[1/23, 22:07] ‪+234 803 619 0581‬: 😭😭😭 ZUBAIDAH😭😭😭

                       01

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_👑Queen Samy Novels Forum....📖📚_


   *Dedicated to all Victims of Rape, never give up, fight for your right, this is not something to be ashamed of your self.  Make the guilty ones feel ashamed of themselves* 🙌🏾🙌🏾🙌🏾🙌🏾🙌🏾


   "Garin Dukku jihar Gombe, gari ne wanda akasarin mutanen dake zaune wajen fulbe ne,  ma'ana fulani ne.  Ni Sameena tafe nake cikin garin ina bin tsarin garin da kallo yayinda zuciyata ta cika da nishad'i.  Can na hangi wata matashiyar budurwa wacce ak'alla bazata gaza shekaru goma sha shida 16 a duniya ba. Daga yanayin halittarta zaka fahimci cewa bafulatana ce ta usul.  Bata da matsanancin tsayi snn bata a layin gajeru,  farinta irin mai d'auke idon  nan ne don saida ta matso kusa sosai na fahimci hakan.  Yanayin suturan dake jikinta zai tabbatar maka iyayenta talakawa ne  sosai. Silipas din dake k'afufunta kuwa duk ya b'ule yaji jiki.
  "Sauri take tamkar mai shirin tashi sama,  yanayin tsoro da firgici da ya wanzu a fuskarta zai tabbatar maka cikin matsanancin tashin hankali take. Kaman ta zunduma a guje haka take tafiyar, Yar  da d'an karan dake hannunta tayi ta soma sassarfa hadi da gudu  gudu sakamakon jiyo muryar dake sata firgici koda a mafarkinta ne tana k'walla mata kira har waje ake jiyowa,. *ZUBAIDAH! ZUBAIDAH, ZUBAIDAH!!!
 
"Ni kuwa  Queen Samy nace " Bari na bi wann yarinya na rubuto wa d'inbin masoyana labarinta mai cikeda tausayi, Al'ajabi da kuma ban mamaki had'i da darrusa masu girgiza zukata. 


    "Dan ubanki sai yanzu kika daman dawowa daga karuwancin naki?  Macen dake tsaye tsakar gidan rik 'e da guga ta fad ' tana watsa wa Zubaida mugun kallo me nuni da cewa zaki yaba wa aya zak'inta.
   "Bakinta na rawa take fad 'in Yaya Hadiza wllhi ban sami Yayan a kasuwa bane shine na k'arasa bakin tasha..... Ai bata gama cewa tasaha ba Yaya Hadiza ta jefa mata gugan dake hannunta ji kake tum ya fad 'I a tsakar kanta.
   "Durk'usawa Zubaidah tayi tana rik'e da tsakar kanta hawaye na zuba bisa k'uncinta.

  Hadiza ta k'araso gamida mak'urota tana fad'in" Dan ubanki ni  na aikeki bakin tasha,  wani munafurcin ne ya kaiki bakin tasha,  auho kice mun karuwanci kika tafi, shegiya Me suffan mayu da aljanai.  Rankwashin da ta sake mata a tsakar ka yasa Zubaidah sakin k'ara sabida azaban dataji.
  "Hadiza ta shiga janta a k'asa tana fad'in" Au kuka ma zakiyi shegiya munafuka saikace wacce na bugeki toh bari kiga na tapkeki sosai sai kiyi mai dalili.
  "Duk kukan da Zubaidah take tana  rok 'on Hadiza tayi hak 'uri ko gizau bata fasa jibgangta ba kaman  Allah ne ya aikota.

   "Inna Furera mak'ociyarsu ce ta shigo a guje don ceton Zubaidah dama mak'ota sun saba shigowa kawo mata d'auki, tunda Hadiza ta tsefe ido taci mutuncinsu tsaf suka daina, saiko Inna Furera ce kawai bata fasa ba.
   "Da sauri tayi tsalle ta kwace Itacen da Hadiza ke jibgan Zubaidah dashi, dama Jadiza irin ingarman matan nanne.
   "Ta shige tsakani tana fad'in" Haba, haba Hadiza, anya kina kuwa tuna mutuwa, kullum sai ki kama wann 'yar marainiya kita jibga ke ko tsoron kamuwar Allah bakya yi.  Cewar Inna Furera .
   "Galala take Kallon Inna Fure kafin ta gyara tsayuwa ta soma fad'in" Fure!  Fure!!  Fure!!? Billahilazim hawainiyarki ta kiyayi ramata,  banda munafunci irin taki ina ruwanki da ita,  ci kike bata ko sha, cikin biyu babu d'aya.  Toh wllhi wllhi ki fice a idanu na.
   "Inna Fure tai murmushin takaici kafin tace " Lokaci ne, da zaran lokacin da Zubaidah zata sami kulawata yazo zata samu kuma ke baki isa kiyi komai ba.
   "Shewa Hadiza ta kwashe dashi kafin tace " Ai dama nasan wajen munafukin wann d'an naki me matse yaran mutane a lungu take zuwa, bacin haka babu abinda zai kaita bakin tasha,  Toh wllhi idan ni Hadiza ina numfashi Zubaidah bazata auri Ummaru dreban tanka ba. Ke na tak'sita maki zance Zubaidaha bazata tan's aure a rayuwarta ba,  makarantar data samu na bari tayi ya isheta, amma aure kam saidai tayitaji k'annen bayanta suna tafiya d'akin miji amma banda ita,  tunda dama sa 'anninta Sun k'are k'annenma sun kusa k'arewa. Ta juyo ta narkawa Zubaidah da har lokacin kukan zuci take hawaye na bin k'umcinta tace " Ke kuma bak'ar munafuka ki tashi ki min wanke wanke kafin ki d'aura sanwa don yau islamiyar ma ba zuwanta zakiyi ba. Daga haka ta wuce d'aki fuuu kamar me shirin tashi sama.
  "Inna Fure ta girgiza kai ta k'arasa ga Zibaidah wacce ke faman mik'ewa da k'yar sabida raunin da Hadiza taji mata da itace, tsugunawa Inna Fure tayi tausayin yarinyar ya cika zuciyarta, a hankali tasa hannu ta goge k'wallan da ya zubo mata. Hannu tasa ta shiga sunce d'aurin da Hadiza tai ma Zubaidah da igiyan guga.
   "Suna had'a ido Zubaida taji wani sabon kuka na shirin kufce mata, ........
[1/23, 22:07] ‪+234 803 619 0581‬: 😭😭😭ZUBAIDAH😭😭😭
                   02
              
*©Sameena Aleeyou... ✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum.... 📖📚_

*Dedicated to all victims of rape, never keep silence, keep fighting for your right, this is not something to be ashamed of your self, let the guilty ones feel ashamed of themselves*🙌🏾🙌🏾🙌🏾🙌🏾

  "Murya na rawa Zubaidah take fad 'in" Inna meyasa iyayenmu suka mutu suka barni dagani sai yaya na, meyasa Yaya na ya kasance haka, meyasa bai zama kaman ko wani d'an Adam ba...... " Tausayin kalamanta sun cika zuciyar Inna Fure, a hankali ta kwance bakin zaninta ta goge wa Zubaidah hawayen dake kwaranya a fuskarta. Hannayenta ta rik 'e suna fuskantar juna kafin ta soma fad 'in" Zubaidah kar ki bijire wa ubangijin ki, kar ki bari shedan ya rinjayi zuciyarki, har yake kawo maki ire iren wad'an nan tunani.  Mutuwa dole ce kan ko wani mahaluk'i, snn kasancewar yayanki cikin mutane marrasa k'oshin lafiyan k'wak'walwa jarabawace daga Allah, wanda kema jarabawar ya shafeki. Shi kansa Habibu baijin dadin abinda Hadiza ke maki, amma babu yanda ya iya, bazai iya k'watan 'yancin kansa ba balle naki daga hannun Hadiza, hak'uri shine zakici gaba da yi.
   "Goge hawayen tayi kafin ta furta a hankali " Kenan shikenan ni bazan tab'a jin dad'in rayuwa ba kenn,  bazan rayu kaman yanda ko wani d'an adam yake rayuwa cikin 'yanci ba. ...."Kasa jure saurarenta Inna Fure tayi sabida tausayi,  mik 'ewa tayi kafin tace "Tashi ki soma ayyukanki kafin ta fito ta sameki.  Jiki a sanyaye Zubaidah ta mik 'e daidai lokacin " Kamalu d'an Yaya Hadiza ya fito cikin shirin tafiya islamiya fuskarsa da alamun bacci ya tashi, yaro d'an shekaru bakwai a duniya.  Rungume Zubaidah ya k'araso yayi yana mata magiyan ta shirya su tafi islamiya,  itama rungumesa tayi tana k'k'arin lalumo k'aryar da zata shata masa, don tasan yau kam babu ita babu islamiya. Inna Fure ta fice tana sak'sak'en lamarin Zubaidah a zuciyarta.

   "Kamalu ya lura da hawayen dake bisa fuskan Zubaidah, Ya kalli gwiwar hannunta yaga jini, shiru yayi kaman bazaice komai ba kafin yace " Na sani yauma Umma tace ta dakeki ta hanaki zuwa makaranta ko Anty. Kame kame Zubaidah ta soma yi don yaron akwaishi da wayo da kaifin basira,  daidai nan Yaya Habibu yayi sallama ya shigo cikin yanayin tafiyarsa na sokaye _Phsycos_ da maganansu.
  Kamalu ne kawai ya tafi ya masa oyoyo Zubaidah kam wucewa tayi bakin rijiya don taran ruwan wanke wanke, tabbas tasan Yaya Habibu ya ganta a haka toh fah haka zai wuni yana kuka.

   "Inna Fure tana shiga gida ta tarar da Umar dawowarsa kenan.  Koda ya gaisheta sama sama ta amsa,  Umar ya lura da yanayinta, don ko tambayarsa ko yaci abinci batayi ba,  kaman yanda take a kullum. don haka zama yayi bisa gefen tabarman da take zaune " Sadda murya yayi kafin yace Innata meke faruwa ya tambaya yana kallon Inna Fure. Sauk 'e ajiyan zuciya tayi kafin ta soma fad'in" Umar shin da gaske kake son Zubaidah.
  "Kallon mamaki yayiwa mahaifiyar tasa kafin yace "Haba Inna wann wace irin tambaya ne, Kowa ya sani duk fad 'in garin nan Zubaidah kadai nake so,  nake burin mallaka, bansan meyasa Zubaidah tak'i barina na kai tambaya gidansu ba. Don wllhi Inna na k'agu na rabata da wann muguwar matan yayan  nata.
   "Inna ta sauk 'e ajiyan zuciya kafin tace " A gaskiya Hadiza bata da imani Ummaru....... "Ganin yanayinta yasa mik 'ewa zuciyarsa na bugawa yake fad'in" Inna ki fad 'a mun me tayi mata, ta kuma dukanta kaman yanda ta saba ko..
  "Gjrgiza kai Inna ta soma tana fad'in a'a Umar don Allah ka zauna,  zauna nace ba dukanta tayi ba,  kawai dai so nake ayi maganar aurenku, da zaran malam ya dawo zan masa batun insha Allah,  take farin ciki ya mamaye zuciyarsa nan ya shagala da zancen......Inna ta bisa da ido yanda yake murna kaman an masa alk'awarin hajji, gwara da ta kawo masa wnn zancen don tasan kalan zuciyar d'anta yanzu sai yaje yayi ma Hadiza kaca kaca.


**********************
*Abuja, Maitama*

"Wasu tagwayen gidaje na hango masu d'an karen kyau, exactly babu abinda ya raba da na gefe, komai iri guda. Wadan nan gidaje gidajen Yaya ne da kuma k'ani,  Alhaji Kasim Dasuki shine Babba, yayinda Alhj Jamil Dasuki shine k'ani.  Alhj Kasim da k'aninsa sunyi kaurin suna wajen hold'an kasuwanci ta yanda k'asashen duniya da dama suke hold'a dasu,  tareda shahararriyar Company dinsu mai suna *Dasuki Holders*,  Ko wannensu Allah Ya albarkacesa da yaro namiji k'wara dad'd'daya,.

SALIM KASIM DASUKI,  da kuma LABIB KASIM DASUKI,   tsakanin Salim da Labib shekara gudane cal,  haka nan yaran suka taso cikin sangarci da rashin tarbiya,  saboda so da iyayensu ke nuna masu, wanda a nasu tunanin gata ne. Babu mai taba masu 'Ya'ya Ya zauna lafiya sai sun ga k'arshensa,  musamman Alhj Kasim shi yafi k'aninsa bak'in zuciya,  wani sa'in Alhj Jamil dinne ke nusar dashi hanya. Haka zai balbalesa tsaf da masifa,  uwa uba  WA'azin da Alhj Jamil ke masa kan su guje dukiyar haramun cikin kasuwamcinsu,  wann dalili Ya soma sakawa Alhj Kasim tsanar Dan'uwarsa har yake tunanin tabbas zasu iya samun sab'ani koma takaisu ga raba dukiyarasu.
[1/23, 22:07] ‪+234 803 619 0581‬: 😭🙍🏻ZUBAIDAH🙍🏻😭

                 03
*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum..📖📚_

    *Dedicated to all victims of rape, never keep silence, fight for your right,... This is not something to be ashamed of your self, let the guilty ones feel ashamed of themselves 🙌🏾🙌🏾🙌🏾🙌🏾*

   "Salim ne kwance saman coach a bakin pool dake a cikin gidansu, da gani daga ruwan ya fito don daga shi sai gajeren wando. Idonsa manne da bak'in sunshade ya k'ura wa rana ido, gefe dashi k'aramar table ne wanda wayoyinsa ne da kuma Chapman akai.
  "A hankali ya kai hannunsa kan table din gamida daukar d'aya daga cikin wayoyin nasa nan ya shiga dialling lambar budurwarsa KAUSAR wacce ake batun saka masu rana.  Sosai suke hiran soyayya daga ji kasan suna tsananin son junansu.

   "Daga can bayansa yanda Labeeb ke tsaye ya k'urawa cousin d'in nasa ido, shakka babu su duka biyu sunyi tarayya wajen son mace guda, zuciyarsa yaci gaba da tafarfasa,  da sauri ya juya ba tareda yayiwa d'an uwan nasa magana ba.

   "KAUSAR TAHIR MARAFA,  shine asalin sunanta,  mahaifin Kausar abokin kasuwancin iyayen Labeeb da Salim ne,  musamman Mahaifin Salim Alhj Kasim Dasuki, Shima Alhj Tahir Marafa dan asalin garin Dukku ne, Kausar basu jima da dawowa Nigeria ba daga k'asar Holland dalilin dawowarsu ma sabida neman muk'akin kujeran Shugaban k'asa da mahifinta zai fara ne, farkon dawowarsu sabo mai tsanani ya shiga tsakaninta da Labeeb a lokacin Salim yana can Scotland yana k'arasa wani course dinsa shi, koda Salim ya dawo Labeeb shi yayi masa introducing Kausar,  tunda Kausar da Salim suka k'yalla ido akan juna soyayya mai tsanani ta shige tsakaninsu,  toh fah run daga wann lokaci Labeeb ya rasa sukuni, a ganinsa cin amana ce wnn k'wace Salim yayi masa.
   "Iyayensu gaba d'aya sunyi farin cikin wann Al'amari  tun basu hadasu ba gashi sun hada kansu,  babu kaman Alhj Kasim Dasuki wanda dama shi Money hungry, baya rab'an mutum sai zai sami alkhairi. Dukda tarin dukiyar da yake dashi baya hanasa hangar na wani. Yasan muddin tilon d'ansa Salim ya auri tilon 'yar Alhj Marafa wataran zasu mallaki gaba d'aya dukiyar Alhj Marafa.

    "JALAL!  Na'am Anna ya amsa gamida ajiye takalmimsa da yake faman gogewa,  fitowa yayi ya tarar da Annah zaune tana stincen wake
. Kallonsa tayi yanda ya shirya tsaf cikin kaya masu kyau da tsada kaman wani d'an hamshak'i.
  "Jalal ina zaka, Jalal farin saurayi dogo mai cikar zati kyakkyawa ya murmusa kafin yace "Annah birthday d'in abokinmu TARIQ zamuje  su Salim suna waje suna jira na. 
   "Fuskar Annah tamau dama tasan zancen bazai wuce haka  ba,  tasha raba Jalal dasu Salim amma baya ji,  yak'i yarda ya tsaya a matsayinsa na talaka bashi da aiki kullum sai k'ok'arin had'a kansa da sangartattun yaran masu kud'i musamman su Labeeb.
 "Gyaran murya Annah tayi kafin ta soma fad 'in" Jalal har yaushe zan maka magana kaji, ka sani kai maraya ne kuma talaka, idan baka tashi ka tsaya ma rayuwarka ba babu wanda zai maka,  kai kullum bakada aiki se biyewa su Salim ko,  toh ka sani su sunada masu masu, sunada gatansu kaifah,  baka dashi , tunda ka gama jami 'a ka'ki neman aiki ka tsaya kana biye masu,   yau kune wancan club din gobe wancan,  kune bin 'yanmata kune shaye shaye...... "Jalal yayi saurin d'ago kai yana kallon Annah,  haba Annah shaye shaye fah kikace nasan dai su Salim suna yi amma ni banayi,  ina dai da 'yammata banyi musu ba amma wllhi bana shan komai tunda kika hanani....... "Rufe mun baki Annah,  ta dakatar dashi kafin taci gaba da fad'in" Da da kakeyi na maka uzuri don na d'auka yarinta ne zaka daina amma yanzu na gane shashanci ne kawai ke damunka, shekaranka 25 ace bakasan abu me kyau ba toh wllhi ka kiyayeni..... "Sallaman Labeeb ya katsesu.

   "Gaisar da Annah Labeeb yayi, ta amsa masa babu yabo babu fallasa,  kafin ya d'an daki kafad 'un Jalal yace Guy let's get going.. Jalal ya mike yana satan kallon Annah kafin yace Annah sai mun dawo,  kallo tabisu dashi har suka fice, girgiza kai tayi kafin tace bazan fasa maka addu'an shiriya ba.

Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:07] ‪+234 803 619 0581‬: 😭🙍🏻ZUBAIDAH🙍🏻😭

                04

*©Sameena Aleeyou..✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum... 📖📚_
  *Dedicated to all Victims of rape, never keep silence. Fight for your right, this is not something to be ashamed of your self, let the guilty ones feel ashamed of themselves🙌🏾🙌🏾🙌🏾🙌🏾*

   "JALAL, abokin su Saleem ne wanda tun tasowarsu tare suka taso, Jalal maraya ne wanda bashida kowa sai mahaifiyarsa Annah, Annah tayi komai a rayuwarta don ganin ta inganta rayuwar Jalal tun yana yaro, kama daga karatunsa har zuwa girmansa,  haka nan ya tashi ba tareda yasan mahaifinsa ba, don Annah ta sanar dashi cewa mahaifinsa ya rasu tun yana k'arami. Annah ta jima tana yiwa matar Alhj  Kasim aiki wato mahaifiyar Salim,  tun wani lokaci da suka zauna a Gombe,  tun yaran gaba d'aya suna k'anana,  Annah ita ta rainesu gaba d'aya,  Salim Labeeb da kuma Jalal  d'inta,  wann dalili yasa lokacin da zasu komo Abuja suka taho tareda ita don tun a lokacin bata da miji ya rasu. Ta zauna da d'anta a nan BQ din gidan Alhj Kasim.
  "Tunda yaran suka taso iyayen ke k'ok'arin rabasu da Jalal, suna nuna masu cewa shi ba daidai dasu bane,  babu yanda basuyi ba don ganin sun rabasu amma abu yaci tura dole suka hak 'ura suka k'yalesu,  amma ko kid'an babu wani abu na arziki da suke masa.
   "Shi kuwa Jalal babban abun da ke masa dad'i shine yanda emmata da samaruka yaran masu kud'u suke zaton shima DASUKI'S ne,  ma'ana shima dan familyn Dasuki ne,  ko ina tare dasu Salim suke zuwa party shisha spot da dai sauransu.  Allah ya masa kyaun hallita gabba d'aya yafisu kyau 'yanmata  suna rubibinsa shiko na ja masu class kaman wani d'an hamshak"i ko kad'an bakace  Jalal ya had'a jini da talaka ba...wann kenan.

 *Gombe,  Dukku*

   "Huci take kaman wata kububuwa tana watsawa  malam Habu mahaifin Umar da abokinsa malam Tanko harara,  Malam Habu suka saki baki suna kallon ikon Allah sanda  Yaya Habibu ya mik'e ya rusuna gaban Hadiza yana tambayanga shin ta amince a karb 'I baikon Zubaidah, .... Mikewa Hadiza tayi kafin ta d'ibi 'yan goron da malam Habu suka shigo dashi ta shiga juye masu a tsakar kansu, tana balbala wutan bala 'i da masifa,  ta yanda take shiga bata nan take fita ba.
"Malam Tanko ya mik'e yana fad'in subuhanallah,  Malam Habu ya baka fad 'a mun haka lamarin yake ba, Malam Habu da kunyar abokinsa mutum mai muhimmaci a gari irin Malam Tanko ya baibayesa,  dama yasan haka ka iya faruwa, shiyasa tun farko bai so Ummaru ya nemi Zubaidah ba dukda ya aminta daehankali yarinyar kuma na tausayinta,  amma ko kad'an bashi fatan abinda zai hadasa da dilalliya Hadiza,..... 
   "Zubaidah dake mak 'ale bayan k'yaure bata san sanda ta sulale  gwiwoyinta a k'asa ba tana hawaye sanda ta jiyo irin fatattakan da Yaya Hadiza tayima iyayen Umar, shikenan itakam tasan bazata tab'a aure ba,  bazata tab'a jin dad'in rayuwarta ba,  mafarkin ta bazai tab'a tabbata ba,  takaicin yayanta da tausayin kansu shida ita ya lullub'e zuciyarta. A hankali ta k'arasa kan tabarman da ya kasance makwancinta ta kwanta tana kuka mai tsuma zuciya.

   "Malam Habu jiki a sanyaye ya shiga bawa Malam Tanko hak'uri,  Malam Tanko yace a'a abokina baza 'a bar wann magana ba tunda yaran suna son junansu ni nasan yanda za'ayi, ka shige gida zan nemeka zuwa gobe,  Malam Habu ya masa godiya sukayi sallama kafin malam Tanko ya hau babur dinsa ya wuce.

*******************
*Abuja*

    "Suna isa wajen partyn pili ya dauki shewa da ihu,  manyan yara wanda duk gabaki d'aya Abuja sunansu yayi k'auri Sun samu halarta,  Tariq ya k'araso yana welcoming nasu sai wani tafe hannaye suke yanda niggas  keyi.  Tariq shine cikon na hud 'u a clik d'insu,  shima mahaifinsa nada shears a companyn *Dasuki Holdings* kampanin mahaifan Salim da Labib, ..

*Zubaidah, Jalal, Umar,  Salim, Labib da kuma  Tariq*




*Ku biyo Sameena don jin labarin gumurzumon da wad'annan matasa suka fuskanta.......... 👌🏾*
[1/23, 22:08] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                              05

*©Sameena Aleeyou.....✍🏾*

_Queen Same Novels Forum...📖📚_

     "Alhj Kasim Dasuki, Alhj Jamil Dasuki da kuma Alhj Yusuf Maina mahaifin Tariq sai Barrister Munir Malami lawyer na company ɗinsu *Dasuki Holdings* kuma yaya ga mahaifiyar Salim Haj Farha Dasuki.
  "Zaune suke gaba ɗaya a babban parlorn taraban baƙin Alhj Tahir, magana suke na tsaida ranar auren Salim da Kausar, an tsayar sati mai zuwa za a yi bikin saka rana. Daga nan suka ɓuge da hiran kasuwanci da siyayasa. Tunda dama Alhj Tahir na neman tsayawa takaran shugaban ƙasa, nan Barr Munir ya bada shawarin a tafi chan Dukku ayi bikin saka rana hakan ba ƙaramin nasara zai kawo wa neman takaransa ba, gaba ɗaya sukayi na'am da batun Barr Munir snn ƴan garinsu zasu tabbatar shi ɗin mai ƙaunar mahaifarsa ne..... Har farfajiyar  gidan Alhj Tahir ya rakosu yanda bodyguards ɗinsu suke... Daga nan ya wuce ɓangaren matarsa uwar ƴarsa Hajiya Raliya don sanar da ita yanda suka tsai da batun auren yaran.
   "Kausar da Asmah ya samu a parlorn ƙasa suna playin PSP, gaba ɗaya suka soma gaidashi... Papa sannu da shigowa amsawa yayi da sakin fuska kafin yace ina momman taku, har suna haɗe baki wajen cewa she's upstirs, ƙarasawa yayi ya nufi stirs ɗin.
  "Kausar da Asmah suka ci gaba da game ɗinsu. Asmah cousin ɗin Kausar ce wacce a shekare baifi ta girme wa Kausar da shekera guda ba, tun dawowarsu  Nigeria Asmah take gidansu daga zuwa kwana biyu Kausar taƙi barinta ta koma dole Aunty Miemie mahaifiyar Asmah ta haƙura da zancen don tasan halin Kausar da kafiya.
  "Momma na zaune gaban dressing mirror tana gyaran fuska as usual don itakam taƙi yarda ta tsufa at her late 40s bats sahun matan nan masu barin gyaran jiki da zaran sunga shekaru ya soma ja masu,... Murmushi Papa yayi gamida rungumota ta baya,  murmushi itama ta sakar masa kafin tace" Papa how do i look like, ɗan jan hancinta yayi kafin yace as always my one you look so gorgeous manna mata peck yayi a goshi kafin suka zauna bakin gado ya soma faɗa mata yanda suka tsai da maganan bikin Kausar, nan da nan idon momma yayi raurau Kausar is her only daughter ƙaunar ranar rabuwarsu tazo dukda tasan dole wata rana hakan ta kasance.... Papa yasan kwanan zancen don haka rungumota cikin jikinsa yayi ya soma lallashinta da kalamai masu taushi, "Haba first lady you need to be very strong you know, sooner or later zaki zama mother of the country insha Allah, bama Kausar kawai ba, the whole country will be yours, and for now akwai Asmah though nasan itama tana samu miji zamu aurarta but atleast zata ɗauke mana kewar Kausar.... Jin yanda mijin nata keta faman riritata yana shagwaɓata yasata sakin murmishi gamida goge guntun hawayenta tace" Pappy you ƙnow what made me cry...." Ɗan girgiza kai yayi har lokacin tana cikin jikinsa kafin taci gaba da faɗin" I dont know why, but har raina banjin son auren Kausar da Salim duk da ɗan aminiyata ne, quite alright nasan gidan girma arziki da mutunci zata but.... Kasan yaran zamani kar Salim ya hurting mana baby girl ɗinmu...."Papa yayi murmushi gamida shafa goshinta zuwa gashinta kafin yace" Raliya insha Allah we won't regret it, bazamuyi danasanin aurar da Kausar wa Salim ba, besides they both love each other wanda kinga hakan akeso ya kasance. Yanzu abunda nake so dake, you shud start preparing we leaving in a couple of days gwara mu mu fara isa tunda mune iyayen bride, I'll make sure the house is ready from now to tomrrw, ki kira su Kausar ɗin ki sanar dasu su fara shiri, barin ƙarasa parlor inada wasu baƙin.. Gyada kai kawai momma tayi da ƙyar kafin ya manna mata kiss a chick ɗinta ya fice.
 "Wann shine rayuwar gidan Alhj Tahir, mutane ne masu Dattako da sanin ya kamata, ko kaɗan basuda ƙyamar talaka kaman Dasuki family, snn abin hannunsu sam bai rufe masu ido ba, da wann dalili yasa akasarin mutane suke mara masa baya a siyaysarsa, yayinda wasu ke ganin The Dasuki family ks iya ja masa cikas a siyasarsa sabida izzan su da ƙyamar talaka ds suke dashi.

   "Kausar da Asmah sai murna suke zasu Dukku dukda kakanninsu gaba ɗaya sun rasu amma skwai sauran dangi, Momsy ya maganar kayan gaskiya ki sake masu waya we need them this week, they shud make it possible this week. Momsy ta ɗan sakar mata harara kafin tace" Kausar this is not Holland fah, na faɗa maki ki rage wann rawar kan taki, ba irin auren da kika saba gani bane na turawa, wann auren fulani ne wanda aka san sansu da kunya so be careful,... Momsy tana ficewa Asmah da Kausar suka kalli junah, suna daroya ƙasa ƙasa don suma har sun ɗagota bata son Kausar ta bar gidan ne Asmah ta ɗau waya tace bari kiga na kira *Mamza beauty* (makeup artist)  na sanar mata, ke kuma pls ki kira Sarah fashion ( Fashion stylist ne a Dubai wanda zasu ɗinka kayyaykin Kausar da zatayi amfani dasu a events) ɗin ki sanar dasu.
   "Rungume pillow tayi gamida lumewa cikin hashaƙin gadon tana tuno farin cikinta Salim, ya kusa zama *Mallakinta* Asmah na mata magana ko saurara batayi ba tayi nisa wata duniyar, girgiza kai kawai Asmah tayi ganida jifar ta da pillow kafin ta fice.


  "Tafe suke suna tangaɗi da gani kasan sun bugu da giya,   da ƙyar suka iya fitowa daga motan ,Alhj Kasim da har loƙacin idanunsa biyu baiyi barci ba ya dubi agogon bango dake maƙale a ɗakin ya nuna ƙarfe uku na talatainin dare, yasan ba kowa bane zai shigo gidan a yanzu sai Salim, kai tsaye down stirs ya sauƙo ya buɗe ƙofar parlor, chan ya hangesu suna tafe suna tangaɗi gaba ɗayansu, Jalal na riƙe dasu don dama duk randa suka je party suka shawu toh shi ke driving nasu da shike shi bai sha yanda za'a gane sama sama yake kora wine maras bugarwa sosai shide barshi da harƙan bin mata, shiɗinma da yawa ƴan matan ke kawo  kansu wasu na zaton shi ɗin ɗan Dasuki Family ne yayinda wasu ke sonsa sabida kyaun da Allah ya masa.
   "Wani mugun kallo kawai Alhj Kasim ke binsu dashi musamman Jalal, shikan ya tsana ganin yaransu da sidecake ɗin,..... "
   "ƴan kame kame Jalal ya soma, tuni Alhk Kasim y dakatar dashi  da faɗin" meyas baka kai shi gidansu ba ya ƙarashe maganar yana nuni da Labib, Jalal da tuni ya shaƙi kallon ƙasƙancin da Alhj Kasim ke masa, a daƙile yace " Gani nayi nan ma gidansu ne......"Jar ubancan haka Alhj Kasim yace a zuciyarsa lallai wnn talakan raini na neman shiga tsakaninsu, baiga laifinsa ba lafin su Salim ne,... Securities ne suka ƙaraso suka shiga taimaka wa Jalal, ɗaya security ɗin daga gidansu Labib yake yazo tafiya dashi don hankali mom ɗinsa ba ƙaramin tashi yake ba duk randa yayi dare a waje, duk da hakan ba sabo bane amma she couldnt get used to it har yanzu. Haka aka wuce da Salim da Labib kaman wasu mutattu don tuni bacci yayi awon gabadasu.
   "Jalal ya ɗaga gira sama kafin ya dubi Alhj Kasim yace" Have a good evening Sir , daga nan yayi wucewarsa can sashensu. Kallo Alhj Kasim yabisa dashi kafin yayi ƙwafa ya shige cikin gida.



     "Washe gari zaune suke gaba ɗaya a babban parlorn Alhj Kasim, Ya kuma duban Hajiya Farha dake zaune gefen Hajiya Nurah mahaifiyar Labib yace" Farha  jeki taho min da yaran nan Labib da Salim suna sashen Salim, babu musu Hajiya Farha tabi umarnin mijinta ta fice kiransu.
   "Sai ihu suke suna buga game na ƙwallo ko saurarenta basuyi ba, da takaici ya isheta batasan sanda ta fincike socket ɗinba....."Whatttt!!!!! Suka fadi a tare, Salim yayi jifa path ɗin hannunsa gamida faɗin " Shitttt, why mum haba haba mum.... Rufe mun baki marassa hankali kawai Mum ta ƙasesu, Labib ya ɗan langɓe kai kana yace" We are sorry favorite Aunty, Kunnens ta janyo kafin tace" Daga yau zaka tashi daga fav son idan baku zama good boys ba, Dad na kiranku bata jira cewarsu ba tayi ficewsrta. Labib yace nasan Uncle ne dama zai sa Fav Aunt ta mana haka he will never change. Salim ya watsa masa mugun kallo kafin ya fice ba tareda yace komai ba.


   " Cikin tafiyarsu na samarin da tarbiya bai ishesu ba suka ƙaraso parlorn, gamida tsayuwa ma iyayayen tsegehe akai.
   "Alhj Jamil, ya sauƙe ajiyan zuciya kafin yace" Seat down boys, zama suƙayi da ƙyar saman carpet Alhj Kasim kuwa banda hararsu babu abinda yake. Kaman jira yake nan ya soma surfa masu masifa " When are you boys going to start acting like real Dasuki's huh?Har yaushene zaku daina alaƙa da wann matsiyacin yaron, he's not one of you ba daidai ku bane get this to your heads..... " Alhj Jamil da mamaki yake kallon ɗan uwan nasa ko kaɗan baisan kan hulɗa da Jalal zai masu faɗa ba, a'a ya ɗauka kan ɗabi'u marassa kayu da suke zai masu faɗa, to his gretest surprised sai jin akasin haka yayi, lallai yayansa yayi nisa.
   "Labib ne ya ɗago kai yanai ma uncle ɗin nasa mugun kallo ƙafin yace" Pls uncle will give us break, idan dai akan Jalal zaka mana faɗa you can keep on doing it but bazamu taɓa rabuwa dashi ba he's our childhood friend a brother from another mother....."Enough Labiiiib! Daddƴnsa ya daka masa tsawa, kafin yaci gaba da faɗin " Ma ucle ɗin naka kake faɗun magana haka, be careful kana jina, Labib yana wani hure huren hanci yake watsa wa uncle ɗin nasa mugun kallo, Barr Munir ya sako baki da faɗin"  Ni kawai a kori ysron da mahaifiyarsa kowa ya huta. Wata harara Labib ya watsa masa kafin yace" Malam ka mana shiru dalla this is family issue who invited you..." Salim ya caƙumo wuyar Labib yana huci yake faɗin " First kayi rashin kunya  wa Dad ɗin second kanayi wa Uncle ɗina, Brothern mahaifiyata how dare you Labib.... Saida aka shiga tsakanin Labib da Salim don kaɗan ya rage basu kaure da faɗa ba.
    " Alhj Kasim ya goge zufar data keto masa dukda ac dake busawa a parlorn, iyayensu matan su suka lallashesu kafin suk sanar ɗasu maƙasudin haɗuwarsu.
   "Take annuri ya cika fuskat Salim tuni ya mance wani baƙin ciki ya soma farin ciki, Yayinda zuciyar Labib taci gaɓa da tafarfasa, a cikin  ransa yake furta " _no way it can't be happening, Kausar is mine not yours Salim Dasuki_
  "ƙarasawa yayi ya ɗan daki kafaɗan Salim yayi con granulating nasa kafin ya fice cikin sauri.zuciyarsa naci gaba da tafarfasa

*****************************

    "Mai anguwa yaci gaba da faɗin' ni mai anguwa ni na karɓi baikon Zubaidah kina jina ya ƙarashe maganar yana duban Hadiza data sadda kai a gabansa ta cika tayi fam. Ƙiris ya rage bata fashe ba.
   "Hamma Habibu kuwa sai wsge baki yake kaman gonar audiga yanai wa mai anguwa godiya, banda hararsa babu abinda Hadiza keyi tanai masa kallon zaka shigi hannu ne. Mai anguwa yaci gaba da faɗin ya ysai da aure nan da wata mai kamawa kowa yaje yaci gaba da shirye shiryensa, kuma uffan Hadiza tayiwa Zubaidah za'a mata hukunci mai tsanani koma ya miƙa case ɗin gaban sarki, daga nan ya sallami Hadiza da Habibu suka wuce.
   "Malam Tanko da mlam Habu sukayi godiya sukayiwa mai unguwa suka ɗan tattauna kafin ya sallalmesu.


   "Tsakanin Ummaru da Inna an rasa wayafi farin ciki, tuni ya ficr ganin masoyiyarsa, mai shirin kasancewa amaryarsa......




Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:08] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                           06


*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


    "Zubaidah zaune bakin murhu tana kan hura wutan girki, ko kaɗan yau bata jin zafin duk tulin aikin da zatayi, snn ko kusa masifan Yaya Hadiza bai ɗaga mata hankali ba, jinta take tamkar sallah, muddin zata bar wann kurkukun dole taji farin ciki a zuciyarta, uwa uba zata ci gaba da karatunta saidai zatayi kewan Kamalu da Hammanta.
  "Wani yaro ne yayi sallama snn yace wai ana sallama da Zubaidah...... "Wulli wulli tai da idanu tana kallon yaya Hadiza dake zaune bakin ƙofar ɗaki ta cika tayi fam ƙiris ya rage ta fashe.
  "Meye kike mun kallon ƙurilla mayya jarababbiya, ai shikenan hankalinki ya kwanta za'a maki auren abinda kike so, ƙaramar karuwa kodayake ba laifinki bane kin riga kin san namiji tun a gantalinki na karuwanci......."ƙwalla suks ciko idanunta kanta na sunkuye a ƙasa, wann mummunar kalma na karuwanci da Hadiza ke jifarta dashi sosai yake ɗaga mata hankali.... Bata gama tunanin da take ba sai ji tayi yaya Hadiza ta janyo wuyarta ta jefata bakin ƙyaure tana faɗin "Wuce kije shegiya mayya kafin ki cinyeni, maza kije yaci gaba da mammatse a lungu yanda ya saba...."
  " Ko ɗan kwalliya da ƴammata keyi idan zasu wajen saurayi Hadiza bata bar Zubaidah tayi ba, haka nan yanda ta tashi daga bakin murhu da warin hayaƙin da komai ta turata waje....

   "Daga can bakin bishiyar da yake tsaye ya hangeta tana goge hawayen da ya jiƙa mata fuska.. Cikin sauri Umar ya ƙaraso yanda take, tuni ta soma matsawa da baya don bata so yaji ƙaurin hayaƙin da take, gashi shi yayi tsaf ya sha gayu abinsa irin na samari daidai da ajinsa.
   " Harɗe hannaye yayi a ƙirjinsa yana kallonta, tausayinta da ƙaunarta na daɗa ratsa ɓargo da tsokarsa,.. Saida ya bari ta gama ƴan goge gogen hawayen kafin ya ɗanyi gyaran murya cikin tattausar murya ya soma faɗi" Zuɓaidah, shiru bata amsa ba har lokacin kanta na kallon ƙasa, kafe ta idanu yayi kafin ya kuma kiran sunan nata, sai snn ta ɗago koɗaɗɗun idanunta ta mar duba guda, Umar yanada ƙwarjini ta yanda duk budurwar da tayi ido huɗu dashi sai ta tsinci kanta da faɗuwar gaba, gashi a yau yafi kullum mata kyau, shi ba fari bane snn ba baƙi can bane, kallo guda zaka masa ka gane asalin bafulatani ne haɗi da kwantattun sumanss da sajensa  da suks ƙara masa kyau da ƙwarjini...."Muryarsa ya katseta sanda yayi mata nuni da wani kututturen dabino yace" Mu karasa ki zauna, babu musu tabi umarninsa......" Har sun soma tafiya suka jiyo muryar Hadiza ashe tana laɓe jikin ƙyaure tana saurarensu nan ta soma faɗin "Ku ƙarasa ina, kai wani irin jarabebbe ne, baka jira akai maka ita ba sai kazo har ƙofar gidansu kana matseta, auho ashema kun saba kinji kunya Zubaidah tuna kika zaɓi zama karuwa, toh ni dai kar ki kawo min abin kunya kafin wata gudan da aka ɗiba maku ya cika taƙarashe maganar tana watsa masu mugun kallo.
   "Umar yabits da kallon mamaki, ƙarasowa gabanta yayi yanda take tsaye kafin yace" Dillaliya kike ko wa? Galala take dubansa cike da mamaki kodashike tasan Ummaru da wann taurin ran nasa zaiyi fin haka, muryarsa ya katse mata tunaninta yanda yaci gaba da faɗin" Yau ta kasance rana ta ƙarshe da zaki saka masoyita kuka, don wllhi kinji na rantse kika kuma kiranta karuwa kotu zan maka ki sai munyi shari'a daga nan har birnin tarayya, kuma da kike cewa ni jarabebbe, naji na yarda idan dai akan Zubaidah ne sai nafi jaraba ma naci, don nasan bazan taɓa ƙosawa da ita ba, ki kalleta da kyau mana, ke ai kina ganinta kinga mace ba irinki ba, nasan hassada ce tsan tsa kike da ita ba wani abu, yayi wata murmushi mai cike da nishaɗi da gargaɗi kafin yace" This should be the last warning idan kunne yaji toh fah jiki ya tsira, daga haka ya dubi Zubaidah da ƙiris ya rage bata saki fitsari a jikinta ba don tsoro kana yace" Amaryata lets go, dont mind this witch, don yasan Hadiza dai ba turanci take ji ba......"Kallon Yays Hadiza tayi alamun tana jiran umarninta" Haba tuni ta soma bambami tana kunfan baki, yo har ni za'a yi ma turanci, ke Zubaida har kinyi kaurin da zaki biyewa saurayi inji ni nayi ɗawainiyar karatun naki, har shine zaki zaɓi saurayi akaina ya zageni da kalman turanci kina tsaye kina biyesa yayi maki kyau, idan dai namiji ne kije gaki gashi ..... Daga haka tasa kai ta wuce cikin gida fuu zuciyarta naci gaba da tafarfasa....

    "Juyowa tayi tana duban Umar, murmushi ya sakar mata kafin suka ƙarasa suka zauna.
  "cikin tattausar muryarta ta gaidashi, ya amsa yana wani kasheta da mayen kallo, ita kiwa duk kunyarsa ya rufeta musamman cewa da yayi, idan dai akanta ne sai yafi jaraba naci, wann kalmomi sun matuƙar mata nauyi, kaman yasan hakan kuwa nan yasa hannu ya karɓi ɗan karan da take wasa dashi aiko nan ta ɗago ido suka kalli juna, tai saurin sadda nata idon,
   "Zubaidah, ki sani ina sonki ina ƙaunarki sann zanyi komai a sabida ke, nasan kalan rayuwar da kike da wann matar, daga rana mai kaman ta yau ki sani bazan sake barinta taci zarafinki ba.
  "Ɗan murmusawa tayi kafin tace" Na gode, cikin muryarta mai daɗin saurare, kaman waccd aka zabura ta miƙe tsaye, ɗan dubanta yayi kafin yace" Yaya dai ko har mun gama hiran ne, ɗan girgiza kai tai kanta na ƙasa kafin tace" A'a gani nayi kaman ƙaurin dake jikina ya dameka.
  "Tsuke fuska yayi ya kira sunanta da dakakkiyar murya, ɗago ki kalleni Zubaidah, ta ɗago tana dubansa, Umar yaci gaba da fadin" Nida ke mun zama ɗaya, bana jin ƙauri ajikinki, akasin haka nike ji, ma'ana ƙamshi nake ji, kasancewa taredake yafiye mun komai ina sonki a duk yanda kike. Murmushi tayi harda ɗan rufe fuska alamun taji kunya,.. Dariya ya ɗanyi mai bayyanar da hƙwara kafin yaxe" Oya faɗa mun kina sona... Ware idanu tayi alamun  bazata iya ba, Umar yayi murmushi kafin yace" Surbajo na nasan kinayi koh... Kasa cewa komai tayi sai murmushi.... Hira sosai suka sha a wann rana kamsr karsu rabu da juna, basu taɓa hira irin haka ba, kullum saidai su haɗu a bakin rafi taje ɗibo ruws ko kuma ta kai saniyar yaya Hadiza kiwo.

*********************

   " Salim ne tafe waya manne a kunnensa yayinda hannunsa ɗaya ke riƙe da coffee cup, "What com'on Tariq pls ka shirya yanzu yanzu, we will fetched you up sai mu wuce airport ɗin... Yeah right , see you soon. Yayi hanging up kafin ya tura ƙofar ɗakin da hannu guda.
   "Cak ya tsaya yana kallon Labib dake baccinsa hankali kwance. Kan gadon ya ƙarasa ya ɗauki pillow ya shiga dukan Labib dashi yana faɗin" Will you get your lazy ass out of bed,...
   "Labib, yayi miƙa gamida cusa kansa cikin bedcover yana faɗin" Shitt, pls mana Salim, kasan ba'a tashina a bacci i'll fall sick.
  "Salim ya shiga yaye blancket ɗin yana faɗin whatever, You know we cant miss this flight, tun jiya Daddy ya mana bucking flight ɗin Gombe mukayi missing still yauma muyi missing what will u expect, they'll get mad ai.
  "Gajeren tsaki Labib yayi kafin yace" Does it really has to be now, " Labib ya miƙe yana wangale labulayen tapƙa tapkan windunan ɗakin kafin yace" The flight is 10am and yet is almost 30mins pass 9.. Tsaki Labib ya kumayi babu salati yake hamma kafin yace" waima ina private jet ɗin Dasuki Holdings ne ba sai mu tafi dashi ba, Salim yace gaba ɗaya Jets ukun suna da prob, Daddy yace zaiyi firing masu maintenance ɗinsu, kaga idan mukayi missing wann flight ɗin tofa saidai mu tafi Gombe by road, kai ina I cnat afford to miss this flight ma, i'm dying ti see my Kausar,.. "Galala Labib ke kallonsa kafin yace" Waye ma kake tunanin zaiyi tafiya mai nisa haka by road, haba ba dai ni Labib Dasuki ba.
  "Salim yayi dariya kafin yace" Freaking Dude sai ka tashi ka shirya ai na masu Tariq da Jalal magana suna shiryaw Ya ƙarashe maganar yana jifan Labib da towel.
   Ba don yaso ba ya miƙe ya nufi bathroom..



   "Gaba ɗaya Annah bataso tafiyar Jalal Dukku ba, don tun yana ƙarami data taho dashi Abuja basu kuma leƙawa ba, tana tunanin abinda ka iya zuwa yazo, kar wata rana daɗeɗɗiyar sirrinta data ɓoye masa ya bayyana. Haka tai kusan kwana zullimi......




*Gombe, Dukku*

_Toh fah readers gasu Jalal, Labib, Salim, da kuma Tariq a garin Dukku, shin me zai faru. Shin me Annah take ɓoyewa Jalal tsawon rayuwarsa. Ku biyo Sameena don jin yanda zata kasance_


Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:09] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                         07

*©Sameena Aleeyou.... ✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_

   "Drivers ɗin da suka ɗibo su daga airport suka soma paka luxurious cars ɗin a farfajiyan tangamemen gidan wanda yasha tsari da kayan alatu, idan ka shiga gidan sai ka ranste ba'a Dukku kake ba.
   "Kai ysaye cikin gidan suka nufa yayinda gurds suka shiga firfito da luggage ɗinsu.


   "Iyayen nasu ne zaune a babban parlorn, ciki harda iyayen Tariq.
   "Tun daga nesa Alhj Kasim ya haɗe giran sama da ƙasa sakamakon abinda ya gani, wayo wann tsinannen mayen yaron saida ya biyosu...... Ko saurarensu baiyi ba sanda iyayayen keta faman hugging yaran suna masu sannu da zuwa, rai ɓace ko kulasu baiyi ba yayi ficewarsa, Labib ya rakasa da harara har ya fice. Cikin sauri Barr.Munir ya miƙe yabi bayan uban gidan nasa.


   "Da yamma lis hadari ne sosai a garin already dama an idda wani ruwan don haka garin yayi sanyi weather yayi dadɗi. Samarukan guda huɗu suka shirya cikin ƙanan kaya kafin suka shige motarsu mai buɗeɗɗen sama don zagaya gari.
  


    "Mutumina na maka murna fah ka kusa zama ango, cewar Balele dake zaune saman mota a bakin tasha, Umar yayi wani murmushin jin daɗi kafin yace insha Allah abokina, Balele ya kashe masa ido guda kafin yace" Ina tausayin yarinyar nan duk randa aka kulleta a ɗaki daga kai sai ita mutumina nasanka fah babu ɗaga ƙafa ranar..."Wata dariya Umar yayi kafin ya dubi Balele ya soma faɗin" Naji tunda nayi haƙuri ban taɓa bin ko wata mace ba, ban taɓa danne ƴar kowa ba ko ƙanwar kowa, kaga dole duk randa na sami nawa nayi budurina, babban farin cikina shine zan kasance da macen da nake so....."Balele ya busa sigarinsa a daidai fuskan Umar yana murmushi gamida jinjina kai.... Wani mugun kallo Ummaru ya watsa masa kafin yace waikai baka gajjiya da kayan maye ne? Murmushi Balele yayi kafin yace tuƙa manyan motoci ai saida kayan maye, gaskiya Ummaru ina gani ƙoƙarinka da ko karar sigari baka sha, Umar ya girgiza kai ba tareda yace komai ba ya soma ƙoƙarin miƙewa.
  "Ina kuma zaka Balele ya biɗa,
  "Bakin Rafi zanje munyi da Zubaidah zamu haɗu can, Balele ya murmusa kafin yace" Zubaidah tsokale idon samarin Dukku, gaskiya kayi sa'a da har ake ƙoƙarin maganar aurenku su Gwatse basu taɓa kai mata hari ba.
   "Umar yayu wata murmushi mai cike da ma'anoni kafin yace" Balele kasanni akan abinda nike so, wallhi duk garin nan babu wanda ya isa ya taƙura Zubaidah muddin ina numfashi matar yayanta ma data tashi gabanta ban ragar mata idan dai akan sanyin idaniyana Zubaidah ne balle wasu ƙananun tsageru su Gwaste, wani murmushin ya kuma kafin yace "Shege ka fasa gasu ga ita......"Balele ya bushe da dariya kafin yace" Kai mutumina daɗina da kai akwai zuciya.... "Ba tareda ya kallesa ba yace" Kaga ni zan wuce idan Oga Kabiru ya iso ka basa uzurina dan Allah.
   "Aff ai yau bazamuga Oga KB ba cewar Balele.
   "Umar ya jiyo gamida mada kallon meyasa.
   "Bakada labarin zuwansu Alhj Dasuki da ƙaninsa da kuma Alhj Tahir Marafa na unguwar dutse, mai neman tsayawa takaran shugaban ƙasa..... "Ɗaga kafaɗu Umar yayu kafin yace" Toh ni ina ruwana da zuwansu, Balele ya sake baki yana kallonsa kafin yace" Toh bikin saka ranar auren ƴaƴansu za'ayi jibi jibin nan kuma ƙofa a buɗe take ga dukk mai niyan zuwa kasan dai yanda suke neman muƙamin nan dile suja talakawa jiki. Na tabbata Oga yana can ana yana neman ganin Su.
   "Gajerwn tsaki Ummaru yayi kafin ya miƙe gamida ɗaukat hankacip ɗinsa da yake riƙe kan starry dashi idan zai tuƙi musamman mai nisa kafin ya wuce ya bar Balele a nan zaune yana shaƙan kayan mayensa, Balele na masa sallama ko kulasa baiyi ba don baiso ya bar masoyiyarsa tayita jira.


    "Wow.... This is so woow I just cant believe it yau gani a mother land ɗina, infact motherland ɗinmu dukanmu cewar Salim dake kwance bayar convertible ɗin shida Tariq yayinda Jalal ke driving  Labib ke zaune mazaunin me zamar banza.
    "Salim yaci gaba da faɗin" Guys mu ɗan bi ta gefen can rafin I knw it will be awesome....."Gajeren tsaki Labib yayu sanda Jalal ya karyi kwanan rafin da gudun gaske..... Ihu Tariq da Salim sukayi suna shewa alamun suna cikin farin ciki yayinda Jalal ke tayasu....."Will shut up for heavens sake, haba... Cewar Labib da gaba ɗaya ransa a jagule yake sabida gani yake shikenan bazai samu Kausar ba ta kufce masa.
   "Guy chill up muna celebrating ne, cewar Salim. Tsaki Labib ya kumayi kafin yace" What's even awesome in this place, this place is sucks dont you see it. Ever since I came to this town nake fama da rashes a jikina for heavens sake i dont even knw who the heck came with the idea a zo nan garin ayi engagement..... Ni idande a nan garin za'ayi ɗaurin aurenka believe me I wont attend your wedding don wllhi na gama zuwa garin nan.
   "Tariq yace" Guy chill pills we wunt stay long here, besides nan shine mahaifarku...."Ɗan tsaki Labib yayi kafin yace" Meyasa tuntuni basa zuwa garin sai yanzu sabida suna neman wani abi a wajen ƴan garin sabida a nuna a Network labarun tara cewa Alhj Tahir Marafah yazo garinsu yayi engagement ɗin tilon ƴarsa, people will be thinking sabida Allah yayi hakan amma mu munsan sabida buƙatarsa yayi don yaci takaran shugaban ƙasa....."Enougj of this Labib, Salim ya dakatar dashi kafin yaci gaba da faɗin" Inlawn nawa kake faɗin horrible things akansa you need to watch your mouth buddy.
  "Murmushi Labib yagi a daƙile kafin yace" And who cared if he's your inlaw, gaskiya ne dole a faɗe ta, nasan Uncle shi ya ya basa wann shawaran don nasan Alhj Tahir is a responsible mutum bai iya ƙaryar ƴan siyasa ba....." Kan yayi shiru saiji yayi Salim ya cakumu wuyarsa yana faɗin" How dare you say those things to my very own father,..... Kan kace me faɗa na ƙoƙarin kufcewa ysakanin Labib da Salim..... Sai sn Jalal da tun fara cecekucensu bai tofah uffan ba dama sun san miskilancinsa sun san bazai ce dasu komai ba don ya saba, burki yaja ya tsaya tsakiyan hanya ƙiiiiiiiiiiiiiiittttttttt" Gaba ɗaya saida suka jirkita. Juyows yayi yana watsa masu kallo kafin yace" Let me know if u done... Daga haka bai kuma cewa komai ba. Tariq ya fuzar da iska kafin yace" Guys pls lets not ruin our day, besides bai kamata kuna haka ba, this is childishness you're all matured enough, snn abinda gayika Labib shi yayi Salim, we are all here because of you guys, what will you expect us to feel idan kuna abu makamancin wann a gabanmu nida Jalal, ku tuna  we arr all friends and we love each other like brothers, pls lets not ruin this special moment especially you Salim this part of your wedding the beginning of your happiness lts chirrr it pls.
    "Murmushi Salim yayi kafin yace" Yeah Buddy you right i shoudnt hve done that, ya kalle Labib kafin yace I knw why my cousin is acting this way sabida nan babu ƴan matansa i'm right.... "Sai snn sukayi murmushi su duka gaba ɗaya harda Labib ɗin ya ɗan daki kfaɗun Salim yace" Sorry Bro for been mean to you...." Its okay Buddy Salim ya faɗi da murmushi saman fuskarsa. Sai snn Jalal yaci gaba da Driving.



     "Tsaye take bakin rafi saniyarta tana shan ruwa yayinda ita kuma Zubaidar keta faman tsane rigarta da ya jiƙe shaƙaf da ruwa sakamakon ruwan da aka tsulala, tafiya mai ɗan nisa ne daga wajen rafin zuwa cikin gari shiyasa har ƴanzu Umar bai zo ba, so take ta tafi amma tana tunanin kar ta tafi yazo bai sameta ba ransa ya ɓaci, don ita kanta tsoron ɓacin ransa take sabida zuciya da yake dashi, don haka dole ba don taso ba taci gaba da tsane kayan duk ya kakkame jikinta shape ɗinta ya fito sosai.


    "Gama parking ɗinsa keda wuya idanunsa suka sauƙa kanta, baiga fuskarta ba sai bayanta, shi tunda Allah ya haliccess zaice bai taɓa ganin mace mai kyawun sura irin ta wnn yarinya ba, haka kurum yaji ya ƙagu ta juyo yaga fuskarta, Su Labib daketa faman selfie basu ko lura dashi ba, Saida Salim ya taɓosa kafin suka hangi abinda ya hango, sai faman tsane rigarta take ko kaɗan batasan akwai wasu halittu a wajen ba bayan ita da saniyarta......" *God have Mercy* Cewar Labib cikin sandarewar murya yayinda su Salim da Tariq suka kasa furta koda kalma guda,.. Haka kurum Jalal yaji baison kallonta dasuke, dukda shi tantirin ɗan iska ne wajen hulɗa da mata amma ko kaɗan yau ji yayi bai son su kalle wann yarinya da har lokacin bai ga fuskarta ba......





Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:09] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                        08

*©Sameena Aleeyou....✍🏾

_Queen Samy Novels Forum.... 📖📚_


     "Cikin sauri Jalal ya tada motan ganin abokan nasa basu da niyyan daina kallon budurwan nan, jin ƙaran mota yasata juyowa babu shiri cike da firgici da tsoro...."
   "Gaba ɗaya suka bi kyakkyawan fuskarta da kallo, Zubaidah ta razana matuƙa da ganin irin waɗan nan samari,  bata taɓa ganin mota irin tasu ba snn yanayinsu yasha banban da samarukan garinsu, sunfi kama da taurarin cikin shirin wasan kwaikwayo wato film.... Cike da tsoro da firgici ta shiga tare jikinta da hannayenta....." Kaman wanda aka tsinkara haka Jalal yaja motar da ƙarfin gaske suka bar wajen, gaba ɗaya sai chaaa suka masa meyasa zai masu haka, meyasa bai bari sunyiwa yarinyar chan magana ba.. Salim ya murmusa a fili yace *"Cow Girl"*  She's very beautiful I've never seen a beautiful girl like her before my whole life, cewar Tariq... Labib kuwa cewa yayi " I already have that imagination me and her on my bed making love together...... " Bai gama rufe baki ba Jalal yaja wata shegiyar burki a tsakiyar titi, sa'an su ɗaya babu mota a bayansu dan kuwa shakka babu da sun bigi juna.
   "Mugun kallo Jalal ke watsa masu yayinda suma suka bisa da kallon mamaki, yana huci yake faɗin"
  " Dont mess with her, I perfectly well know you guys, dont you dare hurt her....."Dariya Labib ya kwashe dashi kafin yace" Man nasan fah duk cikinmu nan babu wanda ya kaika son morewa da mace so I believe kaima da zaka samu mace kamar wancan yarinyar ta ringa ɗebe maka kewa I'm sure da garin nan yafi maka daɗi.....Salim yayi saurin cewa " Wait why you do you even care? Naga baka taɓa yin irin haka ba koda ƴammatan ka muka nema.
   "Jalal ya ɗago ido yana dibansu one by one kafin yaci gaba da faɗin" Salim you are getting married soon ya juyo ya dubi Labib da Tariq kafin yace ku kuma I'm quite sure babu me sonta tsakani da Allah cikinku....." Bai ida ba Labib ya tuntsure da wata dariya kafin yace" For Gods sake Jalal ya kake haɗamu da wann low class chick ɗin kiwo fa take could you even imaging. Com'on Dude a bar wann zancen dukanmu dai muna son jikinta ƙuma kaima nasan kana so...." Wani mugun kallo Jalal ya watsa masa kafin yace" Kaima kasan duk neman matana bana neman yara kaman wann yarinyar don bazan taɓa lalata rayuwar ƴar kowa ba, duk ƴammatan da nake hulɗa dasu kasan matured babes ne daga waɗan da suka girmeni ne sai sa'anni na I see no reason da zai sa na lalata rayuwar ƙaramar yarinya wanda kamata yayi ace tana school kaman wann yarinyar. Nidai na faɗa maku dont mess with that girl, daga haka ya fincike mota suka ci gaba da tafiya.


    "Har lokacin jikinta rawa yake don tana tuno sautinsu sanda suke faɗin " Hi chick, you beaitiful kasancewar tayi karatu har zuwa aji uku na matakin sakandare yasa ta gane wasu dga cikin kalmomin da suke faɗi da harshen turanci, haka kurum taji ta tsnesu ko kaɗan bata taɓa ganin mutanen da ta tsana irinsu ba dukda kyawun hallita da suke dashi... Babu shiri ta kaɗa saniyarta ta soma tafiya don gani take kaman zasu dawo.
   "A daidai bakin kwalta ta haɗu da Ummaru, ganin yanayinta yasa shi ɗan razana, don gaba ɗaya a figice take.
   " Surbajo na yaya dai lafiya ya tambaya yana ƙoƙarin kota maya saniyar, ɗan langaɓe kai tayi cike da yarinta take faɗin" Ba kaine kaƙi zuwa ba gashi ruwa ya min duka.
   "Ɗan murmushi Ummaru yayi dama yasan hakan ka iya kasancewa. Haƙuri ya soma bata yana lallashinta har ta haƙura kafin ya sako zancen tafoyar da zaiyi nan da kwana biyu.
   "Take idanun Zubaidah suka yi raurau, ƙwalla ya ciko idanunta, kaman me shirin kuka take faɗin" Yanzu shikenan tafiya zakayi ka barni...." Nan da nan yaji babu daɗi rausayinta ya cikasa, sandar hannunta ya karɓa kafin yace" Zubaidah ɗago ki kalleni, da ƙyar ta iya ɗagowa tana dubansa, Ummaru yaci gaba da faɗin" Ba jimawa zanyi ba sayi guda kacal zanyi, Shanu zamu kao chan jihar Lagos, na maki alƙawarin bazan wuce sati gudan nan ba. "Turi baki ta kumayi cikin harshenta na fullanci take faɗin" Nide da ka bar wann tofiya mu zauna kawai abinmu. "Umar yayi murmushi yana jin daɗin zance da ita yarintarta da ƙuriciyarta na birgesa, "
   "Kinga kuɗin aurenmu zanje nemowa, ko bakiso ayi auren ne....."Tuni tasa tafin hannunta ta rufe fuskarta dashi alamun kunya, mirmushi kawai yayi kana suka ci gaba da tafiyansu suna hiransu gwanin ban sha'awa..



 ***************************
   "Hankalin Annah ya gaza kwanciya, haka kurum take jin mummunar faɗuwan gaba, tana jin gwara ta kasance da Jalal ɗinta don kuwa ziciyarta tana raya mata mummunan tunani sarara, tasan tabbas taje Dukku da yawa daga danginta zasu gujeta, don haka bazata je wajensu ba ko taje, toh wajen wa zataje ta tambayi kanta, take tunanin ƙawarta Inna Wuro ya faɗo mata hakan kuwa za'ayi don tabbas su Lado sukayi ido huɗu da Jalal zasu iya ganesa kuma zasu faɗa masa komai.. Babu shiri Annah ta hau shiri ta nufi Dukku.


   "Yaya Hadiza ce zaune saman tabarma sai karyan loman tuwo take tana jefawa baki kaman bata taɓa cin abinci ba, dama wann ɗabi'arta ce idan tana cin abinci kai kace wani zai wabce ne, jin sallamar aminiyarta Iyalle yasata saurin wurga kwanon tuwon bayan ƙyaure, nan ta shiga shage miyar kukan jikin rigarga kafin ta amsa sallaman Iyalle, tsegege Iyalle ke kallonta kafin ta taɓe baki tace" Meye kike ɓoye mun.
  "Hadiza ta haɗe gira tace ban gane ba, kaman yaya me zan ɓoge maki, abinci na ida ci yanzun nan.....
   "Taɓe baki Iyalle tayi kafin tace" Umhm ƙawata kenan sekace bansanki ba, keni ba wann ba labari nazo maki dashi na arziki da ɗumi ɗuminta. Tuni Hadiza ta kaɗe bujenta ta gyara zama, ina saurarenki.
   " Iyalle ta zauna da ƙyar kafin ta ciro gudan ƴan dubu dubu cikin pose ɗinta ta goga su idanun Hadiza......
     " Aiko baki sake Hadiza ke faɗin" Ƙawata ina kikayi babban kamu haka, " Iyalle ta murmusa kafin tace" umhm toh ki zauna a nan ke anayi banda ke.
    "Ban gane anayi vanda ni ba, cewar Hadiza,
   " Iyalle ta gyara zama kafin tace" Albishirinki idan kinson waɗan nan bugun habujan kema kina iya samu.
    "Hadiza anji zancen arziki tuni ta miƙe ƙafafu tana faɗin ƙawata ina daurafenki wazaiƙi masu gidan rana ai sede bai samu ba.
    " Iyalle ta mutmusa kafin tace" Ai kindaiji labarin zuwan su Alhj Dasuki da Alhj Marafa me neman kujeran shugaban ƙasa,.... Hadiza ta gyaɗa kai da sauri kafin tace" Ai ancema layin anguwan ba'abi duk sojojine a wajen suke tsaro. Wai idan muyum yabi wajen ke ko ƙwaronr yabi wajen sai an harbe sa
    " Iyalle tace" Toh barikiji na faɗa maki sojoji dai suna tsaron anguwar amma basu hana mutane zuwa ba, ke yau na taƙaice maki ƙofar gidan tamkar kasuwa , a nan aka raba mana dubu biyar biyar duk wanda yaje babu babba babu yaro, inaga dai da ingin buga kuɗi ma suka taho don kuɗin baya ƙarewa.
   " Haba idanun Hadiza sukayi wulli wulli taji kuɗi tuni ta wawuro ƙafar silipers ɗinta tana faɗin " Ƙawata tashi ki rakani, ... " Iyalle ta sheƙe da dariya kafin ta jawo Hadiza ta zaunar kana tace" Ƙawata ai kin makara na yau kam an gama. Hadiza rai ɓace take faɗin amma ƙawata baki kyauta min ba, ai aminta batace haka ba, ni duk yanda naga kaya mai kyau kafin wata dilalliya a garin nan ta sani sai na sanar dake ...."
     " Iyalle tayi dariya kafin tace" Nima yau na sani da ƙyar su Dije suka yarda suka tafi dani kinsan suke aiki  a gidan, toh a daƙilin haka na samu, sann da naji sunce suna neman ƙarin ma'aikata sabida hidiman da zasuyi na bikin ƴaƴansu nace bara na sanar dake kema ki samu, kinga sai ki tafi da wnn aljanar ƙanwar mijin taki tunda naga ta iya kala kalan abinci ko yaya kikace.
    " Hadiza harza buga tsalle don murna kafin tace" Kai gaskiga ƙawata kin burge, kin kyauta min, aiko dolenta ma taje kinga nayi riba biyu ga kuɗinta ga nawa...... Dariya sukayi gamida tafe hannaye suka ci gaba da hiransu, kafin Iyalle ta tafi akan sai sun Haɗu.......




    " Momyn Salim ce keta faman kaikomo yayinda ma'aikata suke take mata baya sai nuna yanda take so wajen da za'ayi event ɗin tsarin ya kasance, mussaman suka taho da masu tsara wajen daga Abuja, Annah ta dubi momy tace" Hajiya idan babu wani aikin zan wuce masauƙi. Momy ta murmusa kafin tace" Haba Annah ai gwara ki zauna a nan, ni banyi zaton jikin naki zai sakeki ki samu zuwa ba, snn wann biki fah na Salim ne kinga kuwa ai yakamata a soma komai dake.
   " Annah ta murmusa kafin tace toh shikenan Hajiya yanda kikace.



     "Isowan su Zubaidah kenan cikin kataparen gidan, daga ita har Yaya Hadiza kallo suka bi gidan dashi ko a mafarki basu taɓa shigowa gida irinsa ba, nan da nan Iyalle ta gabatar dasu ma Dije, Dije sai wani yauƙi take tana masu tambayoyin ƙaƙa uwaka ta haifeka irin ta smi matsayin nan, da ƙyar da roƙo dai ta yarda ta amince ta kaisu gaban momy a matsayin extra ma'aikata da aka ɗauka. Daga nan kitchen suka wuce suka soma aiki babu kama ƙafan yaro.



Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:09] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                           09

*©Sameena Aleeyou....✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


     "Balele nifa kaga irin abinda bana so muzo muna ƙoƙarin kutsawa da ƙyar ɓa don Zubaidah na wajen nan ba wlhi babu abinda zai kawo ni, Cewar Umar dake tsaye gefen Balele suna ƙoƙarin kutsawa cikin gidan da ƙyar.
    "Ko saurarensa Balele beyi ba sai fizgo hannunsa da ya samu yayi suka shige daga kansu kuwa aka kulle gate.

    "Can gefe suka samu suka zauna sai kalle kalle suke irin ƙyale kyalen dake a wann gida, darene amma tamkar rana sabida yanda wutan lantarki ya gewaye ko ina, mutane sai kai komo ake.


    "Momy da Mamin Labib ne tafe suna haƴewa bene yanda baƙinsu suke yayinda Zubaidah ke take masu baya hannunta ɗauke da tray, sai kalle kalle take tana mamakin dama akwai gidaje masu kyau da tsari irin wann a garinsu, kai idan aka ce zata taɓa shiga gida irin haka a rayuwarta zata musa.
   "Suna Mami ta mata umarni ta ajiye. Nan tabi umarnin Mami ta ajiye ta nufi ƙasa, nan ne fah ta ɓata a hanya, don kuwa wann girma gida dole ma mutum ya ɓata musamman irinta da bata taɓa shiga irin gidan ba.
   "Hanyar da ta miƙe dama nan tabi, sai wage waige take, gashi abinda yafi bata mamaki shine wann hanyar yayi shiru da yawa, anya nan suka biyo dasu Hajiya kuwa, haka dai taci gaba da tafiya har ta hangi stirs da sauri tayi wajen ta soma sauƙowa.....
   " Bata ankara ba saiji tayi ta bugi jikin mutum, kallon kallo suka shiga yima juna, haka kueum taji gabanta yayi mugun faduwa snn ta rasa a ina tasan wann fuska, shi kuwa Jalal kasa daina kallonta yayi, haka kurum yaji ya tsinci kansa cikin farin ciki,.... Murya na rawa ta soma basa haƙuri.
   "Dan Allah kayi haƙuri wllhi bansan da mutum bane, kayi haƙuri kaji yallaɓai kar ka sa sojojinku su harbeni......" Jalal kam dariya taso basa ganin duk yanda ta daburce, is Okay is Okay... Ya faɗi fuskarsa ɗauke da murmushi kafin yace zo ki wuce, da sauri ta raɓa ta gefensa ta nufi downstirs,
   "Har ta kusa sauƙa Jalal yace" Emm ina zakije. 
   " Cikin sauri tace dashi sashen ma'aikata. Ɗan murmushi yayi mai bayyana dimpls ɗinsa kafin yace" I think Ƴou miss the way, kallonsa tayi ba tareda tace komai ba don kyaun halittarsa na firgita ta tamjar ba mutum ba haka take dubansa musamman da yayi murmishi.
   "Ganin tayi sakare tana dubansa yasa yin wani murmushin kafin yace "muje na nuna maki, babu musu tabi bayansa, har ƙofan da zai fitar da kai BQ ya fito da ita,.... Da sauri ta nufi ƙofan ba tareda tace dashi komai ba, "Jiyo daddaɗan muryarsa tayi yana faɗin" Baki min godiya ba.
   "Ɗan juyowa tayi gamida masa godiya cikin harshen fillanci,  Shima murmushin yayi ya amsa mata cikin harshen fillanci... Jin yayi mata fillanci yasata ficewa da sauri tana ƙunshe dariyan da yazo bakinta da hannunta don kuwa da kalman tsokana ta masa godiya shima kuma da hakan ya amsa. Itakam tafi bashi balarabe ko bature kwata kwata bata kawo bafilatani bane.... Har ta isa kitchen murmushi take....
   " Wani uwar harara Hadiza ta watsa mata kafin tace" Ke murmushin me kike, snn meyasa kika jima daga kai abu kinsan aiki na jiranki. Kinje kin saki baki da hanci kina masu kallon ƙurillan da kika saba koh.
  " A'a emm dama..... bata gama faɗin abinda zata faɗa ba Hadiza ta jawota da niyan jibganta.... Sauran ma'aikata sai ƴan gulmammaki suke, Annah ce ta shigo dama itace incharge na ma'aikatan tunda ta taho, da sauri ta ƙwaci Zubaidah daga hannun Hadiza tace" Haba baiwar Allah, ko me ta maki ai bai kamata kina dukan budurwa kaman wann ba, Hadiza dai bata ce komai ba sai hararan Zubaidah da take.
   "Annah ta kalli Zubaidah gamida sakar mata murmushi kafin tace " Ɗauko karas ɗin chan kin fere min babu musu Zubaidah tayi yanda tace cike da girmamawa. Haka kurum Annah taji yarinyar ya burgeta ta shiga ranta lokaci guda...


