*PAGE 2⃣6⃣*
Asuban fari alarm na Afzal yayi ringing, bayan ya kashe ya kunna bedside lamp ya kewayo yana kallon Nazeefah dake ta bacci a hannunsa cikin kwanciyan hankali. Peck yayi placing mata a goshi had'e da furta "Allah sassauta miki wannan kishi Rabba'atul Bait, I love you" cike da dabara ya rabata daga jikinsa ya sauk'a daga kan gadon ya nufi bayi. Bayan ya fito yayi shirin zuwa masallaci sannan ya shiga tayar da ita.
"Ta shi kiyi sallah zan wuce masallaci" yana tabbatar da ta tashi ya fice.
Dawowansa ya tarar Nazeefah bata d'akin dama yasan za ayi hakan. Kwanciya yayi kan gadon ya koma bacci kasancewar yau Asabar ne ba aiki. Se wajajen goma sha d'aya ya tashi bayan yayi wanka ya d'au wayansa ya fice parlour inda ya tarar da Nazeefah zaune kan kujera tana faman latsa wayanta. K'amshin turarensa ne ya buga mata hanci, ba shiri ta d'ago kai tana kallonsa ba k'arya yayi kyau ina irin morning shower glow d'innan? Se wani k'yalli fatan jikinsa yake k'ark'ashin ranan dake haskowa ta window. Daga bisani ta kawar da kanta badan wai kallon sa ya isheta ba se don haushinsa da take ji.
"Rabba'atul bait yau ba gaisuwa?" Ya tambayeta yayin da yake takowa zuwa inda take. Shiru ta mai ko kallonsa bata sake d'aga kai tayi ba. "Good morning Babe" ya gaisheta had'e da sauk'e mata light kiss a gefen baki. Hannu tasa ta dirje cike da takaici wanda ya mugun basa dariya amma ya dake tare da yin tari dan korar da dariyan.
"Islamiyya fa yau bazaki je ba?" Shide a dole seya sata magana.
"Mallam kana damuna da surutu please."
"Rabba'atul Bait please kiyi hak'uri haka nan" ya fad'a had'e da zama a gefenta "Nasan nayi miki ba dai-dai ba and I'm sorry bazan gaji da baki hak'uri ba but please kar ki 6ata tsakanin mu saboda Amal."
"Seka fasa aurenta tunda baka son tsakanin mu ya 6aci as simple as that."
"Tayaya kike tsammanin zan iya fasa aurenta bayan an riga an gama komai, mey kikeson incewa iyayenta bayan nan duk hidiman da Abba da Ummi suka yimin ya tafi a iska kenan?"
"I don't care, kade sani zaman lafiyanka da na ita karuwar taka yayi depending akan hakan."
"Subhanallahi! ki daina kwatanta Amal da karuwa Nazeefah tunda bata yi miki komai ba kuma baki ta6a ganinta tana wani alfashan ba."
"Bata yi mun komai ba?" Ta tambayesa yayinda take k'yalk'yalewa da dariya. "Bata yi mun komai ba fa kace? Tana shirin k'wace mun miji ka ce bata mun komai ba?"
"Amal bata da shirin yin hakan Nazeefah, wannan abu da kikeyi shi ze sa in nisantar da kaina daga gareki please cut it out."
"Oh really? So what do you expect me to do then? To fold my arms? K'ara aure fa kake shirin yi, kuma se three weeks to auren kake sanar dani how do you expect me to act? Ince Allah sanya alkhairi?"
"Hak'urin nan dey shi zan cigaba da baki I know am at fault but abinda kike yin nan kuma ba shi ze hanani fasa auren nan ba kisani fa kaman yadda nake son kasancewa dake haka nakeson kasancewa da Amal, nasan da zafi amma idan kika hak'ura komi mey wucewa ne Nazeefah, I'm never leaving your side and as far as am concerned kece Rabba'atul Bait d'ina not Amal."
"K'aryar banza kawai" tayi maganan had'e da mik'ewa "Ni zan fita ina iya kai yamma kumma kafin in dawo kuma."
"Breakfast d'ina fa?"
"Ban girka ba kana iya samun karuwar taka aww sorry amaryar taka ta girka maka" bata kai da jin abinda zece ba ta wuce d'akinta. Nan da nan ta fito sanye da hijabi shide Afzal bece mata komai ba banda binta da ido da yayi. Gabad'aya ya rasa mey ke masa dad'i Nazeefah isn't at all ready to understand him, anya kuwa ze iya da wannan bala'in da yake neman afka masa?
Gidansu aminiyarta Rumaysa ta taje inda take bata labarin abinda ya faru.
"Kar ki gaya mun Babe!" Tayi exclaiming.
"Wallahil azeem aure Ya Afzal ze sake yi, ga chan akwatunan fad'an kishiyansa ko kallonsu ma banyi ba."
"Chab! Amma shiko meyayi zafi da ze k'ara aure? Kode kun samu matsala ne?"
"Wallahi lafiya k'alau Babe ni daya sanar dani ma na kasa yarda I can't believe for all these while he's been deceiving me."
"Ai na miji bashida guarantee komin dad'in ki dashi idan be ci miki amana ba baya jin dad'i yanzu ya zakiyi?"
"Wallahi ban sani ba jiya ina gidan Suwy nake tambayarta mafita tace wai mafitar d'ayace."
"Wai meh?"
"Malaman tsubu."
"Boka de!" Rumaysa tayi exclaiming.
"Hmm ai nima nace ba dani ba a iya fahimtan addinin da nayi Allah na yafe ko wani irin zunubi amma banda shirka har mey yayi zafi akan wata shegiya in jefa kaina ga halaka."
"Gaskiya kam wannan shawara batayi ba amma shin wacece yarinyar wai?"
"Ina ko zan sani yanzu haka wata banza ce."
"Kode ze iya yuwawa yarinyan nan da muka gansu tare ranan a Unimaid garden ne?"
"Waya san masa ne da uban kwashe-kwashen nan nasa."
"Tsaya ya yarinyar take? Kin ta6a ganinta ko a hoto?"
"Eh kuma kinsan mey? Allah ba jiya na fara sata a ido ba tabbas nasan na wayi fuskan nata a wani wajen amma na kasa tunawa."
"Ke ze iya yuwuwa a school ne tunda chan take itama."
"I doubt a school ne, a de wani wajen muka had'u da ita omg! Wallahi na tuna tabbas itace wacce mukayi clashing da ita a asibiti lokacin da Ya Afzal ba shi da lafiya, Wallahi itace. Itace wacce Sultan yake tambaya ta ko naga ficewarta kutuma amma an jima ana raina mun wayo!" Tayi exclaiming.
"Lalle kam ashe har zuwa dubansa tana yi a asibiti."
"Gashi kuwa am very sure flasks d'incan ma da Ya Afzal yace wai na Umman Sultan ne na yarinyar nan ne wallahi Ya Afzal babban mak'aryaci ne."
"Ke ba Afzal naki kad'ai ba fa duk maza mak'aryatan kansu ne wallahi sede kawai k'aryan wani yafi na wani, mutanen nan basuda amana ko kad'an imagine yana gadon asibiti rai a hannun Allah amma still yana cin amanarki, tirrr wallahi."
"Ai shiyasa bazan bari auren nan ya yuwu ba, dole ne in hana aukuwan auren nan."
"Aikam kada ki yarda wallahi ba da keba kishi da 'yar shuwa."
"Aww shuwa ce?"
"Sosai ma bakiga kalan halittarta bane? Shuwa ce kawai ba tayi hasken su sosai bane."
"Shegiya sena tabbata na lahira ya fita jin dad'i ai."
"Yanzu ya zakiyi? Lokaci ya riga ya k'ure miki."
"A'a kam wallahi da saura."
"Kefa kikace sati uku ya rage, how??"
"Wallahi ban sani ba one thing am sure of is aure de komin yaya ne baza a d'aura ba."
"Tsaya tukuna ki kwantar da hankalinki ai ba haka akeyi ba, an dena tada hankali yanzu idan miji ze k'ara aure."
"Ban fahince kiba so kike kice in nad'e hannu kaman sokuwa in zuba masa ido ya k'aro auren nan?"
"Nahhh ba haka nake nufi ba yanzu ya tsakaninki da Afzal d'in?"
"Oho mishi ni tun jiya ban sake yi ta kansa ba, yana ta lalashina yana bani hak'uri amma nak'i hakan. Yanzu haka sau biyu nake girki amma banyi da shi kwanciya ma ba a d'akinsa na kwana ba seda nayi bacci ya cicci6eni ya kaini d'akin nasa muka kwanta, da asuba da na tashi na sake komawa d'akina ba wai shi mata biyu yake so ba ze gani sena d'aga masa hankali ya rasa meke masa dad'i."
"Lmao kai amma Nazeefah bakida dama" ta fad'a tana dariya. "Wanga gashi haka? Karfa ya k'one."
"Ki barshi mana, a jiyan ma ai ya neme ni na hana sa kaina na fake da cewa ina haila."
"Innalillahi! Wallah baki da dama" ta fad'a tana ta faman dariya.
"Allah bakisan yadda zuciyata ke tafasa bane Rumy, da Ya Afzal ya k'ara aure Allah gara na rasa kwalin degree d'ina."
"Kai de don Allah!"
"Wallahi am damn serious, ke bazaki gane irin son da nake yi mishi bane, akanshi fa ina iya yin komi shirka da kisa ne kawai bazan yi ba wallahi."
"Calm down calm down duk beyi zafi haka ba kinsan mey nakeso da kene?"
"Sekin fad'a."
"Pretend like everything is cool kar ki nuna masa auran nan ya dameki in fact ina son idan kin koma gida yanzu kije ki basa hak'uri kiyi tuban muzuru kice kin amince ya k'ara auren."
"A dalilin mey?!" Nazeefah ta katse ta cike da rashin hak'uri.
"Ke matsalata dake gajan hak'uri ki tsaya mana ki saurareni."
"Ina jinki."
"Yauwa kinga by doing so zey amince dake kuma ze yarda dake."
"Kaman ya kenan?"
"Ina nufin zakiyi earning trust nasa ko wani irin 6atancin aka zo aka fad'a akanki da wuya ya yarda koda kuwa maganan daga bakin mahaifiyarsa ce saboda ke kin riga kin nuna masa kin rungumi k'addarar ki a shirye kike da kuyi zaman lafiya da 'yar uwarki. Da fari yanzu zamu bayyana kan mu a dinan auran nasu ne kice masa zaki je don ki tayasu murna, kinga kowa ya ganki seya jinjina miki harta iyayen nata anan kuma se mu samu mu rugurguza musu komai. Babban aikin namu kuma seta shigo gidan, aya zamu gasa mata a hannu, mun ringa had'a kanta dana Afzal d'in kenan ta yadda koda ta fara kai k'aranki gunsa baze saurareta ba sabida ya riga ya amince dake, ya yarda dake, a hankali har k'orafin da take yi masa a kanki ze soma ishansa tunda de ke gashi baki ta6a furta kalman 6atanci akanta ba hasali ma idan kuka zauna da shi yabata kike kinga anan ze fara ganin kaman ita Amal d'in munafika ce tana son ta shiga tsakaninku ne ta fiddaki daga gidan ki. Toh fa anan hankalinsa ze soma karkatowa kanki ita ko idan tayi sake mutuwan auran nata kenan."
"Wow wannan shawara tayi, amma ai ni auren ne gabad'aya bana son a d'aura Rumy, bani ma son ta shigo gidan bale ta samu d'uwawun zama."
"Kema kinsan hakan ba me yuwu bane se de idan zaki d'au shawaran Suwy wanda bazan barki ki d'auka ba."
"Yanzu haka ina ji ina gani kenan zan fara sharing Ya Afzal da wata shegiya ina raba kwanciya da ita?"
"Karki damu zamu ci mata uwa idan ta shigo gidan, da k'afan da ta shigo dasu zata fita trust me."
"Promise you'll not fail me babe."
"Haba har yaushe na ta6a baki kunya I've got you."
"I know I will always count on you thank you so much."
"Karki damu kede kawai ki kwantar da hankalinki wallahi kishiya tayi kad'an ta d'agawa mutum hankali. Kuma kinga ke Allah ma ya taimakeki Afzal nada kirki wallahi wasu mazajen idan suka kusa yin aure wulak'anta uwar gidansu suke amma kiga ke fa har wani tattalinki yake kina mai iskaro."
"Ai yasan abinda yayi be dace bane shiyasa."
"Even still Babe ajinki maza suna da kunya ne? Wallahi dan wata shegiya achan karki 6ata tsakaninki da mijinki nifa idan nine ke wani irin mahaukacin soyayya ma zan fara nuna wa Afzal d'in yanzu, kin gane ai ki haukatar da shi da soyayyarki yadda ko 'yar shuwan chan bata isa ta d'auke mishi hankali ba."
"Kai da wuya fah, kinsan shuwan nan da concussion nasu da iya asirce miji."
"Yafi kayan mata ne, ai da kayan mata suka dogara su ma, dan haka kema zamu nemo miki akwai wata k'awar Mummy tana had'a kayan matan nan kuma bakiga yadda ake saya ba."
"Kai Babe!"
"Ina gaya miki, relax kar ki wani tada hankalinki mugun trap zamu shirya wa 'yar shuwan chan seta gwammace kid'a da karatu."
"Shiyasa nake yinki sosai wallahi har naji hankalina ya d'an kwanta."
"Ai ya kwanta ma gabad'aya, keda Afzal mutu ka raba wallahi takalmin kaza."
****
Bayan sun idar da sallan Azahar Nazeefah ta d'au Rumaisa a mota sukayi gidan k'awar Mummy suka sai mata masu tsadan cikin kayakin, bayan matar tayi mata bayanin yadda za'ayi amfani da su suka sake komowa gidansu Rumaysan ba ita ta koma gidanta ba se wajajen biyar da rabi. Shiganta parlour taci karo da Afzal zaune kan kujera yana aiki akan laptop nasa. Jakan nata ta rik'e da kyau gudun kar ya zame asirinta ya tonu. Gyaran murya tayi had'e da yin sallama. A hankali ya d'ago kansa tare da amsawa sannan yayi mata sannu da zuwa.
A ranta sam bata da niyyar amsawa amma dan dole tayi in order to keep up with the act.
"Kin dawo?" Ya tambayeta yana neman ajiye laptop nasan.
"Eh" ta amsa.
"Your food is ready then" da mamaki ta tsaya kallonsa "Girki kayi?" Ta tambaya.
"Yes spaghetti."
"Wow!" ta numfasa ai ita ta d'au idan ta dawo gida wani fad'an zasu 6arke da ita. Shin wai shi Afzal d'innan wani irin mutum ne? Ko yayi fushi ma ta fita tun safe amma se yanzu take dawowa? Fa duk yadda takeson ta tsanesa hakan ya gagara sema reasons da zesa ta k'ara sonsa yake bata. "Taho muje in had'a miki ruwa ki watsa se muci abinci ko?" Yayi maganan yana k'arisowa inda take.
"Ni a k'oshe nake."
"Ba za kici girkin Ya Rouhin ki ba? Kar kiyi mun haka please" yayi maganan had'e rik'o hannunta cikin nasa. "Let's eat kinji?" Kai ta gyad'a a hankali sannan suka k'arisa d'akin. Bayan ya sirka mata ruwan ya d'auko mata towel ya barta ta cire kayan nata ma yak'i wai sam shi ze cire mata. Haka har bayin ya kaita sannan ya fito bayan ta watsa ruwa ta yi alwala ta fito, wani dogon rigan daya ware mata a gefe ta sanya ta feffeshe jikinta da turare sannan suka fito dining inda yayi serving nasu abincin sukaci. She can say he's very good at cooking saboda ba k'arya abincin yayi dad'i. Sosai take son ce masa girkin yayi dad'i amma tuna yana da niyyan kawo mata kishiya seta fasa. Shi da kansa ya tattare plates d'in bayan sun gama sannan ya ja kujera ya zauna agefenta tare da had'a hannunsu gu d'aya yana shafawa a hankali.
"Nazeefah I'm sorry kinji? Nasan na miki ba dai-dai ba kamata yayi tun kafin asa rana in sanar dake batun Amal amma son zuciya ya hanani I just want you to know that bawai nayi hakan dan inyi hurting naki bane I just couldn't muster the courage to tell you, I respect you alot Nazeefah gani nake idan na sanar dake ranki ze 6aci ni kuma gudun hakan nake, bana son abinda ze 6ata min ke but I'm sorry if my actions ended up hurting you, I'm so sorry kinji?"
"It's okay Ya Rouhi ka dena bani hak'uri haka."
"Eh??" Ya tambayeta cike da k'in gaskata abinda kunnensa suka jiye masa.
"I should be the one who's sorry, forgive me kaji?"
"You have nothing to be sorry for Rabba'atul Bait, na fahimci halin da kike ciki and na sani kishi dole ne hak'uri kawai nake son ki k'ara akan wanda kikeyi."
"Ba komai ya wuce."
"Kin amince in k'ara auren?" Kai ta gyad'a masa a hankali, janyota yayi ya azata kan cinyarsa ba. "Like forreal? Kin amince?" Nan ma kan ta kuma gyad'awa. Besan lokacinda ya had'e lips nasu gu d'aya ya shiga kissing nata ba, bata 6ata lokaci ba ta shiga mayar masa da martani sun d'au lokaci suna abu d'aya sannan a hankali yayi breaking kiss d'in had'e da rik'o fuskanta "I love you Babe, Allah miki albarka."
"Ameen Ya Rouhi I love you too." Wani kiss d'in ya sake sauk'e mata a goshi "Thank you so much da wannan had'in kan da kika bani, bazan ta6a mancewa da hakan ba Nazeefah and I want you to put you trust in me kisani zanyi iya k'ok'arina don ganin nayi adalci tsakaninki da Amal you have my words." Hannunta ta d'aga ta zagayesu a wuyansa had'e da sauk'e masa kiss a gefen lips nasa "I trust you Ya Rouhi, I believe in you ka dena damuwa kaji?" A hankali ya zagey nasa hannun a kunkuminta yana me sake matso da ita kusa da shi.
"Thanks Babe."
"So tell me a ina kuka had'u da Amal d'in?"
"Tun kafin muyi aure muke tare da ita."
"So she was your first love."
"I'm sorry but yes she is."
"Wow toh meyasa baka aureta ba tun farkon?"
"Relationship namu wasn't a love at first sight thing, daga baya ne nayi developing feelings mata and I had to marry you saboda inyi biyayya wa Abba kaman yadda kema kika aureni don yin biyayya wa Daddy ko ba haka ba?"
"Hakane kam so tell me about her, inda hali inason jin komi akanta."
"Ask me anything."
"Like her age, school, family'nsu da komai."
"Itama yarinya ce kaman ki sai dai zata girme ki da shekara d'aya zuwa biyu haka, sannan tana attending unimaid itama."
"Haba wani department?"
"Nursing tana part three."
"Wow kace mun samu likita a gida kenan so waye mahaifinta?"
"Ba wata 'yar babban gida bace, mahaifinta ma ya rasu agun kakanta take."
"Allah sarki wace yare ce toh?"
"Shuwa ce."
"Shuwa?" Ta nanata sekace bata sani ba "Ya Rouhi yanzu da shuwa kakeson ka had'ani kishi? Ni na ma yi surrender, ai kaima kasan ban isa inyi kishi da 'yar shuwa ba."
"Inji waye? Da mey ta fiki ai yadda kike da kyau itama hakan ne."
"Ba wani ta fini kyau."
"Amma ai kin fita hasken fata."
"Bawani ai naga hotonta a wayan ka itama fara ce."
"Even still kin fita, kyau kuma dukan ku kyawawa ne."
"Hmm Allah de baka ikon yin adalci a tsakaninmu Ya Rouhi."
"Se inda k'arfi na ya k'are in shaa Allah Nazeefah shiyasa nake son ki kwantar da hankalinki kisani kece babba a gidan nan, it doesn't matter Amal ta girmeki as far as we all are concerned kece Rabba'atul Bait ba kuma wanda ya isa ya k'wace martaban hakan daga gareki ba."
