayi wai shi ta dauko, haushi ma'u takeji idan jamal yace shi ta biyo, dan haka ta fara daure fuska"
Nafisa ce taita sintiri zuwa gidan da goyota abaya har akayi suna ayanzun yaran nafisa 4 kuma duk maza ne, yayin da ma'u keda 4 amman haihuwanta 3"
***
Yanzun Hassan da Hussaini suna da shekara 10, girma sukai na ban mamaki farare ne tas idan ba wadda ya sansuba baya iya babbaci su"
Wayon tsiya gare su, idan ka kalli ma'u baka taba cewa ita ta haife su, shi kanshi Jamal idan ya fita dasu cewa ake kannin sa ne, dan sun kusa kafardar shi"
Wata rana jamal ya kwaso duk gidan domin zuwa gidan momy, akan hanyar ne hira ta barke tsakanin Jamal da yaran shi, inda yake tambayan so idan sun gama karatu me suke so su zama?
Hassan ne ya fara cewa nidai daddy SOJA zan yi"
Kai amman ka burgeni kaifa hussaini?
Tura kanshi yayi gaban motar inda Jamal da ma'u ke zaune yace.....
Nidai daddy so nake kawaai na auri Hussaina"
Gaba dayan su dariya sukayi ban da ma'u data zafgawa Hussaini harara"
Itama Fatima wadda suke kira shikuriya zuboro baki tayi tare da matso hawaye"
Bayan jamal ya gama dariya ya waiga ya kalli Hussaini yace amman ai saika gama karatu ka samu aiki zakai auren ko?
Kafin Hussaini ya bashi amsa yaga Shukuriyya na shirin kuka dan haka ya juya ya kalli ma'u yace....
Toh fah, ita kuma wannan rigimanmar waya bata mata rai, nakula duk dabi,unta naki ne"
Juyawa yayi ya sake kallon shukuriya yace gaya min wanene ya bata miki rai?
Cikin shagwaba tace ba hussaini bane yake cewa baxai aureni ba, wai Hussaina zai aura"
Murmushi Jamal yayi kadan sannan yace wace wacece Hussaina?, rabu dashi aina zai samu Husaina ?, karya yake yi"
Hassan ne yayi dariya tare da fadin dolowa kawai, yaya za, ayi ya aureki ?, mamarmu daya babamu daya ai ba'a aure, saidai ki Aure mashkur"
Azuciye ma'u ta waga ta daka musu tsawa tare da fadin wlh duk wadda ya kara mgnr aure cikin ku saina fasamai baki, waigawa Jamal yayi ya kalli ta ya dauke Kai domin ya lura kamar ranta bace yake"
Babu wadda ya sake mgn har suka isa gidan' bayan Jamal ya gaida mikewa yayi zaifita saitin kunnen ma'u yaje yace.....
My Sweet Heart idan nina bata miki rai kiyi hakuri, idan kuma yara ne ki musu uzuri yarinta ce ba wani abuba"
Yana gama fadan haka yajuya ya tafi"
Da daddare ya dawo ya dauke su suka koma gida"
Jamal na kwace agefen gadon ma'u yake tambayan ta wai dazun menene ya bata miki rai ne?
Cikin damuwa tace....
Yaya tsoro Hussaini ke bani bashi da zance saina aure kusan kulum sai yayi mgnr, sai naga kamar babu karatu agaban shi"
Murmushi yayi sannan yace......