     " Tun shigowarsa ɗakin yake murmushi ya kasa ce masu komai sai murmushi. Salim dake tsaye cikin closet ɗinsa na shiryawa ango to be, ya kalli Jalal ta jikin mirror kaɗin yace" Whats up with you Buddy, you seems very happy, Murmushi Jalal ya kumayi gamida zama tsakanin Tariq da Labib da suke kan buga PS5..... Ɗaura hannayensa yayi bisa kafaɗunsu yana duban Salim dake tsaye closet kafin yace" Guys I just saw her, I saw her......
    " Da mamaki suke kallonsa har suna haɗa baki wajen cewa" sawWho"???
     " Kaman wanda ya tuna abu, murmushi yayi ya miƙe ya nufi ƙaramin fridge ɗin dake ɗakin ya ɗauko kwalban wine ya tsiyaya a cup ya kurɓa, Labib ya dara kafin yace" Guy wacece ka gani.
   " Jalal yayi murmushi ya kuma kurɓan wine ɗin kafin yace "Never mind its just my imagination... "Dariya kawai sukayi sanda Salim ya ƙarasa shirinsa suka fito gaba ɗayansu suka nufi filin event wanda aka tsara shi kai kace a turai ne, .....
     "Isowar su Kausar kenan fili ya kacame, Salim ya shagala da kallonta don kuwa tayi kyau har ta gaji, wata arniyar silver gown ta saka kai komai nata silver ne sai ta fito tamkar wata me zuwa gasar sarauniyar kyau.
   "Idon Labib ya sauƙa kan Asmah wacce itama tasha gayunta cikin red gown tayi ɗauri irin na yayi da royal blue vail a kanta tayi kyau matuƙa, duk haɗuwan da suke bata taɓa masa kyau irin ta yau ba.
   "Taro yayi taro nan da nan aka soma gudanar da Event.


   "Zubaidah sai leƙe take ta windon kitchen tanason fita taga amaryar don taji anyi annoucing isowarta. Ta ɗan saci kallon yaya Hadiza kana tace" Yaya don Allah naje na kalli amaryar.....Wani uwar harara Hadiza ta watsa mata kafin tace" Bazakije ba don uwarki, shegiya me shegen son kallon tsiya, wann abu duk a kunnen Annah ya faru. Ɗan girgiza kai tayi dukda batasan alaƙan dake tsakanin Hadiza da Zubaidah ba ta tabbata Zubaidah tana shan wuya wajen Hadiza, ƙarasowa cikin tangamemen Kitchen ɗin Annah tayi ta dubi Zubaidah dake ɗaman leƙe ta window tace" Zubaidah kina son kallo ne.
    " Da sauri Zubaidah ta juyo ta dubi Annah gamida kallon yaya Hadiza data sakar mata harara. Annah tayi murmushi don kuwa taga irin kallon da Hadiza tayima Zubaidah..... Baki na rawa Zubaidah tace " a'a Annah ban ƙarasa haɗa waɗan nan parantan ba.
    "Annah ta murmusa kafin tace kar ki damu zo muje ki kalla, juyawa Annah tayi ta dubi Elizabeth ɗaya daga cikin ma'aikatan da suka taho dasu daga Abuja masu uniform kana tace" Elizabeth continue with the plates arrangement" Elizabeth ta amsa da Okay Ma.
   "Duk sunsha mamakin jin Annah na turanci harta Zubaidah saida tayi mamakin jin Annah tana turanci... "Hannunta Annah ta riƙe suka nufi farfajiyan gidan yanda ake gudnar da shagalin.

    "Tun fitowarsu idanun Jalal ya sauƙa kansu, yasha mamaki sosai ganin Annah tare da Zubaida riƙe da hanun juna har suna magana. Toh dama Annah tasanta ne, toh a ina tasan ta??? Kasa samo amsar tambayoyin nasa yayi.
   "Salim dake rawa da bride to be ɗinsa idanunsa suka sauƙa kan Zubaidah, kallon ta yake da mamaki, a hankali ya furta *"Cow Girl"*  me take yi a nan.???
   " Ɗan sunkuyowa yayi saitin kunnen Kausar kana yace" Sweetheart barin je wajen su Labib I'll back in some minutes.
   " Kausar ta murmusa kafin tace" No prblm Dear take ur time. Satan idon mutane yayu gamida manna mata kiss a kumatu...."Zari ido waje Kausar tayi tana dubansa, harda wani kashe mata ido guda kafin ya wuce.
    " Asmah ta taso da sauri tana dariya, a daidai saitin kunnen Kausar take faɗin " Girl I saw that, lallai wann angi naki za'a sha fama, nide kar aje ana kiran mumsy da Papy suzo su kawo.ɗauki, Hararan wasa Kausar ta watsa mata gamida riƙo hannayen Asmah suka soma yin rawan a tare.....


     "Salim yana ƙarasowa table ɗinsu ya samu zancen cow girl suke dun babu wanda yasan sunanta cikn su, as usual Jalal yana warning nasu. Caraf idanun Jalal suka haɗu dana Annah, alama ta masa da hannu kan yazo.
     "Su Salim suka dubesa suna murmushi ƙasa ƙasa suke faɗin yaje ƙila Annah tasnta ne. Zubaidah kuwa tana ganinsu a tare a haka, ta tunosu ta tuno yanda ta gansu bakin rafi, faɗuwar gaba ta tsinci kanta dashi..... Tana cikin tunanin ta jiyo nuryar Annah tana faɗin" Zubaidah barin yi magana da yarona, gyaɗa mata kai kawai Zubaidh tayi ba tare da tace komai ba, har lokacin ƙirjinta na bugawa musamman da Labib ya ɗago mata hannu tare da kashe mata ido guda.

    "Ɗan matsawa gefe Annah tayi itada Jalal tana masa magana amma idonsa da hankalinsa gaba ɗaya suna kan Zubaidah......
     " Daga yanda suke zaune can baya shida Balele ya hangeta sai faman rarraba ido take, ya kuma duban Jalal daya kafe ta da idanu, yaga sanda suka sakar wa junansu murmushi..." Take gabansa yayi mugun faɗuwa Da sauri ya miƙe ya nufi yanda take.
    " Saida ta razana da ganin Umar don batayi zaton zata gansa a nan ba.... Juyawa yayi sukayi ido huɗu da Jalal, Jalal yayi saurin kauda nasa kan gefe.
   " Fuska a tamke tana gaishesa ko amsawa baiyi ba ya soma faɗin" Wanene wancan saurayin da kike masa murmushi.
   "Ido ta zari tana dubansa kafin tayi magana a zuciye yake faɗin" Naga irin kallon da yake maki, ke bakisan yaran masu kuɗin nan ba koh, waima har yanzu aikin uwar me kike da bazaki tafi gida ba,..." Kasa cemasa komai tayi sai kallon data busa dashi, kishinsa yayi yawa bacin bata ga laifin datayi a nan ba ko ƙwara.... " Umar ya kuma hasaƙa ganin tai masa biris,...." Bata gama tunanin da take ba ta jiyo muryarsa naci gaba da faɗin" Wani gulmar ne ma ya fito dake nan keda kike aiki a kitchen, Okay dama kallon maza kikazo yi, fine kici gaba. Yayi maki kyau, ni zan wuce lagos gobe da asubahin fari. Idan kinga dama ki bar wajen nan as soon as u can. Daga haka bai kuma cewa komai ba ya wuce fuuuu, Ko sallama da Balele bai samu zarafin yi ba ya fice abinsa.



      " Labib ya dubi Salim da Tariq kafin yace guys ku kwantar da hankalinku ni nasan maganin Jalal, kan wann ƙazamar talakan yarinyar zai nemi raina mana hankali, muna buƙatan jikinta kuma dole mu samu bamu taɓa neman abu mun rasa ba so bazamu fara yau ba.
      "Jalal na isowa suka sakar ma juna murmushi, farin ciki yakeji na ganin wann yarinyar, baisan me yakr ji gameda ita ba amma tabbas yana jin wani abu.
   "Labib ya sunkuya ƙasan table ya ciro waɓi ƙwaya a aljihinsa ya tsiyayi drink a cup ya jefa a ciki. Hankalin Jalal gaba ɗaya naga neman ta ina ,ubaidah ta koma don bai ganta ba kuma. Be kawo komai a ransa ba ya karɓi drink ɗɗin ya soma sha, nan ya soma jinsa a sama, nan suma suka biyesa kaman suma a bugen suke, Salim ya miƙe ya nufi yanda Kausar da ƙawayenta suke yace mata " bara suje su ɗanyi freshing up dasu Labib, Kausar bata kawo komai ba tace dashi sai sun dawo take care. Kiss ya hura mata kan tafin hannunsa kafin ya wuce" ƴammata ƙawayenta suka ɗauki shewa, cewa suke wow Kausy tayi sa'an miji mai sonta snn romantic guy. Kausar kuwa sai jin kanta take mai sa'a a cikin mata.


   "Zubaidah kuwa sauri sauri ta nufi hanyar fita amma bata cimma Umar ba, ko kaɗan bata son fushinsa, gashi tafiya zaiyi gobe gobe kuma gari mai nisa, itakam bazata so suyi irin wann sallama ba, cikin sauri ta nufi titi tana nemansa, abinka da yarinta ko tunawa da darene batayi ba ga yanayin anguwar babu mutane sosai gini ma can ɗaiɗaiya kake hangowa.snn ko tunawa ta faɗawa Annah batayi ba. Haka Annah tayi neman duniya bata ganta wajen taron ba eata zuciya tace ƙila ta koma kitchen.


    "Haka su Labib suka ja Jalal suka nufi cikin mota dashi, suka fice.... " Zubaidah sai faman shate hawayen fuskarta take tana bin salɓalelen titin nan ƙarshe har ta ƙarasa ƙarshen layin yanda babu kwalta, nan ta soma tunanin anya ma ba ɓata tayi ba, tsoro dafirgici suka shigeta, nan take ta soma ƙwalla kiran sunan Umar tana wani sabon kuka,... Daga yanda suke suka jiyo sautin ta, tuni Labib ya karya kan mota suka nufi wajen.... Zubaidah na hango fitilan mota ta nufota ta soma ja da baya, tuni Labib yayi parking suka fito gaba ɗayansu.... Kan kace me sun gewayeta, kallonsu take tana ƙoƙarin ja da baya amma sai taga wani a bayan nata, idan rayi nan gefen sai wani ma ya tarota.... Duk wani addu'an da ya,o bakinta yinsa take, cike da tsoro da firgici cikin murya irinta me kuka take faɗin" Don Allah kar ku cutar dani, su waye ku meyasa kuke bibiyata......" Bata gama yin shiru ba taji Jalal ya rungumota cikin muryar maye yake faɗin" here she is......" Wani irin ihu Zibaidah ta sake tana mai ƙanƙame jikints, Jalal kuwa da su Labib dariya suka fashe dashi, Jalal yana dariya yana tangaɗi ya ɗora ɗan yatsansa akan bakin Zubaidah yana faɗin" Shiiiiiii, har loƙacin tana rungume cikin hannayensa, Kuka take kaman ranta zai fita, Labib ya ƙaraso gamida fizgeta hannun Jalal.......
      " Dukda ba a cikin hankalinsa take va da ƙyar Labib ya iya fincike Zubaidah daga hannunsa, cikin muryar maye yake faɗin" Don't Labib dont you date think of doing that,........" Yana faɗuwa yana tashiwa da ƙyar, su kuwa su Salim da Tariq me zasuyi banda dariya,.........
        "Ihu Zubaidah tayi sanda su duka uku suka nufota, Saalim Labib da kuma Tariq, Labib ya basu umarni dasu banƙare masa ita, hakan kuwa akayi, Jalal babu yanda ya iya ƙwayan da Labib ya basa ya hanasa taɓuƙa komi k motsi me kyau ya kasa balle ya tashi,
     

      "Allah sarki, haka tanaji tana gani tana roƙonsu tana kuka basu fasa ƙudirin da sukayi niyya akanta ba, Tariq da Salim suka banƙareta ta hanyar rirriƙe mata hannaye, Labib yasa hannu ya kama tun daga wuyar rigarta ya keta daga sama har ƙasa, gaba ɗaya ruɗewa suka yi sanda na shanunta suka bayyana wanda suke a cike manya manya a tsartsaye, tuni Labib yakai masu capka kaman tsohon haka ya ringa wasa da albarkatun ƙirjinta su Salim na tayasa ƙarshe chaa suka mata akai su duka uku kowa nason ya fara biyan buƙatansa, ta yunƙura zata tashi Labib ya kifa mata mari. Bige bige take kamar mahaukaciya ta kuma yunƙura Salim ya danneta, Labib ya jawo wani duysi ya buga mata a ƙafa, tuni ta saki ƙaran azaba, haka su Tariq da Salim suka banƙare ƙafafunta suka rabata da suturanta,.....Wani ihu mai ƙarfin gaske ta sake sanda Labib ya shigeta, gaba ɗaya ba zuwan wasa ya mata ba, tunda Zubaidh tayi wann ƙaran bata kuma sanin yanda kanta yake ba.
      "Haka Labib yayita gurzanta babu tausayi balle imani, saida yayi mai isansa kafin ya miƙe Salim ya soma, shima saida yayi iyaka yinsa kafin Tariq ma ɗora da nasa, haka sukayi ma baiwar Allah nan kaca kaca babu imani babu tausayi valle tuna mahaliccinsu 😭......


Sameena.ce👌🏾
[1/23, 22:10] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                             10

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


    " Komawa gefe sukayi suna maida numfashi, Tariq ya dubi Jalal dake kwance gefe alamun bacci yayi gaba dashi tuntuni, Dariya ya fashe dashi kafin yace" Guys lets get going kafin wani ya ganmu.
   "Salim ya busar da iska kafin yace" Ban taɓa jin mace me daɗinta ba, shes so sweet I wish I could have her everyday...." Labib ya miƙe da ƙyar yana maida belt ɗin wandonsa kafin ya nufi mota ba tareda yace komai ba, jin har ya tada mota yasasu saurin ɗauko Jalal suka saka sa cikin motan, Tariq yakai dubaɓsa ga Zubaidah wscce ke kwsnce lifeless tamkar maras numfashi kafin ya dubi abokansa yace" What about her? Are we gonna leave her here???
   "Tsaki Labib ya buga kafin yace" Dude idan zaka shiga mota mu tafi ka shiga what next, badai ka biya buƙanta ka ba me kuma yayi saura..." Tariq ya ɗanyi jimm kafin yace" Com'on guys we can leave her here lifeless she almost died...." Cike da ƙosawa Labib yace" If you cant leave fine, ka tsaya idan police suka kama ka da dead body sai ka masu bayani, kokuma Dad ɗinka ya ganka da ita kaga he'll definitely be proud of you huh??
   " Salim ne ya riƙo Tsriq suka wuce mota yana faɗin" lets go Buddy I dont think that girl is still alive.
    "Labib kuwa kaman jira yake suna shiga ya fincike motar......



   " Har aka gama event babu Zubaidah babu dalilinta , Neman duniyar nan sunyi basuga Zubaidah ba, Ƙarshe dai Hadiza ta wuce gida da tƴnanin ko Zubaidah ta koma gida..
   "Hadiza ta cika tayi fam sai banbamin masifa da bala'i take" wllhi yau Zubaiidah sai na kusan kasheki a gidan nn..." Hamma Habibu sai faman bata haƙuri yake yana faɗin" Kiyi haƙuri Hadiza zata dawo ne, Kamalu ya ƙaraso ya rungume babansa yana kuka yana faɗin shidai yana son ganin Didinsa.. Rungumesa Habibu yayi suka soma kuka a tare. Wani takaicin ya kuma tokaran Hadiza, ficewa tayi waje ta barsu sunata sharɓan kuka.


   "Mami ta kuma kallon momy datayi jugum duk suna jiran dawowan ƴaƴansu kafin tace" Anya Farha bazamu sa securities neman yaran nan ba, what if simething bad happens to them, nan ƙaramin gari ne ba kaman Abuja ba da suka saba fita suyi dare, nan babu wani wajen zuwan da har zasuyi dare a wajen, they should be home by now...."Momy ta matso ta rungume Mami kafin tace" Its Okay Mami I know they'll be home soon,.....
   "Dammit dammit those boys will never change... Cewan Alhj Kasim cike da ɓacin rai, duban Barr Munir yayi kana yace" Keep on trying their numbers, daga haka miƙewa yayi ya fice zuwa waje...


    "Su Salim kuwa basu suka shigo gidan ba saida suks tabbata kows yayi bacci, cikin sanɗa suka wuce sashensu, gaba ɗaya suka zube a parlor suna maida numfashi.
   "Kaman daga sama sukaji an banko ƙofan an shigo... Daddy ne tsaye yana binsu da mugun kallo,
  "Salim da Tariq kam tsoro ne ƙarara ya nuna a fuskarsu yayinda Labib ke binsa da mugun kallo shima.
  "Where the hell have you guys been??? Dady ya tambaya fuska babu alamun wasa,...
   "Labib ya miƙe yana ɓalle buttens ɗin rigarsa kafin yace" Uncle would ƴou pls stop, why ate you asking us like we are still kids, ya kamata ka gane mun girmafah yanzu we can decide our life.
   "Daddy ya fuzar da iska kafin yace" I see, I see. Ya sauƙe dubansa kan Salim da yayi zuru kamanai tunani kafin ysce" And where is your engagement ring. Sai snn Salim ya duba yatsan sa yaga tabbas babu zoben da Kausar ta saka masa ɗazu wajen engagement. Ɗan shafa kai yayi kafin yace" Com'on Dad I lost it. I'll by another one.
    " We must talk gobe kunaji na, cewar Dad, daga haka sa kai yayi ya fice zuciyarsa na ci gaba da tafarfasa...


  *Washe gari*

" Asubahin fari Hadiza ta fice ta nufi gidan Alhj Kasim, don izuwa lokacin itama ta soma shiga damuwa,. Hamma Habibu kam ko bacci bai sami zarafin yi ba haka ya kwana kuka, idan Kalmalu ya farka a bacci ya tayasa
   "Securities kuwa sam sunƙi barinta ta shiga gidan, sai faman bambamin masifa take...."Anna dake tsaye ta back yard ta jiyo sautin Hadiza, aje bokitin hannunta tayi da sauri ta nufi gate..
   "Hadiza na hangota ta nufota itama cikin sauri tana huci take faɗin" Wllhi kece, kece kikace tazo ki kaita ganin amarya, yun daga lokacin ban kuma ganinta ba. Annah ta riƙo hannunts kafin tace karkiyi magana haka, nida ke duk munsan tun jiya muka nemi Zubaidah wajen bikin nan, keda bakinki kikace gida ta tafi anyi haka ko ba'ayi ba. Snn naga kalan taƙura yarinyar da kikeyi, wnn kaɗai kan iya sa yarinyar ta tsere ma azabarki ƙila ta gaji da wahala da azabtar da ita da kike ne, ko gaban hukuma akaje dole ki bada wann statement ɗin... Haba nan fah Hadiza ta soma borin kunya musman dataji Annah na mata turanci,... Can kuma hawaye suka ciko idanunta ta dubi Annah tace don Allah ki taimaka min bansan yanda zan sameta ba.
   " Annah ta sauƙe ajiyan zuciya kafin tace" Kinga yanzu ƙarfe shidan safiya masu gidan nan basu tashi ba balle nakai ƙoƙon taimakona garesu, Amma yanzu abinda zamuyi mubi layin nan muna tambaya  muna nemanta wataƙila Allah zaisa mu dace. Babu musu Hadiza tabi bayanta suka bazama neman Zubaidah.


    "Har ƙarshen layin suka isa babu ita babu alamunta, gashi basu haɗu da mahaluƙi ko guda ba balle su tambaya.
    "Har zasu juya Annah taji kaman tayi tuntuɓe da mutum cikin ciyawa, aiko tana sunkayawa ta ganta kwance cikin bushesshen jini kaman an yanka dabba, gwiwoyin hannayenta da ƙafafunta gaba ɗaya ta kukkuje kai kace da kate tayi faɗa, ƙofan hancinta jini ne shima ya bushe, haka nan an ɗaure bakinta da farin ƙyalle, goshinta ma jini ya bushe alamun anji mata ciwo.....
   "Annah bata san sanda ta durƙushe a wajen ba gamida fashewa da wani irin kuka wanda hakan yaja hankalin Hadiza,... Tana isowa wajen taga abinda Annah ta gani.
    " Tsugunawa tayi a wajen dirshan, duk rashin imanin Hadiza da wulaƙanta Zubaidah da take yau saida taji tausayin Zubaidah...."Baki na rawa Hadiza ke faɗin " Fyaɗe aka mata, sun mata fyaɗe.... Wani sabon kuka ya kufce mata.
   "Annah tayi saurin saita kanta kafin ta cicciɓi Zubaidah da ƙyar, ta dubi Hadiza tace" Maza ki koma can gidan kice ni na aikoki ki kira min ɗana Jalal kinga ban fito da wayata ba,shi zai taimaka ya taho mana da ƴan sanda don nasan da ƙyar asibiti su karɓemu babu jami'an tsaro, amma yanzu barin fara kaita asibiti don ceto rayuwarta. Gyaɗa jai jawai Hadiza keyi hawaye na zuba idanunta, tana tunanin yau Habibu yaji ko yaga wann zance tabbas sai ya kusa mutuwa, cikin sauri ta juya yayinda Annah ta wuce bakin titi neman adaidaita.
   " juyawan da Hadiza zatayi taji ta taka wani abu kan ƙarfe, sunkuyawa tayi ta ɗauko abin, shakka babu zobene size ɗin hanun namiji, kuma da gani yaji kuɗi zai tsada, sakawa bakin zaninta tayi ta ƙulle kafin ta soma tafiya.....


      "A hankali ya sima buɗe idanunsa da suka masa nauyi, da ƙyar ya iya moƙewa zaune gamida dafe kansa da hannayensa guda biyu yana son tuno me ya faru a daren jiya.
   " Juyawa yayi ya kalli abokansa da suke kan sharan bacci babu sallah balle salati...."A hankali komai ya soma dawo wa Jalal....a fili ya furta *"Zubaidah"*  Kaman wanda aka zabura ya miƙe abubuwan da suka faru suka shiga dawo masa kwanyansa, ya tuno sanda ya riƙota, ya tuno shi ya fara kamata, ya tuno sanda Labib ya fizgeta daga hannunsa, ya tuna sanda Labib ya keta mata rigarta, ya tuno sanda suke wawa akanta kaman almajiri yaga abinci....." Jiri ya soma kwasan sa, Wani wawan ƙara ya sake wanda saida ya tashi duk wani mahaluƙin dake barci cikin gida.....
     *"NOOOOOOOOOOOO"*
 "Ya faɗi da ƙarfin gaske, gaba ɗaya suka miƙe babu shiri suna dubansa, Jalal ya ɗago rinannun idanunsa yana dubansu ɗaya bayan ɗaya, fuskan Labib yake kallo yana tuna sanda ya fara raba Zubaidah da mutuncinta dukda a lokacin yana ckin maye amma hakan bai hanasa ganin komai da fahimtar komai ba....  Tsalle yayu ya cikumo wuyan Labib ya shiga dukansa a ciki kaman Allah ne ya aikosa...yana faɗin" You raped her didn't you, you started it, you imbecile  how dare you...... Da ƙyar Salim da Tariq suka ƙwaci Labib. Kukan kura ya kuma ya jawo Salim da hannu guda snnTariq da hannu guda ya daki ƙofar ɗakin ta buɗe ya nufo downstirs dasu haka ya ringa jansu a ƙasa kan stirs har saida ya fito waje........ Labib ya goge jinin da ya ɓata masa hanci kafin ya biyo bayansu a guje, daidai lokacin dasu Daddy su momy suka fito.......



Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:10] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                       11

*©Sameena Aleeyou....✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


 *Shout Out to all the readers....😘😻*


      "Cikin sauri Labib ya miƙe yabi bayansu. Momy da Mami a balcony suka haɗu kowa ta fito daga ɓangaren mijinta don suma sunji ƙaran da Jalal yayi, a tare suka nufo downstirs... Curus suka tsaya suna bin Labib dake sauƙowa daga ɓangarensu wanda gaban singlet ɗinsa gaba ɗaya jini ya ɓata.... Mami ta nufesa a kiɗime tana faɗin" Baby me ya sameka, ina ja samo jini haka. Ɗan tareta da hannu Labib yayi sai sauri yake ya nufi parlor yana faɗin" Mami its nothing pls ku koma baccinku we can handle this, pls kar ku faɗawa wasu Dad...."Muryasa ya carke sanda ya jiyo muryar Dad daga waje yana falfawa Jalal ruwan ashariya da masifa, Ai Labib kaman zai kife ƙasa haka ya fice daga parlorn ya nufi waje don sauri. A tare Momy da Mami suka rufa mai baya.


    " Barr Munir ya cafe zancen da faɗin" Ai dama tsiyan ka sake wa talaka kenan, yanzu Alhj ka duba yanda yaron nan yayiwa yaran nan snn kaji yanda yake mayar maka da magana tamkar wani sa'ansa..... Shiru yayi sanda ya hangi ƙanwarsa Hajiya Farha na fitowa waje,... Ƙarasow Momy tayi taga fuskan Salim duk a daddauje alamun an lakaɗɗesa.
   "Boy who did this to you, Momy ta biɗa sanda take shafa fuskar Salim. Alhj Kasim ya dubesu itada Mami kana yace" Farha ku shige gida....." Idanun Momy ya sauƙa kan Jalal dake riƙe da sanda alamun shi ya jibga masu yara, ai a tamanin tayi kansa tana faɗin "Dama wnn shegen ne ya dakeku kuka ƙyalesa dashike ku saunaye ne....." Da sauri Dad da Barr Munir suka riƙota suka hanata ƙarasawa ga Jalal dake tsaye a wajen ko gizau baijiba da alama, banda huci babu abinda yake...
   " Barr Munir ya jiyo ya dubi Jalal kana yace" Yanzu kai Jalal abinda zakayi kenan, mutanen da suka ɗaukeka tamkar ɗan uwa shine ka rasa sharrin da zaka laƙaba masu sai na fyaɗe, toh da kasan son yarinyar kake ai ba sai ka mata fyaɗe ba da nemanta da aure kayi da yafi maka.
   "Jalal yayi murmushin takaici yana duban Barr Munir a hankali ya tako ya ƙaraso hat gabansa" Ido cikin ido suke duban juna kafin ya soma faɗin" Barrister bari kaji na faɗa maka, nafi ƙarfin na ɗaurawa su Salim sharri wllhi snn idanakwai waɗanda zan ƙulla masu sharri a wann rayuwa toh badai su Salim ba, sabida ƴan uwa na ɗaukesu inaga dukda dangantakar dake tsakaninku dasu nafika sonsu snn duk neman matan da mukeyi bazan musa maka ba a tare mukeyi snn da kake cewa son yarinyar nake shiyasa na mata fyaɗe kayi kiskure Barr sabida ni a tsarin bin mata na babu fyaɗe gasu nan ka tambayesu, snn koda zanyi fyaɗe ma bazanyiwa ƙaramar yarinya kamar Zubaidah ba, don haka Barr a matsayinka na mai hidima da kotu nasan kafini sanin hukuncin fyaɗe a ƙasar nan, kar ka dubi dangantakar ku kar ka dubi maysayin aikinka a companin iyaƴensu, ka dubi girman laifin a ƙundin tsarin mulkin ƙasa snn ka dubi girman laifin a al'adance snn ka duba a musulunce tunda nasan kai musulmi ne, ka shigar da waɗan nan azzalumai kotu ka ƙwato wa yarinya hakkinta, wnn shine kawai zai proving mana You are not a coward snn kasan aikinka snn kana hukunci da gaskiya......"Enough Barr ya daka masa tsawa kafin yaci gaba da faɗin" How dare kai har ka isa ka faɗa min abinda zanyi, wnn shi yake nuna dafinitely kai kayi raping nata....." Bai gama yin shiru ba suka jiyo muryar Salim yana faɗin"
   "Toh kai Jalal da kake ta faman zare kanka kasan dai wann laifi tate mukayi sa, dukanmu huɗu mukayi raping nata so idan ma hukunci za'a mana harda kai....."Bai gama yin shiru ba su momy suka shiga tafe hannaye suna salati, Mami ta rungumo Labib ɗinta tana faɗin" wllhi bazai taɓa sakuwa ɗana ya karashe rayuwarsa a gidan yari ba, wllhi baku aikata ba, son pls tell me you are not involve..... "Barr ya fashe da dariya kafin yace" Hajiya pls kima daina ɓata hawayenki babu wanda ya isa ya ɗauresu don mune da ƙasa, idan kana kuɗi toh fah sai abinda kaga dama zakayi. Kan wata kucakar yarinya ƴar talakawa baƙauyiya kike tunanin za'a rufe yaran nan, ai hakan ba mai yuwuwa vane.... Ya ƙarashe maganar yana wani shafa haɓarsa.
   "Jalal kuwa gyaɗa kai yayi kafin yace we shall see ya ƙarasa gabansu Labib ya dube fuskokin abokan nada  kafin yaci gaba da faɗin" Da biyu kuka bani abinda zai bugar dani, kunyi hakan ne intentionally don ku aiwatar da mummunar kudirinku akanta, toh wllhi wllhi ku sani each and every one of you must pay..... Daga haka ya nufi hanyat fita......

   "Cak yaja ya tsaya ganin mace ingarmiya wacce a tsaye ta kaisa tsaho tsaye a gabansa ga hawaye na bin ƙuncinta..... Su Dad ma gaba ɗaya suka maida dubansu ga matar. Yaya Hadiza kuwa kaman jira take tuni ta soma cire takalman ƙafafunta tana ƙoƙarin shan ɗammara take faɗin" Kune, wllhi kune ku kuka mata fyaɗe duk sau kunyi bayani...... Ta sunkuya tamkar taɓeɓɓiya tana shirin wawuran duwatsun dake a tsakiyar gidan cikin wani ruwa mai zubowa daga sama zuwa ƙasa.... "

   "Oh my Lord! Shes crazy cewa Alhj Kasim, ya dubi Barr ya ce , Barr take care of her, kar a barta ta fice kasa gurd su kamata sƴ rufeta don wann matar ta fita da wann zance shukeɓan sunanmu ya ɓaci a duniya,... Barr ya gyaɗa kai yana murmushi kafin ya nufi kiran gurds, Alhj Kasim ya dubi Jalal dake shirin fita kafin yace" Dont do anything foolish boy ir you'll live to regret it, ya dubi su Salim kana yace ku wuce muje, babu musu suka bi bayansa kana ganin su kaga sangartattatun yara wanda basu san neman komai ba sede a basu.


     "Kafin Jalal ya karasa wajen matar nan gurds sun kameta, yana da tabbacin matar nan tasan Zubaidah tunda gashi tana faɗi. Cikin sauri ya nufi gate, kai tsaye wajen da suka aiwatar da laifin ya nufa.



    "Tsugunawa yayi a wajen sanda yayi tozali da bushesshen jinin dake malale kan ciyawar, take ya ringa tuno komai, komai ya shiga dawo masa, ji yayi ya kasa jure tsayuwar da yake tuni ya tsuguna a wajen zuciyarda na masa wani irin raɗaɗi tamkar zata fito waje, tunda yake a rayuwarsa bai taɓa nadama irin ta yau ba, bai taɓa danasanin shan giya ba sai yau, bai taɓa jin ya tsana kansa irin ta yau ba, yana wajen suka rabata da mutuncin ta and he didn't do anything to pretect her against them, infact shi ya fara riƙota ma ya damƙamasu ita..... Wani ƙara ya sake gamida kama gashin kansa kamar zai cizge, yasan bazai taɓa yafewa kansa ba, yanzu ina take ina zai ganta. Take matar ɗazu ta faɗo masa, miƙewa yayi cikin sauri, jin ya taka wani abu yasa sa tsayuwa, tsugunawa yayi ya ɗauka abin yana bi da kallo, ɗan hankacif ne data saƙawa Umar me flawowi a jiki, ..
     "Jalal yabi Hankacif ɗin da kallo, a hankali ya manna hankacif ɗin a fuskarsa zuciyar sa naci gaba da zogi. Kaman wanda aka zabura ya soma tafiya....



     "Likita ya dubi Ammi a karo na biyu kafin yace" Baiwar Allah magana ta gaskiya sede fah kiyi haƙuri don babu yanda za'ayi mu karɓi wann case ɗin ba tareda hukuma ba, kinsan yanzu laifin fyaɗe ya zama ruwan dare snn an saka tsattsauran mataki akan irin wnn case ɗin, a gaskiya kije kizo da hukuma don kinga dole a saka a cikin file na asibiti kuma gwamnati ta gani ni za'a kama tunda nine da duty.
     "Ammi ta yarfe zufan da ya keto mata kafin tace" Haba likita taimako fa zakayi snn ka duba fah ka gani yarinyar nan tamkar bata numfashi don Allah ka taimaka idan yaso kar kasa case ɗinta cikin report ɗinku na yau har sai an san su waye masu laifin. Ka taimaka likita ka tuna idan ƙanwarka ce ko ɗiyarka a wan condition ɗin yaya zaka ji, nasan kai musulmi ne don Allah ka taimaka kar mu bari rayuwarta ta salwanta haka nan tunda su waɗan da sukayi laifin abinda suke so kenan, kaga hakan na nufin kaima ka goyi bayan ɓarna.
   "Jikin Dr yayi sanyi da jin kalaman Ammi, fuzar da iska yayi kafin yace" Shikenan Hajiya zan taimaka mata, Godiya Ammi ta soma masa tana hamdala, tuni Dr yasa Nurses su shigo da Zubaidah ɗakin tiyata,
    "Saida ya girgiza da ganin irin cin zarafin da akayiwa Zubaidah, tabbas wann ba don kwananta na gaba ba data tuni ta mace, Allah shi kaɗai yasan dalilinsa na barin yarinyar nan a raye, idan aka ce masa maza goma ne sukayi amfani da ita bazai musa ba, don kuwa sun mata kaca kaca, ta yanda ko dabba bazaiyi irin haka ba. A ƙalla ya samu ciwo a privaye part ɗinta sama da bakwai snn jini ya zuba sosao a jikinta. Tuni ya soma gudanar da aikinsa da taimakon nurses ɗinsa.


      " Gaba ɗaya hankalinsa a tashe yake,shi yama rasa wanne zaiyi sashen da yake tunani nan aka sauƙi  Amminsa ya nufa, yana isa ya tarar bata nan ɗaki ya shige ya kulle kansa cike da naɗamar rayuwa.





      "Hadiza sai wage baki take taji kuɗaɗen da ko a mafarki bata taɓa jin labarin irinsu ba, ta kuma duban Alhj Kasim dake hankince saman kujera kafin tace" Alhj barinyi sauri na ƙarasa asibitin kafin matar nan ta kira ƴansanda.
   "Alhj Kasim yayi murmushin cin nasara kafin ya jawo drwer ɗin dake gefensa ya ciro bandir ɗin ƴan ɗari biƴar ya miƙawa Hadiza yace, ki fars taɓa wann, hannu na rawa Hadiza ta amshe kuɗin ta shiga sunsunawa  tana wani lumshe idanu, a sittin ta miƙe ta nufi waje tana yashe baki kaman gonar audiga....








Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:11] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*


                         12


*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*In Dedication to All Victims Of Rape. Never Keep Silence, Fight for Your Right. This is Not Something To Be Ashamed Of Your Self, Let the Guilty Ones Feel Ashamed Of Them Selves..... 🙌🏾🙌🏾🙌🏾🙌🏾*


    _Wannan Shafin naku ne Barr Asmie n Zainab ina ƙaunarku yanda kuke ƙaunata da labarai na, Allah shi bar ƙauna #1Luv...😘😍_


     "Alhj Jamil ya rapka uban tagumi yana kallon yayan nasa, ɗan gyaran murya yayi kafin ya soma faɗin" Yaya kana ganin abinda muka yi munyi daidai, anya Yaya bazamu miƙa yaran nan ga hukuma ba......" Bai kai aya ba Alhj Kasim ya katse sa,...
   "Jamilu kai har sai yaushe zaka soma tunanin irin ƴan adam, akan wata yarinya ɗiyar talakawa kake magana muyi risking rayuwar yaranmu, ka faɗa mun idan muddin muka bari maganar nan ta fito media shikenan sunan mi ya ɓaci, reputation ɗinmu ya ɓaci snn wa kake so ya gaje mu idan mu muka miƙa tilon yaran mu ga hukuma snn kana tunani Alhj Tahir zai yarda ya aurawa Salim ƴarsa Kausar ne, kai ƙarewa ma duk abokan hulɗanmu na kasuwanci sai sun guje mu, our company will go bankrupt (Kampaninmu zata samu kariyan tattalin arziki) dan haka bana sonjin wani magana daga gareka.
   "Shiru Alhj Jamil kawai yayi yana duban ɗan uwan nasa wanda bashida abinda yafi masa kuɗi a rayuwarsa da kuma tilon ɗansa Salim.
   "Barr Munir yayi wata murmushi kafin yace" S gaskiya Mr President shawarinka yayi daidai yanzu sai musan yanda za'ayi da wann yaro Jalal don nasan definitely yaron ka iya kawo mana cikas tunda dai mun gama da iyaƴen yarinyar. (Alhj Kasim Dasuki shine President na *Dasuki Holdings Of Company*) 
   "Alhj Kasim ya murmusa kafin yace ku bar min wann ni nadan yanda zanyi, Ya juyo ya dubi Mami da Momy da sukayi jugum suna kallonsu kafon yace" Farha kusan yanda za'ayi Kausar da Hajiya Raliya su rigamu isa Abuja...." Momy ta sauƙe ajiyar zuciya kafin tace " Dama Haj Raliya ta faɗa mun washi garin sakun rana zasu koma gaba ɗaya harda Alhj Tahir kasan very busy mutum ne, yau idan yayi sadaka a ƙofar gidansa gobe zasu wuce.
   "Daddy ya jinjina kai amma har cikin ransa mamaki yake ya akayi Alhj Tahir bai sanar ɗashi ba, shashantar da zancen yayi dan yanzu babban ƙalubalen dake gabansa shine ya kuɓutar da ysransa. Jinjina kai yayi kafin ya dubi momy yace " Whete are the boys??   " Momy ta amsa masa da suna sama, kai tsaye stirs ya nufa Barr Munir na taka masa baya, Dad ɗin Labib kuwa ficewa waje yayi yana amsa call....


    "Suna zazzaune kowa da abinda yake saƙawa Daddy ya turo ƙofa suka shigo hida Barr Munir, Kallo ɗaya Labib ya masu ya watsar yaci gaba da ɗunduma gefen fuskarsa yanda Jalal ya ji mai ciwo.
   "Kallonsu One by one yayi kafin yace" Gobe gobe zaku bi jirgin safe ku wuce Abuja, babu wanda ya amsa sa duk cikinsu, ya dubi Tariq da har lokacin hancinsa bai daina zuban jini ba yace" Na kira Dad ɗinka nayi briefing nasa komai a waya don ya riga ya wuce Abuja yau da safen nan, kundai jini kar ku bari kuyi missing flight ɗin safiya, daga haka suka sa kai zasu fice Salim ya katse su da faɗin " Daddy what about Jalal,....." Bai gama rufe baki ba Barr Munir ya katse sa da faɗin " Kaci gidanku Salim, na maganar kuɓutar da rayuwarku kana maganan wani Jalal...." Baki Sal ya turo gaba like a spoiled kid kafin yace" But Uncle we cant leave without him, hes onr of us..... " Wata ashar Daddy ya watsa masa kafin yaci gaba da faɗin" Idan Jalal ɗin ƙanin ubanka ne sai ka jirasa ka tafi dashi, snn ku buɗe kunnuwanku da kyau kujini, babu ku babu Jalal, inace don kunga kuna rayuwa gida ɗaya ne dashi shiyasa kuke ganin kaman ku dashi ate equal ko, toh wllhi kukayi wasa koransu zanyi daga gidana daga shi har uwsrsa...Barr munir yayi saurin cews shikenn kuwa Mr Ptesident kaga kowa ya huta...
    " Labib ya miƙe yana watsa masu mugun kallo mussaman Barr Munir don ya tsane sa ba kaɗan ba, don yana ganin shi yake saka Uncle ɗinsa yin wasu abubuwan snn yaga alama ƙoƙarin raba uncle ɗinsa da ɗinsa yake. cikin dakakkiyar murya yake faɗin " Uncle Idan ka kori su Jalal a gidanka zasu dawo gidanmu. So ba matsala bane....." Cike da mamaki Daddy ke kallonsu, anya Jalal bai asirce masu yara ba, bai kuma cewa komai ba sai karya babban gyaransa da yayi ya fice fuuuu Brr ma yabi bayansa da saurin gaske...




    " Kasa zama yayi a ɗakin sabida ƙuna da ƙirjinsa ke masa, tausayin yarinyar ya saka gaba, ko runtse ido yayi sai ya tuno sanda suke rabata da mutuncinta, quiet alright ba sonta yake ba but tausayinta ya hanasa sukuni,  jinta yake tamkar ƙanwarsa ji yake da ma ƙanwarsa akayi haka tabbas da sai yanda ƙarfinsa ya ƙare, mussaman kasancewarsa shi kaɗai wajarn mahaifiyarsa, tafiya yake baima san yanda zaije ba, shi dai yasan yana bin titi, hankacif ɗinta da ya tsinta kuwa yana nan damƙe  hannunsa kaman mai tsoron kar wani ya wupce, duka lungun da Jalal yabi sai kaji ana yaba kyaun halittarsa babu mata babu maza, kar kuji nace haka, Jalal mutum ne wanda Allah yayi masa halittan kyau wanda harta ƴan uwansa maza suna yaba kyaun halittar sa.


    "Ammi tana ganin fitowsr likita daga ɗakin tiyata yana share zifa tayi saurin miƙewa ta nufesa tana tambayarsa,
   "Ɗan goge zufar goshinsa yayi kafin yace" Hajiya a gaskiya bazan ɓoye maki ba yarinyar nan ta sami mummunar rauni, sauƙin abin guda shine bata kamu da yoyon fitsari ba, amma tana tsananin buƙatar jini, yanzu abinda nake so dake kije ki nemo wani ɗan uwanta ko kuma kuɗin da za'a nemi jini a ƙara mata ....
   " Ammi ta sauƙe ajiyan zuciya kafin tace" Toh likita ko za'a auna nawa. Ɗan jimm yayi kafin yace toh bbabu matsala idan kince haka, amma koda mun auna naki yayi daidai sai kinada wadataccen jinin da zaki iya ba wa wani kafin mu ɗiba, Ammi tace ta amkce, nan aka shiga ɗakin aunin jini da ita, unfortunately jinin Ammi baiyi matching na Zubaidah.
   "Tagumi Ammi tayi tana tunanin ina Hadiza ta tafi, gashi batasan gidanta ba, bata san ina zata sameta ba, wata zuciya tace ki fita ki neme ta tunda ƴar uwarta ce ƙila a sami wanda jininsu zaizo daidai. Haka Ammi ta fice tana tunanin me ya hana Hadiza dawowa.


    "Chan tsalleken titi ta hangesa sai faman tafiya yake, shaff ta mance da Jalal ma gaba ɗaya, hankalinta ya  kaikaita  wajen ceto rayuwar Zubaidah. Da sauri ta nufesa cike da mamKi take tambayarsa ina zaije haka.
    "Ɗan  shafa kai Jalal yayi kafin yace" Kawai dai ina kallon yanayin garin ne...... Zuciyar Ammi ya buga tayi saurin riƙo hannunsa suka tsallaka titi, Jalal dai sai kallonta yake gaba ɗaya da ganin Ammin tasa tana cikin damuwa....... Murya na rawa Ammi take faɗin Jalal babu dai wanda ya ganka ko, Jalal ka faɗa mun....."Da mamaki yake kallonta kafin yace" Ammi are you alright, meke faruwa, waima me kike yi a nan a daidai wnn lokaci.
     "Sauƙeajiyan zuciya tayi kafin tace ba komai Jalal mije cikin asibitin sai na faɗa maka abinda ya fari,
   "Asibiti kuma??? Ya maimaita a zuciyarsa, haka yabi Ammi kaman raƙumi da akala har suka shige cikin asibitin zuciyarsa na ci gaba da bugawa da sauri ɗa sauri.

     "Cak ya tsaya yana kallonta sanda Ammi ta buɗe kofar ɗakin da take, itace dai ba gizo take masa ba, fuskanta na fiskantar sama, idanunta a lumshe tamkar mai bacci gashin kanta ya rufe pillow ɗin da aka mata mayashi dashi, hancinta pointed yana kallon sama ɗan lips ɗinta kaman wacce ta shafa jan baki, ga bandage ta ko ina duk yanda taji ciwo an rurrufe. Take yaji jiri na neman ɗibarsa, Ammi sai faman masa bayanin yanda ta sameta da abunda aka mata take Jalal kam ko saurarenta bai yi, abu guda da yaji shine shigowar likita da tambayar jinin da yayi.
     "Juyowa yayi ya dubi Dr ɗin kafin yace" Dr ka yake my blood..... Kallonsa sukayi daga Dr ɗin har Ammi, Dr ya ɗanyi jim kafin yace " Amma sai mun auna munga ko........" Bai kai aya ba Jalal da tuni jijiyoyinsa sun tashi cikin ysananin ɗaga murya yace" *I said take mine,*
   "Jiki na ɓari Dr Garkuwa yace Okay muje muje, Ammi kuwa kallo tabisu dashi har suka fice.

   "Cikin sa'a jinin Jalal yayi daidai wa Zubaidah nan da nan aka ɗibi har leda biyu aka saka mata.
   "Ammi ta shigo ɗakin da Jalal yake yanda aka ɗibi jininsa yana ƙoƙarin maida rigarsa, nan ta hangi tabon dake a bayan kafaɗansa wanda da gani ba sai ance maka shaida bace, ƙirjinta ya buga da ƙarfi, anya duk ranan da Jalal yasan ba ita ta haifesa ba anya bazai tsaneta ba, Juyiwan da zaiyi suka haɗa ido, murmushin ƙarfin hali ta sakar masa kafin tace "Son sannu da aikin alkhairi Allah ya biyaka.
      "Ɗan mirmushi yayi ba yareda yace komai ba, su duka biyu kana ganinsu kasan akwai abinda ke damunsu,....




        "Iyalle ta dubi Hadiza baki sake kafin tace" Ashe ke shasha ce, yanzu ɗan wann kuɗin har ya isa ya rufe bakinki, ai baki sani ba hanyar arziki ne Allah ya kawo maki a sauwaƙe, yanzu abinda za'ayi tashi zakiyi kije ki sami wann saunan mijin naki kita shera kuka ki faɗa masa abinda akayi wa ƙanwarsa daga nan ki ɗaukesa kuje asibitin ki koma can gidan kiyita masu bore da hauka, kinsan masu kuɗin nan basu fatan abinda zai ɓata masu suna, Snn kinsan anƴi baikon Zubaidah ce masu zakiƴi a al'adan garin nan duk macen da aka sameta ba budurwa ba tofah maido da sadakinta ake snn sunanta da na iyayenta ya ɓaci snn har ta mutu babu me aurenta, ce masu zakiyi saidai su aurawa yaransu ita, nasan bazasu yarda ba kinga dole su ksra maki kudi mai tsoka snn kice dede ku bisu Habuja don a nan tsangwamanku mutane zasuyi. Kinga idan kiks tafi Habuja kya min hanya nima na tafi, kinga muafah shikenn zamu fara neman kuɗi da gaske a can har muzo mu gine gida kalan nasu.......  Hadiza tayi shewa ta miƙa wa Iyalle hannu suka tafe kafin tacr" Ƙawata shiyasa nake sonki yanzu bari kiga da zafi zafi ake dukan ƙarfe. Yawwa ƙawata cewsr Iyalle maza lalumo nawa kasoɓ ki bani ke ai tanzu kin zama hajiya.
    "Hadiza ta zaro kuɗi ta danƙawa Iyalle kafin ta fice.



  "Yanda Iyalle ta tsara mata kuwa hakan akayi, Hamma Habibu yasha kuka shaɓe shaɓe harda majina, tabbas yasan iyayensa bazasu taɓa yafe masa ba ya kasa riƙe masu amanar tilon ƙanwarsa, Hadiza harda hawayen munafunci take basa baki, kayi haƙuri Habibu ina nan tare da kai snn duk wanda yayi wann abu wa Zubaidah bazmu taɓa barinsa ba ko ɗan uban waye, sai an bi mana kadinmu, maza shirya muje asibitin, babu musu ya shirya suka nufi asibiti.


    ""Labib ne ya soma ƙarasowa yanda Jalal ke zaune kafin su Salim.suka karaso, murya kalan na masu nadama suka  soma magana dashi, ko kallo basu ishesa ba ƙarshe ma tashi yayi ya bar masu wajen, ya ɗau aƙwashin ko yau ya koma Abuja bazai ci gaba da zama da Dasuki family ba, ya koyi darussa a rayuwa snn zai tashi ya nemi abun kansa duk wuya duk rintsi.

**************************

*Gombe Fada*


Wata matashiyar mata ce zaune saman Kujeru na alfarma, a shekare bazata gaza shekaru 40 ba, tana sanye cikin kaya na alfarma, fuskan nan nata ko kaɗan babu annuri, ido ta kafe hoton jariri dake manne a tangamemen parlron dashi, wani katutun baƙin cini ya kuma tokare mata maƙoshi, Idan akwai abinda tafi tsana a rayuwarta toh wann tangamemwn hoton ne wanda yake kaman ruhin mijinta Mai marta sarkin Gombe MODIBBO ALIYU MU'ALLAYIƊI.




Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:11] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                            13

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


    "Gimbiya Zahida ce ta shigo parlorn cikin shiga shiga ta alfarma Alkebba fara ƙal sai ɗauke ido yake, daka ganta basai ance maka ga jinin sarauta ba, gefe da mahaifiyarta ta zauna fuskarta ɗauke da murmurshi kana tace" Barka da Hantsi Ummi na, da fatan kin tashi lafiya.
  "Murmushi matar data kira da Ummi tayi kafin ta shafi gefen fuskar Zahida tace " Barka ɗiyar saraki jikar saraki da fatan kin wayi gari lafiya.
   "Murmushi bai bayyana haƙwara Zahida tayi kafin ta riƙo hannun Ummi tace " Ummi kina sani naji kamar watarana zanyi sarauta idan kina koɗa ni haka.
   "Ummi ta jawo Zahida cikin jikinta ta rungume kafin tace" Mai Martaba baida wani ɗa ko jika a doron ƙasa face ke, baida gudan jininsa a duniyan nan face ke ƴar lele na, meyasa kike tunani wataran bazaki mulki garin nan ba.
  "Rausayar daidanu Zahida tayi kafin tace" Ummi a ina kika taɓa jin mace tayi sarauta a ƙasar nan, burina dai kawai shine na auri saraki nima don gaskiya idan ba jinin sarauta ba bazan yi aure ba.
   " Ummi tayi wani dariya mai cike da ma'anoni idanunta suka sauƙa kan tangamemen hoton jaririn dake manne a tampatsetsen parlor kafin tace" Maza tashi muje mu gaida kakarki kafin ta fara mita.
   "Babu musu Zahida ta miƙe Ummi na riƙe da hannunta bayi guda biyu ne ciki harda Jakadiya suka take masu baya snn suka nufi sashen "Madaki wato mahaifiyar mai Martaba.......



    "Tunda ta buɗe ido tayi ido huɗu da lkitan ta ringa mimmiƙewa tana wani irin ƙara haɗi da ƙanƙame jikinta dukda azaban ciwon da takeji, babu yanda likita baiyi ba ya dubata amma abu yaci tura, kai duk wani mutum idan ya shigo muddin na mijini ne to ta rinƙa figita kenan tana wanu irin kuka mai wani irin sauti tana ƙanƙanme jikinta.....
   "Daga can nesa ya tsaya yana kallonta sanda aka kira nurses sukai mata alluran bacci, wani irin tausayinta ne ya cika zuciyarsa, take yaji bazai iya kallon wann hali na ƙunci da wahala da take ciki ba, kaman wanda kwai ya fashe ma a ciki haka ya fito reception.

    "Zama yayi a reception yana kallon Hamma Habibu dake ta faman share hawayen da ya wanke fuskarda gaba ɗaya, Jalal ya kuma jin tausayin waɗan nan bayin Allah sanda yaga Hamma Habibu ya kama wuyar rigarsa yana sharan majina dashi a hankali ya ƙarasa ga Hamma Habibu gamida da dafe kafaɗansa Habibu ya ɗago rinannun idanunsa da suka jiƙe da hawayr yana kallon Jalal kana ya soma faɗin"
   "Bata da kowa sai ni, iyayenmu sun rasu sun bar min amanarta, gashi na kasa cika masu burinsu, na kasa riƙe amanar tilon ƙanwata, idan ta mutu bazan taɓa yafr ws kaina ba.... Kuka mai ƙarfi ya kufce masa sanda yake dukan kansa da duka hannayensa biyu yana faɗin" Bani da amfani, gaskiyar Hadiza ne banida amfani, banida amfanin komai.... Kalmar da ya ringa nanataw knn yana dukan kansa da ƙarfin gaske.
   "Jalal da tuni hawaye sun ciko idanunsa, tausayin Zubaidah da Hamman ta ya cika zuciyar sa, Allaj sarki ashe marainiya ce babu uwa babu uba babu dangi sai Hamman ta wanda yake irin mitanen nanne masu maysalar ƙwaƙwalwa. Abu mai kaman wuya ne ke sa Jalal kuks, zai iya cewa tun yana yaro kai koda yakr yarinta duk tsananin abu bai yin kuka amma wann karan sai ji yayi ya kasa controlling kansa, tuni idanunsa sunyi jazur haka nan farin fatar sa ta koma ja, tsanar aminan sa ne ya cika zuciyar sa haɗi da tausayin Zubaidah da rayuwar da zata fuskanta...
  
   "Annah ce ta bawa Jalal kuɗi ya sayo allura don babu wanda ake buƙata za'a mata a asibitin, cikin sauri ya amsa ya nufi waje, Annah ta karaso ga Hammah Habibu tana basa baki cike da tausayawa.


   "A daidai ƙofa ya haɗu dasu, sun ɓadda kama basu ɗauko luxurious cars ɗinsu ba, Daddy ne sai Barr Munir... "Cikin sauri Jalal yayi niyyan wucewa Barr Munir yayi alama wa Gurd ɗinsu guda ɗaya da hannu, kan kace me an janye Jalal zuwa cikin wata mota mai baƙar glass.
   "Fuzgewa Jalal ya shiga yu da iya ƙarfinsa daidai lokacin da Barr Munir da Daddy suka shigo, banda harara babu abinda Jalal ke masu, a hasale yake faɗin" Me kuke yi a nan marassa imani.
    "Daddy yayi wata murmushi kafin yace" Relax boy, dont di anything foolish, magana ɗaya zuwa biyu zamuyi da kai, if you cooperate fine ka tsira, idan kuma ka ƙi..... Wata murmushi yayi jafin ya kalli Barrister.
   "Barrister yayi gyaran murya kafin yace" Jalal, shin kana da shaida cewa su Salim su suka raping yarinyar nan, shin idan kana tunanin idan kayi gigin sbigar da ƙara kai zaka tsira ne, bazaka tsira ba , tunda dukanku kuna wajen sanda incidence ɗin ya faru, tabbas yarinyar ta ganku gaba ɗaya, babu mai cire ka cikin wnn mess ɗin, she'll admit dukanku ne kukayi raping nata, snn boy ina gani daga idanunka you are madly in love with her....."Da mamki kurum Jalal ke kallonsa.
   "Barr yayi wata murmushi kafin yaxi gaba da zayanno kalamai masu ɓadda tunanin mutum irin nasu na lawyoyi " Ka sake tunani da kyau yaro, idan kayi confessing laifinku zaka tafi prison for the rest of your life don bakada mai tsaya maka, kar ka mance ƙasar nan idan kana da kuɗi babu mai ja da kai, su salim will be free kai ɗaya za'a bar cikin wann mess ɗin don kaine talaka, and poor mum ɗinka da bata da kowa saiki, ƙunci zai kasheta, snn wann yarinya bazaka taɓa kasancewa da ita ba, wataƙila itama depression ya kasheta, kaga ashe tainakon da kayi niyyan yi baiyi rana ba.
   "Jalal ya zuciye tamkar zai jai mai naushi yake faɗin" Stop involving me a cikin mess ɗinsu, ban aikata ba n no one will force me to confrss something I never did, not even you Alhj Kasim.
    "Murmushi sukayi su duka biyi, kafin Barr yace" I like your courage boy, amma dai ka duba maganar da nayi maka, and abu na karshe idan kana so kayi saving life ɗin yarinya ka aureta....
    "Mun riga mun gama magana da likita gibe za'ayi discharging nata kai tsaye kuma Abuja zamu wuce gaba ɗaya including her and her family. So dabara ya rage naka Jalal, ka sani kai za'a bari a rana don mun sami amincewar uwar goyonta da likitan ta, kaga baka da shaida... Daga haka suka buɗe masa marfin mota ya fice jikin sa a sanyaƴe.
   "Wai shin haka duniya ta koma, wai shin shi talaka bashida ikon gudanar da rayuwarsa yanda yake so, shin mutane haka suka zama, abin duniya ya gama rufe idanun kowa, kaico irin wann rayuewa da muke cikinta a yau.....


Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:11] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                           14

*©Sameena Aleeyou....✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


     " Jiki a sanyaye ya tare mai mashin yana tambayarsa ina zai sami chemist mafi kusa don ba sanin garin yayi ba, basu wani tafiya mai nisa ba suka samu, nan ya sai alluran ya koma asibiti. 
   "To his greatest surprise wulgawan motar compnayn *Dasuki Hodlings* ya gani, kuma tabbas ɗazu cikin ta su Daddy suka zo. Toh me ya dawo dasu tambayar da yayi ma kansa kenn, sann babu mai basa amsar wann tambayar nasa yasa ya nufi asibitin kai tsaye.

   "Shaye da mamaki Jalal ke kallon su Mommy da Mami, Annah ce ta hango shi tsaye ya kafe su da idanu,
  "Jalal ƙaraso  mana , Allah dai yasa an sami alluran, Annah ta faɗi daidau lokacin da gaba ɗaya suka maida kallonsu ƙofa, Mami Momy da kuma Yaya Hadiza.
   "Momy ce ta miƙe gamida karɓan alluran hannun Jalal wanda ya koma tamkar gunki bai gama shan mamakin ɗan adam ba saida yaji momy na faɗin" Jalal abokan ka sun wuce sun barka har ina masu faɗan ina suka bari ka, ashe kai kam taimako ka tsaya... Da mugun mamaki kurum yaje binta da kallo sanda taci gaba da faɗin "
  " Allah sarki Jalal yaron arziki, Allah dai ya biyaka kaida mahaifiyarka, irin wann raimako da kukayi ai mu ya kamata mu ringa yin irinsa, ta maida duvanta ga Annah daketa faman murmushi kafin tace" Habs Annah ai irin haka da wuri ake faɗi sai mubada kalan namu gudumawar, ƴanmatan da kaddara da tsautsayi na fyaɗe a auka masu haƙiƙa suna buƙatar taimako da kulawa don haka ne ma Alhj ya yanke shawarin taimaka masu itada familynta, gobe insha Allah zamu tafi Abuja baki ɗaya don hakan ne kurum zai mantar da ita wann mummunar ƙaddara da sameta, zamanta a nan zai ringa tuna mata abin, snn cannin wajen zama zai mantar da ita komai.
   "Mami dai kallon Mommy kawai tayi tana mamakin yanda halin momy da Daddyn Salim yazo daidai, banda lugude da ƙirjinta keyi bata komai sau kallo, dan kuwa saida mijinta ya mata kashedi babu ruwanta a wann zalunci, toh ya zata yu tuɓda ɗanta na ciki, data rasa tilon ɗanta gwara ta biye masu kida hakan ka iya kawo matsala ga aurenta.

    "Annah da yaya Hadiza godiya suka shiga, yaya Hadiza harda share hawayen munafunci tuni ta kaɗo kan Hamma Habibu yazo yayi godiya, bai kawo komai a ransa ba ya ringa masu godiya...


   "Takaici da tausayi ya hanasa ci gaba da tsayƴwa a wajen, tuni ya fice zuwa farfajiayan asibitin.... Ƙasar wata bishiya a samu ya zauna gamida haɗe kansa da gwiwarsa, maganganun Alhj Kasim da Barr suka shiga dawo masa,
   "Kalaman da yafi nanatawa shine *"You are in love with her, Ka aureta shine maka mafita...*
    "Girgiza kai ya soma tamkar zararre, ko ɗaya ko kaɗan baijin abinda yake ji game da ita So ne ,shi bai taɓa yin soyayya ba balle yasan yaya take, abunda ya sani shine yana jinta tamkar ƙanwarsa snn yana tsananin tausayinta, snn ya ɗau alwashin tamaika mata har iya rayuwarsa.... A gigice ya miƙe ya nufi cikin asibitin sanda yajiyo wani irin karan da ta saki.....


    " Mami dai jigum tayi a mota har suka isa gida, tana shiga parlon su ta tarar da Daddyn Labib zaune yana karanta jarida da alama isowarta yake jira.
   "Kamar wacce ƙwai ya fashe ma a ciki ta nufesa tanai masa sannu da gida, ko kallo bata ishe sa ba baƙƙe ya tanka ta. Sanin bazai mata magana ba yasata nufi sama.
  "Daidai step na biyu taji ya kira sunanta, cak ta tsaya ba tare da ta jiyo ba.
   "Saboda kin raina ni shine saida kika biƴewa Yaya da matar sa kuka je ha'intar waɗan nan bayin Allahn ko, kina cikin hankalinki kuwa Salma, na saka maki doka ki take......."Kamar me shirin kuka ta soma faɗin" Haba haba Jamil, me kake tunani, na bari inaji ina gani tilon ɗan nawa ya tafi gidan yari, bazan iya rasa sa ba idan kai baka damu dashi ba...."Mikewa yayi gamida ajjiye jaridar dake hannunsa kafin yace " Shi ya janyo ma kansa, shi ya saka kansa a ciki don haka babu hanuna a kare shi, kuma a yau na isa Abuja zan miƙa sa ma hukuma....."Ihun da Mami ta saki ne ya kaɗo hankulan sauran mutanen dake gida, kuka take kan rusawa tana fadin " Ita babu mai kai mata ɗata kurkuku....
    
   "Alhj Kasim da Hajiya Farha a tare suja shigo, Mami ta karasa gabansu tana kuka take roƙon Daddy, Yaya dan Allh ka masa magana cewa yayi zai miƙa Labib ga hukuma, Yaya ka taimaka min ka hana sa....."Momy ta riƙo Mami tana lallashinta suka nufi upstirs....

     "Wani mugun kallo Alhj Kasim ke waysa wa ƙanin nasa kafin yace" Jamilu wato baka daina maganar nan ba koh, bari kaji na faɗa maka dukda cewa kai ka haifi Labib baka isa ka min iko akansa ba, bari kaji na sake faɗa maka in case u forgotten "Wllhi wllhi babu mahaluƙin da ya isa ya shigar da ɗana prison muddin Naira na aiki a kasar nan, Jamil ga fili ga doki idan kayi shirin yin faɗa dani yayan ka. Kayi abunda kaga dama tunda yanzu har ni nake faɗa kake faɗa.... "Daga haka yasa kai ya fice fuuuu...
    "Kallo Alhj Jamil yabi ɗan uwan nasa dashi, jikinsa yayi sanyi tabbas bazai so yaga rugujewar family ɗinsu ba  hankali ya sulale gamida zama bisa sofa haɗi da zare faran tabarau na ƙarin ƙarfin gani dake idanunsa.....




  *Washe gari*

"Tunda aka sallame ta bara ɗago ido ta kalli kowa ba, snn bata san duniyar take ko akasin haka ba, iyakacin abinda take tunawa shine dariyar su da shewan su sanda zasu rabata da mutuncin ta, haka nan idan ta buɗe idanun ta fuskokinsu take gani, motsi kaɗan idan tayi takan ji zafi zogo haɗi raɗaɗi daga ƙasanta, hakiƙa a galin yanzu tafu shiga sahun marassa ganjali, don kuwa tabbas bata san yanda hankalin nata yake ba, iyaka abinda ta sani shine duk na mijin da yazo kusa da ita takan fita hayyacinta takan koma tamkar mai ciwin hauka....




*Abuja*

   "Batasan a ina take ba, itadai buɗe ido tayi ta ganta a wani gida na daban, mafarki take waɗann samaruka sun nufota da wuƙa tana ihu tana gudu, gabanta kuma Umar ne ya buɗe hannu alamun ta ƙaraso garesa, fuskarsa kaman ba nasa ba ashe shima wuƙar ne a hannu sa.. Da tsoro ta isa gareshi yana ƙoƙarin burma mata wuƙar knn  ɗaya daga cikin samarukan nan ya ture Umar ya rungumeta.........
       "A gigice ta saki wani irin ƙara gamida taƙurewa waje guda, .. Hadiza ce ta shigo gamida jan dogon tsaki jin Zubaidah na kiran sunan Umar,......Yaya na kazo ka ceceni kashe ni zasuyi,
    "Ruwa cikin kopi Hadiza ta ɗebo gamida sheƙa mata..... Babu shiri ta buɗe ido firgit, ta yunƙura zata tashi taɓi zafi, hannunta dake ɗaure da bendeji yanda ta gurɗe taji ya shiga mata zogi alamun ta fama, a gigice ta fito daga ɗakin tana kallon yanagin yanda take, wani ƙara ta saki gamida durƙusawa waje...
 



       "Labib dake tsaye ta windown ɗakinsa yake hangota, wayarsa ya ciro ya shiga neman layin Salim.....



Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:12] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                              15

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


   "Hello guy kana ina ne? Daga ɗaya ɓangaren Salim ya amsa
   "Gidan su Kausar, what akwai wani abu ne.
   "Okay mu haɗu a company things are getting outta control...
   "Dont get u buddy, wau meke faruwa ne.
   "Gajeren tsaki Labib yayu kafin yace" Salim its about that girl....
   "You mean the Cow girl.
   "Dama wacce yarinya nake maka magana aside from her, ka gane Uncle cant tackle this issue alone, we need to talk kafin abubuwa su caɓe wann matan yayan nata zata zame mana sabon matsala, nu banma san meyasa Uncle ya kwaso su ya taho dasu ba,..... "
    "Miƙewa Salim yayi kana yace "Okay fine ka kira Taruq kace masa mu haɗu a company.. Daga haka yayi hanging.
   "Fuzar da iska yayi gamida furta "Dmn dammit..!!!!
   'Daidai nan Kausar ta ƙaraso riƙe ƙaramar tray a hannun ta... Da mamaki take binsa da kallo ganin ya miƙe ya ɗauki car keys ɗinsa.

    "Ajiye tray ɗin tayi saman tabƙe kafin ta bisa da kallo.
   "Ɗan murmushi yayi kafin yace" Sweetheart I'm so sorry but I really need to go.
   "Ɓata fuska sosai Kausar tayi kafin tace" I dont get u, you mean you leaving right now, haba Salim wai meke damunka ne, this days you acting very strange, tun jiya fah ka dawo bakazo ka ganni ba as your fiancee na ɗauka ma da zaran ka iso zaka zo ka ganni, ko waya mukayi da kai bana gane kanka kwana biyun nan, tell ne pls is something bordering  you???
   "Ƙaƙaro murmushi yayi gamida ƙarasowa daf da ita hannayenta ya riƙe kafin yace" Sweetheart don't let those ideas to ur head pls. Babu abinda ke faruwa sai zallan soyayyar ki, Daddy ne ya kirani and its urgent, you know how business men are, always busy,
   "Hannunsa Kausar ta kalla bataga zobensa ba, ɗago ido ta kuma yi tana masa kallon tuhuma kafun tace "And where is your ring.
   "Ƙirjinsa yabada rasss, cikin sauri ya saita kansa kafin yace " Em na cire shi lukacin da zanyi wanka but ina zuwa guda zan saka.
   "Cikin rashin gamsuwa da excuse ɗinsa tace " But that ring is a promise bazaka taɓa cire shi ko yaya,
   "Ɗan fuzar da iska yayi sanda wayarsa ta soma ƙara, da sauri ya saka a silent kafin ya kalleta yace " For Allah's sake Kausar its just a ring, besides mu a nan ƙasar ba auren zobe muke ba, its obvious kin saba ɗabi'un turawan yamma, but its diff here kin gane, whats important is that I love you with all of my heart and I mean it, Ɗan kallan agogon hannunsa yayi kafin yace" Daddy is waiting for me, I'll give you a call, luv u take care daga haka ya fice sai sauri yake kaman zai kifa...
   "Kallo ta bisa dashi har ya fice......
    "Cikin gida Kausar ta wuce jiki a sanyaye, haka kurum take ji wani abu na shirin faruwa tsakaninta da Salim.




     "Ƙura ma Yaya Hadiza ido tayi tana binta da kallon mamaki, she couldn't believe what shes hearing, hawayae na bin ƙuncinta ta sa bayan hannunta maras ciwon ta ɗan goge kafin ta soma faɗin"
    "Meyasa, meyasa kika ɗauko ni daga mahaifata kika kawo nan wajen, meyasa baki bari na mutu ba, meyasa baki bari an bisneni gefen iyaye na ba, meyasa kika rabo ni da garin masoyi na, shin kina tunanin zanci gaba da rayuwa ne, shin kina tunanin ni Zubaida har akwai sauran rayuwa a gaba na, babu ita. Mutuwa a wnn lokacin yafiye mun komai....
   "Tsawan da Hadiza ta daka mata ya jawo hankalin su Momy da Annah gaba ɗaya suka nufo sashen da aka sauƙe su Zubaidah. Janta Hadiza ta shiga yi tana faɗin babu yanda zaki tafi a nan zaki tsaya a nan zaki ci gaba da rayuwa.......
   "A zuciye Zubaidah ta fizge hannunta daga riƙon da Hadiza ta mata, babu alamun tsoro a tattare da ita take kallonta, cikin ɗaga murya take faɗin"
   "Is this all you can do for me, iyakacin abunda zaki iya min kenn? Ki amimce ki biyo waɗanda suka lalata min rayuwa suka durƙusar da rayuwar yarinyar da bata ci masu ba bata sha ba, shin idan kece Zubaidah hakan ta faru dake shin yaya zakiji,..
    "For years kina azabtar dani kina wulaƙanta Hamma na sabida lalura na rayuwa da yake dashi, daidai da rana guda ban taɓa saɓa maki ba, shin abinda zaki saka min dashi knn....
    "Da mugun mamaki Hadiza ke kallon Zubaidah ta canza gaba ɗaya ta koma tamkar ba ita ba lokaci guda, Huci ta soma tana bƙrin kunya....
     "Ɗaga mata hannu Zubaidah tayi kafin taci gaba da faɗin" Kin kula.dani tun ina yarinya Allah saka maki da alkhairi da abubuwan da kika min, Allah ya biyaki na sani nida Hamma na duk muna ƙarƙashin kulawarki ne, Allah ya biyaki. Amma ki sani mutuwata a yanzu tafiye mun komai..... Da ɗingishi ta juya ta koma cikin ɗakin gamida rufe ƙofar.....
   "Bugun duniya Hadiza tayi Zubaidah taƙi buɗewa.  "Taƙurewa tayi can ƙuryan ɗakin tana kuka mai tsuma rai.

   "Momy jiki a sanyaye ta koma sashen ta yayinda Annah ke tsaye a wajen tamkar gunki, abu guda da Zubaidah ta faɗi yayi muguɓ ɗaga mata hankali, *Kika kawoni wajen waɗanda suka lalata min rayuw* kalmar da Annah tayita nanatawa kenn, abinda ya ƙulle mata kai ta kasa fahimta. Jiki a sanyaye ta wuce ɓangarensu tana tunanin lamarin......

   "Daga yanda yake tsaye ya gama jin komai yaga komai a gabansa komai ya faru, Zuciyarsa taci gaba da zogi da raɗaɗi, shin haka zai tsaya yanaji yana gani rayuwarta ta ƙarasa lalacewa,..."A fili ya furta no, no no cikin sauri ya juya ya nufi gate ya fice......