"Bawani nasan tana shigowa ka d'anata zaka mance dani tunda gashi Allah yayi sabuwa dal take a leda."
"Ai kema a sabuwanki na sameki Nazeefah I'll do my best to love you both equally."
"Toh Allah ya baka iko."
"Ameen abinda nake son ji kenan taho muje ki duba kayakin naki."
"Ni bana so."
"Why? Kayan basu miki ba a dad'o wasu?"
"Sekuma in kaisu ina? Ai ahakan ma sunyi yawa kaya sekace nice amaryar."
"Just to tell you how much I love you."
"Thank you Ya Rouhi."
"Always babe, taho muje ki duba toh kin ko san zannuwa iri d'aya Ummi ta sai miki keda 'yar uwarki?"
"Allah sarki Ummi, Allah kad'ai ze iya biyanta." Da haka suka nufi d'akin nata inda ya jera mata akwatunan. Sosai tasha mamakin adadin kayakin da suke ciki tamkar itace amaryar. Bayan sun gama dubawa suka shiga shirin sallan maghrib. Haka nan tun daga ranan ba a sake jin kan Nazeefah da Afzal ba, shawarar k'awarta ta d'auka. Wani irin soyayya da kulawa na musamman ta fara nuna wa Afzal fiye da na da. Afzal couldn't ask for more rannan har buk'atansa tayi da ya had'ata waya da Amal su gaisa, ba Afzal kad'ai ba ita kanta Amal taji dad'in sauk'in kai irin na Nazeefah. Lafiya k'alau suka gaisa har ita Nazeefahn takeyi wa Amal fatan alkhairi.
Tsaf Afzal da Nazeefah suka shirya abinsu yau sukaje duban gidan Amal inda Nazeefah ke ta yabawa kayakin d'akin Amal akan sunyi kyau, hakan ba k'aramin burge Afzal yayi ba, yadda Nazeefah ke k'ok'arin 6oye kishinta don ta farinta masa. Be sanar da ita komai ba bayan kwana uku ta dawo daga unguwa kawai ta tarar an sake furnishing mata parlour da exact kalan kujeru da rug na Amal banbancin kawai color ne. Godiya tayita yi masa, ita kam dad'in har yayi mata yawa, tunda ta nunawa Afzal ta amince da auren nan tasamu wani girmamawa na daban daga garesa, kud'i yake bata anyhow ko bata tambaya ba, ga wani tarerayarta da yake yi.
A haka ne har Allah ya kawo satin bikin Afzal da Amal wanda aka fara da walima wanda aka had'a da na sauk'an Al~Qur'anin da tayi, ita tazo na biyu a gwajin da akayi musu. Sosai ta samu kyautuka da dama ciki harda kujeran hajji wanda ta bawa Papi, kaman yadda Abba yayi alk'awari shiko kyautan mota ya bata k'irar Matrix. Bayan walima akayi Kamu washegari wanda Amal ta bala'in yin kyau acikin pitch asoebin ta, ga lallen nan da makeup nata komi ya zauna. Afzal kansa ya kasa daina kallonta through out the event sece mata yake tayi kyau. Washegarin kamu akayi wushe-wushe wanda ta sanya laffayan da Afzal ya sai mata. Ranar Asabar aka d'aura aure akan sadaki dubu d'ari da sisin gold arba'in. Da yammacin ranan dangin ango sukazo suka d'aukan amaryarsu, kukan da Amal taci kam ba a cewa komai da k'yar aka samu aka fiddota daga gidan nasu aka kaita family house nasu Afzal inda aka shiga shiryata for dinner. Achan Nazeefah da k'awarta suka saci idan mutane suka d'auke head na Amal. Bayan an gama kwalliya za a shiga d'aurin kai, d'ankwali yace ku neme ni. Ba duban duniyan da ba'ayi ba amma babu hankalin kowa ya tashi gashi lokaci se k'urewa yake. Cikin masu neman head ana jan Allah ya isa aharda Nazeefah da k'awarta.
Da shirun yayi yawa ne Afzal ya kira Amal don jin ko lafiya.
"Yaya an d'auke mun head d'ina" ta sanar dashi tana kuka.
"Kaman ya an d'auke? Tayaya?"
"I don't know" tana fad'in haka ta katse wayar don yadda kukan yaci k'arfinta. Hawayenta Maamah ta shiga share mata tana bata hak'uri akan in shaa Allah za'a samu. Ummi ya kira next ya tambayeta meke faruwa.
"Wallahi head na Amal aka d'auke."
"Tayaya Ummi? Shin baku ajiye mutum ya kula da kayakin nata bane?"
"An sa wallahi har mata biyu ni kaina ban san yadda hakan ya faru ba."
"Toh yanzu ya za'ayi?"
"Akwai wani bridal head wrap na 'yar k'awata Umaima yanzu haka ta fice taje d'auko mata nata da ta sa a bikinta tace color d'in exactly iri d'aya da na Amal ne."
"Please make sure she looks perfect Ummi and ki bata hak'uri ta daina kukan I love her."
"Karka damu ka kwantar da hankalinka zan kula da komai" da haka sukayi sallama. Bayan 20 minutes Umaima ta iso da bridal head wrap nata sosai kuma ya shiga da kalan kayan Amal kaman yadda ta fad'a. Nan da nan makeup artist ta d'aura mata da ikon Allah kuma d'aurin ya mugun amsan Amal har ma fiye da yadda asalin head natan ze kar6eta, Nazeefah da Rumaysa haushi kaman ya kashesu. Sosai maroon color d'in ya kar6i skin na Amal se hoto ake tayi mata ta ko ina. Nan da nan aka shiga tafiya, motan ango na isowa su Maamah suka k'arisa da Amal ciki. Afzal na iya rantsewa be ta6a ganin kyakkyawan halitta kaman ta ba.
"My bride you look so beautiful" ya sanar da ita.
"Thank you Yaya, you're not looking bad yourself."
"Is everything okay?" Kai ta gyad'a a hankali "I'm just nervous."
"I've got you okay?" Yayi maganan had'e da sauk'e mata light kiss akan hannunta. K'aramar murmushi ta sakar masa ahaka har suka k'arasa wajen da za'ayi event d'in. Nazeefah sarai tasan an hana zuwa da yara ta kikki6i wata cousin nata mey shekara shida taje da ita. Ana cikin presentations progammes of event kafin a k'ariso na cutting cake Nazeefah ta tura cousin natan da taje ta ture table na cake d'in. Ana shagali kawai aka ji k'aran rushewan abu a k'asa, da table da cake d'in duk sun tarwatse. Hankalin kowa ya tashi a wajen barin ma na Amal da Afzal wannan wani irin musiba ce? Nan aka shiga tambayan kowa yashigo da yaro sede ba wanda keda masaniya game da hakan, yarinyar ma k'aramar munafuka ana tambayanta wa ya shigo da ita ta bushe ido wai babu mota kawai ta gani ta shigo. Securities kuwa koda aka tambayesu dalilin da yasa suka bari ta shigo se sukace su basu ga shigewarta ba k'ila tabi cikin manya ta 6ace acikin su kasancewar Nazeefah ta biya su kud'i ta rufe masu baki.
Kuka kawai Amal ta farayi wajen farko head nata aka d'auke yanzu kuma aka tarwatsar mata da wedding cake. Haka aka lalla6a aka kammala event d'in ba walwala tattare da kowa barin ma Ummi data sha aiki don tabbatar da cewa komi ya tafi dai-dai. Se hak'uri Afzal keta bawa Amal cikin motan amma ina ta gagara yin shiru. Ajikinsa ya kwantar da ita har suka isa gidan nasu wanda se wajajen sha d'aya da rabi k'awayen Amal suka watse ya rage Afzal kad'ai da amaryarsa.
Kazan amarcinsu ya shigo dashi d'akin inda take zaune a tsakar gadon kanta a sunkuye se kuka take tayi ta ciki-ciki. Ledan ya bud'e yayi serving nata se anan ya tuna be ibo cups ba, dawowan da zeyi kawai ya tarar da Amal tana kuka shark'af-shark'af. Da hanzari ya nufi kanta yana tambayarta ko lafiya amma ina ko amsasa ta kasa banda kukan nata ma daya tsananta.
"Lily what's wrong? Wani abu ne?" Kansa ne ya mugun d'aurewa kode missing k'awayenta take ya tambayi kansa "Lily please stop crying" hak'uri ya shiga bata saidai ta gagara yin shirun. Daga bisani kawai ta fad'a jikinsa yayin da kukan nata ya tsananta, rungumeta yayi gam a jikinsa yana shafa bayanta yana mey fad'a mata kalamai masu kwantar da hankali. Sun kai tsawon minti talatin a haka, "Lily?" Ya kira sunanta lokacinda yaji tayi lamo a jikinsa. "Lily?" Duba fuskan ta da zeyi ya tarar har bacci ya d'auketa.
A hankali ya d'agata daga jikinsa had'e da mik'ar da ita akan gadon. Wayanta da ya kusan fad'i a k'asa ne yayi sauri ya tare kafin yace ze ajiye idonsa yaci karo da sak'on da ya nuna last Amal ta karanta wanda ya kasance daga unknown number. Har ya ajiye wayan watak ra'ayin tace masa ya karanta, kasancewar wayan nata ba password haka ya basa daman bud'ewa ya shiga karantawa kaman haka
_My dearest Princess, today two souls of yours have turned into one, I want you to know that you two are the most beautiful couple I’ve ever seen. May your love grow stronger and stronger during your married life. May you always be together as one and never split apart no matter the difficulties you may face in your future life._
_Yours Abdul, Xx_ 😘
Har cikin ransa shima yaji ba dad'i tabbas ya shiga tsakanin wannan masoya guda biyu, Allah sarki ashe akan Abdul take wannan kuka. Mayar da wayan yayi ya ajiye sannan ya rage kayan jikinsa ya fad'a bayi ya watsa ruwa. Da towel d'aure a kunkuminsa ya shiga wardrobe na Amal inda ya ciro mata d'aya daga cikin sabin kayakin baccinta. K'arisawa kan gadon yayi ya shiga tada ita sede ina baccin nata yayi nauyi daga k'arshe ya yanke shawaran barinta ta kwana da kayan kawai sede kuma yayi tunanin kayan zeyi nauyi da wuya idan zata ji dad'in bacci aciki. Outerwear d'in ya cire a hankali ya rage fitted gown na cikin, a hankali ya zuge zip d'in har k'asa har anan bata tashi ba cewa da yayi bari ya ja kayan k'asa mutumiyar ku ta tashi a firgice had'e da k'urma wani d'ankaren ihun daya kusa tunzurar da Afzal daga kan gadon.
"Shh! It's me Afzal calm down calm down" ya shiga ce mata a hankali yayinda take ta hak'i tana ja da baya.
"Ba wani abun zan miki ba kayanki nakeson in canza miki gani nayi kaman ya miki nauyi bazaki iya kwanciya da shi ba." Kanta tayi saurin kawarwa ganinsa da tayi ba kaya ajikinsa banda towel dake d'aure a kunkuminsa.
"Lily?" Ya kirata amma shiru tayi gun se neman kare jikinta take tana tattara wuyan rigar nata sama kasancewar ya zuge zip d'in k'asa se k'ok'arin zamewa yake. "Lily?" ya sake kiranta sede tak'i juyowa ta kallesa murmushi ya sakar gano wai kunyan ganin sa ba kaya take mik'ewa yayi ya nufi side nasa acikin wardrobe d'in ya zaro jallabiya d'aya ya sanya "Juyo to nasa kaya" ya sanar da ita bayan ya dawo ya zauna. A hankali ta kewayo da kallonta a garesa "Taho in tayaki cire kayan kisa wannan ko zaki watsa ruwa tukuna?"
Kai ta kad'a a hankali.
"Toh ai ya kamata ki watsa ruwa tunda kin tashi Lily kiyi refreshing kanki you'll feel much better." Nan ma kan ta sake kad'awa "Okay na gane kunya na kikeji ko? Zan fita in baki waje ki shiga kiyi wankan idan kin shirya sekiyi mun magana okay?" Ganin bata da niyyan amsa sa ya mik'e ya fice. A hankali ta janyo wayanta ta shiga sak'on da Abdul ya tura mata had'e da sake karantawa yayinda wani kukan ke neman kauce mata. Typing reply tayi as;
_Thank you so much Ya Abdul, Allah yabar zumunci._ sannan ta ajiye wayan ta mik'e da shakka-shakka ta shiga rage kayan jikinta gudun kar Afzal ya bankad'e k'ofar ya tarar da ita ba riga.
Acikin minti ashirin ta gama duk wani shafe-shafen da zatayi, kayan da Afzal ya d'auko matan ta d'aga tana duba. Yanzu wannan d'an iskan kayan yake tsammanin zata sa? Ai ba maraban wannan da babu komi na jikin mutum gani za ayi. Wardrobe natan ta nufa ta shiga neman wani na daban sede inaa duk kayakin bana kamala a ciki. Yau akeyinta meyasa Ummi za tayi mata hakane? Ko d'an me riga da wando babu se masu net guntaye iya cinya ai kuwa bacci da towel ya kamata. Hijabi ta sanya akan towel d'in ta koma kan gadon ta zauna. Wani d'an banzan yunwa ne ya soma damunta bata san lokacinda ta hau kan kazar data gani k'ulle cikin ledan ba ta shiga ci ana cikin haka Afzal daya ji shiru yace bari ya lek'o, bud'e k'ofan da zeyi suka had'a ido hud'u da Amal. Kunya ta jiyo tamkar ta nitse k'asa, da sauri ta kawar da kanta ta shiga ture ledan gefe. Murmusawa yayi ya k'araso ya zauna kusa da ita. "Ci abinki kinji? Dama naki ne" Juice d'in yaja ya tsiyaye mata a cup tare da tura mata gabanta. A hankali ta shiga ci bayan dan ta gama ta kwankwad'e juice d'in akai.
"Kin k'oshi bazaki k'ara ba?" A hankali ta gyad'a kanta "Thank you" ta furta.
"Don't mention kina buk'atan wani abu?" Yadda kuka san kurma haka ta cigaba da amsa tambayoyinsa da jiki.
"Lets sleep then ko baki fad'a ba nasan a gaje kike." Yana tu6e jallayabiyan nasa Amal ta shiga kare fuskanta oh! Shi kam ya had'u da aiki. Daga chan k'arshen gadon ta ja pillonta ta kwanta, had'e da juya masa baya. Da mamaki ya tsaya kallonta bade da hijabin take shirin kwanciya ba? "Lily?"
"Uhmm?" Ta amsa ba tare da ta juya ta kallesa ba, shi kam wai baya jin kunya ne yake tsayuwa akan gajeren wando zalla a gabanta? Ta tambayi kanta, ita kam kunya ma baze barta ta kallesa ba.
"Da hijabin zaki kwanta?"
"Uhmm" ta amsa. Takowa yayi izuwa gabanta ya zauna nan ta kulle idanta gam. Hannu yasa ya gwada d'aga hijabin nata da mamaki ya tarar da towel k'ark'ashi. Tirk'ashi!
"Lily!" Yayi exclaiming, bud'e idon da zatayi taga yana rik'e da k'asan hijabinta nata da hanzari ta k'wace ta shiga rufe jikinta.
"Wai mey haka? Da towel d'in zaki kwanta?"
"Uhmm" ta amsa.
"Dalili?" Wai har ma dalili yake tambayarta? Shin bega kalan kayan bane ko a haka yake tsammanin zata sa? "Kefa Lily!"
"Yaya baka ga kayan bane" se anan ta bud'e baki ta amsa idanta a rufe har yanzu.
"Meya samesa?" Ya buk'ata.
"Bazan iya sawa ba" ta amsa a takaice. Kayan ya d'ago daga kan side drawer yana kalla, besan lokacin da dariya ya kauce masa ba. "God help me" ya furta a hankali. Anya kuwa ze iya da kunyan nan nata? Yaga irin kayan da Nazeefah ke kwanciya da su kenan wasun ma wannan yafi su kamala.
Ido d'aya ta bud'e tana kallonsa.
"Mey anan d'in da bazaki iya sawa ba Lily? Hungo tashi kisa."
"Ni gaskiya bazan saba kabarni haka kawai I'm good seda safe."
"A ina aka ta6a kwanciya da towel ki tashi kisa mu kwanta bacci nakeji."
"Toh Yaya na hanaka kwanciya ne?"
"So kike muyi fad'a ko?" Yayi maganan had'e da komawa gefenta ya zauna "Ko kisa kokuma in sa miki na k'arfi kinsan ba Mami bale kice zakiyi ihu ta taimakeki."
"A'a Yaya dan Allah kayi hak'uri karka mun haka."
"Toh amsa kisa."
"Yaya bazan iya sawa ba dan Allah kayi hak'uri."
"Fa bazan barki ki kwanta da towel ba."
"Kayi hak'uri zuwa gobe zanje kasuwa in sai kayan baccin masu riga da wando se in fara sawa I promise bazan sake kwanciya da towel ba amma ka barni na yau d'in." Dariya sosai ta basa wai kam da abinda takeyi d'innan idan da kuma cewa yayi su raya first night kaman yadda kowasu ma'auratan keyi fa? Ashe seta tara masa jama'a. Ganin fa bata da shirin sanya kayan kawai ya damk'o hannunta. Wai d'an karen ihu tasa seda ya tsaya toshe kunnensa. Shin wani irin laushi hannun nata keda sekace auduga.
Kuka ta shiga yi yayinda yake k'ok'arin raba ta da hijabin nata.
"Zan sa wallahi zan sa da kaina dan Allah karka cire min hijabin Wallahi towel d'in ya warware kayi hak'uri" nan ma dariya ta basa sosai amma ya bone se kokowan cire hijabin yake. Kuka Amal ke tsakaninta da Allah tana rantsuwa akan ya saketa zata sa da kanta. Seda ya bata wuya sannan ya saketa "That's my Lily sanya toh da hannunki ina kallonki ko zaki shiga bathroom?"
Kai ta gyad'a a kid'me.
"Je ki sanya toh ina jiranki." Batayi musu ba ta mik'e har tana neman cin tuntu6e ta nufi bayin. Hijabin nata ta kwaye ta ajiye a gefe sannan ta d'ago kayan ta shiga neman ta inda zata sa. Chan ta samo wuyar rigar ta sanya, gaban mirror ta tsaya tana kallon kanta surrata kap ba abinda be nuna ba, amma ko se Allah ya d'ibe ma baturen daya d'inka wannan kaya albarka. Yanzu a haka ne Afzal yake son taje ta samesa su kwanta sekace wata sabuwar karuwa? Uhn uhn kam gaskiya baza ayi haka da ita ba. Ina ma ace da brazier a ciki da d'an sauk'i amma haka ba komai gaskiya da sake. Tunanin ya zata fita ta d'auko bra ta sanya ta soma ana cikin haka kawai taji Afzal ya wangale mata k'ofar ba notice. Ashe bata sa key ba, wani irin d'ankaran ihu ta k'urma had'e da juya mai bayanta yayinda ta shiga kare k'irjinta tana kakkarwa.
RANA D'AYA!
#RD
Love... King Miemiebee👄✨
[13/08, 09:34] +234 907 483 8352: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
July, 2018
beeenovels.blogspot.com
_Written by Miemiebee👄_
*PAGE 2⃣7⃣*
Murmusawa ya tsaya yi yayinda yake k'are wa surar jikinta kallo, lallai Allah yayi halitta anan gata 'yar siririya amma fad'i gareta ta k'asa. Na d'an lokaci ya karanci tana da aniyar janye hijabin nata ne dake rataye jikin sink ta sanya, kafin ta aikace hakan yasa hannu ya janye.