Ki daina damun kanki Husna yarinta ce ke damun shi, babu abin da ya sani fada kawai yake"
Washari da safe daddy ya bugawa Jamal waya cewa nafisa ta haifi 'yan biyu duk mata"
Cikin fara'a Jamal ya fadawa ma'u, shiri tahau yi cikin tsan tsan farin ciki"
Tunda Hassan da hussaini sukaji suka kama murna tare da rukon suma zasu"
Lokacin da suka isa gidan cike suka samu falon ciki harda dadddy da momy, alhaji bashir da ummi, deeni har kuka yake saboda farin ciki, kasa amsa barkan da Jamal kemai yayi sai hawaye dake zuba a idon shi, bayan shi Jamal ke bugawa tare da fadin ba kuka yakamata kayiba ka godewa Allah"
Addu'io Jamal yayiwa Hassana da hussaina sanan ya mikawa ma'u"
Kwlla cike da idonta bakinta dauke da murmushi take kallon su"
Damunta yan biyu sukayi dan haka ta mikawa husaini Hasssana girza kai yayi tare da fadin momy Husaina zaki bani"
Hararan shi tayi sannan kowanne ya dauki takwaran sa"
Kinbawa kowa su sukayi, momy ce tace, nifah 'yan biyu ban gane bane, me kuke nufi?
Dariya ummi tayi tare da fadin kika sani ko yar gida za'ayi?
Dariya daddy yayi sannan yace kudai kuce kishi na damun ku"
Tun daga ranan ma'u ke zarya zuwa gidan har akai suna, kulum idan ma'u zata tafi sai 'yan biyu sunce ashafa musu kan jarirai"
Abba da kanshi ya kawo mama suna sannan yaita sawa yaran albarka dayaga deeni be iya shaidashi ba, saida daddy yagaya masa"
Ma'u nakai ziyara kano akai akai, inda lokaci bayan lokaci yaya usman yake kai mata fa'iza da dada"
Wata rana dada ta kawo mata ziyara da gangan tajata gidan nafisa, suna shiga tsakiyan harabar gida ma'u ta juya ta kalli dadda tace......
Dada kinsan Gidan wa na kawoki?
Saikin fada takwara"
Dariya ma'u tayi sannan tace gidan me kare"
Rawan jiki dada ta fara tare da fadin La haula fisha'atillahi azubika, Allahu akkubar Allah da kirma kake, fitsari ne ya fara zubowa ajikinta, banda dariya babu abinda ma'u keyi"
Daida kokacin deeni ya fito daga gida, ganin haka yasa ma'u ta tsaya da dariya tare da kama hannun Dada tana fadin zomuje"
Tirjewa dada take tana cigaba da surutun ta"
Deeni ne
ya matso yana fadin yaya akayi ne dada?
Yauwa bawan Allah zoka tai make ni, ka maida ni Kano ya riyar nan bata kyaunata so take taga bayana, zata kaini inda za'a akashe ni"
Ganin in da dada take arikece yasa ya kama hannun ta, motar shi ya bude ta shiga, ma'u dariya take tayi badan kar dada ta sumaba data kara cewa wani abu, cikin gidan ta shige"
Shiko deeni bayan sunyi nisa yaga jikin Dada ya daina rawa, anan ya fara tambayanta meya hadata da asma'u?
Warware mishi komai tayi, kwashewa yayi da dariya acikin zuciyan shi yace sai yashe asma'u zatai hankali ta daina tsokana, daman har yanzun tana nan da halinta?
Gidan daddy yakai dada sannan ya gaya musu abinda ke faruwa, dariya sosai daddy yayi sannan yace ai ga mekaran nan agaban Ki"
Mamaki ne ya kama dada daman Abba ya gaya mata deeni ya shirru Amman batasan takai haka va"
Hira sukaci gaba tsakanin deeni da dada daddy da Momy na souraran su"
Bayan shekara 10
Soyayya ce me karfi tsakanin Hassan da Hassana, Husaini da Hussaina, tun suna kana suka taso da kyaunar juna, duk da cewa su hassana basu wuce shekara 12 ba"
Jamal da deeni zumuci suke sosai har sun yake shawaran hada inbiyun su aure, da zaran ko wannen su ya kammala karatun shi"
Ma'u tun daga shikuriyya bata sake haihuwa ba, Jamal kara shagwabata ma'u yake idan ka gansu adaki bakace suna da yara 'yan shakara
20 da duriya ba"
ALHAMDULILLAH
Heat Beat
The End🙋🏻
*Mmn Yazeed*
Download Bugun Zuciya Littafi Na Daya Complete HausaNovel
0 Comments
Thank you for this comment