    "A ƙofar *Dasuki Holding* suka haɗu su duka uku. Salim ne ya soma fitowa daga motarsa kafin su Labib da Tariq suka fito dama tare suke Labib ya biya ya ɗauki Tariq, Securities ne suka ƙaraso suka karɓi keys ɗin motocinsu suka ƙarasa da motocin parking space snn su kuma suka shige cikin companƴ ɗin wanda yake ko ta ina glass ne tamkar a turai kake.



       "Guys gaskiya nifa na fara nadamar abinda mukayi don wllhi my Dad is totally mad at me, cewar Tariq yayinda suke ƙoƙarin shigewa cikin lift, Salim ya ɗanyi gajeren tsaki kafin yace nima dai abin ya soma damuna don Kausar ta fara tunanin I'm hidding something from het. Tsaki Labib yayi sanda suka isa floor ɗin Daddy kafin ya juyo ya dubesu yace" Thats precisely why we are here, to talk with our parents, they shouldnt have brought that girl here in the first place. Gaba ɗaya suka kaɗa kansu suka ce haka ne.
     "Duk yanda suka wuce gaushe su ake *The Dasuki's* ba yara masu ji da kansu da ƙarfin arzikin iyayensu......


    "Sakatariyan Daddy ta ɗan dubesu cike da rusunawa tace " Am sorry but Mr president is at the middle of a meeting right now, you cant see him now....
     "Dmmit!!!!! Labib ya faɗi da karfi gamida buga tabƙe ɗinta wanda yasata zabura.
   "kwanto da kansa saitin fuskarta yayi fuska a tamke yake faɗin " If you dont want to get self fired then go in right a way, and tell him we wanna see him right now.
   "Da sauri ta miƙe kafin tace Ok ok sir right a way sir,ta wuce ta nufi Conference hall .....


          "Ana tsakiya da meeting sakayariyar sa ta kawo masa saƙon, fuzsr da iska yayi cikin ransa yace " Those boys wunt kill me, excusing kansa yayi kana yayi alama ma Lauyan sa Barr Munir kan cewa ya biyo bayansa, babu musu Barr ya miƙe yabi bayansa...



       "Babban parlon dake cikin Office ɗin suka ƙarasa, shigarsu yayi daidai da banko ƙofar wanda hakan ya ja hankalinsu gaba ɗaya suka kalli ƙofan. Cikin wani irin yanayi suke dubansa.
    "Barr yayi saurin faɗin " How dare you barge in here, ku talakawa really have no manners.
      "Daddy ya girgiza kai kafin yaci it is not his fault, I have to make it clear to those stupids securities  that this filthy jark isnt my son, he cant just come in here inti this very company.....

   "Alhj Kasim we need to talk for the sake of these spoiled brats ya ƙarashe maganar yana nuna su Salim da tuni sun sha jinin jikinsu....


Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:12] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                               16

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum....📖📚_


     "Kallon mamaki suka bisa dashi, Alhj Kasim ya dubesu kafin yace "Excuse us, Labib ya kalli Uncle ɗin nasa kaman me son yin magana sai kuma yabi bayansu ya fice.
   "Jalal ya dubi Barr Munir dake zaune saman ɗaya daga cikin royal chairs ɗin da aka ƙawata parlorn dasu kafin yace" Kaifa Barr aren't gonna excuse us...."Dakatar dashi Alhj Kasim yayi ta hanyar ɗaga masa hannu kafin yace " Boy ko me zaka faɗa min ka faɗa min gaban lawyer na, nida shi babu wani shamaƙi a tsakanin mu so just go ahead and talk.

    "Ƙarasowa cikin parlorn yayi gamida zama bisa kujera mai kallon na Alhj Kasim tuni idanunsa sun rine zuciyarsa ta shiga masa zafi sabida abinda zai faɗi, bashi da wani choice rather than it..."Barr ne ya katse masa shirunsa da faɗin " Jalal we don't have the whole day, Mr President is a busy man so kayi abinda ya kawo ka.
  
   "Fuzar da iska yayi kafin ya ɗago ido ƴana dubansu kana yace" *Zan aureta* daga nan shiru yayi bai kuma cewa komai ba, sai faman murza hannunsa yake jijiyoyin jikinsa sunyi ruɗuruɗu haka nan idanun sa sun koma jawur....


   "Surprisedly suke kallonsa...
     "Fari'a ne ya cika fuskokinsu mission ɗinsu goes well wann na ɗaya daga cikin dalilin da yasa suka taho dasu, don sun san muddin Jalal ya aureta toh magana ta ruhu har abada babu abinda zai kuma tono ta.
   " Kafaɗan Jalal Alhj Kasim ya shiga bubbugawa a hankali kafin yace" Now you proved to us you are capable of helping her, da kayi gigin kai report da shine ka cuceta ka kuma cuci kanka, don bazaku taɓa kancewa tare ba, you'll endup in jell and ita kuma she might commit suicide ko depression ya karta gaba ɗaya, and ƴour poor mother will loose her only son, Jalal you did the best thing.

    "Har lokacin dai Jalal bai ce masu komai sai kallon gefe da yake yi.
     "Alhj Kasim yayi ma Barr ido, check Brr ya ɗauko ya rubata mar kuɗi kafin ya miƙa masa yace" Ka je ka nemi hida sai ku yare gaba ɗayanku a can....." Bai gama rufe baki ba Jalal ya miƙe yana masa mugun kallo kafin yace" Bana son komai daga gareku, auren Zubaidah sji kaɗai na tambayeku sabida a halin yanzu ku kuke iko da ita tunda kuke iko da wicked sister inlaw ɗinta......

    "Murmushin bossawa sukayi baki ɗaya kafin Alhj Kasim ya dubi Barr ya masa ido, Kallo suka bi Jalal dashi wanda tuni ya fice....

    "A first parlor ya hangu su Salim suna zazzaune, Harara yabisu dashi ɗaya bayan ɗaya, Labib ne ya miƙe da sauri ya nufesa, saidai kafin ya iskesa ya tura sliding door ɗin ya fice.....


    "Alhj Jamil da Alhj Maina Dad ɗin Tariq suka ƙaraso parlorn after the meeting don jin me ake ciki, Alhj Kasim yace kar su damu he can take care if everything.... "Kallonsa dai kawai sukayi amma sunsan Alhj Kasim zai iya yin komai to get rid of his problems.
   "Alhj Jamil ya ajiye masa wasu documents saman table ɗinsa kafin yace
   " Yaya our company its at risk of going bankrupt, we might loose some of our employees sabida fake golds da aka fitar zuwa NewZeeland,...
   "A zabure ya miƙe yana kallon ƙanin nasa, tunu ya cire hular kansa ya shiga fifita duk da sanyin AC ɗin dake parlorn "
   "Jamil yaya akayi suka gane Zinaren bogi ne, Jamil we can't go bankrupt you need to do something.... Gaba ɗaya kaman zaucecce yake maganar, Waya ya ɗaga ya kira sakatariyarsa yace ta masa scheduling meeting da *Marafa Group Of Companies* Barr da Alhj Jamil sai kallonsa suke yanda ya zauce lokaci guda.
   "Kallon Alhj Jamil ya kumayi kafin yace " Ka kira duk wani bankin da ka sani ka karɓo aron kuɗi kafin business venture ɗinmu da Marafa group of companies ya bunƙasa, we cant loose our company brother, do as I said pls,...
    "Alhj Jamil ya dubesa da mamaki kafin yace" Yaya bashin banki fah kake magana, kasan....." Bai ƙarasa rufe baki ba Alhj Kasim yace " Haba Jamil so kake mu rasa company ɗinmu, ko billion nawa ne kasa hannu ka karɓa idan yaso daga baya sai mu wanye dasu, amma yaya kake gani yau udan baba ya taso yaga company ɗin da yasha wuya akansa ƴaƴan sa his very own children sun kasa maintaining, pls brother just do as I said for the sake of our company, for the sake of *Dasuki Holdings* Fuzar da iska Alhj Jamiƙ yayi kafin ya riƙo hannun ɗan uwan nasa yace " Yaya zanyi yanda kace, daga haka ya miƙe ya nufi Office ɗinsa.....

    "Yana ficewa Alhj Kasim da Barr Munir suka kwashe da dariya harda tafe hannu,.
  "Barr yace " Mr president baka da kyau, Alhj Kasim ya murmusa yana karkaɗa pen kafin yace" Let him borrow the Money, with that I'll ruin him completely dariya suka kuma yi hadi da tafe hannu...


¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤¤

*A Dukku fah*

     "Inna wai har yau babu wanda zaice min ha yanda Zubaidah take, ya kuma tambaya a karo na biyu.
   "Ajiye rariyan tankaɗen dake hannunta tayi fuska a tamke kafin tace" Baba Wuro (Haka take kiran Umar) Har sau nawa zan faɗa maka nima bani da taƙamammen masniyar yanda suka tafi, iyakacin jitajitan danaji cikin gari shi na faɗa maka, Zubaidah bada kanta tayi ma ɗaya daga cikin yaran masu kuɗin nan da suka zo, bayan sun gama lalatan su, suka tattara suka bisu garinsu wasu ma cewa suke da maƙudan kuɗi suka sayesu.....
      "Girgiza kai ya shiga yi idanunsa jazur yake faɗin" Inna ni nasan ƙarya ake mata sharri ne, Zubadah na bazata taɓa bada kanta ma wani ba, bazata taɓa bin masu kuɗi ta barni ba, nasan tana sona......" Baffah ne ya fito daga kewaye ya tarar suna zancen....
   "Ajiye butar hanunsa yayi gamida zubar da ruwan dake bakinsa kafin ya juyo yana ma Umar mugun kallo kana yace " Wato har yanzu bazaka daina maganar wann yarinyar ba ko, toh idan baka sani ba ka sani, maganar da mahaifiyarka ta faɗa maka gaskiya ne, idan da ba gaskiya bane ai da sun mana sallama kafin su tafi musamman ita Zubaidar tunda akwai baikon ta akan ka...


        "Idanuwansa suka ciko ƙwalla, da sauri ya miƙe ya shige ɗaki gamida kulle kansa, da gaske ne Zubaidah ta barsa sabida wani, take ya yuna sanda tayi aikin wuni guda gidan Alhj Dasuki, ya tuna irin kallon da wani saurayi ne kyau yake mata, ya tuna yanda itama ta masa murmushi, tabbas ko wata mace zata iya barin masoyinta akan wann saurayin sabkda ya haɗa komai na rayuwa, ka kuɗi ga kyau,....."Share hawayen da suka zubo masa yayi yana jin zuciyarsa na masa ƙuna, bazai iya barin Zubaidah ba, bazai iya rayuwa babu ita ba, dole ya fice ya neme ta dole ya dawo da ita gareshi don kuwa tabbas Zubaidah *Mallakin sa* ne......


     "Iyalle ta dubi ƙanwarta shafa wacce ke mutuwar son Umar amma besan tanayi ba, tayi murmushi kafin tace" Shafah ki kwantar da hankalinki Ummaru kaman kin samu an gama, ni nan da kike gani ni na kitsa wa Hadiza yanda zata yi, bacin haka ina taga kwanyar yin wnn tunani, ni dai abinda nake so dake kisan yanda zaki saye zuciyarsa tunda naga har kusan mutuwa nikayi sanda yakai baikon Zubaidah.
    "Shafa tayi wani murmushin jin dɗi, don yanzu jinta take tamkar sarauniyar mata tunda Zubaidah ta tafi kafin tace" Ai wllhi bakiji wani daɗin da nake ji ba, yanzu kika tabbatar min ke ɗin yayata ce, Umar kuma dole yaso ni tunda wancan me kama da aljanai ɗin tayi gaba.. Dariya suka kuma yi a tare harda kashe hannu....



*Gombe, Fada*

      " Abba barka da war haka , cewar Zahida yayinda take ƙarasawa kusan mahaifin nata,
   "Murmushi yayi mai fitar da ƙwarjininsa kafin yace "Barka Gimbiya ƙarasi mana, ya matsa mata gefe da tumtim ɗin da yaɗan kishingiɗa akai ta ƙaraso gamida zama daf dashi. Hannayenta ya riƙo gamida sunbatar su kafin yace" Allah ya miki albarka ɗiyata. Murmushi tayi tana mai kallon mahaifin nata wanda a kullum cikin tausayin sa take sabida damuwan da bar yau ya kasa mance ta sama da shekaru ashirin da huɗu.
   "Ɗan gyaran murya Zahida tagi kafin ta kalli tapkeken hoton jaririn da duk wani parlor a gidan akwai hoton kafin tace " Abba meyasa baza a cire hotunan ba tunda naga ɗaga maku hankula yake musamman kai da Madaki, snn ya mutu Abba inaga ajiye hotonsa a parlor haka babu wani alfanu
      "Girgiza mata kai yayi idanunsa naga hoton kafin yace "Zahida Yayanki bai mutu ba, ni inaji a cikin jikina bai mutu ba, nasan watarana Allah zai haɗani dashi, ina ganinsa kullum cikin mafarkina, snn Suhaima tana faɗa min cikin mafarki na ɗanmu yanada rai, snn ta bar min amanarsa duk randa na hafu dashi......."Baki Zahida ta saki tana kallon mahaifinta wanda ba don jinin sarauta dake yawo a jikinsa ba da sai tace tabbas kwanyarsa ta kusan samin matsala, a hankali ta miƙe da zummar barin wajen, don tasan mai martaba muddin ya soma waɗan nan batu toh a ranar haka zai wuni bai fita fada ba..
   "Ummi dake maƙale jikin labule tana kallonsu, take taji zuciyarta na mata zafi, shin wnn wani irin yaro ne, shekara da shekaru yaci ace mai martaba ya mance sa shida uwarsa gashi har yau yana tunasu, gashi har yau bata cimma burinta na mallakan ɗa namiji ba wanda zai kasance magajin sarki.... Da wnn ƙunci ya juya ta nufi sashenta ba yateda ta shiga sashen mai martaba.


      "Zahida kuwa tana komawa ɗaki wayatya ta kunna ta hau facebook don abokin hitarta knn sai amintattun bayinta guda biyu, kasancewar kullum a killace take a guda bata fita ko ƙofa.
   "Hira ta soma yi da kawarta wanda basufi kwana biyu da haɗuwa ba, hura da yayi dadi sai aka koma waya daga chating...



*Abuja*
[1/23, 22:12] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                               17

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


   *"Dasuki Mansion"*

 "Matashin saurayi ne wanda aƙalla bazai haura shekaru 35 ba zuwa da shida ya shigo cikin parlorn cikin shiga irinta guards, baƙaƙen kaya daga sama har ƙasa, idanunsa manne da ɓaƙar tabarau.
   "Cike da rusunawa ya miƙa wa ogan nasa saƙon dake hannunsa. Alhj Kasim ya murmusa kafin yace " Good job Faisal, I trust you, I know I can always count on you, kaci gaba da aiki me kyau.
   "Faisal ya kuma rusunawa haɗi da yin gajeren murmushi kafin yace " At your service Sir,
   "Daddy yace " You can leave now,.
   "Kuɗaɗene shirye cikin babban jakar wasu in dollars wasu kuma Naira, murmushi yayi sanda suka kalli juna shida Barr Munir.
  "Barr ya shafi haɓarsa yana murmushi kafin ya jawo jakar ya buɗe, ..
   "Documents ɗin dasuke cikin first folder ya ɗauko ya shiga buɗewa,.
  "Murmushi yake yana kallon takardun kafin ya kalli Alhj Kasim yace" Everything perfect, gaskiya yaron nan bazamuyi wasa dashi ba yasan kan aikinsa, ka duba kaga yanda yayi copying signature ɗin Alhj Jamil tamkar shi yayi,....

   "Alhj Kasim yayi wata murmushi kafin yace" Barr I know what I'm doing nasan irin mutanen da nake aiki dasu, Wann yaro Faisal is very talented bazamu barsa ya tafi haka nan ba, dole naja sa sosai a jikina, yanzu abinda nake so da kai yanzu kayi attaching attaching waɗan nan documents ɗin da wanda yayi signing na karɓan bashin banki, kaga idan akayi presenting a  conference meeting babu wanda bazai yarda sa hanunsa bane, daga nan mission dina na mallakan *Dasuki Holding* ya kusa zama sucessesful... Dariya suka fashe dashi kaman ba manyan mutane ba....
  "A tare suka miƙe suka nufi waje Barr na biye bayansa ɗauke da rapan en ɗari biyar rufe cikin envelop kai tsaye sashen su Jalal suka nufa...


    "Annah na tsaye tana kwasan shanya taji sallaman su, cike da tsananin mamaki ta bar abinda take ta ƙaraso tana amsa sallaman, mamaki ma ya hanata gaishesu, da ƙyar ta lalumu kalamai tai masu sannu, suma sun lura da hakan.

   "Har Annah tai masu iso suka shigo ta shimfiɗa masu darduma bata daina mamaki ba.
  
    "Bayan sun gaisa ne Daddy yai gyaran murya kafin ya soma magana.
   " Hannatu nasan zakiyi mamakin ganinmu a ɓangaren ki, Toh magana ta gaskiya its about your Son Jalal.....
 
    "Ɗago ido Annah tayi tana dubansu kafin tace" Lafiya Alhj me ya sami Jalal.?
   "Daddy ya ɗanja fasali kafin yaci gaba da faɗin" Jalal was at my office earlier, Yaje shi office ɗina on an a serious matter, bansan ko kin sani sabida naga tun da incidence ɗin ya faru   kin yi iya ƙoƙarinki wajen kula da yarinyar, in short ke kikayi saving life ɗinta......
   "Gaba ɗaya ya ƙulle kan Annah, ko kaɗan bata gane me yake nufi ba kokuma ina ya dosa.... "Murya cike da damuwa tace " Alhj saidai ban gane me kake nufi ba, what did this had to do with my son.
   "Ko yayi maka wani abin ne....

    "Daddy da Barr suka kalli juna kafin  Barr yayi gyaran murya yaci gaba da faɗin"
   "Tabbas bakida masaniya akan abinda ke faruwa amma yanzu ya zama dole ki sani tunda abin yakai ga aure, da alama Jalal ya ɓoye maki amma gaskiyan magana Jalal shi yayi ma yarinyar nan Zubaidah fyaɗe wanda hakan yasa Alhj taimaka masu tunda basuda kowa snn Jalal ma bashida kowa sai shi.......
    "Kaman almara haka Annah take jin maganar, ƙirjinta ya buga da ƙarfin gaske tasan Jalal manemin mata ne amma bata taɓa kawo zai iya yiwa wata yarinya fyaɗe ba..... Take hawaye ya shiga zarya a fuskar Annah.
  
   "Alhj Kasim da damuwan munafunci ya nuna a fuskar sa yaci gaba da faɗin" Hannatu keda Jalal duka ƴan uwa muka ɗauke ku mussaman Jalal na ɗauke sa tamkar ɗa bazan gansa cikin matsala na ƙyalesa ba dan kuwa shida su Salim daidai na ɗauke su. Snn laifin da ya aikata yayi nada wann dalili ne yasa amincewa zai auri yarinyar su rufa wa junan su asiri.
   "Barr ya ajiye kudin gabanta kafin Daddy yaci gaba da faɗin" Yau da dare insha Allah zamu ɗaura auren snn ga wann Jalal yayi amfani dashi don neman muhalli,..... "Kasa magana tayi har suka fice bata san sun fice ba.....

     " Ido ta ƙura wa kuɗin har lokacin idanunta na hawaye, "Innalillahi wa inna ilaihirraji'un " Fyaɗe, Fyaɗe Jalal, Jalal, ɗinta shi yayi raping Zubaidah....  Hannu tasa ta goge hawayen,  dukda ba ita ta haifi Jalal ba tana masa so irin wanda uwa keyi wa ɗanta, her whole life burinta Jalal ya zama ɗa na gari, amma sai ya kasance akasin haka, kaico kaicon irin wann rayuwa.
    "Sai yanzu komai ya shiga dawo mata daki daki tun ranar bikin sakun rana Salim,  ta tuna Jalal ya tambayeta sunan yarinyar da suke tare, ta tuna irin kallon da taga yana mata ta tuna yanda hankalin sa ya tashi lokacin da Zubaida ke asibiti wann a dalilin haka har rana me kaman ta yau bata gane kansa ba, ta tuna yanda yayi donating jininsa ma Zubaidah, ashe dama sabida yasan laifinsa ne dole ya damu..... Maganar Zubaidah na ɗazu ya dawo mata kwanyar ta yanda take faɗi wa Hadiza *"Kika kawo ni wajen waɗanda suka lalalta min rayuwa* tabbas da Jalal take, shine ma komai ya tabbatar mata shine tunda gashi su Alhj har sun sani, no wonder bai mata maganar ba, no wonder ya tafu kai tsaye ya sami Alhj ba tare da saninta ba. Durusawa tayi wajen zuciyarta na mata ɗaci......



     " Suna fita daga sashen su Jalal suka nufi sashen da aka ba wasu Zubaidah su zauna.
    "Har lokacin bata buɗe ƙofa ba tana rufe ƙuryar ɗaki tana kuka.
    "Hadiza tana ganinsu ta miƙe tana washe baki tana gyara ɗaurin kwali, gaishe su ta soma yi har tana tuntuɓe wajen ɗaga masu kayan da Zubaida ta ringa watsi dasu.
   "Gaba ɗaya suka sakar mata murmushi kaɗin suka tambayeta Zubaidah...
   "Nan ta soma jero masu ƙarya da gaskiya na abinda Zubaida tayi da wanda bata yi ba. Barr ya fuzar da iska dan bai zaci yarinyar zata zame masu matsala har haka ba, Barr ya kuma tambayar Hadiza ina mijinta, ta bashi amsa da fadin" Sun fice ganin gari shida Kamalu
  "Alhj Kasim ya murmusa kafin ya ciro wayar sa yayi dialing wani lamba ya ƙara a kunne. "Hello James ya kashigo cikin guda ina neman ka, Barr zaizo ya directing naka yanda nake, daga gaka ya kayse wayan.


      "Jim kaɗan Barr da wani murtuƙeƙen mutumi sanye cikin baƙin kaya da baƙin tabarau , da gani basai ance maka guard dinsa bane suka shigo a tareda Barr.
    "Daddy ya dubesa kafin yace " James nasan kanada makullin duka ɗakunan gidan nan, I want you to open this door right a way.
   "Kames ƴa rusuna kafin yace " Considered it done sir.

    "Kan kace me James ya buɗe ƙofar ɗakin da Zubaida ke ciki.....
    "Aikuwa tana ganinsu ta saki wani ƙara  ta shiga tattaro gaba ɗaya kayan jikinta tana rufe jikinta, manne wa sosai tayi ta taƙure can ƙuryan ɗakin jikin garu, banda rawa da jikinta keyi bata komai, sai faman cije bakinta take tana kuka maras sauti.
     "Alhj Kasim yayima James Ido. Take James ya ciro ƙaramar bindiga a cikin suite ɗinsa yayi pointing bindigar a kanta cikin miryarsa mai cike da tsoro yace " Quittttttt....!


Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:13] ‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                           18

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


    "Daɗa mannewa tayi jikin garu gamida runtse idanunta wanda suke a jiƙe da hawaye,
    "Alhj Kasim ya durƙusa a gabanta gamida ƙura mata ido, hannu yasa ya ɗago fuskarta......
   "Wani irin kyarma jikinta keyi jin hannunsa a jikinta, tamkar garwashin wuta aka ɗora mata haka take ji, ƙara ta saki gamida ƙanƙamewa waje guda,...." Murya a dake yace " Kalle ni nan...
    "Bata kallesa ba sai runtse idanunta da tayi.
  " James ya kwaɗa mata ƙasar bindigan a keyar wanda yasata buɗe ido babu shiri, da ƙarfin gaske James ya ɗago ta gamida riƙe hannayenta, jin bazata daina kuka ba yasa James ɗaure bakinta da wani farin ƙyalƙe, yana riƙe da ita ya ɗago ta tana facing Alhj Kasim...."
  
   "Barr yayi wata silent murmushi kafin yace " Yarinya ki bada haɗin kai ki sami tsira, bata kallesu ba sai hawayen dake zuba daga idanun ta....
   "A zuciye Daddy ya pinciko gashinta da ƙarfin gaske gamkda ɗago kanta, kallonsa kawai take da idanun tsana hawaƴe na bin idanunta.
   "Daddy yaci gaba da faɗin" Idan kika bi umarni na kin tsira Shashan yayanki wanda ya kasa kula da rayuwarki ya tsira, ki buɗe kunnuwanki da kyau kiji abubuwan da zan faɗa maki.
   "Kukan azaba kwai Zubaida keyi riƙon gashinta da Daddy yayi na mata ciwo, haka nan raunukan dake jikinta basu gama warkewa ba.... "Daddy yaci gaba da faɗin
   "Idan kika ƙi yin abu guda da zan umarce ki zan kashe ki snn na kashe ɗan Hamman ki kinga na tabbata wann sokon yayan naki wanda hankali bai ishe sa ba, idan ya rasa ki ya rasa ɗansa nasan baƙin cikin duniya zai taru ya masa yawa, bayan na gama azabtar dashi snn na kashe shi,..."Wani irin runtse idanunta tayi hawaye na bin ƙuncinta jin irin kalaman da yake faɗa mata.

   "Zan aurar dake a yau ɗin nan ma wanda naga dama, snn wllhi wllhi kinji na rantse naji wann magana ya fita waje zanyi yanda na faɗa maki zan kashe ki na kashe ɗan Hamman ki na kuma azabtar da Hammanki, don haka kar naji kar na gani bakin ki ƙanin ƙafarki, maganan fyaɗen da aka maki ya zama tarihi... Kina jina ya ƙarashe maganar yana zungurin kanta da bakin bindiga.
   "James ya kifa mata wani gigitaceccen mari kafin yace " Answer!!!!! Da ƙarfin gaske...
  "Daɗa runtse idanunta tayi kafin ta gyaɗa kanta da ƙyar sabida azaba.

   "Barr ya ajiye mata kuɗi bandir ƴan ɗari biyar a gabanta kafin yace " Amarya wann kiyi anfani dashi wajen sayayya don nasan amare ba a rabasu da sayayya.... Daga haka James ya suce mata baki gamida yin wurgi da ita tsakiyar ɗakin kafin suka fice.
 
    "Yaya Hadiza dake laɓe bakin window ta gama ganin komai, dariya tayi a hankali gamida watsa wa Zubaida dake kwance helpless a ƙasa wani uwar harara kafin tayi saurin ƙarasawa yanda su Daddy suke.

   "Murmushi suka sakar ma juna kafin Daddy yace " Kar ki damu kaman yanda na faɗa maki aurenta yau da daddare a parlor na ina fata yayan nata bazai zame mana matsala ba.
   "Hadiza ta kuma murmusawa kafin tace" Yo ai Alhk kar kaji komai tunda kanada ni, wann shashashan kuma ai ba mutum bane don sai abunda nasa sa shi zaiyi,..
   "Barr da Daddy suka kalli juna kafin suka sakar ma juna murmushi.
    "Barr yasa hannu cikin jakar ya ciro rapan ƴan ɗari biyu ya miƙawa Hadiza baki har kunne tasa hannu ta amshe. Barr ya kalleta xike da jin daɗin yanda Hadiza ta kasance mace mai son kuɗi babu wuya yanzu sai ka saye imaninta.


    "Hadiza sai ysallen murna take ta nufi cikin gidan, ɗakin da Zubaidah ke yashe a ƙasa ta shige...
      "Tana nan kwance a kasa kukan ma baya fita, Allah sarki ƴar marainiyar Allah.😭.
    "Harara Hadiza ta watsa mata gamida zama gefenta, ɗaukan kuɗin tayi ta maƙe a hammatar ta, take ta canza fuska zuwa kalan damuwa sai ka rantse har ranta ne.
   "Tallafo Zubaidah tayi ta rungume gamkda goge hawayen munafinci kafin ta soma faɗin" Kiyi haƙuri Zubaidah ki amince ki auri wanda ya aminta da aurenki ki sani taimaka maki zaiyi don wllhi yanzu babu me yarda ya aureki ko Ummarun da yake waƙar soyayyarki muddin yaji abinda ya sameki ba aurenki zaiyi ba. Kuma bari na faɗa maki babban rufin asirinki shine rufuwar maganar nan din kuwa muddin kowa yasan abinda ya sameki haka za'a keta zancen ki ana nuna ki da yatsa, mutane zasu ƙyamace ki haka nan babu mai kallon da wata daraja baƙƙe kima.....





Sameeena ce👌🏾
[1/23, 22:13] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                         19


*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


     "Toshe kunnuwanta tayi da ƙarfin gaske alamun bata son jin kalaman Hadiza, wani uban tsaki Hadiza ta buga kafin ta tureta daga jikinta ta faɗi ƙasa, idan kin ga dama kiyi yanda kika so tunda ke ba'a maki abin arziki, ai ba akan ki aka fara fyaɗe ba kuma wanda aka masu ma suna ci gaba da rayuwa, idan kin gama kukan munafurcin kinya iya tashi kizo ki min aiki don ba baiwar gidan ubanki bane...."Daga haka ta kaɗe sawayenta tayi ficewarta..


     "Asmah ce ta shigo tapkeken parlorn da sallama cikin shiga irinta lauyoyi wato cooperate, har ta cire belt ɗin dogon takalminta Kausar dake zaune a parlorn bata sani ba, da alama tayi nisa duniyar tunani...
   "Ɗago kai Asmah tayi tana dubanta kafin ta ƙaraso daf da ita ta dafata....
   "A ɗan zabure Kausar ta kalleta kafin ta sakar mata murmushi...
   "Ah Attorney yau har kun taso daga sch ɗin ne.
    "Asmah ta murmusa tana mai ajiye tapkeken littafin ta saman tabƙe kafin tace" Ai na faɗa maki Law School ba kaman degree program bane ba lalle mu ringa jimawa ba... Asmah ta canza zancen da faɗin
   "Ehen wai meke damunki ne, kwana biyu nan you dont seems your self, is anything bothering you?...
    "Shiru Kausar tayi gamida ƙurawa Tv dake kan faman aiki idanu..
   "Asmah ta matso daf da ita gamida dafa kafaɗunta kafin tace " Sis I'm here for you, you can talk to me may be I can help.
    "Kallonta Kausar tayi still damuwa ne a face ɗinta kafin tace " Cousin bazan ɓoye maki ba its about Salim.
    "Asmah ta gyara zama kafin tace " Ehen me ya sami Salim ɗin.
   "Kausar ta ɗan rausayar da idanu wanda ɗabi'arta ne kafin tace " These days he's been acting very strange, gaba ɗaya tamkar bashi ba, I'm afraid he might be hidden something from me, and ɗazu yazo ya tafi sauri sauri wai Daddy na kiransa, ni the most abinda ya ƙuƙƙen kai ma shine rashin ganin engagement ring ɗinsa da banyi ba a hannunsa.......
    "Dariyar da Asmah ta fashe dashi ne yasata cin birki, wani mugun kallo take watsa mata kaɗin tace " What, is it funny?
   "Asmah ta ɗan tsaigata dariyar nata kafin tace" Wait hold on Kausar, you mean akan rashin ganin ring a hannunsa kika shiga damuwa haka, tabbdijam toh ai mu musulmai ba auren zobe muke ba, ke bari kiga naje na faɗawa Mumsy islamiya zamu shiga don wllhi turawan nan sun juyar maki da tunani...
    "Harara Kausar ta kuma watsa mata har lokacin Asmah bata daina dariya ba kafin tace"
   "Look at you jor, ce maki akayi ban sani bane, well I'm only used to it ne nothing more, nasan musulmai basa auren zobe you dont have to inmply anything, besides ni jikina ne ke bani something drastic is about to happen.... Miƙewa tayi ta suri car key ɗin Asmah gamida jan mayafi ta yafa."Asmah baki sake take kallonta.. "Wait ina kuma zaki.
   "Kausar ta gama saka takalminta kafin ta juyo ta kalli Asmah tacd" Kinsan tunda aka sa rana na Mumsy bata so ina fita, so thats why zan fita da motarki don nasan bazata gane na fita, so kindly ina si ki miƙe ki wuce ɗakin ki, and help me close my door kafin one of those maids masu neman gidin zama wajen Mumsy su kai mata rahoton na fice.
   "Asmah ta kalleta galala kafin tace" Aiko basu faɗa mata ba ni zan faɗa mata...
   "Pls mana Attorney ,
  "Murmushi Asmah ta ɗanyi kafin tace " But you've to be fast, sai kin dawi Allah ya tsare, hugging juna sukayi kafin Kausar ta fice cikin sauri.....



      "Hamma Habibu yayi shiru yana duban Hadiza, harara ta kuma galla masa a kari na biyu kafin tace" Meye kake kallona haka, kamata yayi kamin godiya ba ka tsaya kana kallona haka nan ba tunda da taimakona ta sami mijin aure, bacin haka waye kake tunanin zai kwashi wnn ƙanwar taka sauran kan layi...
   "Kallon Zubaidah dake matse cikin garu yayi har lokacin bata dawo daidak ba kafin ya maido da dubansa ga Hadiza, murmushi ya ƙaƙaro kana yace" Eh eh haka ne haka ne Hadiza, mun gode maki daba don ke ba da yanzu muna can garinmu anata zagar min ƙanwa.
   "Ya kuma duban Zubaidah kafin yace " Kiyi haƙuri kiyi haƙuri ƙanwata kin sami me auren ki...... "
   "Miƙewa tayi tana cije baki kallon tausayi tabi Hamman ta dashi kafin ta juyo tana duvan Hadiza,
   "Murya na rawa take faɗin" Bazan aure sa ba wllhi ko waye bazan aure sa ba, bazan taɓa aure ba bazan ci gaba da wann rayuwar ba, da na auri wani ba Umar ba gwara mutuwa na, snn a halin yanzu banjin zan iya auren nasa,... Ta ƙarasa ta riƙe hannun Hamanta kafin tace " Hamma ka yafe min, ta shafi kan Kamalu dake bacci bisa tabarman kafin ta soma tafiya da baya da baya... Kan kace me ta fice a guje dukda ciwo da azaban da take fama dasu...

   "A guje suka bi bayanta suna kiran sunanta, har suka fito haraban gidan wanda hakan yaja hankaƙin illahirin mutanen gidan...
 
      "Daidai lokacin aka buɗe wa Kausar tangamemen gate ɗin ta kuwa shigo a guje wanda ita kanta bata san dalilinta na shigiwa a guje ba, kodayake tunanin da take ciki yasata yin hakan.... " Kowa dake wajen runtse idanunsa yay don kuwa daidai ƙarasawan Zubaidah wajen knnn.....
   "Shigowarsa gudan knn yayi jifa da abinda ke hannuna ya nufeta gamida ƙwalla mata kira.....
   "ZUBAIDAHHH..... Daidai lokacin da Kausar ta danna wani uban birki babu shiri, Jalal kuma ya rungumota suka zube ƙasa suka shiga juyi a ƙasa, ya tareta ta ko ina yanda bazata ji ciwo ba...

     "Salim dake tsaye balcony ƙirjinsa ya buga da ƙarfin gaske ganin Kausar ce ta shigo, ai a talatin ya zura shkrt ɗinsa ya nufi downstirs...

    "Buɗe idon da zatayi tayi ido huɗu dashi, fuskan da bazata taɓa mancewa ba, fuskan da shine mutum na farko da ya kai mata sura, ɗaya daga cikin fuskoki huɗu da bazata taɓa mantawa a tarihin rayuwarta ba, ɗaya daga cikin mutane huɗu da suka lalata mata rayuwa, farin fuskan da ya koma mata tamkar baƙin kumarci......."Wani irin kara ta saki don kuwa gaba ɗaya abinda ya faru da ita ya shiga yawo a kwanyanta...
    "Tunda tayi wann ƙaran bata kuma motsi ba,... Hankali tashe ya shiga jijjigata yana kiran sunanta,.. Kausar ma hankali tashe ta shiga taya Jalal, gaba ɗaya sauran mutanen suka karaso Hammah Habibu kam durƙusawa yayi a wajen ya shiga shera kuka...
       "Hadiza ta yaɓe baki take da baeinta kukayi ta mutu tunda abinda tafi so kenan, sekace akanta aka soma fyaɗe..... "Kausar ta ɗago tana duban matar dake magana kaɗin tace " You mean Rape???
    "Daidai lokacin da Salim ya fito farfajiyan gidan... Dafe kansa yayi a hankali ya furta "Shitttttt! Cikin sauri ya juya ya koma cikin gidan.
      "Mummy tayi saurin ƙarasawa ta riƙo Kausar ta faɗin " Daughter taso mu shige ciki...
    "Kausar ta ɗan kalleta kafin tace " Mummy bari a sa mata ruwa ta farka, she panic nd then fainted......"Ido Mummy tayiwa Hadiza alamun su shige ciki....
      "Kan su ankara Jalal ya sureta ya nufi ciki da ita, gaba ɗaya suka bisa da kallo.
    "Hadiza ta gallawa Hamma Habibu harara kafin tace" Sai ka taso mu shige ciki ai me ƙanwa,... Kausar ta bisu da kallo har suka shige
   Kafin ta juyo ta dubi mummy wacce itama kallon tabisu dashi.
      "Suna haɗa idanu Kausar ta sakar mata murmushi da iayakacinsa fatar baki. Mummy ta rungumo kafaɗun Kausar kafin tace mu karasa Daughter.....







sameeena ce👌🏾
[1/23, 22:13] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                             20

*©Sameena Aleeyou... ✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum... 📖📚_


  *Dedicated To All Victims Of Rape*



    "Shiru Kausar tayi tana duban Mummy,  a hankali ta furta "Jalal,  so Jalal can rape someone....
   "Mummy ta matso gamida rik'e hannun Kausar cikin nata kafin tace " Daughter ki bar D'anAdam yanda kika gansa, muma bamuyi zaton Jalal can do such thing ba, anyway they are getting married, at least sun rufa asirin junansu......
  
   "Kallon Mummy ta kumayi da mamaki kafin tace " Mummy this is a very serious crime,  why would you cover-up for him,  let him pay for his crime, bai kamata a k'yalesa haka nan ba.
    "K'irjin mummy ya bada dummm!  Tamkar Wanda aka sauk'e mata guduma.
   "K'ak'aro murmushi tayi kafin tace " Kausar the girl refused to talk, tak'i to shigar da k'ara tace duk wanda ya dameta da maganar shigar da k'ara zata kashe kanta,  snn Jalal yayi nadaman abinda yayi ya nemi yafiyarta snn ya amince zai aureta so kinga gwara a barsu su sami Chance na kasancewa tare.....
   "Jinjina kai Kausar tayi da jin hujjojin Mummy, on the other hand ta tsinci kanta cikin rashin gamsuwa da labarin da Mummy ta bata gameda Zubaidah,  haka kurum taji tana son jin gaskiyar labarin,  snn tana son kasancewa da Zubaidah don akwai abinda take so taji daga gareta.... bata kuma cewa komai ba har Mummy ta mik'e tana rangad'a kira wa Cook Jane don tazo tayi serving Kausar...

  
    "Dafe kansa ya kuma yi a Karo na biyu yana hangen k'ofar parlorn....
    "Ganin Mummy ta fito yasa sa k'arasasa da sauri... Wani uwar harara Mummy ta watsa masa kafin tace " Ni na gama nawa part d'in I made her believed Jalal was the one who raped the girl...  Yanzu saura ya rage naku kai da Daddynka,  yasan yanda za'ayi su bar gidan nan zuwa gobe kai kuma ka fara tunanin zama namiji for once, and stop being so Mama Boy......  Daga haka tasa kai ta wuce......
  

    "Sauk'e ajiyan zuciya yayi kafin ya murd'a marfin k'ofan a hankali, zaune ya hangeta da gani tunanin wani abin take..
    "Yayi saurin saita kansa kafin ya k'arasa yana fad'in " Baby kece a gidan namu,  what a surprise..

    "Mik'ewa tsaye tayi fuska babu walwala kafin tace " Mummy nazo gaisarwa don tun dawowarsu daga Dukku bamu gaisa ba ko a phone ne, and I'm leaving right now....
   
   "Ohhh com'on baby so soon, at least mud'an gaisa mana...
   
 "Hararansa take ba tare da tace komai ba ta suri Jakarta...
   "Da sauri yasa hannu ya rik'e jakar kafin yace " What why the face, wai make damunki me huhm Sweetheart.
  
    "Kallonsa take ido cikin ido kafin tace " Salim duk yanda akaga guda d'aya dole aga sauran ukun,  what I Mean duk yanda aka ga Jalal dole a ganku kai,  Labib and Tariq,  don kuwa nasan bakwa rabuwa, Salim I perfectly well know you and your friends, nasan all of you are womanizers, now tell me the truth and when I said the truth I mean only truth, are you involved in that horrible crime?????

    "Da mugun mamaki yake kallonta da k'yar ya iya lalumo kalamai saman harshensa kafin yace " Sweetheart I don't get you.....  Which... Which crime are you talking about.

    "Huci kawai Kausar keyi kafin tace " The crime your very own friend your childhood friend Jalal had committed, and still ka b'oye min baka dad's mun ba.   

    "Tattare naman goshinsa yayi gamida fuzar da iska kafin yace" For God's sake Kausar stop talking ridiculous, I swear to you I had nothing to do with that,  Why must you accused me of such dirty crime, haba haba sweetheart I tought kinmin farin sani by now kinsan abinda zanyi kinsan wanda bazanyi ba,  wllhi tun ranar da na d'aura idaniyana akanki ban sake kula ko wata mace ba,  If I want zuwa zanyi na kama hotel na shek'e ayata da iya adadin 'yammatan da nake so without you knowing it ba wai na tsaya ina raping mere girl irin wann yarinyar ba,  rashin fad'a maki kuma da banyi ba gani nayi wann ba abun fad'a bane abin takaici ne da Allah wadai... Jalal is my very good friend but believe me wllhi banda hannu kan abunda ya aikata,  hasalima nida Daddy taimakonsu muke shida yarinyar su gina sabon rayuwa amma idan baki yarda dani ba fine banida choice..... Ya k'arashe maganar yana ware hannaye sai ka rantse gaskiya ya gama fad'i....

    "Jikinta ya d'anyi sanyi amma har yanzu ba wai ta aminta bane. Gyara mayafinta tayi kafin ta d'ago kai tana dubansa snn ta soma fad'in" Salim zan iya zama da kowani irin mutmun a duniyar nan amma banda *Rapist* if I finds out kanada hannu ciki believe me I will not marry you and you can forget about me,  excuse me....  Daga haka tasa kai ta soma tafiya....

     "Dammit,  dmmitttt,  Ya fad'i gamida murza duka hannayensa biyu cikin gashinsa,  da sauri ya bud'e k'ofar ya shiga kiranta yana binta da sauri......


     "Daidai K'ofar da zai sadaka da haraban gidan ta had'u da Labib,  kallo d'aya ta masa ta watsar don kuwa gaba d'aya haushinsu take ji...
   "Ohhh our bride to be yau kece a gidan namu,  Labib ya fad'i yana wani shi'umin murmushi....

   "Gajeren murmushi tayi snn suka gaisa a tsaitsaye kana tace "Ita zata wuce gida,

   "Labib ya kalli Salim dake tsaye bayansu yana muzurai kaman munafuki kafin ya ware idanu yace " Aww this is so soon though bansan time d'in da kikazo ba,  gashi inaso muyi 'yar wata magana about your cousin Asmah,  but anyway zamu zo gida nida abokina then we talk....

    "D'an yak'e tayi kafin tace " That wud be much better, bye for now...... Wucewa tayi ta nufi motar,  Labib yayi ma Salim ido alamun meke faruwa, ido ya masa kawai kafin yabi bayan Kausar da sauri.....

   "D'an tab'e baki Labib yayi kafin ya nufi cikin gidan.....



     "Har lokacin ya kasa motsa koda d'an yatsansa ne sai hawaye dake neman kufce masa.......  Baki ya bud'e da k'yar da niyyan magana tayi saurin dakatar dashi ta hanyar d'aga masa hannu kafin taci gaba da fad'in
.    "Jalaluddeeen,  ban tayar da kai ta hanyar banza ba,  Allah shine shaida na,  my whole life I've been struggling for you to have a better future, Why Why Jalal,  meyasa ka zab'i ganin kukana,  meyasa ka kasa rik'e amanar da Allah ya d'aura maka a matsayinka na d'an Adam.  Meyasa ka lalata rayuwar innocent girl irin Zubaidah. Idan ka kubce wa Shari'an duniya ka sani bazaka kubcewa Shari'an mahaliccinka ba......

     "I zuwa lokacin ya kasa rik'e hawayensa.....  A hankali ya k'araso gamida d'aura kansa bisa cinyarsa ta,  kuka yake kaman k'aramin yaro,  babu yanda ya iya bashida wani zab'in da ya wuce d'aukan laifin da ba nasa ba,  Alhj Kasim is very rich and powerful Man,  he can destroy Zubaidah and her family muddin ya fad'i gaskiya so as Annah  too,  he needs to this for Zubaidah and Annah, take yaji zuciyarsa tana dad'a basa k'arfin gwiwa..... 
   "Kuka Annah keyi har lokacin kansa na bisa cinyarta,  hannayenta ya rik'o a hankali yayi kissing nasu kafin ya soma fad'in"

       "I hope one day you'll forgive me my Annah, yeah I was stupid and also a coward, I was drunk that I couldn't stop...."Burki yaja cikin ransa kuwa k'arasawa yayi da fad'in "I couldn't stop them, na kasa hanasu cin zarafinta......

       "D'ago ido yayi yana kallon Annah kafin yace " I'll never ever forgive my self for what I did...... Wayarsa ne tayi k'ara gabansa yayi mugun fad'uwa ganin me kiran "Alh Kasim Dasuki ne.  Jiki a sanyaye ya d'ago ido yana dubanta kafin yace " I'll Marry her Annah,  I'll help her to live again, I'll stand by her to overcome this horrible experience, I'll help her to heel all the damages I caused her...... Daga haka ya fice cikin tafiyar da tafi kama da sassarfa.
   "Annah ta bisa da kallo har ya fice,  wani ikon Allah sanyi ne taji ya ziyarci zuciyarta,  hak'ik'a Jalal yanada baiwa da wani babban Al'amari a tattare dashi wanda ita kanta bata isa tace ga abun ba......


Sameena ce👌🏾
[1/23, 22:14] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                            21

*©Sameena Aleeyou.... ✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


   *Dedicated To All Victims Of Rape*


   *How painful it is... 😭😭😭 I barely slept well last night when I received the saddest story. Three girls were raped at a University in one night, and you know what frightens me the most, one of the victims was raped by three men just like ZUBAIDAH, she's now receiving treatments at a hospital ..... 😭😭😭*

  *Shin har yaushene za'a daina yiwa mata cin zarafi ta hanyar fyad'e a k'asar nan, shin shuwagabannin mu basu ganin abinda ke faruwa ne, shin wai shi talaka bashida ikon rayuwa ne, Hak'ka yanzu nake jin k'warin gwiwar rubuta wann littafi kuma ina fata sak'ona zai isa ga jama'a mussam THE RAPISTS AND THE VICTIMS da kuma shuwagannimu,  Dan Allah matasa aji tsoron Allah kar ka b'ata rayuwar da baka san yanda aka jima ana ginata ba Ka tuna idan baka haifah ba meyuwa ka haifa a gaba idan Allah beyi zaka haifah ba toh bazaka rasa 'yan uwa wanda nasan bazaka tab's so kaga wani yayiwa naka wann cin zarafi ba,  Oh my Brother in Islam ka tuna whatever goes around comes around Dan Allah mu kiyaye......... , 'Yar uwa wanda wann mummunar tsautsauyi da k'addara ya apka maki kar kiyi fushi da lamarin ubangiji kar kice shikenan baza kicigaba da rayuwa ba kaman da although it's very difficult but don't worry Allah is with you, you'll never be alone, give your self a chance to live.. And Don Allah a ringayin gaggawar Sanar da hukuma idan irin haka ta faru don taimakwa wajen tsayar da b'arna....... "Ku kuma jami'an tsaro kuji tsoron Allah ku ringa hukunta masu irin wann aiki da irin hukunci da aka tanadar domin su, idan kun tawye hakkin 'yar wani ku sani Allah bazai barku ba don baya hukunci da zalunci....... Allah Ya kawo mana k'arshen wann musiba a doron k'asa.. Ameen*



     "Jiki a sanyaye ya k'arasa cikin parlorn, ga mamakinsa Hamma Habibu ya gani zaune k'asa gefen Alh Kasim,  daga gefe kuma saman kujera Lamin masallacin Alh Kasim ne gefe dashi kad'an Alh Jamil ne, d'aya kujera me kallon tangamemen glass door d'in dake parlorn kuwa Alh Maina ne Dad d'in Tariq da Barr Munir ne suke zaune akai...... Jalal yabisu da kallo One by one kafin ya k'arasa shigowa,  Hamma Habibu kasa rufe baki yayi sai murmushi yake,  gefensa ya muskuta yabawa Jalal,
   "Jalal ya d'an sakar masa murmushi kafin ya zauna.....


    "Zamansa keda wuya suka soma gudanar da abinda ya tarasu, Hamma Habibu shi yayi alwali wa k'anwarsa Zubaidah yayinda Jalal ya wakilta  Alhj Jamil ya karb'a masa auren Zubaidah....!
   "Cikin mintuna da basufi biyar zuwa goma ba aka d'aura auren *Jalal da  Zubaidah* kan sadaki Naira dubu talatin tare da shaidu kaman yanda yake a tsarin musulunci....

   "Hammah Habibu ya kamo bakin rigarsa yana share k'wallan da suka ciko idanunsa, tausayinsa ya hana Jalal motsawa daga yanda yake,  kamo hannun Jalal yayi har lokacin na sharan k'walla kafin yace " Ka kulamin da ita bata da kowa a duniyan nan sai ni  sai kuma kai a yanzu......"Bai iya ci gaba da maganar ba sakamakon rushewa da kuka da yayi..... "duk wani mai imani a wajen saida ya tausaya wa Hamma Habibu.

   "Alh Jamil da Jalal suka rik'osa har haraban gidan, har lokacin Jalal kasa cewa komai yayi ba,  dukda ba auren soyayya yayi da Zubaidah ba saida yaji canji a yanayinsa,  har Hamma Habibu ya wuce sashensu bai sani ba.
   "Kafad'unsa da yaji an dafa ne yasa juyowa da sauri,  Alhj Jamil ya gani fuskarsa cike da damuwa.... "D'an bubbuga kafad'un Jalal yayi kafin yace "Jalal Allah ya saka maka da mafificin Alkhairi..... Jalal bai iya cewa komai ba sai kallon da ya bisa dashi.... Har Alh Jamil ya wuce gidansa dake manne dana d'an uwan nasa Jalal bai daina kallonsa ba,  A hankali kuma ya maida dubansa ga sashen su,  Jiki a mace ya soma tafiya zuciyarsa ta shiga tambayarsa "Anya hukuncin da ka yanke kayi daidai, wata zuciyar ta shiga k'arfafa masa gwiwa kan cewa wann shine hukunci mafi kyau, Allah yaga niyan ka bazai barka haka nan ba , da wann tunani ya isa sashensu wato BQ..


     "Zaune ya taddata ta had'a tagumi komai ya faru kaman a mafarki, komai ya faru all of a sudden, ta kasa gasgata lamarin wai Jalal d'inta yau yayi aure, tabbas abinda ta jima tana son gani kenn dukda ba wani girma can yayi ba..  Saidai auren yazo ba ta yanda tayi zato ba,  snn a halin da ake ciki a yanzu batasan makomar auren ba....."Zaman da yayi gefenta ne ya katse mata tunaninta......
    "D'ago ido tayi tabb k'walla tana kallonsa shima k'wallan ne a idanunsa..... "Bud'e baki yayi zaiyi magana Annah tayi saurin rungumesa, rungumeta shima yayi sosai gaba d'aya suka soma hawaye...

   "You did the right thing son,  Allah albarkaci rayuwar aurenku, maza tashi kaje kaci abinci....
   "Mik'ewa yayi da k'yar tamkar maras laka a jiki da k'yar ya iya furta na k'oshi Annah wanka zanyi yanzu daga haka bai kuma cewa komai ba ya shige  d'akinsa.......



      "Yana tsaye jikin mirror bayan ya fito daga wanka , ya k'urawa tabon dake gefen cikinsa ido tunani iri da kala suna yawo a kwanyarsa, kaman daga sama ya soma jiyo hayaniyar mutane, babu shiri ya k'arasa jikin window ya d'an jaye labule kadan yana lek'ewa......

    "Mummy da Hadiza ne rik'e da ita, Fuskarta a kod'e alamun taci kuka, da gani basai an fad'a maka dole aka mata ba, k'irjinsa ya shiga bugawa da sauri da sauri,  juyawa yayi babu shiri gamida zama bisa katifarsa.  Har lokacin k'irjinsa bata daina luguden da take ba......


     "Annah ta fito domin tarbansu,  Hadiza kuwa sai yab'a mata habaici da mugun kallo take, Mummy tayi saurin jan Annah uwar d'aki don tattaunawa.


     "Ina d'an naki yake,  ya fito ya kaimu gidan da zamu zauna,  don nauyi ne sosai ya hau kansa,  tunda ya iya danne d'yar mutane ya keta mata haddi na tabbata yayi girman ya d'auki d'awainiyar mutane da yawa....... "Jin wann kalamai na Hadiza yasa Zubaidah sakin wani k'ara gamida kame kanta,  tak'urewa tayi can k'arshen garu tana kuka gamida k'ank'ame jikinta sosai, duk k'ok'arin dasu Annah suke abu na neman fin k'arfinsu,  duk wanda ya nufota ihu take sakewa tana matsewa cikin garu..
   "Daga d'akinsa yake jiyo kukan nata, dafe kansa yayi sabida zogi da yaji zuciyarsa na masa,  cikin sauri ya  fice daga gidan dukda dare ya d'an soma ja......

   "Suna tsaye gate din gidansu Labib suna shirin tafiya gidansu Kausar suka hangosa,  shima kallonsu yake daga yanda yake tsaye.......





Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:14] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                          22

*©Sameena Aleeyou.... ✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_

*Dedicated To All Victims Of Rape*


    "Cikin sauri Labib yabi bayansa...

   "Jalal pls mana let's talk Buddy, I promise I won't take much Of your time....."Hannunsa yasa ya rik'o hannun Jalal guda d'aya wanda ya hanasa ci gaba da tafiya....
  
   "Kallon hannunsa yayi yanda Labib ya rik'e gam kafin ya d'ago rinannun idanunsa yana duban Labib, a hankali ya furta "Let go of my hand......
   "Girgiza kai Labib yayi kafin yace " No Jalal, I won't let you go until we finally talk,  for goodness sake Jalal we can't go on like this, I.....I know bamuyi daidai ba but please let's reconcile our friendship....."D'aga masa hannu yayi alamun dakatarwa, murmushin takaici yayi kafin ya soma fad'in"
   "Labib Dasuki, You and I have nothing to talk about, I already made my decision and I didn't ask for Opinion.
   "Kunyi abinda kuke so sabida kunada masu tsaya maku a wann rayuwar, kunyi destroying innocent soul, kun b'ata mata rayuwarta sabida bata da mai tsaya mata a rayuwa,  kunyi amfani da k'arfin dukiyar da kuke dashi kun rufe bakin kowa,  even the girl who's suffering right now bata da ikon kare kanta, sabida nasan Alh Kasim bazai tab'a bari tayi magana ba fine...  Amma ka sani baku k'arfin Allah ba,  And let make this clear to you,...."Dafa kafad'an Labib yayi kafin yaci gaba da fad'in" I didn't marry her because I wanna cover up for You, No!  Na aureta ne to save her life,  to help her continue living, and also to PROTECT her, Snn na rantse da Allah I'll never leave her side for as long as I will live.... Da d'an yatsansa yake nuni kan k'irjin Labib kafin yaci gaba da fad'in
    "And let me give you this message ka isar ma sauran abokan naka da kai kanka and also to your so called uncle, Zubaidah is now mine, she's now my wife,....."Ya d'an ja fasali kafin yayi wata murmushi da bazakace ga nufinsa ba kafin yace " You don't Owe me any Explanation... Daga haka ya wuce ba tareda ya kuma cewa komai ba....

   "Shafe fuskarsa Labib yayi da hannunsa gamida fuzar da iska.
   "Sai sann Salim ya k'araso yana masa alama da ido kan me ya faru.  Gajeren tsaki Labib yayi kafin yace " Let's get going Salim,...
    "Kallonsa Salim yayi kafin yace " Wait just wait Labib, tell me what exactly you guys discussed, and... And ka fad'a masa kar yacewa Kausar komai gameda wann mess d'in in case she ask him? Huh?  Com'on Salim say something.......

    "Foz kawai Labib yayi yana kallon Salim cikin zafin nama yake bud'e hannayensa yake fad'in " Enough, enough of this Salim,, for God's sake be a man for the first time, haba haba I can't stand your attitude of always being Mama boy,  be responsible for once, kai da anyi magana Kausar Kausar,  Baka tunanin wann abun can also ruin our reputation so as our parents,  you always think of your relationship with kausar, enough of this,  kai wllhi na fasa raka ka ma,  inaga nan gaba hiranma ni zan ringa maka...... A zuciye ya wuce ya nufi k'ofar gidansu..... 
   "Gajeren tsaki Salim yayi gamida dukan tayan motarsa da k'afa yana first shitt!!! Cikin gida ya nufa gamida cilla wa security guda d'aya car keys d'insa yace " Get my car in.....
   "Sashen mummy ya nufa sai ture turen baki yake kaman.... Sak spoiled child.

*************************

   "Gida ne d'an madaidaici mai d'auke da d'akuna hud'u sai brander a tsakiya,  daga can gefe kuwa kitchen. D'aya d'akin daga can gefe yake tamkar d'akin samari.....


     "Tun daga waje yake jiyo hayaniyar Hadiza ta yanda take shiga bata nan take fita ba,....
     "Ke ki bud'e kunnuwanki da kyau kijini wllhi tallahi sai kinyi k'aura zuwa d'akin mijinki, uban me zaki zauna ki mana,  kokuma raba yayan naki zamuyi nida ke,...... Iyakacin abinda ya iya jure ji kenn cikin sauri ya nufi d'akin Annah....


    "Zaune ya tadda ta da alama taji komai itama,  murmushi ta sakar masa kafin tace " Shigo Son.  Babu musu ya shigo gamida zama gefenta. ....



*Manage this, zakujini later insha Allah...*


Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:14] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*


                            23

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum... 📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape..*



    "Hannayensa Annah ta rik'o tana dubansa sanda suke jiyo kukan Zubaidah da yanda Hadiza ke azalzalansu ita da Hammanta....."À zuciye ya mik'e da niyan ficewa, da sauri Annah ta rik'o hannunsa tana girgiza kai kafin tace "
   "Dakata Jalaluddeen.....
   "Kallon Annah yayi da rinannun idanunsa kafin yace "Annah dan Allah ki barni naje na sami matan nan,  ya kamata tasan a yanzu bata da iko da Zubaidah,  she can't keeps on torturing her da kalamanta masu zafi...

   "Annah ta jinjina kai kana tace haka ne Jalal, Amma a yanzu idan kaje ka sameta you will endup ruining everything thing, think of Zubaidah,  how would she react idan ta ganka, komai sai a hankali Jalal...
   "Shiru ya d'anyi yana nazarin kalaman Annah kafin ya jinjina kai yace hakane Annah, Zubaidah ta tsaneni kaman mutuwarta musamman da yanzu tasan nine mijin da aka aura mata.

   "Sauk'e ajiyan zuciya Annah tayi kafin tace " Shiyasa nake so muyi magana nida kai.
   "Gyara zama yayi sosai yana dubanta kafin taci gaba da fad'in"
   "What are you planning Jalal,  me kake shirya wa rayuwarka,  kaga yanzu I'm not longer working for the Dasuki's,  snn Kai baka da aikin yi,  snn ga nauyin iyali da yanzu ya hau kanka. Snn wani hukunci ka yanke akan zamanka da Zubaidah.....

   "Maganar ta na k'arshe yasa saurin d'ago kai yana dubanta,  sadda kansa k'asa yayi kaman mai nazari,  a hankali kuma ya soma fad'in"
  "Annah idan zaki iya tuna wani aboki na Usman wanda kullum yake min nasihar na rabu dasu Labib....

   "Shiru Annah tayi na d'an lokaci kafin ta jinjina kai," Na tunashi yaron kirki ne k'warai babu shakka.

  "Jalal ya d'an fuzar da iska gamida had'e hannayensa yace " Toh ya sama min aiki a workshop d'insu yanda suke aikin kanikancin su tunda dama I already have the experience, snn wann gidan ma a wajen ogansu na amshi haya..... 

   "Murmushi Annah tayi kafin tace "Toh Alhamdulillah.... "Kaman wanda ta tuna wani abu ta tsagaita da fari'an nata kafin tace" Toh Jalal idan kud'in da Alhj Kasim ya baka ya k'are kanaga zaka iya ci gaba da biyan hayan....

   "Hannunta ya rik'o cikin nasa don bayaso ta d'ago komai,  don kuwa kud'in hayan ma Unman ne ya ranta masa don yayi alk'awari kwabon da ya fito daga Dasuki family bazai tab'a ba, Ya adana kud'in sabida akwai ranar maidasu ga Alhj Kasim.
  "K'ak'aro murmushi yayi kafin yace "Annah insha Allah hakan bazata zama matsala ba tunda gashi yanzu na soma aiki...

   "Hak'ik'a har cikin ranta taji dad'i wai yau Jalal ne ya zama very responsible mutum haka, Allah yasa ya rabu da bin matan banza da shan kayan maye kenn... kasa b'oye farin cikinta tayi wanda har saida Jalal yaji dad'in haka.
   "Kaman yasan tunanin da take, Ya dafe hannunsa cikin nata yace "Annah Insha Allah duk wani hallayana marassa kyau na dainasu, ki ci gaba da min addu'a Allah yayi mana jagora.....
  "Murmushi ta sakar masa kafin tace "Babu ranan Allah da zai fito ban maka addu'a be Jalal,  kullum cikin blessings d'ina kake Allah shiyi maka Albarka ya kuma albarkaci rayuwar aurenka....

   "Addu'anta na k'arshe yasa jin wani abu ya tsargar masa,  shiru yayi gamida k'urawa ledar tsakar d'aki ido....

   "Annah ta fahimce sa tsaf, a hankali ta dafe hannayensa kafin ta soma fad'in" Kar ka damu d'ana I'll look after her for you, zan kula da ita har zuwa lokacin da zata zama ta rabu da wann k'uncin dake damunta, nida kai Will  make a great team wajen taimakata har ta dawo cikin farincikin data rasa....."Baisan sanda ya rungume Annah ba tausayin kansu ya rufesu.......


   "Zaune ta sameta can k'uryan d'akin Hamma Habibu da Kamalu suna rarrashinta,  Hadiza kuwa sai faman cin magani take.
   "Annah ta ajiye flask d'in abincin dake hannunta kafin ta nufi yanda Zubaidah take.

     "Hannu Hadiza tasa ta jawo kulan ta shiga k'ok'arin bud'ewa,  wani uwar tsaki ta buga gamida tab'e baki kana tace "amma dai Allah sawak'e tsiya mutum ya baro shinkafa a garinsa yazo Habuja ma yanaci..... Wani tsakin ta kuma bugawa kafin tace "Allah sawak' naci abincin tsuntsu...Tasa k'afa gamida shure flask d'in....

  "Annah bata ce komai ba sai girgiza kai datayi, gefen Zubaidah ta k'arasa ta k'ura mata idanu tana karantar ta,  a hankali tasa hannu ta d'aura saman nata.

   "Sai snn Zubaidah ta d'ago idanunta wanda gaba d'aya sun kod'e sun canza launi, Kallon Annah take wasu hawayen suna k'ok'arin ciko idanunta, don tabbas bazata mance ranar data fara gamuwa da Annah ba,  daren da ya zame mata bak'in dare a tarihin rayuwarta dukda Annah was kind to her,  amma bazata mance cewa harda d'anta cikin mutane hud'u da suka shafa wa rayuwarta bak'in fenti,  suka mayar mata da farin cikinta akasin haka snn wai a yanzu shi aka aura mata a matsayin miji,  take taji wani sabon kuka ya kufce mata,  komai ya shiga dawo mata kwanyarta,  ihunta a lokacin da suke k'ok'arin rabata da mutuncinta da kuma dariyarsu wanda sautinsa ya kasa b'ace mata daga kunnuwarta......
   "Fizge fizge ta shiga yi tana Screaming...Wanda duk wani mai imani sai ya zubda k'walla idan ya ganta.....

  "Rungumeta Hamma Habibu yayi yayinda Kamalu ma ya had'e ya rungumeasu,  gaba d'aya suka shiga rera kuka........ 

   "A fusace Hadiza ta shigo d'akin gamida watsa masu mugun kallo kafin ta janye d'anta,  tana huci ta dubi Annah take fad'in" Baiwar Allah dan Allah ki tattara ta ki kaima wanda jin kukan ya zame masa dole, don nikam na gama nawa,  naji da kula da wann hau d'in yayan nata ne ko kuwa da yarona zanji,  ta k'arasa gamida finciko Zubaidah daga jikin Hammah Habibu ta hankad'ata k'ofa,  da sauri Annah ta rik'e Zubaidah cikin jikinta tana watsa wa Hadiza kallon k'yama...  Tama rasa kalma guda a bakinta a hankali ta rik'o Zubaidah dake d'ingishi suka nufi b'angaren d'akinta.
    "Hamma Habibu ya mik'e zaibi bayansu Hadiza ta jawosa da bayan rigarsa ta zaunarsa k'asa kafin tace " Ka rufe min baki ka wuce ka wanko hannunka da na Kamalu kuzo kuci abinci.
    "Banda felek'e da iyayi saikace kanta aka fara fyad'e a duniyar nan, kar Allah sa ta hak'ura suje can su k'arata.
[1/23, 22:15] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                            24

*©Sameena Aleeyou... ✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum... 📖📚_

*Dedicated To All Victims Of Rape...*



   "Girgiza kai take tana kallon Annah kafin taci gaba da fad'in" Dan Allah kar ki kaini wajensa wallhi mutuwa zanyi, na tsanesa na tsanesa, bana son na sake ganinsa har abada.....  Cikin kuka take kalaman nata.

  "Cike da tausayawa Annah ta rungumota jikinta kafin tace "Bazan kaiki wajensa ba Zubaidah, kin yarda dani? Zaki zauna tare dani..?

   "Samun kanta tayi da gyad'a kanta alamun ta amince.
  "Annah ta sakar mata murmushi snn suka ci gaba da tafiya,..
   "Da kanta tayi serving Zubaidah abinci  snn ta mata wa'azi sosai kan kalman kisa da take ambata ma kanta,  ta nuna mata illan hakan ka iya jawo mata fushin mahaliccin ta koda ace ita aka zalunta.
   "Lokaci guda Allah Ya jefa k'aunar Annah a zuciyar Zubaidah,  samun kanta take da bin umarninta. A b'angaren Jalal kuwa ko kad'an bai gigin shiga hark'anta, ko Annah ya shigo gaidawa Zubaidah tayita karkarwa kenan tana runtse idanu tana mannewa jikin garu had'i da k'ank'ame jikinta, wani lokacin ta shige d'aki a guje... Dukda sosai abin ke damunsa amma ganin ta sake da Annah har tana mata labarai yasa jin dad'i sosai cikin zuciyarsa,  koda ace har yanzu shi Monster ne a idanunta,  burinsa dama shine ta samu ingantaceccen rayuwa ...

   "A b'angaren Hadiza kuwa sosai Annah ke taka mata burki da hallayanta, harta Jalal saida ya tan's mata concert warning akan tak'ura Zubaidah da take,  toh abun ya d'anyi sauk'i saidai kunsan ance me hali bai canzawa, ..
   "Hamma Habibu yaji dad'i sosai ganin yanda Zubaidah ta d'an sake ba kaman da ba.


    "Yau satinsu guda knn da tarewa a unguwar Suleja. Kausar kuwa bata fasa k'udirinta ba don kullum cikn  binkicen yanda su Zubaidh suka koma take amma har yau bata samu ba,  a b'angaren soyayyarta da Salim kuwa bata nuna masa komai ba don kuwa ba tareda saninsa take gudanar da binciken ba..

   
   "Yau ta kama alhamisa,  Hamma Habibu ya fice bakin tasha yanda yake kasa lemu yana saidawa, su Annah da yaya Hadiza ma sun fice gaba d'aya harda Kamalu, 
   "Makarantar primary da Annah ta sami aikin kula da yara suka tafi yanda za'a sama wa Kamalu gurbin karatu,....

   "Zaune take a maidaidaicin parlorn Annah yau har TV ta kunna tana kallo,  lokaci guda tunanin Umar ya fad'o mata,  ko wani hali yake ciki,  shin a yanzu zai iya amincewa da soyayyar ta,  take taji hawaye na neman kufce mata, koda shike zuban hawaye ya zame mata jiki......
   "Ya jima yana tsaye yana kallonta,  sai yanzu ya samu daman k'are mata kallo gaba d'aya, dukda ba farin sani ya mata a da ba yasan ta rame sosai, sabida damuwar dake k'unshe cikin zuciyarta. tausayinta na dad'a fizagarsa.

    "Jikinta ne ya bata ana kallonta,  aiko tana d'ago ido suka yi ido hud'u.  Yana sanye cikin k'anan kaya red shirt da black jeans wanda ya fito da tsantsar farin fatarsa da kyawun halittarsa.....  Ai tuni jikinta ya soma kyarma kaman mazari,  a guje ta mik'e zata shige d'aki saidai tuni Jalal ya rik'ota ta fad'o jikinsa, k'ank'ame jikinta tayi tana k'k'arin k'walla ihu yasa hannu ya rufe bakinta, dukda  yaji a jikinsa sosai kasancewar yanda jikinsu ya manne dana juna, don rabonsa da kusantar wata mace tun bayan had'uwarsa da Zubaidah,.....
   "A hankali yake kallonta yana girgiza mata kai alamun tayi shiru, ...
   "Batayi shirun ba sai ihu take dukda hannunsa na rufe saman bakinta,  bata fasa kai masa duka da duka hannayenta biyu ba..

   "Dad'a matseta yayi sosai cikin jikinsa suna jin bugun zuciyar junansu kafin ya soma fad'in" Dan Allah kiyi shiru kiyi hak'uri ki saurareni,  babu abinda zan maki.....
   "Jin kukan nata ya tsagaita yasa sa bud'e mata baki gamida sakinta a hankali..

     "Aiko tuni ta matsa can gefe ta shiga jan rigarta tana rufe illahirin jikinta dashi.... "Cikeda tsiwa take fad'in" Malam ka fice kafin na maka ihu.....

   "D'an fuzar da iska yayi kafin ya durk'usa a gabanta, nan da nan ta shiga ja da baya har ta isa k'arshen garu...
  "Jalal ya k'urawa yatsun k'afanta ido wanda yasata saurin lullub'e k'afarta.
  "Kauda kansa gefe yayi kafin yace " Meyasa kike tskrona...

  "Jin tambayar tayi gatsau,  d'ago rinannun idanunta tayi tana watsa masa kallon k'yama da tsantsar tsana, lokaci guda kuma taji ta kasa jure kallon nasa,  Kauda kanta gefe tayi kafin tace " Sabida na tsaneka,  na tsani ganin ka, sabida kai d'aya ne daga cikin mutanen danafi tsanar su fiye da komai a duniya,  nafi tsanarka fiye da yanda na tsani shed'an.  Kuma wllhi wllhi sai ka sake ni sabida ni Zubaidah matar wani ne akwai baikonsa akaina kafin ku bayyana a rayuwarmu,  kafin ku canza mana farin cikinmu zuwa bak'in ciki,  idan baka sake ni ba,  toh ni ina iya tafiya na bar maku gidan.......


   "Hannu yasa duka biyu ya shafi sumarsa gamida fuzar da iska" Ya jima kaman bazaice komai ba har ta cire ran bazaiyi magana ba ta jiyo muryarsa cike da taushi yana fad'in" Zubaidah bazan sake ki ba koda ace ba auren soyayya mukayi ba,  dukda nida ke bamu son junanmu amma k'addara ta had'a.......... " Baikai aya ba ya jiyo siriryar muryarta cikeda tsiwa tana fad'in" No k'addara bai had'ani da kai ba,  sabida ni ba matar aure bace,  lokaci na d'ibar wa kaina kuma lokacin na cikawa zanyi tafiyata ba tareda neman shawarin d'aya daga cikinku ba not even my Hammah.