Wai meyasa Yaya yake mata haka ne? A hankali take jin footsteps nasa suna dosoto, har6awa zuciyanta ya shiga yi yayinda k'afafunta suka shiga yin kakkarwa na sosai. A dai-dai saitin bayanta ya tsaya, hannu ya aza a kan bayanta a hankali yana tafiya sama, idanunta ta rufe gam yayinda wani irin sparks suka soma bin jikinta. Ji tayi ya tsaya chak se kuma taji yana shafa mata gashin kai, ribbon nata data nannad'e gashinta ajiki taji ya kama yana k'ok'arin sincewa. Kafin tayi wata k'wak'k'warar motsi taji ya since nan gashin nata data nannad'e jiki ya shiga warwaruwa. Da mamaki ya tsaya yana kallon irin tsawon gashin nata, har tsakiyan bayanta ya sauk'a yana lilo lub-lub yana shek'i. Har anan Amal bata juya ta kallesa ba se faman kakkarwa take, a hankali taji ya shiga takawa kuma, idanta ta rufe gam lokacinda ta gansa tsaye a gabanta, k'irjinta ta shiga karewa fiye dana d'azu yayinda takeji kaman tasa kuka dan kunya. Yafi minti d'aya tsaye a gabanta yana kallonta yana mey mamakin how fragile and delicate she is, hannu ya d'aga a hankali ya aza akan kafad'arta yana bin hannunta da wani irin shafa, se mamakin laushin jiki irin nata yake sekace auduga. Na sosai jikin Amal ya d'au wuta da irin abinda yakeyi mata. Ganin bata da niyyan bud'e ido ta kallesa ya kirata cikin sanyayyar murya.
"Lily?" Shiru tamai "Lily k-" katse sa tayi ta hanyan rungumarsa, hannayenta ta zagaye gagam ta rik'esa a jikinta yadda ko kykkyawan motsi baze iyayi ba yayinda ta datse idanunta.
"Goodness Lily" ya kira sunanta yana k'ok'arin raba jikin nasu sede ina ya kasa dan wani irin damk'an da tayi masa.
"Lily I can't even breathe let me go" yadda kuka san da iska yake magana haka ta mayar dashi ta kuma k'i sakin nasa ita a dole bata son ya kalle mata surar jiki kuma hakan ne kawai take ganin mafita. Ganin fa bata da niyyan sakesa ya shiga jasu waje a hankali, k'ank'amewa tayi a jikinsa har suka k'arasa izuwa bakin gadon nasu.
"Toh sakeni haka ki kwanta" nan ma kota motsa. "Lily da ke fa nake magana" ba suratan da beyi ba amma tak'i sakesa wane gum haka ta manne mai ajiki, haka ba yadda ya iya ya shiga sauk'a k'asa da ita har suka juye akan gadon sede tak'i sake sa har yanzun. "Lily yi hak'uri ki sakeni in kashe mana wutan kinji?" nan ma shiru duk kalan suratan da yatayi hakan besa ta sakesa ba haka a tak'ure manne da juna suka kwanta har bacci 6arawo ya d'auketa. Bayan da Afzal ya tabbata baccin nata yayi nauyi ya shiga raba ta daga jikinsa sede ina tak'i barin hakan se faman sake shigewa jikinsa take. Wai acikin baccin ma? Ya tambayi kansa. Haka sukayi baccin wahala ranan barin ma Afzal da ko nishi me kyau baya iya yi.
Asuban fari alarm nasa ya shiga ringing, da ya ce ze motsa dan kashewa se Amal ta sake kankamesa haka alarm d'in ya tayi har izuwa lokacinda ya tayar da ita daga baccin itama.
"Yi hak'uri ki sakeni muyi niyyan sallah kinji?" Dan albarkacin sallah kawai ta sakesa wanda da wuri ta juya mai baya ta shiga kare k'irjinta da pillow murmusawa yayi ya mik'e had'e da mik'ar da k'asusuwansa da suka murmurk'ushe, hijabin nata ya ja daga gefe ya wulla mata "Hungo sa abinki" ya sanar da ita chan ciki-ciki yace, "A hankali zaki sake da ni" bata 6ata lokaci ba ta amsa ta sanya murmushi kawai yayi ya k'arisa bayin bayan ya watsa ruwa yayi alwala ya buk'aceta da ta tashi tayi niyya itama. Yana kallonta ta shige cikin bayin da hijabin nata kafin ta fito har ya shimfid'a musu sallaya ya sanya jallabiyansa shima. Wardrobe nata ta k'arasa ta d'au zani d'aya ta d'aura sannan ya jasu sallan bayan sun idar sun kammala Azhkar nasu ta gaishesa a hankali cikin siririyar muryarta.
"Good morning Yaya."
"Ba suna na ba kenan don haka bazan amsa ba" ya ce mata da mamaki ta d'ago kai tana kallonsa cike da neman k'arin bayani.
"Eh kin jini da kyau ni suna na ba Yaya ba."
"Toh mey sunan naka?"
"Afzal mana."
"Amma ai kasan ba na kiranka da sunan ko?"
"Yes KITTEN."
"Toh ya kakeso inyi?"
"Look for a name and start calling me with it, I'm your husband now not yaya anymore."
"Amma ai duk d'aya ne Yaya."
"Toh ni bana so."
"Toh seka kawo sunan da kakeso."
"Ni zan kawo ko ke zaki nema?"
"A ina zan neman? Allah ban sani ba yi hak'uri ka amsa kaji?"
"Nak'i se an min sabon suna."
"Kayi hak'uri ka amsa na yau d'in zan nemo wani sunan in baka amma ba yanzu ba."
"Se yaushe?"
"Yaya ban sani ba nima."
"Aww baki ma sani ba? Toh shikenan har se idan kin samo mun sabon suna bazan sake amsa gaisuwanki ba."
"Yaya-"
"Shhh na soke sunan chan so good morning my adorable kitten."
"Kitten?" Ta tambayesa had'e da kafa masa fararen idanunta.
"Yes Amal."
"Why Kitten?"
"You wanna know why?" Kai ta gyad'a a hankali.
"Come here sena fad'a miki."
"A'a bar shi kawai."
"Ba wani abin zan miki ba Kitten don't you trust me?"
"I do Yaya."
"Nifa na ce miki suna na ba Yaya ba."
"Toh kayi hak'uri mana ka bari ko zuwa gobe idan nayi tunani ai kaima seda kayi tunani kafin ka samo Kitten d'in."
"Ko kad'an Amal, kallonki zanyi sau d'aya sunaye sama da d'ari su taho min akai because you're just perfect in my every situation." Murmushi ta sakar masa "So matso kinji? Matso in fad'a miki sirrin dake bayan sunan naki."
Kafad'a ta buga "Trust me ba abinda zan miki."
"Dagaske?"
"Wallahi" seda taji ya rantse ta amince, a hankali ta k'arasa kusa dashi hannunsa ya bud'e mata da nufin ta shiga ciki, seda ta kallesa sau d'aya again sannan ta mik'a ta kwantar da kanta a k'irjin nasa, hannayensa ya zagaye a bayanta yana mey sake matso da ita kusa dashi sannan yayi placing mata light kiss a kai yayinda yake perceiving k'amshin turaren dake tashi daga jikinta.
"So kina son kiji meyasa nake ce miki Kitten?" Kai ta gyad'a hankali.
"Kinsan mage (kulya) ba?"
"Uhumm" ta gyad'a kai tana sauraronsa.
"Kina son halittar?"
"Gaskiya ni tsoronsu nake."
"K'ananan su fah?"
"Awwn I love those ones."
"How do they look?"
"Cute and adorable, koda yaushe na ga d'aya sena ji kwad'ayin in d'auka."
"That's exactly how you're to me Amal or even more, you're so cute and adorable, soft, delicate and fragile and anytime I see you kawai se inji ina son in rik'e ki a hannu without letting you go."
"You too HABIB ALBY" ta amsa.
"Iyyehh say it again" kunya sosai taji ta sake lumewa jikinsa tana kare fuskarta.
"Kitten..." k'ok'arin d'agota ya shiga yi daga jikinsa amma ya kasa dan yadda ta k'ank'amesa ba k'aramin burgesa wannan kunyan nata yake ba. "I love you so much My Kitten and wannan kunyan naki, it is the most expensive jewelry you'll ever wear, never change who you're not even for me kinji? I want you to remain true to yourself, be the Amal I've fell in love you okay?"
"Thank you Ya- Habib alby" tayi sauri ta gyara. Light kiss ya sauk'e mata a goshi. "Don't mention Kitten" Haka suka cigaba da zama wajen suna shak'ar k'amshin jikin juna yayinda zuciyoyinsu ke bugu wa juna har bacci yayi awon gaba da su. Wajajen takwas Afzal ya farka d'agata yayi a hankali ya mayar da ita kan gadon had'e da cire mata hijabin nata da kuma zanin da take d'aure dashi ya bar mata kayan baccin nata kad'ai. Haka kawai ya tsinci kansa cikin annashuwa da yake k'arewa surar jikinta kallo. Rungumarta yayi tsam a jikinsa wane mutum na shirin gudu masa da ita, ahaka ne har ya komma bacci.
Wajajen sha d'aya Amal ta tashi a hankali ta shiga bud'e idanunta har ta sauk'esu akan Afzal dake ta shar6an bacci a gefen ta. Mik'ewan da tace zatayi taji hannunsa rik'e da jikinta gam ta6a kanta da tayi kuwa taji ba hijabin ta ba kuma zani har yaushe ya tu6eta bata ji sa ba? Yanzu ya kalla mata jiki kenan? Kallon kanta tayi tana mey jin takaicin hakan. Duk yadda taso fita daga rik'on da yayi mata ta kasa dan haka kawai ta hak'ura. Kai ta d'ago ta shiga kallonsa tana mey k'arewa kyakkyawan halittarsa kalo. Tabbas Yaya kyakkyawa ne ta fad'a a ranta. Silky gashin girarsa dake nan a kwance luf ta tsaya tana kalla daga bisani ta d'aga hannunta a hankali ta aza akai tana shafawa, daga haka ta wuce izuwa dogayen eyelashes nasa da suke nan sekace na mace, daga nan ta koma kan hancinsa se kuma tabi sajen sa haka tayita shafa kowani inchi a fuskansa tana tafiya har ta sauk'o zuwa kan lips nasa da sauri ta cire hannunta gudun kar ta wuce gona da iri. Sekace wacce aljanu suka shigeta kawai taji tana son ta6a lips nasa, a hankali ta mayar da hannunta ta aza a kai, shafawa ta shigayi da zaran ya motsa seta cire hannun nata haka ta cigaba da yi har seda ta farkar da shi. Da sauri ta sauk'e hannunta gudun karya ganta saidai ina tuni ya ganta. Cusa kanta tayi a jikinsa tana neman gun la6ewa yayinda wani irin kunya ya kamata wane ta tone k'asa ta shiga. Shin meya kaita?
Murmushi ya sauk'e ashe de ba mafarki yake ba dagaske ne tun d'azu anata shafa mishi baki. "Kitten good morning" ya fad'a yana sauk'e mata peck cikin gashinta me uban yawa yayinda k'amshin shamponsa ya buga mai ganci. Chan ciki-ciki yaji ta amsa "Good morning Yaya."
"Nak'i in amsa."
"Good morning Habib Alby."
"Masha Allah toh ya kika daina? Actually I was enjoying your touch kitten."
"Nifa ban ta6a ka ba" ta k'aryatasa.
"Nide nasan ba mafarki nake ba" shiru tayi ta bata sake cewa komai ba "Tashi toh let's freshen up and have breakfast." A hankali ta zame daga jikinsa sede yayi sauri ya tareta kafin ta gama fita "Baki fad'a mun mey ma'anan Habib Alby ba Kitten I wanna know."
"Yaya so kake kace baka jin larabci?"
"Eh bana ji tell me" yay mata k'arya so yake yaji fassaran daga bakinta.
"Ban yarda ba."
"Nide tell me."
"It means the love of my heart (abun alfaharin zuciyata)"
"Masha Allah I'm totally in love with the name zaki fara shiga ko sena fito?"
"Kaje seka fito."
"Alright" mik'ewa yayi ya nufi bayin in less than 10 minutes se gashi ya fito d'aure da towel a kunkuminsa kaman yadda ya saba. Idanunsu na had'ewa da Amal dake kallonsa ta shiga kare fuskarta cike da kunya, murmusawa yayi "You're next" ya sanar da ita. Tunanin ya zata fara tafiya acikin d'akin sanye da wannan kaya take, juyawa tayi in search of hijabi ko zaninta sede babu anan kusa Afzal daya gano hakan seya k'arasa ya d'auko mata da kansa. Amsa tayi cike da kunya had'e da yi mai godiya. Hijabin ta sanya ta rik'e towel d'in a hannu sannan ta mik'e ta shiga bayin. Kafin ta fito har Afzal ya shirya tsaf d'akin se k'amshin turaren jikinsa yake, yellow T shirt yasa wanda ya bayyana well defined abs nasa da black three quarter wando sosai yayi kyau barin ma yadda skin nasa ke wani glowing.
"Kallon nan beyi yawa ba Kitten?" Kai tayi saurin kawarwa cike da kunya. "Kode nayi kyau ne?" Kai ta gyad'a masa a hankali "Thank you."
"Youre welcome ta amsa ciki-ciki tana gyara fuskan hijabinta.
"Bara inyi excusing naki ki shirya in kin gama sekiyi mun magana kinji?" Kai ta gyad'a masa, nan ya mik'e ya fice ba k'aramin dad'i taji ba daman tunanin yadda zata fara sa kaya a gaban idonsa take se gashi yace ze bar mata d'akin ma gabad'aya.
Ta fannin Afzal kuwa gano irin tsananin kunyan da take dashi yasa yayi tunanin binta a hankali, baze yi rushing nata ba, a shirye yake da ya jirata har izuwa lokacinda zata fara sakewa dashi, so yake ta koyi sonsa da kanta bawai ya sata na dole ba inde akan Amal ne toh he is willing to wait for forever this's just how much he loves her. Nan da nan ta ciro kayan shafe-shafenta dana k'amshi ta shiga shafawa, light makeup tayi applying daga powder, se jan baki se kajal a ido amma wani irin d'ankaren kyau da tayi, barin ma yadda maroon jan bakin ya amshe shape na lips nata. Wardrobe nata ta nufa ta ciro d'aya daga cikin sabin d'inkunanta ta sanya. Sosai d'inkin ya zauna a jikinta daram, gaban mirron ta koma ta zauna ta shiga taje sumarta. Sauk'an knock taji a bakin k'ofa "Bismillah" tace da mey shi. Afzal taga ya lek'o.
"Zan iya shigowa ko in koma?"
Dariya ya bata dan haka ta murmusa "Kai da gidanka kuma Yaya" gira ya had'e take nan take ta gyara kanta "I mean Habib Alby ka shigo." K'arisawa ciki yayi ya nufi gaban mirron inda take zaune, hannunta yayi saurin rik'owa ganin ta d'au ribbon tana shirin kama gashinta.
"Mey zakiyi?"
"Zan kama kaina ne."
"Meyasa?"
"Haka nakeyi kullum."
"Bana so."
"Eh?" Ta kewayo cike da rashin fahimta tana kallonsa.
"Kibari haka kinfi kyau."
"But Yay- Habib Alby" ta gyara da sauri.
"Trust me kinfi kyau haka" yayi maganan yana amshe ribbon d'in daga hannunta. Comb dake ajiye akan mirron ya d'aga ya shiga taje mata sumar nata ya kwantar mata a baya. "See kinfi kyau haka muddin kina gida bana son kina kama gashin ki barshi haka kinji Kitten?" Kai ta gyad'a masa a hankali. "Muje mu karya ko?" Nan ma kan ta kuma gyad'awa had'e da mik'ewa. "You look beautiful Kitten" ya sanar da ita bayan ta mik'en.
"Thank you Ya- Habib Alby" tayi sauri ta gyara, hannu yasa ya jawo ta jikinsa sannan ya d'ago fuskanta da yatsarsa ta yadda take kallon cikin idanunsa sede da sauri ta sake sauk'ar da idan nata.
"Hold on! Ina aka kaimun gashin girarki da nake mutuwan so d'innan?" Tun d'azun yake kallon fuskanta se gani yake wani iri ashe gashin girarta ne babu.
"Ba makeup artist da ka d'auko d'in bane bata sanar dani ba kawai ta kama ta aske mun gira" ta amsa tana turo bakinta.
"Subhanallah bata tambayeki ba?"
"Bata tambaya ba nikuma ban san me take ba kawai duba mirron da zanyi naga duk ta kwashe."
"Sorry Kitten."
"Its not your fault Yaya."
"Dena fushi you're still beautiful even like this."
"Thank you, muje mu karya yunwa nakeji."
"Alright amma kafin nan tsaya in d'aukeki hoto."
"Ya- I mean Habib Alby bana so."
"Kitten bade kunya na kike ba? Nine fa Yaya yau na fara d'aukanki hoto ne?"
"Ba kace kai ba Yaya na bane yanzu ni kunyanka nakeji."
"Naji nide ki tsaya."
"Ni o'o" ta amsa tana buga kafad'arta.
"Sena miki kuka tukun?"
"Toh in ka d'auke ni nima zan d'aukeka ka yarda?"
"Ni bana son hoto ai kema kin sani."
"Toh ni d'in nace ma ina so ne."
"Kitten ni kike ma rashin kunya ko? Ba damuwa dama na san bakiya sona" yana fad'in haka ya juya wai shi a dole yayi fushi. Hannunsa tayi saurin rik'owa chak ya tsaya had'e da kewayowa yana kallon hannun nata dake rik'e da nasa. Da sauri ta sake "I'm sorry" ta furta.
"Ni bana buk'atar hak'urinki let's go eat."
"Toh ka tsaya ka d'aukenin."
"Nayi fushi bana so ba rowan kanki kike mun ba."
"Yaya mana."
"Kuma ni suna na ba Yaya ba."
"Toh yi hak'uri Habib Alby gashi na tsaya ka d'aukenin" ba k'aramin dad'i yaji ba amma ya moze "Ni bana so" gabansa ta shawo da sauri "I'm sorry kaji?" Wayansa ya zaro daga aljihunsa ya shiga d'aukanta ba shiri.
"Toh Yaya ka tsaya mana inyi posing tukuna" tana mai magana amma se d'aukanta yake kawai ta ko ina.
"Masha Allah am sure zan samu masu kyau sama da ashirin anan."
"Toh saura kai."
"Ni bana hoto."
"Yaya mana!"
"Nak'i."
"Haba Habib Alby tsaya kaji?" Da wayo cike da dabara ta d'auko wayanta kan mirror ta shiga camera kaman yadda yayita d'aukanta papparazi ta ko ina ita ma hakan ta rama daga k'arshe seda ya k'wace wayar. "Se kin kashe mun ido tukuna." Tana dariya tace, "Yi hak'uri toh ka tsaya muyi selfie yanzu" beyi gardama ba suka sha hotuna acikin wayanta da nasa. Kawai seta tuna da Ya Abdul. Lokaci d'aya yanayinta ya canza, Afzal ya nemi walwalan ta ya rasa.
"Kitten?" Ya kirata a hankali. "Kitten are you crying?" Cewa da tayi bari ta amsa sa kawai kukan yaci k'arfinta, wani irin masifaffen kuka ta 6arke da, a kid'ime Afzal ya janyota jikinsa ya rungumeta yana shafa bayanta a hankali yana mey bata hak'uri.
"Kitten I'm so sorry idan wani abin na fad'a ya 6ata miki rai please kibar kukan haka."
"Yaya ba kai bane" ta sanar dashi cikin tsananin kuka a hankali ya d'agota daga jikinsa. "Waye ne toh?" Ya tambaya yana share mata hawayen.
Kai zalla ta iya ta kad'a masa.
"Talk to me kitten I'm here please."
"I'm sorry but I can't" ta sanar da shi.
"Abdul ne? Is this about him?" Ba k'aramin k'una zuciyarsa ta shiga yi masa ba na wannan tambaya da yayi mata. Har yaushe Amal tasa zata na kuka akan wani na miji haka? Yasan bayida right da ze hanata amma zuciyarsa bazata iya d'auka ba, yana tsananin kishinta.
"Yaya I'm sorry please forgive me I just can't help it, I miss Ya Abdul I terribly miss him I'm so sorry please ka yafemun." Na matuk'a ta basa tausayi rungumarta ya sakeyi a hankali.
"It's okay Kitten, na fahimci halin da kike ciki, ki dena bani hak'uri kinji?" A hankali yaji hannunta a bayansa tana hugging nasa back.