     "Kallonta kawai yake yanda take maganar,  lallai tanada courage sosai,  girgiza kansa yayi dukda bata dubansa kafin yace " Ba sai kin tafi ba  Zubaidah,  ni zan taf har sai rananar da kika sami gurbi na yafe min a cikin zuciyarki.  Amma akwai abu guda da ni Jalal nake so ki sani,......" D'ago ido tayi ta dubesa kafin ta kauda kai gefe.

    "Jalal yaci gaba da fad 'in" Wllhi wllhi na rantse da mahallici na ban aikata ba......... " Da sauri tasa hannayenta biyu ta toshe kunnuwanta gamida k'walla k'ara,  don kuwa komai ya shiga dawo mata,  bata manta wann farin fuskar nasa wanda a idanunta bak'kk'irin yake lokacin da ya soma rik'ota........" Ganin ya kasa controlling d'inta yasa mik'ewa da sauri, tuni ta shiga d'aukan duk abinda ke gefenta tana jifa masa tana fad'in ya fita ta tsanesa....

   "Dole Jalal ya fice zuciyarsa cike da tausayinta,  Lallai dole su nemi taimakon likitita dole su nemi taimakon *Therapist* dan kuwa abin yayi affecting Zubaidah sosai.......


*********************


*K'asar Gombe*



    "Gimbiya Zahida ce kwance saman tapkeken gadonta na alfarma,  waya manne a kunnenta da alama da k'awarta take wayan..

" Kai Kausar friend amma nai maki murna, Allah Ya baku zaman lafiya keda angonki Salim.
  "Daga d'aya b'angaren Kausar ta murmusa kafin tace " Na gode " Princess Heeda, nidai babban farin cikin da zanyi shine ki halarci bikina...

   "Zahida ta d'an ware ido had'i da yin murmushi kafin tace " Friend I can't promise you that,  sabida na fad'a maki yanda mahaifina Mai martaba  yake,  bai barina ina zuwa bikin k'awaye koda a cikin Gombe ne balle har wani gari,  idan kinga naje biki toh shakka babu bukin dangine a cikin fada. ..
  "Kausar ta d'an juya idanu fuskarta d'auke da murmushi kafin tace " Pls try and ask him nasan shima me yuwa zaizo d'aurin aure, tunda shine babban mutum a gari,  kinga fah dukanmu daga gari guda muke,  pls Heeda ki kwatanta tambayarsa, Ummi tasa baki,  pls pls pls.......
      "Zahida ta murmusa kawai dan kuwa duk yanda zatayi bayni wa Kausar bazata gane ba.Dan haka ta amince zata gwada tambayarsa......

 "Ummi ce ta turo k'ofar ta shigo bayan Zahida ta gama wayar......





Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:15] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                          25

*©Sameena Aleeyou... ✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum... 📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*


   "Zahida ta fad'ad'a murmushinta sanda Ummi ta zauna gefenta.
  "Ummi barka da shigowa ta fad'i tana duban mahaifiyar nata.
   "Murmushi mai cike da k'asaita Ummi tayi kafin ta shafi gefen fuskar d'iyar tata tace " Barka Princess,  who were talking to on the phone, you seems very happy.
   "Zahida tayi murmushi kafin tace " Ummi zaki iya tuna wata k'awata da nace maki we met on facebook.
  "Ummi ta d'an juya idanunta kafin tace " K'warai na tuna,  ba kince 'yar gidan Tahir Marafa Dukku ba,  me neman takaran kujeran shugaban k'asa.
  "Zahida tayi saurin gyad'a kanta kana tace " Eh ita fah Ummi,  she's getting married in couple of weeks, so..... So....  Ta d'anyi shiru don tunanin abinda take shirin fad'i.
  "Ummi ta rik'o hannayenta cikin nata kafin tace" uhum go ahead.
  "Dama Ummi tunani nake ko Mai martaba zai barni naje...

   "D'an kallonta Ummi tayi gamida sauk'e ajiyan zuciya don kuwa tasan abu ne mai kamar wuya.
  "Girgiza kai tayi kafin tace " Zahida kinsan halin mahaifinki,  kinsan irin kula da tsaron da yake baki bazai yarda ki tafi wani gari biki ba, bikinma na k'awa duka nasan shima na iya zuwa d'aurin aure amma kinsan bazai barki ba,  don haka Karma kisa wa ranki abinda ba samu zakiyi ba.  Idan ban manta ba rabonki da yin tafiya mai tsawo tun azumi da muka tafi harami don gudanar da Umra,.

   "Zahida fuska a turb'une tace " Ummi ina son sarauta amma ko kad"an banson wann kulle da ake wa matan sarauta, ni shiyasa nafi so ni nazama sarauniyar komai saida iko na,  and that's when da zan ringa barin matan babban gida suna fita kaman sauran mata.... "Ganin magaifiyar Tata ta zuba mata ido tana dubanta yasata gyara zama kafin ta jeho wa Ummi tambaya.
  "Wai Ummi meyasa Abba nashi kullen yayi tsamari, har yau bai barni naci gaba da karatu ba snn yak'i ya min maganar aure har yanzu. Haba we are in a 21st century fah, ai an daina irin wann sarautar,  naga  k'awata Mardiya Saraki d'iyar sarkin Katsina kwatakwata Babanta bai masu irin wnn kullen ita da k'annenta,  Wllhi  Ummi they are leaving their lives like ordinary people.....  Amma miyasa Abba yake haka.


  "Dafata Ummi tayi kafin ta Kai Dubanta ga hoton jaririn dake ajiye gefen bedside d'in Zahida tace " Meyasa kike ajjiye da wnn hoton.
  "Zahida tayi murmushi gamida shafa hoton da hannunta tace " *Hamma Lamid'o Modibbo* saida gaban Ummi yabada damm jin an ambaci sunansa.

   "Zahida taci gaba da fad'in" Ummi wllhi wataran nakanji inama ace nima inada d'an uwa ko 'yar uwa,  jiya na gani cikin d'akin Madaki na d'auko na kawo shi d'akina, ....

   "Ummi tayi kicin kicin da fuska, wai har yaushene iyalanta zasu daina tuna Modibbo Lamid'o,  a zahiri baya taredasu amma tabbas a bad'ini yana tare dasu,  she wants to get rid of him completely.
   "Murmushin da baikai wuya Ummi tayi kafin ta rungumo Zahida tace " Gimbiya Zahida, ke kad'ai kin ishe mu  a gidan nan, muna sonki fiye da komai, a dalilin sonki da yawa da mahaifinki ke maki yake maki wann kullen. Dalili na biyu kuwa.  Ta sake duban hoton Modibbo kafin tace " Tun lokacin da mahaifinki ya rasa Modibbo yake fatan sake samun magajj,  shiyasa koda aka haifeki yake kafaffa da rayuwarki don gani yake kaman kema na iya rasaki.

   "Murmushi Zahida ta d'anyj zuciyarta cike da tahsayin mahaifinta,  mik'ewa tayi kana tace " Ummi barinje wajen madaki na mata alk'awarin zan shiga tayata hira.  Kai Ummi ta gyad' mata kafin tace "A sauk'a lafiya Gimbiya.....

   "Zahida ta dubi Jakadiya dake tsaye bakin k'ofa da sauri Jakadiya ta rusuna ta shiga mata kirari, ba tareda tabi takan Jakadiya ba tayi shigewarta don kuwa tak'i jinin matar gaba d'aya.....


   "Jakadiya ta shigo gamida duban Ummi cikin ladabi,  mikewa Ummi tayi kafin tace "Ki sameni a d'akina, wucewa tayi ba tareda ta tsaya jin me jakadiya zatace ba sabida k'unan da zuciyarta ya shigayi tunda ta kula Zahida gudar jininta ma son wnn maceccen yaron take.


     "Tafe take a hanyar da zai sadaka da Babban gwani da kuma b'angaren Madaki kakarta. Kaman daga sama ta hangesa sai sauri yake.
  "Murmushi yayi sanda shima ya hangeta,  maida masa martanin murmushin nasa tayi kafin tace " Yaya Shatima form where?
   "My Lady!!!!!  Ya fad'i had'i do sadda kansa k'asa lokacin da yake k'arasowa.
  "Kai Ta Shatima ni dan Allah ka daina bani wann girman haka.
  "Shatima yayi murmushi kafin yace "Be abunda kike so ba kenn ko kin daina son sarautar ne?  Ya k'arashe maganar tensely.
  "D'an murmushi tayi kafin tace " kaima kasan bazan daina so ba don ajini na yake kawai dai zan canza tsarin sarautar ne idan na hau....
    "Shatima yayi murmushi mai bayyana hak'wara kafin yace " Haka ne Your majesty, gaba daya suka dara kafin yace " Zahida you'll never change, will you?
  "Abokina dai yanada aiki.....

  "Nan da nan Zahida tayi kicin kicin da fuska tace " Wllhi Karma ka fara, bakasan yanda na tsani wann abokin naka ba......

    "Shatima na dariya yace "Au kema kinsan Khalifah jinin sarauta ne,  kuma kince bazakiyi aure ba sai saraki  toh kinga ai daidain ki knn....


 👌🏾
[1/23, 22:15] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                        26

*©Sameena Aleeyou... ✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum... 📖📚_

*Dedicated To All Victims Of Rape...*


_Dear Lovers kuci gaba da manejin gajerun posts pls, wllhi this days I'm fully occupied ne, will continue adjusting insha Allah .... Luv you all😘_



    "Tafiya Zahida ta soma yi ba tareda ta masa sallama ba, .
   "Da sauri Shatima yasha gabanta yana murmushi, Harara ta kuma galla masa a karo na biyu kafin tace " Ya Shatima Allah zamu b'ata.
  "Still fuskarsa d'auke da murmushi yace " Allah huci ran Gimbiya kuma k'anwata,  kiyi hak'uri na daina.
  "D'an kallonsa tayi dole tayi murmushi don kuwa bata iya juran dad's da Shattima,
  
   "Idan Gimbiya ta barni zan k'arasa Babban gwani wajen mai Martaba. Ya fad'i yana sadda kai k'asa.

   "Murmushi tayi mai fito da asalin kyaunta kafin tace " Saurin me kake ne haka wai.

  "Shattima ya d'ago Taliesin hanunsa gamida girgiza su yace " Wllhi kin gani tun jiya Mai Martaba yake expecting wad'an nan takardun ban kai masa ba, gashi aike na zaiyi zuwa Abuja cikin satin nan da zaran ya kammala sa hannu a takardun.

   "Jin ya ambaci Abuja yasa Zahida ware idanu, inama Mai Martaba zai bari ta tafi tareda Shattima, sanin abune ba mai yuwuwa ba yasata d'anyi murmushi kafin tace " Ya Shattima kuma yaushe zaka dawo idan ka tafi, ...

  "Business trip ne Princess bansan yaushe zan dawo ba gaskiya amma probably bazan wuce sati uku ba.

  "Zahida ta sauk'e ajiyan zuciya kafin tace " Shiknn Allah Ya bada sa'a. Murmushi yayi kana ya amsa da ameen snn suka jera suna tafe, har cikin ransu suna k'aunan juna matsayin yaya da k'anwa.

  "Shattima d'a ne ga mai girma Waziri,  Mai Martaba ya aminta da Shattima sosai sabida hankali da kamala da Shattima kedashi, shiyasa tunda Shattima ya kawo girma ya kammala karatun degree d'insa Mai Martaba ya d'aura sa kan duk wani hidima  na kasuwancinsa. Wanda yawan shigowa cikin gidan da mu'amala da ahalin gidan yasa suka sami shak'uwa sosai da Gimbiya Zahida......


********************

  "Balele ya kallesa a karo na biyu kafin ya sauk'e ajiyan zuciya yace " Umar kayiwa ka cire yarinyar nan a zuciyarka,  bata sonka ta sami madadinka,  da ace tana sonka da ta dawo gareka,  amma bata dawo ba bata waiwayeka ba,  ka k'yaleta tunda ba itace autar mata ba,  ka zab'a cikin 'yammatan da suke sonka ka Aura, amma har yaushe zaka bari tunanin mace ya maida ka haka.....

   "Umar ya jefa d'an k'aramin dutsen dake hannunsa cikin rapin,  kallon wajen yake yana tuna kalan soyayyan da suka sha da Zubaidah a wann waje,  yana tuna nan shine wajen had'uwarsu,  amma Zubaidah ta mance komai taci amanarsa....
  "Kauda kansa gefe yayi  kafin yace " Balele kasan irin son da nake ma Zubaidah,  kasan itace farin ciki na a wann rayuwar,  bazan iya auren wata mace ba face ita,  ko kad'an ban tab'a kawo Zubaidah zata iya min abu makamancin haka ba,  amma babu komai zan manta ta,  zan manta da duk wani abu da ya shafeta,  zan tafi na bar wajen nan, zanyi nesa da garin nan, zan fara daga farko a can yanda babu wanda yasanni...... "Ya k'arashe maganar yana nannad'e handkachip d'in da tab'a basa a hannunsa...
  "Balele ya dafa kafad'ansa yace " K'warai abokina zaka iya aiki a wani garin ba nan ba da sannu Allah zai cire maka ita gaba d'aya daga cikin zuciyarka,  Allah yayi maka jagora.... Bai iya cewa amin ba sai mik'ewa da yayi, a tare suka bar wajen suka nufi cikin gari shida Balele....

*Abuja*

*Dasuki Holding of companies*

 _At the conference meeting_

   "Da mugun mamaki Alhj Jamil yake bin documents d'in da shakka babu sa hannunsa ne akai, yaushe a ina ya amso wad'an nan kud'ad'e,  dafe kansa yayi da hannayensa biyu yana karanto innalillahi.  
   "Daddy ya kuma tura masa takardun in a furious tune yake fad'in" Why why Jamil, Where do you expect us to get that kind of money, you are nothing but a disaster to business..... Shiru Alhj Jamil yayi bai iya cewa komai ba,

   "Sauran shearHolders suka soma maganganu k'asa k'asa.
  "Alhj Maina mahaifin Tariq yace " A gaskiya inada kusan 5%  a wann company and idan aka samu Bankruptcy zaiyi affecting d'ina sosai don Banki ba yarda zata yi ba WA'adin da ta bada yana cika zata mallake company d'in gaba d'aya,  snn Banki ba d'aya ba kuma Bankunan k'asashen waje, so gaskiya inaga zan cire shears d'ina,  anyone from the shear holders wanna join me, Ya k'arashe maganar da alaman tambaya.
  "Nan masu k'anan shears da manyan shears suka soma k'orafi suma.
  "Alhj Kasim da Barr Munir suka shiga basu baki suna nuna masu lallai bazasu bari wann company mai tarin albarka ta ruguje ba.

   "Wakilin Alhj Tahir Marafa yayi gyaran murya kafin yace" *Marafah Construction  Company*  zata saka hannun jarinta, zata ciro 50% daga company d'inta ta saka a Dasuki Holdings,  take Daddy ya washe baki farin ciki ya lullub'e sa suka had'a idanu shida Barr Munir, plan d'insu ta tafi daidai... Da haka aka k'arashe meeting Alhj Kasim ya shaida masu lallai shida k'aninsa zasuyi yanda zasuyi su biya wad'ancan kud'ad'en...
  "A b'angaren Alh Jamil kuwa k'rjinsa ne ya shiga masa zogi da rad'ad'i had'i da wani irin ciwo har ya isa gida......





   "Tafe suke ita da Annah bayan sun ajiye Kamal a makaranta, don yau Annah mussaman ta d'au hutun aiki sabida Zubaidah tana so suyi spending time sosai,  da k'yar Zubaidah tabi Annah saida Kamal yayi ta magiya kafin ta yarda ta rakasu...

   "Daga yanda motar ta ke pake ta hangosu zasu shige gida,  da sauri ta fito daga motar ta nufo su...
   "Zubaidah.......  Ta fad'i tana k'arasowa yanda suke, a tare Zubaidah da Annah suka tsaya cak gamida juyawa, cike da mamaki suke Kallon Kausar,  Zubaidah kam k'irjinta ne ya shiga bugawa da sauri da sauri.
  "Jan hannun Annah ta soma tana fad'in Annah pls mu tafi.....
  'Kausar ta k'araso da sauri ta rik'o hannun Zubaidah tace "Don Allah Zubaidah listen to me I won't take much of your time, pls.... Ta d'an dubi Annah tace pls Annah.
   "Gyad'a kai Annah tayi cike da mamakin wani magana Kausar zatayi da Zubaidah?  Wata zuciya tace k'ila hak'uri zata bata lokacin da tayi kusan kad'eta.
  "Toh ku shigo ciki mana Annah ta fad'i.
    "Kausar ta girgiza kai tana murmushi har lokacin hannunta na rik'e da na Zubaidah kafin tace " No Annah karki damu ba jimawa zamuyi ba, daga haka taja hannun Zubaidah zuwa benchin dake gefen k'ofar gidan, Annah kuwa tayi shigewarta ciki...    



Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:15] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                               27

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum... 📖📚_

*Dedicated To Victims Of Rape...*


    "Meye zaki fad'a mun, a ina na sanki, snn me ya tab'a had'ani dake da har kike son yin magana dake...???
   "A jere Zubaidah ta jeho wa Kausar wad'an nan tambayoyin.

   "Kausar ta karanceta tsaf kafin ta soma fad'ina,  "Nasan zaki iya sani na,  sunana Kausar Marafa, snn wacce tayi kusan kad'eki da mota sati biyu da suka shige a gidan Alhj Kasim Dasuki dake Maitama close Abuja, still nice Fiancee d'in Salim Dasuki....."Sunan Salim data ambata yasa Zubaidah saurin mik'ewa, Kausar tayi saurin rik'o hannunta.
 
   "Malma ki sake ni na tafi, babu abu d'aya da ya had'ani da zantukan da kike min,  idan kuma bugeni da mota da kika kusa yi ne,  ba laifinki bane, laifi na ne,  don Allah ki tafi ki k'yaleni....
  "Kausar ta sauk'e ajiyan zuciya kafin tace " Zubaidah shin Jalal shi kadai ya maki fyad'e ko harda Salim..???

   "Tambayan da Kausar ta mata yasata fara loosing control, cike da masifa ta fizge hannunta daga rik'on da Kausar ta mata" Cikin kuka take fad'in" Leave me alone,  bansan abunda kike fad'a ba don Allah ki k'yakeni ki tafi and never come back.... Daga haka ta wuce cikin gida da sauri tana k'ank'ame jikinta, tana jawo rigar ta tana rufe jikinta.....
  "Sosai ta bawa Kausar tausayi,  da gani kasan pain d'in abun yana damunta  zaiyi wuya ta sami had'in kanta a yanzu, cikin gidan ta shige itama da sauri....


   "Zubaidah ba tare da tabi takan Annah ba ta wuce d'aki gamida banko k'ofa....
  "Jin haka yasa Annah fitowa da sauri daga kitchen,  a tare sukayi kicib's da Kausar ta shigo gidan.
  "Annah ta kalleta da mamaki kafin ta tambayeta ina Zubaidah Kausar ta ciro wani d'an Card a jakarta ta mik'awa Annah tace " Pls Annah ki bata wann lambar wayata ce when ever she feels ta min magana she can contact me through this number, na gode.....  Daga haka Kausar tasa kai ta fice daga gidan... Annah ta bita da kallo har ta fice kafin ta shiga juya takardan hannunta tana kallo.....



   "A daidai k'ofar fita daga gidan suka had'u da Jalal,  kallon mamaki yabita dashi,  ita kuwa k'ak'aro murmushi tayi kafin tace " Jalal kayi wuyan gani, d'an maida mata murmushin yayi kafin yace " Me ya kawo ki nan...

   "Kausar ta sauk'e ajiyan zuciya kafin tace " Jalal abunda nake son tambayarka nasan tanada nauyi but please be honest with me and tell me the exact truth.

   "Jalal ya kuma binta da kallon mamaki kafin yace "Umhun inajinki go ahead.

   "Jalal nasan ku hud'un nan ba'a raba ku, kai Salim Labib da kuma Tariq, Don Allah ka fad'amun gaskiya " Are you the rapist or all of you, pls tell me if Salim was involved?... I was told that you're the guilty one,  pls ka fada mun iyakar gaskiyarka....

   "Take idanunsa suka kad'a sukayi ja, tambayar data masa yayi matuk'ar sosa masa rai, but he don't want to ruin everything, he's doing this for the girl..
  "D'agowa yayi ya dubeta kafin yace " Gaskiya suka fad'a maki Salim ya fad'a maki iyakar gaskiyarsa,  now that you learned the truth kar ki sake dawowa nan pls kinji na rok'eki....

   "Kausar da jikinta yayi sanyi ta gyad'a kai a hankali kafin tace " Bazan sake daowa ba insha Allah,  your wife told me thesame...... "Da sauri ya dubeta kafin yace " You mean you talked to Zubaidah????

   "Gyad'a masa kai tayi a hankali.......


   "Fuskarsa cike da damuwa ya furta "Oh nooo,  cikin sauri ya shige gidan Kausar ta bisa da kallo har ya b'ace mata kafin ta nufi yanda ta paka ride d'inta......




     "Bai samu kowa a tsakar gida ba don haka kai tsaye d'akin Annah ya nufah......

  "Yanda ta gansa ya shigo parlorn cikin sauri yasata k'walla wani irin k'ara ta tak'ure jikin garu tana k'ank'ame jikinta.....  A hanzarce Annah ta nufo parlorn,  shi kuwa Jalal ko motsi ya kasa sai kallon da ya bita dashi.....


    "Annah ta watsa masa mugun kallo kafin ta k'arasa ta rungume Zubaidah tana rarrashinta....

   "Jikinsa a sanyaye ya ajiye b'akar ledan da ya shigo dashi kana ya fice,  d"akinsa ya wuce gamida zama bisa katifa...
  "When will all these end??  When?  When?????  Kwanciya yayi bisa gado tausayin kansa da rayuwar da yake fusakanta suka cika zuciyarsa.....


    "Wayanta ta ciro tayi dialing lambar Asmah snn ta saka a speaker... Bugu uku Asmah ta d'aga.

  "Hello Barrister kina gida ko school??

"Daga d'aya b'angaren Asmah tace " Ina school, akwai wani abu ne, ??

 "Okay shiknn sai kin dawo gida we need to talk ASAP.

"What for, maganar me bani hint you sounds serious....

"Okay amma driving right now, when I get home I'll call you back....

"Wait driving, ina kikaje da safen nan, ?

"Suleja  naje...

"Suleja, suleja,  wajen wa,  Asmah ta tambaya cike da mamaki.... Kufa Journalist d'in nan kuna da bin diddigi don kunfi mu lawyers ma...

 "Kausar tayi murmushi kafin tace "We will talk at home...

"Okay bye...

"yeah see you then......  Daga haka tayi hanging up zuciyarta cike da jin dad'i at least yanzu tasan Salim d'inta is innocent, zata ci gaba da shirin biki da k'warin gwiwarta........



    "Ko office bai fice ba sabida zafi da k'irjinsa ke masa, ciwo kaman wasa babu yanda Mami batayi a kira Family Dr dinsu ba Alhj Jamil yak'i yarda,  Labib ne ya shigo fuskar sa cike da damuwa ya k'arasa ya d'an zauna gefen gadon da mahaifinsa ke kwance, ya dubi Mami dake k'ok'arin had'a masa tea kana yace " Wai Mami har yanzu yak'i yarda a kira Dr d'in, mik'ewa yayi yana k'ok'arin ciro wayarsa a aljihu yake fad'in "I'm calling Dasuki Hospital Mami, bazamu biye nasa ba..... "Bai gama yin shiru ba yaji Dad d'insa ya rik'e hannunsa, juyowa yayi yana dubansa da alama bakinsa ya karkace....  Hannun Mami ya rik'o ya had'a dana Labib, cikin muryarsa da bai fita sosai  ya soma fad'in
  "Na bar maku amanar junan ku,  Labib kabi mahaifiyarka snn kema ki kula dashi and pls protect him........ "Baki na rawa  Labib yake fad'in" No no Dad pls stop saying all this,  you gonna get better, we taking you to the hospital right away, Mami kam ta kasa nagana sai k'unshe bakinta da tayi tana kuka..... Labib duk ya daburce ya rasa wanne zaiyi,  k'walla kira ya shiga yi wa ma'aikatan gidan,  Alhj ya kuma rik'e hannun Labib gam kafin yace " Be careful with your uncle son..... Daga haka suka ji kaman yana salati dukda muryar ba sosai take fita ba....  Cikin mintuna k'alilan suka ji difffff komai ya tsaya........





Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:16] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                            28

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum... 📖📚_

*Dedicated To All Victims Of Rape...*



   "Jijjigasa ya shiga yi da iya k'arfinsa yana fad'in " Dad Dad,  no pls wake up Dad....!  Kuka mai k'arfi ya kufce masa sanda ya rungume Dad d'insa da k'arfin gaske yake kuka yana ambatan sunan sa,  bai kula da Mami ba da tuni ta sume, ...

   "K'aran kukan Labib da suka jiyo yasa sata nufo d'akin d'akin babu shiri,  Iya Dala ta Saki salati ganin Alh Jamil tamkar maras numfashi ga Labib na kuka rungume dashi,  wani k'arin tashin hankalin shine hango Mami datayi zube a k'asa tamkar bata numfashi.
   "A tamanin Iya Dala ta fice ta nufi gidan Alh Kasim...


   "Yanda Mummy ta ganta gaba d'aya a rikice yasa hankalinta mugun tashi,  gankalinta bai gama tashi ba saida taji labarin da Iya Dala ta kawo mata....
   "Momy duk ta rikice da k'yar ta iya duban Jane tace ta kira Company a fadawa Daddy ya dawo gida babu lafiya,  a tare suka nufi gidan Alh Jamil ita da Iya Dala,...

  "Tsaye yake a saman penthouse(sashensa) d'insa ya hangi Momy da alama bata san yanda take jefa k'afafunta ba,  ai babu shiri ya sauk'o ya nufo su..

  "Momy lafiya meke faruwa?  Salim ya tambaya cike da damuwa ganin hawaye a fuskar Momyn tasa..  . Rungumesa tayi tana kuka take fad'in" It's your uncle Salim.... "Gabansa yayi wani irin fad'uwa,
  "A hankali ya furta "My uncle, what.... What happened to him Momy...
  "Jawo hannunsa tayi suka nufi gidan tana fad'in I don't know Salim, let's go and find out......



   "Sosai hankalinsu ya tashi da irin abinda suka gani,  Mami dai ta farfad'o da aka yayyafa mata ruwa,  Alh Jamil kam sa'i yayi don kuwa ya amsa kiran mahaliccinsa,...

   "Rungume gawar mijinta tayi tana kuka mai tsuma zuciya, " Jamil kar ka tafi ka barni,  bazan iya juran rayuwa cikin rashinka ba,  don Allah kar ka tafi ka barni mijina.... Momy da itama hawayen take ta k'arasa ta rungumeta tana rarrashi...

  "Labib yana ganin Salim suka rungume juna yana fad'in" Salim tell me my Dad is'nt dead, tell me he will wake up, tell me he can go through this,  tell me I'm not gonna loose him.... Sosai Salim Ya rungumesa hawaye shima na k'ok'arin kufce masa....


  "A kid'ime Alh Kasim da Dr suka shigo cikin d'akin,  Alh Kasim tamkar mutumin arziki ya k'arasa kan d'an uwan nasa yana fad'in" Jamil my brother, what on earth is happening to you??  Dr ne ya matso ya shiga yin aikinsa,  ya buk'aci su d'an basu waje, gaba d'aya suka fice parlour....


   "Alh Kasim da Barr Munir sai kai komo suke saika rantse har ransu abin damunsu yayi....

    "Dr ne ya fito daga d'akin jikinsa a sanyaye, gaba d'aya suka nufo sa suna son jin ba'asi.....
   "Alh Kasim yace " Dr ya d'an uwa na,  wani hali yake ciki,  kafin Dr ya bud'e baki Labib ya rik'o hannunsa yana hawaye yake tambayarsa" How's my father Dr,  tell me I can see him right now and he can talk to me.....

   "Sauk'e ajiyan zuciya Dr yayi kafin yace " I'm sorry there's nothing I can do, sorry for your loss....

   "Tashin hankali maras misaltuwa suka shiga idan ka d'auke Alh Kasim da  Barr Munir Wanda hakan ba k'aramin farin ciki ya jefasu ba,  burin Alh Kasim na mallakan Dasuki Holding ba tareda k'aninsa ba ya cika,  matansa da d'ansa kuwa abune mai sauk'i....


   "Abunka da babban mutum kan kace me an yad'a a kafafun watsa labaru, kan kace me gidan ya cika fal da jama'a....


  


    "Suna zaune a barander suna tsinkan zogale itada Annah, dukda bata san dadin uwa ba amma tabbas tana jin dadin zama da Annah,  tana jin kaman ta sami wani abu ne wanda a da bata samu ba a iya zamanta da Hadiza,  jefi jefi Annah take janta da hira.
 
  "Kamar wacce aka wurgota haka Hadiza ta diro masu aka kunnenta manne da Radio sai faman k'ara murya take tana fad'in" Kuji k'anin Alh Kasim Dasuki,  Alh Jamil Allah ya masa rasuwa yau da safen nan..... "K'irjin Annah ya yanke ta shiga karanto innalillahi.....  A b'angaren Zubaidah kuwa ko kad'an basu bata tausayi ba tunda tasan  mahaifin Labib ne, k'arshema tashi tayi a wajen ta shige d'aki abinta,  Hadiza tabi bayanta da kallo don yanzu ko maganar arziki bai shiga tsakaninsu.....




  "Alh Kasim na zaune at the center a babban parlonsa da aka wangame gaba d'aya don Karb'an gaisuwa, mutane sai tambayan Labib suke suna so su masa ta'aziya, ciki harda su Alh Marafa da sauran tawagansa na siyasa,  da kuma tawagan Ministoci da sanatoci da dai manyan 'yan kasuwa masu fad'i aji a garin Abj,
   "Daddy ya kalli Salim yace " ina d'an uwanka?
  "Salim yace " Yana penthouse d'ina,  Daddy ya gyad'a kai yayi kafin yace "Okay Daddy ya nufi sashensa.....


    "Zaune ya taddasa ya k'urawa aquarium d'in dake gefen closet d'insa ido,  bin kifayen ciki yake da kallo amma hankalinsa gaba d'aya baya wajen,  Maganar mahaifinsa na k'arshe ita tafi yawo cikin zuciyarsa *Be careful with your Uncle* meyasa Dad zaiyi wnn furuncin,  tabbas idan ya gano Alh Kasim has anything to do with his father's death, he will kill him for sure...  Dafasa da Salim yayi ne ya katse masa tunanin da yake.

   "Kallo d'aya ya masa ya watsar,  Salim ya d'an zauna gefensa gamida jero masa kalamai masu taushi "
  "Labib you need to be strong for your Mom, idan kai namiji ka kasa jurewa ya kake tunanin mahaifiyarka zatayi, she needs you now,  she needs you more than ever, pls be a Man I know you can go through this, besides you are not alone,  you have us all,  together we will through this as a family,  tashi muje people are waiting for you to give you their condolence greetings,  Daddy yace ka fito they are all waiting for you....


    "Jin ya ambaci Daddy yasa sa kallonsa kaman zai mik'e sai kuma ya zauna yana girgiza kai yake fad'in" Kaje kawai Salim banjin dad'i, pls ka rufe mun k'ofa idan ka fita....
   "Da mamaki Salim ke kallonsa kafin yace " Haba Labib daurewa zakayi mekake tunanin zanje nace wa manyan mutanen da suke jiranka, haba haba,  saikace wani k'aramin yaro.....

  "A harzuqe yace " I said leave me alone Salim, I f go out there, I'm pretty sure I'll see that Bastard and I assure you things are gonna get out of control, so leave pls,  go tell them what ever you think.... Daga haka ya koma gaban window ya shiga kallon waje......


   "Da mugun mamaki Salim yake dubansa, zaiyi magana knn Tariq ya shigo don yaji shirun yayi yawa daga fitan Salim yaje ya shigo da Labib sun kwashe mintoci....

   "Kallon Labib dake tsaye bakin window yayi kafin ya dubi Salim,  alamun tambaya ya masa da ido,  Salim ya ware hnnaye gamida bud'e idanu alamun bai sani ba.....


    "Tariq ya k'arasa ya rik'o kafad'un Labib yace " Let's go Labib, . "D'ago kai yayi ya dubi Tariq kaman raqumi da akala haka ya soma binsa,  Salim ya d'an fuzar da iska gamida bin bayansu,  cike da mamakin maganganun da Labib yayi,  a iya saninsa Labib kwana biyu bai tari fad'a da kowa ba toh ko da waye yake yi sai Allah.......




   "Har ya gama gaisawa da illahirin mutanen dake parlorn idonsa akan Alh Kasim yake,  banda watsa masa mugun kallo baya komai,  kai k'arshe har Labib ya bar parlorn idanunsa na kan Alh Kasim,  gaba d'aya Alh Kasim yasha jinin jikinsa da irin kallon da Labib ke masa,  a hankali ya saci jiki yabi bayan Labib.....





Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:16] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                          29

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_

*Dedicated To All Victims Of Rape...*



     "Har aka gama kwana uku basu gane kan Labib ba,  wuni yake zubur a d'aki ba tareda ya shiga sabgan kowa ba, ranar da Alh Jamil ya cika sati guda cif da rasuwa Daddy ya had'asu a parlor,  Mami Labib da kuma Barr Munir.
  "Banda mugun kallo da yake watsa ma uncle d'in nasa baya komai...

   "Ko darajar gaisuwa basu samu daga Labib ba, .
   "Alh Dasuki yayi gyaran murya ya soma magana dangane da business d'in marigayi Alh Jamil, kama daga yawan shears d'insa dake Dasuki Holding bashin da ya ciwo daga bankunan k'asashen waje, k'arshe ya tabbatar masu Alh Jamil bashida single cent da yayi saura a Dasuki Holding sabida mak'udan bashusshukan da ake binsa...... Ai bai ida rufe baki ba Labib ya mik'e yayi kansa gamida cakumo bababban rigarsa yana fad'in" How dare you Kasim Dasuki,..... Mami a zabure ta mik'e tana daka wa Labib wani irin tsawa,  Barr Munir yayi saurin k'watar mai gudansa...

  "Finciko Labib dake kan faman huci Mami tayi tana watsa masa mugun kallo mamaki ya hanata magana, "Har lokacin bai dana huci ba yake nuna Alh Kasim da d'an yatsa kafin yaci gaba da fad'in" Mami let me teach this Man a lesson, how dare he zaice Dad bashi da single cent a company d'in da kowa yasan hard working d'insa ne, wllhi kayi kad'an Kasim Dasuk...... "Muryarsa ne ya sarke sanda yaji sauk'an wata mari meji da lafiya a k'uncinsa,  d'agowa yayi yana duban Mami dake faman huci ga hawaye na bin k'uncinta....
   "Rik'e k'uncinsa yayi yana dubanta da mugun mamaki,  abune da tun tasowarsa babu wanda ya tab'a masa,  mugun kallo kawai yake watsa wa mahaifiyar nasa kafin ya soma fad'in" Mami you slapped me because of this worthless Man, Mami wllhi na tabbata Dad bai amso bashi ba, idan ma ya amso toh for the sake of the company ne, snn na rantse Alh Kasim was behind my father's death......"Labiiiiiib....!
   "Mami ta daka masa wani irin tsawa hawaye na bin k'uncinta,  Daga Alh Kasim har Barr Munir mamakin Labib ya hanasu koda motsawa...

   "K'arasowa yayi gaban Alh Kasim kafin yace " Sai na zama ajalinka, ka rubuta ka ajiye....  Daga haka ya wuce sama yana tafiya kamar wani kububuwa.....  "Durk'usawa Mami tayi a wajen ta shiga rera kuka....

   "Mik'ewa Alh Kasim yayi yana sab'a babbar rigarsa ya fice a parlorn, zuciyarsa kuwa tamkar zata fashe,  wai shine Labib ke gaya masa maganganun da duk duniyar nan babu wanda ya tab'a gaya masa yana a matsayin yayan mahaifinsa,  lallai kuwa zai saita yaron nan yanda baya tsammani. 

   "Kai tsaye office d'in cikin gidansa suka wuce shida Barr snn ya danna wayar Faisal yace yazo yana bemansa urgently......



   "Annah ta dubesa a karo na biyu kafin tace " Kaje kayiwa su Labib ta'aziyan.
  "Ajiye spanner d'in dake hannunsa yayi gamida goge gumin fuskarsa kafin yace "Annah zanje yau insha Allah da zaran na tashi a aiki,
  "Gyad'a kanta tayi kafin tace " Toh shiknn make sure kaji pls, dan idan baka je ba yaukam nida kai za'ajimu,
   "Murmushi yayi mai bayyana dimples d'insa kafin ya goge bak'in man da ya b'ata masa hannu ya kamo hannayen Annah yace " Annah na Annahn Jalal na maki alk'awarin zanje insha Allah.
  "Murmushi tayi kafin ta gyad'a kai tace nasan zakaje Jalal,  Allah shi maka albarka,...."Usman ne ya k'araso wajen yana fad'in" Ah ah Annah har kin gama kallon shagon namu, ni nan nazo na zagaya dake wajen da ake gyara manyan motoci ne....
   "Annah ta murmusa tace "Kar ka damu Unman ai na gani a haka ma,  ubangiji ya dafa maku cikin sana'arku.... Ameen suka amsa dashi baki d'aya fuskokinsu d'auke da murmushi.

  "D'an bubbuga hannun Jalal tayi kafin tace" Toh Jalaludden ni zan wuce gida na bar Zubaidah ita kad'ai, ta juyo ta dubi Usman dake tura tayan mota tace " Usman Allah Ya saka maka da mafificin Alkhairi,  ga boy d'ina ka kulamin dashi....  Murmushi Unman yayi kafin yace " Ai babu komai Annah ai nida Jalal abu guda ne, kuma insha Allah zan kula dashi kamar yanda kikace ya k'arashe maganar yana dariyawa Jalal,
  "Harara Jalal ya watsa masa kafin ya k'arasa ya rik'o hannun Annah suka fice har waje ya tare mata adaidaita, har saida yaga barinsu wajen kafin ya dawo cikin workshop d'in..

   "Unman sai masa dariya yake wai anya ba shagwab'a yake wa Annah ba shiyasa take treating nasa like a kid.
   "Murmushi da gefen bakinsa yayi kafin yace "She's always like that, and I love her so much, she's my parents, bansan dad'in mahaifi ba sai nata, she was my only family until Zubaidah came into my life....
   "Jikin Usman ya d'anyi sanyi da jin kalaman Jalal, .... Shiru ya d'an biyo baya kafin Usman yace " and you're very lucky to have them as family she and your wife Zubaidah.....  "Kallonsa Jalal yayi kafin ya gyad'a Kai a hankali yace "Yeah I know....  A wani b'angare na zuciyarsa kuwa tunani yake anya shida Zubaidah zasu iya kasancewa wann family d'in kuwa, kai abun da kamar wuya tunda already ya amince zai tafi ya bata waje tasha iska, k'ila idan ta jima bata gansa ba ta mance komai...... "K'aran horn ne ya dawo dashi daga duniyar tunanin da ya tafi....



      "Wata rantsattsiyar BMW 2016 ne ta shigo cikin garejin gyaran motocin, gani yayi Usman ya mik'e da sauri ya nufi mai motan,  handshake sukayi fuskokinsu d'auke da murmushi kafin yaji Usman yace "Allah taimaki Shattima, Allah k'arawa Shattima tsawon rai.... Dariya sukayi su duka biyu kafin Shattima yace "Likitan mota Allah ya shiryaka,  wato dai bazaka daina min wann tsiyar ba,  Unman ya kuma yin gajeren Dariy kafin yace" Rankashidad'e irin gaisuwar data kamaceku knn..
   "Murmushi kawai Shattima yayi kafin yace " Kasan meye wllhi sauri nake zan wuce Kaduna yanzu yanzun nan shine nace barin zo ka kwance min wad'an nan tayun don jiya na iso Abuja kuma tun jiyan nake jin kaman suna rawa ...


  "Wai urgent kake so,  gaskya saidai ka barta ta kwana a nan don wllhi ni yanzuma gidan abinci muka nufa, cewar Usman

 "Haba Car Doc,  kar muyi haka wllhi idan sak'on nan bai isa Gombe jibi ba ran Mai martaba zai baci kaga bai kamata ayi failing d'insa ba.

   "Usman ya d'an tab'e baki kafin yace "Toh wai kai inji ne,  daga Gombe ka nufi Abuja daga nan Kaduna ka kuma dawowa Abuja snn ka koma Gombe shin bazai maka uzuri ba,  kai sudai masu mulkin nan izza da isa ne dasu, yo ba dole mota kullum a gareji ba...

  "Gajeren tsaki Shattima yayi kafin yace "Wllhi kaifah kanada iskanci Usman, ce maka akayi mai Martaba na magana biyu,  yarda dani da yayi ai shiyasa ya d'aurani kan hidimominsa,  snn wann sunnar sarakuna ne basu magana biyu.
"Kai Why do I have to explain my self ma,  gyara ne dole ka mun yanzu yanzun nan...
 
  "Nannad'e hannayen rigarsa yayi ya sunkuya gamida wanke hannunsa da ruwan dake a cikin buta,  ya d'iba yana d'an buge wondon jeans d'insa ba tareda ya kuma ce ma Shattima komai ba.

    "Karya k'afa kawai Shattima yayi gamida turo hula gaban goshi yana kallon Unman cike da mamaki,  koda ke ba abin mamaki bane idandai Unman ne yayi fin haka.
 
  "Jalal muje idan ka gama ya fad'i haka yana k'arasawa wajen Jalal da ya canza kayan jikinsa daga blue uniform d'insu na aiki zuwa shirt da Jeans, fuskarsa ruwa ya kwanta luff...

    "Wanda aka kira da Jalal Shaittima yake kallo,  haka kurum ya tsinta kansa da fad'uwan gaba, snn wann daga gani miskilin k'arshe ne don ko kad'an Shattima bai kawo akwai wani a wajen ba  don tun fara maganarsu kanzil bai furta masu ba.

   "Shattima ya k'arasa gamida mik'a masa hannu yayi masa sallama,  a tak'aice Jalal ya amsa sukayi masabaha. Shattima yace "Don Allah Jalal ka taimaka min kar ka biye na wann maras kirkin wllhi tafiyace a gabana,  kuma ni idanba wann garejin ba bana zuwa ko ina,  ni shinema in particular yake gyara min mota,  don yaga na rik'e amanarsa ne shiyasa yake min wulak'anci.....

    "Usman ya katse sa dariya gamida zubar da ruwan dake bakinsa kafin yace "Ayya mai sarauta ai kuka kakai gidan mutuwa idan dai wann ne ya fini dizgi barikaji,  don shi har backing d'insa ake, wann da kake gani ma sana'arsa ma miskilanci yake shiyasa nake son zuwa naga wani irin tarairaya matarsa ke masa.....


   "Kallon Unman kawai Jalal yayi gamida girgiza kai kafin ya dubi Shattima yace "Am kar ka biye nasa nidashi zamu duba maka yanzun nan....

   "Kutt zaka duba masa dai don ni wllhi yunwa nakeji.  ..... Baibi takansa ba sai jifa masa kayan aikin dake hannunsa yayi.  Shattima kuwa me zaiyi banda dariya ganin yanda Jalal yasa dole suka soma duba masa mota....


  "Mintoci kad'an suka gama d'aura masa wasu tayu had'i da warming motar abinka da k'wararru.  Hararansu kawai Unman keyi,  k'arshe daga Sbattima har Jalal dariya suka ringa masa Shattima yayita rok'onsu Allah Annabi suje suci abinci tare a eatery fir Jalal yak'i amincewa don shi alk'awari ya d'aukar wa kansa bai kuma rab'an wani mai abin duniya..
   "Haka dole Shattima ya hak'ura ba don yaso ba,  Usman kuwa mita yayita masa wai ai don yasan yanada mata me girka masa a gidane shiyasa yak'i amsar tayin Shattima,  Tab'e baki kawai yayi kafin yace "Ai ban rik'e k'afarka ba, a tak'aice..

"Har yau Unman baisan me ya had'a Jalal dasu Labib ba shi dai kawai yasa ma ransa lokacin shiryuwan Jalal ne Allah ya kawo har yayi aure snn ya nisanta daga su Labib.......



  "Ya jima yana kalllan k'ofar gidan kaman bazai shiga ba, sai kuma ya k'arasa yayi sallama wa securities d'in kafin yace "Su masa iso da Labib,  gaba d'aya mamaki ne ya ishesu don kuwa sunsan a baya Jalal bashida shamak'i da gidan amma gashi yau neman iso yake.

 "Babu musu d'aya daga cikinsu ya d'aga land-line d'in dake gate d'in ya kira cikin gida ya isar da sak'on Jalal....





  "Mintuna k'alilan Labib ya fito don yasan ko yace ace Jalal ya shigo ba shigowan zaiyi ba......

  "Tun daga nesa suke hango juna,  for the first time da Jalal yaji tausayin Labib tun bayan incidence d'in da ya auka masu,  gaba d'aya Labib yayi looking aabuntausayi shakka babu mutuwar mahaifinsa ya shiga jikinsa....
      "Gaisawa sukayi ta hanyar musabaha kafin Labib yace "Mu k'arasa ciki mana,.
    "Girgiza kai Jalal yayi kafin yace "No ba jimawa zanyi ba,  I just came to say sorry for your loss,  Allah Ya jik'ansa ya gafarta masa...
    "A sanyaye Labib ya amsa da "Ameen, na gode Jalal.

  "Jalal ya d'an dafa kafad'arsa kafin yace "Babu komai,  ka gaida Mami pls sauri nake..... Ni zan wuce,

   "Har ya juya yaji muryan Labib ya kira sunan sa
.   "Jalal!

   "Juyowa yayi yana dubansa,  har gavansa Labib ya k'araso kafin yace " Na gode k'warai,  and pls ka yafe mana abunda ya fraru a baya..

    "Jalal ya d'an saka hannunsa cikin aljihun wandonsa kafin yace " Nasan kun bani k'waya nasha a daren sabida hankalina ya gushe ku cimma burinku akan yarinyar,  kar ka damu ni na yafe maku wann,  abunda bazan iya yafewa ba shine,  I'll never ever forgive my self Labib,  snn tsakaninku da yarinyar wnn babu nawa a ciki,  idan ta yafe maku fine,  abunda na sani shine na aureta ne to protect her,  and I turn out to be her worse enemy, well I promise her zan tafi far away from her until she forgets everything, I'm pretty sure my Mum will take care of her har naje na dawo......

      "Labib ya shafi gashinsa cike da kunyar kansa ko ince guilty conscious da ganin idon Jalal, don kunyar duniya da Labib sunyi hannun riga.....

     "I'm happy for you bro,  I wish you success in life Jalal,  ya karsa gamida hugging kafadarsa,  sallma sukayi Jalal ya wuce,  har ya b'ace ma ganinsa kafin ya shige gida......



*Gombe,  Dukku*


Baffah ya kallesa a karo na biyu kafin tace " Ka tabbata tafiyan shi yafi maka zama damu a nan.
  "Ummar ya rataya jakarsa a kafad'ansa kafin yace "Baffah kar ku damu insha Allah zan dawo nan bada jimawa ba, snn na tabbata aikin da zan samu a wani garin zai fiye mun nan,  snn zan manta da Zubaidah mantawa ta har abada.....
  "Innah ta murmusa gamida goge k'wllan da suka zubo mata ta k'arasa ta dafa kafad'arsa,  addu'an samun nasara suka masa daga ita har Baffah,  suna d'agawa juna hannu har ya fice daga gidan.....


   "Har bakin tasha Balele ya raka sa yanda ya shiga motar da zata fitar dashi zuwa Gombe,  daga Gombe naga ya nufi motar danaji ana kiran garin *Abuja*


_Toh fah readers ga Umar ya tunk'aro garin Abuja,  shin Me kuke tunanin zai faru,......? Jalal yana gab da barin Zubaidah.....  Would she be safe??????_


Ku biyo QueenSamy don samun amsoshin.......


Sameena ce
[1/23, 22:16] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                               30

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum... 📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*



   "Wata kyakkyawar budurwa ce a gefensa wanda ak'lla bazata gaza shekaru 24 ba,  farace tass amma saidai daga ganin farin zaka gane akwai surki da man kanti, tufafin dake jikinta kuwa kaida ka gani kasan me tsadan gaske ne, a hankali take taunar chewing gum kaman bata son yi.
  
   "Tun zamansa ta kafesa da idanunta,  sosai ta kwad'aitu dashi, jikinsa ne ya basa ana kallonsa, d'an juyowa yayi aikuwa nan sukayi ido hud'u,  murmushi ta sakar masa har lokacin idanunta na kansa, 
  "Bai maida mata martanin murmushinba saima kallon window da ya soma yi, budurwar ta ciro wayarta k'irara iPhone7 ta soma dannawa....


   "Har suka kusa shigowa garin Abuja wann budurwa bata daina bin Umar da mayen kallo ba. Gaba d'aya ya tsargu da irin kallon da take masa,  suna isowa tasha kowa ya soma fita daga motan.

   "Raba ido ta soma yi tana neman ina ya shige, zaune ta hangosa saman wani benchi yana kallon mutane masu kaikomo, murmushi tayi kafin ta k'arasa wajensa cikin salo na tafiya da dogon takalminta mai d'ankaren tsini...

   "Sannu bawan Allah, ta fad'i daidai sanda ta k'araso yanda yake zaune.
  "D'ago ido yayi ya dubeta,  tsaf ya ganeta budurwan nan ne wacce ta tsaresa da kallo a mota.
   "A tak'aice ya amsa mata daga haka bai kuma cewa komai ba,..
  "K'ok'arin zama ta soma yi gefensa yayi saurin mik'ewa tsaye yana binta da kallon mamaki kafin yace " Baiwar Allah lafiya kike bibiyata...

   "Murmushi tayi kafin tace " Da farko dai sunana *Zulaihat* snn ba bibiyarka nake ba hanyace dai ta had'amu,  da alama Kai bak'o ne a garin nan,  don naga kowa na watsewa kai kana zaune,  snn dokar wann tashar idan ka wuce lokutan rufewa za'a cika tara. Amma kodayake bansan dalilinka na zama a nan ba, ina ka nufa???

   "D'an kauda kansa gefe yayi yana rage girman idanunsa kafin yace " K'warai ni bak'o ne a garin nan,  snn kamar yanda kika fad'i vansan dokoki da tsarin tashar nan ba,  na gode k'warai da kulawarki ni zan wuce,  daga haka ya sab'i hakarsa ya soma tafiya 

   "Kallo tabisa dashi har ya nufi gate,  d'an sauk'e ajiyar zuciya tayi kafin ta ciro wayarta cikin jaka ta shiga neman layin d'aya daga cikin samarukanta da take wanka...

   "Hello Tariq, pls kazo tasha ka d'aukeni yanzu dawowata daga Gombe....

   "Daga d'aya b'angaren Tariq yace " Uban me kikaje yi a Gombe Zulaihat,  ki fad'a min kiran wani shegen Alhjin kika amsa...

   "Gajeren tsaki Zulaihat tayi kafin tace "There you go again,  shiknn bazanje naga dangina ba how many times do I have to tell you,  Gombe garin iyayenane.....  "Katseta yayi da sauri yana fad'in

" Look karki nemi raina mun hankali na sani sarai daga Yola kika zo Abuja neman abun duniya,  kuma saida kika amince min bazaki sake bin wani ba bayana wato shine kika zaga kika tafi Gombe don kinga kwana biyu ban zauna ba koh,  toh wllhi kikayi wasa zan k'wace makullan gidan dana kama maki haya.....



   "Dalla malam ya isheka,  Why do I even have to explain my self, you don't owe me any explanation, rayuwata ce nayi yanda naso da ita,  kan wani shegen gidan da ka kama min kake neman yimin gori,  wllhi kaima sanin kanka Tariq ni ba ajinka bane kuma kar ka sake nemata daga yau kashe wayar tayi gamida yin k'wafa....


   "D'an gajeren tsaki yayi kafin yayi dialling lambarta,  saida ya kira sau uku tana ejecting kafin a na hud'u ta d'aga tana wani yamutsa fuska,  hak'uri ya soma bata yana lallashinta,  da k'yar ta hak'ura kafin yace " Tayi hak'uri yanzu haka Dad d'insa ya aikesa ne urgent, he can't fetch her but he promised da zaran ya gama da Dad dinsa zaizo...

  "Tana kashe wayar taja tsaki a fili ta furta k'aramin d'an iska,
   "Tana fitowa gate ta hangesa har lokacin na tsaye bakin titi. Murmushi tayi kafin ta k'arasa wajensa....




     "A firgice ya farka daga mummunar mafarkin da yayi,  rufe fuskarsa yayi da tafukan hannayensa kafin yayi addu'a,  mik'ewa yayi ya lek'a barrandan Annah,  zaune ya hangosu ita da Annah suna duba litattafan da aka sayo mata na makaranta daga gani zaka gane suna cikin farin ciki,  don ya nuna a fuskokinsu,  sauk'e ajiyan zuciya yayi yana tuno mafarkin..

  _"Wai gashi nan rataye da jakarsa zai tafi,  har ya soma nisa yajiyo muryar Zubaidah tana k'walla masa kira, juyowar da zaiyi yaji ta rungumesa cikin jikinta,  a hankali yaji tace "Na yafe maka Jalal duniya da lahira,  rungumeta sosai yayi cike da farin ciki ta rakosa har k'ofa,  har ya shige mota tana masa waving tana murmushi......  "Gefe da ita kwatsam ya hango Labib Salim da kuma Tariq suna Torrik'e da makamai suna wani irin dariya.... Da sauri ya fito daga motan ya nufota saidai kafin ya k'araso ya hangi tsohon saurayinta Umar ya sureta da k'arfin gaske yasa gudu,  ihu take tana kiran Jalal,  saidai kafin ya k'araso mota tabi kansa...._

   "A hankali ya sauke ajiyan zuciya,  ya dubi 'yar k'aramar agogon dake mak'ale bangon d'akin ya nuna k'arfe 5:30 na yamma,  bathroom ya shiga ya sakar ma kansa shower sabida zafin da ake sosai a garin....


  "Fitowa yayi cikin shiga ta k'anan kaya, sun karb'esa sosai,  hayi taje gashinsa da yasha aski da gyaran fuska Wanda ya fito da asalin kyaunsa,  kallo d'aya ta masa ta d'auke kanta sanda yake nannad'e hannun rigarsa, tsuka taja a hankali take annurin fuskarta ya d'aukewa ga wani irin fad'uwar gaba data tsinci kanta dashi. D'an karasowa yayi yana satan kallonta yake gaida Annah, Hadiza ne da d'anta Kamal suka shigo.
  "Kamal ya tafi da gudu ya rungume Jalal yana fad'in "Uncle Jay,  rungumesa Jalal yayi yana dariya ya d'agasa sama yana masa wasa,  da gefen idonta ta saci kallonsu,  sosai Kamal da Jalal suka shak'u......
  
   "Gaisawa suke da Annah amma hankalinta naga Zubaidah dake faman shirya littafan gabanta, tab'e baki Hadiza tayi kafin ta dubi Jalal da har lokacin wasa yake da Kamal kafin yab'e baki  tace "
   "Ni ban tab'a ganin irin wann aure ba,  ace miji bashida iko da matarsa halan kai ka bata izinin komawa makaranta,  ta k'arashe maganar tana duban Jalal,..
  "Mik'ewa Zubaidah tayi tana binta da mugun kallo kafin tace " Ni ba matar aure bace kar ki sake kirana matar aure, daga haka ta kwashi books din ta wuce d'aki kaman zata tashi sama.....  "Dariya Hadiza ta kwashe dashi harda rangad'a guda, burinta knn dama ta k'untata wa Zubaidah.... 
   "Daga Annah har Jalal kallo suka bita dashi,  Jalal ya girgiza kai kafin ya sauk'e Kamal dake kafad"ansa yabi bayan Zubaidah......



Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:17] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                              31

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*



     "Da saurin gaske ya finciko hannunta ta fad'o jikinsa,  wani irin yanayi suka shiga su duka biyun,..Yanda k'irjinta yake bugawa da sauri kuwa har cikin jikinsa yake ji.....
   "K'ok'arin k'wace kanta ta shiga yi da iyakan k'arfinta tana fad'in ya cika ta,
   "Kallonta yake fuskarsa a tamke kafin ya shiga jan hannunta.....
   "Tirjewa take tana fad'in "Malam ka cikani nace, ni ba 'yar iska irinku bane,  dalla cika ni ina zaka kaini.....  Bai kuma saurarenta ba sai suranta da yayi ya azata a kafad'a had'ida toshe bakinta da hannunsa.....
  "K'ok'arin ihu take kanyi tana neman hanyar k'watan kanta, Bai ajiyeta a ko ina ba sai d'akinsa..... 
  "Innalillahi jikin Zubaidah ne ya soma kyarma sosai, take ta shiga tuno fuskokinsu,  jada baya ta soma yi tana jawo rigarta tana k'ok'arin rufe jikinta,  tama kasa ihun sai mannewa jikin garu da takeyi tana cije leb'enta tana girgiza kai...

   "Sanda ya zauna gefe da ita,  ta yunk'ura zata tashi had'i da k'ok'arin kwand'ara ihu.....
   "Rik'ota yayi ta fad'o kansa suka zube saman katifar yayi amfani da d'aya hannunsa ya toshe bakinta....  Banda kuka da kyarma da jikinta keyi bata komai....

   "Duk sai yaji babu dad'i it wasn't his intention to scared her...  A hankali ya rungumeta tsam cikin jikinsa kaman me rad'a haka ya soma fad'in" I'm sorry, I didn't mean to scared You, I only want us to talk,  babu abinda zan maki  so pls listen to what I'm gonna say.

  "Jin lallausar fatarsa take tamkar garwashin wuta ne a jikinta,  d'akin kuwa jinsa take tamkar cikin wuta aka jefata,..

   "Jin tayi shiru yasa sa bud'e mata baki still tana rungume cikin jikinsa,.

   "Jalal yaci gaba da fad'in" Zubaidah nasan bazaki tab'a yafemin ba duk da ban aikata laifin ba,  but believe me I will never forgive my self either for not stopping them, I'll live with the pain..... 
  "Jin maganganunsa take tamkar ana zubawa kunnuwanta ruwan dalma dukda dad'i da muryarsa kedashi, toshe kunnuwanta tayi tana ci gaba da hawaye....

   "A haka take fad'in" Wllhi wllhi na tsaneka na tsani ganinka, don Allah ka tafi ka k'yalemin rayuwata ka sakeni kowa yaje yayi rayuwarsa,  na tsani na tuna waini Zubaidah inada auren mutumin danafi tsana  a duniya a kaina,.... A hankali taci gaba da fad'in" Bazan tab'a manta wann fuskar taka ba,  kai ka fara rik'oni a lokacin da nake k'ok'arin tsere ma sharrinku,  lokacin da nake k'ok'arin tserewa mutuncina da martaba ta, duk bakuga wann ba sabida bakuda 'Ya'ya snn baku da k'anne dukanku, kuka k'etan haddi na ba tareda d'and'ani tausayi ba balle imani, sabida kunada masu tsaya maku, aka hanani magana snn aka aura min mutumin da yafi kowa zalunta ta a duniya,  shin kuna tunanin Allah zai k'yaleku, kun lalata rayuwar yarinyar da bata ci maku ba bata sha maku ba, an dunk'ule rayuwata an jefa cikin wani 'yar takarda na kud'i an damk'a maka sabida asirin 'Ya'ansu ya rufu. Ka sani bakufi k'arfin Allah ba da Sannu zai saka min d'aya bayan d'aya...... Kuka ya kuma kufce mata ta shiga matsewa cikin garu kamar wacce ta tuna wani abu....

   "Zogi da rad'ad'i zuciyarsa take masa take idanunda suka kad'a sukayi jazur, tabbas duk abinda Zubaidah ta fad'i haka ne....
  "Kallonta yake yanda ta matse jikin garu tana kuka,  tausayinta ya cika zuciyarsa,  k'ok'arin matsowa kusanta ya soma yi,  tayi saurin d'ago kai had'i da girgiza kai tana fad'in kar kayi gigin matsowa kusana, ka bud'e mun k'ofa na fice....
  "Jiki a sanyaye ya mik'e yayi yanda tace.

  "Da saurinta tazo zata shige yayi saurin tare k'ofar da hannunsa, d'ago kai tayi tana dubansa, gani tayi gaba d'aya fuskarsa tayi ja sosai haka nan idanunsa,  gajern tsaki tayi kafin tace " Malam zan wuce.
  "D'an fuzar da iska yayi kafin yace " Tambaya d'aya nake so na maki....

   "Murmushin takaici tayi kafin tace " Darajar Annah kaci wllhi shiyasa ma na tsaya saurarenka,  tanada mutunci tanada kirki wllhi batyi deserving d'a irinka ba,  so let pass....

   "Gyad'a kansa yayi kafin yace "K'warai she deserves a son better than I, Na sani. Shiyasa  nake so na sake cin darajarta ki amsa min wann tambaya nawa.
 "Idan na tafi zaki yafe mun...

  "Kallonsa tayi gamida kauda kai gefe kafin tace " Har abada bazan tab'a yafe ma d'aya daga cikinku ba,  don Allah ka tafi ka bar rayuwata and never come back...
   "Sauk'e ajiyan zuciya yayi kafin yace " I hope one day you'll forgive me and you'll realize that I'm doing this to protect you....

   "Murmushin takaici tayi kafin tace " I never need your protection snn ko gawarka ce a gabana bazan tab'a yafe maka ba...
  
    "A hankali ya sauk'e hannunsa ya bata hanya kafin ya furta zan tafi as you wish.... Ficewa tayi cikin sauri kaman zata kifa k'asa...


    "Hadiza dake lab'e taga fitowarta daga d'akin Jalal,  tayi saurin k'arasa tasha gabanta tana dariya harda shewa kafin tace " Ashe a gabanmu ne kike gwada baki sonsa baku ko magana,  ashe dai har turakansa kike zuwa,  ayyirririr ni Dije naga Salon soyayyar zamani......
   "Hararanta kawai Zubaidah keyi da idanunta da taci kuka,  wani kukan ne ya kuma kufce mata, cikin kuka take fad'in nidae wllhi ba matar aure bace, kar ki sake kirana matar aure..... Daga haka ta nufi barandar Annah tana kuka.
   "Hadiza tayi wani shewa kafin tace " idan baki sonsa me ya kaiki d'akinsa,  dogon tsaki taja kafin ta wuce tana rangad'awa mijinta kira....


   "Kan Annah ta fad'a tana kuka, har magrib Annah na lallashinta tana akin abu guda....








     "Kallo yake kan faman bin layin dashi,  yanayin mutanen da yake gani suna wucewa ya tabbatar masa babu kamun kai wajen.
  "Juyowa Zulaihat tayi tana dubansa kaman ta gane tunanin da yake tayi d'an murmushi sanda ta saka d'an makulli tana bud'e k'ofar kafin tace " Kaga yanayin layin namu haka ko,  kasan akasarin mazauna unguwar nan 'yan makaranta ne kaman ni, ka kwantar da hankalinka ka saki ranka.

  "Gajeren murmushi yayi sanda tai masa nuni da saman sofa ya zauna.

  "Kayi hak'uri fah gidan nawa babu wani abin tab'awa kasancewar yanzu na shigo garin. Amma barin dafa mana abu me sauk'i.
   "D'an murmushi yayi kafin yace "Kar ki damu masauk'in da kika min ma na gode zuwa gobe zan tafi neman abinda ya kawo ni.

  "D'an murmushi tayi kafin ta cire d'an mayafin dake jikinta,  take suran jikinta cikin matsettsen d'inkinta wanda tamkar a jikinta aka d'inka ya bayyana,  saurin d'auke kansa yayi daga barin dubanta,  tayi wani murmushin cin nasara kafin ta soma tafiya cikin kwarkwasa ta nufi kitchen.
  "Mintuna kad'an ta dafo masu indomie da soyayyen kwai.

   "Gaba d'aya kasa sakewa yayi sabida kayan dake jikin Zulaihat,  rabin k'irjinta a waje yake, snn da gangan take sunkuyawa komai ya bayyana, da kanta tayi serving nasa sai jansa da hira take tun yana basar da hiran nata har ya soma amsata jefi jefi...


   "Amma me ya kawo ka Abuja Umar, nasan bai kamata na maka wann tambayar ba,  but I don't may be I can help.

   "Shiru yayi yana tunani cikin zuciyarsa,  ya fad'a mata ne ko kuma kar ya fad'a mata,  Wata zuciya tace  ka fad'a mata k'ila tasan gidan da kazo nema.

   "D'an karkad'a spoon d'in hannunta tayi saman fuskarsa tace " you there...


   "Murmushi yayi kafin yace" Wani gida nake nema a cikin Abuja ko kin sani.

  "Wani gida kenan, ta tambaya tana dubansa.

 "Gidan Alh Kasim Dasuki.

  "Murmushi Zulaihat tayi kafin tace "Ai duk garin nan babu wanda baisan gidan Alh Dasuki ba,  k'ila ta'aziya kazo masu.

   "Baison jan zancen Don haka kai tsaye ya gyad'a mata kansa ba tareda yace Komai ba, a fili yace zaki bani adress din gobe insha Allah.
   "Ba tareda ta kawo komai ba ta gyad'a kanta kana tace " Yeah sure,  for now finished your food I'll right back ta fad'i tana mik'ewa.

  "Gyad'a kansa yayi a cikin ransa ya furta " JALAL, kwanan ka ya k'are your dead has arrived...


Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:17] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                             32

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_

*Dedicated To All Victims Of Rape...*



    "Shiru Zulaihat tayi tana tunanin anya batayi gangancin sauk'an stranger a gidanta ba,  wata zuciya tace " But You fell for him the very moment you saw him.
   "D'an jimm ta kuma yi kafin zuciyarta taci gaba da ayyana mata "Anya kuwa bazata kira Tariq ta tambayesa ba tunda he's related to the Dasuki's,  toh kuma idan kika kira sa fah,  what about your plans for this hot guy da kike tsananin sha'awan had'a jiki dashi?.. Just let him be, ki zuba masa ido kiga gudun ruwansa snn kiyi k'ok'arin samun abinda kike nema wajensa.. Da wann tunani Zulaihat tayi murmushi kafin ta mik'e ta nufi parlor cikin wasu arnan kayan baccinta wanda suda babu dangin juna ne.


    "Yanda ta barsa kishingid'e kan sofa haka ta dawo ta taddasa,  kafe sa da ido tayi komai nasa ya burgeta, irin mazan da take tsananin son huld'a dasu knn, a hankali ta k'araso gamida zama hannun kujeran,  d'an rank'wafowa tayi ta tsura wa labb'ansa ido,  a hankali ta had'iye miyau,  d'an yatsanta tasa ta shiga lailaye fatar bakinsa gamida hura masa iskan numfashinta tana wani lumshe idanu....

   "Kaman a mafarki haka yaji wani bak'on Al'amari na faruwa dashi,  cikin sauri ya bud'e idanunsa masu d'auke da bacci ya sauk'esu kanta,  a razane da yanayin nata ya matsa k'arshen kujeran gamida kauda kai gefe don kuwa wann shiga nata ko kad'an bai dace ya kalla ba.

   "D'an saita kanta tayi don tasan wnn dole tasha wuya kafin ta samesa da gani baisan hark'arba.

    "Ganin ya bita da kallon tuhuma yasata saurin mik'ewa tana had'a igiyar rigarta kafin tace " Sorry I didn't mean to wake you up,  dama ce maka zanyi da ka koma d'aki ka kwanta kan gado you will be more comfortable kaman kujeran ta kasa maka....

   "Gajeren tsaki yayi kafin yace " Nan ma yayi min na gode,  daga haka ya juya da fuskarsa gefe,  ba don yana so ta basa adreshin gidan Dasuki's ba da tuni ya cika ma rigarsa iska....

   "Zulaihat ta sha jinin jikinta ganin irin dizgin da yayi mata,  amma dashike ba kunya bace da ita,  zagayowa tayi ta gabansa snn ta soma tafiya cikin kwarkwasa ta yanda duk wani gab'a na jikinta ke motsawa. Fuska d'auke da murmushi tace mu kwan lafiya.....
  "Bai iya amsa mata ba sai had'iyan miyau da yayi snn ya kasa daina kallon salon tafiyarta,  a hankali ya dafe kansa sanda ta shige d'akin,  wani irin yanyi maras fasaltuwa ya ziyarcesa.....



 *Washe gari*

   "Mami zan amsa kiran Uncle ne sabida ke, dan idan ta nine wllhi ko fuskarsa banson gani...  Bata amsa sa ba sai ci gaba da had'a masa buttons d'in hannun rigarsa data ci gaba da yi.
   "Tallafo fuskarta Labib yayi da hannunsa kafin yace" Are you still mad at me,  com'on Mami I said I'm sorry,  shikenan fine I promise you I'll try to control my temper and I'll learn how to put up with him, but he would explain to me how the heck my Dad borrows those money.... Manna mata peck yayi a kumatunta sanda ta gama hada masa aninin hannun rigar, Jacket dinsa ya d'auka suka nufo downstairs a tare, da kanta tayi serving nasa breakfast, ma'aikata sai kai komo suke,  suna masu mamakin yau Labib kaman ba shi ba,  da alama na cikin farin ciki don kuwa har suma ya gaisa dasu yau...
   "K'arfe 8:15am daidai ya fito daga mansion din ya nufi motarsa k'irar Mercedes Benz,..


    "Cak ya tsaya da motarsa ganin wani mutumi sai faman fafatawa suke da securities both masu tsaron gidansu da masu tsaron gidansu Salim dashike gidan a manne ne komai iri guda idan baka sani ba ma saika d'auka gida guda ne., Tuhumarsa suke me ya biyo dashi layin.
   "Horn ya masu sukayi saurin k'arasowa suna fad'in" Sorry Sir had'i da wangame masa babban gate d'in wanda yake k'arafuna ne sanda sanda kana iya hango waje.

   "Labib yace " Who's that Man Jerry?

  "Sir we have no idea who he's,  but we are suspecting him hes up to something, or may be someone sent him to spy on you *The Dasuki's*

   A hankali yayi wata silent smile, "what if this man is after Kasim Dasuki, what if he's planning to take revenge on Alh Kasim, k'ilma   wani business partner dinsa ya cuta shine ya turo wnn mutumin ya masa bincike don ya tarwatsa Alh Kasim don yasan Uncle dinsa is a very wicked person, lallai kuwa idan zarginsa ya tabbata haka he'll work hand in hand da wann mutumin don su ruining Alh Kasim....  "Cikin sakanni da baifi biyar ba yayi wann tunani kafin ya murmursa a hankali ya furta " My Uncle....  Kafin ya wani foze ya dubi Jerry yace "

   "Bring him to my penthouse dags haka ya fice daga cikin motar ya nufi cikin gida da k'afa don kar Mami tasan cewa bai wuce amsa kiran yayan mahaifin nasa ba a chan company.


   "Yana zaune a bar D'ins suka shigo dashi a rirrik'e,  da sauri ya mik'e gamida daka masu tsawa yace "Let him go "

   "Sakesa sukayi kafin suka soma apologizing. D'aga masu hannu yayi kana yace " Kuna iya tafiya,  a tare suka fice Labib ya d'an Bud'e murya ya kira Jerry,
   "Yes Sir,  ya amsa Gamida tsayuwa yanda yake,  saitin kunn Jerry yace cikin rad'a" No one should know about this not even my uncle.  Gyada kansa Jerry yayi cike da girmamawa yace " Okay sir, daga haka ya fice...

   "Labib ya juyo suna fuskantar juna shida UMAR..




   "Yanzu ke Zulaihat kan me zaki taimaka ma wann mutumin,  baki sansa ba baki san shirinsa akan Dasuki's ba kawai kinsa mun kawo sa what if mugu ne,  kema fah kinada kamisho,  Cewar IMAM,  matashin drivern taxi wanda kullum Zulaihat tayi shirin fita satark'fa muddin bata so Tariq yasan ta fita toh shi take kira ya Kaita,  Zulaihat da Imam sun saba sosai tun yana mata nasiha tana basarwa tana tsigalesa tana fad'in ya tsaya matsayinsa na dreban taxi har ta gaji ta soma jure sauraren wa'azin  sa,  amma ko yayi wucewa take ta bayan kunne don ba shiga kanta yake ba. Shi kuwa Imam yasha alwashin bazai tab'a gajjiyawa dayima Zulaihat wa'azi ba yana junta tamkar k'anwarsa dukda ratan dake tsakaninsu a shekare akk'alla bazai wuce shekara d'aya zuwa biyu ba...