"I'm so sorry" sun d'au tsawon lokaci a haka sannan ya d'agota daga jikinsa tare da mik'awa yana kissing tears nata away. "Stop crying okay? I'm here and I love you."
"Thank you Habib Alby."
"Muje muci abinci I'm starving" da hannunta rik'e cikin nasa suka k'arisa dining d'in.
"Waya kawo kulolin nan?" ta tambayesa "Na d'au fa zanyi mana girki ne."
"Har kina tunanin zan bar ki kiyi girki Kitten? 'Yar uwarki ce ta kawo mana."
"Nazeefah?" Kai ya gyad'a mata da nufin eh "Allah sarki ita da kanta?"
"A'a ta turo me gadinta ne."
"Ayya zan kirata ko inyi mata godiya."
"Let's eat first" ya bari tayi serving nasu ma k'i yayi shi da kansa ya zuba musu a plate d'ay bayan nan ya barta taci wai sam shi ze bata. Rigima suka 6arkr da, ita Amal tace sam ita zata ci da kanta shiko yace shi ze bata, da k'yar ya iya ya shawo kanta ta amince. Akan cinyarsa ya ajiye ta idan yaci ya bata haka har suka k'oshi sannan ta kira Nazeefah suka gaisa tayi mata godiya nan Afzal yace shima ta basa.
"Ya Rouhi" ta soma da cewa.
"Na'am Rabba'atul Bait ya kike?"
"Lafiya k'alau kai fa?"
"Alhamdulillah thank you for the breakfast."
"Don't mention Ya Rouhi anything for you amaryar mu na kula mun da kai ko?"
"Ai nace mata idan bata kula dani ba ma kince zaki kawo mata hukuma."
"Ai kuwa I'm missing you alot ko bacci na kasa yi jiya, I miss your arms around me."
Juyowa yayi ya kalli Amal yana me fatan Allah yasa bataji kalaman Nazeefah ba, se gani yayi tana harkan gabanta nema tana watsa da yatsunta. "I miss you too nida Amal zamu shigo miki karki damu."
"Toh shikenan sekunzo."
"Yauwa take care."
"I love you."
"I love you too" da haka sukayi sallama.
"Sharri zaka yi mun gun Rabba'atul Bait taka ko?"
"Cewa tayi idan baki kula dani in fad'a mata ta turo miki hukuma."
"Zaku taru kumin taron dangi ko? Ba matsala."
"Ai amarya bata laifi Kitten" yayi maganan tare da had'a yatsotsinsu gu d'aya yana wasa da su.
"Kitten?"
"Na'am Yay- Habib Alby" tayi sauri ta gyara kanta.
"Do you love me?"
"Yaya..."
"Just answer me Kitten, do you love me?" Shiru tayi ta kasa cewa komai "Feel free to tell me duk abinda ke cikin ranki kinji? You mustn't have to lie idan bakiya sona its simple just tell me."
"Habib Albi ina son ka sani cewa ita fa zuciya tana son duk me kyautata mata ne ko kana tsammanin Allah kansa ze barni ne idan na bud'i baki nace bana sonka? Ni kaina bazan ta6a yafe wa kaina ba idan nayi hakan, abubuwan da kayi mun aduniya bayan Allah da mahaifana ba wanda ya kwatanta yimun irinsu. Banida kaman ka Habib Alby koda hankalina yana tare da Ya Abdul kasani zuciyata taka ce, sabida ba wanda ya cancanceta kaman ka bana son kana tada hankalinka a kaina bana son ciwon ka ta tashi bana son abinda ze ta6a mun lafiyarka Habib Albi."
"Does this mean you love me?" Kai ta gyad'a masa a hankali. "Then say it to me Kitten you really don't know for how long I've been waiting for this day, I really need to hear these words please tell me" murmushi ta sakar masa sannan tace, "I love you Ya Afzal my Habib Albi, banida kaman ka." Afzal baze iya kwatanta irin dad'i da farin cikin daya ziyarci zuciyansa ba. Ba k'aramin nishad'i kalamun nata suka sanya sa ba all he knows is that he's never felt this happy.
"Please say it again Kitten tell me you love me again."
"I love you again and again and again Habib Albi and I'll choose you over and over and over again even if I where to be given another life." Rungumarta yayi yana mey zagaye hannayensa a bayanta yayinda ta kwantar da kanta jikinsa tana hugging him back.
"Thank you so much Kitten yau kin cika mun burina, koda mutuwa naui yau zan mutu da murmushi kwance a fuskana saboda kin sanar dani mafi daddad'in kalamun da kunnuwana suka jima suna kwad'ayin son ji. I want you to know that I'll do everything in my power to make you smile and happy, I'll take care of you and adore you like the Queen that you're, thank you so much Allah yayi miki albarka."
"Ameen Habib Albi don't mention" a hankali ya saketa tare da zaro wani k'aramar pack daga aljihunsa. Wata had'ad'd'iyar zobe ce aciki wanda ko ba a tambaya ba ansan me tsada ce don wani shek'in da takeyi. 6allo ta yayi a hankali daga cikin gidan nata tare da d'ago hannun Amal.
"I want you to have this Kitten."
"Yaya isn't this expensive? Bana son kana kashe kud'i extravagantly akai na."
"Kitten you're worth every diamond, you're worth morethan a gem so dan Allah ki dena damuwa idan ban 6ata kiba, matar wani zan 6ata?" Suul zoben ya wuce ring fingarta ba kuma k'aramin amsarta yayi ba.
"It's so beautiful Ya- Habib Albi" ta gyara kanta da wuri.
"Sede bekai rabin kyan da Allah yayi miki ba Kitten so do you love it?"
"Absolutely" ta amsa tana mai murmushi yayinda ta kasa daina kallon zoben.
"Then do I get an appreciation kiss?(Sunbatan godiya)"
"Yaya..." kunyansa ta shiga ji tana sauk'ar da idanunta a k'asa.
"I don't mean on the lips nasan ko sama da k'asa zan had'a ba iya kissing lips d'ina zakiyi ba, a kumatu ma ya isheni" shiru tayi ta kasa cewa komi wajen. "Please Kitten" nan ma shiru. "Kitten idan kina haka har zuwa tsawon yaushe zaki fara sakewa dani ko kin manta ni mijinki ne?" Kai ta kad'a masa a hankali.
"Then peck me I'm waiting."
"Yaya zan d'auraye plate da muka ci abincin akai" ta sanar da shi wai a dole zatayi masa waya. Hannunta ya rik'o cikin nasa "Kiss me first ko kuwa bazan sake kiba."
"Yaya..."
"Shhh! Anan kawai" yayi mata nuni da kumatun damansa sede ina bata jin zata iya.
"Alright let's do it this way, zan rufe ido na, I'm waiting" kai ta d'ago tana kallonsa "Allah baka rufe me kyau ba nasan kana gani na."
"I'm serious I can't watch you." Hannu ta d'aga tana waving a fuskan nasa don tabbatar da ko ya rufe d'in dagaske. A hankali ta shiga matso da fuskanta kusa da nasa dab zata sunbaci kumatun nasa kenan seya matsa kad'an da gan-gana, hakan yasa bakinta ya sauk'a akan nasa. Sandarewa tayi zaune a wajen, sun kai seconds goma a haka sannan daga bisani taja da baya. Mik'ewa tayi take ta ruga d'akinsu a guje, murmushi Afzal ya sa had'e da lasan lips nasan. Oh! Wannan kunya nata seya cire mata shi da ikon Allah.
RANA D'AYA!
#RD
Love... king Miemiebee👄✨
[13/08, 09:35] +234 907 483 8352: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
July, 2018
beeenovels.blogspot.com
_Written by Miemiebee👄_
*PAGE 2⃣8⃣*
Wayansa ya d'ago yayi texting nata _I'll be going out, I won't take long_ bayan minti d'aya sega reply nata _Allah kare seka dawo._
Wani sak'on ya sake tura mata,
_Won't you miss me?_ murmusawa tayi ta sake tura masa reply _Ko kad'an ma._
Dariya ya saki ya sake texting nata _😫😫😭._ da hanzari tayi replying nasa _I'm kidding kar kayi kuka, I'll miss you 😘_
Yana murmushi ya tura mata _I'll miss you too take care Xx 😘_ seda ta tabbata ya fita sannan ta fito parlourn, d'akunan ta bi each tana kalla dama chan ranan da suka taho da Afzal bata samu dama tayi kallo kaman yadda takeso ba gudun karya cemata 'yar k'auye ta cika kalle-kalle. Bayan ta dawo ta zauna a parlour so take ta kunna TV'n amma kuma gudun karta rikitar da wani abun ta fasa dan haka ta zauna kawai. Wayan ta da take rik'e da shi ne ya shiga ruri dubawanda da zatayi taga Maamah ke kira da hanzari ta d'aga.
"Mata agidan Ya Afzal" ta soma da cewa.
"Uhmm ya kike?"
"Ai baki amsa ba nace mata a gida Ya Afzal."
"Kin fara ko?"
"Ko yana kusa ne bakison ki d'aga murya ya jiki?"
"Seki kwantar da bokatin hankalinki Yaya baima gida ya fita."
"Ashe shiyasa aka d'au wayana nasan da yana nan da bazaki d'auka ba."
"Haka dey kikace."
"Toh ya kike?"
"Lafiya k'alau."
"K'alau k'alau de?"
"K'alau mana" ta amsa a tak'ure.
"Ba wata jinya?"
"Allah Maamah ke 'yar iska ce."
"LOL" ta furta tana dariya "Ai gaskiya ce toh ya jiki?"
"Ce miki akayi ina jinya?"
"Ai ba se an fad'a ba da ganin Ya Afzal an san uhm uhm uhm ne."
"Ni wallhi ba ruwa na."
"Ohh Amarsu ina yaje toh ya bar mana ke kad'ai a gida?"
"Ni kawai cemin yayi ze fita and ban tambayesa ina zasa ba."
"Kode gidan uwar gidansa zasa?"
"Ban sani ba."
"Kuma baki damu ba?"
"Toh mutum da matarsa? Na isa in hanasa ne?"
"Ahh ashe k'awar tawa bata da kishin hauka ai dama jin bakinki nake bale nasan ma ba gidan Nazeefah zasa ba."
"Uhm so ya hutu?" hira suka ta6a sannan chan sukayi sallama. Tunanin me zatayi ta shiga yi zama hakan ne ya isheta gashi Afzal be dawo ba, chan dabara ta fad'o mata kitchen ta zarce ta shiga fito da groceries, had'ad'd'en jollof na spaghetti ta girka da minced meat ta ko ina a ciki, frozen chicken data ga a fridge ta ciro ta yanka ta gyara tayi pepper chicken da shi, bayan nan ta had'a zo6o me d'ankaren dad'i tayi slicing abarba aciki. Kan dining table d'in ta shirya gwanin sha'awa sannan ta kunna wuta ta turare gidan se k'amshi ke tashi. Nan ta kaiwa me gadi abincinsa sannan ta dawo ta fad'a bayi tayo sabon wanka tana fitowa ta idar da sallah ta ciro sabon d'inki ta sake sawa ta feffeshe jikinta da turare tayi kwalyanta ras. Har ta d'auko ribbon zata kama kanta seta tuna da kalamun Afzal na d'azu akan cewa tafi kyau idan ta sauk'e gashinta. Tajewa tayi ta sake a bayanta yana lilo, tana cikin d'aukan selfie taji k'aran bud'uwan gate nan fa gabanta ya fad'i seji tayi kaman ta goge kwalyar ma gabad'aya.
K'amshin turaren wuta ne ya bugi hancin Afzal yayin da ya sa kai cikin parlourn, ga k'amshi kota ina amma ba hayak'i unlike Ummi and Nazeefah da idan sukayi turare se hayak'i ya fitimi mutum na Amal k'amshi ne kawai ke tashi. Gaskiya he's really impressed. K'arisawa dining da yace zeyi don sauk'e ledan abincin daya siya musu ya tarar da kulolin abinci suna masa sallama. Da mamaki ya bi yana bud'ewa abinci ya tarar da dama aciki wow! Shin meyasa be sanar da ita cewa ze sai musu abinci ba? K'arisawa d'akin yayi tare da yin knocking, Amal naji ta gudu ta la6e bayan k'ofan sede Afzal ya ga shigewan ta kaman a kyaftawan ido murmushi ya sakar yayi kaman be ganta ba "Kitten?" Ya kirata yana lellek'a d'akin irin yana nemanta d'innan wajen bayin ya nufa yayi placing knock "Kitten are you in there? Bara in duba kitchen kota na chan" yace da kansa, ficewa yayi yaja k'ofan nan Amal ta sauk'e ajiyar zuciya cewan da tayi bari ta fito daga 6uyan Afzal ya wangale k'ofar "Got you!" Yayi shouting yana mata dariya, sosai ta firgita tare da dafe k'irjinta "Yaya you scared me!" Tayi complaining had'e da turo baki.
"I'm sorry Kitten come here" a hankali ta k'ariso, hannayensa ya zagaye a bayanta had'e da sake matso da ita kusa da shi. "You smell so good Kitten."
"Thank you Habib Alby."
"Wannan kwlaya fah? Duk ma ni neh?"
"Toh kuma da wa me gadi zanyi wa ne?" Ta amsa tana turo mai baki.
"You look so beautiful Kitten."
"Thank you Habib Albi lets eat I cooked."
"Haka na mance ban fad'a miki zan sai mana abinci ba."
"Siyan abinci kuma Yaya?"
"Yes Kitten ko kin manta amarya bata girki ne?"
"But Yaya I want to cook for you."
"I appreciate that Kitten amma kibari in kin gama amarcin ki tukuna kinji?"
"Nide na gane kawai baka son cin girki na ne shikenan" ta fad'a tana 6ata rai.
"Not at all Kitten" yace yana mey shafa dogon sumarta "Bana son kina aikin wahala ne, na kawo ki gidan nan dan ki huta ne ba din kina aiki ba kinji?"
"But ai hak'k'i na ne a matsayina na matarka in yi maka girki Yaya."
"Kitten bana soke sunan nan ba?"
"I'm sorry Habib Albi I just wanna cook for you dukda nasan girkin nawa ba dad'i I still want to cook for you."
"Wayace baki k'ware a girki ba Kitten? Kin tuna rice and stew da kikayi mun lokacinda na dawo daga Hajj?" Kai ta gyad'a a hankali. "It's still my best Kitten, har yau banci Rice and Stew da yamin dad'i kaman shi ba."
"Dagaske?" Ta tamabaya tana jin dad'i.
"Sosai Kitten I'm hoping you can cook it for me again."
"Sure Habib Albi ko a gobe zan girka maka."
"A'a mu bari se amarcin naki yak'are."
"Har zuwa yaushe?"
"2 months kacal."
"Wata biyu kuma Habib Albi? Ina laifin sati d'aya?"
"Are you kidding me?"
"Toh sati biyu."
"Why don't we do it this way tunda kina son yi min girki se muna yin na safe tare, kiyi na rana se na dare kuma muna ci a waje, okay
"Habib-"
"Please say yes Kitten" ya katseta cikin sauk'i.
"Sau d'aya zanna girki kenan?"
"I'm sorry but yes."
"Ina da alfarma toh."
"Anything for my Kitten."
"Amarcin ya zama na sati biyu."
"Am not allowing that ko Nazeefah ma seda muka kusan two months sannan ta fara girki so kema haka."
"Habib Albi toh wata d'aya please don't say no" ta rok'esa da fuskan tausayinta.
"Alright Kitten one month."
"Yeyy! Thank you so muje inyi serving naka" har ta juya ya rik'o hannunta tare da kewayo da ita kafin ta gane abinda yake da anniyar yi kawai taji sauk'an lips nasa akan nata it was a very short kiss cikin seconds ya saketa. "I love you Kitten" kunya taji sosai kaman ta nitse k'asa. "I said I love you Kitten." Chan ciki-ciki tace "I love you too Habib Albi let's go." Dad'i yaji sosai suka k'arisa dining d'in abincin da ya siyan ya sa a microwave da niyyan anjima se suci. A plate d'aya ma suka ci abincin kaman d'azu, haka har suka k'oshi suka koma d'aki suka yini tare, sallah kad'ai ke fitar da Afzal, da dare yayi kuma da kansa yayi musu microwaving abincin daya siya d'azun suka ci.
**** 9:57pm
Fitowan Afzal daga bayi kenan "You're next Kitten" mik'ewa tayi sanye da hijabi da towel ta ciki ta nufi bayin kaman jiya yau ma kafin ta fito har Afzal ya kimtsa gajeren wando zalla yasa d'akin se k'amshin turaren jikinsa yake. Gaban dressing mirror ta nufa ta shiga yin shafe-shafenta sannan ta k'arisa wardrobe ta shiga neman kayan baccin da zata sa sede duk ba marabansu da na jiya. Oh Rabbi ya zatayi? Tana cikin tunanin mafita kawai taji sauk'an hannun Afzal akan nata a kid'ime ta kewayo tana kallonsa.
"What's wrong Kitten?"
"Ya- I mean Habib Albi I'm sorry ina neman kayan da zansa ne."
"Baki samu ba har yanzu?" Ya tambayeta a hankali. Kai ta gyad'a "Ka bani minti biyu" kafin ta juya ya tsayar da ita "Wait" tsayawan tayi a hankali ya matsar da ita gefe bekai seconds talatin cikin wardrobe d'inba ya zaro d'aya daga cikin kayakin baccin nata shigen irin na jiya sede har gara na jiyan ma bak'i ne wannan milk color ne don haka yafi transparency. "Here wear this" amsa tayi ta d'aga tana kalla.
"Habib Albi I can't."
"Why Kitten?"
"Habib Albi..." se kuma tayi shiru.
"Look Kitten" yayi maganan tare da aza hannunsa akan kafad'unta yana murzawa a hankali "I'm not your Yaya anymore I'm your husband, kuma addini na ya halatta mun in kalleki acikin ko wani irin yanayi, ba haramun bane dan kinsa kayan nan na kalle ki Kitten."
"Habib Albi I know kawai..." se kuma tayi shiru.
"Tell me kinji? Mene?"
"Habib Albi kunyanka nakeji ina tsananin jin kunyanka and I don't know why."
"I guess I know why" ya sanar da ita.
"Really?" Ta tambayesa da mamaki.
"Yes Kitten saboda we started off as a brother and sister and not as lovers. It pains me that yadda kika d'aukeni da zuciya d'aya a matsayin wanki ni na kasa yin hakan. I know koda wasa baki ta6awa kawowa a ranki cewa aure ze shiga tsakanin mu ba one day se gashi zuciyata tayi karanbanin fad'awa tarkon sonki har ya zammana idan ban sameki ba rayuwata tana iya fad'awa cikin matsala. I'm very sorry Kitten amma ina son ki sani love is a feeling and not a decision one makes wallahi idan da zan iya bawa zuciyata hak'uri akan sonki da nayi kodan ki kasance tare da masoyinki Abdul amma ba daga ni bane, I can only control my mind and not my heart I'm really sorry" ya k'arisa tare da sauk'ar da kansa. Hannunta ta mik'a ta rik'o nasa wanda hakan ya sanya sa d'ago kansa.
"Habib Albi dan Allah ka daina magana haka kasani bazan ta6a k'inka don zuciyarka ta za6eni ba, abun alfahari ne ma ace Yaya na guda ya samu macen aure a tattare dani don d'abi'ata ko makamancin hakan."
"Toh ki rage jin kunya na haka, gani nake kaman bakiya sona idan kina kunya na haka, is like kina adana jikin ki ma wani ne and not me:"
"Yaya har kana tunanin zan ajiye kaina ma wani na miji sama da kai? I'm sorry if you felt that way."
"Its okay Kitten just wear this."
"But-"
"Please Kitten."