   "Harara ta gallawa Imam kafin tace ka kama kanka nd pls stop talking n concentrate on your job.....
   "Murmushi kawai yayi gamida maida hankalinsa kan titi.,
  "Ina muka nufa? Ya tambaya sanda yake sharan kwana..

   "A tak'aice ta basa amsa " Any nearby eatery don ni yunwa nake jima,  ko karyawa bai bari munyi ba muka fito,  ta k'arashe maganar tana mai saka hannu cikin Jakarta,  wata 'yar takarda ta ciro,  nan ta tuna jiya ne ya fad'i daga jakan Umar kuma ta manta bata basa ba. A hankli ta soma warware takardan,  ta karace sa tass...

  "A fili ta furta "Jalal,  Zubaidah" innalillahi sai yanzu tasan asalin dalilinsa na neman gidan Alh Kasim Dasuki,  shakka babu tasan sunan Jalal a wajen Tariq amma bata tab'a ganinsa ba,  kenn Umar tattaki yayi tun daga Gombe sabida budurwarsa,  take taji kishin Zubaidah ya tokare mata mak'oshi dukda ba saninta tayi ba.....

     "Har suka isa gidan cin abincin hankalinta bai jikinta har saida ta jiyo muryar Imam yana fad'in" Na fito na rakaki ne,  d'an harara ta watsa masa kafin tace " Ka raka wa, kana taxi driver d'in Allah sawak'eni,  ai saika kashe mun market ka sani ko nayi new catch a restaurant d'in....
   "Murmushi kawai yayi ya bita da kallo har ta shige kafin ya fito ya d'ale saman mota ya zauna......






   "Labib ya mik'a masa hannu alamun musabaha kafin yace " Labib Dasuki,...
   "Kallonsa Umar yake yi kaman bazai basa hannu ba sai kuma ya mik'a masa shima kana yace " Umar Sanda.
    "Let me go straight forward kafin ka tambayeni, .
   "I'm here to take my revenge on your brother or what ever JALAL Dasuki. Nazo ne na amshe abinda ya k'wace daga gareni the love of my life Zubaidah,  and finally give him what he deserves....  KILL HIM......

    "Gaban Labib yabada dummm, abu na neman juye masa yayi zaton mfaraucin Alh Kasim ashe mafaraucinsu ne don kuwa da ace zaisan Jalal bai aikata laifin ba su suka aikata da shine first on the list....
   "Saurin saita kansa yayi kafin ya mik'e tsaye ganin yanda idanun Umar suka koma jazur he's capable of taking revenge.
   "Dafe kafad'un Umar yayi kafin yace " So she was to marry you before Jalal ruins everything,  I'm sorry I really pity your condition,  it isn't easy to lose someone you love....

     "Buge hannunsa yayi yana masa mugun kallo kafin yace " Ban rasata ba kuma bazan rasata ba,  and to make it clear to you, that precisely why I came here,  to take her back with me,  to take back what was stolen from me, what's rightfully mine...

     "Baki Labib ya hangame yana kallonsa he never thought wann mutumin can speak English fluently, lallai d'aukan revenge akansu bazai masa wahala ba,  he needs to do something before he learns everything....
   "Calm down pls,  kayi hak'uri ka zauna and let's talk sensibly.
   "Sauk'e ajiyan zuciya Labib yayi kafin yaci gaba da fad'in" Jalal,  Jalal,  ba d'an Family d'inmu bane hasalima mahaifiyarsa aikatau take a gidan nan,  mahaifanmu sun ruk'esu bisa gaskiya da amana,  muma haka muka d'aukesu gaba d'aya,  cuz we followed our parents steps.
  "Bamu ragesu da komai ba,  a lokacin da mukaje Dukku bikin sakun ranar cousin d'ina Salim Jalal saw her,  yayita bamu labarin yanda yake sonta coz we're like brothers we didn't hide things from each other.
   "Duk mun zaci son gaskiya yake mata until the incidence happens,  although yace da son ranta hakan ya kasance coz duk sun kamu da son juna,
  "His poor mother cried hard lokacin da labari ya isketa,  sukayita rok'on Uncle d'ina kan ya Aura masu juna don kar su zamo abun nunawa a gari,  My uncle did as they wanted,  na fada maka iyayenmu basu vanbantamu da Jalal,  babu wanda yace masu su bar gidan nan suka tattara suka koma yanda babu wanda ya sani cikinmu,  despite all the good things da aka masu basu mana sallama ba balle musan yanda suka koma,
   "Ya d'an fuzar da iska kaafin yaci gaba da fad'in" But I'll help you find him,  I promise you that, you have my word..

    "Kallonsa Umar keyi cikin wani irin yanayi without saying a word, ashe dama Jalal ba d'an Dasuki Family bane,  he's just no body like him,  lallai yak'in bazai masa wuya ba,........  Amsa wayan da yaji Labib nayi ne ya katse masa tunanin nasa.

   "Hello Buddy. Ya akayi ne, cewar Labib bayan ya k'ara wayar a kunnensa.
   "Daga d'aya b'angaren Salim yace " What's wrong with you Labib,  kowa Ya taru a conference hall kai kawai ake jira,  the meeting is about to start Don Allah kayi ka k'araso....
  "Okay okay fine,  I'll be there right away,  you know me I never dose things on time...  Sai na iso daga haka ya katse wayar....

    "K'arasowa yayi yanda Umar yake kafin yace " Ni zan wuce office inada meeting ni kawai ake jira and kaga bai kamata na bar mutane suyita jirana ba,  You'll continue daga yanda muka tsaya,  za'ayi serving naka breakfast to lunch har na dawo,  just feel at home,  ya nuna masa wani d'aki wanda basai ance maka guest room bane yace " You can keep your luggage in there....  Daga haka sukayi sallama har lokacin jikin Ummaru na mace....


       "Tunda ta shigo restaurant d'in take kallonsa yanda yake cin abincinsa cikin tsanaki,  waiter na tambayarta order ko saurarensa batayi ba ganin guy d'in nan ya ciro cell phone d'insa yana waya....

  "Hello Jalal,  gani na shigo cikin Abuja yanzun nan,  yeah wllhi meeting nake dashi 10:am yeah, da zaran na gama zan d'auki hanyar gombe shiyasa  ma na kiraka don karkuyita jira na,  eh na kira layin Usman bai zuwa,  yauwa na gode ka gaida min amarya Zubaidah pls,  next time dai zanzo mu gaisa,
     "Ya  d'anyi murmushi kafin sukayi sallama ya katse wayar.... 


      "Kallo ta bisa dashi,  a hankali ta furta Zubaidah Jalal, tabbas sune mutanen da Umar yazo nema,  ganin yana gab da k'arasa cin abincinsa yasata mik'ewa ta nufi Table d'insa.....


Sameena ce 👌🏾👌🏾👌🏾
[1/23, 22:17] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                             33

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


 *Dedicated To All Victims Of Rape...*


   "Zama Zulaihat tayi kujera mai kallon nasa fuskarta d'auke da murmushi, ..
   "Ajiye fork d'in hannunsa yayi yana dubanta fuska d'auke da alaman tambaya.

   "Sannu bawan Allah ta fad'i tana mai fad'ad'a murmushinta.
   "A tak'aice ya amsa mata had'i da yin gajeren murmushi,  ganin murmushi saman fuskarsa yasata samin k'warin gwiwa, kan tayi magana ya d'anyi gyaran murya kafin yace "  How may I help you?.

   "Em..em da Allah dama so nake ka ajiye min jakata I want to use the restroom.

  "Ba tareda ya kawo komai ba yayi muushi yace " It's not a problem, kina iya zuwa,  amma idan kika wuce 10mins zan tafi don akan hanya nake..

   "Murmushi tayi kafin tace " I won't take long,  daga haka ta wuce tana sakar masa wani shu'umin murmushi...

  "Mintuna kadan ta dawo don dama babu abinda ya kaita restroom d'in wanke hannu kawai tayi ta fito, 
   "Nan da nan Zulaihat taja Shattima da hira,  shi da kansa ya tambayeta me zata ci,  cike da kwarkwasa da Mad'e ta fad'a masa,  waiter yayima alama da hannu yazo kafin ya fad'a masa abinda zai kawo wa Zulaihat,  hira sosai Shattima da Zulaihat suka sha har saida ya kusa makara zuwa meeting d'in nasa,  k'arshe exchanging phone number sukayi yace mata zai dawo Abuja soon...



*Dasuki Holding*

   "Babban ofishin taron tayi tsit yayinda suke gudanar da meeting d'in cikin tsanaki.
  "Shaidun da suka gabata gaban Labib yasa jikinsa yin sanyi, tabbas da gaske ana bin mahaifinsa bashin mak'udan kud'ad'e snn yaga yanda Alh Kasim ke k'ok'arin ganin ya saving company d'imsu from going bankrupt...

   "Muryar  Alh Kasim ya katsesa sanda yaci gaba da fad'in"  As you all know we are not financially stable, taimakon Allah guda da yasa  muna tare da mutane da suke son ganin ci gabanmu,  thank you all for your financially supports,  snn nayi alk'awari zanyi clearing duk wani bashin da marigayi k'anina ya ciyo da sunan wnn company...
   "Haka har aka k'arashe meeting d'in mutane na allason barka da Alh Kasim...

   "Sanda kowa ya watse ya rage daga shi sai Barr Munir sai kuwa Labib dake zaune tamkar dutse a wajen,  kallon juna sukayi shida Barr Munir kafin suka sakar ma juna mayaudarin murmushi,  a hankali ya d'an d'agawa Barr Munir babban yatsan sa a sace kafin ya k'araso ya dafa Labib yace
 "Son wnn shine abinda nake kan fad'a maka ka kasa fahimta,  shiyasa nace gara kazo ka gane wa idanunka,  ba don taimakom Allah da kuma taimakon Alh Tahir Marafa ba,  who knows wani irin karayan tattalin arziki zamu fuskanta. Yanzu abinda nake so da kai ka tashi ka tafi office d'inku kaida Salim yana nan floor d'in office d'ina..
   "OK kallo basu ishesa ba,  haka kurum yake jin bai yarda da Uncle d'in nasa ba,  tunowa da yayi da Umar yasa sa sakin wata murmushi, da wnn tunanin ya gwada masu komai ya wuce harda hugging uncle dinsa ya basa hak'uri kan abubuwan da ya masa kafin ya nufi office d'insu shida Salim....


    "Salim yana hangosa ya kwashe da dariya kafin yace " Dan iskanci saida ka gama shanya manyan mutane snn ka sami isowa.
  "Tab'e baki Labib yayi kafin yace " So...

   "Salim ya girgiza kai kawai kafin ya soma turo masa files gabansa yana fad'in" here there's alot of work.

   "Kallonsa kawai Labib keyi yana wata murmushi kafin yace " If I ruined you I know Kasim Dasuki will definitely die coz you are his life,  his only precious son.....
   "Wai murmishin Me kake tayi ne, Salim ya tambaya sanda yake Bud'e McBook me d'auke da tambarin Dasuki holding wato *D¤H*

   'Bai cemasa komai ba sai mik'ewa da yayi ya nufi fridge......



     "Sanda Labib ya koma gida basu samu sunyi magana da Umar ba,  don ya Sanar dashi yana son komawa gida gobe da sassafe an yo masa waya Baffansa bashida lafiya sosai,  Labib yace babu komai har gida zaisa a kaisa snn idan ya tashi dawowa waya kawai zai masa ya tura driver, har wani d'an sabo sukayi a rana guda...  Duk wann wainar da Labib ke tuyawa a gidan Mami batada masaniya.....


   
    "Zaune suke a parlor Annah tana koyawa Kamal assignment, Annah na zaune gefe tana kallon Tv jefi jefi tana tayasu home work d'in...
  "Sallama yayi had'i da turo labulen a hankali,  Annah ta amsa masa gamida masa iso,
   "Kaman wani b'arawo haka ya soma shigowa cikin sand'a.

    "Murmushi Annah ta sakar masa ya k'arasa gefenta ya zauna yana satan kallon su Zubaidah,  gaba d'aya tun shigowar sa ta canza,  Kamal kuwa tuni ya tafi wajensa yana zuba masa surutu,  wani mugun haushi takeji idan Kamal Ya kirasa Uncle Jay, ta tsanesa ta tsani ganinsa babban farin cikinta shine saura sati guda chif ya tafi kaman yanda ya fad'a mata.
   "Da dabara Jalal yasa Kamal komawa wajen karatunsa da shike ta d'an gefen parlorn suke zaune...

   "Hiran wajen aiki Jalal da Annah suke tab'awa amma rabin hankalinsa baya gareta yana ga Zubaidah da ta had'e rai kaman taga ajalinta.
   "Labarun tara da aka soma ne yasa Jalal canza tashan,  kaman daga sama sukaji ana sanar da auren Salim Kasim Dasuki da kuma Kausar Tahir Marafa, sati me zuwa wanda za'ayisa a babban masallacin gwamnantin tarayya  National Mosque Abuja..
 "hotonsu da aka hasko kuwa ba k'aramin kyau sukayi ba.
 
   "Take taji zuciyarta ya soma mata zafi zogi da rad'ad'i,  fuskokinsu cike da farin ciki alamun auren soyayya zasuyi,  yayinda ita suka tarwatsa nata rayuwar suka rabata da masoyinta na asali snn suka Aura mata mak'iyinta d'aya daga cikin mutane hud'un data tsana a rayuwarta.... 
   "Da sauri ta tashi ta shige d'aki gamida rufo k'ofar da k'arfin gaske ta fad'a kan gado tana kuka mai tsuma zuciya.

   "Annah ta bita da kallo cikin rashin gane dalilinta na barin parlor,  wata zuciya kuwa ce mata tayi k'ila hakan nada alak'a da shigowar  Jalal,  kallon Jalal tayi wanda har lokacin kallon k'ofar d'akin yake.
  "Murmushi Annah ta sakar masa kafin tace " Kar ka damu it will pass,  gyad'a mata kai kawai yayi gamida yin gajeren murmushi kafin ya gyad'a kansa alamun eh.
  "Cikin ransa kuwa yasan dalilin da yasa Zubaidah barin wajen ba bai wuce ganin tallan auran Salim bane a TV...  Jan hannunsa da Kamal keyi yana fad'in" Uncle Jay ka k'arasa min home work d'ina Kata Didi tak'i k'arasa min... Wnn magana na Kamal shi ya dawo dashi daga duniyar tunanin da ya tafi.
   "Murmushi ya sakar ma  Kamal kafin yace " Of course Champion let's go to my room,  d'aukansa yayi ya azasa a wuya suka fice daga parlorn sai murna Kamal keyi,  yana tsananin son Jalal.
    "Annah kuwa kallo ta bisu dashi fuskarta cike da murmushi tana mai jin Dad'in yanda Jalal da Kamal suke son junansu....
     "Ficewarsu da kad'an itama ta mik'e ta shige d'aki wajen Zubaidah.....




*Gombe Fada*

   "Zaune suke saman wasu kujeru wanda basai an ce maka na shak'atawa bane, da ganin fuskokinsu zakasan suna jin Dad'in hiran da suke.

    "Ya Shattima wllhi biki nake dashi a Abuja Next Week amma nasan Mai Marta won't allow me to attend the wedding. Zahida ta fad'i sanda take gyara zaman alkyabban jikinta.

   "Murmushi mai sauti Shatima yayi kafin yace " Princess kinada kayan dariya,  ai ya kamata ace by now Kin saba da dokan mahaifinki,  kiyi mata addu'a daga nan ya wadatar basai kinje ba...

   "D'an b'ata fuska tayi gamida turo baki gaba tana kallonsa a shagwab'ance tace " Aw kaima irin halinka knn kulle wa mutane, instead ka rokar min shi for the first time ya barni naje shine zaka ce na hak'ura...

    "Dariya taso basa ya d'an dake kafin ya soma lallashinta,  Com'on lil sis,  kema kinsan ba haka bane,  da inada iko dake zakije duk yanda kike so fad'in duniyar nan matuk'ar zai sakaki cikin farin ciki. Kawai dai ya kamata ki saba da wnn tsarin ne, tunda kinsan mai Martaba baya magana biyu.

   "Sauk'e ajiyan zuciya tayi kafin tace " Haka ne ya  Shatima that's why nake ji da kai da Madaki sabida kuna saurin fahimta ta......

   "Wayarsa data soma ringing ne ya katse masu hiran tasu.

    "Zulaihat ya gani kan screen din wayar,  sai yanzu ya tuno da wata Zulaihat tun bayan barinsa restaurant d'in...

      "Tunda suka soma magana fuskar Zahida ya canza,  haka kurum ta tsinci kanta da jin haushin wacce yake magana da ita.

      "Zulaihat kuwa gogeggiyar 'yar bariki tuni ta kalallame Shatima da kalamai masu Dad'in saurare,  har yaso ya mance Zahida na zaune a wajen.
  "Mik'ewa tayi tana kakkabe alkyabban ta alamun zata tafi.
      "Da sauri Shatima ya rik'o Alkyabban gamida d'aga mata yatsa guda alamun ta basa minti d'aya...

      "Sallama sukayi da Zulaihat kafin ya dawo da hankalinsa kan Zahida da ta cika tayi fam..

     "Tsokanan ta ya soma wai kodai kishin yayan nata take ne,  dariya kalamansa yaso bata don bata ga dalilin da zaita kishi akansa ba.
  "Suna a haka suka hangi Khalifah ya doso yanda suke cikin tafiyarsa na isa da gadara wanda ya zame masa jiki.

     "Take ta had'e rai kaman ta ga dodo,  Khalifah ya k'araso gamida mik'awa Shattima hannu sukayi masabaha,  yana masa kirarin "Ranka ya dad'e Allah baka gidanku....
    "Khalifah yayi wani k'asaitacccen murmushi don babu abinda yake so kaman a kod'asa.
    "Kaman bata san ya iso wajen ba haka taci gaba da danna wayarta har saida Shatima ya  mata ido kafin ta gaishesa a dak'ile ko sakon biyu mai kyau bata k'ara a wajen ba ta shige cikin gida.

   "Nan Khalifah da Shattima suka ci gaba da hira,  yana fada masa tsarin da mahaifinsa yayi masu shida Zahida.

  "Khalifah d'a ne ga k'anin mai martaba  kuma Chiroman garin Gombe,  basuda buri shida mahaifanda kaman suga ya auri Zahida. Ita kuwa ko kad'an tak'i jinin Khalifah,  tun tana 'yar k'arama ta tsani Khalifah wanda hakan yasa harta 'yan gidansu tsanar ya shafa,  dukda bata da wa ko k'ani bata fatan bayan ran mahaifinta sarautar garin ya koma gidan Ciroma,  don kuwa gaba d'aya shida iyalansa mugun hali ne dasu,  basuk'i mai martaba ya mutu a yau su d'ale mulki ba......



 *Abuja.....*


    "Gidansu Kausar babu masaka tsinke kasancewar bikin ya k'arato sosai,  Su Mumsy su Asmah babu zama,  hidima ake kanyi babu kama k"afan yaro,  Pappy kuwa daga k'asashen daban dabam Ya gayyaci mutane zuwa d'aurin aure da bikin tilon 'yarsa.

     "Ana saura kwana uku d'aurin aure suka gudanar da brutal shower ita da k'awayenta, washe gari aka yi kamu,  kai tunda satin bikin ya shiga ake gudanar da events.

       "Gidan Alh Kasim Dasuki ma ba'a barsu a baya ba,  gayya sosai yayi,  toh gayyan nasu ma kusan dangin abu guda ne,  tunda yawancin mutanen da suka gayyata sun san juna,  Mummy hidima babu kama k'afan yaro,  Mami ne dai take takaba bata samu halartan shagulgulan ba,  su Momin Tariq da matan ministoci da sanatoci kawai kake gani a event d'in....

  "A ranan da aka d'aura aure ake shirin gudanar da dinner a babban hall d'in nan na wane da wane dake birnin tarayya Abuja wato AClass Hall.

        "Tun a wajen daurin aure Umar ya masa waya ya sanar dashi ya iso Abuja,  Labib yace " ya shiga kawai gurds sun san da zuwansa,  akwai duk wani abin buk'ata,  bazai samu dawowa gida da wuri ba sabida bikin cousin dinsa da sukeyi.....


      " wajajen k'arfe 6:56pm Gidan babu kowa daga ita sai Kamal kasancewar su Hadiza da Annah sun bi sawun Hamma Habibu don har yanzu bai dawo daga kasuwa ba wajen sana'ar saida kayan lambunsa....


     "Abubuwan suka ringa dawo mata kwanyarta, ta tuna sanda Salim ya fincike rigarta,  ta tuna yanda sukayita ihu suna shewa suna dariya,  ta tuna cewa har yanzu cikin farin ciki suke,  she's the one suffering,  sun zalunceta snn suna ci gaba da rayuwarsu peacefully, ta tuno zuwan Kausar lokacin data zo tambayarta gameda Salim....  Kaman wacce aka zabura haka ta mik'e ta nufi akwatin kayanta,  takarda me d'auke da lambar Kausar wanda ta bata kwanaki ta d'auko,  duk ta cukwikwiya sa,  warwarewa ta shiga yi a hankali kafin ta hangi wayan Annah kan gado da alama mancewa tayi. 
     "Cikin ssauri ta k'arasa ta d'auki wayar gamida dialing lambar Kausar.......



Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:18] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                              34

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*

    "Tuni dama an kai amarya gidansu ango dashike an d'aura aure...

    "Tayi kyau cikin doguwar rigarta da yake sharan k'asa,  fuskar nan kuwa tasha makeup,  Asmah sake baki tayi tana kallon yanda aminiyar tata k'anwa kuma k'awa a gareta tayi kyau...
  "OMG! You gorgeous Kausar, rungume juna sukayi cike da murna,  Makeup artist d'in sai murmushi kawai take masu,  Mumsy da masu d'aukan pics d'in amarya ne suka shigo.

  "Mummy ta shigo don ganin komai ya tafi Saudi kallo tabi surkar tata dashi kafin ta k'arasa ta rungumeta tace,
  "Oh my daughter you look so gogorgeous.... 
  "Murmushi Kaiser tayi cike da kunyan Mummy *"Mai Gaskiya photography* yace" Em Madam let's take a picture of yours...  Gyarawa sukayi akata kashe masu pictures suka k'arasa parlorn Daddy suna d'aukan wasu pics d'in....
   "Daidai nan su Salim da friends d'insa suka k'araso cikin luxurious cars d'insu,  Nan fah aka soma kwasan friends da wasu daga cikin dangi.
   "Komawa d'aki Kausar tayi sabida cellphone d'inta data mance..

  "Cak ta tsaya tana sauraren Asmah dake receiving call da wayarta.

  "Baiwar Allah kiyi hak'uri but you really can't talk to Kausar right now.....  D'an jim  tayi kafin tace Okay acemata waye....
   "In a shock Asmah ta furta *ZUBAIDAH*.... "

   "K'irjin Kausar ya bada wani irin k'ara,  da sauri ta fizge wayan daga hannun Asmah, kallo Asmah ta bita dashi don ta d'auka har ta isa wajen event.

  "Hello Zubaidah nice Kausar ce,

  "Daga d'aya b'angaren Zubaidah tace " Kar ki auri mutumin nan,..

  "Bugun k'irjinta ya k'aru,  baki na rawa take furta " Ban fahimce ki ba,

  "Zubaidah da tuni muryarta ya soma shaking alamun kuka taci gaba da fad'in" I said don't get married to that Man, he's a heartless a miserable jerk. ....

   "Kausar da tuni ta soma zuban hawaye take fad'in" How dare you,  how dare you ruin the most important day of my life,  are you trying to frame him or what.....

   "Kukan Zubaidah Ya k'aru sanda take fad'in" Kince kina son sanin gaskiya kince kina son sanin idan mijin da zaki aura was involved or not,  well believe it or not he's a monster a criminal, dukansu mugayene azzalumai wanda suke laifi su b'uya da inuwan kud'in mahaifansu..... Kuka yaci k'arfinta bata sanda ta latsa wayar ta kashe ba ta durk'usa a wajen tana kuka,  Kamal da tuni shima ya soma hawaye ganin Didin sa na kuka ya k'arasa Ya rungumeta....


    "Jifa Kausar tayi da wayar gamida toshe bakinta ta durk'usa kan gwiyoyinta,  Asmah ta k'araso a razane ta rungumeta ta shiga tambayarta lafiya meke faruwa..

   "Kausar na kuka take fad'in" She's saying the truth Asmah, gaba d'aya click dinsu ne sukayi raping d'inta,   Asmah I married a rapist,.....
   "Mikewa Asmah tayi ta saka Key ma k'ofan kafin ta dawo ga Kausar,
  "Pls Kausar don't be so naive, bakida tabbasa akan abinda ta fad'i,  who knows she might be making stories, ta yaya za'ace maza sama da biyu sunyi raping din Mace guda a dare d'aya bata mutu ba,  kema kinsan hankali bazai kama ba,  snn Jalal da bakinsa Ya fad'a maki gaskiya,  com'on tashi ki gyara fuskar ki,  kar ki bawa iyauenki kunya.... Asmah bata kai aya ba sukaji ana buga k'ofa, 
  "D'aya daga cikin friends d'insu ne,  Mardiya Aleru...
  "Asmah what the heck you guys doing in there,  ku fito mana pls....
   "Mummy ce ta k'araso ta dubi su Mardiya da sukayi cirko cirko a k'ofa tace " Yaya dai ina amaryar
.  "Mardiya ta d'an Tab'e baki kafin tace " K'ila dai mummy sai Salim yazo da kansa ya fito da ita,  murmushi Kawai Mummy tayi kafin ta shiga knocking k'ofar a hankali tana fad'in "Kausar lafiya dai ko, ko kina son wani abu ne....
   "Asmah ne ta sami strength d'in amsa Mummy Kausar kam gaba d'aya ji take ta tsanesu...

    " " Mummy ga mu nan fitowa..
  
  "Okay Asmah maza ku hanzarta ko the Grooms are waiting,  cewar Mummy kafin ta wuce.
    "Tsaki Kausar tayi a ranta wai uwar miji ne haka babu kamun kai.
    "K'arasa gyara ma Kausar Face d'inta Asmah tayi kafin tace oya muje kuma pls kiyi yanda nace if you really don't want you embarrass your parents..
   "Harara kawai Kausar ta jefa mata fuskar nan kana gani kasan babu lafiya haka ta fito, Ko kula su Mardiya bata yi ba ta wuce,  Asmah ta d'an basu hak'uri snn suka wuce kowa na mamakin sudden change d'in Amarya Kausar.....




      "A daidai tangamemen k'ofar glass d'in parlon Daddy ta hangosa,  yayi kyau sosai cikin shiga irin nata, tun daga nesa yake washe baki,  Labeeb na gefensa yana karantar amarya,  a ransa yace " I hope you two will never be happy.

   " Bayan lemozin d'in aka bud'e masu,  Salim Ya tattara mata bayan rigarta suka shige,  su Labib suka kwashi sauran k'awayen da suka rage.....


     "Gaba d'aya bai gane mata ba,  a hankali ya mataso dab da ita yana k'ok'arin shigewa jikinta yake fad'in "My beautiful bride is anything bothering you, huh Baby na,  ya jawota gamida kwantar da ita cikin jikinsa yana faman shinshina wuyarta......
   "Kausar da gaba d'aya hankalinta bai tare dashi sai snn taji abinda yake mata,  tayi saurin turesa tana hararansa take fad'in" What's with the rush huh?  Bazaka iya hak'uri akai maka ni bane or what....

    "Da mugun mamaki yake kallonta,  d'an matsawa gefe yayi gamida latsa wani waje ruwa ya zubo a cup snn ya kurb'a,  he couldn't believe it,  kaman ba itabace d'azu suka gama waya kaman su cinye juna,  Kallon yanda ta k'urawa window ido yake kafin yace with a soft voice " I'm sorry sweedy I didn't mean to upset you kinji, but I can't keep my distance with you especially yau that you are completely mine,....

     "Gajeren tsaki tayi kafin tace " You know what I already have headache.... Kallo ya kuma binta dashi bai kuma cewa komai ba har suka isa hall d'in....


     "Koda Salim Ya sakalo hannunta ma janyewa tayi a hankali,  Asmah ta mata alama da ido, Kausar ta d'auke kanta,  Labib kuwa kallo yabisu dashi yana son gano wani abin....

   "Ko gama event ba'ayi ba,  k'arfe 8:30 Kausar tace bata jin dadi ita tafiya zata yi,  babu yanda Salim beyiba haka dole ya hak'ura suka baro wajen, 


    "Wasa wasa dai babu Hamma Habibu babu labarinsa,  duk sun tambayi masu zama bakin kasuwa sunce tabbas sunga tafiyarsa,  Hadiza fah ido ya raina fata,  haka tayita rok'on Annah kan su k'ara shiga cikin Kasuwa,  gashi Annah bata d'auko wayarta ba balle su kira Jalal gashi empty suka fito babu sisi... Haka suka Dad'a kutsawa cikin kasuwa dukda dare da ya soma ja......


    "Su Mummy gaba d'aya sunji mamakin saurin dawkwarsu,   
    "Ana bud'r mata k'ofa ko ta kansa batayi ba tayi shigewarta,  Labib yayi saurin rik'o hannun Salim dake k'ok'arin bin bayan Kausar kafin yace " Wai meke damunta ne??

   "Gajeren tsaki Salim yayi kafin yace " I don't know, she's been acting strange, tace dai wai kanta ke ciwo,
    "Silent murmushi Labib yayi kafin yace " Kaje kaji abinda ke damunta bro, we are here for you,  nida Tariq, ya k'arashe maganar yana kallon Tariq da kwana biyun nan ya koma wani sukuku dashi,  yanzu haka ma kansa kife yake a stairry d'in mota...

     "Gus's kansa kawai yayi kafin yabi bayan Kausar....


     "D'an k'wank'wasa k'ofar yayi daidai lokacin da take k'ok'arin zuge zip d'in rigarta,  Asmah tayi masa iso,  gaba d'aya k'awayen suka soma zolayarsa wai ko koransu yazo yi,  biye masu dai yayi suna ta hiran barkwanci kafin suka fice suka basu waje....


      "Ko kallo bai isheta ba vlballe tasan da hallita a wajen,  k'arasawa yayi ya kame hannunta yana k'ok'arin zuge mata zip d'in yake fad'in let me help you with it Baby.....

   "Da k'arfin gaske ta turesa gamida jawo mayafi ta rufe jikinta tana watsa masa mugun kallon k'yama take fad'in " Allah Ya sawak'e someone like you Ya Kalli jikina ko nima Raping d'inanan kazo yi.....


Fozzzz yayi yana binta da kallon mamaki yayinda k'irjinsa ke lugude....


Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:18] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                               35

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_

*Dedicated To All Victims Of Rape...*



   *Where is you my Amazing Fans here comes your chappy.... Hey You know I love you all so freaking much.... 😘😻*




     "Kallonta yake da mugun mamaki without saying a word, muryarta ya jiyo sanda taci gaba da fad'in"

   "You are a monster Salim,  you are my worse nightmare, I regret the day I met you, I regret falling in love with you, snn auren ka shine babban kuskurena a rayuwa.  Kuma wllhi kaji na rantse da Allah saika sake ni,  wllhi bazan tan's zama da azzalumi irin ka ba,  dana zauna da rapist a matsayin miji wllhi gwara na zauna da mazinaci.  Ka cuceni ka yaudareni Salim kuma wllhi Allah bazai tan's barinka ba.....  Kuka ne ya kufce mata ta yunk'ura zata fad'a bathroom yayi saurin rik'ota ya rungumeta,
  "Dukda bugun da zuciyarsa ke masa bai hanasa shirya zance saman harshensa ba..

   "Sweetheart don't be such a naive,  how could you believe such scandal for Allah's sake,  yanzu ni knn baki yarda dani ba,  haba Kausar I thought we already done with that issue,  Kausar wllhi ko saninta banyi ba,  kar ki biye zancen mutane mahassada masu neman ganin sun rabamu da alak'ar dake tsakanin iyayenmu,  haba my baby pls don't let our enemies ruin the most important day of our lives....

   "Da  k'arfin gaske ta fuzge jikinta daga rik'on daya mata,  mugun kallo take watsa masa ga hawaye dake bin fuskarta kafin taci gaba da fad'in
.  "The next moment you intend to put your filthy hands on me,  snn  NE zan shayar da kai mamakin da baka tan's Sha ba your whole life. Da kake cewa I shouldn't let people ruin our wedding night ,  you are the one who ruins everything, tun daren engagement d'inmu ka b'ata komai,  snn ita wacce kuka yi mata fyad'en ita ta kirani ta sanar dani komai,  you must be ashamed of your self, you are despicable, I hate you....  I hate you for good. Lastly ka rubuto min takardan sakina kafin 'yan biki su watse don wllhi na ranste ba don kar na bawa mahaifina kunya ba ya zama *Media circus*ace tilon 'yarsa ta kashe aurenta kafin a gama biki ba wllhi da ko kwana a gidan nan bazanyi ba...... Fuuu ta shige bathroom ta barsa nan tsaye tamkar gunki...

   "Da k'arfi ya daki coach d'in dake gefe yana fad'in" Damn it,  damn everything, that filthy mere girl will never shut her mouth,  I'll kill you with my hands....

   "Labib dake lab'e bakin k'ofa ya gama jin komai,  tsaki yayi shima yana cusa hannu cikin gashinsa, damn that girl she ruined my plans...  Tsaki ya kuma bugawa gamida doka k'afarsa a garu....  Salim ne ya fito sukayi ido hud'u take Labib ya saita kansa kafin yace da Salim.

   "So how's she feeling now,  are you show baza'a kira Doc ba, tunda friends d'in nata sun wantse mun sallamesu,  Asmah ma ta wuce tace ba kwana zatayi ba,  gobe da safe zata dawo...

   "Tsaki Salim yayi don ko kad'an bai gane me Labib yake cewa,  dafe kansa ya kuma yi kafin yace " I swear I'm gonna bury that girl alive or my Name isn't Salim Dasuki.... 

    "Dafasa Labib yayi kafin yace " What's going on ango, wace yarinya kake magana..

  "Jawo hannun Labib yayi suka sauk'a downstairs kafin yace masa *"The cow girl"*

   "In details ya fad'awa Labib gaba d'aya abinda ya faru. Dafa sa Labib yayi kafin yace " This is serious bro,  kar ka damu I'll take care of this,  just go back to her kaci gaba da lallashinta,  ni zanyi dealing wancan issue d'in from now on bazata sake gigin yin magana ba...

   "Har k'ofar d'akin Labib ya rakasa kafin ya fito ya tadda Tariq na jiransa,  wayarsa ya ciro yai dialing wata lamba..

    "Hello James ka shirya mana mota d'aya na gurds daga haka ya jawo hannun Tariq suka fice waje,  tuni James ya cika umarnin Labib ko gida bai shiga ba suka shige bayan wata hamshak'iyar mota shida Tariq bayansu kuma Mota ne mai d'auke da zallan guards all in black...

    "Why you in a rush snn ina muka nufa,  Tariq ya tambaya yana kallon Labib,
   "Murmushi Labib yayi da gefen bakinsa kafin yace " Just wait and see.

   "D'an tab'e bakinsa Tariq yayi ba tareda ya kuma cewa komai ba,  ganin suna shirin barin cikin Abuja sun nufi suleja,  yasa Tariq kuma kallon Labib fuska d'auke da alaman tambaya.

   "Hey relax Buddy wani aiki zamuje mu aiwatar,  Labib ya fad'i yana wani shu'umin murmushi yana bubbuga kafad'un Tariq...


     "Da mugun mamaki Tariq ke kallon gidan da sukayi parking a k'ofar,  fitowa Labib yayi snn yayi alamu ma guards d'in su biyosa,  babu musu sukayi yanda yace.
    "Ya dubi Tariq kana yace " Aren't you coming with us.

   "Tab'e baki Tariq yayi ba tareda yace komai ba,  ya mik'e jikin seat gamida ciro earpiece ya saka wak'a a kunnensa....


     "K'aran tsayuwar mota dataji yasata saurin fitowa duba ko su wanene,  ko su Annah ne aka kawosu a mota,  ko Hammanta yayi nisan zango ne aka Samosa.

   "Ganin motocin ya sauk'ar mata da mummunar fad'uwan gaba,  kan ta nufi d'aki yanda ta kwantar da Kamal don already yayi bacci taji an daki k'ofar gidan da k'afin gaske saida ya b'alle......

    "Tsayuwa tayi cak a tsakiyar gidan suka soma kallon kallo,  mummunar fuskar da bazata tab'a mantawa ba ya bayyana a gabanta,  take ta soma recalling abubuwan da suka faru,  ta tuna sanda Labib ya d'auke ta da mari,  ta tuna irin wulak'anci da cin zaraifin da suka mata, ...
    "Take ta soma ja da baya gamida k'walla k'ara,  zata nufi cikin d'aki knn Labib ya damk'ota.....

   "Tun daga waje yaji k'aran data Saki,  dawowarsa knn daga wajen aiki,  ganin manyan motoci k'ofar gidan ya kuma razana sa,  a sittin yayi jifa da ledan hannunsa ya shige gidan....


   "Ihu take tana k'ok'arin k'watar kanta, ....

    "Idon Jalal ya sauk'an Labib da ya shak'eta,  kutumar ubancan......  Da k'arfin gaske ya furta "Labiiiiib....  A sittin yayi kansa Labib yace wa gurds din get himm...

     "Ina kafin su k'araso Jalal ya sauk'e wata wawan naushi a hancin Labib wanda saida yayi sanadiyar zubewarsa k'asa,  jini ya kece a hancinsa,...

    "Da sauri ya rungumo Zubaidah data zama out of control sai faman k'ank'ame jikinta take tana kuka,  fad'i yake " It's okay Zubaida I'm here,  Babu abinda zai sameki I pro........  Bai kai aya ba yaji sauk'an k'asan takalmi akansa bayan an sharb'esa....
   "Wani sabon kuka Zubaidah ta kurma gamida yunk'urin guduwa,  saidai kafin tayi wani katab'us Labib ya kuma capko ta, gashinta ya kame da k'arfin gaske tana kuka tana fad'in ya saketa...  A kunnenta yake fad'in If you don't remain silent I'll kill you,  snn na kashe shi wanda ya d'aure maki gindin kike iskanci wa mutane,  tsatta masa yawu tayi dukda azavan da take ji,  Labib yayi jifa da ita saida ta gwaru da garu.....

     "Duk dukan da suke masa bai hanasa fad'in" Labib let her go,  I swear I'll kill you,  you Bastard.....
    "Goge jinin bakinsa yayi kafin yace wa gurds d'in beat him up to the point of death....

    "Juyowa yayi ga Zubaidah da ta rungume Kamal suna kuka suna kallon yanda ake lapkan Jalal, kafin yace " I warned you for the last time,  If you dare try to ruin our reputation I'll not think twice about it, I'll kill you... Daga haka ya fice yana goge jinin bakinsa,  yana murmushi don kuwa damk'ar Zubaidah da yayi a yanzu ya tuna masa wancan daren.....


      "Saida sukayi ma Jalal  lilis kafin suka k'yalesa....


Sameena ce
[1/23, 22:18] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                             37

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*Dedicated To All Victims Kg Rape...*


    "Murmushi Labib ya sakar wa Umar kafin yace " Na zaci kayi bacci ai.

   "D'an girgiza kai Umar yayi kafin yace " Not yet,  so how's the wedding ceremony..?
  "Umar ya tambaya sanda suka k'araso parlor suka zauna bisa sofa..

  "it was spectacular... Cewan Labib lokacin da ya danna power button na TV...
   "Kai tsaye bar d'insa dake cikin parlorn ya wuce ya d'auko masu glass cups da Champaign...

  "Saman center table ya  ajiye kafin yayi serving nasu...  Sai snn Umar ya lura da ciwon dake bakin Labib, Karb'an cup d'in da ya mik'a masa yayi kafin yace " Me ya sameka..?

   "D'an murmushi Labib yayi had'i da shafan gefen bakinsa yanda yaji ciwo kafin yaci" Oh this, I had a minor car accident,  I almost run over a girl, kasan yara da maganar tsallakan titi,  but it's nothing serious, Allah Ya kiyaye...

   "D'an jim Umar yayi, haka kurum yaji bai gamsu da zancen Labib ba a fili kuwa cewa yayi,  Allah Ya k'ara kiyayewa..
  "So ya maganar mu,  a ina muka kwana??

   "Murmushi Labib yayi gamida karya k'afafu ya kurb'i drink d'insa kafin yace
  "By tomorrow everything will gonna be over,  I'll take you the bastard and you'll finally get your revenge.

  "Murmushi Umar yayi gamida k'urawa cup d'in hannunsa ido, ji yake bazai iya jira gobe tayi ba...
 
   "Mik'ewa Labib yayi kafin yace " I'm off to bed see you tomorrow... Daga haka ya wuce d'akinsa zuciyarsa cike da farin ciki,  sabida already Salim Ya fad'a cikin trap d'in,  k'arashi ne ya rage masa wanda zaiyi amfani da  Umar to ruin his so called uncle and to finally get his revenge....
   "Wata dariya yayi gamida zubewa kan gado ko takalmi bai cire ba kaman ba d'an musulmi ba...





   "Mamaki ne ya ishesu ganin jini tun daga k'ofar gidan,  gashi an b'alle k'yauren,  gaba d'aya salati suke har suka shige cikin gidan....  Da sauri Annah ta lek'a parlornta basa ciki,  Hadiza kuwa hankalk taste ta shiga ambato d'anta,  ganinsa kwance a d'akin Annah yasata sauk'e ajiyan zuciya.

   "Annah da Hamma Habibu kuwa gaba d'aya hankalinsu ya tafi ga neman Zubaidah,  ko tunanin duba d'akin Jalal ma basuyi ba,

   "Hadiza ta shiga tashin Kamal tana tambayarsa ina Didinsa me ya faru? 

   "Kuka Kamal ya soma yi Wanda gaba d'aya yaja hankalimsu yana fad'in
  "Wasu mutane sunzo sunyi duka ma Uncle Jay sunce sai sun kashe Didi na,  kuma Uncle Jay yasansu har yana kiran sunansu...

  "Gaba d'aya suka zaro ido waje da jin zancen Kamal,  Annah ta rik'o hannunsa tace " Kayi shiru bazasu dawo ba,  ina Didin naka da Uncle Jay, mutanen sun tafi dasu ne...??

  "Girgiza kai yayi yana goge hawayen idonsa yace " Tace mun zataje tabawa Uncle Jay magani...... 
   "AI tun kan yayi shiru suka nufi d'akin Jalal don basuyi zaton suna ciki ba sunji shiru,  snn sunsan Jalal,  Ya Zubaidah basa ko ga maciji.....


    "Yana kwance saman katifa,  yayinda Zubaidah ke zaune k'asa a gefensa hannunsu rik'e cikin na juna, ...
   "Annah da Hamma Habibu basu san sanda suka Saki murmushi ba.
  "Hamma Habibu cikin yanayin maganarsa yake fad'in" Bacci suke,  bacci suke,  mu k'yalesu kar mu tashe su..

    "Shewan da Hadiza ta saki yasasu farkawa a firgice babu shiri,  da shike dama naccin tsoro sukayi....

  "Mik'ewa tayi zunbur tana binsu da kallo,  ganin hannunta rik'e cikin na Jalal,  yasata saurin fuzge hannunta,  kallo ya bita dashi,  ya d'an yunk'ura ya mik'e zaune..

   "Ashe dai sai bama gidan nan ake cin soyayya a shanyeta,  don munafunci a gabanbu a nuna ba'a kula juna,  ni dama nasan irin wad'an nan sunfi kowa iyayi da feleke da nuna zumu'di kan namiji....
   "Tsawa Annah ta daka mata,  ganin Zubaidah ta soma tattare rigarta tana tauna leb'en bakinta tasan yanzu sai ta zama out of control...
    "Jawo hannun Hadiza tayi suka fice daga d'akin don takaici...


    "Zubaidah tayi saurin nufan k'ofa ya d'an tako yasha gabanta, 
  
   "Harara ta watsa masa tana tattre rigarta tana rufe jikinta da sauri ta kauda kanta gefe ganin buttons d'in rigarsa a bud'e suke k'irjinsa ya bayyana a waje..
  "Da k'yar ta iya furta " Let me pass...

    "Murmushi yayi jin sautin datayi amfani wajen masa magana ya bambanbanta da wanda take masa a da...
  "Matsa mata yayi,  tayi saurin sa kai zata wuce saiji tayi ya rik'o hannunta....

   "Dago kai tayi tana dubansa fuska a murtuk'e,  da tsiwa ta kuma cewa " What again...

   "Murmushi yayi kafin yace " THANK YOU "

    "Tsaki tayi gamida fizge hannunta ta fice....

   "Shi kad'ai yake jin farin ciki na ratsa zuciyarsa,  had'e buttons d'in rigarsa yayi kafin ya wuce yabi bayanta....


     "A barranda Zubaidah ta samesu, har lokacin ta kasa had'a ido da d'aya daga cikinsu sabida yanda suka taddasu ita da Jalal,  wani mugun haushinsa ya tokare mata mak'kshi,
   "Hadiza sai kallonta take tana murmushin mugunta tana watso mata habaici...
    "Sa kai tayi zata wuce Annah tayi saurin rik'ota tace " Zi nan Daughter kar ki biye nata.... 
    "Kuka Zubaidah ta Saki tana fad'in wllhi ni bana sonsa,  na tsanesa ta daina cewa ina sonsa,  ni kawai na taimaka masa ne sabida I'm not a heartless being like him, kuma don ya amince zai tafi ya bar mun rayuwata shiyasa na taimaka masa....

    "D'an jim yayi yana sauraren kalamanta,  k'irjinsa yabada wani sauti jin dalilin taimaka masa da Zubaidah tayi wato sabida ya amince zai tafi ne...  K'araowa yayi gamida zama can gefe saman d'an dakali sanda  Annah ta rungume Zubaidah tana lallashinta lokaci guda tana watsa wa  Hadiza kallon zamu had'u ne....

    "Gyaran murya Annah tayi kafin tace " Jalal me ya faru,  su waye suka zo har suka maka illa,  snn Kamal yace kaidasu kunsan juna?...
   "Jalal Me  ya had'aka da mutane????  Annah ta jero masa tambayoyin....


    "Tun zamansa yake aikin watsawa Hadiza mugun kallo,  ji yake yana gab da saita ta muddin ta bari hak'urinsa ya gaza kan irin abubuwan da take ma Zubaidah.. "Tambayar da Annah ta masa yasa dawo da hankalinsa gareta.....

    "Saida yakai dubansa ga Zubaidah,  a ransa yace "Lokaci yayi da gaskiya zata bayyana...

      "Kai nake saurare Jalal,  Annah ta kuma fad'i a d'an tsawace..

      "K'irjin Hadiza tuni ya soma bugu, ba tareda tasan dalili ba,  haka kurum take shakkan Jalal,  musamman idan ya watsa mata wani kallo...

     "D'ago kai ya kumayi yana kallon Zubaidah kafin ya soma fad'in" Annah lokaci yayi da zaki san gaskiya, ...

       "Da mugun mamaki take kallonsa, sanda yaci gaba da magana,  bai b'oye mata komai ba duk abinda ya faru....
     "Jikin Annah yayi matuk'ar sanyi,  wani b'angare kuwa na zuciyarta tafarfasa yake,  haba biri yayi kama da mutum,  ashe laifin na 'ya'ayansu ne,  sabon tausayin Zubaidah ya taso mata...
  Kafe Hadiza tayi da ido tana binta da kallon tuhuma...

   "Ganin irin kallon da Annah ke mata yasata soma nad'e tabarma da borin kunya...
  "Miye kike mun irin wnn kallon,  Alh Kasim Dasuki sunada kud'i da iko,  bamu isa muyi shari'a dasu ba ko muja da sharudd'an da suka gindaya mana,  kuma ai kud'in da suka bayar bamani suka bada ba,  ma Zubaidah suka bada kuma suna nan ajiye ban tab'a ba,  snn ai shima Jalal d'in ya amsa kud'in Alh Kasim...... "

      "Dakatar da ita Annah tayi ta hanyar d'aga mata hannu kafin tace " Ya isa haka.... Ta juyo tana kallon Zubaidah data tak'ure waje guda tana kuka....

    "Tuni k'walla sun ciko idanun Annah,  muryarta na rawa take fad'in" Justice must be served, they should all pay for it,  they will be punished,  babu d'aya daga cikinsu da zai tsira da babban zaluncin da suka aikata,.....

    "Toshe kunnuwanta ta soma sakamakon tuno kashedin da Alh Kasim ya mata cewa sai ya kashe yayanta muddin tayi magana,  a guje ta tashi ta nufi d'aki gamida kullewa tana wani irin kuka....


Sameena ce
[1/23, 22:18] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                            36

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*


    "Suna fitowa suka shige motocin su,  suka bar layin..

   "Kallo Tariq yabi Labib dashi kafin yayi saurin cire earpiece d'in dake kunnensa, 

  "Labib kuwa sai shafa bakinsa yake yanda ya fashe lokaci guda yana tuno soft skin d'in Zubaidah...

   "What did you Labib,...  Mi kayi cikin gidan chan,???
  "Tariq ya tambaya yana watsa kallo wa  Labin..

   "Murmushi Labib ya kumayi kafin yace " Tana nan yanda take,  Coca-Cola shape d'inta na nan yanda yake,  she reminds me of that night, Mennn I wish I could pull her in my arms,  ba don wnn munafukin Jalal d'in yazo ba da na sake d'anata.... Ya k'arashe maganar yana wani tand'e leb'e kaman tsohon maye...

   "Tsaki Tariq ya buga don sai yanzu ya gane abinda Labib yayi,..
 "So dama gidan Jalal  kazo, kayi threatening matarshi,  What's wrong with you Labib,  anya kuwa da sauran imani a tattare da kai,  Jalal doesn't deserve that at all,  remember he sacrificed his life for Us,  we all know that he's innocent yet baka k'yalesu ba,  haba haba labib this is going out of hand....

  "Kai Malam dalla ya isheka,  Jalal never sacrificed for Us,  on the contrary son yarinyar yake shiyasa ya aureta,  don haka kar ka kuma cewa  ya sacrifising mun wani abu,...

  "Hold on,  to bansan dalilin da ya kawoka gidan su,  kaga wllhi ka kuma jawo wani abin bana ciki,  wanda nayi ma ina nadama...

  "Gajeren tsaki Labib yayi kafin ya kwashe duk yanda abin ya kasance ya fad'awa Tariq..

  "Tab'e baki kawai Tariq yayi daidai layin gidan Zulaihat yace su ajiyesa,....




   "A tare suka k'arasa garesa ita da Kamal,  dukansu kuka suke,..
   "A hankali take furta "Ka tashi... Ka tashi pls...

   "Ko hannunsa bai iya motsawa da kyau sai Bud'e lumshasshun idanunsa da yayi a hankali, da k'yar ya iya furta "
  "Are you okay,  did they hurt You.. Sun maki wani abu... Tari ya soma yi yana yunk'urin tashi yana rik'e k'irjinsa dake masa azaban ciwo...

   "Girgiza kai ta soma yi har lokacin tana hawaye kafin tace " Basumin komai ba,  ka tashi daga k'asan nan you are bleeding...

   "Yunk'urin tashi yayi ya kasa,  a hankali yake fad'in" I can't, bazan iyaba Zubaidah...

   "K'rjinta yaci gaba da lugude ga hawayen dake bin k'uncinta sanda take k'ok'arin d'aura hannunta a jikinsa,  kasa tab'a as tayi sai karkarwa da hannunta keyi....

   "Ganin ya kuma lumshe idanunsa alamun babu k'arfi ko kad'an a jikinsa ga jini dake bin hancinsa yasa ta runtse idanunta kafin tayi ta maza ta tallafo sa dukda nauyin da yake dashi,  ga shaking da jikinta keyi,  d'an dafe garu yayi tana rik'e dashi har suka shige d'aki, taimaka masa tayi ya kwanta akan gado....

   "Da sauri ta fice daga d'akin gamida sakin nannauyan ajiyan zuciya,  k'arasawa d'akin Annah tayi ta tabbatar Kamal ya koma bacci kafin ta fito tana tunanin ta duba Jalal ne ko ta barsa....


      "Hadiza ta d'aura hannu aka tana fad'in na shiga uku ni dije,  hande bim boni,  yanzu ina wann shashasahn ya shiga sai Allah...

   "Annah ta watsa mata mugun kallo kafin tace " Ke rayuwa komai bai zama ishara a gareki,  zagin miji kin maidasa ba komai ba,  ki zauna kiyita zaginsa kiga ko zagin zai fito maki dashi...  K'wafa Annah tayi kafin ta ci gaba da tambayan rumfar gabanta...

   "Hadiza ta bita da kallo baki a Tab'e kafin tace "Chan maki idan kinji haushi na....

   "A can wani rumfar suka hangosa an saka kallon k'wallo an cika rumfar sai faman wage baki yake yana dariya....  Annah hamdala tayi ta nufi rumfar ai bata ankara ba sai hango Hadiza tayi tana jawo kunnensa tana fad'in" Yaushe ka soma cin kasuwan dare ban sani ba,  hak'uri ya shiga bata yana k'ok'arin k'watar kunnensa.
  "Yanda Hadiza take shiga bata nan take fita ba,  hannu tasa ta shiga lalume aljuhunsa tana fad'in" Ina kud'in Lemon  naka yanzu haka ka bari sun laleka ko kana nan ka hangame baki da hanci kana kallo ko,  toh  wllhi gwarama tun wuri ka nemo kud'in nan don wllhi bazan sake baka jari ba...

   "Kuka ya soma mata Don kuwa shakka babu an lale sa tass a wajen...

   "Mutanen wajen kuwa me zasuyi banda dariya...

    "Annah kunya kaman ta nitse cikin k'asa,  k'arasawa tayi fuska a tamke ta rik'o Hadiza da k'arfi gaske kafin tace "Idan munje gida sai kicigaba daga yanda kika tsaya uwar shi.....


   

    "Tana kwance tunaninsa ya addabeta,  yau sati guda knn babu shi babu labarinsa,  k'ila ya koma Dukku ne,  k'ila bazata sake ganinsa ba,  a hankali ta sauk'e ajiyan zuciya,  lokaci guda taji ana mata knocking,  zuciyarta ta cika da addu'an Allah sa Umar ne.....
   "Da azamarta ta nufi k'ofar ta bud'e fuskarta cike da fari'a....

    "Cak taja ta tsaya ganin akasin sa,  Tariq ta gani tsaye jikin k'ofar da ganin fuskar sa kasan babban abu na damunsa...

   "D'an k'arasawa tayi snn ta basa light hug kaman yanda ta saba kafin tayi saurin d'aura fake smile a Face  d'inta don kar ya gane halin da take ciki.....

   "Tanata masa magana babu response, d'an jim tayi tana karantar sa kafin tace " My Tee lafiya kuwa, meke damunka..

    "Kallonta ya d'anyi kafin yayi gajeren tsaki yace lafiya, me kika gani ya k'arashe maganar yana kurb'an drink d'in datayi serving nasa..

    "Sauk'e ajiyan zuciya tayi kafin tace " You don't seem well ne...

   "Gajeren murmushi yayi da gefen bakinsa kafin yace " Na gaji ne kawai kinsan kwana biyu ban zauna ba tunda muka soma bikin Salim.  Ya k'arashe maganar yana bud'e mata hannuwansa kana yace " Oya come here,
  "K'arasawa tayi cikin k'irjinsa ya rungumeta very tied,  a hankali salon nasu ya soma canzawa,  cak ya sureta suka shige d'aki... *Allah ka tsaremu Ameen.......*



    "Tafi minti biyar tsaye a k'ofar d'akinsa hannunta d'auke da ruwa da tawul, banda lugude babu abinda k'irjinta keyi, a hankali ta sauk'e ajiyan zuciya kafin tasa hannu ta murd'a handle d'in,  har lokacin yana nan kwance yanda ta barsa idanunsa a lumshe....

    "K'arasawa tayi k'irjinta sai fat fat fat..  Yake.

   "Ciwon fuskarsa ta soma gogewa da ruwa da towel d'in,
    "A hankali yaji sauk'an abu mai d'umi a Face d'insa,  ya bud'e lumshasshun issuing nasa da kyar,  ya sauk'esu kan kyakyawan fuskarta mai cike da firgici da tsoro, a hankali ya Saki murmushi,  tayi saurin sadda idanunta,  bugun k'irjinta na k'aruwa,  lumshe idanunsa ya kuma yi ba tareda yace komai ba...
    "kyakkyawan fuskan nasa yana fad'o mata sanda ya rik'ota yana dariya yana tangad'i ya mik'ata ma  Labib,  ta goge hawayen da ya zubo mata ta yunk'ura zata tashi saiji  tayi tattausan hannunsa cikin nata ya rik'e gamm...
   "A hankali ta juyo tana dubansa har lokacin idanunsa a lumshe yake fad'in" Pls saty, pls don't leave, kar ki fita su sake dawowa,  I'll never forgive my self if they harm you.,  let me protect you pls.....

   "Kuka ne ya kuma kufce mata, a hankali ta durk'usa tana k'ok'arin toshe kukan da ya zo mata...



  *Dasuki Mansion*

 "Agogon hannunsa ya duba k'arfe goma da mintoci,  yasan Mami tayi bacci by Now,  kai tsaye Penthouse d'insa ya nufa yanda Guest d'insa yake,  kaman daga sama yaji muryar Mami daga balcony tana kiransa,  gabansa ya fad'i don baiso taga ciwon dake bakinsa..

     "K'arasawa yayi suka had'u a parlor k'asa,  sai faman kauda kai gefe yake sanda suke gaisawa,

       "Ina ka fito bayan securities sunce min tun d'azu kuka dawo daga wajen sinner d'in.

      "D'an gajeren tsaki yayi kafin yace " For Allah's sake stop treating me like kid Mami,  wai yaushene zan girma a gidan nan a daina tuhumata ina na fito ko ina zanje,  I'm a business man fah yanzu Mami,  karki mance na soma aiki da Dasuki Holding,  pls Mami ki daina sa ma ranki damuwa kinga Dr ya hanaki shiga damuwa tun bayan rasuwar Dad.

      "Gyad'a kai Mami tayi kafin tace " Dole na damu da kai Labib coz you are my only child,  ina sonka fiye da yanda kake tunani,  bana fatan wani abu ya sameka Son...

     "D'an jim yayi kafin yace " I love you too Mami and I promise you I'll take care of my self,  yayi maki.
  "A hankali ta gyad'a kanta daga haka pecking goshinta yayi yace goodnight Mami....

   "Kallo ta bisa dashi,  tana son tambayarsa a ina yaji ciwo amma bai bata Chance d'in tambaya ba...  Kallo ta bisa dashi cikin zuciyarta tana masa addu'an kariyar ubangiji,  tana son d'an nata dukda ya kasance gagararre maras jin magana musamman yanzu data rasa mahaifinsa....


     "Yana shiga penthouse d'insa ya hangi k'ofar d'akin da Umar yake alamun wuta a kunne,  knn beyi bacci ba,  da sauri ya nufi hanyar d'akinsa saidai kafin ya cimma k'ofarsa sukayi kicib'us a bakin k'ofa......



   "A haka hannunta na rik'e cikin na Jalal bacci yayi awon gaba dasu baki d'aya.....



*This all you can have for today,  I hope it will shine your day..... 😜😜😻😻😂*

Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:19] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                          38


*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*




   "Faisal ya mik'a takardun hannunsa ma Alh Kasim cike da rusunawa yace" Its done Boss,  na gama binciken da zanyi akansa baki d'aya,  he's here to seek his revenge,  yanzu haka yana gidan Labib babu wanda yasani, Boss I think Labib is using the guy,  I'm quite sure he's up to something.....

    "Murmushi Alh Kasim yayi kafin yace " K'warai kuwa so yake ya had'a min trap,  he couldn't accept the fact that I have nothing to do with his father's death, ..... Ya kuma yin wani murmushi suka kalli juna shida Barr Munir kafin yace " Yaro dai yaro ne.

   "Drawer ya jawo ya ciro wani check ya mik'a wa Faisal yace make sure anyi withdrawing kud'in nan before azahar....

   "Faisal ya karb'a cike da rusunawa kafin yace " Considered it done sir... Daga haka ya fice yana saka check d"in cikin suitpocket d'insa...

   "Barr ya kalli Alh Kasim yana murmushi kafin yace " Alh karfa ka mance Nephew d'inka ne don't mess his life..

   "Murmushi Daddy yayi kafin yace " The boy is somehow desperate, He's trying to protect him self but he don't know how, mikewa yayi yana gyara suit dinsa kafin yace " On the contrary I'm doing this to protect him,  tunda na gama da mahaifinsa snn ban bar masa komai ba  kaga ai ya kamata na kula dashi..  Gaba d'aya sukayi dariya su duka biyu...
  "Barr Munir kuwa cikin zuciyarsa cewa yayi shed'an ma na tsoron Alh Kasim....
  "Intercom ya danna kafin ya soma magana da sakatariyansa kan ta kira wayan Labib tace yana nemansa a office dinsa....


    "K'arfe 9:00am daidai ya nufi d'akin da take,  a hankali  yasa hannu ya murd'a k'ofan d'akin tana zaune gaban dressing miro d'aure da towel tana shiryawa...

   "Ko kad'an bataji shigowarsa ba sai ganinsa tayi akanta...
   "Wani uban tsaki taja kafin ta mik'e tana fad'in" Don't even know how knock.... Ta k'arashe maganar tana watsa masa harara kafin ta wuce ta nufi bathroom,  da sauri Salim ya rik'ota ya rungume tsam murya na rawa yake fad'in"

   "No... Pls no Kausar,  don't do this to me, don't reject me pls,  I can't help it anymore, I'm dying to be with you, you know how I waited so long for this ....  Kissing d'inta ya soma kota ina kaman wani tsohon maye....
   "Da k'arfin gaske Kausar ta turesa gefe tana fad'in" Let go of me,  how dare you,  na tsaneka Salim,  na tsaneka.. Why can't you understand..
  "Hannu tasa tana share hawayen idonta ta nufi bathroom...  Da sauri ya kuma rungumota da iyaka k'arfinsa wann karan.  K'afa yasa ya tura k'ofan d'akin had'i da murd'a lock...

   "Jikinta ya soma rawa,  kallon mamaki take masa kafin tace " What are you doing Salim,  pls don't,  I beg of don't....

   "Bai tsaya saurarenta ba ya shiga zuge belt d'in wandonsa... 
  "Tsalle ta kuma yi zata tashi ya danne ta..... Sosai ya murd'e hannayenta, cikin wani irin yanayi yake sunbatar ta,..
 
   "Bakinta bai mutu ba taci gaba da fad'in" Yanzu na tabbatar Kai ka mata fyad'e,  now I believe you are capable of raping... Na tsaneka na tsaneka for good..

   "Sassauta rik'on da yayimata yayi a hankali,  idanuwansa sun kad'a sunyi jazur...
   "Da k'yar yake iya fad'in" Kausar I couldn't help it,  I'm desperate to feel your body,  you know I've been dreaming of this,  Kausar I love you,  I love everything single thing about you...  It was never my intention na maki abunda na maki yanzu but pls consider my situation,  haba haba ta yaya zaki d'auki maganar wata ki amince sama da nawa,  wllhi k'arya take min pls believe me sweetheart,  ko saninta banyi ba, k'arya ta maki sabida ta d'auka Jalal d'an gidan  nan ne, sai bayan ta basa kanta ta gane ba d'an gidan nan bane shine duk abin duniya ya dameta coz bata cimma burinta ba na auren Dasuki Family,  pls believe me my love I'm telling you the truth...

   "Harara kurum take watsa masa ta goge hawayen idanunta kafin tace " Naji,  ka tashi ka fita idan ba so lake ni na fice na bar maku gidan ba...

   "Fuzar da iska yayi gamida shafa gashin kansa kafin ya mik'e jiki babu k'wari ya nufi k'ofa,  yana fita taja dogon tsaki ta shige bathroom wai sai ta sake wanka tunda ta had'a jiki dashi.....



     "A parlour Salim ya tadda Mummy fuska fal fari'a take kallon d'an nata...
    "Goodmorning Son,  ta fad'i tana k'arasowa kusa dashi,  ganin fuskarsa babu walwala tamkar ba ango ba yasata cin birki...
  "Yaya dai Salim,  Lafiya,  ta tambaya tana k'arasowa...

   "K'arasa d'aura tie d'insa yayi ya d'an rank'wafo ya manna wa Mummy peck a chick d'inta kafin yace " Good morning Mom,  Daddy fah is he still asleep..

   "Kallonsa kawai Mummy tayi kafin tace " Ya wuce Office tuntuni...

   "Gyada kai yayi kafin yace " I'll see him at the company..

  "Wai lafiya Salim,  meke damunka,  wani abin ne ya sami Kausar..

   "Dessert d'in dake saman table d'in ya d'an cakala,  kafin ya dubi Jane dake jera abinci bisa dinning yace " Jane tell Mike to get my car rady....  Daga haka ya d'auki mug ya soma sipping coffee..

    "Magana nake maka  Salim meke faruwa,  and me zai fitar da kai bayan kana hutun aiki...

   "Gajeren tsaki yayi kafin yace " Oh please Mum,  I don't wanna talk about it,  I already lost my appetite...  Ya mik'e gamida d'aukan phone d'insa yace " Na wuce office....  Kallo Mummy ta bisa dashi cike da mamaki..  Yana ficewa ta nufi sashensa yanda aka ajiye Kausar don sai sun dawo daga Honeymoon kafin su  tare a gidansu.....


    "Knocking Mummy tayi a k'ofar parlorn,  jin ba'a amsa mata ba yasata tura k'ofan a hankali ta shige,  ganin Kausar zaune saman kujera yasata sakin murmushi,  ta k'arasa ta ajiye tray d'in dake hannunta saman dining table....

    "Mummy ta k'arasa ta zauna d'aya daga cikin kujerun..  Da k'yar Kausar ta iya gaisheta...

     "Mummy ta tsareta da ido tana son karantar wani abu..

     "Kausar is everything alright,  ta tambaya tana kallon Kausar wacce hankalinga kacaukam yake ga TV...

     "Sai snn Kausar ta juyo tana duvanta ta Saki wani murmushi takaici kafin tace " Everything is not alright mummy until your Son finally divorce Me, daga haka ta mik'e ta nufi  d'aki...  Mummy ta daskare tana binta da kallo...

     "Har ta isa k'fan d'akin kafin ta juyo ta dubi Mummy da kyau tace " Banyi kama da zama matar criminal ba,  so pls kisa d'anki ya sauwake min,  snn kar kuyi asaran kud'inku wajen sayan tickets babu yanda zanje da Criminal son dinku,  excuse me....  Daga haka ta wuce d'aki had'i da banko k'ofar ta bar Mummy nan zaune kaman an dasa....




    "Mamaki ne ya ishi Annah ganin Jalal  baya d'akinsa,  sam batayi tunanin Jalal zai fita aiki ba sabida raunukan dake jikinsa,  to her surprise ya fita,  babban abin da yafi damunta shine ko gaisawa basuyi ba balle sallama,  bayan tasan d'an nata ba haka yake ba...  Juyawa tayi da tray d'in dake hannunta zuciyarta cike da zullumi....



      "Koda Umar ya tashi ya tarar Labib ya fice,  Kallo ya ringa bin gidan dashi yanda aka zubar da Naira,  komai na gidan abin sha'awa ne,  wnn shine irin rayuwar da yake Madelin samu,  tabbas babu abinda Labib ya nema ya rasa....  A hankali ya k'arasa k'ofar d'akin Labib ya d'an tura k'ofar yajita a bud'e, sandarewa yayi sanda ya shiga cikin d'akin duk kyaun d'akin da aka sauk'esa bai kama k'afar wann ba,  kai his whole life bai tab'a ganin d'aki mai kyau irin wnn ba,  k'arasawa ciki yayi yana tafiya cikin k'asaita yanaji inama ace this is his life..
   "Kai tsaye closet d'in Labib ya wuce yanda yaga kaya tamkar shago,  komai an jerasa in an arrange manner.
   "wajen suit daban wajen tie daban wajen jampa daban wajen k'anan kaya daban,  Kai komai dai da wajensa..  Takalma kuwa tamkar kantinsu,  drwers din agogo masu d'an karan tsada da links daban, gabansa ne ya fad'i ganin bindiga cikin drower din,  ya jima yana juya bindigar kafin  ya ajiye,  zuciyarsa tana raya masa k'ila ya ajiye bindigar ne don kare kansa,  k'ila yanada license....
    "d'aukan agogo d'aya yayi yana juyawa yana kallo,  label d'in agogon na jiki,  idan kayi converting to Nigerian currency wajen dubu d'ari biyar kud'in agogon,  d'aurawa Umar yayi a hannunsa yana kallon kansa a mirror,  a gefen bedside ya hangi wani hoto,  su hud'u ne jikin hoton sun daddafe kafad'un juna kowa da sunansa a k'asa.....  Idonsa ya sauk'a kan sunan Jalal,  ya d'ago hoton sosai yana kallon wanda aka rubuta Jalal a k'asansa..... 

      "Kaman daga sama yaji ana bubbuga k'ofar penthouse d'in ana fad'in "Labiiib,  Labiib  come down here you bastard...

    "Da sauri ya lek'a ta window.. A fili ya furta WHATTT!!!! Juyawa yayi ya kuma kallon hoton tabbas wnn shine Jalal,  a sittin ya suri bindigar ya nufo k'asa......



Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:19] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                             39


*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*


    "Da k'arfin gaske Umar ya Bud'e k'ofar for good 3mins suna k'arewa juna kallo kafin Umar ya finciko Jalal cikin parlorn,  fuskarsa tayi turning to red haka nan idanunsa, wani wawan naushi yakai ma Jalal saida yakaisa k'asa, 
   "D'ago kai yayi cike da mamaki yake kallon mutumin da ya naushesa wanda keta faman huci kaman kububuwa,  shafa hancisa yayi yaga jini...
  "A zuciye ya mik'e dukda raunukan dake  jikinsa bai hana kai ma Umar duka ba,  ya rik'o wuyarsa yana fad'in " Ina boss d'in naka da yak'i sauk'owa, ya turo ka,  yana tsoro ne kar na kashesa..? Go and tell him,  if he dare try to come near my wife,  I swear na rantse sai na kashesa without thinking twice, Go and tell him Zubaidah is not alone,  She's with me,  and I'll protect her till my very last breath...  Daga haka yayi jifa da Umar ya fad'i gefe...

   "Goge bakinsa yayi yana kallon Jalal,  komai ya shiga dawo masa, ya tuna shi kad'aine ya hanasa kasamcewa da farincikinsa Zubaidah... bindiga ya d'aga yayi pointing kan Jalal dashi snn ya soma fad'in" You don't deserve to live you coward, Barin irinku a doron k'asa masifa ne,  You are the only reason Why Was separated from her, Zubaidah left me because of you,  I'll all make you pay kaida ita,  zan kasheka snn na kasance da ita har k'arshen rayuwarmu... Zubaidah is mine, mine alone.... D'ana bindigar yayi saidai kafin ya harba Jalal yayi dabaran take carpet d'in baya da k'afarsa wanda yasa Umar yayi loosing step,  take bindigar ta fad'i tsalle d'aya Jalal yayi ya d'auka,  Umar kuwa buga kansa yayi jikin kujera,  Kukan kura ya kumayi ya nufo Jalal,  Ganin bindigar a hannunsa yasa yin surrender....