"Habib-"
"Please Kitten I want you to be free with me like old times, ki sanya kinji? Zan fita in kin gama shirin se in dawo" da fad'in haka ya mik'a tare da sauk'e mata light kiss a goshi sannan ya juya ya fice. Nauyayyan ajiyar zuciya ta sauk'e tana tunanin ta inda zata fara sa kayan, ta d'au tsawon minti biyu tsaye wajen sannan ta shiga kwaye hijabin nata, ba don tana so ba se don ya zama mata dole ta zira kayan ta k'arisa gaban mirror tana adjusting. "Huh!" Ta numfasa yayinda take kallon kanta acikin madubin kash sede bata tunanin zata iya yawo da kayan nan a gabansa da sauri ta sake mayar da hijabin ta sanya. Ita kanta haushin kunyan nan nata take, na sosai tana son ta sake da Afzal ko dan ta farinta masa rai amma kunyan nan ke hanata haka ta cigaba da tsaye a wajen har Afzal yayi knocking bisa k'ofan. Bayanta ta juya da wuri lokacin da ta ji ya bud'e k'ofar. A hankali take jin k'aran footsteps nasa suna iso ta chak ya tsaya a gabanta nan ta kafa idonta a k'asa. Hannunta taji ya kama acikin nasa yana murzawa a hankali yayinda ya shiga d'age mata hijabin da d'ayan hannun sa. Da sauri tasa hannu ta rik'e hijabin nata tana tsayar da shi.
"I've got you okay?" Da hankali ya sauk'e hannun nata ya shiga d'aga hijabin har ya kai ga kwayewa ta zare hannunta daga nasa ta shiga rik'e hijabin "Yaya I'm sorry but I don't think I can do this."
"Shhh I've got you Kitten I've got you" cike da dabara ya sauk'e hannayen nata sannan a hankali ya kwaye hijabin ya cire daga jikinta kafin ta d'au hannu tace zata tare k'irjinta ya rik'o hannayen nata biyu cikin nasa.
"There" ya furta a hankali "Na fad'a miki ai zaki iya koba haka ba?" Hannun nata take kokawan k'wata daga nasa amma ta kasa har anan kuma ta kasa d'ago ido ta kallesa. "Kitten you're so beautiful" ya furta yayinda yake bin surar jikinta da kallo kunya tajiyo kaman ta nitse a k'asa a lokaci guda ta fisge hannayenta ta fad'a jikinsa tana kare fuskarta. Be hankara ba ya zageye hannayensa a bayanta yana shafata a hankali, wani irin wuta take ji yana bin jikinta. Bayan d'an lokaci ya d'agota daga jikinsa se sauk'ar da fuskanta take. Yatsa yasa ya d'ago fuskan nata "I love you Kitten" ya sanar da ita sede ta kasa cewa komai "Wani sa'in har tsoron irin soyayyar da nakeyi miki nake saboda ina ganin duk ranan da na rasaki toh tabbas nima za a rasani."
"Yaya I'm here bazan ta6a barinka ba no matter what."
"Thank you Kitten" a hankali ya shiga shafa fuskanta yana mey sa duk wani gashi a jikinta tashi, a nitse ya shiga matso da fuskansa kusa da nata har lips nasa suka sauk'a akan lallausar kumatunta, kisses ya shiga peppering mata tako ina har seda ya sauk'o k'asa zuwa wuyanta. Mutuwan tsaye Amal tayi wajen yayinda jikinta ya shiga rawa banda nishi masu nauyin da take sauk'ewa takasa yin komai. Kisses Afzal yata raining mata a fuska daga bisani kawai taji ya had'e lips nasu gu d'aya kafin ta iya turesa yayi sauri ya kama hannun ta cikin nasa yana mey cigaba da kissing nata, dukda cewan tak'i basa had'in kai hakan besa ya hak'ura ba. Wasu irin abubuwan ya shiga yi mata wanda tuni ya rikitar da Amal ya kuma mugun kashe mata jiki, a hankali yaji hannayenta cikin gashin kansa yayinda ta shiga kissing him back, sake matso da ita kusa da shi yayi tare da rik'o 'yar kunkuminta. Tafiya suka shiga yi a haka manne da juna har seda suka kai jikin bango. Na lokaci kad'an ya saketa kafin ta sauk'ar da kanta ya sake owning lips nata in a more demanding way, gabad'aya abinda yake mata ya gama tafiya mata da imani da k'yar ta iya pulling out tana maida numfashi, goshinta ta sauk'e saitin ha6arsa yayinda wani irin kunya ya rufeta. Bata tsammanin zata iya sake kallon cikin idanunsa. Oh Rabbi shin mey Afzal yakeyi mata haka? Meyasa ta kasa tsayar da kanta? Swollen lips nata ta shiga lasa a hankali yayinda ta rufe idonta gam. Hannunsa taji yana shafa fuskarta yana k'ok'arin sata ta kallesa sede tak'i, da k'yar ya samu ya ci nasaran hakan. Yatsansa ya kai akan lips nata da sukayi ja suka kumburo yana shafawa a hankali. Amal kad'ai tasan irin abinda take ji ajikinta.
"Kitten?" Ya kirata cikin hankali "Look at me" ya buk'aceta amman ta kasa kunya baze barta ba. "Don't feel shy Kitten, please look up."
Duk yadda taso ta kallesa kaman yadda ya buk'ata hakan ya gagara da k'yar ya samu ta d'ago lumsassun idanunta ta sauk'e a kansa.
"There" ya furta yana mata murmushi yayinda yake tura gashin da suka rufe mata fuska baya. "Kin sani wani abu Kitten?" Ya yambayeta dan yadda suke kusa da juna har nishinsu had'ewa yake. Cike da kunya ta kad'a mai kanta.
"Your lips are probably the most sweetest thing I've ever tasted" ya sanar da ita yana shafe kan lips nata a hankali da yatsan sa. "May I get another taste?" Ya tambayeta amma kunya baze barta ta amsa ba duk da cewan she enjoyed kissing him also, itama tana iya rantsewa bata ta6a d'ana abu mafi dad'i kaman lips nasa ba, ga wani k'amshin mint da bakinsa yake.
"Kitten I badly want to kiss you again amma bazan yi hakan ba seda amincewar ki, may I?" Kai ta gyad'a masa a hankali idonta na kallon k'asa.
"No I want you to answer me with a yes or a no looking straight into my eyes."
"Habib-"
"Shhhh!" ya katseta yana mey cigaba da shafe kan lips natan. "May I kiss you again?"
Seta bud'e baki zata amsa seta kasa sau biyu yake sake tambayarta se ana uku tukuna ta amsa "Yes Yaya" wani mak'irin murmushi ya sakar sannan ya sake owning lips nata in a more possessive and demanding way, wasu irin abubuwa ya shiga yi wa Amal wanda tuni yasa ta fice daga hayyacinta, duk yadda taso keeping up da pace nasa ta kasa ba k'arya Afzal is a bad kisser, da k'yar ta iya tayi breaking kiss d'in tana maida numfashi yayinda jikinta ya d'au wuta gabad'aya. Bata hankara ba taji ya d'aga ta sama chak in a bride-like style.
"Hab-" toshe bakin nata yayi da wani kiss nasa se a kan gado ya direta inda ya cigaba da sarrafata iya san ransa banda maida numfashi ba abinda Amal ke iya yi gabad'aya ji tayi jikinta ya mutu. Yana ce bari ya gwada sauk'ar mata da hannun riga ta rik'e hannun nasa gam tana kad'a mai kai. Ba yadda beyi ba amma tak'i, gano dalilin hakan kawai seya mik'a hannu ya kashe wutan d'akin a hankali cike da k'issa irin nasa ya samu yaci nasara akanta har ya rabata da rigar nata...
A daren ranan Afzal ya mai da Amal tasa cikakkiyar mace bayan gogormayan da ya sha. Daga kukan da takeyi har bacci ya d'auketa k'arshe. Yana cikin kallonta kwance a hannunsa shima har bacci me nauyi ya sacesa.
Da k'yar ya iya mik'a hannu ya kashe alarm d'in bayan da ya shiga ruri. Gani yayi yanzu ya kwanta amma wai har Asuba yayi. Wutan d'akin ya kunna sannan ya sauk'ar da kansa yana kallon Amal da tayi lamo tana bacci cikin hannunsa har yanzun, tabbas da ba don yana da hak'uri ba da sunyi bori da ita jiya saboda yadda ta gajar da shi ta yita basa wuya har ya samu ya biya buk'atansa. Haka kawai ya tsinci kansa cikin tsananin murmushi tuna sautin kukanta daga daren jiya, ai kam Nazeefah jaruma ce ganga da Amal. A hankali ya rabata daga jikinsa yaja towel ya nufi bayi bayan yayi wanka ya d'aura alawala akai sannan ya had'a mata warm water ya fito. D'aya daga cikin sabbin jallabiyansa ya zira sannan ya nufi kanta inda take ta faman bacci. Fuskanta ya shiga shafawa tun tana kawar da hannun nasa har ta tashi daga k'arshe. A hankali ta sauk'e idanunta da suka d'an kumburo akan fuskansa dake d'auke da murmushi, ba shiri ta sake kullesu. Dama yasan za'ayi haka.
"Good morning my adorable Kitten" ya gaisheta sede kaman ce mata yayi tashi ki gudu. Bedsheet da take rufe da shi d'inne ta shiga tattarewa a jikinta yayinda take ja da baya. Dariya sosai hakan ya basa amma ya moze.
"Tashi kiyi wanka kiyi alwala muyi sallah ko? Na had'a miki warm water a tub" ya sanar da ita sede ko ta kyafta ido balle tasan yana yi. "Ko in miki da kaina ne?" Ya tambayeta ba shiri ta bud'e baki ta amsa sa "uhm uhm."
"Tashi toh" sede ko ta sake motsawa.
"Kitten?" Nan ma shiru "Okay zan fita idan kin kimtsa seki mun magana okay? I love you" still shiru tayi masa seda taji k'aran ruhuwan k'ofa sannan a nitse ta bud'e idanun nata. Kallon gefe-gefe ta shiga yi dan janyo kayanta ta sanya amma ina kayan ya mata nesa dan haka ta mik'e da bedsheet d'in nannad'e a jikinta da zaran tace zata tsuguna kuwa se ta jiyo wani irin d'ankaren zafi a k'ark'ashinta bayan nan ga yadda cinyan nata yayi tsami. Haka a sannu a sannu ta k'arasa bayin hannu tasa cikin ruwan d'umin daya had'a mata har yaushe yake tsammanin zata iya shiga wanna ruwa mey uban zafi. Na sanyi ta bud'e ta tara seda yayi mata dai-dai sannan ta shiga ciki. Ta kai minti biyar ciki sannan ta fito ta bud'e shower tayi wanka ta d'aura alwala akai sannan ta fito se k'ingishi takeyi. Key tasa bakin k'ofan yadda Afzal ma baze iya sake shigowa d'akin ba. After everything bata tunanin zata sake iya kallon cikin idanunsa. Vest ta sanya ta d'aura zani tana cikin sanya hijabi tajiyo knock a bakin k'ofan tsabagen firgitan da tayi har chan k'asanta tajiyo zafin.
Da mamaki Afzal ya gwada bud'e k'ofan yaji bai bud'uwa. "Kitten?" Ya kirata, shiru tayi tsaye cikin d'akin.
"Kitten ba de kulle k'ofar nan kikayi ba" Nan ma shiru jijjigawa ya shiga yi sede ina bai bud'uwa gashi spare keys na k'ofofin gidan gabad'ai suna a cikin d'akin tirk'ashi! Rok'arta ya tayi da ta taso ta bud'e amma haka tana jinsa tak'i koda motsawa dan kansa ya bar wajen ya nufi d'ayan d'akin inda ya idar da sallansa ya kwanta. Bayan ta idar da nata itama ta tattara besheet d'in ta shiga bayi tasa a washing machine akan cewa da safe zata wanke. Sabon bedsheet ta shimfid'a sannan ta kashe wutan d'akin ta kwanta.
Se chaan wajajen goma na safe ta tashi nan ma a sanadin ringing da wayanta yake ne da sauri ta d'aga ganin Mami ke kira.
"Halo Mami?"
"Na'am Baby ya kike?"
"Lafiya k'alau Mami ina kwana?"
"Lafiya ya gida? Ya Afzal?"
"Lafiya k'alau ya Papi?"
"Yana nan k'alau shima ya fita d'azun."
"Ayyah ba komai ko?"
"Ba komai na ce bari in kira inji ko kina lafiya."
"Thank you Mami."
"Banda rashin kunya fa Baby, kiyi masa ladabi da biyayya duk abinda yace kiyi kiyi, wanda baya so kuma ki bari ba ruwanki da yima uwar gidansa rashin kunya kuma."
"Mami na sani kin fad'a mun."
"Toh Allah miki albarka bayan kwana biyu seki kira Ummi ki gaisheta kuma."
"Toh Mami thank you."
"Yauwa se mun sake waya." Sauk'e wayan tayi tana hamma duba agogon da zatayi taga goma da rabi tirk'ashi! Breakfast na Afzal fah? Mik'ewan da tace zatayi daga kan gadon tasa wani d'ankaren ihu bisa ga zogin da tajiyo a k'asarta a hankula ta mik'e ta shiga takawa sede kaman sake tsami cinyan nata yayi yau ta shiga uku. Ji take kaman tayi kuka haka ta nufi bayin ta yi wanka ta fito ta shafa mai da turarukanta sannan ta sa wata doguwar rigar da ta mugun amsarta. Powder zalla ta shafa da farin lip gloss, tana cikin taje sumarta taji sauk'an knock bakin k'ofa, gabanta ne ya mugun fad'i amma bata ce komai ba.
"Kitten?" Ta jiyo muryan Afzal "Kitten I know you're awake ta shi ki bud'e mun kinji? Breakfast is ready" Kunya taji sosai taya yana mijinta zeyi girki ita ta kwanta kaman kayan wanki tana bacci.
"Kitten open up okay? Ko sena kira Papi tukuna ince gashi kin kulleni a waje?"
Ce tayi wasa yake seda taji ya sa wayan a handsfree taji muryan Papi na sallama tukun. Ba shiri ta mik'e ta bud'e k'ofar murmushi ya sakar mata
"Dama nace in gaisheka ne Papi."
"Toh Afzal nagode ko? Komai lafiya dai ko?"
"Alhamdulillah."
"Toh madallah."
"Yauwa se mun sake waya."
Toh ka gaishe mun da Baby."
"Zata ji" nan ya kashe wayan. Baki ta turo sannan ta juya mai baya da k'ingishi ta shiga takawa har izuwa gaban mirron ta zauna. Kallonta ya tsaya yi yana mamakin ko meya sameta take tafiya haka. K'arisawa yayi ya sameta "Kitten?" Ya kirata.
"Ina kwana?" ta gaishesa ba tare da ta kallesa ba.
"Taho kinji?" Hannunta yaja ya mik'ar da ita had'e da rungumarta. Lamo tayi ta kwanta a jikin sa "I'm sorry okay?" Ta ji ya fad'a.
Ko hak'urin mey yake bata? ta tambayi kanta. "Forgive me if I went rough on you last night Kitten" ya sanar da ita had'e da d'agota daga jikinsa. "I'm really sorry."
"Ka dena bani hak'uri Habib Albi baka mun komai ba" ta fad'a ba tare da ta bari k'wayan idonsu ya had'u ba.
"Pain d'in sosai ne?" Ya tambayeta cike da tausayi, kai ta kad'a masa a hankali.
Fad'a mun gaskiya kinji?
Ba sosai bane don't worry" yatsa yasa ya d'ago fuskanta seda idanunsu ya had'e "I saw the way you were walking, mu kaiki clinic su duba ki?"
"Ni banaso ze warke da kansa."
"Toh let's go and have breakfast I cooked after then seki sha pain killer ze rage zafin okay?" Kai ta gyad'a mai a hankali. "Sannu ko Baby?"
"Thank you Yaya" juyawanda zeyi yaga harta canza bedsheet na d'akin.
"Ina bedsheet d'in?" Ya tambaya.
"Na riga na wanke" ta sanar da shi.
"Kitten bana son kina sa kanki aiki."
"Toh Yaya so kake in barka ka wanke da kanka ne?" Hannayensa ya zagaye a 'yar kunkuminta yana mey matso da ita kusa da shi. "Last night was amazing Kitten thank you."
"Ni ka daina maganan bana so" ta fa'a cike da shagwa6a.
Dariya ya tsaya yana yi mata sannan ya shiga kwaikwayonta "Yaya ni bana so-"
Rufe mai baki tayi take "Dan Allah ka daina" hannun nata ya sauk'e yana mey cigaba da neman tsokanarta sauran abubuwan da yake fad'an ma ko wuk'a aka sa mata a wuya baza ta iya tuna lokacin da ta fad'esu ba. Ganin tana shirin yi masa kuka ya daina "Na daina toh muje let's eat" a hankali suka shiga takawa ganin tafiyan na bata wuya kawai ya d'agata sama a hannunsa har dining space ya kaita sannan ya zaunar da ita akan cinyansa. Bayan sun gama karyawa ya 6allo mata maganin kashe zafin ya bata ta had'iye.
"Zaki iya fita yau kuwa?"
"Ina?" ta tambayesa.
"Ina son muyi miki passport ne mu fara processing visan mu to Saudi."
"Baza mu iya bari zuwa gobe ba Habib Albi?"
"Ciwon sosai ne haka?"
"Zuwa gobe ze daina in shaa Allah."
"I'm sorry Kitten I didn't mean to bruise you."
"It's okay Habib Albi."
"Kikace baza mu kaiki Clinic ba?"
"Ni gaskiya bana so."
"Sannu ko Baby?" Kwantar da kanta tayi bisa k'irjinsa yayinda ya zagaye hannayensa a bayanta yana shafa gashinta a hankali.
Yini sukayi suna bacci ranan se wajajen k'arfe uku Afzal ya tashi a hankula ya sauk'e Amal daga jikinsa ya mik'e ya nufi bayi. Brushing yayi ya d'aura alwala sannan ya ajiye mata note gefen gado. Gentle kiss ya sauk'e mata a lips sannan ya sanya kayansa ya feffeshe jikinsa da turare ya fice.
Da la'asar Amal ta tashi mik'an da zatayi taji ba Afzal akan gadon. A hankali take bud'e idanunta inda suka sauk'a akan note da ya ajiye matan. Bata hankara ba ta d'aga ta karance kaman haka;
_Will be back soon with our lunch don't mind cooking anything I love you, xx_ 😘
"Be back safely Yaya" ta furta tare da mik'ewa sede har yanzu da k'ingishin take tafiya bayi ta k'arisa tayi alwala tayi brushing sannan ta fito tayi sallah. Bayan ta kammala azkhar nata ta zarce gaban mirror tayi sabon kwalliya abinta kaman jiya yau ma tana cikin d'aukan selfies taji me gadi na bud'ewa Afzal k'ofa. Har ta bud'e k'ofa zata je ta taresa se taji muryan wani na tashi da hanzari ta koma ciki. Bada dad'ewa ba sega Afzal ya bud'e k'ofan ya shigo, ba k'aramin dad'i yaji ba ganinta da yayi da sabon kwalya.
"Kitten!" Yayi exclaiming cike da jin dad'i.
"Welcome back Habib Albi" hannunsa ya bud'e mata "Ni ka k'ariso" ta ce ganin takawan ze bata wahala, k'arisowan yayi sannan ta fad'a jikinsa. "Ya jikin naki toh?"
"Da sauk'i" ta amsa.
"Sannu ko? Kinyi sallah?" Kai zalla ta gyad'a mar "Muje mun taho da Sultan yana son ku gaisa."
"A'a nikam gaskiya bazan fita ba."
"Kitten why?"
"Kaman ya why Habib Albi? Da k'ingishin kakeso in fita ya ganni yasan..." sekuma tayi shiru. Dariya sosai ta basa amma ya moze "Kitten bazaki fita ku gaisa da aminin nawa ba kenan yanzu?"
"Kace mishi ina bacci ni gaskiya bazan fita yamun dariya ba" yanzu kam dariya sosai Afzal yasa "Ya Sultan fa Kitten bazaki fita ku gaisa ba?"
"Ba duk kai bane ka jimun ciwo" ta sanar dashi tamkar zatayi kuka "Kuma ka daina mun dariya" sake rungumarta yayi yana shafa gashin kanta a hankali "Yaya is sorry kinji? Baze k'ara ba." Kai ta gyad'a masa a hankali.
"Bari inje in same shi toh, in kawo miki abincin ki nan ko zaki jira in ya tafi muci tare?" Ya tambayeta bayan ya janyeta daga jikinsa.
"Zan jiraka jeka same shi" peck ya sauk'e mata a goshi sannan ya fice.
"Se yanzu amaryar ta barka ka fito kenan" Sultan da har d'uwawunsa yayi tsami dan zama yace. Da fari Afzal yayi niyyan masa k'arya yace Amal na bacci ne amma yanzu da Sultan ya kamasa haka ai ba halin yin k'arya kuma again.
"Actually..." ya furta yana sosa k'eyarsa yayinda yake tunanin wani k'aryan ze had'a.
"Na gane kar ka damu tace bazata fito ba tana jin kunya na."
"Fvck! Keep your voice down Sultan kada ta jiyoka" ya sanar da shi cautiously.
"Hakan ne kuma ko?" Ya tambayesa yana dariya.
"Wallahi taji ka ba ruwa na nide ba ni na fad'a maka ba."
"Triple A ansha k'amshi" yace da shi cike da neman tsokana. Punch Afzal ya kai masa a hannu yayin da ya zauna a gefensa "Ba kak'i kayi aure ba yau kaine a gidan nan gobe kaine a chan ka kasa settling da mace d'aya."
"Ka bar matan nan kawai maza a jinka samun kaman Amal da sauk'i ne? Duk kud'in mutum kawai suke so ba komai ba."
"Se muje k'auye mu auro maka d'aya ai kaga chan su kansu be waye ba basu san dad'in kud'i bama."
"Amma Allah ya isa wallahi se gani na d'au 'yar k'auye na ajiye a gaban mota wai ita matata ko? Wallahi mugu kake Triple A."
"LOL wai fa shawara ce."
"Toh uwarka da shawaran ni da Allah kawo mun abinci inci."
"Ai babu."
"Kaman ya babu? Gidan amarya guda? Allah baza ta saku ba, in k'i cin abinci saboda zani gidan amarya kace mun ba abinci?"
"Allah babu sede su chin-chin da dambu idan kana so."
"Dalili?"
"Amal d'ina bata girki" ya sanar da shi yana d'age mai gira.
"Jakar uba! Allah ban yarda ba."
"Wallahi ba a idonka na shigo da ledan abinci ba kana gani?"
"Waiiii morewa haka! gaskiya nima zanyi zuciya inyi auren nan."
"Ahtoh ana fad'a maka kana wasa aure dad'i gareshi wallahi."
"Kai maza!"
"Niko nake fad'a maka."
"Toh shikenan ha inyi nima in shiga daga ciki." Hira suka sake ta6awa kad'an Afzal harda korin Sultan wai ya tafi Amal tasa ta gaji da jiransa, iskanci ya ta yiwa Sultan yana neman tsokanansa k'arshe ya rakasa sannan ya je ya kira Amal dake d'auke da Qur'ani tana karatu. Seda ya jira takai k'arshen aya sannan ya gyara muryansa hakan yasa ta gano da mutum cikin d'akin.
"Masha Allah Kitten yaushe zaki fara bani karatun nima?"
"Kai Habib Albi."
"Taso to muje muci abinci" da kansa ya mik'ar da ita kaman d'azu ya d'auke ta har izuwa dining.
****
Da daddare bayan ya fito daga bayi yace da Amal "Tashi ki shiga na sirka miki warm water ki samu at least 7-10 minutes aciki ze miki healing ciwon kinji?"
"Ni bana so."
"Kaman ya bakiya so Kitten, meyasa?
"Zafi Habib Albi."
"Bakiya son ki warke ne?"
"Inaso."
"Toh ai se kinyi hak'uri kin shiga gashi ma na saya miki man zafi, idan kika fito semu shafa miki, tashi ki shiga kinji?"
"Ni bana so" lalashinta yatayi da k'yar ya samu ya jata cikin bayin "Ina tsaye a waje ina jiranki kinji?" Hannu tasa cikin ruwan "Wallahi yayi zafi."
"Kitten in ba haka ba bazaki samu sauk'i da wuri ba fa."
"Zan k'ara ruwan sanyi kad'an toh."
"Kitten kar kisa fa in tu6eki anan in saki cikin ruwan nan da kaina."
"A'a kayi hak'uri."
"Toh ki shiga kuma karki k'ara ruwan sanyi akai, zan tsaya a waje kisani idan kika k'ara kuma zan sani."
"Tayaya bayan kana waje?"
"Are you daring me?" Ya fad'a cikin tattausar murya kai tayi saurin kad'awa "Good kar fa ki k'ara ruwan sanyin nan."
Tana murmushi tace "Barin k'ara ba."
"Kitten ba fa wasa nake ba."
"Nace naji ka fita kar ya huce."
"Ban yarda dake ba ki rantse bazaki k'ara ruwan sanyi akai ba."
"Rantsuwa ba kyau ni gaskiya bazan rantse ba."
"Kitten! So kike in miki wankan da kaina ko?"
"A'a dan Allah zanyi da kaina."
"Rantse bazaki k'ara ruwan sanyi akai ba toh idan na fita."
"Allah bazan k'ara ba wallahi."
"That's my kitten ki samu at least 7 minutes aciki it'll help in shaa Allah." Kai ta gyad'a mar sannan ya fice. Kayan jikinta ta tu6e sannan a hankali ta shiga tub d'in da k'yar ta iya ta zauna a ciki seda ta kusan minti takwas a ciki ta tashi lokacin har ruwan ya huce, watsa ruwa tayi, tayi brushing ta d'aura alwalan bacci ta fito.
Bayan ta gama shiri ta sanya kayan baccin ta da kanta yau amma bata tu6e hijabin ba seda ta iso gadon ta zauna. (Su Amal an fara sakewa da Afzal.)
"Zamu shafa miki man zafin ko?"
"Habib Albi is it necessary?"
"Yes it is Kitten bakiya son ki warke da wuri ne?" Shiru tayi bata kuma cewa komai ba har ya d'auko maganin ya dawo ya zauna k'afafun nata ya mik'ar akan cinyansa sannan ya d'an tattare rigan nata sama sede yana tattarewa tana sauk'arwa.
"Wai mey haka Kitten?"
"Toh kamun a haka mana seka d'age mun kayan ne" ta amsa tana turo mai baki.
"Nasan maganin fitsararren bakin nan ai" shiru tayi bata sake cewa komai ba har ya kuma tattare kayan sama "ina ne?" Ya tambayeta nuni da wajen tai masa sannan ya shafa maganin a wajen cewa da yayi bari ya murza ta sa wani d'ankren ihu.
"Wayyo Mami naaaaa!!!" Tare da cire hannunsa.
RANA D'AYA!
#RD
Love... King Miemiebee👄✨
[13/08, 09:36] +234 907 483 8352: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
July, 2018
beeenovels.blogspot.com
_Written by Miemiebee👄_
*PAGE 2⃣9⃣*
A rayuwa ba abinda yake rikita wa Afzal lisafi kaman sautin ihun Amal, kad'an ya rage be fad'i a k'asa ba. "Haba Kitten!" Yayi exclaiming yana murza kunnensa "So kike ki kurmantar da ni ne?"
"Toh Yaya haka ake shafawa mutum man zafi ne? Ba a hankali ake yi ba kasan mey? Bar shi ma kawai in shaa Allah ze warke da kansa."
"Raguwa kawai."
"Ayya Habib Albi amma ai kasan k'arfin mu ba d'aya ba ko?"
"Toh Baby tsaya in miki a hankali" da zaran yace ze murza seta sa ihu dan ba wasa ba cinyoyin nata sun mugun yin tsami, ganin fa ba bari zatayi ya shafa mata ba ga shi lokaci se tafiya yake kawai ya had'e hannayen nata gu d'aya ya danneta sannan ya shiga murzawa maganin, duk kalan ihun da takeyi hakan besa ya saketa ba seda ya murza ya kuma tabbata maganin ya shiga ciki tukuna.
Kuka take sosai harda majina yayinda cinyoyin nata suke yi mata zogi, ba k'aramin dariya ta basa ba amma ya moze, gaban mirror ya nufa ya kawo mata tissue "Hungo share hawayenki Kitten kukan ya isa haka" ko ta kansa batayi ba se lek'a k'afan nata take yayinda take jin yadda maganin ke shiga jikinta.
"Haba Baby naa yi hak'uri kinji? Yaya is sorry" Yayi maganan had'e da zama a gefenta yana k'ok'arin fara share mata hawayen, cike da takaici ta k'wace tissuen nan ta shiga sharewa da kanta bayan ta gama ya amsa yayi disposing "Let's sleep okay?" Ko kallonsa batayi ba taja pilonta izuwa k'arshen gadon ta kwanta, murmushi yayi sannan ya kashe musu wutan ya haura gadon ya kwanta. Pillonsa ya matsar kusa da nata had'e da ya6a hannunsa akan cikinta wanda ta cire da sauri. Mayarwa ya sakeyi itako ta sake cirewa.
"Haba my Baby yi hak'uri bazan sake ba" shiru ta mai bata amsa saba.
"I'm sorry bazan sake ba, yi hak'uri ki juyo mu kwanta my arms feels so empty without you."
"Haka kawai don kaga kafini k'arfi kayita mun mugunta ba, ni gobe zan koma gida gun Mami na."
"Laaa yi hak'uri beyi zafi haka ba Kitten" cike da dabara ya juyo da ita had'e da aza kanta akan k'irjinsa yana mey shafa bayanta a hankali. "Sannu kinji? Yi hak'uri, kika tafi ai bazan iya rayuwa ba" da haka har bacci mey nauyi ya d'aukesu duka.
Ko a washegari Afzal be bari suka fita d'in ba saboda gani da yake kar cinyan nata suji tafiya su k'ara yin tsami. Sosai ya tausaya mata barin ma idan yaga yadda take k'ingishi, banda wanka be sake bari ta koda d'aga tsinke ba.
Da k'yar Amal ta barsa ya fita siya musu abinci ita sam wai ita zatayi girki shi kuma ya rantse seta samu sauk'i tukun. Gidan Nazeefah ya fara nufa dan duba lafiyarta, shi kansa kunya yakeji ace tun da ya k'ara aure be lek'o uwar gidansa ya duba lafiyarta ba sede suyi magana a waya, yau yini na uku kenan.
Sallama yayi yayinda ya shiga parlourn kasancewar bata nan se ba wanda ya amsa. K'arisawa yayi ciki ya lek'a kitchen ganinta da beyi ba seya zarce d'akinta knocking yayi sannan ya bud'e zaune kan gado tana waya ya tarar da ita.
"Ya Rouhi!" Tayi exclaiming had'e da katse wayan, a guje ta mik'e taje tayi hugging nasa, "My Rabba'atul Bait I miss you" ya furta yana mey matse ta gam a jikinsa. Sun d'au tsawon lokaci a haka sannan ya sakota a hankali.
"Ashe zaka kewayo nan."
"Kuma wani irin magana kike haka Rabba'atul Bait?"
"Eh mana Ya Rouhi gashi tun da kayi amarya ka mance ni."
"Ba haka bane Rabba'atul Bait-"
"Toh yaya ne?" ta katse sa "Nayi maka uzuri a ranan farko amma ai yaci ace ka lek'o ni jiya koba haka ba?"
"I'm really sorry Nazeefah nasan nayi miki laifi but forgive me okay?"
"Ba komai dama nasan baka damu da ni ba."
"Inji waye?" Yayi maganan had'e da zaro wata k'aramar pack daga aljihunsa cike da rashin hak'uri ta tsaya tana kallonsa yayinda yake bud'ewa "Here I want you to have this" ya sanar da ita lokacin da ya bud'e pack d'in. Zobe ne me kyau aciki shigen irin na Amal sede akwai banbanci kad'an.
"Wow Ya Rouhi" ta numfasa hannunta ya d'ago a hankali ya sanya mata zoben sirr aciki. "Its so lovely Ya Rouhi thank you!" Ta sanar dashi had'e da brushing masa light kiss a baki yayinda ta kasa daina kallon yadda zoben ke yalk'iya, ko ba a tambaya ba ansan me tsada ne. "It's so beautiful."
"Don't mention Rabba'atul Bait so kin yafe mun?"
"Ai Ya Rouhi baya laifi."
"That's my girl, so ya kike?"
"Lafiya ya Amal?"
"Lafiyarta k'alau na barota tana bacci if not da mun taho tare."
"Ayyah I miss you Ya Rouhi."
"I miss you too Rabba'atul Bait I miss you even more."
"Anya kuwa? Kaida Amal ke d'ebe maka kewa."
"Ke daban ita daban Nazeefah ki daina had'a kanku kinji?" Kai ta gyad'a mar zalla "I hope you're okay ba wata matsala ko?"
"Babu just that I miss you."
"Na kusa dawowa ai."
"4 more days fa ya rage Ya Rouhi anya kuwa zan iya?"
"Zaki iya mana Rabba'atul Bait I trust you" ya fad'a yana placing mata kiss a kumatu. "Uhm kin tuna sanda muka tafi Umarah tare?" Kai tayi saurin gyad'awa "Good ina son mu tafi da 'yar uwarki itama."
"Ni kuma fa?" Wani irin kishi maras misaltuwa ne taji ya rufeta.
"Nazeefah ba mun tafi dake ba why not with Amal yanzu?"
"No Ya Rouhi bazan yarda ba, bayan ka gama yi mata sati kuma ka sake d'iban k'afa ku tafi Umara har zuwa yaushe? Ni shikenan ni kad'ai na zan na cigaba da zama a gidan nan? Kana ganin ka mun adalci kenan?"
"Nazeefah calm down please ya kike magana haka? Please calm down. It's not as if ban ta6a tafiya dake ba, in fact dake ma na fara tafiya to avoid circumstances like this ko kin manta kece Rabba'atul Bait d'ina and komi zanyi daga kanki zan fara? Please calm down ba komai aciki fa dan na tafi da Amal yanzu please understand."
Da fari tayi niyyan tada mai bori amma tuna kalamun Rumaysa na cewa "_Kar ki ta6a nuna masa kishinki duk abinda ya shafi Amal ki nuna mai baki da damuwa da hakan_" seta canza ra'ayinta na dole ta shiga yayyafa wa zuciyarta ruwan sanyi.
"Nazeefah nasan kishi da zafi but Allah ya riga ya k'addaro miki sede ki k'ara hak'uri akan wanda kikeyi wallahi I appreciate and respect you alot and I love you so much, kin cika uwar gida a duk inda ake neman hakan please don't change, it gives me pleasure when you and Amal are getting along. In shaa Allah idan Allah ya dawo damu lafiya daga baya zamu shirya dukan mu uku mutafi I promise you." Murmushi yaga ta sakar tana zagaye hannayenta a wuyansa "It's okay Ya Rouhi kayi hak'uri na amsan dana baka bisa ga rashin yin tunani, na amince kai da Amal ku tafi Umran tare after all ai nima ka kaini kuma addini yace kaso wa d'an uwanka abinda kaso wa kanka so kaman yadda naji dad'i da ka kaini Umaran itama Amal zanso taji dad'in nan." Da mamaki ya tsaya yana kallonta tunda ta fara maganan wai shin wannan Nazeefar da ya sani ne?
"Rabba'atul Bait" ya kirata se kuma ya kasa cewa komai. "Are you sure?" Shi kansa ya kasa amincewa da ita.
"Yes Ya Rouhi I'm totally cool with it, yaushe ne tafiyan naku?"
"Da saura dan bamu fara processing visan bama tukun I wanted to let you know on time."
"Thank you Ya Rouhi I love you so much."
"I love you even more Rabba'atul Bait" ya amsa had'e da kai mata light kiss.
"Toh bari zan koma."
"Bazaka tsaya kaci abinci ba?"
"Don't worry bana jin yunwa" har gun mota ta rakasa inda ya irga dubu goma ya mik'a mata. "Na mey kuma wannan Ya Rouhi?"
"Ki k'ara akan wanda na baki and keep it kinji?"
"Ya Rouhi kud'in beyi yawa ba? I barely even touched that one."
"Kin manta Ke Rabba'atul Bait ce?" Dad'i sosai taji tayi hugging nasa "Thank you so much."
"Don't mention" ya amsa had'e da d'agota "Ka gaishe da Amal idan ka isa."
"In shaa Allah you take care okay?" Kai ta gyad'a mar a nitse, seda taga ficewarsa sannan ta koma ciki wayarta ta d'aga ta dannawa Rumy kira.
"Babe yane?"
"Ba k'alau ba wallahi."
"Meya faru?"
"Ni dama tun farko na fad'a miki plan d'innan be min ba da bari kikayi naci uwarta tun kamin ta shigo."
"Keko meya faru haka?"
"Gashi ta samu d'uwawun zama wai har Saudi ze kaita."
"Kai dan Allah!"
"Wallahi yanzu dan Allah ya zanyi?"
"A ina kika jiyo labarin?"
"Yanzun Ya Afzal yazo ya sanar dani."
"Ina de baki nuna masa hankalinki ya tashi ba?"
"Kad'an ya rage amma sena sake calming kaina."
"Good this is to our benefit Babe."
"Ban gane ba kina jin zasuyi tafiya kina zancen benefit?"
"Ke dad'i na dake gajan hak'uri wallahi ki barsu suyi tafiyan, kinga idan suka dawo se mu nemo mata 'yar aiki muce kar aikin gida yayi mata yawa."
"Mey riban hakan? A dalilin uwar mey zan nemo mata 'yar aiki?"
"Ke kuwa calm down mana ai ba wai don tsakani da Allah bane, akwai yaran mey mana aiki guda biyu a k'auye zan yi ma uwar nasu magana ta kawo mun su kinga seki d'au d'aya mu bawa Amal d'aya itama, we will make her part of our plan duk wani mak'ircin da mukeso da ita zamuna amfani da infact kinga komi ma zefi zuwa mana da sauk'i tunda ita tana cikin gidan instructions kawai zamu na bata in shaa Allahu se mun fidda Amal kowa take daga gidan."
"Kai Babe ban san ya zanyi ba ke ba wallahi, Allah tsunduma mun ke cikin aljannah."
"Ai muddin ina raye baza kisha wuya ba barsu suje Saudi su dawo tashin hankali na nan yana jiransu."
"Toh kiyi ma matar magana tun yanzu da Allah ba se idan lokaci ya k'ure ba."
"Karki damu kede kawai ki kwantar da hankalinki kuma komin yaya kar ki nuna masa kishinki balle ki bud'e k'ofan da ze zarge ki."
"Toh shikenan Babe thank you."
****
Washegari su Afzal suka fita inda akayi wa Amal passort aka shiga yi mata processing, yini sukayi a wajen se wajajen biyar suka dawo gida. Washegari da safe still suka sake fita se wajajen uku suka bar wajen nan ma ba don an gama ba se don suna son su d'anyi ziyara. Gida gun Ummi suka fara zuwa, sosai Ummi taji dad'in ganinsu, hira suka ta6a kad'an sannan Afzal yace zasu tafi yana son su duba Nazeefah. Spices da dama ta d'ibo ta bawa Amal inda tayi godiya sosai. Daga nan suka wuce gidan Nazeefah. Dan munafirci harda hugging Amal, da fara'a sosai ta kar6esu tayi serving nasu drinks da snacks ba wanda zece wai duk fara'an nan na munafirci ne se hira suke su uku suna dariya. Da suka zo tafiya kuma Nazeefah harda cewa wai Afzal ya bar Amal yaso se dare yazo ya d'auketa.
A kwana na uku suka gama processing International passport na Amal sannan suka shiga yin na visansu, shi wannan d'in be basu wuya ba kasancewar akwai abokin Afzal da ke aiki a wajan, yanzu jira kawai suke idan visan ya fito su fara shirin tafiya.