   "Jalal  ya gane wanene wnn a yanzu,  ya gane shine Umar d'in Zubaidah wanda aka masu baiko ada...  " Cikin kakkausar murya ya soma fad'in"
  "You don't deserve her,  where were you when she was suffering, where were you lokacin da suka ci zarafinta,  ina kake lokacin da suka saka takunkumi wa rayuwarta,  ina kake lokacin da suka tilasta mata auren wanda bata so,  ina kake lokacin da sukayi dnying right d'inta suka hanata magana akan abinda aka zalunceta,  ... Muryarsa ya soma rawa sanda yaci gaba da  fad'in" Baka nan,  an fad'a maka magana ka d'auka ka hau kai ka zauna  ba tareda yin k'wak'waran bincike ba,  If you really loves her the she loves you bazaka yarda da duk abinda aka fad'a maka ba,  Zubaidah tana sonka tana k'aunarka,  but clearly you don't deserve her,  she needs someone that will protect her from the Dasuki's.... Ya d'an ja fasali sanda yaga jikin Umar yayi sanyi kafin yaci gaba da fad'in" Kana son sanin the guilty ones.

  "Labib Dasuki is guilty,  Salim Dasuki is guilty so as Tariq Maina......  "Yatsu uku ya d'aga kaman mai k'irge kafin yaci gaba da fad'in" Maza uku,  three Men raped her lokaci guda,  ka gaya min bata buk'atan taimako bata buk'atan wanda zai tsaya ma rayuwarta,  she is going through alot of pain,  she almost died of depression....
   "Idonsa ya kawo ruwa sanda yaci gaba da fad'in "
  
  "Yes I was there when they raped her, I couldn't stop them because I was a coward,  until now I still can't forgive my self,.... But I promised she will never be alone,  I'll stand by her till my very last breath....
  "Wllhi duk wanda ya nemi tak'ura rayuwar Zubaidah sai yanda k'arfina ya k'are koda kaine....
   "Ya k'arasa ya damk'a bindigar a hannun Umar kafin ya d'ago hannunsa ya manna bindigar a goshinsa yace " Now that you learned the truth go ahead,  go ahead and kill me,.....

   "Kasa tab'uka komai yayi sai wani irin ciwo da zuciyarsa ke masa,  durk'ushewa yayi a wajen ya kasa aiwatar da komai...

   "Juyawa Jalal yayi ya fice daga gidan yana d'ingishi.....


     "A sittin ya koma sama ya suri d'aya daga cikin car keys d'in Labib da suke jere cikin shell d'insu......
   "Mami kanta saida taji mamakin ficewar mota bayan tasan Labib ya tafi office tuntuni,  cikin sauri tasa a kira mata securities masu duty.....



     "Tariq na zaune cikin motarsa a gefen titi yana loda recharge card bayan ya fito daga gidan Zulaihat ya hangi motar Labib sai falfala gudu yake,  cikin sauri ya gama abinda yake ya shiga bin bayan motar......


  *Dasuki Holding*

    "Daddy ya dubi Labib yace " Baka fad'a min dalilinka na ajiye Ex fiancee din yarinyar nan a gidanku ba, what if something bad happens to you,  huh,  the world would blame me,  za'a ce ban rik'e amanar k'anina ba, na bari wani abu ya sami d'ansa....

   "Labib ya d'an shafi sumarsa kafin yace " Uncle believe me I'm doing this for us nida su Salim,  gudun kar wnn mutumin yaji gaskiyar labarin a wani waje shiyasa na aniyesa a gida kuma na fada masa Jalal ne mai laifi....

     "Alh Kasim ya k'arasa gamida dafa kafad'un Labib kafin yaci gaba da fad"in " Then you should have told me,  sai nasan abinda zanyi,  yanzu daka ajiyesa gida baka san yaya halinsa yake ba,  ga mahaifiyar ka  a gidan baka tunanin wani abu ka iya faruwa,  what if he rubbed you and run away huh??? Ko ma yayi kidnapping Mum d'inka yayi garkuwa da ita har sai an basa huge amount of money  tunda yaga gidan kud'i ne,  you shouldn't be naive Son,  mutane yanzu babu yarda...

   "Shiru yayi yana nazarin kalaman Daddy kuma fah haka ne komai ka iya faruwa,  kuma tabbas trap d'in da yake shirin had'awa Salim shima na iya fad'awa.... 


     "Securities suna ganin motar suka hangame tapkeken gate d'in company d'in tunda sunsan motar,  yana gama parking ya fito ya nufi cikin company d'in,  Kana ganinsa kasan ya gama taro duk wani Bala'i komai ta fanjama fanjam...

   "Ganin ba Labib bane ya fito cikin motor yasa Tariq bin bayansa da sauri, ganin ya b'ace masa yasa sa saurin nufan office d'in su Salim yanda ya tadda Salim ne kadai shima kallo yake a laptop din ba aiki ba..


     "Kai tsaye Office d'in President ya nufa,  babu yanda sakatariyan batayi ba wajen k'ok'arin hanasa shiga ta kasa k'arshe ta danna kiran securities,  cak Umar ya d'agata ya wullata gefe snn ya danna kai cikin Office d'in.....

    "A tare Daddy Barr Munir da kuma Labib suka mik'e tsaye,  Labib ya razana da ganin yanayin Umar,  murya na rawa yake fad'in" Umar I tot munyi da kai sai na dawo daga office muje.......  "Shurrrupppp you  Bastard .....!!!!!!  Ya daka masa tsawan da yasa sa yin shiru,  Jate sakatariyan Daddy da securities suka shigo,  baki na rawa take fad'in" I'm sorry Sir I couldn't stop him,  securities suka soma k'ok'arin capko sa,  Daddy ya d'aga masu hannu kafin yace " It's okay kuje ku rabu dashi....

    "Cike da rusunawa suka fice...

     "Alh Kasim ya k'araso yana fad'in" You must be her exfiancee,  kar ka damu I'll handle that matter,  Jalal ba matsala bane.......  "Kafin Daddy yayi shiru Umar ya d'ago bindigar yana pointing Labib kafin ya soma fad'in" What if I want my revenge on Labib Dasuki,  Salim Dasuki and Tariq Maina.....


      "Da mugun mamaki suke kallonsa kafin yaci gaba da fad'in " Na riga nasan komai you won't fool me,  you bunch of liars.....


"Mikewa Salim yayi kana ya saka pause a kallon da yake kafin ya dubi Tariq yace barin kira Labib d'in don tun jiya bamu had'u ba.....



      "Baki na rawa  Barr Munir yake fad'in" Lower your gun,  don't be stupid.....  Labib kam kasa cewa komai yayi sai idonsa da ya raina fata  yaga mutuwa k'arara.....

       "Mirya a dake yake fad'in" I'll finished you all,  miserable cowards..... Daddy yaci gaba da fad'in" Put the gun down let's talk sensibl......  Bai kai aya ba aka bud'e k'ofa aka shigo.....
    "A razane Umar ya already ya d'ana bindigar tauuuu kake ji k'aran harbi....

    "A razane suke kallon wanda aka harba,  A guje Daddy yayi kansa yana fad'in" Saliiiimmm... 



Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:19] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                           40


*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_



  *"Allah mai jefa soyayyar sa cikin zukatan bayi, DUNIYAR NOVELS GROUP hak'ik'a kuna d'aya daga cikin groups d'in da suka fi bibiyar labarai Na kuke nuna min soyayya nida rubutu na,  Ubangiji ya bar k'aunar dake tsakaninmu,  idan babu ku babu ZUBAIDAH..... THE WHOLE CHAPTER IS Yours kuyi yanda kuka so dashi💃🏻💃🏻💃🏻....  Sameena Aleeyou AKA Queen Samy loves you oceans and galaxies...😻💖💝❤*



    "Dafe yanda aka harbesa yayi gaba d'aya hanunsa ya b'aci da jini,  da k'yar yake iya fad'in. " Dad... Daddy...  Hep... Help Meh.....

   "Rungumesa Daddy yayi cikin d'imauta yake fad'in" Just hang in there Son,  you not gonna die,... D'agowa yayi kaman zararre yake fad'in " Call an ambulance,  hurry....

   "Tuni an capke Umar an kullesa cikin wani store mai duhun gaske...

   "Ambulance tana isowa aka kwashi Salim aka nufi downstairs dashi,  hankali tashe su Labib da Tariq suka rufa masu baya, 
   "Daddy ya dubi Faisal da bai jima da shigowa ba hannunsa rik'e da kud'in da yayi withdrawing yace " Take care of that Bastard, make sure he didn't escape... Bai jira amsar  Faisal ba ya nufi lift kaman zai kifa da k'asa, Barr Munir na biye dashi....


   "Ana zuwa asibiti aka wuce dashi theater room,  Barr ya jawo Daddy gefe kafin yace " Calm down Mr President babu abinda zai sami nephew d'ina besides a kafad'arsa bullet d'in ya samesa mu godewa Allah,  ni wnn  abu ma kaman ribar mu ne...  Ya fad'i yana sakin murmushi k'asak'asa... 
   "Wani banzan kallo Daddy ya watsa masa kafin yace " My only son is dying and yet kana cewa ribar mu ne,  are you insane Barr or what???

   "Barr Munir ya shafi tand'alelen sok'onsa da yayi kusan raba tsakiyan kansa kafin yace " Kai kam bari ka gani,  da wnn zamuyi amfani mu ci nasara kan yarinyar nan da take neman kawo mana cikas, ya kashe ido guda kafin yace  "Kausar,  yanzu dai barin tafi gidan...
  "Tuni Daddy ya d'ago nufin Barr don haka murmushi ya saki yana jinjinama Attorney Munir...
  "Mik'ewa Barr yayi ya fice daga asibitin ya nufi motarsa....

**********
  "Tsaye take tsakar gida tana gyara hijabinta don yau zata soma zuwa school,  ta sami gurbin karatu a wani sec sch maras nisa da unguwarsu,  yanda aka bata matakin aji biyar sabida kwazonta, ....
   "Da mamaki take kallon Jalal dake k'ok'arin shigowa do alama raunin jikinsa sun k'aru ko kuma ya fama,  kaman zata juya ta koma d'aki sai kuma ta fasa ta d'an sha kunu...  Saida ya iso dap da ita kafin ta gaishesa da kalma guda...

    "Cike da mamaki yake dubanta don tunda suke bata Tab'a gaishesa ba sai yau,
   "D'an murmushi yayi kafin ya amsa snn ya k'ara da ina zaki je...

     "Galala ta dubesa kafin ta kauda kai gefe tace " Ba lallaine kaji yanda zanje ba..... Karaf sai a kunnen Hadiza,  dariya ta tuntsure dashi kafin ta soma zuba uwa kurna,  "Yo dole ma yasan yanda zakije don wllhi duk yanda kika taka bada amincewarsa ba wuta kika taka,  shegen iyayi da feleke karatu ya wuce maki amma kice sai kinyi......  Maganganun Hadiza yasa Annah fitowa babu shiri.
   "Yama rasa me zaice ma wnn matar gashi shi be iya hayaniya ba kuma darajar Hamma Habibu take ci a idanunsa, .. Muryar Zubaidah ne cikin kuka ya dawo dashi daga duniyar tunanin da ya tafi, fad'i take..
    "Ni wllhi baikai ya bani izinin fita ba sabida babu aurensa akaina....  "Saida Annah ta lallasheta kafin tayi shiru,  ta dubi Jalal dake kallonsu kurum without saying anything, 
   "Kai kuma da wnn jikin naka ina ka fito,  Annah ta tambaya,  kai tsaye yace.  
   "I went Dasuki's....

    "You what,  lafiyanka Jalal mai zaikai ka wajensu kuma salon su k'arasa ka,  jin haka yasa Hadiza saurin dawowa don da har ta nufi b'angarensu...

   "Jalal yace " Annah bazasu zo har cikin gidanmu suci mmana zarafi su tafi a banza ba,  idan mukayi shiru muka k'yalesu they will keep bothering us,  at least ko munada talauci su sani cewa we do have a heart.... Ya d'an ja fasali yana kallon Zubaidah data daina kuka alamun tana sauraren maganganunsa kafin yaci gaba da fad'in"
    "Unfortunately ban samesu ba amma na sami wanda zai isar masu da sak'onsu,  its seems they are allied or maybe sunyi manipulating d'insa sun sayesa da kud'i kaman yanda suka saba...

   "Da mamaki Annah tace "WA kenan??

   "Har lokacin idonsa da sukayi jazir na kan Zubaidah kafin yace "UMAR, wanda aka masu baiko a da, I confronted him and told him everything,  The whole truth ..... 
    "A zabure ta d'ago idanunta da yake jik'e shakaf da hawaye tana dubansa shima ita yake duba fuska a tamke..
   "Girgiza kai take kaman zararriya take fad'in" Umar yazo nan garin Umar d'ina,  snn yana gidan azzaluman nan,  ba Umar ka gani ba saidai mai kama dashi,  don na tabbata da kunyi ido biyu dashi da baka dawo da rai ba...
   "D'an murmushi yayi da gefen bakinsa don yana son ganin tana magana kafin yace " Bansan shi ba balle nasan kamanninsa,  shi da bakinsa ya fad'a min ko shi wanene,  and na fada masa duk abinda ya faru,  da yaso kashe ni da yayi don ya sami chance.....  Yana gama fad'in haka yace wuce muje na kaiki makarantar... 
   "Kallon mamaki ta bisa dashi ganin ko alamun wasa babu a tattare dashi gashi yasha mur sosai,  .... Ganin sunyi cirko cirko suna kallon juna yasa Annah cewa "A'a Jalal ka huta dama ni zan kaita...
    "Girgiza kai yayi kafin yace " Annah those people are very dangerous, I don't want her to get harm,  let me protect her da taimakon Allah pls...
    "A hankali Annah ta gyada kanta gami da sakin Zubaidah tayi masu Addu'an kariya...
    "D'ago Kai tayi zata masa tsiwa taji ta kasa ba tareda tasan dalili ba, ... Wuce muje,  ya fad'i yana zura hannu maras ciwon a aljihu wanda nake zaton kud'in jikinsa yake lalumawa...

     "Sai snn Hadiza ta sauk'e wani nannauyan ajiyan zuciya,  Umar a garin nan,  lallai dole taje ta kira Iyalle taji Wata uwar wainar aka tuya tun bayan barinsu Dukku...

***********

    "Asmah I can't stand him anymore,  I hate him I hate him like hell, He's already disgusting to me... Ta k'arashe maganar cikin rawar murya...
   "Hannayen Kausar Asmah ta rik'o kafin tace " Sis stop saying all this pls,  ni a ganina ba gaskiya bane don idan da gaskiya ne su Daddy bazasu bari hakan ta kasance ba tunda responsible mutane ne,  you should have at least give him a chance,  listen to him, you don't have to shut him out he's your husband no matter what...

   "Hararanta Kausar tayi gamida tab'e baki kafin tace " Wato kema kin yarda da k'aryan nasu ko,  wllhi Asmah na yarda hundred percent Salim yayi raping yarinyar nan, ke ai kinsan hukuncin fyad'e tunda fannin da kike knn a kotu...
   "Gyad'a kanta Asmah tayi kafin tace " But this is different cousin the victim married the rapist,  batayi magana ba  bata nemi hakkinta ba,  she chooses to be with her rapist then fine let them be,  kar ki zama mak d'aukam zantukan mutane don shaidan fyad'e babban Al'amari news kotu,  sabida fyad'e babban laifi ne,  pls Kausar ki nutsu a gidan aurenki , me kike tunani idan aka sake ki a yanzu  Me  zaki ce wasu  Mumsy da Pappy,  bayan farin cikin da kika sasu kina son jefa su cikin bak'in ciki ne,.....

   "Kausar dai shiru tayi sai k'walla da suka ciko idanunta,  Asmah cike da tausayawa ta kuma rik'o yatsun hannun 'yar uwar tata kafin taci gaba da fad'in    "     Reconcile, talk to your husband fix everything together okay,  I know it might be difficult but pls do it for the sake of your marriage kinji...

   "Ba tareda tace komai ba ta rungume Asmah tana hawaye....

    "Mummy na zaune a parlor tana kallon tashan labarai Barr Munir ya shigo kaman an jehosa,... 
    "D'an zabura tayi kafin tace " Brother lafiya ka shigo min parlor haka,  you gave me a fright....

    "Shafa sank'onsa yayi kafin ya shiga zagaye parlorn,  a tamanin Mummy ta mik'e ganin yanayin nasa sosai ya razanata,
  "Wai meke faruwa ne??  Ta kuma tambaya.


      "Zama yayi bisa sofa kafin yace "Farha Ina Kausar??

    "Tana sashensu,  cewar Mummy

   "Ki kirata kuzo muyi magana,  ya fad'i yana matse k'wallan idonsa...


      "Wai meke faruwa ne,  Mummy ta kuma tambaya sanda muryarta ya soma shaking.... Ka fada min meke faruwa Ta Munir na rok'i arzikinka....


      "Tasowa yayi daga kujeran da yake ya dawo kujeran da take zaune ya rik'e hannayenta yace " Calm down pls Farha,  idan baki kwantar da hankalinki ba bazan iya fad'a maki ba,....  Shiru tayi tana k'unshe bakinta da kuka ke neman b'alle mata,  k'walla kira yayi wa  Jane dake kitchen d'in Mummy kafin yace ta kira masa Kausar..  Nan da nan Jane ta wuce kiran Kausar....




        "A tare suka shigo parlorn itada Asmah,  Sai faman cin magani take ba don Asmah ta matsa mata ba ma da ba zuwa zatayi ba..

     "Gaisar da Uncle Munir sukayi kaman yanda Salim ke kiransa,  Sun sha jinin jikinsu da ganin yanayin Mummy, 
    "Barr yace su Zauna magana zasuyi akan Salim....  K'irjinsu yabada Rass ..!!!

     "Mummy cike da damuwa take fad'in me ya sami Salim...  Ka fad'a min Munir...






Sameena ce
[1/23, 22:20] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*


                             41

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*




    "Shiru parlorn yayi suna sauraren Barr Munir,  banda bugun k'irajensu baka jin komai, ...

   "Saida ya kuma goge k'wallan idonsa kafin ya soma fad'in" Salim.... Salim was trying to commit suicide, he shot himself...... Ai baikai aya ba Mummy ta saki wani irin k'ara....
   "Kausar ma toshe bakinta tayi tana k'unshe kukanta ta fad'a jikin Asmah wacce itama tashin hankalin ne ya ziyarce ta...

    "Cikin tsananin kuka Mummy ta rik'o yayanta Barr Munir take fad'in" No..  No Munir this is ridiculous,  tell me ba gaskiya bane,  Oh my baby boy me yake nema a duniyar nan bai samu ba har yake yunk'urin kashe kansa...  Mik'ewa ta kuma yi tana fad'in" Take me to him Munir,  I really want to see my boy, ...

   "Mik'ewa Kausar ma tayi idanunta sharkaf da hawaye take fad'in" I'll go with you mummy...

   "Barr ya d'an dubeta kafin yace " Inaganin Kausar ki zauna a gida,  don zuwan naki ka iya haifar da wani abin,  sabida magana ta gaskiya A DALILIN KI ne yake yunk'urin kashe kansa....  Gaba d'aya suka zaro ido harda Mummy,  Asmah tasa hannu a k'irji ta dafe..
   "Barr yaci gaba da fad'in" Salim was trying to kill himself because of you Kausar,  That filthy girl called you and told you k'aryar data saba,  wanda DAGA TAIMAKO abin nasu ya koma sharri,  a dalilin yunk'urin raba aurenku da kike k'ok'arin yi shi yasa Salim yanke shawaran kashe kansa Don bazai iya rayuwa babu ke ba, yana sonki yanda baki tsammani, don haka inaga ki zauna a gida kawai shi yafi... Hannunsa Mummy ta shiga janyo hannun Barr duk da jin zancen nasa yayi matuk'ar girgiza ta bai hanata  watsa wa  Kausar mugun kallo ba  don tasan komai ka iya faruwa tunda an jima ana b'oyewa Kausar da iyayenta, ficewa sukayi itada Munir cikin sauri....



    "Bud'e baki tayi zatayi wa Asmah magana sai kuka,  Asmah ta rungumota tana lallashi,  jin dirin motar Barr yasata d'ago kai a zabure tana fad'in" Asmau mu bisu kar su b'ace mana, I really want to see Salim,  take me to him pls...  Ta k'arashe maganar cikin fashewa da kuka....
   "Gyad'a kanta kawai Asmah tayi kafin ta rik'o hannunta suka fice suka nufi mota....


     "Mai taxi yana ajiyesu tasa kai zata shige,  saurin rik'o hannunta yayi kafin yace " I'll be waiting for you here har ki gama classes d'in naki..

    "Da mugun mamaki take duban yanda ya rik'e mata hannu ga mutane nata faman kai komo,  gaba d'aya jinta a tsarge take,  gani take kaman kowa su yake kallo, ..
  "A hankali tace " Give me back back my hand.. Tana maganar tana kallon mutane a tsarge,  d'an matsowa kusanta yayi yana murmushi kafin yace " Sai kin min alk'awarin zaki amince nazo d'aukanki snn zaki soma Therapy class d'inki as well...

   "Jin hannunsa cikin nata yana haifar mata da wani irin yanayi don haka da sauri ta gyad'a kanta kana tace " Eh naji na amince but that doesn't mean you'll be fetching me up everyday.... "

    "Murmushi ya kumayi wanda ya jima baiyi irinsa ba har saida fararen hak'waransa suka bayyana he couldn't believe wai yau Zubaidah ke masa magana haka cikin sanyin murya har tana cewa ta amince da buk'atarsa...
   "D'an sakin hannunta yayi kafin yace " I'll get you later,  take care....

    "Ba tare da tace komai ba cike da k'osawa tayi shigewarta,  k'irjinta na bugawa da sauri da sauri,  sai faman dunk'ule hannunta da ya rik'e take,  don ji take kaman har yanzu hannayensu na cikin na juna....



*Dasuki Hospital*

    "Daddy yana hango Mummy ya tafi ya rungumeta,  kuka mai k'arfi ya kuma b'ark'e mata tana fad'in" Kasim our son,  our only son,  tell me he can go through this....  Zaunar da ita Daddy yayi yana calming d'inta, Labib dake tsaye tare da Tariq yayi saurin taro ruwa a dispense ya mik'awa Mummy yana fad'in "Have some water Aunt,
   "Karb'a tayi tana kallon Labib d'in kafin tace " Tell me your brother will get out of here soon...
    "Durk'usawa yayi gaban kujeran da take zaune ya rik'e hannayenta kana yace " Insha Allah Aunt,  very soon, I know my cousin is a fighter he can get through this, ki kwantar da hankalinki pls Aunt, Yasa hannu ya amshi ruwan ya Kai bakinta kafin yace " Drink your water..
  "Gyad'a masa kai tayi ta shiga kwankwad'an ruwan...


   "Nurses ne suka Bud'e k'ofar kana suka soma turo sa kan gado mai tayu....  Ai tuni sukayi kansa gaba d'aya hakan yayi daidai da isowar su Kausar.
  "Da sauri ta k'arasa jikin gadon tana kiran sunansa,  Nurses kuwa sai faman tattaresu suke don har lokacin bai farfad'o ba snn ga oxygen saman hancinsa...

    "Intensive care  aka saka sa snn aka hana kowa shiga,  saidai suna hangensa ta glass..

    "Mummy tamkar baud'eddiya haka ta koma,  saida Mum d'in Tariq ta iso kafin ta d'an sami nutsuwa...


   "Suna zazzaune gaba d'aya a reception, gaba d'aya Kausar jinta take a tsarge ganin kowa da kalan kallon da yake mata,  she felt guilty for what happened, Asmah ta lura da haka taja 'yar uwarta ta kwantar bisa kafad'a coz she knows exactly how she feels.
   "Asmah bani wayarki ban fito da tawa ba,  Kausar ta fad'i cikin rawar murya ,
   "Mik'a mata Asmah tayi ba tareda tace komai ba..



    "Mumsy da Pappy suna bisa dinning table suna breakfast lokaci guda suna firan d'iyar tasu da sukayi kewarta wayar Mumsy ya soma ringing,  d'agawa tayi tana murmushi take duban mijin nata kana tace "Kaga muna zancenta ga wayar Asmah, k'ila tana can gidan nata..
    "Murmushi kawai pappy yayi gamida sipping coffee d'insa sanda Mumsy ke amsa wayar...

    "Jin muryar Kausar ce ba Asmah gashi cikin wani irin ta yanayi yasa hankalin Hajiya Raliya tashi wanda yasa Alh Tahir ajiye mug d'in hannunsa babu shiri...

    "Wani asibiti kuke,  okay gamu nan zuwa,  Mumsy ta fad'i kafin ta kashe wayar tana duban mijin nata wanda shima ita yake duba..

     "Meke faruwa,  waye a asibiti,  Pappy ya tambaya sounding curious...

     "A daburce ta soma fad'in" Wai Salim ne babu lafiya yana intensive care,  Pappy our daughter need us tashi muje pls,  oh my poor baby kuka take sanda take min magana...


    "Subhanallah d'auko min wayata a sama barince Lawan ya fito da mota,  cikin sauri Mumsy ta amsa kafin ta nufi upstairs.....

***********


   "Wani farinciki maras misaltuwa yake ji haka kurum wanda shi kansa baisan dalili ba,  ni kuwa Sameena nace (Jalal keep on saying  taimakonta kake..... you are into the girl irin totally d'in nan..... 😜)
   "Shiryawa yayi tsaf cikin k'anan kaya,  Ash shirt da brown chinos,  yayi kyau sosai dukda raunin dake jikinsa bai hana kyaun halittarsa fitowa ba.  A gurguje yayi sallama wa Annah ya sanar da ita zai d'auko Zubaidah snn daga chan zasu wuce gidan Dr Khaleesat therapist wacce zasu na therapy classes da Zubaidah,  sosai Annah taji dad'i ganin abubuwa sun soma canzawa tsakanin Jalal da Zubaidah...



    "Tana fitowa daga gate d'in makarantar ta hangesa tsaye kasan wata bishiya,  haka kurum taji mugun fad'uwar gaba,  d'an saita kanta tayi kafin ta soma tafiya cikin tsanaki...

    "Tun daga nesa yake murmushi kumatunsa saielotsawa suke, har ta k'araso yanda yake ta tsaya daga can gefe, fuskar nan tana tamau babu alamun fari'a...
   "Yasan bazata masa magana d'an kallonta yayi kafin yace " Shall we..

    "Ba tareda ta kallesa ba ta soma tafiya.
     "So how's your first day at school, ya tambaya sanda suka k'arasa bakin hanya..

   "Shiru kaman bazata amsa ba sai kuma tace "Lafia a tak'aice...
   " Har suka shige tasi d'in bata kuma cewa komai bar,  shima shirun yayi har suka isa gidan Dr Khaleesat....

   "Bayan sun sauk'a a tasi d'in ne ta bisa da kallo alamun tambaya.

    "Yasan hakan zata kansance kai tsaye yace " D'aya class d'in zakiyi a nan...

   "Tab'e baki tayi gamida kauda kai gefe kafin tace " Niba mahaukaciya bane babu therapy d'in da zanyi...


    "D'an shiru yayi yana kallonta kafin yace " You promised me.

    "Kallonsa tayi yanda yayi maganar cikin sigan tausayi, d'an jimm tayi kafin tace " Eh ai sabida ka amince min zaka tafi shiyasa nima na amince " Gyad'a kansa yayi dukda fad'uwar gaban da yaji,  yasan ya mata alk'awarin barin rayuwarta amma baijin zai iya cikawa,  he leave her all alone.
   "D'an ware madaidaitan idanunsa yayi wanda basu faye girma sosai ba sai tsawo da shape me kyau kafin yace " Fine naji na amince mu k'arasa,  bata kuma cewa komai ba ta soma binsa a baya.. 



       "Bayan sunyi knocking mai gadi ya bud m'e masu ya tambayesu ko Dr tasan da zuwansu,  Jalal ya shaida masa ta sani snn ya buk'aci ya sake masu iso,  ba tareda b'ata lokaci ba aka masu izinin shigowa...



        "Masuk'i aka masu a parlour,  mintoci kad'an wata mata 'yar gayu ta fito at her early 40's,  da murmushinta ta k'araso tana masu sannu da zuwa,  Da gani tanada barkwanci.

       "Bayan sun gaisa ne Jalal yace shine wanda ya tura mata sak'o ta mail d'inta tace suzo gida su sameta....

      "Murmushi Dr Khaleesat tayi kafin tace " Ai tun daga ganinku na ganeku Jalal,  ta kalli Zubaidah lokaci guda tana karantar ta yanda ta zauna can gefe Jalal na wani kujera na daban.

    "Kan kace me an cika gabansu da drinks,  Dr Khaleesat ta kalli Zubaidah ta kalli Jalal kafin tayi murmushi tace " Mr Mrs Jalal  ya kuka zauna kujera daban,  kallon juna sukayi a tare babu wanda ya iya cewa komai,  Dr tayi murmushi sanda take mik'awa Zubaidah cup na drink kafin tace " Kina tsoronsa ko??

  "Kallon mamaki Zubaidah ta mata,  Dr ta kuma yin murmushi kafin ta dubi Jalal tace " Mr Jay ka d'an jira mu a wancan waiting parlour d'in,  ba tarda b'ata lokaci ba Jalal yayi yanda tace.


        "Kafe Zubaidah dake faman juya Cup d'in hannunta da ido tayi kafin tace "Feel at home kinji,  gidan nan be'azuwa ba'aci komai ba,  so ina jinki, tsoron mijin naki kike...

      "Sai snn Zubaidah ta dubeta kafin tace " Ni ba tsoronsa nake ji ba, tsanarsa nayi ,  snn ba mijina bane don ya kusa tafiya ya bar min rayuwata, ...

     "Dr ta murmusa kafin tace "Nasan bashi kad'ai ba duk wani namiji ma kin tsana,  Zubaidah ta gyad'a kanta kafin tace " Hamma na ne kawai ban tsana ba,
   "Jinjina Kai Dr tayi kafin tace " But what makes you hate them,  kallonta tayi kaman bazatayi magana ba sai kuma tasa hannau tana share idonta alamun hawaye sun zubo mata,  Dr ta d'auko tissue paper kana ta goge mata hawayen kafin tace "I know it hurts,  it's very hard to start again,  but you have to fight your Devastation,  don't let it get into you,  only then you'll live again... Ta d'an ja fasali kafin taci gaba da  fad'in" First kiyi k'ok'ari kisami soyayyar kanki,  ki k'aunaci kanki  snn kisa a ranki Allah ba yak'i ki  bane ya baki irin wann jarabawan,  no it's a trial,  it could happen to anyone, second be happy with the people around you, people that shows you love and compassion,  don't ever push them away,  don't let them go, such people are blessing from Allah.  Snn duk mutanen da kika Allah Ya ciresu daga rayuwarki you are not meant to be with them,  because sometimes absence of some people makes us something in life...

  "Tunda ta fara magana Zubaidah ta nutsu ta bata hankali sosai,  maganganun Dr Khaleesat ya haifar mata da tunanin da bata tab'a yin irinsa ba.
   "Hira Dr ta ringa jan Zubaidah dashi tana mata tambayoyi gameda rayuwarta, d'an lokaci k'ank'ani taji ta sake da Dr Khaleesat,  daga bisani Dr tacee" Toh Zubaidah ni a yanzu k'awarki ce kuma aminiyar shawarin ki,  snn pls I need you to be honest with me,  no hiding things okay......
  "Murmushi Zubaidah tayi gamida gyad'a mata kai don shakka babu taji relief a d'an wann hiran da sukayi da Dr Khaleesat.


    "Bayan sun gama da Zubaidah ta nemi ganin Jalal shi kad'ai shima,  nan ta d'anyi briefing nasa yanda sukayi snn ta basu Time d'in da zasu na zuwa,  sosai Jalal yayi godiya wa Dr ya tambayeta yanayin biyan kud'in.
   "D'an murmushi tayi kafin tace " Ta jima tana wann taimaka wa mata 'yan uwan ta da mummunar k'addara ta fyad'e ta auka masu,  she's not doing it for money,  snn labarin Zubaidah ya banbanta da wanda taci karo dasu a baya,  don haka she really wants be part of her Story....

      "Godiya sosai ya mata gamida jinjina mata, tabbas da za'a sami mutane irin Dr Khaleesat da Al'ummah taci gaba sosai,...  Allah ka yawaita mana irinsu ameen...

       "Ana kiraye kirayen sallan la'asar mai taxi d'in ya ajiyesu a k'ofar gida....

***********


    "Zaune suke  a joint d'in da suka had'u kwanakin baya,  Zulaihat ta rausayar da idanu kafin tace " Your highness har na cire ran bazan sake ganinka ba  tunda k'anwarka me kishin nan ta d'au wayarka sanda na kira..
   "Murmushi Shattima yayi kafin yace " Ai na fad'a maki Abuja gida ne a wajena,  you can see me any moment,  mayaudarin murmushi ta kuma yi sanda wayarsa tayi k'ara,  Usman ne me kira,  d'aya wayan yayi suka gaisa suna tsiya ma juna kaman yanda suka saba...

   "Zan shigo garejin ku anjima ka fad'awa Jalal pls kar ya tashi da wuri ina nan zuwa, cewar Shattima

   "Speaking of Jalal,  halan baka san ya d'an yi accident ba  ko,  jiya da yau baizo gareji ba... Usman ya fad'i...


   "Subhanallah wllhi banida labari pls ina zuwa anjima sai ka kaini gidan nasa na gaishesa,  ai na ce maka pls,  ban son iskanci wllhi zanzo..   Yauwa see you soon...  Daga haka yayi hanging up...


        "Jin anyi maganar Jalal gaba d'aya hankalin Zulaihat ya karkata kan tunaninta,  this is the only chance da zata samu su had'u da Zubaidah.......

Sameena ce 👌🏾👌🏾
[1/23, 22:20] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                               42


*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*



      "Pls let me accompany you, I insist.... Ta k'arashe maganar cikin siga na Salon yaudara.
 
 "D'an tab'e baki yayi kafin yace " Baki tunanin za'a nemeki a gida, this is totally wrong...

   "Pls Shattima don't say no,  besides we are not doing anything wrong,  Dan Allah ka bari nayi maka rakiya,  my Aunt would understand me,...

   "D'an jim yayi kafin ya gyad'a kansa yace " Okay fine amma daga can direct gida zan ajiyeki sai mu gaisa da Aunt d'inki....

   "Cikin Zulaihat ya bada quu,  don kuwa k"arya ta shera wa Shattima cewa karatu tazoyi Abj snn a gidan Aunt d'inta take zaune,  amma ko kad'an bata so tayi loosing wnn Chance d'in musamman yanzu da Tariq ya bata labarin abunda ya faru....


   "Tura masa address Usman yayi don yace bazai sami zuwa ba aiki ya cab'e masa a garejinsu musamman yanzu da babu Jalal....
   "Hakan sai yafi ma Zulaihat Dad'i....


"Ana kiraye kirayen sallahn magrib suka isa gidansu Jalal dake suleja, waya ya masa ya sanar dashi gashi a k'ofar gidansu,  unbelievably ya fice daidai lokacin da ya ida alwalan sa.
   
"Jalal yayi mamakin ganin Shattima a gidansu, nan ya fad'a masa Usman ne ya sanar dashi baiji dad'i ba,  gaisawa sukayi,  snn suka gaisa da Zulaihat ma,
   "Jalal ya masu iso cikin gida wajen Annah...

   "Da hannu bibbiyu Annah ta karb'esu,  suka gaisa cike da karamci, 

    "Bayan Annah ta mik'e kawo masu ruwa Shattima ya dubi Jalal yace "Ina Madam,??
 "Saida gabansa ya fad'i kafin ya d'an murmusa yace " Tana ciki,  let me call her..

  "A'ah kaji ma an shiga sallah,  mu k'arasa masallaci dai first,... A baranda had'u da Annah suka sanar da ita zasu mosque,  parlorn ta wuce yanda Zulaihat ke zaune sai k'are ma gidan kallo take,  tana ganin Annah ta mik'e ta amshi tray d'in da fari'ar ta, haka kurum Annah taji Zulaihat bata kwanta mata ba,..

  "Zulaihat kuwa sai k'ok'arin jan Annah da hira take,  Duk ta gundura da ita,  saida Annah tace mata bari taje sallah snn itama ta shiga ciki wajen Zubaidah tayi, kafin ta sami sauk'in surutun Zulaihat,  sam yarinyar bata mata kama da mai kamun kai ba,  shi kuwa Shattima daga ganinsa kaga yaron arziki.. Da wnn tunani ta isa bakin randa yanda butocinta ke jere tayi alwala,  a baranda ta shimfida abin sallan ta...


    "Zubaidah na zaune tana duba books d'inta don hutun sallah take,  Zulaihat ta shigo d'akin da sallama, amsa mata tayi gamida juyowa gaba d'aya...

    "Gaban Zulaihat yayi mugun fad'i da ganin Zubaidah,  tabbas dole Umar ya haukace akanta.  Murmushi ta sakar mata gamida k'arasawa tayi hugging nata without any hesitation,   Hello Zubaidah it's a pleasure to meet you,  na jima ina son had'uwa dake,  ni matar da abokin mijinki Shattima zai Aura ne,  inajin yanda Jalal ke fad'in irin soyayyar da yake maki,  so I've been dreaming of meeting you in person..

   "Cike da mamaki kawai Zubaidah ke dubanta,  d'an murmushi yak'e tayi kafin tace " Pleased to meet you too.

   "Kallon juna sukai na d'an mintoci kafin Zulaihat ta kuma rik'o hannunta tace" oh by the way sunana Zulaihat nd ina karatu a nan jami'ar Abuja snn a gidan Aunty na nake zaune,.. Hira take kan jan Zubaidah dashi,  daga bisani Zubaidah tace " Zakiyi sallah ne??

   "Girgiza kai Zulaihat tayi dukda ba hutun sallan take ba kafin tace " No I'm off. Muje parlor gasu sun dawo daga sallahn,  ba don Zubaidah taso ba haka tabi bayan Zulaihat suka fito parlorn,  gaisawa da Shattima Zubaidah tayi sai janta da hira yake yanama Jalal tsiya,  um da um um sai smile,  iyakacin abunda Zubaidah ke fad'i knn a hiran nasu..
   "Tsaf Zulaihat tana lura daeyanayin Jalal da Zubaidah,  tabbas tsakaninsu babu jituwa,...
   "Sun d'an jima suna hira kafin suka mik'e don tafiya,  Zulaihay harda rik'o hannun Zubaidah alamun itama tai masu rakiya...

   "Zaune suka tadda Annah saman darduma tana lazimi sukai mata sallama,  tai masu godiya da fatan Allah kiyaye hanya...

"Jalal da Shattima suka nufi mota sanda Shattima ya juyo yayi sallama ma Zubaidah..
   
"Zulaihat ta rik'o hannun Zubaidah kana tace "Toh Zubaidah naji Dad'in kasancewa dake sosai,  Allah sa k'awancenmu ya d'aure, d'an murmushi nan dai kawai ta kuma yi  kafin tace " Na gode nima, sai anjima Allah ya tsare hanya...

    "Da sauri ta juya zata shige gida,  muryar Zulaihat ta tsinkaya tana fad'in" Kinga zamu rabu bamuyi exchanging phone no ba..

   "D'an murmushi yak'e Zubaidah tayi kafin tace " Ban haddace no d'ina ba,  kar ki damu zamu sake had'uwa ai...

    "No ai yafi muke gaisawa Zulaihat ta fad'i sanda take zura hannu cikin jakarta,  paper da Biro ta ciro kafin ta rubutawa  Zubaidah No d'inta tace " Gashi contact d'ina idan kin shiga sai kiyi saving,  karb'a Zubaidah tayi tana murmushi,  Zulaihat ta kuma hugging d'inta kafin sukayi sallama.....  
 
   " Ganin Jalal na nufowa yasata saurin soma tafiya cikin sauri...

  ***************

   "Mumsy ta kuma jefawa Kausar dake kan zuban hawaye wani mugun kallo kafin tace " How could you be so stupid, Da iliminki da hankalinki zakyi abu makamancin haka,  ta juyo ga Asmah itama mugun kallon ta watsa mata kafin tace " And you know about it,  from the very start baki fad'a mun ba,  you all are stupid,..
 
  "Mumsy I never thought it would turn out to be serious, shiyasa ban fad'a maku ba,  Asmah ta fad'i a hankali...

 "Gajeren tsaki Mumsy tayi kafin taci gaba da fad'in" I don't know what's wrong with you Kausar,  ta yaya zaki yarda da zancen wata ki ajiye na mijinki,  for Allah's sake....
   "Mumsy I didn't mean it,  believe me so nake na tsira da mutunci na shiyasa, I know you won't want me to end up with a rapist,  a criminal....
    "Jawota Mumsy tayi ta rungume kafin tace " Of course my baby amma ba  haka ake yi,  kinyi bincike kinga gaskiya,  shi kansa mai laifin ya fad'a maki gaskiya,  meyasa daga baya zata maki waya ranar aurenki ki amince, da tanada gaskiya data fada maki tun da wuri... Oya tashi muje ki shiga kiga mijinki ya farka...


      "Rik'o hannunta tayi suka nufo d'akin da Salim yake,  a k'ofar d'akin suka had'u da Mummy,  Kausar ta sadda Kai k'asa cike da kunyar abinda tayi was Mommy,  a hankali ta soma fad'in
    "Mummy I'm sorry...... Rungumota mummy tayi kafin tace " It's okay daughter,  we all understand you,  if there's anyone who's responsible to wnn munafukar yarinyar ce marassa godiyar Allah.... Ki kwantar da hankalinki kinji your husband will soon get well ku tattara ku koma gidanku.....  Murmushi sukayi gaba d'aya suka nufi cikin d'akin yanda suka tadda Pappy da Daddy har lokacin fad'a suke wa Salim he shouldn't be stupid,  abinda yayi hauka ne ba soyayya ba cewan Pappy,  ransa b'ace ya nufi k'ofa,  mugun kallo ya watsa wa Kausar kafin ya wuce...
     "Daddy kuwa kai kace iyakar gaskiyarsa knn sai sababi yake yana nuna rashin jin Dad'insa har saida Mumsy tasa baki yayi considering situation d'in Salim kafin yayi shiru.
   "Ficewa yayi yabi bayan Alh Tahir,  jinjina lamarin suka kuma yi a wajen ma kafin Mumsy ta fito suka wuce.
  
    "Suna wucewa Alh Kasim drebansa ya kira yace Company suka nufa..
     "Wayarsa ya ciro ya shiga neman layin Barr Munir,  bugu biyu ya d'aga kana yace " Me ake ciki,  ya amince ya amshi kud'in ko kuwa??

      "Daga d'aya b'angaren Barr yace " He's strong head iina gaya maka,  he refused to cooperate,.

     "Fuzar da iska Daddy yayi yana fad'in" Damn it Damn it,  ka gane he must negotiate with us for his own good, yayi wata murmushi kafin yace " No one messes with the Dasuki's,  idan bai amince da buk"atarmu zanmu b'atar dashi kaman yanda muka b'adda sauran...... Munir do what ever you can to make him cooperate, If Alh Tahir learn the truth we are done,  so ka fad'a masa kud'in da ko a mafarki bai tab'a jin irinsu ba,  gani nan am on my way there, ...

"Murmushi Barr yayi kafin yace " Kafi gaban haka  how's my nephew, is he out of the comer?

     "He's much better,  Ya fad'i a taik'ace kana ya katse wayar....



       "Barr ya shiga store d'in da aka d'aure Umar,  Faisal dasu James suna tsaitsaye da bindigogi,  ya dubi Umar dake faman huci ya durk'usa gabansa kafin yace " Ka gode wa Allah my nephew is still alive,  da ya mutu daka bak'unci lahira .....

       "Yana huci yake fad'in" it's what he deserves, jerk like him Ya cancamci mutuwar wulak'anci....

      "Barr yayi murmushi kafin yace da Faisal ya mik'o masa briefcase d'in, 
   "right away sir,  Faisal ya fad'i gamida mik'a masa,

    "Bud'e jakar Barr yayi,  kud'i in dollars suka bayyana, ya mik'asu gaban Umar kafin yace " Idan kana mafarkin zama mai arziki dama ta sameka,  remember they say opportunity comes but once,  think about it idan baka karb'a ba you will be the great looser,  coz you'll never be free, rayuwarka na cikin had'ari coz you are now involved in the mess, and lastly remember you lost the girl alresdy, so think wisely,  bara na baka 5mins kayi tunani,  daga haka ya fice yana mayaudarin murmushi.....




Sameena 👌🏾
[1/23, 22:20] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                             43


*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum... 📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*


  " Shiru yayi gamida k'ura ma kud'in gabansa idanu,  zuciuarsa na masa sogi,  he wants to be rich, he wants to take his revenge, but ta yaya zai iya ja da  wad'an nan mutanen,  they are powerful and loaded,
 "Zan karb'a kud'insu idanyaso daga baya sai na yak'e su,  by that time na k'wato Zubaidah daga hannun wancan Jerk d'in...
  "A hankali yasa bayan hannunsa ya share hawayen da ya fito masa....


    "Driver d'insa na gama parking ya shige cikin company d'in,  daidai lokacin da Labib da Tariq suka iso...

   "Kai tsaye ya nufi yanda suke,  Barr ya soma hangowa sai mayaudarin murmushin da ya saba yake..
   "Murmushi Daddy ma ya soma kafin yace " I guess everything went perfect...
  "Barr ya mik'a wa Daddy hannu sukayi handshake kafin yace " Haba rankashidade wa ya isa yayi rejecting offer d'inka,  wama ya isa yaja da kai,  we're done with the boy....

   "Murmushi Daddy ya kuma yi daidai sanda Umar ya fito rik'e da jakar kud'in...
  "Banda mugun kallon da yake watsa masu babu abinda yake.

  "Daddy ya murmusa kafin ya k'arasa yana bubbuga kafad'un Umar yake fad'in " Kayi tunani yaro,  now you may leave,  and get lost completely. .

  "Cikin zuciyarsa yake furta I'm not done with you, I'll surely come back to you, all of you must pay, a fili kuwa baice komai ba ....  Daga haka ya nufi k'ofa,  caraf suka kusa yin karo da Labib da Tariq...

   "Wani mugun kallo yabisu dashi su duka biyu wanda yasa su shan jinin jikinsu kafin yayi ficewarsa cikin sauri kaman mai shirin kifawa k"asa...

   "Labib na jin k'aran tada mota ya lek'a ta window  da sauri ya furta "What!!!!  No way he's going with my car,  juyowa yayi da sauri alamun zai sauk'a k"asa, Daddy yayi saurin rik"o arms d'insa yana girgiza kai yake fad'in" Um'um don't be stupid,  let him go with it,  it's just a car, ...

    "Rai b'ace Labib ke fad'in " But Uncle this is my Fav Ride for crying out loud,...

   "Meye mota, kaje Dasuki Motors ka zab'i irinta,  amma wann kam ka barsa as far as babu wani important stuff d'inka a ciki,  besides we finally got rid of him....
  
   "Shiru kawai Labib yayi yana hangen window,  yanaji yana gani Umar ya fincike Motar da k'arfin gaske ya fice daga company d'in.....




    "Tana zaune tana tunaninsa, tabbas yau taga Zubaidahn Umar,  kai dole ma ya d'imaice da rashinta,...
  "Runtse idanu tayi tana rungume da pillow d'in da ya kwana akai sanda yazo, soyayyarsa na cika zuciuarta,  tunanin Shattima ya fad'o mata,  she's only using him to get close to Zubaidah,  if he knows her real intention on him,  he will hate her for good..
   "A hankali ta sauk'e ajiyan zuciya gamida furta " I'm sorry,....!!!!

   "Kaman daga sama taji ana knocking da k'arfin gaske kaman za'a cire mata k'ofa,  tsuka tayi kafin ta soma fad'in" Ina zuwa dalla,  ita kadai take zancen zuci sanda ta nufi d'aki d'auko riga  don daga ita sai pant da bra take zaune... "Yanzu haka Imam ne,  ko wann shegiyar matar me gidan hayan, ni bansan meyasa  Tariq bai biyata kud'inta ba har yanzu.....  Da haka ta isa k'ofa... "Sandarewa tayi sanda ta gansa,  idanunsa jazur, daga ganinsa kasan ba lafiya ba...

   "A hankali ta matsa gefe kafin ta sakar masa murmushi tana mai binsa da kallon mamaki tace " Bismillah....  A maimakon ya shige sai rungumeta yayi tsam cikin jikinsa, 
  "Zulaihat ta razana da lamarin nasa,  bata gama shan mamaki ba saida taji d'umin hawayensa a kafad'unta...

   "Cikin muryar kuka yake fad'in" I lost her,  na rasata har abada,  she's with him right now,  her so called husband, sun rabani da ita,  sun rabani da farin cikin raguwata....

   "Dukda kishin da ya tokari Zulaihat bai hanata rungemsa very tied cikin jikinta ba, lallashinsa take kanyi at the same time tana seducing d'insa with her ways, ...

   "Zuciyarsa sai Dad'a tunzurasa take kan aiwatar da abinda Zulaihat ke masa, duk ajiye kansa da killace kansa da yayiwa Zubaidah ta watsar tana chan tare da waninsa, da wann mummumanar tunani da shed'an ya haifar masa ya soma biye mata... a haka ya ringa biyeta har basu sanda suka raba jikkunansu da suturunsu ba,  da jan hankali da k'issa tai masu masauk"i cikin d'akinta...  "Wa iyyazu billah.... "


*********

   "Fuskarsa take kan shafawa hawaye tab idanunta,  a hankali ta yunk'ura zata mik'e taji ya rik'o hannunta, ...
   "Da sauri tasa hannu ta share hawayen kafin tace " I woke you up ko, ...

   "Girgiza kai yayi yana murmushi kafin ya rik'o hannunta yayi kissing...
   "Cikin muryar kuka Kausar ke fad'in" You're so stupid, How could you came up with that,  what if ka mutu,  Me zaka ce kace wa mahallicin mu,  you know you're so freaking crazy.. Ta k'arashe maganar tana share hawayenta...

   "Murmushi ya kuma sakar mata kafin ya d'aura hannu maras canola a Face d'inta kana yace " Yeah I'm crazy about you sweetheart,  banga amfanin rayuwa without you at my side ba, I did it out of love Sweetheart,  I couldn't believe you don't trust me. Kinfi yarda da zancen wata mak'aryaciya akaina...  Yana maganar in a furious tune,..... 
  "Da sauri tasa hannu ta rufe masa baki kafin tace " Dr yace banda yawan surutu zaka fama ciwonka,  ...

   "Murmushi ya sakar mata kafin yace " I love you....

    "Murmushin itama ta masa a hanakali ta furta "I'm sorry....

    "Turo baki yayi yace " Ban yarda ba, sai kin min kiss..

   "D'an zaro ido tayi tace " A asibitin,  gyad'a mata kai yayi without any hesitation, d'an rausayar da idanu tayi sanda ya mik'e ya jinginu da pillow,  kan tayi wani aune taji ya pulling d'inta ya soma kissing d'inta ba tareda la'akari da ciwon dakejikinsa ba,  knocking d'in da akayi ne yasa sa sassauta mata rik'on,  ta d'an ja baya tana bada izinin a shigo,

    "Labib da Tariq ne,  Labib yabi bakin Salim da kallo sanda Tariq ke gaisawa da Kausar,  murmushi yayi ya  k'arasa yana kashe masa idanu...
   "Take Salim yaji baiji Dad'in shigowarsu ba,  don kuwa duk yanda matarsa take baison ganin Labib a wajen,  don yasan waye Labib....

 **********

    "Zulaihat ranan ta kwana cikin farin ciki,  burinta ya cika,  ta sami abunda ta jima tana kwad'ayi,  shafa bayansa ta ringa yi yana bacci,  idanunta ya sauk'a kan d'an makullin mota,  da mamaki take bin keys d'in da kallo,  a iya saninta bashida mota  toh a ina ya samo mota,  kai bari dai ta mik'e ta lek'a waje,  ai kuwa nan ta hangi hancin mota,  " Bak'ar Mercedes Benz GLK 350, asalin new grand,  mamaki ya cika Zulaihat,  wann ba motan k'anan mutane bane toh a ina ya samu.???....
   "Kallonsa ta kuma yi yanda yake baccinsa hankali kwance,  sauk'e ajiyan zuciya tayi kafin ta mik'e ta nufi bathroom,  tana shigewa ya mik'e don dama idanunsa biyu,  kayansa ya saka cikin sauri...
     "Zulaihat na cikin wanka taji k'aran tada mota...  A guje ta fito daga bayin saidai kafin ta fito waje sai k'uran motarsa ta gani,  durk'usawa tayi a wajen gamida fashewa da wani irin kuka.....

  
    "Takaicin kansa ya ishesa, duk yama rasa wanne zaiyi,  Hotel ya wuce ya nemi d'aki ya kama,  haka kurum yaji zuciyarsa ta cika da k'unci.....

************

   "Satin Salim guda a asibiti aka sallamesa,  yanzu kam sun d'inke sosai da Kausar d'insa,  ita take jinyarsa cike da kulawa,  Mummy kaman ta zuba ruwa a k'asa tasha sabida farin ciki,  ranar da ya cika kwana uku da sallama ya nace saidai su tare gidansu, a gaban kowa yake nuna tsananin buk'atar sa ga matar sa,  Kausar kuwa duk a cikin so ta d'auki haka..

   "Mummy da kanta ta taya Kausar suka shirya kayan Salim,  da daddare ta kaisu har gidansu dake asokoro, gida da ya amsa sunansa gida,  tsayuwa fad'in tsarin gidan b'ata lokaci ne,  a wann dare Salim Ya gurza amaryarsa,  suka ci soyayyarsu,...  Yayinda Labib yayi kusan kwana zaune yana bak'in cikin hakan.....


      "A b'angaren Zubaidah fah,  makaranta ya zmar da ita busy,  snn her therapy classes is going well with Dr Khaleesat,  wani lokacin tare da Jalal suke therapy d'in,  wani lokaci ita kad'ai wani lokaci Jalal shi kad'ai,  rayuwa ta soma tafiya masu normal,  a halin yanzu Zubaidah ta soma sakin jiki da Jalal,  basu wani hiran soyayya saidai tana jin she can trust him even though bata yafe masa ba har rana mai kaman ta yau,  tana son watarana ta yafe masa,  amma bata jin zata iya yau class d'in da tayi da  Dr Khaleesat tambayar data mata knn shin yaushe ne take jin zata iya yafewa Jalal,  amsar da ta kasa bata knn wanda hakan yasa Dr ta maida mata shi Assignment.
    "Shi kuwa Jalal assignment d'in da Dr ta bashi shine "Shin yana son Zubaidah" shima ya kawo mata amsar tambayar ta in their next class....

   *Manage this habibaties,  kwana biyu zakuna jina ba kullum ba due to some wasu 'yan lalura, but as far as komai ya zama normal zakuna jina as in kullum kamar yanda aka saba,  love you all.....  Stay tuned guys..... 😜😻💋❤*
[1/23, 22:21] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                                44

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_



*Dedicated To All Victims Of Rape...*


  
    "Zaune yake bisa coach ya k'ure Kid'a sai ka rantse club ne,  hannunsa rik'e da kwalban whiskey, lokaci zuwa lokaci yake sauk'e ajiyan zuciya....  Mom taci gaba da buga k'ofar da iya k'arfinta...

   "Da sauri ya mik'e yayi saurin b'oye whiskey d'in kafin ya nufi k'ofa yana k'ok'arin kintsa kansa...

   "Kallo ta bisa dashi a dak'ile kafin tace " Would you turn that thing down,  ta fad'i tana nuni da kayan kallonsa,..
  "Ko kad'an baiso su had'a ido don baiso ta gane halin da yake ciki...

   "D'an murmushi yayi gamida bud'e duka hannayensa biyu kafin yace " Okay... Okay... Fine.

    "Kallo ta bisa dashi tana karantar sa , a hankali ta shigo cikin parlon nasa,  nan taji warin barasa ya cika parlorn,  toshe hancinta tayi da hannu tana binsa da kallo,  kafad'unsa ta dafa kafin tace " Are you drinking again...?

   "D'an buge hannunta yayi kafin ya zauna gijif saman sofa...

   "A tsawace ta kuma cewa "Tambayarka nake Tariq uwar me kake sha???

   "D'ago rinanun idanunsa yayi yana kllon Mom kafin yace " Would you please give me break,  for crying out loud Mom I'm dying if depression, Mom nayi nadaman laifin da muka aikata,  nayi danasanin zuwa engagement d'in Salim,  Mom babu hali na kwanta sai nayi mafarkin yarinyar nan either Tana chasing d'ina or tana wani irin yanayi, .. Ya d'anja fasali idanunsa suka kad'a sukayi ja kafin yaci gaba da fad'in" Mom I couldn't have peace of mind ever since we raped that girl, Mom I don't know but I'm not my self anymore.... Ya k'arashe maganar yana cusa duka hannayensa biyu cikin gashinsa...

   "Jiki a sanyaye Mom ta zauna gefensa, rungumosa tayi kan k'irjinta kafin ta soma fad'in" It's okay Tariq,  that girl is already married now,  she's living a new life,  ka cire komai a ranka kaci gaba da rayuwarka kaman normal...

   "D'agowa yayi yana dubanta kafin yace " But how mom,  how would I suppose to do that,  you know what kills me the most,  Jalal is completely innocent mom,  yet we put the blame on him, Mom we're so selfish... Ta yaya zamuyi ma abokinmu haka,  among all of us he's different,  he's not a coward like us... Ya k'arashe maganar yana mik'ewa tsaye...
 
   "Kallo mom ta bisa dashi kafin tace " Ina zaka je..?

   "Ba tare da Ya kalleta ba yace " I'm sorry mom but.....  But I think I'm gonna confess, I'll confess everything.....
   "Ai baika aya ba mom ta fizgosa ta zaunar tana huci ta mik'e tsaye tana binsa da mugun kallo kafin tace " Are you going insane,  meke damunka Tariq,  so kake ka k'arashe rayuwarka a gidan kasu,  kar na k'ara jin maganar nan a bakinka idan ba haka ba sai na maka baki kaga sai kayi zaman gidan kasu da dalili....

   "D'an kallonta yayi kafin yace " Mom I can't go on like this,  I ruined my life since that night,  snn mom nayi rashin aboki kaman Jalal,  I wish zamu koma kaman yanda muke da,  I wish things would turn out the way it was before.... Ya k'arashe maganar yana rik'e da pic d'insu mai su hud'u fuskokinsu cike da Annuri...

   "Sauk'e ajiyan zuciya tayi kafin ta rik'o hannunsa cikin nata tace " Son always remember that we're here for you,  me and your Dad,  Tariq bazai yuyu ka fad'i gaskiya ba,  you will endup in jell,  and we can't let you do that, coz you're our only child,  kai kad'aine d'anmu,  pls Son don't do something stupid,  you need to remain steady,  don't let that get over you okay....

    "Kallon Mom yayi idanunta tab k'walla a hankali ya rungumeta shima hawayen ne suka zuba masa....

**********

   "Usman Ya dubesa a karo na biyu gaba d'aya ba sai ance maka duniyar tunani ya tafi ba,  d'an bubbuga kafad'unsa Usman yayi kafin yace " What's up with you,  tunda kazo yau gaba d'aya cikin tunani kake..

   "D'an murmushi Jalal yayi kafin yace" I'm that obvious?...
   "Zama Usman yayi gefensa kana yace " Clearly, da gani wani abu na damunka...

     "Murmushi yayi a karo na biyu kafin ya kira yaron gefensu ya basa wasu kayan aiki yace Ya kai ma Emeka... Daga haka ya soma k'ok'arin cire kayan aikinsa...
    "Kallonsa Usman yayi kafin yace " Kai wllhi baka barin wajen nan sai ka fad'a mun meke damunka ya k'arashe maganar yana rik'o rigar Jalal..

   "D'an dariya Jalal yayi kafin yace " You so stubborn you know.. Okay fine let go of my shirt zan fad'a maka...
   "Sake masa riga Usman yayi yana murmushi kafin yace " Ai maganin miskilai irinku sai mu.. Oya go ahead and tell me,  ina saurarenka..

   "Tab'e baki Jalal yayi kafin yace " Tambayarka zanyi idan ka sani ka bani amsa.
 
   "Ina dai saurarenka, cewar Usman da Ya kafe sa da idanu...
 
   "Pls yaya ne idan mutum na son wani zai gane,  okay yaya ake so,  Oh my.. Kai I don't know how to put it,  may be you get me...?

   "Baki sake Usman ke dubansa,  dariya ya fashe dashi harda kama ciki.

    "Mugun kallo kawai Jalal ke watsa masa kafin yace " You such a jerk,  gajeren tsaki yayi gamida mik'ewa tsaye snn yace idan ka gama dariyar ni na tafi na fad'a maka dama yau da wuri zan tashi sabida inada wajen zuwa...

   "Hannunsa Usman Ya rik'o still laughing kafin yace " Yi hak'uri Mr miskilanci,  kai ni banma san wani sahu zan saka ka ba,  I can't believe you asking me that,  toh wai abokiyar zama zakayi ma matarka ne kake tambaya ko kuwa har yau baka yarda kana son matar taka bane...


  "D'an kallonsa yayi da gefen idanu kafin yayi murmushi da gefen bakinsa yace " You know me,  when it comes to women, a da kasanni womanizer ne I won't deny it, they gave me pleasure but only on bed...  Nothing more nothing less,  kai in fact ni amfaninsu a wajena ma knn until I met Zubaidah... Shiru ya d'anyi gamida k'ura ma tayan mota idanu kafin yaci gaba da fad'in" But Zubaidah.... she's different,....Snn labarin aurenmu ya banbanta dana kowa,  maybe it's not a happy marriage,  amma ina son ganinta cikin farin ciki dawamammiya.... our story is quite different,  you might not understand what I'm telling you right now, sabida baka san labarin ba,  labarinmu akwai sark'ak'iya da tarin jarabawa na rayuwa,  everything is complicated,..... So please ka fad'a min abubuwan da mutum keji ya gane he's in love...

     "Kallonsa Usman yayi cikeda Al'ajabi da tausayawa,  yanayin Jalal yasa jikinsa yin sanyi,  d'an murmushi yayi kafin yace " From the looks you got in your face kana sonta,  snn daga maganganunka kana sonta,   snn daga gani something serious is going on between you two, And destiny brought you together. Koma dai menene don't ever let her go  Jalal,  coz she's the love of your life,.....

   "Kallonsa Jalal yayi kafin yace " What if she's in love with someone else,  what if she hates me for good,  kana tunanin inada wani ghost of chance...? Ya fad'i yana kallon Usman idonunsa cike da damuwa...

  "Dafasa Usman yayi kafin yace " Don't ever give up on her, no matter the hadships and the challenges might come your way...... Kallon juna sukayi gamida sakar ma juna murmushi......
   "K'arfe shad'aya da wasu mintoci Ya nufi gida...
   "Wanka yayi ya shirya tsaf kafin ya nufi parlorn Annah,  sun jima suna fira kafin ya fice.....

  


"Zaune take k'asar bishiyar data saba jiransa, yauce ranar karb'an assignment d'in Dr Khaleesat gashi bata jin ta samo wann amsar,  runtse idanunta tayi tana tuno abubuwan da suka faru a rayuwarta,  ko babu komai Jalal yanada matsayi babba a wajenta koda bata yafe masa ba,  tunanin Umar ya fad'o mata,  tabbas baya sonta yanzu,  tabbas ya gogeta a babin rayuwarsa, shin ita kuma fah??  Ta daina sonshi ne ko kuwa....  Bata kai ga samo amsa ba sai jin daddad'an muryarsa tayi yana mata sallama... Da sauri ta d'ago tana dubansa, yana sanye cikin jampa ruwan k'asa harda hula,  yayi matuk'ar yin kyau,.... Sosai ta shafa'a da kallonsa....  Har saida ya k'araso gamida karkad'a d'an yatsan sa saman Face d'inta yayi gyaran murya kafin yace " Am I that handsome that some couldn't stop starring at me huh...? Ya k'arashe tensely.....

      "Da sauri ta zaro ido gamida furta "What,  Allah sawak'eni,  na gaji da jira ne,  you kept me waiting,  while kasan Dr tana jiranmu....

     "D'aga giransa yayi kafin yace " I'm sorry,  so tell me,  have you done your assignment...?

    "Hararansa tayi kafin tace " Ba damuwanka bane,  ta k'arashe maganar tana mik'ewa tsaye  sanda ta soma tafiya.
 
    "Rik'o hannunta yayi gamida k'ura mata ido,  itama kallonsa take,  a hankali ta sunkuyar da idanunta.

     "Murya can k'asa yace " Will you forgive me...?

      Kallonsa tayi gamida gano tsantsanr gaskiya a k'wayar idanunsa kafin ta sadda kanta k'asa....

    "Har ya cire ran bazatayi magana ba ya tsinkayo muryarta tana fad'in" JALAL....  For the first time data kira sunansa snn taci gaba da fad'in" I really want to forgive you one day,  ina son na yafe maka watarana,  but I don't know how and when, all I can say now is that I trust you,  Na yarda da Kai,  snn na yarda bazaka cutar dani ba...... Sandarewa kawai yayi yana saurarenta.
   "A hankali ta d'ago kanta tana dubansa snn tace " Ka mun alk'awari ka rabu da wad'ancan abokan naka har abada...

   "Matse hannayenta tsam yayi kafin yace " You don't have remind me of that, they are already in the past,  Na rabu dasu har abada you have my word.... .... Jin d'igan hawayen ta saman hannunsa yasa sa yin shiru....

      "Tausayinta da soyayyarta ya cika zuciyarta,  baisan sanda yayi hugging nata very tied ba,  a hankali yake furta " I'll never let you down,  I'll never leave your side,  I'll always be here for you til my very last breath....
  
    "Gaba d'aya ta mance cikin k'irjinsa take,  k'aran wucewan motoci ne ya dawo da hankulansu....  Cikin sauri ta turesa daga rik'on da ya mata..  Kasa d'ago kai su had'a idanu tayi ba tareda ta dubesa ba ta soma tafiya...

     "D'an murmushi yayi da gefen bakinsa gamida karkad'a kai kafin yabi bayanta......

****************


   Haka rayuwa taci gaba da tafiya cikin jin Dad'i a hankali suke sabawa da juna,  da taimakon Allah da taimakon Dr Khaleesat,  da kuma mutanen da suke tare dasu....


       "A b'angaren Tariq abun yayi affecting d'insa sosai,  ya koma tamkar bashi ba, wayarsa ya ciro yayi dialing lambar Jalal..


 "Da mugun mamaki Jalal ke bin wayarsa da kallo,  d'an tsaki yayi gamida yin rejecting don alk'awari yayiwa Zubaidah babu abinda zai kuma had'asa dasu , saida ya kira sau kusan biyar kafin Usman yace " Ka d'aga pls, ka sauraresa kaji me zai fad'a maka...

       "D'an fuzar da iska yayi kafin ya d'aga a dak'ile ya soma fad'in" What is it again...

      "Daga d'aya b'angaren Tariq yace " Jalal pls let's meet in person,  let's talk about it for the last time,  I promise I won't bother you again,...

       "Hold on,....  Jalal Ya dakatar dashi kafin yaci gaba da fad'in" Bana buk"atan jin komai from either of you,  stay out my life pls, and don't you dare call me again.......

    "Da sauri Tariq yace " I beg of you don't hang up the phone,  for the sake of old times.... Jalal dan Allah kayi hak'uri mu had'u later,  it might be our last goodbye, I don't I can continue living here,  I'm leaving to abroad,  dan Allah Friend let's meet for the last time......


      "Sauk'e ajiyan Zuciya Jalal yayi kafin yace " Okay I'll see what I can do,  idan na tashi a aiki zan kiraka na fad'a maka location d'ina sai mu had'u.....  Daga haka yayi hanging....



     "Tana nan zaune yanda ta saba jiransa shiru shiru bai iso ba,  d'an duba agogon hannunta tayi taga Time ya tafi sosai,  d'an sauk'e ajiyan zuciya tayi kafin tace " K'ila bai tashi a aiki bane.. Maybe he has alot to finish.  Mik'ewa tayi ta nufi bakin titi ta tare a daidaita ta shiga,  gida ta nufa kasancewar yau babu zuwa gidan Dr Khaleesat....


    "Suna tafe cikin adaidaita jefi jefi tana tunaninsa,  batasan daga yanda ta tsinto murmushi saman fuskarta ba,  haka kurum taji babu Dad'I yau da baizo d'aukanta ba,  tunda ta soma zuwa sch bai tab'a fashin kawota ko zuwa d'aukanta ba......  Cak ta daina murmushi gabanta ya shiga lugude sanda ta hangesa da d'aya daga cikin fuskokin datafi tsana,  dukansu suna murmushi suna hugging juna....



Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:21] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                             45


*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*



    "Tariq yayi hugging Jalal kana yace " I'm leaving soon Bro,  thanks for everything, na gode da duk karamcin da ka mana,  I know I owed you alot...

   "Mik'a masa hannu Jalal yayi sukayi handshake kafin yace " Allah Ya kiyaye hanya yasa tafiyarka shine alkhairi... 

   "Gyad'a kansa yayi kafin yace " Ameen, goodbye Bro.

  "Kallonsa Jalal ma yayi kafin yace goodbye,  daga haka Jalal ya soma tafiya don dama sauri yake yaje ya fetching Zubaidah daga makaranta.

   "K'arasowa gabansa Tariq yayi da motar sa yanda yake tsaye bakin kwalta kafin yace " Let me give you a ride...

   "D'an girgiza kai kawai Jalal yayi kafin yace " A'a ka barshi kawai,  na gode and don't insist pls..

  "Gyad'a kansa Tariq yayi kafin yace " Okay goodbye again...  D'aga ma juna hannu sukayi kafin Tariq yaja motarsa ya bar wajen...


   "Agogon hannunsa ya kuma dubawa gamida yin gajeren tsaki,  yasan ta gaji da jiransa,  hannu yasa da sauri ya tari mai mashin d'in da ya iso gabansa, cikin sauri ya d'ale yana mar bayani.... 





   "Malam ajiye ni a nan,  ta fad'i cikin rawar murya,  Mai adaidaita ya juyo ya dubeta kana yace " Hajiya ai ba nan kikayi zan kawo ki ba ko kin fasa ne...

  "Gyad'a kanta tayi tace " Na fasa ajiyeni a nan.

  "Mai adaidaita yayi yanda tace...

   "K'asar wata bishiya ta samu ta zauna,  abunda ta gani ya kasa b'ace mata a idanunta,  who would she trust,  so all these while Jalal is been lying to her. Meyasa ya bari saida ta aminta dashi,  a tunaninta bazai cutar da ita ba ashe duk k'arya yake mata,  all men are the same,.... A hankali ta goge hawayen da suka zubo mata,  a fili take furta " I was such a daft da har na yarda dashi,  idan da na aminta baiyi raping d'ina ba,  yanzu kam na Dad'a yarda yayi,  harda shi, maybe shine yin k'arshe,  dukansu munafukai ne mak'iyana,  I shouldn't have believed him.  He's also lying.... I won't go back there,  bazan koma ba, bazan ci gaba da zama dashi ba,..... Kuka mai k'arfi ya kufce mata saida tayi mai isanta kafin ta d'ago kanta kaman wacce aka zabura,  tunani ta soma yi,  ina zanje wa na sani a garin nan....

   "Take tunanin Zulaihat ya fad'o mata,  ita kad'ai ta sani a garin nan,  da sauri tasa hannu cikin jakar makarantar ta don dama ciki ta ajiye lambar da Zulaihat ta bata...

   "Gefe da ita business center ne nan ta k'arasa ta biya kud'i ta soma kira....


   "Zulaihat was very surprised jin Zubaidah ce,  jin tana kuka yasa hankalin Zulaihat tashi, cikin sauri ta tambayeta location d'inta.  Nan ta mik'a ma masu wayar suka mata kwatance,  Zulaihat ta ringa kwantar mata da hankali snn tace gata nan zuwa right away....



  "Lambar Imam Zulaihat ta kira Allah yasa yana kusa nan suka wuce d'auko Zubaidah.....




   "Neman duniya yayi bai sameta ba,  haka kurum yaji gabansa na mugun fad'uwa,  what if she get lost tunda ba sanin gari tayi ba,  kaman zararre ya soma girgiza kai shi kad'ai yana furta No no ta isa gida safely insha Allah,  a sittin ya kuma tare mashin ya nufi gida.....




   "Tunda suka shigo layin Zubaidah ta kasa sakewa,  bataga alamun mutunci a wajen ba,  a iya saninta Zulaihat tace mata she's leaving with her Aunt,  bata ga alaman Auntyn Zulaihat ba har suka shige ciki....  Zama tayi dirshan saman sofa a parlor,  sai k'are ma yanayin gidan kallo take cike da tsoro.


    "Fitowa Zulaihat tayi wajen Imam while Zubaidah na zaune a parlor..
  
  "Kannare idanu Imam yayi kafin yace " Wacece  wancan yarinyar gaskiya tayi min,  sabuwar shiga hark'a ne, kafin ki had'ata da wani Alh gaskiya nidai tayi min,  ke da aure ma ni zan nemeta...  " Ya k'arashe maganar yana wani kashe ido...

 "Baki a tab'e kurum Zulaihat ke dubansa kafin tace "Kai dalla jacan,  kai har wani namiji ne,  ni dalla ba wann ba,  kaga yarinyar nan babu ruwanka da ita , zan fad'a mata kai k'anina ne sabida yanayin shigarka gidan nan babu control...

    "Dariya Imam yayi yana kad'a key din tasi d'insa kafin yace " Ah haba k'ani saidai yaya kema kinsan na fiki...

   "Dalla ni yimin shiru ka gane taimaka min zakayi, kaga bani da cash account d'ina ma yayi k'waras bansan meke damun Tariq ba kwana biyu,  nasan dai cikin satin nan zai turo min monthly allowance d'ina,  so pls idan da kud'i a jikinka ka sayo min dangin su macaroni pls kaji....


    "Zaiyi magana ta tura kansa cikin mota tana fad'in" tafi tafi banson complain abeg.... 
  "Dariya kurum yayi ya shige mota kafin yace " Zan had'a cikin balance d'inki..
  "Eh dai jeka ta fad'i tana rufe k"ofar parlorn....



  "Kallonta Zubaidah tayi sanda ta shigo parlorn, Zulaihat ta sakar mata murmushi kafin tace "Feel at home ki Saki jikinki. Ta mik'e ta kawo mata drink..

   "Zubaidah dai bata sake ba,  ta d'an kurb'i ruwan kafin tace " Kince min da Aunty d'inki kike zama,  where is she..?

  "Gaban Zulaihat ya bada dammm,  tama mance tayi wann k'aryar..  Murmushi yak'e tayi kafin tace " Oh aww,  ai Aunty ba Me  yawan zama bane,  ta tafi wani seminar a Jos,  yanzu haka ma nida wancan k'anin nawa da ya kawo mu ta bari a gidan......  "Zubaidah ta zaro ido waje kana tace "Oh you mean shima a nan gidan yake kwana..?

   "Da sauri Zulaihat ta girgiza kai kafin tace " No a campus yake zama,  yakan d'an zo mana weekend dai amma yanzu tunda kinzo I'll ask him to leave..

   "Jim tayi gamida sakin murmushi a hankali,  Zulaihat dai sai karantar ta take,  tabbas akwai yaranta tsundum a lamarin Zubaidah amma me zaisa ka baro kowa naka ka taho wajen k"awar da rana guda tak kuka tab'a had'uwa...  Mik'ewa tayi ta shige d'aki tana fad'in kisha lemo fah yanzu Imam zai kawo aike na d'aura mana abinci..

   "Murmushi kawai Zubaidah tayi gamida gyad'a kai....


   "Tunda ta shige d'aki take neman layin Umar bai d'aga ba,  k'arshs ta hak'ura tasan ba lallai bane ya d'aga don tunda yasa k'afa ya fice daga gidan bai kuma kiranta ba... Sauk'e ajiyan zuciya tayi ta tsunduma kogin tunanin ko ta masa text ne....

*************

   "Annah ya kamata ace ta dawo by now,  I can't loose her,  what if wani abu ya sameta,  I'll never forgive my self sabida laifina ne banje na d'auketa ba,  ya k'arashe maganar yana hargitsa gashin kansa........  Cak ya tsaya sakamakon jiyo sautin kukan Hamma Habibu da sukayi... Cikin harshen fillanci yake kan sunbato yana ambaton Zubaidah k'anwarsa....

   "Kallo kurum suka bi Hadiza dashi don kuwa ita ta taso sa gaba tana fad'in k'anwarsa ta b'ace,  basu ma san wayagaya mata ba cewa Zubaidah bata dawo ba,  shakka babu ta masu lab'en data Saba ne...

     "A hankali Jalal ya furta " Oh my Allah give me some strength,  I need to remain steady,  they all rely on me... Annah ce ta k'arasa tana bama Hamma Habibu baki amma kaman cewa take ya k'ara,  k'arshe zama masu yayi dirshan a k'asa yana kuka yana jejjefa k'afafu,  Kamal ya k'arasi ya rungume baban nasa suna ci gaba da kuka...

    "Hadiza kuwa banda tab'e tab'en baki bata furta komai...

   "Annah ta juyo ta dubi Jalal wanda damuwa ce k'arara a Face d'insa,  tausayin d'an nata ya cika zuciyarta,  tasan he's in pain sabida tasan irin son da yake ma Zubaidah,  zatayi magana yayi saurin k'arasowa ya rik'e hannayenta cikin rawar murya yace " I'll find her Annah,  don't worry she'll be safe, just take care of them okay...  Ya k'arashe maganar yana nuni dasu Hamma Habibu wanda shida Kamal bakace wanene k'aramin yaro ba sai kaga girman jiki...

   "Har ya isa k'ofa Annah ta kira sunansa,  tsayawa yayi yana dubanta idanunsa fal damuwa,  k'arasowa Annah tayi gamida shafa fuskar sa tace " Ka kira Dr Khaleesat,  gyad'a mata kai yayi tamkar k'aramin yaro da k'yar ya iya furta " Bata je ba Annah,  I've bad feelings something bad might happen to her....

  "Girgiza kai Annah tayi kafin tace " Babu komai insha Allah,  I know she's safe,  where ever she is....

   "Gyad'a kansa yayi kafin ya fice cikin sauri,  lmbar Usman ya shiga nema ya sanar dashi abinda ke faruwa a gurguje, sosai hankalin Usman ma ya tashi ....

   







 "Neman duniyar nan sukayi shiru babu ita babu dalilinta, ga dare yaja sosai wajejen k'arfe 10:pm.  Usman yace " Amma kanaga batasan kowa a garin nan ba,  share k'wallam da ya zubo masa yayi abunka da farin mutum fatar tayi jazur haka jijiyoyin gishinsa sunyi rud'u rud'u green shar dasu
   "Da kakkausan murya yake fad'in" I'm nothing but a coward na kasa tsareta daga sharrinsu,  I couldn't protect her"
    "Jalal pls ka daina d'aura ma kanka laifi,  haka Allah Ya k'addara dole hakan saita faru, nidai inaga maybe akwai wanda ta sani k'ila tana chan,  she might probably be mad at you muddin ta ganka da one of your friends,  tunda kace a bakin hanya ka had'u da Tariq nidai inaga ta ganku ne.
  "Usman batasan kowa a garin nan ba,  ina zataje,  what if the Dasukis harm her,  what if they are responsible , ..... Kaman wanda aka zabura haka ya mik'e yana fad'in" I must go to them,  nasan sune,  su kad'aine zasuyi haka,  Those bastard I'm gonna kill them all....  Cikin sauri Usman ya rik'o hannunsa yana fad'in" Calm down,  calm down Jalal,  don't be stupid abi abun a sannu,  what if bata wajensu,  what would you expect huh,  what if they file a complaint against you,  ka masu sharrin kidnap,  if police got involved your little secret is exposed,  think about it... 
    "Da k'arfin gaske ya fizge hannunsa yana huci yake fad'in" Hoe would I suppose to calm down,  matata Tana cikin halin da van sani ba and yet kana ce min I should calm down.... They must all pay I don't care....  I don't care anymore Usman,  let anyone gets what he deserves, I swear to you if they did any thing to her,  I swear I'll kill them with my very own hands....... Wayan Unman ne ya soma ringing "Shattima ne ya bayyan a jikin screen d'in...

     "D'an sauk'e ajiyan zuciya yayi kafin yayi picking, " Mai sarauta ya akayi,  cewan Usman bayan yayi sallama.


      "Daga d'aya b'angaren Shattima yace " I just arrived at the city ina kake,  don idan ban baka kud"in nan ba bazaka barni nayi bacci mai kyauw ba.

     "D'an fuzar da iska yayi ya saci kallon Jalal,  kafin yaja gefe ya shiga labarta wa Shattima abinda ya faru,  sosai hankalkn Shattima ya tashi,  cikin sauri yace Usman ya masa texting location he's on his way there...



   "Zama sukayi su duka biyu kan madaidaicin darduman dake a parlorn,  Zubaidah dai ba wani cin abincin take ba,  gaba d'aya a tsarge take jinta,  tun sanda taji mak'otan Zulaihat sun shigo suna maye.... Zulaihag sai k'ok'ari take ta kawar mata da tunanin lokaci guda tana shan cikin Zubaidah tana son jin dalilin da ya baro da ita gida.
    "Zubaidah bata ja hiran ba,  saidai tace wa Zulaihat ta gaji ne kawai da zama sasu she needs some space and bata san wajen wa zata je ba,  so that they shouldn't find her...
  "Gyad'a Kai Zulaihat tayi gamida d'aurs fake smile saman face d'inta....
   "Suna gama ci Zulaihat ta raka ta har d'aki ta bata kaya masu sauk'i sabi fil dasu tace ta shiga ga bayi tayi wanka,  murmushi Zubaidah ta sakar mata gamida mata godiya....
  "Wyarta ta d'auka sanda Zubajdah ta shige toilet kana ta turawa Umar text

_We need to talk, ASAP,  call me when you have time_
Sauk'e ajiyan zuciya tayi ganin sak'on ya tafi...




  "Jalal kayi hak'uri mu k'arasa gidan da nake sauka a nan Asorock  mu kwana is already late,  idan yaso first thing tmrrw morning sai muyi reporting police station da kafafen yad'a labarai....
    "Ba don yaso ba saidon tilasta masa da sukayi,   baccin da baiyi ba,  yanda yaga rana haka yaga dare. K'arshe yanke shawarin fitowa parlour yayi don yin nafilfili..

       "Fitowar Shattima knn daga balcony ya gama amsa wayan Mai Martaba ya hangi Jalal ya kwab'e riga daga shi sai singlet alamun zai shiga bayi alwala......


    "Sandarewa Shattima yayi yana kallon shatin tambarin dake a gefen kafad'ar Jalal ta hannun dama,  wanda bashida maraba da tambarin masarautar su....



Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:21] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                               46


*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*





   "Hannun Shattima yaji bisa kafad'unsa,  da sauri ya juya yana dubansa, dubansa Shattima ma yayi har lokacin hannunsa naga kafad'ar Jalal,.

   "Murya cike da Al'ajabi Shattima yace " Ina ka sami wann mark d'in..

   "D'an murmushi Jalal yayi kafin yace " I was born with it...

  "Shiru Shattima yayi sai k'ura masa idanu da yayi,  don kuwa ya tuna akwai lokacin da coincidence yaga irin wann tabo exactly a kafad'ar mai Marta wani rana yana sanye da 'yar shara suna hira da Shattima irin na d'a da mahaifi dukda bashi ya haifesa ba,  ya tuna Mai Martaba ya basa labarin wann tabo da ya gani a gefen kafad'arsa cewa,  babu wani sarki a masarautarsu Face yanada wann shaida, ..... Sosai ya k'ura ido yana k'are wa shaidar kallo batada maraba dana Mai Martaba....  Muryar Jalal ne ya dawo dashi daga duniyar tunanin da ya tafi...
 
   "D'an dafa kafad'ar Shattima Jalal yayi kafin yace " Don't get wrong idea nasan zakayi tunanin k'ila tatu ne nayi ko,  to ba haka bane,  I'm a good Muslim nasan babu kyau yin tattoo, Believe me I was born with it,  yanda ka gansan nan..

  "D'an murmushi k'arfin hali Shattima yayi kafin yace " Kayi alwalan ka I'll make some coffee,  it will help you...

   "Gyad'a kansa kawai Jalal yayi kafin ya shige bathroom...

   "Gaba d'aya jikin Shattima yayi sanyi,  kai wani babban Al'amari na shirin faruwa dashi,...

*************

   "Washe gari tun ida sallahan asuba suka nufo suleja,  to their greatest surprise Dr Khaleesat is there too,   tana ganin Jalal ta sakar masa murmushi tace " You can go through this, don't worry kaji,  we would find her...

  "Murmushin k'arfin hali kurum ya sakar mata ba tare da yace komai  ba..

   "Annah ta rungumesa tana maida hawayen da ya kufce mata,  Murya na rawa Jalal ke fad'in" Annah I couldn't find her,  what if something bad happens to her,  I'll never forgive my self......  Shigowan Hamma Habibu da Hadiza ne ya katse  su don dama sunji tsayuwar mota...

   "Kai tsaye hannun Jalal ya k'arasa ya rik'e yana fad'in" Jalal ka samo mun k'anwata,   ka samota koh,  nasan kai kad'aine zaka iya kular min da ita,  ka fad'a min ka samota tana cikin k'oshin lafiya,  idan wani abu ya sameta Inna da Baffah zasu gani daga makwancin su koh,  zasu ce ban kula da ita ba ko,........
  
  "Tausayi ya cika illahirin zukatan mutanen dake wajen.

   "Hannayensa Jalal ya rik'e gamida zaunar dashi saman dakalin dake a veranda d'in kafin yace " Ka kwantar da hankalinka Hamma,  I promise I'll find Zubaidah where ever she's,  nayi alk'awarin zan samota duk yanda take da izinin Allah koda hakan zai zama sanadin rasa rayuwata, ka kwantar da hankalinka Zubaidah bazata so ganin hankalinka a tashe ba,  kayi mata addu'a kaji...

   "Haka Hamma ya ringa gyad'a kansa yana goge hawayensa da riga tamkar k'aramin yaro.....

   "Kaman daga sama sukaji wayar Annah na ringing,  Hadiza tayi saurin shigewa d'aukar wayan don Annah kam bataci ta kula waya ba.

   "Jin muryar Zubaidah cikin wayar yasata fitowa da sauri tana fad'in itace Zubaidah ce.....
   "Daga d'aya b'angaren kuwa Zubaidah cewa take " Ki bani Annah da Hamma na,.....  Daidai sanda Annah ta fizgi wayar,  Jalal kam mutuwar tsaye yayi yana binsu da Kallo.

   "Daughter where have you been,  we were all worried about you,  Annah tace cike da nuna damuwa...

  "D'an jim Zubaidah tayi duk sai taji babu Dad'i, Annah bazataji dad'in abunda tayi ba,  despite all her efforts on her.  A hankali take fad'in" Annah ina nan lafiya shiyasa ma na kira na sanar daku don kar ku damu,  I just want some space ne,  I'll come back to you soon,  ina Hamma na....  Ta k'arashe a hankali.

  "Annah bata iya furta komai bar,  sai manna wayar a kunnen Hamma Habibu da tayi....

   "Shida baya tareda su ya tafi duniyar kuka jin muryar Zubaidah a waya yasa sa mik'ewa zunbur yana murmushi, 
  "Zubaidah,  Zubaidah na,  Zubaidahn Baffa da Inna,  ina kikaje....  "Jalal ya damu dake.....  Gaba d'aya suka dubesa jin statement d'insa...
  "Hamma yaci gaba da fad'in" Nima na damu dake,  Don Allah ki dawo garemu kinji k'anwata, duka muna sonki,  muna sonki....

   "Share hawayen da ya zubo mata tayi kafin tace " Nima ina sonku Hamma,  zan dawo kwanan nan kaji,  kar ka d'aga hankalinka idan ba haka ba kuma bazan dawo ba,  ka kwantar da hankalinka kaji.....


   "Muryar Jalal taji cikin wayar yana fad'in"  pls come back,  if you want I'll leave the house,  but pls don't put your self in danger, Hamma is worried so much about you,  ki dawo don Allah ko kuma ki fad'a mun yanda kike,  I'll get you right a way....

  "Cike da masifa take fad'in" I won't listen to your lies again,  I hate you even more,  snn kar kayi tunanin zan dawo nan kusa,  and lastly don't you dare involved police idan ba haka ba,  wllhi kaji na rantse I'll leave you all for good,  snn bazan dawo ba...

  "Yanajin sanda tayi tsuka ta kashe wayar.....

  "A hankali yana mai lumshe ido ya k'arashe da " I love you.... Be safe dear.......

    "Gaba d'aya suka k'ura masa idanu cike da tausayawa.
 "Dr Khaeelsat tace yi mun dialing number d'in,  babu musu ya sake dialing amma sai jinta yayi a kashe,  a sanyaye yace " is switch off..!!
   "Gyada kanta tayi kafin tace let's talk private, babu musu yabi bayanta...
 
*************
  "Mik'a ma Zulaihat wayar tayi tana mai zama bisa sofa ta shiga share hawaye, Zulaihat ta dafa ta kafin tace " Meyasa bazaki koma ba,  suna sonki,  you're so lucky da kika sami family haka masu sonki da yawa ta k'arashe zancen sanda take cire sim d'in da zubaidah tayi amfani dashi don dama extra sim d'inta ne wanda take solo ma Alhazawanta dashi, ..

      "Girgiza kai Zubaidah tayi kana tace " No bazan koma ba,  snn ko zan koma sabida mutane biyu ne,  Annah da Hamma na,  su kad'aine basa min k'arya...

  "Zulaihat ta sauk'e ajiyan zuciya kafin ta mik'e tana gyara mayafinta tace " Okay ni zan fita breakfast na kitchen,  ki shiga kici duk abinda kike so, zaki iya kulle gidan gaba d'aya.
  "Gyad'a Kai Zubaidah tayi kafin ta dubi Zulaihat tace " Na gode,  thank you for your kindness.
  "Gajeren murmushi kawai Zulaihat tayi kafin ta suri jakarta tace " See you soon.
 
     "Window Zubaidah ta k'araso tana lek'en Zulaihat da Imam,  Imam harda mata murmushi da waving,  bata kulasa ba sai sauk'e labulen da tayi ta k'arasa ta rufe k'ofar parlorn....

*************
    "Annah dasu Jalal harma da Dr Khaleesat suka ja gefe  suna tattauna lamarin bayan Dr sun gama ganawarsu da Jalal, ,
   "Shattima yace " Nifa ina ganin we should report that to the polic,  the earlier the better...

   "Girgiza kai Jalal yayi kafin yace " Tace muddin mukayi reporting bazata dawo ba,.

  "Are you sure babu wanda ta sani ko a cikin Abuja ne,  Dr Khaleesat ta tambaya.

   "Da sauri Annah ta kuma d'ago kai ta dubi Shattima, ta  tuna kwanaki ya kawo masu budurwarsa,  cikin sauri ta k'arasa gabansa tace " Kai kuwa ina yarinyar da kazo da ita kwanaki gidan nan,  matar da zaka aura don ban mace ba haka ta fad'i mana,  ita kad'ai Zubaidah ta sani me yuwa gidansu taje...

  "Jalal yayi saurin mik'ewa yana recalling tabbas anyi haka...
   
   "D'an jim Shattima yayi harga Allah Ya mance tare suka zo da Zulaihat amma ta ya ta zama matar da zai Aura, rabonsu da waya ma yana ganin tun wancan lokacin ne, k'ila ita tace masu haka knn...
  "Da sauri ya furta "Zulaihat,  Annah ta gyada kai tace k'warai...


   "Kan kace Me  Jalal ya fuzgo hannun Shattima yana fad'in" Muje pls take me to their house....

  "Wait Jalal wllhi bansan gidansu Zulaihat ba,  ban tab'a zuwa ba...


    "Wani mugun kallo Jalal ya watsa masa kafin yace " Matar da zaka aura d'in ne baka san gidansu ba,

   "Matar da zan Aura..?  Shattima ya maimaita.

      "Annah ta gyad'a kai tace "K'warai haka tace mana,.

   "D'an girgiza kai kawai Shattima yayi kafin yace " Wllhi ko gidansu ni bansani ba........  Baikai aya ba Jalal ya shak'ure masa wuya yana fad'in" K'arya kake,  then why did you bring her here,  meyasa ka kawota nan....  Usman yayi tsalle yana k'ok'arin ceton Shattima...... Annah ta tafi da sauri tana Janye Jalal....


    "Da k'yar aka k'waci Shattima daga mak'uran da Jalal ya masa....

 "Janye hannun Jalal Annah tayi suka wuce d'aki rai b'ace...

  "Ni bansan yanda zaka kai wann zuciyar taka ba,  haba haba Jalal,  idan kayi haka me kake tunanin Habibu zaiyi,  You always let your temper get the best of you, kamata yayi ka nustu musan abin yi,  idan neman Zulaihat d'in za'ayi sai ayi,  and wnn yaro da ka masa haka bai deserving haka ba,  he's here to help he cares about you, me kake tunanin Usman zaiji .

    "D'an shiru yayi amma har lokacin huci yake a hankali ya furta " I'm sorry Annah....


   "D'an dafa kafad'arsa tayi ta sassauta murya kafin tace " Son I know this is difficult for you,  it hurts me ganinka a wann condition d'in,  but we all need to remain steady,  akwai mutanen da suka fimu rauni cikinmu,  think about her brother abin yayi affecting d'insa sosai,  pls kayi composing kanka kaji Son,  and Dr Khaleesat bazataji dad'i ba regarding what you did earlier,  tashi muje and apologize to them...

   "Gyad'a kansa yayi kafin ya mik'e jiki a sanyaye..



  "Gaba d'aya basuji zafin abinda yayi ba,  saima tausaya masa da suka yi,  Shattima ya dafa sa kafin yace " I know exactly how you feeling,  and I'm willing to help Jalal,  na kira wayan Zulaihat munyi magana tace " Zubaidah bata wajenta,  but she sounds very wired like something is wrong with her,  batayi rawan kan nata data saba ba,  she was quite strange , the best abu shine mu fita mu nemi resident d'inta...


      "Gaba d'aya sunji Dad'in shawarin Shattima,  Jalal ya d'an dafa kafad'arsa yace " I'm sorry again Shattima,  murmushi kawai yayi yace " That's what bothers are for,  let's get going the earlier the better...

    "Gaba d'aya suka gyad'a kai,  Dr Khaleesat ma Office tace zata wuce ganin k'arfe takwas tayi snn tace " suyi keeping nata update duk abinda ake ciki,  a tare suka fice,  Dr Khaleesat ta nufi motar ta yayinda Su Jalal suka wuce Ride d'in Shattima...

***********
 *Sheraton Hotel,  Abuja*
"Kallon d'akin da yake kwance a ciki yayi,  ya dubi suturun dake jikinsa masu d'an karen tsada,  his life is different now, komai ya canza,  he's rich handsome and educated, abu guda da ya rasa shine ZUBAIDAH She suppose to be here with him enjoying the luxury, this is the life he's been dreaming of, finally ya samu,  what next now????  Ya tambayi kansa.  Zuciyarsa ne ta basa amsa kai tsaye
  "GET HER BACK,  Get your girl back,  she's yours,  she's meant to be with you no one else, get back what's rightfully yours...

    "Mik'ewa yayi ya soma shiryawa, cikin drawer ya hangi tsohuwar phone d'insa wanda tunda yayi kud'i ya jefarta ya sai iPhone8, sauk'e ajiyan zuciya yayi sanda ya tuna irin baran baran d'in da sukayi da iyayensa sanda ya koma masu yayi kud'i dare d'aya,  gaba d'aya basu yarda da arzikin nasa ba,  d'an tab'e baki yayi kafin ya d'au wayan halama sun kirasa,  duba wayar ya soma yi yaga sakk'wanni da kira masu yawa, yyawanci na abokinsa Balele ne da Zulaihat, na Zulaihat ya soma dubawa,  ya shiga kiran wayarta yaji a kashe,  ita kuwa masu amsan kud'in gidan haya ne da Shattima suka sakata kashe wayarta, ya kira ya kira a kashe,  karanta sak'on data tura masa yayi, 
      "D'an jimm yayi kafin ya furta " I shouldn't have abandoned you anyway,  you help me sanda na zo,  fita yayi ya wuce  Mall ya soma mata shopping, kaya sosai ya saya mata kafin ya nufi gidanta......




Sameena ce
[1/23, 22:21] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                              47

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_



*Dedicated To All Victims Of Rape...*



*"Salam. Ina rok'on Allah yayi maki albarka fiye da k'ok'arinki,  Ya shirya maki iyalanki fiye da tarbiyarki,  Yayi maki Rahama fiye da tubanki,  Yaji k'anki fiye da tunaninki,  Ya k'ara azurtaki fiye da nemanki,  Ya karb'i ibadunki fiye da k'wazonki....  Allah yayi ma Mahaifanki gafara ba tareda binciken ayyukansu ba, Allah Ya rufa maki asiri duniya da lahira.... Ina maki barka da Jumma'ah*

*"Sak'onki a gareni  💅🏼Maman Sadiq💅🏼......👆🏽*

*Na gode na gode k'warai da gaske da kyawawan addu'o'inki da nuna k'aunarki a gareni, Ubangiji ya saka maki da khairan,  Sameena na k'aunarki, Alkhairin Allah Ya kai maki duk yanda kike... 🤝🤝the whole chapter is yours dear😍😘*


   "Imam don Allah ka bar duk abinda kake kazo muje,  wann mutumin ba mutunci ne dashi ba,  wai Ya kira Tariq ma bai d'aga wayarsa,  he's talking nonsense, wai saidai ya kwana dani tukunna zai d'aga min k'afa,  kasanni bakina baya shiru nan na gaggaya masa magana son raina,  probably nasan yana hanyan zuwa gidan ya min watsi da kaya ga Zubaidah tana can pls kayi sauri....  Ta k'arashe maganar tana yarfe hannu...

  "Daga d'aya b'angaren Imam yace " Gani nan zuwa,  just send me your location, cikin sauri ta amsa gamida tura masa....

*******

  "Tana zaune gaban kayan kallo tana kan duba plates d'in da suke jere a cikin drawer d'in dake mak'ale jikin TV stand,  yawanci Americans films ne saiko Nigerian films,  bangon d'aya kaset d'in ne yayi mugun d'aga mata hankali don kuwa abin babu kyaun gani basai ance maka bluefilm bane,  k'irjinta ya shiga bugawa da sauri da sauri,  tayi saurin jifa da kaset d'in ta shiga k'ank'ame jikinta ita kad'ai tana matsawa jikin garu....  Hakan yayi daidai da soma knocking,  Zubaidah ta kuma firgita,  toshe bakinta tayi da iyaka k'arfinta da duka hannayenta biyu,  tsoro da firgici ya mamaye ta baki d'aya....  Da alama mai knocking gajjiya yayi kokuwa ya tafi.

  "Cikin sand'a ta isa jikin labulen window tana lek'awa,  kasa gasgata abinda idanunta suka gane mata tayi,  is that really him, ba don ta masa faran sani ba tabbas zata ce bashibane k'ila an canza sa,  this one's different from the Umar she knows,  sanye yake cikin kaya na alfarma hannunsa rik'e da d'an makullin mota,  fuskarsa sunkuye yana rubutu jikin takarda,  gama rubutun da zaiyi ya k'arasa jikin wata da ba sai ance maka taji kud'i ba,  Zubaidah tana gani ya shiga lodo kaya yana ajiyesu bakin k'ofar had'i da d'aura note d'in saman shopping bags d'in....

   "Sulalewa tayi a wajen k'irjinta na barazanar tarwatsewa,  ta nemi kukan da take ta rasa,  tana jin tafiyar motar tayi saurin fitowa ta d"auki note d'in....  Abinda ta gani a ciki yafi komai girgizata.

_Hello,  I've been calling your  number wasn't going,  I wanted to  thank you for your kindness and for accommodating me, snn to be honest with you,  akanki na soma sanin  Wata mace so bazan mance ki a rayuwata ba,  when ever you've time pls phone up me.. ... UMAR_

   "Durk'ushewa tayi a wajen kaman zararriya ta soma fad'in" No bashi bane,  it wasn't him,  Umar bazai tab'a yin haka ba,.......  Kuka mai k'arfi ya kufce mata,  tana tsaka da kukan taji an daki windown dake gefenta da sauri ta mik'e tsaye tana tattare hijabinta.
 
  "Wani murtuk'ek'en mutum bak'ik'irin ta gani idanunsa tamkar garwashi sai muzurai yake,  tsawa ya daka mata tuni ta yarda takardan dake hannunta,  ta shiga ja da baya.

   "Da kakkausar murya mutumin ya soma fad"in" Ina zaki gudu munafukai kawai,  tsayawa zakiyi ki fad'a mun yanda shegiyar k'awar taki ta tafi,  don nasan plan kuka had'a tunda na gaya mata zanzo amsar kud'ina tunda daduro ba k'anwar uwarta bane balle na ubanta, shegu kawai kunsan bazaku iya biyan kud'in haya ba kuka baro gidajen iyayenku kuka fito daduro,  toh wllhi akanki zan amshe kud'ina,  munafuka harda wani hijabin munafunci saikace sallahn kuke, .......

   "Jiki na kararwa Zubaidah ke ja da baya tana fad'in "Wllhi bansan kom......  Bata kai aya ba ya kai mata sura tayi wani tsalle had'i da ihu,  daidai nan Zulaihat da Imam suka shigo,....

   "Zulaihat baki na rawa take fad'in" Duguja wani irin bura'uba ne wann yaya zaka tsorata min k'awa....  Wawan naushi ya kai mata a baki saida jini ya fettsesu...  Zubaidah ta kuma sakin wani k'ara cike da firgici,  Imam kuwa kukan kura yayi ya cakume Duguja da duka,  Ai Zubaidah na ganin haka,  ta zura hannu bakin k'ofa ta suri jakarta ta soma gudu tamkar zararriya...  Zulaihat dake kwance shame shame a k'asa da k'yar take iya k'walla kira wa Zubaidah amma inaa,  ko juyowa batayi ba,  tamkar mahaukaciya haka take gudu bisa layin,  mutane 'yan layin kuwa wanda akasarinsu karuwai ne suka fito bama ido abinci sai shewa ake memakon ayi yunk'urin rabasu,  babu tarbiya sam...  Allah ka tsare Al'umman musulmi ameen...



    "Da k'yar da mak'ek'yata suka sami wanda yasan gidan Zulaihat,  har layin aka kaisu,  tundaga nesa gabansu ke fad'uwa ganin yanayin mutanen dake wajen da yanayin layin mmusamman sabida fad'an da akayi.. tabbas wann waje babu danshin tarbiya.

   "Murya na rawa Jalal ke fad'in" I can't believe my wife is here,  Shattima this is a Barracks bana tunanin matar aure me mutunci could leave in this place, Shattima ya paka motar kafin yace " Nima dai abinda zance knn,  but she says she's leaving with her Aunt muje dai muga... Usman cewa yayi I'm speechless, that bitch lied to you...

   "Tunda suka soma tafiya matayen wajen ke admiring d'insu,  duk macen da suka wuce saita Bank'are masu k'irji ko kuma tayi wani salon wasu harda fad'in" Wow cuties.... gaba d'aya suka sha jinin jikinsu.. 
   
"Suna isa suka tarar k"ofa a Bud'e har lokacin bala'i ake Duguja yana fad'in sai ya amshi kud'in hayarsa a jikin Zulaihat Imam ya kasa ya tsare yace bai isa ba..... 

     "Da mugun mamaki suke kallon wann sure d'in,  Ganinsu yasa Duguja guduwa don ya d'auka kiransu sukayi su kamasa. Yana gudu yana juyowa yana fad'in" Shegiya kariya nasan kiransu kikayi ban gama dake ba ina nan dawowa wllhi sai na amshi kud'ina,  idan suna sonki su biya maki ko ki biya da jikinki agwagwa kawai... 

   "Kallonta kawai Shattima keyi cike da k'yama yana girgiza kai,  unbelievably.  Jalal kam tuni ya shige cikin gidan sai bankad'e banked'e yake yana neman Zubaidah.

   "Imam ne yabi bayan Jalal yana fad'in malam lafiya,  yaya zaku shigo gidan mutum ku hau masa bincike...
  "Wani mugun kallo kawai Jalal ya watsa masa jijiyoyin jikinsa sunyi rud'u rud'u yake fad'in" Where... Is..... She....  Word by word yayi maganar, 
   "Imam kuwa Ba tareda ya fahimci me Jalal ke nufi ba yake dubansa , wani uban tsawa Jalal ya kuma daka masa " Where's My wiiifeee!  I know she's here,  just tell me ina takeee,.. Ya k'arashe maganar yana mank'uran Imam,  da sauri cikin kakari Imam yake masa nuni da waje kafin yace " She left,  she left......  Sake sa yayi ya fito waje a guje yanda su Shattima suke.  Gaban Zulaihat ya k'arasa yana bata wani irin look wanda da an maka sunanka sorry kawai, ...

    "Ina take???  Ya tambaya yana daka tsawa,  baki na rawa Zulaihat take fad'in" Wllhi ta... ta tafi tun sanda aka soma fad'an nan...

     "Idanunsa sun kad'a sunyi jazir, kana iya jin hucin da yake kaman kububuwar maciji,  shak'eta yayi da iyaka k'arfinsa ya had'a da jikin garu yana fad'in" I'll kill you Garbage, .... "Da k'yar su Shattima suka k'waceta ganin zaiyi kisa...


   "Sumkuyawa tayi tana tari tana sosa wuyarta ga jinin da ya kuma b'allewa a bakinta ciwon da Duguja yaji mata,..  
  
      "Yana fiffizgewa yake fad'in" If something bad happens to her I swear you'll  kill you,  tell me are you working for them,  you're working for them right,  you are working for the Dasukis,  admit,  just admit  you bitch...

    "Da k'yar ta d'agi kai tana fad'in" I've no idea what you talking about,  Zubaidah ita ta kawo kanta nan,  I didn't drag her here,.....


     "A zuciye Shattima yace " Then why did you lie to Us,  meyasa kika min k'arya,  why did you even show up in my life,  idan ba kinada wani bad intentions dinki akan Zubaidah ba,  . First you lied to me cewa da Aunt d'inki kike zaune,  while ba haka bane you're  just a prostitute,  second kinma Zubaidah k'arya cewa ke fiancee d'ina ne,  tell us what do you have in mind,  what ate your intentions...

    "A zuciye ta mik'e cike da jin zafin maganganun Shattima kafin taci gaba da fad'in" Yes I lied to you I admit,  I was only using you to get close to Zubaidah sabida na gane mutumin do nake so gangar jikinsa da ruhinsa na gareta,  mutumin nan ba kowa bane illa Umar her Xfiancee,  he loves her very much wanda har takai bazai iya kallon wata mace ba face ita,  wann shine dalilina,  snn zaman da Zubaidah tayi a wajena ban cutar da ita ba Allah shine shaida na....  Ta k'arashe maganar tana hawaye .....


   "FFuskar nan tasa tayi jajazur gashin jikinsa sun mimmik'e haka idanunsa sunyi jazur,  kaman mutun mutumi haka ya tsaya a wajen,  sai dunk'ule duka hannayensa biyu da yayi...


    "Shattima ma ya zama shocked sosai,  a hankali ya soma jan hannun Jalal yana fad'in" Let's get out of here,  babu musu ya soma binsa tamkar rak'umi da akala,  har sun isa jikin mota Shattima ya juyo ya dubeta kafin yace " I'll never forgive you..  Daga haka ya soma k'ok'arin bud'e mota,  Usman ne ya karb'i keys d'in yana fad'in" Let me drive,  babu musu Shattima ya mik'a masa ya koma seat d'in baya .....


    "Kifa kansa yayi gaban mota sanda yaji wani irin hawaye mai k'una ya ciko idanunsa. Why all this,  why why,  why life has to like this,...  Jin zuciyarsa na neman kaucewa rahamar ubangiji yasa soma karanto innalillahi wa Inna ilahirraji'un,  Allahuma ajirni fi musibati wa aklifli khairan minha....



Sameena ce
[1/23, 22:22] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                               48


*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_



*Dedicated To All Victims Of Rape...*




   "Tafi minti biyar tana durk'ushe a wajen tana kuka,  for the first time data soma jin takaicin irin rayuwar data jefa kanta ciki,  rarrsshin duniya Imam yayi tak'i kulasa,  sai snn ya kula da shopping bags d'in da akayi patali dasu a gefe,  k'arasawa yayi ya tattaro su,  komai na cikin jakar are sealed, daga can gefe ya hangi 'yar k'aramar takarda,  d'aukowa yayi ya ajiye gabanta kafin yace " Kiyi hak'uri ga sak'o nan I'm sure is yours..

   "D'ago rinanun idanunta tayi tana bin kayan da kallo wanda ita kanta batasan dasu ba sai yanzu, goge hawayen idanunta tayi ta amshi takardar ta soma dubawa,  tana gama karancewa ta kuma fashewa da wani matsanancin kuka.... Tunowa da tayi tabbas Zibaidah ta karance takardan nan koma tayi arba da Umar yasata sakin wani murmushi,  ko babu komai yanzu Zubaidah zata fahimci Umar ya barta for good snn da har yanzu yana sonta da bai tafi ya k'yaleta ba,  da ya tafi da ita...
  "Wani murmushi Zulaihat ta kuma Saki kafin ta shiga bubbud'e kayan,  kaya ne masu d'an karen tsada haka ta ringa fitfito dasu Imam na tayata, fad'i yake,  ai gwara ki kira mutumin da ya kawo kayan nan ya biya maki kud'in hayar ki,  don daga gani he's loaded, ..

  "Zulaihat dai bata kulasa ba sai firfito da kaya take,  wayarta ta d'auka ta shiga dialing lambar Umar sand take umurtan Imam ya shigar da kayan ciki....

   "Bugu biyu ya d'aga wayan, ba tare da ta iya furta komai ba sai kukan data fashe dashi....  "Cike da damuwa yake tambayarta lafiya..

  "Cikin salo Zulaihat ke shesshek'an kuka tana fad'in " Pls come to my place,  dan Allah kazo yanzu,  come before he kill me... Daga haka ta katse wayar...

  "Hankali Tashe ya bar breakfast d'in da yake ya fito ya nufo gidanta...


   "Mintoci kad'an ya kawosa apartment d'in Zulaihat,  tana ganinsa ta fad'a jikinsa tana shesshek'ar kuka,  sosai ya razana da ganin yanayinta,  fuska a daddauje gashi Tana kuka,..
 
   "Rungumeta yayi cike da tausayawa,  murya cike da mamaki yake fad'in" What happened to you,  who did this to you...

  "Cikin kuka Zulaihat ta labarta masa komai na maganan gidan haya,... 

  "Rai b'ace yake fad'in" If I see that jerk I'll make him pay,  ta yaya zai bugeki, you should have called me right away,....

   "Goge hawayen tayi ta kuma matsewa cikin jikinsa kafin tace " Banyi tunanin haka ba,  I thought you will never come back to me, ...
   "D'ago ido tayi tana dubansa sanda ya k'ura mata idanu,  hannayensa ta rik'e kafin tace " Me ka fad'a wa Zubaidah,  I thought idan ka ganta you won't let her go,  now I believed you feel something for me,  ka zab'eni ko..??  Ta k'arashe maganar tana sakar masa murmushi....


   "Jin maganganun nata yayi kaman almara,..

 "Wait you mean to say Zubaidah's here with you..?  Ya tambaya yana zaro bold eyes d'insa...

   "D'an jim tayi tana tunanin toh kodai basu had'u bane kafin ta d'an girgiza kai tace " but not anymore,  she left awhile ago...

  "Mik'ewa yayi yana fad'in" Ina kike tunanin ta tafi,  ina zan sameta, ... Wait how did you know her...???

   "Ganin gaba d'aya ya rikice yasa jikin Zulaihat yin sanyi...

   "Mik'ewa tayi ta shiga tattaro kayayyakin da ya saya mata ta shiga jibgawa a gabansa tana fad'in" You'll never stop loving her,  will you,...  Just get out of here,  I don't wanna see you ever again..... Turasa ta shiga yi da iya k'arfinta tana dukan k'irjinsa har suka isa k'ofa kafin ta rufe k'ofar ta durk'ushe wajen tana kuka...

   "Hannu yasa ya shafi askinsa wanda yake low-cut  kafin fuzar da iska, cikin ransa yake fad'in" No Zulaihat I can't leave you,  zaki min amfani wajen cimma burina,  I need to work with you,  I must know ta yaya kika san Zubaidah har tazo gidanki while halayyan ku ya banbanta.. you must be an important person to her....

  "Jingunuwa yayi jikin k'ofar gamida k'ank'an da murya kafin ya soma fad'in" Pls Zulaihat let's talk,  don't shut me out pls,  I'm sorry I mean it....

   "Cikin kuka take fad'in" Ka tafi don Allah bana son ganinka and don't show up ever again...

   "Bai tafi ba sai ma magiya da ya ringa mata,...  A haka Imam ya iso ya iske a bakin k'ofa ga sautin kukan Zulaihat da yake jiyowa,..  A sittin Imam yayi kansa ya cakume masa wuya yana fad'in" What's it again,  who are you..  Me ka mata...

   "Jin Imam ya kaure Umar da fad'a yasata saurin bud'e k'ofar tsakaninsu ta shiga ta rabasu gamida daka wa Imam tsawa tana fad'in" Just go Imam I can handle this,.. Cikin tsawa shima yake fad'in"No I won't let any jerk lay a finger on you again..

   "Then nace ka tafi ka tafi pls, is not what you thinking....  Mugun kallo ya watsa wa  Umar kafin ya k'araso gareta ya rik'e kafad'unta yace " Always remember that you can count on me,  I'll be here when ever you needs me,  kin wuce k'anwa a wajena...

   "Murmushi ta sakar masa gamida gyad'a masa kai,  daga haka Imam ya fice yayi tafiyarsa.

   "K'arasow Umar yayi gamida bata light hug cikin k'ank'an da murya yace " I'm sorry, gaba d'aya sai ya tafi da Zulaihat,  tuni ta mak'ale cikin jikinsa tana sauk'e ajiyan zuciya..

   "A hankali ya soma fad'in" I didn't mean to hurt you Zulaihat,  ki min uziri, what I went through babu sauki,  I was to marry her,  dakawai baikona a kanta kafin wann Jerk d'in Jalal ya aureta,  Zubaidah betrays me,  my whole life nayisa ne bisa sohayayyarta but still she chooses to be with that imbecile, ba komai yasa nake son sanin yanda take ba a yanzu illa to take my revenge on her and her so called husband,  I want to make them pay I wanna see them suffering,... Ya d'an Dad'a matseta cikin jikinsa kafin yace " Believe me I'll never leave you again,  you have me completely....  Da sauri ta d'ago idanu tana dubansa gyad'a mata kai yayi kafin yace " Yeah I promise,  all I want from you is to tell me everything every single thing you know about Zubaidah kinji my luv...


   "My luv ta maimaita a hankali batasan sanda murmushi ya kufce mata  ba... Da sauri ta kuma rungumarsa very tied....

    "Murmushi shima yayi gamida k'urama waje guda ido,  cikin zuciyarsa yake fad'in" You'll help take Zubaidah back,  she's mine.....

**************

    "Neman duniyar nan basu sameta ba,  ga dare ya soma yi,  ga ruwan da ake kan zabgawa kaman da bakin k'warya,  gaba d'aya ya fita hayyacinsa,  duk tausayinsa ya rufe su,.. 

   "Usman ya dafa sa yace " Bro mu mik'a cigiya kafafen watsa labarai ko Allah zaisa a sameta,  kaga dare yayi ga ruwan da ake kan zabgawa,  kaga yanda ruwa ke d'iga a jikinka zakayi ciwo.....

   "Kallon Usman yayi da rinannun idanunsa kafin ya soma fad'in" I don't care Usman ban damu nayi ciwo ba,  All I want is to see her again,  what if she couldn't take care of her self,  what if something bad happens to her,  me kake tunani....  Yasa hannunsa gamida kwantar da sumansa da ruwa ya jik'a had'i da fuzar da iskan bakinsa,  ga wani sanyi da ya soma kad'asa...

   "Juyawa yayi ya kalli Shattima wanda har yanzu cikin damuwar abinda Zulaihat tayi yake kafin ya k'arasa k'asar bishiyan da yake....  Bud'e bakin da zaiyi da niyyan magana wa Shattuma ya hangi mutum kwance bayan katakon shagon dake k'ark'ashin bishiyar,  hijabin makarantar ta ne a jikinta,  kwance take tamkar maras numfashi da alama ruwan ya jima yana bugunta..... bai iya ce masu komai ba sai k'arasawa wajen da yayi,  cikin sauri suma suka k'araso wajen gaba d'aya....



Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:22] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                                49


*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*




   "D'agota yayi ya rungume cikin jikinsa hannayensa na rawan sanyi,  murya na rawa yake fad'in" I'm sorry, you'll be I got you.... Zafin jikinta da nasa suka gauraya waje guda yana jin fitar turirin numfashinta a hankali , haka ya ringa sumbatu still tana rungume cikin jikinsa,  Shattima ne ya dubi Usman kana yace " Get the car buddy, 
  "Yeah sure,  Usman ya fad'i ya nufi yanda suka faka motar ya k'araso da ita yanda suke,  ...

  "Dafe shoulder d'in Jalal Shattima yayi kafin yace " Muje Jalal... Babu musu ya mik'e gamida d'aukanta a hannu tamkar baby...  Shattima ya bud'e masa back seat suka shige yayi saurin wucewa mazaunin Me zaman banza....


   "Dr Khaleesat ta d'an ja medicated glass d'inta k'asa kad'an ta duba agogon dake d'aure a hannunta na hagu ya nuna k'arfe 10 da wasu dak'ik'ai sauk'e light breath tayi kafin ta dubi Annah data rapka uban tagumi tace " Ki kwantar da hankalinki Insha Allah everything will be alright,  is getting late ni zan wuce gida idan yaso gobe sai muyi reporting to the police snn mu kai cigiya kafafen yad'a labarai...
   "Gyad'a mata kai kawai Annah tayi ba tare da ta iya cewa komai ba.....  Kaman daga sama suka jiyo muryar  Hamma Habibu yana fad'in

"Annah Annah sun sameta,  sun samo k'anwata,  Jalal ya samo mun ita....

  "A tare Annah da Dr Khaleesat suka mik'e,  Hadiza ce mai d'aga labule Hamma na gyara mata,  Tana nan rik'e a hannunsa ya shigo bai tsaya ko ina ba  sai bedroom d'in Annah cikin sauri suka d'unguma suka bi bayansa,  ajiyeta yayi saman bed ya shiga rarumo bargo yana rufa mata,  sai gaishesa suke faman yi amma bai sami zarafin amsa su ba,  she dai kawai yaga Zubaidah ta zama safe, ... "Jin jikinta ya kuma yin zafi yasa sa d'ago kai yana duban Dr kafin yace " Her temperature is burning ko asibiti za'a kaita..

  "Let me see,  cewar Dr Khaleesat , da sauri Jalal ya matsa gefe ya bata waje  sunkuyawa tayi tana tattab'a jikin Zubaidah jafin ta girgiza kai tace " No babu komai tsananin fever ne kawai kuma ruwan da ya jima yana sauk'a jikinta ya saka mata give her paracetamol idan ta tashi and I'll prescribe her medication as soon as I get home idan yaso sai na maka texting,  ta d'anyi murmushi tana duban Jalal kafin tace " Mr Jay baka lura kayan jikin matar taka a jik'e suke ba ka ajiyeta haka and still ka rufa mata bargo, take off the clothes ka saka mata wasu snn a matsa mata jikinta da warm water with a towel sabida zafin jikin ya sauk'a.....
   "Kaman jira Hadiza take nan tayi karaf tace " Ni Dije zanga yanda za'a canza wann kaya mutanen da ko kwana d'akj guda basu tab'a yi ba shine za'a ce ya sake mata ka......  "Aya ta saka ma zancen nata ganin wani irin muguwar kallon da Jalal ya watsa mata.... "Babu wanda yace k'ala sai Dr Khaleesat data kuma duban Jalal tace "   you should change your clothes too before you fall sick,  kai nasan kaima baka da lafiya,  zan maka prescribing magani kaima,  don I'm pretty sure ciwon soyayya kuke....  Gaba d'aya suka murmusa harda Hamma wanda ke durk'ushe yana rik'e da hannun k'anwarsa.
  "Toh ni zan wuce and pls a guje duk wani abinda zai b'ata mata rai for now....  Dr Khaleesat bata Kai aya ba Hamma ya dubi Hadiza yace " Kinji koh Hadiza likita tace kar a b'ata mata rai dan Allah kar ki mata masifa kinji.....

  "Kallon fuskokin mutanen wajen Hadiza tayi kafin ta kafesa da wani mugun harara tace " Da shike nice uwar 'yan bala"i koh,  dan na nuna damuwata akanta ashe nayi laifi....  Banji ba ban gani ba balle kuce nace....  Ta buga wani uban tsaki gamida ficewa fuuuu....

   "Gaba d'aya suka bita da kallo,  Hamma ya mik'e yana dariya wanda shi a tunaninsa murmushi yake ya dubi  Dr yace " Kar ki damu haka take,  haka take...  Zan je na mata magana,  ya k'arashe maganar yana nuni da k'ofa, ...

    "D'an murmushi kawai Dr tayi gamida gyad'a kanta... Annah kuwa kaman ta nitse sabida takaicin Hadiza,  sallama suka kuma yi da Jalal kafin Annah tayi ma Dr rakiya....



    "Tsura mata dogayen idanunsa wanda basu faye girma ba yayi yana tunanin ta yanda zai soma canza mata kaya, .

    "Mik'ewa yayi jiki babu laka ya nufi drawer d'in da yake tunani nata ne kafin ya bud'e,  kayanta ya gani a shirye tsaf a ciki....  D'an fuzar da iska yayi kafin ya ciro wasu kayan. Ya dawo yanda take...

   "Ya jima yana durk'ushe gaban gadon yana dubanta, fuzar da iska ya kumayi kafin yasa hannu ya yaye bargon,...  K'irjinsa ya shiga bugawa da sauri da sauri sanda yake k'ok'arin rabata da rigar jikinta....  Abubuwan da suka faru a wancan daren suka shiga dawo masa,  fuskokinsu yake hangowa sanda suke keta mata rigarta....  "Da k'arfin gaske ya runtse duka idanunsa biyu...  Kasa cire mata rigar yayi sai mik'ewa tsaye da yayi cikin sauri ya nufo parlor,  a k"ofa suka had'u da Annah sai rawan sanyi yake....  Kan ta sami zarafin magana yayi saurin mik'a mata kayan Zubaidah dake  hannunsa yace "Barin duba su Shattima..... Ya k'areshe maganar cikin rawar murya irin ta maras lafiya....

   "Kallonsa Annah tayi kafin tace " Ah sun tafi ai,  sunce zakuyi waya.... "Baka da lafiya ne,  she added..

  "D'an jim yayi kafin yace" I'll be fine Annah just take care of her, I'll be in my room idan kina nema na..

    "D'an gyad'a kai kawai tayi ta bisa da kallo cike da tausayawa har ya fice..


    "Layin Shattima ya soma kira yajita a kashe,  nan ya kira na Usman, .
  "Usman ya sanar dashi Shattima ke da journey gobe da sassafe, zaije sa Kaduna and daga chan maybe ya wuce Gombe...

     "Jalal ya kuma tak'urewa cikin bargo kafin yace " I feel bad  you know,  I couldn't have chance to thank you...  Zan sake kiransa gobe da safe insha Allah... Na gode na gode sosai Usman " You guys are incredible Allah Ya bar zumunci...
  "Haba Jalal ka daina fad'im haka pls,  that's what brothers are for..  I'll see you tomorrow Allah k'ara rufa asiri...

     "Ameen Jalal ya amsa dashi sukayi sallama kafin yayi hanging up...

   "Washe gari tunda ya tashi tun safe bai fita ko k'ofa ba dukda jikin nasa ya masa dama dama breakfast ma har d'aki Annah ta kai masa,  lokaci zuwa lokaci yake tambayar ko Zubaidah ta tashi..
  "
   "Wajajen k'arfe sha biyu da rabi goshin azahar ya fito ya nufi d'akin Annah...

**************

  *Dasuki Holding*

"Zaune yake yana juyi saman kujeran nasa waya mak'ale a kunnensa ba sai ance maka da sahibarsa yake wayan ba,  banda uwar harara babu abunda Labib ke watsa masa....

   "Salim yaci gaba da fad'in" are you serious sweetheart, wait how comes bansan kina shirin had'a mana spectacular dinner ba.
  "Murmushi yayi sanda ta basa answer kafin yace " Okay kice k'aramar biki zaki kuma had'a mana,  okay zan fad'a wasu Daddy right away tunda duka suna nan har Pappy...  Ohh my Baby can't wait to see you,  kar dai kiyi aiki sosai ki gaji kinji Baby na...  Ya kuma yin want murmushi mai sauti yana juyi bisa kujeran kafin yace " Okay my darling kisses to you.....


    "Har ya k'arashe wayar Labib bai daina danna masa harara ba...

  "Mik'ewa Salim yayi yana gyara suit d'insa ba tareda ya dubi Labib ba yake fad'in" Kausar is inviting us all for dinner tonight zanje na fad'awa su Daddy right away su Mummy ma will be there,...  Bai damu da rashin ansa sa da Labib beyiba idan da sabo ya saba da halin d'an uwan nasa...

    "Har ya kai k'ofa ya juyo yace " Pls ka kira Tariq ka fad'a masa though his family is invited too,  amma dai pls ka fad'a masa idan yaso sai ya zama kaman farewell party d'insa...

    "Bai amsa sa ba  sai faman kad'a biro da yake,  yana ficewa  yaja tsuka gamida furta " Useless..



Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:22] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                               50


*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*



*I've received your messages masoyan k'warai wllhi lisaffo sunayenku ma aiki ne sabida yawanku.. Nonetheless ina sonku irin totally d'inan Alkhairin Allah Ya kaimaku duk yanda kuke...😍😘❤*


   "Ya jima yana tsaye bakin k'ofa hannunsa a Hard'e kan k'irjinsa,  kallon siraran hawayen da suke bin k'uncinta yake...

   "Jikinta ne ya bata da kwai mutum a wajen snn wann k'amshin nasa bai barin hancinta da sauri ta d'ago kai tana dubansa,...  Fuskan nan nasa a mirtuk'e babu alamun Fari'a,  yana sanye cikin inner red Mai V-neck had'i da lallausar wando Wanda da kad'an ya wuce gwiwarsa....

   "Cikin sauri ta kauda kai gefe don bata juran kallonsa...

   "Taku kad'an yayi ya k'araso cikin parlorn.... Cak ya tsaya a gabanta cikin dakakkiyar murya ya soma fad'in"

  "Why... Me yasaki yin haka, .... "K'ara sautin muryar yayi cikin tsananin fad'a yake fad'in" Tell me why,  what... What if I couldn't find you,  what if I couldn't protect you.... Do you even realize the kind of trouble you almost got your self into huhhh..?? Do you think you the only suffering..?
  "D'agota yayi sanda kukanta ya k'aru ya rik'e arms d'inta da k'arfin gaske suna fuskanta juna yaci gaba da fad'in" Look into my eyes and tell me what the heck did I do to you this time around...

  "Bud'e jik'akk'un idanunta da suke sharkaf da hawaye tayi ta sauk'esu kan farin fuskarsa da ya turning red,  siriryar jijiyar goshinsa ta fito sosai,  siraran dogayen idanunsa sun firfito waje,  sirirn hancinsa wanda bai faye tsawo ba k'ofofin sun bubbud'e, his cute pink lips keeps blowing kaman ya shafa lipstick....
   "Ta tuna yanayin data gansu da Tariq zuciyarta ya shiga mata zogi da rad'ad'i..
  "Da k'arfin gaske cikin tsananin kuka take fad'in" Eh gwara na tafi ko ina ne,  'cause you all the same, you... Are... Just... Like... Them...  You all raped me...  Snn I saw you with him hugging each other probably planning something again ...
  "Are you going to deny it, huhh.. Ka fad'a mun Me kuke shiryawa akaina,  ka fad'a mun kuna shirya yanda zaku...... ENOUGH.!!!!!! YA daka mata wata tsawan da saida hawaye ya fita daga idanunsa....  Annah dake kitchen saida ta yarda ludayi....

   "Ita kanta Zubaidah shaking ta soma tana kallonsa bata tab'a ganinsa cikin irin wann yanayi ba.... 

    "Ido cikin ido yake dubanta in a furious tune yaci gaba da fad'in" I love you.... I love you ultimately more than you might think. And you know I'm not asking you to love me back.. All I want is protect you and to keep you safe koda hakan zai zama ajalina....  I don't care anymore if you don't believe me.....  Daga haka ya juya ya fice daga parlorn cikin sauri.......

  "A bakin k'ofa suka had'u da Annah,  bata sami zarafin masa magana ba ganin yanyain nasa,  ta jima bataga irin wnn yanayi a tattare da d'an nata ba, ... "Cikin sauri ya nufi d'akinsa.  Kallo Annah ta bisa dashi har ya shige. Sauk'e nannauyan ajiyan zuciya tayi ta shiga parlon tana addu'an Allah Ya kawo k'arshen wann Al'amari.....


   "Har lokacin kuka Zubaidah take,  lallashi ya zame ma Annah jiki...


    "Yana shiga d'akinsa wandosa ya canza zuwa ta jeans kafin ya fice.
  "Suna jin ficewarsa ko sallama bai masu ba.

  "Zubaidah ta kuma shigewa jikin Annah hawaye na fita idanunta,  tausayin kanta ya kuma kamata,  for the first time dataji babu Dad'i abinda tayiwa Jalal,  Kalman *I love you and I'm not asking you to love me back* ta ringa nanatawa cikin zuciyarta, wani hawayen na kwarara mata musamman idan ta tuno abunda Umar da Zulaihat suka mata....



*******************

*Police Department Headquarter Wuse2 Abuja*


    "D'aga idanunsa yayi ya kuma karantawa,  zuciyarsa tana Dad'a basa k'arfin gwiwa akan abinda yayi niyya, kai tsaye ya kutsa kai ciki,  tuni ya nemi ganin IG, ba'a basa daman ganin sa ba,  ya jima yana jiran neman  ganinsa bai samu ba har saida IG ya fito daga meeting, haka kurum yaji yana son ganin Jalal,  nan aka masa izini.....


    "Kai tsaye bayan sun gama gaisawa IG ya tambayesa "How may I help you young man.

   "Without any hesitation Jalal yace " Sir I came to confess...

   "Kalllonsa yayi da kyau kafin ya kuma tambayarsa,  kai tsaye Jalal ya kuma nanata masa... In details Ya fad'i komai bai b'oye ba mai d'aukan rahoto bisa computer Ya rubuce komai.

   "Inspector yasha mamakin abun sosai,  don kuwa babban mutum a k'asa irin Kasim Dasuki bai zaci zai yi haka ba,  koda yake mutane for their children babu abunda bazasuyi ba...
    "Kallon Jalal yayi da kyau kafin  yace " Mr Jalal I've heard your confession and zamu rik'e Ka a nan,  but before muyi arresting sauran sai ita victim d'in tayi magana you understand what I mean say tayi filing complaint..

   "Intercom ya danna kafin wani Sargent ya shigo ya fita da Jalal...


   "Annah tasan halin d'an nata idan yayi fushi tasan kalan zuciyan Jalal, sai iya shafe sati ba tareda sun gansa ba,  lambarsa ta shiga nema,

     "Sargent d'in da ya d'auka ne ya sanar da ita Jalal na police station. Ai tuni Annah ta mik'e tsaye tana tambayarsa me ya kai d'anta police station,  Kai tsaye Sargent d'in ya mik'a ma Jalal wayan...

    "Cikeda tashin hankali ta soma magana,  Jalal,  me kayi aka kama ka,  me ya faru......
  
      "A hankali yace " Annah ki kwantar da hankalinki ni na kai kaina, I confessed everything,

   "Annah ta nanata a fili daidai sanda ta juya taga Zubaidah ta mata k'uri alamun tana saurarenta...  Da sauri ta k'araso tana fad"im Annah Dan Allah barin masa magana,  tana maganan cikin rawan murya zuciyarta cike da takaicin kanta don kuwa ita tayi provoking d'insa.....


   "Pls come back home,  dan Allah ka dawo I promise bazan sake ba, kaji but pls don't leave me all alone by my self.....  Abunda yaji knn cikin kunnuwarsa wanda ya kasa gasgatawa.

    "Damk'e wayar yayi sosai kafin ya soma fad'in" I'm doing this for us to live in peace, all I want from you is to talk,  don't remain silent,  File a complaint against your enemies,  don't let them get away with it,  kiyi magana kiyi magana,  talk kinji babu rufarufa from this very moment,  let the whole world know the truth, let us get what we deserve, kinji... Pls talk.

   "Kaman na ganinta haka take nodding kanta tana hawaye take fad'in" I'll talk Right away,  I'll speak up, kaji,  you'll be safe and you'll be free.....  Kuka ya kuma kufce mata,  Annah ce ta karb'i wayan ta tambayesa station d'in da yake......

****************


   "A hankali ta turo k'ofar d'akin har lokacin zuba kaya yake cikin luggage d'insa,  dafasa mum tayi kafin tace " Tariq da gaske tafiya zakayi ka barmu,  Tariq you are our only son bazan iya jure rashinka ba.....

   "D'an jefar da rigar hannunsa yayi ya d'ago yana dubanta kafin yace " Oh com'on  Mum do we have to talk about it again, bazan iya ci gaba da rayuwa a nan bar,  I need a change of environment Mum,  I need to forget everything that happened here,  I need to start a fresh....
   "D'an goge hawayen idanunta tayi kafin tace " Zan ringa visiting d'in ko  yaushe, ..

    "Murmushi yayi gamida hugging d'inta da hannu d'aya cikin arms d'insa kafin yace " Bazaki iya visiting d'ina ko yaushe ba, munyi nisa,  Moscow da nan akwai nisa sosai Mum,  all I can say you'll always remain here.... Ya k'arashe yana nuni da k'irjinsa ma'ana heart d"insa... Murmushi ta sakar masa itama ta rungume sa sosai... Sa hannu yayi ya share mata hawayen idanunta...

   "Tayasa arranging kayan taci gaba dayi,  sunayi suna hiran sanyin da zai tarar a Moscow, nan ta tambayesa ko zaije dinner d'in da Kausar ta had'a anjima..

    "D'an jimm yayi kafin yace " I'm not so sure coz flight d'ina da safe ne so banson nazo ban tashi da wuri ba...

   "Shafa kansa tayi tana fad'in" No excuse you are going,  at least kayi sallama da kowa....  Zaiyi magana ta d'aura hannu bisa lips d"insa tace" Final you are going na gama magana....

  "Murmushi yayi kana yace " Alright Mum just because you insist,  that's my boy ta fad'i sanda take zipping jakar....




   "Around 7:00pm ya nufo stirs d'in Mum don jin kota shirya su tafi tare,  wayan da yake jiyowa daga d'akinta yasa gabansa ya yanke ya fad'i.

     "Mum taci gaba da fad'in" Haba Barr Munir na fad'a maka zanzo zanzo , idan Tariq ya tafi ma mun huta had'uwa a hotel coz gobe zai tafi,  tayi wani dariya kafin taci gaba da fad'in" Haba kar ka damu alak'armu bazata Tab'a yankewa ba don bazan tab'a bari Alh Maina ya sani ba.....



    "Bibbiyu Tariq ya soma gani,  ya kasa gasgata abubuwan da ya gama ji,  cikin sauri ya juya ya sauk'a k'asa,  kai tsaye motar sa ya nufa ya fice a guje,  fuskar Barr Munir kawai yake hangowa,  shi kad'ai yake huci yake fad'in" I'll kill that Bastard with my very own hands.........


   *At the company*

" Salim Ya kuma duban Labib kafin yace " Hey stop being so stubborn,  dalla ka tashi mu tafi, kaifa mugun D'angelo iska ne,  you wai uwar Me zaka tsaya yi ko  anan zaka kwana ne.

    "Da wutsiyar Ido Labib ya kallesa kafin yace " Do I always have to explain my self,  nace maka bazanje ba fine,  ka tafi mana abunka...

     "Rufe laptop d'in gaban Labib Salim yayi yana wata murmushi yake fad'in" Hey your crush is gonna be there too,  Asmah I'm pretty sure tana chanma probably helping Kausar,  com'on don't be stubborn tashi muje.....

   "Hararansa kawai Labib yayi kafin ya mik'e yana zungurin k'eyarsa yace " You such a jerk you know.... 
  'Dariya  Salim yayi yana fad'in whatever....  Dariya kawai Labib d'inma yayi kafin suka nufi lift suka sauk'o k'asa.




     "Dukansu motar Salim suka shige,  Labin yayabawa wani security car keys d'insa yace ya kaimasa gida....


    "Suna fitowa k"ofar company d'in motocin police , cike da tashin hankali suke bin polisawan da kallo,  guda d'aya ne ya fito ya nufi motarsu...  Tuni suka bud'e motar..

   "Cike da gadara Labib yake fad'in" Lafiyanku wa kuke nema  snn bakusan nan company bane,  and idan wani kuke nema working hours zakuzo ba yanzu ba...  Police biyu Suka fito, 

  "I'm Detective Amir you need to come with us to the station..

       "Sai snn Salim ya fincike marfin mota ya fito yana fad'in" Officer what the heck are you talking about,  you can't arrest us just like that,  besides meyasa zamu biku station...


     "Idan munje chan kwaji bayani ya fad'i sanda ya kalli Sargent biyu yace ARREST THEM , No... No you can't do this to Us,  kunsan su waye mu,  kunsan mu 'ya'yan waye..  You will all regret this,  you doing this to loose your job....  Salim ya fad'i sanda yake kallon securities d'in company d'insu yace" Call my Dad right away.....


   "Haka sunaji suna gani aka tasa k'eyarsu.....


*At Salem's House*


      "Su Daddy da Pappy suna parlour suna hira,  akasarin hiran kan business ne  da kuma forthcoming election,  Alh Kasim yana bawa Alh Tahir shawarwaei kan garuruwan da ya kamata suje convention su kuma gudanar da Rally....

   "Mummy da Mumsy suna k'aramin parlon Kausar suna nasu hiran,  yayinda Kausar da Asmah da ma'aikatan ta guda biyu suke zarya daga kitchen zuwa makeken dining area d'inta wanda table d'in ke d'auke da kujeru goma sha bbiyu...

   "Barr na waje yana amsa kiran da aka masa cewa anyi arresting su Salim,  kaman daga sama yaji sauk'ar naushi a kumatunsa sa saida wayar ta tarwatse  a k'asa,  cakumosa Tariq ya kumayi yana fad'in" I'll kill you,  you Bastard....




Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:22] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                            51

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*



   "Kaman Allah ne ya aikosa haka yake dukan Barr Munir da iya k'arfinsa....   "Hankulan securities masu tsaron Gate ya tashi cikin sauri suka nufi cikin gidan suka sanar dasu don sun kasa dakatar da Tariq da irin dukan da yake ma Barrister..

   "A sittin suka fito gaba d'ayansu hakan yayi daidai da isowan su Mum d'in Tariq da Dad d'in sa...

   "Su Mumsy su Mummy Kausar da Asmah gaba d'aya suka daskare suna kallon wann ikon Allah...

   "Alh Tahir da Alh Kasim suka yi kansu suna rirrik'e Tariq..

   "Fuzgewa yake yi yana fad'in "Let go of me,  let me go....  Let me kill this Animal.... Alh Kasim ya janye Barr yayinda Alh Tahir ke rik'e da Tariq...

   "A tamanin Su Mum d'in Tariq suka fito daga mota suka nufo su.... 
 "Da gudu tayi kansa tana fad'in" Tariq my Baby Me  ya faru....

   "Idonsa na zubda hawaye yake nunata da yatsa yaci gaba da fad'in" Don't you dare come near me,  you have no idea how shameful it is being your son....  You are disgusting, I can't believe you're his mistress. Na tsaneki na tsaneki snn ke ba mahaifiyata bace.

   "Juyawa yayi ya kalli Barr dake zaune shame shame a k'asa fuska duk jini yace" I'm not done with you, you miserable coward,  sai na kashe ka har lahira Worthless imbecile...  Mark my word....  Cikin sauri ya nufi motar sa yana haki....

   "Kallon k'yama da mamaki Alh Maina ke watsa wa Mum d'in Tariq dake tsaye tana zuban hawaye....  Jin yanda Tariq ya kwashi motar yasan komai ka iya faruwa yasa sa saurin shigewa motarsa yabi bayan d'ansa....


   "Gaba d'aya jikkunansu sunyi sanyi babu kaman familyn Kausar,  this is a disgrace,  ace uncle d'in Inlaw d'insu ne wann,  Mum d'in Tariq jiki a sanyaye ta fice daga gidan cike da kunya da nadama...

 
   "Mummy da Daddy suka ja Barr suka nufi guestroom dashi,  yanda take shiga bata nan take fita ba,  yanda kasan ba yayanta ba haka take tsefe sa,
   "Ka rasa wa zaka nema sai k'awata kuma matar aure, matar abokin mijina uwar abokin d'ana haba haba gaskiya nidai baka kyauta min ba ...
   "Daddy ne ya shiga lallab'anta yana nuna mata kuskurene da sharrin shed'an Amma he can fix this taje taji da bak'i...

   "Mummy ta kuma narka masa harara kan nan nasa a k'asa kaman munafukin k'adangare,  bai iya furta komai...  Tsaki tayi ta fice fuuu tana tunanin da wani ido zata kalli Haj Raliya Mum d"in Kausar....

   "Mummy tana fita Alh Kasim ya matso kusa dashi kafin yace " Kayi kuskure yaya zaka nemi wacce you are somehow closed to her family,  ai idan zakayi bariki waje zaka fita ka nema,  kaga yanzu ga abinda ya haifar, me kake tunanin Alh Tahir zai d'auke mu,  Irresponsible mutane ko me??? ....

   "Dafe kansa yayi gamida buga uban tsaki yana goge jinin bakinsa kafin yace " Ai wann Me sauk'i ne kan abinda zan fad'a maka...

   "Police arrested Salim and Labib,  wayan da aka mun kenn ana gaya mun kafin d'an iskan yaron nan ya iso,  nasan shima the cops are after him Allah sa su capke shege.....
  "Wait. Wait.. Wait.....  Daddy ya dakatar dashi da fad'in haka,  kafin yaci gaba da fad'in" Kana nufin kace " An kama only son d'ina.... 

   "Galala Barr ya kallesa kafin yace " Me yasa basu iso ba har yanzu,  for your information your precious little boy is spending the night in a jell....

   "Mik'ewa Daddy yayi yana girgiza kai yake fad'in" k'arya ne wann,  babu wanda ya isa ya kulle mun d'ana,  tashi maza ka tafi,  you are their lawyer,  kar ka bar wani shege ya tab'a mun lafiyan yaro.. 

   "Mik'ewa Barr yayi yana goge hancinsa mai zuban jini yake fad'in" Yarinyar nan ta b'allo ma kanta aikin da bazata iya ba....  Turasa k'ofa Daddy yayi yana fad'in" Just go I'll take care of the situation here....


     "Duk sunyi jigum jigum a parlor suna jimamin abinda ya faru,  kowa da kalan tagumin da ya rapka,  suna hango Daddy Kausar ta mik'e tana fad'in" Daddy ina Salim he should be here by now,  me ya hanasu isowa har yanzu.....


   "Jim Daddy yayi yana duvansu kafin yace " ..... The girl..... Shiru yayi sakamakon k'irjinsa dake bugawa,...  Dakewa yayi yaci gaba da fad'in" The... Girl Filed a charges against them. An tafi dasu police station......  Ai bai gama rufe baki ba Kausar ta Saki wani irin k'ara gamida zubewa k'asa,  cikin sauri Mumsy da Asmah suka rik'eta....

   "Kuka take tana fad"in" Na sani na san ba k'arya take mun ba,  kune mak'aryata macuta mayaudara azzalumai kuka bari na auri criminal son d'inku......  Pappy ne ya dubi Mumsy da Asmah yace su haura da ita sama...

  "Fuzgewa Kausar ta kumayi ta k'araso gaban Mummy tana watsa mata mugun kallo take fad'in" Aren't you going to say something Haj Farha,  kiyi magana mana Ashe kinsan d'an iskan d'anki rapist n....... Bata kai aya ba Pappy ya d'auketa da wani wawan mari..... D'agowa Kausar tayi tana dubansa cike da mamaki tun tasowarta ko zunguri bai tab'a had'ata da mahaifinta ba sai gashi yau ya mareta...  Cikin kuka dafe da k'uncinta take fad'in" Pappy you shaped me because of these worthless people....  Da k'arfin gaske ya kuma fad"in " Raliya I said take her up stirs...