Afzal na iya rantsewa wannan sati d'aya da yayi tare da Amal shine one of the best weeks of his life, ba fad'a ba tashin hankali ba fargaba ba komai se zallan soyayya kawai. Tabbas son Amal daga sama aka turo masa shi, komin yaya yayi baze ta6a iya had'a soyayyarta da na wani ba bayan iyayensa, soyayyarta a jininsa yake idan ba ita baya jin ze iya rayuwa. A gobe Allah ze kai su k'arshen sati inda kwanan Afzal ze k'are. Tunda Amal taga ya shiga tattara kayakinsa jikinta yayi sanyi se taji gabad'aya bata so ya tafin dan yadda suka saba na sati gudan nan. Sosai Afzal ya saba mata da zama ajikinsa muddin yana gida toh fa se ajikinshi take zaune take kwanciya, ya zata yi yanzu idan ya tafi? Gaskiya Nazeefah tayi na mijin k'ok'ari da har ta bar mata Afzal na sati guda ita kwana biyu kacal zeyi ya sake dawo mata amma seji take kaman ta bisa.
"Kitten bazaki tayani shirya kayakin nawa ba?" Ya tambayeta yayinda yake nannad'e boxers nasa yana sasu cikin wata k'aramar akwati. Bata 6oye mai ba tace "Bana son ka tafi Habib Albi."
"Are you gonna miss me?" Ya kewayo yana tambayarta. Kai ta gyad'a masa a hankali cike da shagwa6a.
"Toh ai tafiya ya zama dole Kitten kwananki na sun k'are anan ko bakiya son inje in samu 'yar uwarki?"
"Ina so mana kawai zanyi missing naka ne" ta sanar da shi.
"I can't even tell how am gonna miss you Kitten but two days kawai zanyi in sake dawowa."
"Mesa baza ka na mana kwana d'ai-d'ai ba toh?"
"A'a bibbiyun de zefi Kitten d'ai-d'ai akwai gajiya."
"Toh shikenan" ta furta ba walwala tattare da ita.
"Come here" ya kirata batayi gardama ba ta mik'e taje ta samesa akan cinyarsa ya zaunar da ita. "Bar had'e ran haka kinji?" yayi maganan yana shafa fuskanta "Two days kacal zanyi in dawo in shaa Allah" Kai ta gyad'a mar a hankali sannan yayi crashing lips nasa akan nata kissing her slowly with tender touches. Na d'an lokaci ya saketa, nan ta fad'a jikinsa, hannayensa ya zagaye a bayanta yana shafata a hankali.
"Kin san wani abu?" Kai tayi saurin kad'awa tare da d'ago kanta daga jikinsa. Jan bakinta daya kama bakinsa ta shiga goge mai a hankali.
"Muyi wanka tare yau."
"Wanka tare kuma Habib Albi?" Ta tambayesa had'e da zaro ido.
"Yes Kitten aren't you gonna miss me?"
"Of course I'll amma wanka tare kuma..."
"Toh ba Annabi ma nayi da matansa ba" shiru tayi bata ce komai ba "Ko baki sani ba?"
"Na sani" ta furta ciki-ciki.
"Good I want us to bathe together too just me and you Kitten" Kanta ta sauk'ar akan k'irjinsa had'e da zagaye hannayenta a bayansa "Ni kunyanka nakeji" ta sanar da shi murmushi ya sakar had'e da zagaye hannayensa a bayanta shima.
"Zaki daina in shaa Allah" taya shi tayi ya gama shirya kayakin nasa, bayan nan suka tu6e suka d'aura towel sannan suka shiga bayin a tare. Shi da kansa ya sirka musu ruwan d'umin dam yacika bathtub d'in sannan ya zuba shower gel aciki ya kad'a seda yayi bubbles (kumfa.)
"Toh ki fara shiga."
"Habib Albi..." ta furta cike da shagwa6a tana turo mai baki. "Ni ka fara shiga."
"No Kitten after you."
"Toh ka juya bayanka."
"Kitten wai mey haka?"
"Ni de ka juya bayanka kawai" murmushi ya sakar sannan ya juya d'in "Ni ban yarda ba, nasan sena tu6e zaka juyo ka kalleni ni bazan yarda ba."
"Kitten don't you trust me?"
"I do."
"Toh ki shiga."
"ka rantse bazaka juyo ba."
Dariya yake sosai yace "Na rantse toh shikenan? Yi ki shiga" seda ta k'are masa kallo sannan a hankali ta sauk'e towel d'in da sauri ta k'arisa ta shiga cikin tub d'in, yana jin k'aran splash na ruwa ya juyo se ganinta yayi ciki se faman tattara kumfan take a jikinta yadda baze samu ya gane mata jiki ba."
"There" ya furta yana admiring nata. "Saura ni ko?" Kai ta gyad'a masa a hankali acewanta ze bari seta juya kanta ta kafin ya shiga kawai taga ya tu6e a gabanta kai tayi saurin kawarwa shi yake amma ita ke ji mai kunya. A hankali taji ya shiga ya sanyata a tsakankanin k'afafunsa. Kanta ya kwantar a jikinsa, da zaran ya ta6ata se tayi wincing haka suka tayi har seda ta saba da hannunsa na yawo a jikinta. Hira da wasa suka tayi cikin tub d'in kaman ba gobe, chan Amal tace tana jin bacci don haka suka wanke jikinsu suka fito kayan baccinta ta sanya shima yasa gajeren wandonsa sannan suka haye gado suka kwanta. Tun ranan da abu ya shiga tsakaninsu Afzal be sake nemanta ba se yau, dalilinsa kuwa befi baya son ya sake fama mata ciwon ta ba. A hankali a hankali yana tarerayarta da kalaman soyayyarsa har ya rabata da kayan jikinta, sosai suka gamsar da junansu ranan daga k'arshe suka fad'a bacci.
Tunda suka koma baccin Asuba basu tashi ba se wajajen sha d'aya nan ma tare suka sakeyin wankan sannan suka fito suka shirya suka nufi kitchen suka had'a breakfast.
Rice and stew had'ad'd'iya ta girka musu for lunch bayan sun k'are ci ya tattare wajen sannan yajata sukaje parlour inda ya zaunar da ita akan cinyarsa kaman kullum.
"Kitten ban ta6a ganin kin kunna TV a gidan nan ba shin bakiya kallo ne?"
"Inayi" ta amsa.
"Meyasa bakiya yi toh?"
Bata mai k'arya ba tace "Ni gudu nake kar na rikitar da wani abun ban ma iya kunna TV'n ba."
"Toh ai sekice in koya miki Kitten."
"Toh ka koya mun" dad'i sosai Afzal yakeji yadda Amal ta sakewa da shi yanzu.
"Mik'o remote d'in toh" bayan ta mik'o masa ya sake zaunar da ita kan cinyansa sannan ya shiga nuna mata.
"Akwai tashan Sunna TV ko Manara?Ina son ina jin wa'azi."
"Masha Allah that's very thoughtful of you Kitten" scrolling yayi ya kai mata kai "Shikenan?"
"Thank you Habib Albi."
"Don't mention Kitten" mik'awa yayi tare da pecking nata a gefen bakinta.
"Se microwave d'innan shima ka koya mun amfani dashi incase zanyi heating abinci baka nan." Kitchen d'in suka nufa ya nunnuna mata yadda akeyi sosai kuwa ta fahimta. Wajajen shida na yamma Afzal yace ze tafi Amal gabad'aya bata son ya tafi se gani take kaman idan ya tafi baze sake dawowa ba. "Bazaki rakani ba Kitten?" Hannunsa ya mik'a mata tana sanya nata a ciki ya mik'ar da ita har waje suka kai bayan yasa akwatin nasa acikin motar ya kewayo kawai me ze gani Amal harda 'yar k'wallanta.
"Ohh Kitten" janyota yayi had'e da kwantar da kanta a k'irjinsa yana shafa kanta "Shhhh! Please don't cry, zan dawo ai kukan ya isa haka kinji? Bar kukan haka."
"I'll miss you Habib Albi."
"I'll miss you even more Baby" ya fad'a had'e da d'agota. K'aramin fuskanta ya rik'o cikin hannayensa sannan ya shiga kissing tears nata yana share mata su "Ya isa kinji?" Kai ta gyad'a masa a hankali had'e da aza hannunta kan nasa dake rik'e fa fuskan nata. A hankali ya mik'a yayi capturing lips nata, wani irin mugun kiss mey ratsa jiki ya bata, be sake ta ba seda ya tabbata ya gushar da duk wani tsoron dake tattare da ita.
"I love you Hun" ya sanar da ita lumsassun idanunta ta d'ago a hankali ta aza kan kyakkyawar fuskansa "I love you too Habib Albi" hannunta ta sauk'e kan lips nasa tana goge masa jan bakinta daya kama.
"Wani abu ne?" Ya tambayeta.
"Lipstick d'ina ne ya kama ka tsaya in goge kar Rabba'atul Bait ta gani ka had'a kanmu." Murmushi ya sakar mata "Toh goge ina jiranki."
"There ya fita" ta sanar da shi had'e da sauk'e hannunta.
"Ina zuwa" yace da ita cikin motansa ya shiga ya fito da wata envelope "Ga wannan ki rik'e incase wani need yayi arising" yace yana sa mata envelope d'in cikin hannu.
"Habib Albi na mey kuma? Please ka rik'e" ta fad'a tana k'ok'arin miyar mai. Hannun nata ya rik'e "Shhh naki ne kinji? And don't hesitate to call me if you need more I'm just a call away."
"Habib-"
"Please Kitten spend it, it's all yours."
"Thank you Habib Albi Allah k'ara bud'i."
"Ameen koma ciki toh."
"Ni senaga ficewanka tukun" be sake yin musu ba ya shige motan waving suka ma juna yana kallonta ta mirror har seda mai gadi ya kulle gate sannan ta dawo ciki. Tuk'i yake amma hankalinsa gabad'aya na akan Amal.
****
"Oyoyo Ya Rouhi" Nazeefah ta ruga aguje had'e da rungumesa tana yi masa sannu da zuwa lokacinda ya shigo parlourn. Da k'yar ya iya ya ajiye akwatin nasa sannan ya d'agata chak a sama.
"Rabba'atul Bait you look so beautiful" ya sanar da ita tare da sauk'e ta, ba k'arya kuwa tayi kyau, tasha makeup sosai ga kitso da lallenta duk masha Allah.
"Duk kwaliyan nan ma ni ne?"
"Eh mana Ya Rouhi."
"Gaskiya dole na biya kud'in kwalyan nan kin ganki kuwa?"
"Kai Ya Rouhi banda zolaya."
"Allah fa dagaske kinyi kyau sosai."
"Thank you sweetheart" jakan nasa ta tsuguna ta d'aga suka k'arisa d'aki "In had'a maka ruwa ka watsa?"
"Yes please" nan da nan ta sirka mai ruwa ya shiga ya watsa sannan ya fito da alwala. A gida suka idar da sallah bayan nan ta jasa dining inda tayi serving nasa fried rice and chicken da coleslaw da ta had'a sosai abun yayi armashi se praising girkin nata yake kaman ba gobe. Chan dare bayan duk sun watsa ruwa Nazeefah ta kwantar da shi tana mai massage (tausa) daga nan suka wula duniyar ma'aurata.
Ita da kanta ta shirya Afzal office washegari kasancewar hutun sati d'aya da aka basa ya k'are se wani tarerayarsa take abinda bata ta6a yi masa ba ma ta fara yi yanzu duk don ta burgesa, sosai yake jin dad'in kulawanda yake samu daga gareta har gun parking lot ta rakasa ta basa good luck kiss sannan ta dawo ta koma bacci abinta.
Afzal na isa office bayan ya kammala necessary abinda ya kamata ya kira Kitten nasa ba k'arya yayi missing nata. Tana cikin bacci taji rurin wayanta cike da gyangyad'i ta mik'a hannu ta d'aga ko duban waye batayi ba.
"Halo?" Ta furta cikin sleepy voice nata.
"Good morning my adorable Kitten" taji muryan Afzal.
"Habib Albi" ta fad'a cike da mamaki batayi tsammanin ze kirata early this morning ba.
"Na'am Kitten ya kike?"
"Lafiya" ta amsa tana hamma, yana jin muryanta ya gano bacci take shi ya d'agata.
"Na tada ke daga bacci ko?"
"A'a kar ka damu ina kwana?"
"Lafiya kwanta kiyi baccinki kinji? I'll call you back later."
"Okay Habib Albi."
"I love you."
"I love you too" da haka ta katse ta koma bacci. Wajajen goma ta tashi wanka ta farayi sannan ta had'a breakfast nata da na mai gadi. Bayan ta gama ci tayi sharanta da wanke-wanke ta koma d'aki ta tsara kwalyanta ta baza gashinta a baya sannan ta yima Afzal video call. Yana cikin aiki a office ya ga shigowan call d'in da mamaki ya tsaya yana kallon screen d'in wai Amal da ya sani ne take yi masa video call? Lallai! be 6ata lokaci ba ya d'aga da kyakkyawan fuskanta ya soma cin karo.
"Wow!" kawai ya ke iya furtawa.
"Good morning Habib Albi" ta gaishesa.
"Good morning my adorable Kitten."
"Ya kake? Ya office?"
"Alhamdulillah you look amazing Kitten" ko kyafta ido ya kasa se kallonta yake kaman ze zak'ulota ta wayan.
"You're not looking bad yourself Habib Albi yaya Nazeefah?"
"Lafiyarta k'alau tana gida ba wani matsala ko?"
"Ko kad'an."
"Kinyi breakfast?" Kai ta gyad'a masa "Mey kika ci?"
"Toasted bread da tea."
"Hmm interesting baki tambayeni mey naci ba ni."
"Bana son inyi shisshigi ne Habib Albi."
"Toh ask me" ya buk'aceta yana had'e rai. Murmushi tasa wanda ya mugun k'ayata ta.
"Toh Habib Albi mey Rabba'atul Bait namu ta girka maka?"
"Fries and omalet."
"Kaifa d'an gata ne Habib Albi."
"Really? Ai kema 'YAR GATA CE Kitten."
"Gata na be kai naka ba ai."
"Allah ko meyasa kikace haka?"
"Because ka na da mata biyun da zasu iya kwantar da ransu dan soyayyar da suke maka."
"Really? Kina so na har haka Kitten?"
"Of course Habib Albi kaman yadda Rabba'atul Bait taka keson ka ko fiye da haka ma."
"I'm impressed yau Kitten ce take admitting feelings nata haka kode dan missing d'ina da takeyi ne?"
"Ko ba don hakan bama Yaya cikin d'an satin nan da mukayi tare na gano you're so special to me."
"So you are to me, you're my long lost medallion Baby I love you so much."
"I love you too Habib Albi I'm sorry if it took me long to admit."
"I was ready to wait until eternity for you Darling so ki daina bani hak'uri kinji?"
"Toh Habib Albi bari in barka haka kayi aiki take care okay?"
"I'll and you too" kiss yayi mata blowing ta screen d'in ita kuma tayi pretending kaman ta kama tayi placing a kumatunta da haka tayi stopping call d'in. Murmushi Afzal yatayi shi kad'ai a office d'in wajajen sha biyu sega call d'in Nazeefah be hankara ba ya d'aga.
"Halo my Rabba'atul Bait."
"Na'am Ya Rouhi ya kake?"
"I'm good you?"
"Lafiya ya office?"
"Very boring I'm missing you."
"Same here Baby mey kakeso kaci for lunch?"
"Yau kuma Rabba'atul Bait? Ba ke kike yin komai ba?"
"A'a kai nakeso kayi deciding yau so what do you want to eat for lunch Baby?"
"Anything will be fine."
"No specify."
"Let's see..." ya fad'a yana nazari "cous-cous da miyan yakuwa."
"Oh! Ya Rouhi kowa na bin dama kai kana hagu yaushe aka fara cin cous-cous da yakuwa?"
"Ni haka nake so bana son tuwo."
"Toh Baby consider it done."
"Thanks babe."
"Don't mention seka dawo I love you."
"I love you too take care" nan ta kashe. Maida wayan yayi ya cigaba da aikin gabansa yayinda kalamun Amal suka shiga dawo masa _Because ka na da mata biyun da zasu iya kwantar da ransu dan soyayar da suke maka._
Tabbas tayi gaskiya sabida ze iya rantsewa akan kalan soyayyar da Nazeefah takeyi masa fatansa kawai Allah ya basa ikon kwatanta adalci ne a tsakaninsu.
Be zarce ko ina ba se gida daya taso daga office inda Nazeefah ta kar6esa, sosai yaji dad'in kwana biyun da yayi mata, ba fad'a bale tashin hankali. Duk abinda yakeso shi Nazeegah ke masa, ana gobe ze tafi bayan ya dawo daga sallan Isha suka shirya tsaf suka ci abinci a waje daga chan suka wuce 3G gallery yasan Nazeefah da son jaka duk sanda yake son farinta mata nan d'in kawai yake kaita tayita kwasan jakukkuna. Yau k'waya uku ta kwasa designers masu kyau.
"Yau uku ya isheki kenan?"
"Uhm" ta gyad'a masa kai tana murmushi "Bari in d'auka wa Amal itama toh." Wani irin kishi taji ya tokareta a rayuwa ba abinda ta tsana kaman taji yana maganan Amal kokuwa yana cewa zeyi mata wani abun. Halan ya karanci yanayinta se ji tayi yana tambayarta "Ko kar a saya mata ita?"
"A'a Ya Rouhi ka d'auka mata please" murmushi ya mata sannan ya mik'e wata purple jakar channel mey chain ya d'auka mata da ja saboda Amal na son wannan colors d'in se da wani bak'in valentino. Nazeefah tsabaragen kishi ita fa ta za6i nata da kanta amma ganin wanda ya za6a wa Amal se taga gabad'aya natan ma ya bar mata kyau, taji na Amal d'in kawai takeso amma ya ta iya? Idan har tana son cimma burinta dole tayi hak'uri, bayan ya biya kud'in aka sanya musu a seperate leda sannan suka taho gida.
Washegari da yazo tafiya Nazeefah harda munafurcin basa wani turaren wuta wai ya kaiwa Amal Mummy ce ta siyo mata shine tayi tunanin ta raba musu. Sosai Afzal yaji dad'i had'e da yi mata godiya itama har gun motarsa ta rakasa sannan ta dawo ciki bayan daya sallameta. Da goshin Maghrib ya iso gidan Amal, itakam don yadda tayi missing nasa ta kasa jira ya shigo ciki tun daga waje taje taransa, yana fitowa daga motan ta fad'a jikinsa, hannayensa ya zagaye a bayanta yana mey maste ta ajikinsa yayin da yake shak'an daddad'an k'amshin turaren jikinta.
"I miss you Habib Albi" ta sanar da shi.
"I miss you even more My adorable Kitten" yace had'e da d'agota daga jikinsa. "Masha Allah, gaskiya Allah ya miki baiwan kyau Kitten you look... you look" yama kasa k'arisawa se kallonta kawai yake.
"Beautiful? Is that the word you're looking for?"
"Yes Kitten you're looking spectacularly beautiful."
"Thank you Habib Albi welcome home."
"Thanks Baby" ya amsa had'e da juyawa cikin motan wata leda ya ciro nan ta mik'a hannu zata kar6a.
"A'a Kitten ze miki nauyi."
"Haba Habib Albi."
"Bari zan rik'e kinji?"
"Toh shikenan tunda kace haka" nan suka k'arisa ciki, se faman k'amshi gidan yake, ya fad'a turaren wutan Amal daban yake dana kowa ya rasa ya take cire hayak'in tabar k'amshi kad'ai wataran seya gwada tambayarta shima ya koya wa Nazeefar sa. Ruwa ta had'a masa amma ya rantse shi idan ba da ita ba bazeyi wankan ba itako bata dad'e da yin wanka ba bayan nan so yake ta goge wannan kwalyar da tayi duka? Yau fa harda foundation ta shafa kaman yadda Maamah ta koya mata gaskiya baze saku ba.
"Habib Albi please mana Maghriba fa tayi."
"Toh ki taho muyi wankan tare semuyi sallan."
"Ba lokaci."
"Toh shikenan na fasa."
"Toh yanzu so kake in goge kwaliyan nan gabad'aya?"
"Ba lalle ba."
"Toh an ta6a yin wanka kwalya be gogu bane?"