   "Mumsy da k'walla ya ciko idanunta da sauri ta shiga jan Kausar Asmah na tayata suka haye sama d'akin Kausar.


     "Mummy jiki a mace take kuka ta nufi balcony...


    "Wani mugun kallo Alh Tahir ke watsa ma abokin nasa kurum...

   "Daddy ya d'an fuzar da iska kafin yace " I guess we need to talk,  babu musu Alh Tahir yabi bayansa suka koma cikin parlorn suka zauna....

   "Bud'e baki Daddy yayi zaiyi magana Alh Tahir ya dakatar dashi ta hanyar d'aga masa hannu kafin ya soma fad'in"  No more lies Alh Kasim,  just go straight to the point and tell me the exact truth....  In a furious tune yayi maganar....


    "Sauk'e ajiyan zuciya Daddy yayi kafin ya soma 'yan kame kame.... 

   "Ai Mr President kasan halin yaran yau,  kwata kwata basa jin magana,  duk iya k"ok'arinka na ganin ka wadata su sai Sun sab'a kasan yar..... Da wutsiyar ido kawai Alh Tahir ke kallon Alh Kasim kafin ya d"aga masa hannu alamun dakatarwa yace " Mr President go straight to the point,  Did they commit the crime or not..???

    "Tura hulansa baya yayi kafin yace " Yes the Did,  but...but....

   "Period abinda nake son ji kenan,  cewar Alh Tahir Marafa kafin yaci gaba da fad'in" Ban tab'a zaton amincin dake tsakaninmu zaisa ka rufa wann babban laifi da d'anka ya aikata ba ka bari na aura masa tilon 'yata,  ka bani kunya Alh Kasim.

     "Cikin sauri Daddy ya soma fad'in" Yaran nan yara ne,  kuma ita yarinyar mun wadatasu da kud'i rashin godiyar Allah ne yasata maka k'ara....

    "Jinjina kai Alh Tahir yayi kafin yace " Yanzu na gane cewa kai wani irin mutum ne,  na d"auko dukiyata na zubata a company d'inka snn na d'auki only daughter d'ina na Aura ma d'anka....  For your information I'm taking all my money I mean all my shears out of the company,  I don't want you to drag me and my family into this mess of yours.....

    "K'ok'arin mik'ewa ya soma Alh Kasim ya k'arasa ya dafe kafad'arsa kana yace " You already in the mess kar ka mance d'ana na auren 'yarka snn if you are thinking sabida siyasarka zaka yanke alak'a damu then you are mistaken sabida you can't go anywhere without us,  Alh Tahir you perfectly well know Me,  kasan kalananyan mutanen da nake dasu a k'asar nan,  kasan I can ruin you, your carrier in politics and last your Reputation,  so ina mai baka shawara just back down, muci gaba tunda kaima ka shigo cikin mess d'in....


     "Buge hannunsa Alh Tahir yayi kafin yaci gaba da fad'in" Your criminal son must divorce my daughter don ban haifa mata ma criminal irinsa ba,  snn da kake maganan you can ruin me,  fine go ahead,  abu guda ne nasan bazan bari ka lalata mun ba shine Reputation d'ina,  you can go ahead and ruin my carrier in politics but I'll not allow you to ruin my reputation a idanun duniya kaman yanda naka sunan yake gab da b'aci.....  Daga haka ya fice cikin sauri yana sab'a babbar riga,  gaba d'aya ma ya mance dasu Kausar.....


    "Kallo Daddy yabisa dashi har ya fice, da  k'arfi ya daki garun parlorn da yasha ado da golden wallpaper yana fad'in" Damn it dammit...... I'll not allow you to bring me down you filthy mere girl....




     "Mumsy wllhi sai na bar gidan nan,  ko kwana bazan kumayi ciki ba,  snn wllhi dole Salim Ya biyo ni da takarda na ko na maka sa a kotu, ..... Ta k'arashe tana jefa kaya cikin trolley d'inta,  Asmah dai tama rasa wanne zatayi,  haka suka had'u ita da Mumsy suketa faman lallashin Kausar.....  Ana haka Mummy ta turo k'ofa tana k'ok'arin shigowa jiki a sanyaye uwa munafuka.....  Harara kawai Kausar ke b'alla mata sabida duk sun san gaskiya suka take....

   "Mik'ewa tayi tana fad'in" What are you doing here,  kin karb'o mun takardan Saki na ne ko me..??

    "Cike da b'acin rai Mumsy ta daka mata tsawa gamida zaunar da ita,  bana son rashin hankali Kausar,  kina shaye shaye ne kike fad'a wa manyan mutane maganganu irin haka,  especially uwar mijinki.....

     "Cikin kuka Kausar take fad'in" Mumsy wllhi ni ba uwar mijina bane,  wllhi sai ya sakeni....


 "Kallon Asmah Mumsy tayi tace " Rik'eta ku sauk'a k'asa ina zuwa,..  Gyad'a kai kawai Asmah tayi kana ta rungumo Kausar suka nufi downstairs....


    "Mummy ta Kalli Mumsy jiki a mace,  da k'yar ta iya bud'e baki da niyyan magana,  Mumsy ta dakatar da ita...

.   "Haj Farha I know you must be having a hard time,  but inaso ki sani dukanmu muna cikin tashin hankali a yanzu,  ban zaci zaki iya manipulating d'ina haka ba,  claiming to be my friend,  ta yaya zaki bari Yata ta auri criminal bayan kinsan mafarkin ko wata uwa 'yarta ta kasance cikin auren soyayya da kwamciyar hankali,  my daughter is suffering,  tunda muke da Kausar bata tab'a zama maras kunya ba sai yau,  ko da yaushe cikin obeying d'inmu take,  kema shaida ce,  dole ma abin yayi affecting d'inta,  ta yaya zakiji ace ga mijinki ana shari'a dashi ya aikata babban laifi irin fyad'e,  ko ke da kike mahaifiyarsa abun bazaiyi affecting d'inki kaman matarsa ba,   abu guda da zai dameki shine rashinsa da zakiyi muddin aka jefasa gidan yari, So pls kar ki soma tunanin zan lalashi Kausar tayi zaman gaibu da d'anku,  snn kema mace ne,  ko baki haifi d'iya mace ba,  kiyi tunanin irin k'uncin rayuwar da yaranku suka jefa wancan yarinyar a ciki,  iyayenta wani hali suke ciki,  ni Mace ce kuma mother of Mace, Ni dai abunda zan iya cewa Allah shi karb'a wa mai gaskiya hakkinsa..  Snn maganar auren Salim da Kausar dole a datsesa.. Daga haka Mumsy taja akwatin Kausar ta nufi k'asa rai b'ace...


    "Mummy kam kifa kanta tayi bisa gado ta shiga rusa kukan abubuwan takaicin da suka sameta a yau...


  "Cikin tsananin tashin hankali Dad d'in Tariq yaci gaba da suka gewaye motan yana fad'in call an ambulance....  Cikin mintoci kankani ambulance ta iso aka saka Tariq da ya kwankwatse a mota aka wuce dashi emergency



***************

*Gombe, Palace*


   "Kai tsaye parlorn mai Martaba Babban gwani ya nufa,  he's looking tired and exhausted,  bisa ga alamu bai jima da shigowa garin ba...

  "Tundaga waje fadawa ke masa kirari, 
  "An gaisheka Shattima,  Sallama ya gaisheka,  Madawaki ma gaisuwa yake,  An gaisheka D'an  Wazari  badad'in Mai Martaba, ...... Gyad'a masu kai kawai yake yana mai ci gaba da tafiyar sa,  yana isowa k'ofa Shamak'i ya basa hanya yana gaishesa yana fad'in" Shiga cikin aminci baka da Shamak'i....

    "Zaune ya taddasa da shalelensa Zahidah...  Da sallama kai a k"asa cike da ladabi irinta babban gida Shattima ya shiga wargajejen parlorn....  Rusunawa yayi yana mai mik'a gaisuwarsa ga mai Martaba,  Ta k'asa k'asa Zahida ke kallonsa tana tunanin yaje yaga sahibarsa Zulaihat... D'an satan kallonta shima yayi sanda ta mik'e tana gyara alkyabbanta ta rusuna tace " Abba na barka lafiya. Murmushi yayi kana yace " Allah Ya sada mu da Alkhairi mamata...  Ficewa tayi Shattima ya d'an biebayanta da kallo don baiso Mai Martaba ya Kula kallon Zahida yake,  juyowan da zaiyi ya sauk'e idonsa kan makeken hoton babyn nan,  gabansa ya yanke ya fad'i sakamakon hango fuskar Jalal da yayi cikin hoton.....



Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:23] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                          52


*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*



   "Har lokacin ta kasa saka komai a cikinta,  hawaye na kan zuba a idanunta, Allah sarki Jalal koda ace yayi raping d'inta Ya cancanci yafiyarta balle ma ta yarda dashi tasan iyakar gaskiyarsa knn beyi ba,  sa bayan hannunta tayi ta goge hawayen,  Kamal ne ya matso kusa da ita kana yace " Didi wai inji Mama na uncle Jay bazai tab'a dawowa ba  wai kullesa za'ayi...

   "Wani hawayen ta kuma gogewa kafin tace " Zai dawo zai dawo garemu,  idan kayi sallah ka ringa masa addu'a kaji.. Gyad'a kansa yaron yayi fuska fal damuwa kafin yace " Ina sonshi bana so ya tafi ya barmu...  Kema kina sonshi ko Didi...  Wani sabon kukan ya kufce mata,  batasan sanda ta shiga nodding kanta da sauri ba gamida jawo Kamal ta rungumesa...

   "Annah dake hangosu daga veranda ta goge k'wallan da suka cika idanunta....


     "Cell d'in gefe da Jalal aka jefasu, ... Salim fad'i yake Officer you can't arrest us just like that,  you've no clue who you really messing with...

   "Labib kuwa hango Jalal yayi,  fincikian k'arfen ya shigayi yana fad'in" This is all your fault you Trader,  I swear I'm gonna make you pay for this,.... " Da k'arfi Jalal ya mik'e yana fad'in" Shut your Trap you criminal....

   "Labib ya kuma watsa masa harara kafin yace " You're nothing but a Trader,  how dare you betrayed us,  bari kaga na fito daga wajen nan  sai na sata ta k'aryata abinda ta fad'i......

  "Naushin da Jalal ya kai masa ta cikin k'arafunan Ya hanasa k"arasa maganar,

  "You Imbecile ka gama maganganunka akaina but the moment ka sake wani magana akan matata sai na kashe ka.  Bas... tard..... Ya fad'i sanda yake komawa wajen zamansa...

   "Janyo Labib Salim yayi kafin yace " K'yalesa kasan tsiyan talaka abinda ya gada knn,  'cause bai gaji arziki ba,  we are getting out of here soon, and we will take our revenge.

  "Zama kawai Labib yayi bisa benchin yana goge jinin bakinsa yana watsa mugun kallo wa Jalal...

***************

   "A ranar da suka cika kwana biyu aka fito dasu za'a canza masu cell,  gaba d'aya families d'in sun had'u a station harda Mamin Labib data riski labarin gangaratsau....

 "Babu yanda Barr beyi ba akan abada belin su IG ya hana yace sai an shiga kotu sati mai zuwa duk abinda alk'ali ya yanke fine.. Coz bashida say a yanzu tunda ta shigar da k'ara..

   "Hannayensu cikin handcuffs aka fito dasu,  su mummy da Mami Me zasuyi banda kuka,.....  Salim girman carpet da Ac jikinsa har wani daddaujewa yayi,  jajazur kaman me borin jini a d'an kwana biyun da yayi cikin cell.... 

   "Mummy Daddy pls take me out of this place,  I can't stand it,  pld Dad do something, don't let them take me away....  Haka Salim ya ringa fad'i polisawa na turasa suna fad'in move..

   "Labib kuwa da taurin zuciya sai k'arfafa gwiwa wa  Maminsa yake..

   "Barr ne ya fito yana fad'in" Kar ku damu zanyi komai wajen tsaya maku...  Uncle pls do something..  Salim Ya kuma fad'i...

  "Kausar bata bari Asmah ta gama parking ba ta bud'e motar ta isa gaban Salim tana fad'in" You liar this is where you belong,  make sure ka rubuta min takardan sakina....
   "Kausar my love pls don't believe her,  she's just lying...  Bai kai aya ba Kausar ta kuma fad'in" Just shut up you imbecile,  I'll  give her my unconditional support,  until I see you locked up in jell... Asmah ta shiga jan Kausar baya ganin Journalist sun cike wajen sai d'aukan rahoto suke,  sai faman d'aukan fuskar Kausar suke yanda take zuba masifa ma Salim...

   "A kunnenta Asmah take rad'a mata Kausar let's get out of here,  kinsan su Pappy basu san mun fito ba,  zasu k'ara fushi sosai tunda an hanaki fita...  Kan su ankara sai ganin abokan aikinta Journalist wa'enda basa good terms suna d'aukanta suna fad'in" Mrs Salim Dasuki da alama kema baki bayan mijin naki knn da gaske ne kema kin yarda ya aikata laifin da ake zarginsa ko kuma dama wann hali d'abi'Anas.......  Jawo mayafinta Kausar tayi ta shiga rufe fuskarta tana tutture Jama'a tana neman hanyan fita daga wajen....


    "Daidai sanda aka bud'e masu motar masu laifi adaidaitan su Zubaidah ya paka a wajen itada Annah...

   "A guje ta fito gamida k'walla masa kira da k'arfin gaske " JALAAAL,  a hankali ya furta Zubaidah,  saurin juyowa yayi sukayi ido hud'u gaba d"aya mutanen dake wajen kallo ya koma kanta....  Gefe da ita ya hangi Umar ya paka motarsa ya fito....

   "Fincika yayi da k'arfin gaske yana fad'in" Don't come near my wife,  don't you dare come near her,  I swear I'll kill you....  Gaba d'aya kallo ya kuma komawa kan Umar....


   "Gaban Zubaidah yayi wani irin yankewa Annah ta rik'eta sosai tana fad'in" Kar ka damu Jalal,  I'll look after her for you,  I'll take care of her...
  "Just take care of yourself son...


  "pls Annah do that for me, ki kular min da ita....


  "Cikin kuka Zubaidah take fad'in " Don't worry I'll be safe,  promise me you'll come back to me....


   "Siriryar hawaye ta fito daga idanunsa sanda ya furta I love you....  Kafin ya shige bayan motar....

    "Hanki d'in hannunsa kawai take hangowa har motar ta wuce....

    "Annah tayi saurin rik'ota suka nufi adaidaitansu sanda Journalist sukayi chaaa akanta suna jefo mata tambayoyi.....

  "Alh Kasim ya kafe Umar da ido kafin ya sunkuya saitin kunnen Barr yace " I thought we made it clear to that idiot that he should get lost,  what heck is he doing here??

   "Barr kuwa wata murmushi ya Saki kafin yace " Zai mana amfani,  bai jira cewar Alh Tahir ba ya saci idon Jam'ma'a ya nufi motar Umar, zama yayi a Front seat yana fad'in " Keep driving...

 "Galala Umar ke kallonsa kafin yace " Ban gane ba ina zan kaika,...
   "Gajeren tsaki Barr yayi gamida fuzar da iska kafin ya kuma fad'in" Don't be such an idiot just keep moving.

    "Karya staring mota yayi kafin suka mik'a titi.....

***************

  "Tunda suka soma tafiya hankalin Annah ya karkata kan tunani guda,  ina zasu samu lawyer wani lawyer ne zai tsaya masu,  kai komai na duniyar yanzu ma saida kud'i yaya zatayi....

   "Hannun Zubaidah taji cikin nata,  tayi saurin d'agowa tana kallonta,.

   "Murya na rawa take fad'in" I'm sorry Annah, believe me nima bana son ganinsa cikin wann halin,  da nasan zai tafi police station da banyi provoking d'insa ba.....

    "Damk'e hannunta sosai Annah tayi tana girgiza kai kafin tace " None of this is your fault Zubaidah,  abinda Jalal yayi yayi daidai,  let them all be punished,  sun zalunceki,  they shouldn't get away with it,  Allah yana nan baya bacci da sannu zaibi kadin mai gaskiya...
    "Babban abinda ke gabanmu a yanzu shine samun lawyer....  D'an jimm Zubaidah tayi kafin ta d'ago da sauri tana fad'in " Dr Khaleesat,....  We should talk to her right away maybe she can help....


     "Shiru Annah tayi tana dubanta tana nazarin maganan nata kafin tace " Dr Khaleesat tana mana k'ok"ari I don't want us to be a burden to her...

    "Damuwa ya kuma nunawa  a fuskar Zubaidah,  shiru tayi ta shiga wani tunanin daidai lokacin da mai tasi ya ajiyesu....


   "Da mugun mamaki suke kallon motar dake pake k'ofar gidansu,  k'irjinsu ya yanke ya fad'i lab'ewa bayan Annah Zubaidah ta soma tana fad'in" Annah bazasu tab'a k'yalemu ba na sani....

    "Annah ta rik'e hannunta sosai cikin nata tana fad'in" Kar ki damu babu abunda suka isa su mana,  muje...


    "Kausar tana hangosu tayi saurin fitowa a motar,  ganin Kausar ya basu mamaki,  take Zubaidah ta had'e rai tana fad'in" Me kike nema a nan,  me ya kawo ki nan,  kinzo ne ki kuma k'aryatani kaman yanda mak'aryacin azzalumin mijinki yayi,  idanma kinzo sayan mu da kud'ine kaman yanda kuka saba toh ki sani bakuda arzikin da zaku sayemu...  We won't back down.  Justice must be served.....
    "Annah ta dubi Kausar kafin tace " Kinji da kunnuwanki toh tun wuri ki tafi kafin muyi filing retraining order against you....

   "Rik'ota Asmah ta soma tana fad'in" Mu tafi Kausar....

   "Kausar ta soma girgiza kai cike da tausayi kafin tace " Kar kuyi tunanin ina tareda su,  wllhi bana tareda su,  nima babban burina shine na gansu behind bars, hawaye ya soma zuba a idanunta sanda taci gaba da fad'in" Auren Salim shine babban kuskuren da na tapka,  ta rik'o hannayen Zubaidah duka biyu taci gaba da fad'in" I'm here for you,  I want to help I want them to be punished,  pls don't push me away,  let's do this together.....

    "Girgiza kai Zubaidah ta soma kafin tace " Pls leave we don't want more trouble,  idan suka san we are seeing each other,  things might get more complicated.

     "Annah ta gyad'a kanta tacee" Haka ne Kausar,  kinga family d'inku are related Don Allah ku tafi kafin ku b'allo mana wani abun...


   "Goge hawayen idanunta tayi kafin tace " They will never find out,... Kun sami lawyer ne..??  Ta tambaya tana dubansu..


   "Shiru kaman babu me cewa komai cikinsu Annah tayi murmushi tace " Kar ku damu zamuyi komai cikin talaucinmu Ko bamuda kud'i do mulki munada Allah,  da sannu zai kawo mana mafita,  snn abu na k'arshe dan Allah kuyi nesa da gidan...  Mun gode k'warai da kulawarku..  Daga haka taja hannun Zubaidah suka shige gida...

    "Asmah taja hannun Kausar suka shige mota..


   "Suna tafe Asmah ta d'an juyo ta dubeta sanda take karya Stairing mota kafin tace " Kausar I think they are right,  we shouldn't be creating more problems,  the Dasukis have eyes everywhere,  they might be watching all our movement especially now that we are against them....


   "Harara Kausar ta galla mata da rinanaun idanunta masu zuban ruwa kafin tace " I don't care,  they can do their worse but I swear I won't back down har sai na gansu cikin k'unci da damuwa like the way they caused me ,  I want to see them suffering,  I want to see them going down....  Ta k'arashe maganar tana huci ita kad'ai.....

      "D'an sauk'e ajiyan zuciya kawai Asmah tayi gamida maida hankalinta ga driving....


      "Suna gama parking a haraban gidan suka hango Pappy daga saman balcony hannayensa hard'e a k'irji ya kafesu da ido fuskan nan tamau..  K'irjinsu ya soma dukan uku uku......


Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:23] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                               53

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*





*Where are you Bintu Abiha and Habiba love...  This one's for you guys, I read your chats jiya and nasha dariya sosai sosai oo 😂😂... 😍😘*



     "Sosai Pappy Ya masu fad'a Mumsy ma fad'an tayi masu sosai,  Harta car keys d'insu saida ya karb'e yace " No should drive again har sai komai ya lafa....

    "Kafin dare an soma yad'a abinda Kausar tayiwa Salim a social media 'yan adawan siyayasan Pappy abu ya masu Dad'i..

   "Shiru yayi gamida k'ura ma Video d'in ido,  yasan wann kad'an ne da aikin Alh Kasim,  he promised to ruin him completely, kan kace  me party chairman d'insu ya kira urgent meeting akansa,  a halin yanzu ana gab da amshe ticket d'insa na presidential election....


   "Zama yayi yana nazarin kalaman Barr.

_We want you to testify against Zubaidah in court_

   "Zulaihat ne ta zauna gefe dashi gamida rungumo kansa cikin k'irjinta tana wani mayaudarin murmushi.  Gani tayi gaba d'aya hankalinsa baya tare da ita,  d'an rik'o kumatunsa tayi kafin tace " Hey what's the matter, meke damunka....

   "Sauk'e ajiyan zuciya yayi kafin yace " Zubaidah Filed a complaint...

   "Zama da kyau Zulaihat tayi kafin tace " So,  meye naka na damuwa ka kyalesu suci kansu...

  "Shafa fuskarta yayi kafin yace " Kin tuna nace maki you'll help me to get my revenge on them ita da mijinta....

    "D'an jim Zulaihat tayi kafin tace " We are living a happy life nida kai bana so muyi engaging kanmu cikin wani matsala...

   "Mayaudarin murmushi yayi kafin yace " No matter what I'll never leave you alone,  just help me do this kinji baby na.

  "Ganin tayi jim tana dubansa yasa kamo kugunta sosai snn yaci gaba da fad'in" Pls Baby do this for me ko baki son ganin farin ciki na ne, 

   "D'an tab'e fuska tayi kafin tace " Toh me zaisa ka damu dasu bayan yanzu haka ma cikin tashin hankali suke...


   "Wata murmushi ya kumayi kafin yace " Idan naga ta rabu da Jalal har abada zaifi komai yi mun Dad'i,  snn na maki alk"awari bazan koma mata ba,  kinsan ina sonki,  as they say,  if they love you they will come back to you,  kinga da na tafi ai na dawo gareki meaning I can't do without you,  so iyaka abinda zaki iya mun shine ki taimaka min na d'au fansan abinda aka mun...


    "Murmushi Zulaihat tayi kafin tace " Toh how may I help you,

   "Shafa low cut askinsa yayi kafin yace " Zubaidah spent a night here with you, meaning ta gudo daga Chan gidansu,  I want you to give your testimony in court...


    "Da mamaki Zulaihat ke kallonsa kafin tayi magana yace " this is all I'm asking of you my love,  I'll explain everything to you later. Yanzu barin mana placing order ina zuwa,  daga haka ya mik'e ya fice yana neman layin Barr Munir...


*************

  "Tun daga k'ofar abisitin tasha jinin jikinta,  kamar wacce k'wai ya fashe ma a ciki haka take tafiya.....  Ai tun daga k'ofar ward d'in da ya hangota ya mik'e yana fad"in " Kar ki k'araso nan,  kar ki kuskura kiyi gigin zuwa kusa da  d'ana kije wajen d'an iskan sairayin naki tunda mun baku space sosai yanzu a gidan,  but don't you dare think of coming closer to my son...

   "Mum rakub'ewa tayi jikin garu tana kuka.... Daidai nan cops suka iso, Alh Maina ya mik'e da sauri yana fad'in " Lafiya officer..

   "Guda d'aya daga cikinsu yace " Lafiya Sir,  muna nan ne don tsaron d'akin da d'anka yake
...

   "No.. No Officer you can't do this,  my son isn't out of comer yet,  idan ya ganku hankalinsa zai kuma tashi...

   "We are sorry but we are only doing our job..You there you over there.... Haka ogan nasu ya jejjefasu kowa da wajen da ya tsaya.....


 ***************

    "Yau ya rage saura kwana uku a shiga kotu gashi basu sami lawyer ba,  gashi Dr Khaleesat bata nan ta tafi wani seminar a Lagos, gaba d'aya abu ya rincab'e masu,  Gashi tun baya kama su Jalal Usman bai lek'o ba,  Annah har garejinsu taje bata sami Usman ba,  abokan aikinta na makaranta ma ta baza cikiya neman good lawyer,  amma kunsan mutum a yau komai saida abin duniya...  Zubaidah kullum cikin kuka take,  Ga Hadiza ta sakata gaba da tsangwama tana cewa laifinta ne,  datayi hak'uri da Jalal bai kai kansa ma polisawa ba,  kuma wllhi ta zama bazaura bazata zauna da ita ba,  tayi d'awaiyinyarta tun k'uruciya bazatayi har zauwarci ba....

   "K'unci ya taru ya mata yawa,  kullum cikin addu'a da neman taimakon Allah suke.....

***************

   "Asmah pls,  wllhi nasan basu sami lawyer ba,  you know how people are nowadays,.....


    "Ajiye littafin hannunta Asmah tayi kafin tace " For crying out loud Kausar me kuma kike so nayi,  kina ganin irin fad'an da aka mana da irin dokar da aka sa mana a gidan nan,  me kike so nayi,  na gaji da taro mana damuwa da kike yi....

  "Tasowa tayi daga saman gadon kafin tace " Kina zuwa school kina samun Chance na fita,  that's why I'm asking you to do this,  don Allah ki samar masu lawyer I'll take are no fun his bills all I want is for justice to be served, Asmah kema fa mace ce,  kuma kar ki manta ciwon d'iya mace na d'iya mace ne,  it could happen to us,  zamu iya zama Victims muma,  pls Sis let's do this.....


    "Shiru Asmah tayi kafin tace " You are absolutely right,  but abun da muke niyyan yi yanada matuk'ar had'ari ba garemu kawai ba harda family d'inmu,  idan suka sani zasu sa wa pappy harma damu takunkumi,  kiga videos d'in da suka watsa suka sa aka dakatar da pappy a jamk'iyarsu,  what if they find out we are helping her,  things might get worse...

    "Kausar ta goge hawayen idanunta kafin tace " Na sani, kar ki damu akwai Allah bazai barsu suyita zalunci ba,  let's do it...

    "Asmah ta rik'e hannunta sosai kafin tace " Zanyi zanyi Kausar sabida ina son ganin murmushinki randa aka jefa Salim a prison. Rungume juna sukayi suna hawaye....

*************

"Tsaye suke a bargan dawakin Mai Martaba suna zab'an dokin da zasu hau su fita kilisa,
   "Khalifa ya dubi Shattima da gaba d'aya 'yan kwanakin nan ya canza,  dafasa yayi kafin yace " Wai meke damunka ne,  kwana biyun nan kana looking dull,
    "Murmushi Shattima yayi Wanda iyakacinsa fatar baki kafin yace " Babu komai kwai banjin Dad'i ne kwana biyun nan...

    "Khalifa yayi wata k'asaiteccen murmushi kafin yace " Ko kuma kana tunanin Gimbiya Zahidar ka ta kusa zama Mallaki na a ranar da za'a nad'ani sarautar Yariman masarautar nan...

  "Galala Shattima ke kallonsa kana yayi murmushi yace " Zahida ta fah kace.

    "KKhalifa ya gyad'a kai yace " K'warai kuwa kowa yasan irin shak'iwar dake tsakaninku tamkar yaya da k'anwa,  a ranar data zama matata zan saka maka katangar k'arfe tsakaninku tunda de kai ba muharraminta bane..

   "Murmushi kawai Shattima yayi sanda yake d'ale doki had'i da yin gajeren tsaki kafin yace muje da Allah,  dan wllhi muka k'ara minti biyu bamu fita ba zan fasa fita kilisan nan....


    "D'ale doki Khalifa yayi yana mai ci gaba da fad'in jikina na bani nine sarki mai jiran gado.

    "Shattima baice komai ba sai tunanin da yake yawan yi a 'yan kwanakin wanda ya rasa ma waye zai soma fad'i gashi abun ya damesa sosai...

  *Manage this 'yan uwa zaku jini later insha Allah... 😘😍*
[1/23, 22:23] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZIBAIDAH*

                               54


*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*



    "Kai tsaye gida ya wuce bayan sun sauk'a daga dawakin.

   "Parlron Ummansa ya shige ya tarar babu kowa sai TV dake faman aiki.
  "Zama yayi gijif cikin sofa gamida turo hulansa gaban goshi ya lumshe idanunsa,
  "Umma ce ta fito tana k'wala kira wa  Ameera k'anwar Shattima....  A'ah Shattima yaushe ka shigo,  Umma tace sanda take zama cikin d'aya Daga cikin kujerun.

  "D'an mik'ewa yayi ya zauna sosai kafin yace " Ummah barka da gida.

   "Tsaresa tayi da idanu don ta lura da canzawansa kwana biyu.
  "Bud'e murya Umma tayi kafin tace " Kai wai lafiyanka kwana biyu kake neman zama lusari,  gaba d'aya ka canza kaman bakai ba,  idan akan auren yarinyar nan Zahidah da Khalifa ne,  na fad'a maka ka cire ta a ranka,  Zahidah ba matarka bace  sanin kanka Baba Ciroma ba barin wani zaiyi ya auri Zahidah ba tunda ya k'wallafa ma wann d'an nasa  mai wuya kaman marken lema....

   "Tunda ta soma magana Shattima ke kallonta,  Umma dai bazata Tab'a canzawa ba,  wnn masifa nata ya rasa taxation da ita...

  "D'an jim yayi kafin yace " Umma am I that obvious??

  "Wani uwar harara ta kuma watsa Masa kafin tace " Bana son iskanci Karma ka soma min turancin rashin kunya ka bud'e baki ka fad'a min abunda ke damunka baka da wacce ta wuce ni mahaifiyarka...

   "Shattima ya kuma sauk'e ajiyan zuciya kafin yace " Ummah ba tunanin Zahidah nake ba,  besides na cire Zahidah a raina tuntuni tunda yau wata uku cif ya rage aurenta da Khalifa childhood friend d'ina,  abinda ke damuna wani abu ne daban snn  tun da akayi maganar aurenta take avoiding d'ina,  Umma bazan iya jure rashin maganarta a gareni ba..

  "Shek'ek"e ta kallesa kafin tace " Au ka yarda ka bari wani ya aureta,  ka yarda ka badakai a aura mata wanda bata so...

  "Kllonta kawai Shattima keyi cike da mamakin halin Umma saikace ba itace yanzu take masa fad'an ya cire Zahidah a ransa ba..

  "D'an fitowa yayi daga cikin kujeran ya turo gaba kafin yace " Umma ba wann ba,  wani tambaya nake so na maki..

   "Ina jinka menene??  Ta fad'i tana karyan goro.

  "Tab'e fuska yayi yana dubanta kafin yace " Umma wai Don Allah ke ba tsohuwa ba sai cin goro,  bakisan illansa ba koh..

  "Tab'e baki tayi gamida ci gaba da taunar goronta tana fad'in" Idan ka gama iyayinka da felek'en sai ka sanar dani Likita bokan turai,  kai wannan da likitanci ka karanta da kad"ifirin naka da yauk'in yafi haka..

 "Shafa kansa yayi gamida bata hak'uri.

 
  "Saida ya cire hular kansa ya ajiye saman hannun kujera kafin yace " Umma kince mun matar Mai Martaba ta fari d'iyar sarkin Zazzau k'awarki ce kafin Allah Ya mata rasuwa...


   "Cak ta tsaya da taunar goron da take tana dubansa, k'walla ya ciko idanunta,...

   "Shattima yaci gaba da fad'in" Umma wai meye asalin labarin mutuwarsu itada jaririnta Modibbo,..

   "Umma ta goge hawayen idanunta kafin ta soma fad'in" Dadda (sunan da ake kiran marigayiya matar mai martaba a masarautar)d'iya ce ga sarkin Zazzau wanda yake sonta sama da sauran 'ya'yansa, zata girme mun a shekare sabida lokacin da aka auro ta masarautan nan ba'a ma soma maganar aurena ba,  auren soyayya na saurayi da budurwa sukayi da Mai Martaba,  a lokacin da akai masa wankan nad'in sarauta a lokacin aka Aura masa ita..

   "Sun d'au lokaci sosai Allah bai basu haihuwa ba,  don har akayi aurena da mahaifinka shiru babu labari,     Nida Matar  Ciroma k'anin Mai Martaba a jere muka haifeku kaida Khalifa amma har lokacin shiru matar Mai Martaba bata haihu ba,  kasan babban gida da k'anan maganganu musamman ganin K'aninsa ya haihu shi bai haihu ba,  ..

   "Mahaifiyar Modibbo da kanta ta rok'i Mai Martaba ya k'ara aure,  snn ita da kanta ta zab'awa Mai Martaba yarinyar da zai Aura,  ko ya sani a masarautar nan baya son auren amma sabida Mahaifiyar Modibbo da kuma Mahaifiyarsa shi kansa Mai Martaban suna so yasa sa amincewa,  nan aka auro mahaifiyar Zahida a lokacin bata fi shekaru goma Sha biyar ba zuwa sha shida,   ashe tun lokacin da akayi auren Mai Martaba da Ummin Zahida Dadda nada juna biyu babu wanda ya sani....  Bayan biki da kad'an cikinta ya bayyana,  nan fah kulawa ya tattara ya koma kanta gaba d'aya,  Mai Martaba har mancewa yayi yayi amarya, Madaki mahaifiyar Mai Martaba nan itama kulawarta ya k'arau sosai akan Dadda,  wann dalili ya sanya Ummin Zahida cikin tsananin bak'in ciki ga k'uruciya da yarinta,  a lokacin har saida suka sami sab'ani sosai da Mai Martaba,  Dadda matar arziki 'yar Babban gida ita ta gyara komai,  suka ci gaba da zamansu lafiya,  taci gaba da rainon cikinta,  wata tara cif ta haihu,  haihuwar da ba'a tab'a irinsa ba a masarautar nan, anyi biki na haihuwarsa wanda ba'a tab'a irinsa ba yanda yaro yaci sunan Modibbo Lamid'o.......  Kukan Umma ya tsananta..  Shattima ya tashi daga kujeran da yake ya dawo gefenta ya zauna gamida rik'o kafad'unta...

     "Goge hawayen tayi kafin taci gaba da fad'in Daren da akayi suna da kwana bakwai daren data zama bak'in dare a wann masarauta daren da ya sauya farin cikin wann masarauta zuwa bak'in ciki,  daren da har yau ya kafa tarihi a masarautar nan,  daren da aka masa lakabi da BAK'IN DARE,  a wann dare aka wayi gari aka tarar da gawan Dadda snn aka nemi Yarima Modibbo aka rasa......


    "Kuka sosai Umma keyi har saida Shattima yaji dama bai d'ago maganar ba,  da k'yar ya samu ya lallashi Umma tayi shiru.  Mik'ewa yayi ya fice ya nufi d'akin sa yana tunanin al"amarin " What if Modibbo is still alive,  what if.....  K'irjinsa ta shiga bugawa da sauri da sauri,  What if Jalal is Yarima Modibbo,  But....  How's this be possible....? No way Jalal has his own family , mahaifiyarsa tana nan da rai, ta yaya ma zai soma fad'in wann abu,  da Mai Martaba zai soma ko kuwa da Jalal zai soma.... Toh wai ma how did he come up with all this,  dafe kansa yayi gamida zama bisa sofa,  yana addu'an Allah Ya bayyana Modibbo a duk yanda yake matuk'ar yana raye...


*****************

  "Hamma ne ya fita ya amsa sallamar da ake,  ganin mutum cikin bak'ak'en kaya black suit yasa sa komawa cikin gida da gudo yana neman abun d'auka,  can ya hangi muciya wajen wanke wanke ai nan ya rarumo muciyar nan ya nufo waje a guje......  Zubaidah dake kwasan shanya a sittin ta biyo bayansa tana tambayarsa lafiya....,  Annah ma fitowarta kenn daga bayi ta ajiye butar hannunta tabi bayansu cikin sauri.

  "Hamma kam fad'i yake " Turoka sukayi koh,  wai zaka gane kuranka.....  Da iya k'arfinsa ya nufi bawan Allahn nan,  Zubaidah tayi ta maza ta k'wace muciyar hannun Hamma tana fad'in" A'a a'a Hamma....

   "Barr Ansar Kumo dafe kansa yayi yana jiran ta Allah ta samesa...

   "Zubaidah ta shiga jan Hamma yana fizgewa yana fad'in" Ki barni na gama dasu ki barni dasu Zubaidah,   sunga babu Jalal suna tunanin zamu bari su ci zarafinki...

    "Gida ta shige dashi yayinda Annah ta k'arasa ga Barr Kumo tana fad'in" Lafiya bawan Alla, idan Dasuki ne suka turo ka tun wuri gwara ka tafi kafin mu kira maka 'yansanda...

    "Kallonta Barr Kumo yayi kafin ya sauk'e nannauyiyan ajiyan zuciya yace " Sannu Hajiya.... Em by the way sunana Barr Ansar Kumo,  ni lauya ne daga k'ungiyar kare rajin hakkin bil adama musamman Mata da k'anan Yara....

   "Cike da rashin hamsuwa Annah ke kallonsa don tasan Dasuki's zasu iya turo sa,... Zubaidah ce ta fito Hadiza na biye da ita....

   "Barr Kumo ya dubi Zubaidah data masa k'uri yace " Kar ku damu banazo nan bane don cutar daku sai don taimaka maku ......
Katsesa Hadiza tayi da fad'in" Malam ka dubeka kasha bak'in kaya uwa d'an fashi kai ai da ganinka ma babu alheri a tare da kai, .. Hararan da Annah ta narka mata yasata yin shiru....

.  "Girgiza kai Zubaidah ta soma kafin tace " Malam ka fad'a mana gaskiyan wanda ya turo ka  wajenmu nasan sai ankai k"orafi kungiyarku snn kuke ba wa mutum d'auki,  mu kuwa bamu kai ba don bamu da hanya,  nasan su suka turo ka don fad'ar damu a kotu,  Kayi wa Allah ka tafi ka k'yalemu,  ka tuna idan hakan ya faru akan d'yarka yaya zakaji.  Don Allah kar ka taimaka masu su ci gaba da zalunci...

  "Tausayinta ya cika zuciyar Barr Ansar,  sauk'e ajiyan zuciya yayi kafin yace " Kinyi gaskiya Zubaidah snn labarinki ya zama media circus,  yasa hannu ya ciro jarida cikin 'yar jakan dake hannunsa ya nuna mata kafin yace " Kin gani,  a halin yanzu labarin ki is everywhere a cikin k'asar nan,  people are curious to know more about you, Zubaidah ni na kawo kaina nan da ra'ayina ba tareda taimakon wata k'ungiya ba.......  Idonsa ya kad'a yayi ja sosai sanda yaci gaba da fad'in" Those Despicable are hiding behind their shadows,  they must pay for each and single crimes they had committed....

    "Gaba d'aya suka bisa da kallon mamaki sanda yasa bayan hannunsa ya goge hawayen da suka zubo masa.
   "Annah jiki a sanyaye tace mu shiga daga ciki.....


     "Daga yanda Faisal ya paka motarsa ya danna wayarsa,  bugu biyu Alh Kasim ya d'aga " Ina saurarenka Faisal..

  "Sir no doubt they've got an attorney.......

   "Mik'ewa tsaye yayi yana fad"in what.!!!!!
  "No way they can't find a lawyer,  abinda nake so da kai follow him and see who's helping them,  Faisal bana so a sami failure make sure kayi clean aiki...  Yeah I trust you.....  Daga haka ya katse wayar yana safa da marwa shi kad'ansa a parlour....


   "Yanda Alh Kasim ya umurcesa haka yayi.....  Har suka shigo cikin Abuja Barr Kumo baisan ana biye dashi ba. A k'ofar gidansa dake unguwar APO yayi parking ganin Asmah cikin tasi tana jiran isowarsa....

   "Fitowa tayi daga tasi d'in sanda shima ya fito daga motarsa suka sakar ma juna murmushi. A hankali tace " My chewing gum how does go.

  "Murmushi Barr Ansar yayi kafin yace " My silly girlfriend na fad'a maki ni nafi k'arfin your chewing gum saidai your super glue. D'an hararansa Asmah tayi kafin tace " I'm not your girlfriend you know.... 

  "Murmushi yayi kafin ya kuma cewa we can't talk here mu d'an shiga daga ciki,  hararansa ta d'anyi kafin tace " I hope su mommin ka na ciki...


    "K'walla ya kuma ciko idanunsa sanda ya soma tafiya ba tare da yace mata komai ba,  d'an girgiza kai kawai tayi tabi bayansa tana fad'in" Ansar bazaka daina wann hali naka ba,  a da nayi zaton ko wani abu ke damunka amma yanzu kam na gane tsaf halinka ne....

  "Gida ne apartment me kyaun gaske,  saidai tun daga waje Asmah ta gane kaman shi kad'ai yake rayuwa a gidan,  parlorn sa tsaf yasha furnished sai picture wanda ba sai ance maka na family d'insa bane,  saidai duk hotunan yana yaro ne Wanda bai wuce shekaru sha biyu ba,  harda 'yan k'annensa mace da namiji guda biyu....
   "Drinks ya kawo ya ajiye mata ta dubesa da kyau kana tace " Attorney kasan dai bazan sha komai a nan ba tunda da alama 'yan gidanku basa nan.....

   "Mik'ewa tsaye yayi in a furious tune yake fad'in " Yeah basa nan kuma bazasu tab'a dawowa ba,  I'm all alone,  I've no family,  ya k'arasa ya d'auko hoto guda d'aya yana nuna mata yake fad'in" Kinsan dalilin da yasa farko nak'i amince wa buk'atarki, kinsan dalilin da yasa nace maki " I didn't want to have anything to do with that Despicable Kasim Dasuki...????

    "Zaro ido kawai Asmah take tana girgiza kai,  Ansar yaci gaba da fad'in" That Bastard is the reason why I'm all alone now,  that imbecile destroyed my Family, 
  "My Father was an international Business Man,  Kasim Dasuki ya yaudaresa ya saka kud'ad'ensa gaba d'aya a company d'insu,  back then bana zama a k'asar nan,  ina can Qatar da Grandmother d'ina,  My Dad my Mum and my two siblings were living here in Nigeria,  rana d'aya heart attack ya kama mahaifina sabida karyasa da Kasim Dasuki yayi,  Dad d'ina ya shigar da k'ara baiyi nasara ba,  sabida Kasim Dasuki is very powerful Man, Mum d'ina tayi jinyarsa ya soma, babu yanda banso naga Mahaifina ba amma babu kud'in da zanzo Nigeria,  Grandma d'ina da take jinya itama a can Qatar depression na ciwon mahaifina ya mata yawa,  kwana kad'an Allah yayi mata cikawa,  ni kad'aina no family no relatives ga k'arancin shekaru haka da taimakon bayin Allah na k'warai aka kai grandma makwancinta,  Dad d'ina yana riskan labarin shima Allah Ya masa cikawa,  .... Kukansa ya k'aru sanda yaci gaba da fad'in" I couldn't have chance to say goodbye to my Dad,  Mum d'ina ta d'aukaka k'ara dare d'aya gidansu tayi gobara k'urumus,  da Mamata da k'anne na guda biyu all died a gobaran.  Ban tashi sani ba  sai lokacin da na saka k"afata a k'asar nan,  bayan shekaru masu yawa,  bayan all the hardships I gone through ni kad'aina a k'asar Qatar, aikatau babu kalan wanda banyi ba,  har na sami kud'in jirgi na dawo,  na tarar da wann bak'ar labari wanda nasan ba aikin kowa bane illa aikinsa sabida Mum d'ina ta d'aukaka k'ara shiyasa ya halak'asu.  Wann shine dalilina na zama lawyer to bring Justice to the society,...... Zama yayi bisa sofa hawaye na bin k'uncinsa, 
    "Tausayinsa ya cika zuciyar Asmah batasan sanda hawaye ya shiga gangara mata ba. Hanki ta ciro cikin jakarta ta mik'a masa,  ya karb'a ya goge hawayen kana yace " Thank you....

   "Har Asmah ta isa layinsu jikinta a mace yake da jin labarin Barr Ansar,  ta k'ofar baya ta shige hide....



   "Faisal da sai lokacin ya karya kan motarsa ya danna wayar uban gidansa kana yace " Sir the Marafa's are the ones helping them....

  "Murmushi Alh Kasim yayi kafin yace " Alh Tahir Marafa dabinmu da kai bata k'are ba,  I'll prove to that no one messes with the Dasuki's.......

   "Wayan Barr Munir ya kira kafin yace " Ka bincika wanene wann lawyer d'in nasu his profession at work and his family....  Sai naji feeback,  do that fast attorney we don't have much time,  kwana d'aya jal ya rage mana a shiga kotu....


  "K'asar akwatin ta ta bud'e ta ciro zoben tana murmushi,  tasan wann ba k'aramin amfani zai masu ba tunda za'a shiga kotu,  tasan Alh Kasim Dasuki zai biyata mak'udan kud'i ta gudu ita da d'anta taje ta sami miji mai hankalk tsaranta ba wann susu shashan ba.....  Wata dariya Hadiza ta kuma fashewa dashi kafin ta sunce bakin zaninta ta d'aure zoben,  mayafin ta ta shiga yafawa.....



Sameena ce 👌🏾👌🏾
[1/23, 22:23] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                            55

*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*




   "Sauri sauri ta fice daga gidan cikin canza kamanni bayan ta saci idon mutanen gidan...

   "Saida ta sauk'a k'asa da layinsu kafin ta tari tasi ta shige....

************

   "Alh Tahir yayi signing petition d'in kafin ya mik'e yana watsa wa Alh Kasim mugun kallo yake fad'in" It's over,  we are done,  one thing da ya rage mun daga gareka shine takardan sakin d'iyata,  make sure your dear son Ya sakar mun d'iyata, she's not meant to be with a criminal like him.... To make it clear, From now on babu business tsakanin Dasuki Holding da Marafah Construction.... PA d'in Alh Tahir ne ya shiga tattara documents d'in har lokacin Daddy bai iya cewa komai ba sai kallon saman table da yake yi yana karkad'a pen.

   "Gaba d'aya sauran shear holders suka sha jinin jikinsu,  dama bayan Alh Kasim da yake da 50% Alh Tahir shike da kusan 30% which means the company is at risk of going bankrupt....

  "Mik'ewa yayi yana huci ya fice daga conference hall d'in.  Barr ya dubi sauran mutanen yana fad'in " Excuse us....

   "Barr na masa magana ya daka masa wata uwar tsawa...  Just shut the hell up,  that damn man really crossed the line, I'm gonna make his life a living hell.

   "Danna intercom yayi kana yace " Jade tell Cimon to get my car ready....  Daga haka ya katse ya k'arasa ya d'auki babbar rigarsa dake jikin hanger yana k"ok'arin ficewa,  Barr na biye dashi yana fad'in" Mr President you need to calm down,  ka tsaya a bi komai a sannu...
.
   "Bai kulasa ba sai k'arasa lift da yayi ya danna down floor,.....

   "A parking Space suka hangi motar Umar,  yana ganinsu ya fito yana murmushi...

   "Fuzar da iska Daddy yayi kafin ya furta " Oh damn it,  nasan kaima kud'i kazo nema,  Brr take care of him bazan iya magana ba I'm completely pissed...

   "K'arasowa gabansa Umar yayi yana murmushi kafin yace " Alh Kasim seems you're in a rush,  anyway I'm not gonna take much of your time,...

   "Kallonsa Daddy yayi yana huci kafin yace " What is it again,  me kuma kake so,  kowa maganan kud'i I can't loose my company....

   "Wata murmushi Umar ya Saki yana shafa sumansa da yasha low-cut kafin yace " Relax Mr Dasuki,  you ain't gonna loose your company,  but what if you lose your only Son,....Ya kuma yin wata murmushi kafin yace  I know you never want that to happen..

   "Karkata babbar rigarsa yayi yana duban Barr,  da sauri Barr ya k'arasa ya dafa Umar yana fad'in" Me kuma kake nema bayan kud'in da muka k'ara maka.

  "Da gefen bakinsa Umar yayi murmushi kafin yace " It's not enough,  besides wancan kud'in nawa ne,  what about the girl that is gonna testify against Zubaidah ita kuma ina nata kason, ....

   "Fuzar da iska Barr yayi yana jawosa yake fad'in " Let's not talk about this here....  Cak Umar Ya tsaya yana girgiza kai kafin yace " No it has to be here,  a gaban Alh Kasim coz ni zan yanke amount d'in da zaku bada,  to prove to you inada abunda zaku defeating case d'inku in court let me present to you .... Juyawa yayi yana kallon motarsa gamida latsa wayarsa kafin yace " Fito nan ki same mu...

   "Da mamaki suke kallon motar saiga Zulaihta ta fito sanye da bak'ar sunshade a idanunta....

   "Kallonsu Zulaihat keyi kafin tace " Gentle Men Im gonna testify that Zubaidah is a prostitute ta zauna dani a lokacin da suka saka ma raguwarta takunkumi suka hanata fita yawon karuwanci.....

   "Ai basu san sanda suka soma wage baki ba suna dariya,  Alh Kasim harda shek'ewa kafin yace " Kai abokin aiki ne,  tafiyar saida Kai, ....

   "Umar Ya kuma yin wata murmushi yana rik'o hannun Zulaihat suka kalli juna suka sakar ma juna murmushi... 
  "A take suka yanke kud'in da za'a basu Alh Kasim yace Faisal should take care of them...  Faisal ne ya rubuta masu check d'in huge amount of money da suka demanding.  Alh Kasim ya nufi gida hankali kwance dukda had'arin kariyar arziki dake barazanar samun kampaninsu, yayinda Barr ya nufi gidan Barr Ansar dake Apo.

***********
*Maitama crescent ,  Dasuki Mansion*

   "Tana hango motocinsu tayi saurin fitowa a tasi d'in ta nufo su da sauri tana jan mayafi tana rurrufe fuskarta....  Kan mai gadi ya hangame masu Gate tayi saurin isa jikin motar tana bubbuga glass...

  "Securities suka nufota da sauri zasu kamata Alh Kasim ya dakatar dasu snn ya fito daga motar yana kallonta,  tsaf ya ganeta...  Bud'e murya ya d'anyi kafin yace " Me kuma kuke nema,  ko kun janye k'aran da kuka shigar ne,  ina mai tabbatar maku kabarinku kuke tonewa...

  "Ba tareda ta amsa sa ba,  sai maganarsa yake,  hannu tasa ta warware bakin zaninta ta ciro engagement ring d'in Salim sai Shek'i take kafin ta Saki wata murmushi...


   "Ai cak Daddy ya saka aya wa maganganunsa ya shiga binta da kallo yana k'ok'arin kai hannu jikin zoben don tsaf ya gane zoben a Dubai yasa aka k'era guda biyu kacal iri d'aya exactly don Salim da Kausar......


    "Matsar da hannunta baya tayi tana wata murmushi kafin tace " A'a bazan baka ba,  nasan sarai kasan me zoben,  na tsinceta ne a daren bikin baikon d'anka Salim da Kausar yanda suka yi fyad'e ma Zubaidah,  nasan Zoben zatayi kud'i sosai snn zata taka rawar gani a kotu,  shiyasa banyi k'asa a gwiwa ba na kawo maka ka sake saya, snn kar kayi tunanin bansan kud'in kaya ba ka bani k'aramar kud'i...  

   "Murmushi Daddy yayi yana duban gefe da gefe kafin ya Bud'e mata bayan mota yace shige muyi magana,  babu musu ta shige... Wayarsa ya danna ya kira Faisal ya kawo masa kud'i in cash right away....


*****************


   "Ya jima yana jiran Barr Ansar a parpajiyan gidansa,  can jimawa ya fito fuskan nan babu walwala don haka kawai yaji Mutumin bai kwanta masa ba.

   "Barr Munir na murmushi ya mik'a ma Barr Kumo hannu yace " Sunana Barr Munir Anka lawyer me Kare wa'enda client d'inka take k'ara......  Fuzge hannunsa Barr Ansar yayi take fuskarsa ta canza ya soma nuna masa gate yana fad'in" Get.... Out... Of....here.

    "Barr Munir ya d'an shafi kansa kafin yace " Attorney you and I really need to talk for your own good...

  "Matsowa daf dashi Barr Ansar yayi kafin yace " You and I have nothing to discuss,  idan hakan ta zama dole zamu had'u a kotu gobe,  so why don't you leave it till tomorrow...

   "Attorney listen to me,  We can offer a huge amount of money,  abu guda muke so daga gareka shine kar ka bayyana a kotu....

    "Tsalle Barr Ansar yayi ya shak'e wuyan Barr Munir yana fad'in" How dare you,  you imbecile,  you are despicable,  baka San aikin ka ba,  snn ka wulak'anta kwalin karatunka,  get out of here and don't ever show up again,  idan na sake ganin fuskar ka a nan, I'll file a case of harassing against you.... Now leeeeave.......!   Ya k'arashe yana nuna masa k'ofa....


   "Sosa wuyarsa Barr Munir yake yanda Barr Ansar ya mak'uresa yana tafiya yake fad'in" You'll regret this Attorney,  Mark my word....

  "Get out you shameless coward... Ansar ya fad'i sanda yake raka Barr Munir da kallon k'yama.....

**************


   "Barr Munir ya kuma kurb'an ruwa yana kallon Alh Kasim kafin yace " That Jerk is really an Imbecile,.....
    "Murmushi Daddy yayi kafin yace " He have no idea who he's really messing with.  Bamuda sauran damuwa tunda mun had'a abubuwa da dama,  Yanzu abunda ya rage mana mu tafi asibiti mu sami yaron nan kafin Police suyi interrogating nasa,  na fad'a wa Alh Maina kar ya kuskura ya bar Tariq yayi magana ba tareda lawyernsa yazo ba...

   "D'an jim Barr yayi kafin yace " Gaskiya ina tsoron ganin wad'an nan mutanen, ... Dafa sa Daddy yayi kafin yace " Let's get going bamu da sauran lokaci the cops will arrive by 8:00pm yanzu kuma already k'arfe bakwai tayi...
  "They have no choice dole kaine lawyansu , badon d'ana ba bazan tsaya ma d'an kowa ba....  Mik'ewa Barr yayi suka fice....

   Daga parlor Mummy taji k'aran fitar motocin su,  goge hawayen idanunta taci gaba da yi,  Jane ta kawo mata coffee,  tana fad'in" Ma'am your coffee.....

***************


   "Daddy ya dafa kafad'an Alh Maina kana yace " Ya jikin Tariq,...  Sauk'e ajiyan zuciya Alh Maina yayi kafin yace " Jikin sai ya d'an lafa sai kuma ya kuma rikicewa musamman idan yaga mahaifiyarsa,.
  "Daddy ya d'an shafi gishinsa kafin yace " Yeah is not easy,  I know both of you are suffering, I feel sorry for your family...

    "D'an gyad'a kansa Dad d'in Tariq yayi kafin yace " 'yansanda suna jiran lawyer d'in they gonna Interrogate him now.

   "Yeah sure Daddy yace kafin yayi alama ma Barr ya shigo,....  Ai babu shiri Dad d'in Tariq ya mik'e yana nuna Barr da yatsa yake fad'in" This Man,  you even have guts to show your face....  Juyowa yayi yana kallon Alh Kasim in a furious way yake fad'in" This Man could be my son's lawyer after my dead body....

    "Kafad'unsa Alh Kasim ya kama ya zaunar kafin yace " Calm down,  don't be such an idiot,  don't forget we are in this together,  is left to you ka shawo kan d'anka to cooperate,  abunda ya riga ya faru ya faru,  we are talking about our childrens freedom here,  ka ajiye duk wani grudges aside daga baya ayi dealing wann, and remember arzikinka na k'ark'ashin company d'ina,  I can ruin you if I want....  Kallonsa kawai Dad d'in Tariq keyi hawaye na ciko idanunsa.


   "Barr Munir bai samu ganin Tariq ba haka police basu samu daman interrogating nasa ba sabida rikicewa da jikinsa ya sake yi......


*On the Day Of the Trial*

_National High court, Abuja_


Sameena ce 👌🏾
[1/23, 22:24] ‪+234 803 619 0581‬: 🌘🌘🌘🌘 *ZUBAIDAH*

                                56


*©Sameena Aleeyou...✍🏾*

_Queen Samy Novels Forum...📖📚_


*Dedicated To All Victims Of Rape...*


"Annah ta Kalli Barr Ansar wanda gefensa wani lawyer ne abokin aikinsa kafin tace " Ansar wann shine lawyer d'in daka d'aukar ma Jalal,  gyad'a kansa yayi yana murmushi kafin yace " Annah meet Barr Hafiz he's a best friend of mine,  and he's willing to help,  sunyi magana da Jalal already...
  "I hope kin gane dalilin da yasa muka d'au ma Jalal lawyer,  sabida Confession d'insa,  Zubaidah didn't file a complaint against him but kafin ya wanke kansa daga confession d'in da yayi dole saida lawyer tunda this is a court case..
   "Annah ta goge k'wallan daya zubo mata sanda Barr Hafiz yake gaidata,  ashe akwai mutane irin haka,  tama rasa da wani irin kalma zata soma masu godiya sai hawaye...  Ansar ya d'an rage murya kafin yace " Let's be getting ready Annah,  ki sanar dasu Zubaidah yanzu zamu shiga,  gyad'a kanta kawai tayi ta nufi yanda su Zubaidah dasu Hamma suke..

   "Su Mommy dasu Daddy sai kallon mamaki suke bin su Kausar da Mum d'inta Hajiya Raliya basu tsammace zasu zo shari'ar ba...

 

      "Kotu tayi tsit kowa ya zauna,  Alk'ali yana shigowa suka mik'e gaba d'aya....

   "Bayan Ya zauna me karanto laifi ya karanto,  Alk'ali ya buk'aci a shigo da wa'enda ake k'ara...

    "K'irjinta sai bugawa yake da sauri da sauri,  abubuwan da suka faru a wancan daren suka shiga dawo mata sanda aka shigo da Labib da Salim,  gaba d'aya bata kula da Jalal ba sai jiyo sautin ihun su da dariyarsu da take Yi a kunnuwanta......  Idonta ya sauk'a kan Jalal dake faman kallonta yana girgiza kai alamum don't panic remain strong....
   "Saman kanta tayi da gyad'a masa kai hawaye na k'ok'arin ciko idanunta..


   "Bayan an gama karanto confession d'in Jalal,  Alk'ali yayi gyaran murya ya soma kirawo sunayensu kaman haka

 "Depending Labib Dasuki, depending Salim Dasuki,  depending Tariq Maina and Depending Jalal Ibrahim.... Gaba d'ya suka mimmik'e a akurkin tuhumar da suke zaune ciki...

   "Alk'ali ya tambaya ina Tariq Maina,  Barr Munir ya mik'e yana fad'in" Your honor I'm Barr Munir Anka his lawyer,  my client is in the hospital right now receiving treatments sabida had'arin mota da yayi,  he couldn't show up...

   "Alk'ali yayi rubutu kafin ya d'ago ya ambaci wanda yayi confession d'in wato Jalal.

   "Alk'ali ya dubesa bayan ya amsa kafin ya d'ago takardan hannunsa kafin yace " You made this confession ranar ishirin da d'aya ga watar Augusta a ofishin 'yan sanda dake Wuse,  shin ka tabbata kun aikata wann laifi.

  "Jalal ya kalli Zubaidah itama shi take kallo kafin ya soma fad'in" Your Honor ban aikata ba amma abokaina sun aikata......  Cakumosa Labib yayi da k'arfin gaske yana fad'in" You Trader.....  Alk'ali ya buga benchi cikeda b'acin rai..  Barr Hafiz ya tare Labib yana fad'in" Don't touch my client... Barr Munir kuwa rik'e Labib ya soma yi yana bawa Alk'ali hak'uri.

  "Alk'ali yace " Barr Anka tell your client to behave himself this is a court...

  "Fusfuzgewa Labib yake yana fad'in" He's lying your Honor...  Silent......  Alk'ali ya kuma fad'i kafin ya dubi Jalal yace " Go ahead.

   "Jalal yaci gaba da fad'in" I was drunk your Honor that I couldn't stop them,  Labib started it then Salim then Tariq....  Hawaye ya ciko idanunsa sanda yaci gaba da fad'in" Na koma wajen da safe ban sameta ba,  saidaga baya na sameta a asibiti tareda Mahaifiyata da kuma matar yayanta,  The Dasuki's threaten her that they will kill her family muddin tayi magana,  snn nima sunyi threatening d'ina cewa zasu kashe Mahaifiyata muddin na bari maganar ta fito fili,  All I wanted your Honor is to protect Zubaidah sabida tana cikin damuwar da takai tana yunk'urin kashe kanta I thought of marrying her to keep her safe from harming her self and also from the Dasukis, a zatona na aureta ne out of pity but I realized it wasn't out of pity it was out of love,  ...... I love her....  Ya fad'i yana dubanta wanda itama shi d'in take duba...
  Saida ya d'an d'au lokaci kafin yaci gaba da fad'in, "Su da kansu suka so na aureta sabida asirin 'ya'yansu ya rufu.But they never leave us alone as they promised to.... Ya d'anja fasli kafin yaci gaba da fad'in It wasn't a happy marriage from the beginning although we started to get to know each other all of a recent , amma rad'ad'in abun na tare da ita,  na gane pain d'in bazai rabu da ita ba har sai an karb'a mata hakkinta,  that's why I went straight to the police and confessed cos that is the only way for her to let go of her agony, ya k'arashe maganar yana kallonta...

  "Alk'ali yayi rubutu mai d'aukan rahoto ma na kanyi.

  "D'agowa yayi yana duban Jalal kafin yace " According to your statement,  kace " Ka sameta a asibiti tareda Mahaifiyarka da matar yayanta idan suna cikin kotun nan,  kotu na buk'atar ganinsu a gabanta..

  "Babu musu suka mimmik'e, Hadiza sai rarraba ido take kana ganinta kaga maras gaskiya.

   "Da Annah aka soma,  Alk'ali yace Kinyi rantsuwa zaki gaya wa kotu iyakar gaskiyan ki...

  "Annah ta gyad'a Kai tace " Eh Ya Mai Shari'a

  "Mai Shari'a yayi rubutu kafin ya soma jefo mata tambaya kaman haka.

" Relationship to the Victim?

  "Annah tace " She's my in-law,  my Son's wife..

   "Alk'ali yayi rubutu kafin ya kuma cewa " Matar  d'anki, D'anki kamar yaya, Adopted Son,  ko kuwa guide son ko real biological Son d'inki ne...????


    "Gaban Annah ya yanke ya fad'i tunda take babu wanda ya tab'a mata irin wann tambayar,  Kotu yayi tsit ita ake saurare yayinda k'irjinta yaci gaba da lugude tunowa da tayi tayi ranstuwa idan an tambayeta gaskiya zata fad'i,  shin ta shirya fad'a wa Jalal gaskiya......  Muryan Alkali ne ya katseta sanda yake fad'in" Ke muke sauraro Malama Maryam...

   "Juyowa tayi tana kallon Jalal wanda shima ita yake kallo fuskar sa cike da shakku da tarin mamaki...  Annah tana kallonsa hawaye na gangaro mata tace " D'ana ne dana rainesa amma bani na haifesa ba....

  "Gaba d'aya mutanen dake wajen Sun zama shocked harta Zubaidah da take cikin tashin hankalin ganin fuskokin mak'yanta...  Jalal kam tamkar dutse haka ya koma a wajen ya kasa fahimtar komai...

   "Annah taci gaba da bada labarin yanda ta tsinci Zubaidah har zuwa aurensu da Jalal...

   "Mai Shari'a ya gama rubuce shaidar ta kafin ya buk'aci witness na gaba wato Hadiza,  itama irin tambayoyin da akayi ma Annah aka mata ta amsa komai saidai bata fad'a alak'arsu ta makirci dake tsakaninta da Dasukis ba,  harta Hamma saida tambayoyi ta k'araso kansa.


    "Witness na k'arshe Kausar ce yanda ta bada nata shaidan iyakacin abunda ta sani da kuma b'acewar engagement ring d'in Salim a daren bikin baikonsu, ta k'arashe bada testimony d'inta tana watsa wa Salim mugun kallo.

    "Rubutu ya kumayi kafin ya jefo wa Labib tambaya.

   "Labib Dasuki kaji acquisition d'in da Malama Zubaidah take akan ka,  shin ka amsa laifinka...??

   "Girgiza kai Labib yayi kana yace " No your Honor ban amsa ba, I'm not guilty.....

    "Mik'ewa Zubaidah tayi tana kuka take fad'in" Ka fad'a ma kotu gaskiya you liar.... Order.......  Alk'ali ya fad'i gamida buga benchi.....  Bata bar kuka tana fad'in Labib ya fad'i gaskiya ba....  Gaba d'aya ta zama out of control, Jalal kam gaba d'aya bai ma gane me ake ciki ba,  Alk'ali ya buk'aci a fitar da Zubaidah kafin shari'a taci gaba,  Annah ce ta kamata ta fice da ita har lokacin bata daina kuka ba tana fad'in k'arya suke,  da sauri Barr Ansar ya d'au excuse yabi bayansu..  
    "Barr Ansar yace da Annah is better idan suka zauna a wani parlor he can take care of everything, daga haka ya koma cikin zauren gudunar da shari'a..


   "Shari'a taci gaba.....

"Alk'ali yaci gaba da fad'in" Kotu tana saurarenka Malam Labib kayi bayanin abunda ka sani game da zargin da ake maka,  iyaka gaskiyanka..

    "Labib yayi gyaran murya ya soma karanto k'aryar da Barr Munir ya karanta masu su fad'i a kotu kamar haka.
  "Ya mai Shari'a Jalal ya kasance abokinmu wanda ba'a rabamu gaba d'ayanmu mu duka hud'u,  A ranar da muka isa garin Dukku don gudanar da bikin sakun ranar d'an uwana kuma abokinmu Salim,  Jalal ya fad'a mana yaga wata yarinyar da ta tafi da tunaninsa ma'ana yaga yarinyar da yake so,  mukayita jan kunnensa kar ya yaudareta kaman yanda ya saba yaudaran 'yammata wayayyu a nan Abuja,  a daren engagement d'in Salim Ya nuna mana yarinyar sabida mu bamusanta ba sai ranar,  Ashe tana d'aya daga cikin ma'aikatan da akayi hiring nasu,  so bamusan yaya akayi ba don dukanmu bamu kwana a gida ba,  mun kwana ne a gidansu abokinmu Tariq Maina,  babu yanda bamuyi ba Jalal yazo mu tafi gidansu Tariq yaqi zuwa yace " He needs to take care of something tonight,  we didn't force him to come with us,  muka k'yalesa mukayi tafiyarmu,  da safe Jalal yazo mana crying yana fad'in" I forced her slept with me, this is all I know your honor,  daga baya family d'inta suka k'i amincewa sabida akwai baikon wani akanta, Jalal ya roki uncle d'ina ya nema masa auren yarinyar don asirinsu ya rufu kar su zama abin kwatance a gari.  My uncle did as they wanted,  all of a sudden mugaji wann sharri da suka k'ulla mana babu gaira babu dalili.....

  "Barr Ansar girgiza kai kawai yake sanda ya buk'aci kotu ta basa dama yayi ma Labib wasu tambayoyi,  kotu ta basa dama,  haka ya ringa jefo tambayoyi masu rikitarwa wa Labib Barr Munir na karesa,  ... Bayan an gama da Labib ne Alk'ali yayi ma Salim same tambayan da yayi wa Labib.
  "Shima yayi denying ya bada irin statement d'in da d'an uwansa Labib ya bada....

   "Barr Munir ya k'arasa gaban kotu kana yace " Ya mai shari'a ina buk'atan kotu ta bani daman gudanar da shaidun da zasu tabbatar cewa lallai k'age da sharri akayi wa Clients d'ina,..  Kotu ta baka dama Barr Anka..

   "Na gode ya mai sharia ya fad'i sanda ya gabatar da Umar a gaban kotu...

  "Kotu tana son sanin sunan Malamin ya fadi yana duban Umar,  Umar yace sunan Umar Sanda,  Barr Munir ya gyad'a kai kafin yace " Ko menene alak'arka da wacce take k'ara.

   "Ni Ex Fiancee d'inta ne wanda akwai baikona akanta kafin ta auri Jalal,..

    "Barr ya gyad'a kai kafin yace " Ko meyasa baka aureta ba.

  "Dalilin da yasa ban aureta ba shine labari ya gama yad'a gari cewa ta bada kanta ma wani d'an me kud'i snn ta bisu sun tafi tare,  don lokacin da na dawo ban taarar da familynta ba gaba d'aya sun tafi...

   "Barr ya gyad'a Kai kana yace " Mun gode Malam Umar,  Ya juyo yana dyvan Mai Shari'a kafin yace " Ya Mai sharia wann bawan Allah tsohon saurayin Zubaidah ne wanda ada yake shirin aurenta kafin taci amanarsa ta bada kanta ma wani ta gudu ta k'yalesa, da wann hujja nake son wann Kotu Mai Alfarma ta dubi irin cin zarafin da akayi ma Babban Family responsible mutane a k'asar nan irin Dasuki Family tayi watsi da wann sharia Mara's asali balle tushe,  Na gode ya Mai shari'a...

   "Rubutu Mai sharia yayi kafin yace " Ko lawyern wanda take k'ara yanada tambayan da zzaiyi ma tsohon saurayin wacce take k'ara.

   "Barr Ansar ya mik'e yace k'warai Ya mai sharia inaso kotu ta bani dama, 

  "Kotu ta baka dama Barr Kumo. Alkali yace..

  "Na gode Ya Mai sharia Barr Kumo yace kafin ya k'arasa gaban Umar yace " Malam Umar ko meyasa da ka dawo daga tafiyarka baka bincike asalin abunda ya faru da Zubaidah ba ka bi maganganun mutanen gari,  shin anya kasan hukuncin kafa hujja da zargi a Sharia....


   "Zare ido Umar Ya farayi ya rasa me zaice ya soma 'yan kame kame... " Eh Ba zargi nake ba iyayena dasuke mak'ota dasu sun tabbatar da haka.

    "Toh meyasa da kace kaji a bakin mutanen gari......  OBJECTION MY LORD... Barr Munir yace kafin ya k'arada,  Ya kamata Lawyern wanda take k'ara ya gane cewa Umar yazo nan ne bada shaidan iyakan abunda ya sani ba yazo ne don a tuhumesa ba...

  "Alk'ali yace korafi ya karbu Barr Kumo ka gyara Kalman ka..


     "Gyada kansa yayi kafin yace " Na gode your Honor...  Tambayoyi yaci gaba dayi ma Umar wanda harta Alh Kasim saida zufa ta karyo masa,  shakka babu suna da aiki ja a gabansu..

     "Bayan Shaidan Umar Barr Munir ya kuma gabatar da shaida na gaba Zulaihat,Yanda itama t bada nata statement d'in lokacin da Zubaidah ta gudu gidanta....

   "Daga k'arshe Barr Munir ya kuma nuna engagement ring d'in Salim Alk'ali ya buk'aci ganin na Kausar tabbas iri guda ne babu aunda ya banbanta....


  "Alk'ali ya bukaci ganin Likitan da yayi treating nata a asibiti in the forthcoming trial snn aka d'aga k'ara har zuwa nan da 2 ga watar October a lokacin Tariq Maina ya sami lafiya snn za'a ci gaba da tsare wa'enda ake k'ara a gida tasku har na tsawon watanni biyu lokacin da za'a gudanar da sharia na gaba...

   "Snn Kotu tabada belin Jalal for he is only trying to save and protect the Victim amma hakan ba yana nufin ya wanku daga confession d'in da yayi bane....



    "Barr Ansar da Barr Hafiz suka rungume juna...




   " Salim fad'i yake Daddy uncle pls do something I can't stay there for two months,  Labib kuwa sai huci yake yana hararan Jalal dake Zaune a wajen kaman wanda aka dasa,  har saida Ansar ya kamasa suka fito,  tsaye ya hangi Annah da Zubaidah..  Annah kanta a k'asa don bata san ta yaya zata soma fuskantar sa ba...

Kallonsu kawai yake babu ko kyafta idanu sai jijiyoyinsa da gashin jikinsa da suka mimmik'e.....



Download Zubaidah Littafi Na Daya Complete HausaNovel