"Matso kiga" matsowan tayi ba gardama kafin ta gane meyake shirin yi kawai taji sauk'an lips nasa akan nata, be saketa ba seda ya tand'e jan bakin tas ga wani k'amshin berries da jan bakin keyi, ko ragowa be bari ba. "There kinga yanzu babu so let's bathe."
Wajen mirror ta nufa da mamaki kuwa taga ya tand'e jan bakin tas.
"Haba Habib Albi! Haba!"
"Kefa kikace bakiya son kiyi asaran kwaliyar ki."
"Toh yanzun ba asaran jan baki kayi mun ba?"
"Ba asara bane tunda Habibin ki ne ya tand'e koba haka ba? Taho to muyi wankan."
"Kaga yanzu Maghrib yayi kabari idan mukayi sallah kaci abinci ka huta semuyi wankan k'arshe?"
"Ni yanzu nakeso."
"Habib Albi bakaji kiran Sallah ba? Kuma kaga wankan mu tare ai yana d'aukan lokaci koba haka ba? Let's pray first okay?"
"Okay darling duk abinda kikace taho muyi alwalan toh" ba musu ta k'arisa suka shiga bayin suka d'aura alwala suka fito sukayi sallah, bayan nan taja hannunsa izuwa dining inda ta cike kan table d'in dam da abinci kala-kala ga smoothies har kala biyu aldeb da zo6o wow! His Amal is so extra. Kaman yadda suka saba cin abinci a plate d'aya hakan ma sukayi yau sede yau Amal tace ita zata basa beyi musu ba ya barta, haka ta basa ta bawa kanta har suka k'oshi. D'aki suka koma inda ya d'auko ledan daya shigo da shi d'azun ya ciro jakukkunan "Gashi wannan naki" ya fad'a yana tura mata su gabanta.
"Duka Habib Albi?" Ta tambaya da mamaki.
"Yes Kitten."
"Wow!" Ta numfasa had'e da d'ago jan duk shi yafi yi mata kyau kodan tafi son abu ja ne. "Habib Albi basuyi yawa ba?"
"Not when they're to be presented to a damsel like you Kitten."
"Thank you so much Habib Albi kai da kanka ka za6a kuma?"
"Mey kika ga?"
"Ai naga ba na aibantawa ne aciki, ace guda d'aya zan d'auka ciki toh sede ruwan ido ya kasheni don duka sunyi kyau wallahi."
"Ni na za6a mana."
"Kai Habib Albi anya kuwa ba wata mata kasamu acikin shagon kace ta za6a maka ba?"
"Kina iya kiran Nazeefah ki tambayeta a gaban ta na d'iba miki."
"Ahh na yarda gaskiya mijin nawa ya iya za6i."
"Abba ma seda yace haka ranan farko da ya fara sanya ki a ido."
"Kai Habib Albi."
"I'm telling you."
"Wai meyace?" Ta tambayesa cike da jin dad'i.
"Mey kuwa? Ai kaman yadda nake fad'a miki cewa yayi you're very beautiful."
"Allah sarki Abba kasan ko jiya ma seda ya kirani wallahi naji kunya sosai tunda akayi auren ban nemesa ba se gashi kwatsam ya kirani."
"Ayyah wai mey gaisuwa?"
"Eh bayan nan kuma yace duk sanda ka mun abinda be gameni ba kar inji tsoro in kirasa in sanar da shi yace ze zane ka."
"Abban dey?!" Yayi exclaiming.
"Sosai ma kuwa" ta d'age mai gira tana faman dariya.
"Toh bani jakana na fasa bakin bani kayana" tattarewa tayi da wuri ta matsesu a jikinta. Hannu yasa zey k'wace ta hanasa cakulkuli ya shiga yi mata nan ta fad'a kan gadon da baya yayinda ya d'ale kanta se faman yi mata cakulkulin yake tana dariya.
"Ha- Habib Alb- Habib Albi ya isa please wallahi cakulkuli k'anin mutuwa ne" ta samu ta fad'a da k'yar dan dariya har hawaye take se anan ya ga daman sake ta. Fuskansa ya matso gab kusa da nata sannan ya share mata hawayen "Yanzu in Abba yace ze zaneni seki barsa Kitten?" Kai ta gyad'a mar tana dariya.
"Ha in tattara kayakina in koma gun Rabba'atul Bait d'ina dama chan nasan ba sona kike ba" kafin ya sauk'a daga kanta tayi sauri ta janyo hannunsa had'e da zagaye hannayenta a wuyansa.
"Kai baka san wasa bane Habib Albi? Ai wasa nake maka, shi kansa Abba acikin raha ya fad'a kuma idan ma ta kama ze zane ka d'in ai sede in shiga a zaneni a madadinka I wouldn't want anything to harm you Habib Albi" a hankali kalaman nata suke kwanciya a kan zuciyansa.
"How much do you love me Kitten?" Ya tambayeta cike da jin dad'in kalamunta yayinda yake shafe kan lips nata da yatsansa.
"10 on the scale of 10 Habib Albi, a shirye nake da in rasa farincikina saboda naka, rayuwata gabad'aya zan iya sadaukarwa dan inceto naka I love you so much." Yanzu kam ya kasa 6oye farin cikinsa "I'm ready to sacrifice the last kobo I have to make you happy Kitten, I will travel a thousand miles without food or water just to be with you, this's just a little out of how much you mean the world to me."
"Thanks Habib Albi" matso da fuskansa ya sake yi ta hanyan rufe duk wani gab dake tsakaninsu kissing k'asan hancinta yayi sannan a hankali ya gangaro kan lips nata da suka fi masa dad'i fiye da komai a duniyan nan ya shiga yin gadamansa dasu.
RANA D'AYA.
#RD
Love... King Miemiebee👄✨
[13/08, 09:36] +234 907 483 8352: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
August, 2018
beeenovels.blogspot.com
_Written by Miemiebee👄_
*PAGE 3⃣0⃣*
Getting enough of her strawberry lips, a hankali yayi breaking kiss d'in had'e da mik'ar da ita suka zauna "Ya kamata kayi wanka Habib Albi akwai office gobe."
"Kin manta tare zamuyi wankan ne?"
"Toh tashi muyi ka samu ka huta ka kwanta."
"Ni massage (tausa) nakeso."
"Komey kakeso zanyi maka Habib Albi yanzu de ka mik'e tukun."
"Kafin nan" yayi maganan had'e da zaro roban da Nazeefah ta basa akan ya bawa Amal "Ga wannan daga gun 'yar uwarki" amsa tayi tare da kaiwa hancinta don shinshinawa "Wow turaren wuta!" Ta fad'a cike ca jin dad'i. "Allah sarki Nazeefah yanzun zan kirata inyi mata godiya kafin in manta."
"Yakamata kam."
"D'an mik'o mun wayana" nan da nan ta kira Nazeefah tayi mata godiya inda ita kuma ta nuna mata ba komai.
"Yauwa Kitten may I ask you something?" Ya tamabyeta bayan ta ajiye wayan.
"Anything Habib Albi."
"Shin ya kikesa turaren wutan kine?"
"Mey kaga?"
"Unlike na Ummi da Nazeefah naki hayak'in baya yin yawa se k'amshi zalla."
"LOL Habib Albi kai baka san shuwa da turaren wuta bane? I think tun ina shekara goma na fara kunna turaren wuta."
"Nasani I'm just curious so tell me."
"LOL okay ni ba se dab zaka dawo nake sawa ba, timing lokacin da zaka shigo nakeyi se in kunna 20-25 minutes before haka."
"Window a kulle ko a bud'e kike sawa?"
"Ina kulle windows in sauk'ar da curtains, idan nabi gidan da turaren gabad'aya se in bashi kaman 10-12 minutes ya kama haka sannan in bud'e windon kad'an in kunna fan hayak'in ya fita, yana d'an fita se in sake kullewa kar k'amshin yabi iska shima a hankali har hayak'in ze watse gabad'aya yabar k'amshi."
"No wonder mana kullum inyita mamaki."
"Yanzu ka gane?"
"Yes Kitten" ya amsa nan da nan suka d'aura towel suka nufi bayi inda sukayi wanka, sun dad'e aciki sannan suka fito d'aure da alwala. Sallan isha suka idar suka kammala Azkhar nasu sannan suka sanya kayakin baccinsu. A hankali ta kwantar da Afzal akan k'afarta sannan ta shiga yi masa tausar, kasancewar hannayen nata sirara suke kuma k'anana se ji yake kaman cakulkuli takeyi masa. Duk lokacin da ta ta6asa seya sa dariya haushi ya bata k'arshe ta turesa daga jikinta.
"Ni na fasa yi" ta fad'a a fusace had'e da gangarawa wajenta. Bin ta yayi ya haye kanta ya shiga showering mata kisses tun daga wuya har izuwa fuska yana teasing nata sannan ya mik'a hannu ya kashe musu wutan d'akin. Xxx
Washegari bayan sun idar da sallan Asuba ta taya Afzal shiri dukda cewa da yayi karta damu ta koma bacci ze iya shirya kansa, seda ta rakasa har waje sannan ta dawo ciki ta koma bacci. Kaman yadda yake kiran Amal kowace safiya da yake gun Nazeefah haka ma ya kira Nazeefar yau suka gaisa seda ya tabbata bata da wata matsala sannan sukayi sallama.
Wajajen k'arfe biyu Amal ta d'au waya ta kira Afzal bayan ta tamabayesa ya aiki tayi gyaran murya "Habib Albi se nawa kake tashi daga office yanzu?"
"Wani abu ne Kitten?"
"I miss Mami and Papi" ta sanar dashi.
"Kina son kije ki dubasu?"
"Eh."
"Toh ba ga motarki ba?"
"Toh Habib Albi na iya tuk'i ne?"
"Haka kuma fa semun koya miki a hankali."
"Nifa tsoron tuk'i nake."
"Toh haka zaki ta kallon motan naki Kitten?"
"A'a in zaka iya seka nemo min driver yana kaini duk inda nakeso amma nikam bazan iya tuk'i ba."
"Me zai hana ki Kitten? We'll discuss that later so kikace kinason ki duba su Mami?" Kai ta gyad'a wane yana gabanta.
"Alright bari inyi clearing schedule d'ina se in taho muje."
"Dagaske Habib Albi? Ban shiga ma hak'k'in office ba ko?"
"Ai aikin office na zuwa ne a bayan farin cikin Kitten d'ina so I'll be home in a jiffy kinji?"
"Toh Habib Albi seka zo I love you."
"I love you most Kitten" da haka ta katse wayan. Girkin nata tayi sauri ta kammala ta zubawa mai gadi nasa sannan ta shirya kan dining. Bayan nan ta tsaya yin shawara ta kunna turaren wuta ne kota fara shiga wanka daga k'arshe de ta fara da shiga wankan. Bayan ta fito ta shafa mai ta tsara kwalyarta sannan ta sa wata bak'ar lace da touches and stone works na golden sannan ta fice parlour. Show glass nata ta bud'e ta ciro kwalban data juye turaren wutan da Nazeefah ta bata, haka kawai taji bari ta gwada kunnasa taji k'amshinsa yau. Gawayinta na kamawa ta zuba cikin kasko sannan ta barbad'a turaren akai se sauri take kar Afzal ya taho yanzu ya tarar da hayak'i. Tana zuba turaren akan gawayin kawai wani irin hayak'i ya shiga tashi tunda take bata ta6a ganin abu haka ba hurawa ta shiga yi a hankali amma ina se k'aruwa hayak'in yake har yana sanyata tari, shin wani irin turaren wuta ne wannan Nazeefah ta bata? Gashi nan da nan ya k'one ya fara bada warin k'onuwa da hanzari ta fita waje dashi ta k'ofan kitchen ta zubar.
Sabon gawayi ta d'ibo zata had'a kwatsam taji k'aran motan Afzal sosai gabanta ya fad'i parlourn ta dawo da wuri amma ta rasa ta ina zata fara fidda wannan uban hayak'i. Inda ma ace hayak'i ne zalla da da sauk'i amma ga warin k'onuwa gabad'aya ya d'umama gidan yau ta shiga uku. Afzal na bud'e k'ofan parlourn yayi sauri ya koma baya dan wani irin hayak'in dayaci karo da.
"Subhanallahi!" Yayi exclaiming da sauri had'e da zaro hanky yana toshe hancinsa. "Kitten ki fito kafin hayak'in ya miki illa" yace da ita yana mamakin ya akayi take tsaye har yanzu cikin tsabar hayak'in nan. "Kitten hurry!" kamar wacce k'wai ya fashe ma aciki ta fito ta samesa a waje.
"Ya haka meya faru?" Yayi saurin tambayanta.
"Yaya-" se kuma tayi shiru, gabad'aya ta kid'ime.
"Abu ne ya k'one miki?" Kai zalla take iya kad'a mai "Ya gidan da hayak'i haka toh? Ga kuma warin k'onuwa." Har ta bud'e baki zata sanar da shi turaren wutan da Nazeefah ta bata ne ba kyau se kuma ta tuna nasihan da Mami tayi mata na cewa;
_Ko da wasa karki fara ki had'a kansa da na matarsa, komin mey ta miki kar kice zaki kai k'ararta gunsa idan har kece da gaskiya toh Allah da kansa ze wanke ki dan shi ba azzalimin bawa bane_ wannan lafazi yasa ta canza ra'ayinta tayi shiru.
"Yes??" Ya sake tambayarta jin tayi shiru.
"Ermm... Naje ina kula da girki ne se har turaren ya k'one akan gawayin I'm sorry."
"Shikenan ba komai ina de baki k'one ba?"
"A'a."
"Shikenan don't worry mu zauna anan se hayak'in ya ragu kafin mu shiga."
"Barin shiga in bubbud'e windows d'in in d'aga labule zefi fita da wuri."
"So kike ki shak'i wannan uban hayak'i har seya miki illa Kitten?"
"Toh Yaya in ba haka ba baze fita da wuri ba har ka samu kaci abinci mu fita."
"Toh muje in tayaki se muyi da sauri."
"A'a ka jirani anan."
"No Kitten I insist" haka suka k'arisa ciki suka shiga bubbud'e windows d'in, da hanky mak'ale a hancin Afzal amma dukda haka wari da hayak'in be barsa ba, gabad'aya jikin Amal yayi sanyi sam ba haka taso abinta ba. A waje suka zauna seda hayak'in ya ragu sannan suka koma ciki bin parlourn tayi da turaren Khumra don kashe warin. Bayan ta sirka masa ruwa yayi wanka suka fito dining don cin abinci sede tun d'azun yake kallonta gabad'aya tayi shiru ba walwala tattare da ita.
"Kitten?"
"Na'am?" Ta amsa tana d'ago kai.
"Yau achan zaki zauna?" Kai ta gyad'a zalla "Why?"
"Yaya I'm sorry."
"Why? What for?"
"For the inconvenience wallahi ban san ya akayi turaren ya k'one haka ba please forgive me."
"Ohh Kitten!" Ya numfasa "Come here" ba gardama ta mik'e daga kujeran nata ta samesa, a cinyarsa ya zaunar da ita "It's really okay dear, kullum kinayi me kyau dan an samu akasai yau kuma seya zama abun magana? Kidena damun kanki kinji? Ni baki mun komai ba."
"Thank you" tace dashi cikin sanyi, shi da kansa yayi serving nasu sannan ya shiga feeding nata seda suka k'oshi tukun suka jira La'asr yayi suka yi sallah suka shiga shiri, se wajajen biyar da rabi suka dawo gida se hira Mami take jansu da.
Bayan sallan Maghrib Amal da Afzal suna zaune a parlour Afzal ya mik'ar da k'afafunta akan cinyansa tana tayasa kallon sports se wayanta ya shiga ruri dubawan da zatayi taga Nazeefah ke kira bata hankara ba ta d'aga.
"Assalamu Alaikum."
"Wa'alaikumus salam Nazeefah" ta amsa '"Yar uwa ya kike?"
"Lafiya k'alau ya gida da wahala kuma?"
"Wani wahala ne kuma, gida k'alau ya Ya Afzal?"
"Lafiyanshi k'alau."
"Nace kinyi amfani da turaren wutan nan kuwa?"
"Eh."
"Gosh! Dama kira nayi ince karkiyi amfani dashi bashida kyau yanzu Mummy ta kirani take sanar dani matar da ta sayar matan ta cuce tane" ta shirya mata k'arya don dama da gan-gan ta bata turaren wutan sanin bashida kyau.
"Ayyah wallahi har na kunna d'azu."
"Ba dad'i ko?"
"Unfortunately gashi yata hayak'i kuma yana k'onewa gabad'aya ya d'umamamun gidan."
"Subhanallahi Ya Afzal na gida kuma? Kinsan bayi son hayak'i."
"Wallahi abun beyi ba sam, ina cikin sawa ya dawo."
"Allah sarki kiyi hak'uri dan Allah ban san bashida kyau ba da ban baki ba."
"Ba komai Nazeefah ai bazaki cutar dani da gan-gan ba."
"Toh bari in barki haka kar in shiga hak'k'in Ya Afzal."
"A'a fa karki damu."
"Toh ki gaishesa seda safe."
"Allah bamu alkhairi" da haka sukayi sallama. "Huuh!" Tayi exhaling had'e da ajiye wayan "Waye ne? Nazeefah ce?" Ya tambayeta.
"Eh tana gaisheka."
"Ina amsawa maganan mey naji kuke haka?"
"Batun turaren wutan ne kasan wanda ta ba nin na kunna ashe wai bashida kyau matar data had'an bata k'ware ba seta damfari Mummy dama kira tayi tace kar in kunna nace ai tun d'azu na kunna."
"Ayyah kinga bama laifinki bane kike ta tada hankalinki daga turaren wutan ne."
"Ai toh naga baka son hayak'i ne shine hankalina ya tashi."
"Next time ki kwantar da hankalinki kinji?" Kai ta gyad'a mar a hankali sannan ya shiga tickling toes nata ya na mata cakulkuli, dariya ta tsaya yi na sosai chan wajajen tara da rabi suka kashe TV'n suka yi wanka suka kwanta.
Washegari da yamma Afzal ya koma gun Nazeefah, tsaf ta gyara gidan ta itama ta kunna turare sede hayak'in ne yayi yawa. Bayan sun yi Sallah sun ci abinci suna zaune a parlour Afzal yayi gyaran murya ya kira ta "Rabba'atul Bait?"
"Na'am Ya Rouhi" ta amsa.
"Shin ya kike sa turaren wutan ki ne kam?"
"Mey kaga?"
"I'm just curious ya kike sawa?"
"Dab zaka zo nake sawa."
"Shiyasa hayak'in yake yin yawa."
"Yana damunka ko?"
"I'm sorry but yes kinsan bana son hayak'i."
"I'm sorry a haka fa na bubbud'e window ma dan ya d'an ragu."
"Kinsan ya Ummi takeyin nata?" Beso ya ambaci sunan Amal ba gudun kar hakan ya sanyata kishi. Kai ta kad'a a nitse.
"Kunnawa take 20-25 minutes idan tana expecting bak'o saboda hayak'in ya tafi."
"Toh Ya Rouhi k'amshin ai se k'are kafin nan."
"Nop kinga zaki kulle windows ki sauk'ar da curtains seki sa ki basa like 10-12 minutes haka ya kama, then ki d'an bud'e window ki kunna fan ya tafi da hayak'in yana d'an fita sekiyi shutting back windows d'in kinga haka k'amshin ki yana nan hayak'i kuma ya tafi."
"Kai amma Ummi akwai fasali na gane Ya Rouhi nima haka zan fara sawa in shaa Allah."
"Yauwa Rabba'atul Bait shiyasa nake sonki."
"Uhm Ya Rouhi?"
"Yes Babe?"
"Wallahi wata tambaya nake son inyi maka amma bana son kamin mumunar fahimta."
"What is it? Feel free to ask me."
"Bazaka mun mumunar fahimta ba?"
"Just ask me Nazeefah."
"I've been curious for a while tun da aka kusan auranka ciwon zuciyanka be sake tashi ba shin dama mey dalilin? Meyake jawo maka attack d'in?"
"Naze-"
"Please tell me Ya Rouhi the last time I asked you banji dad'in yadda ka nuna mun a fili bazaka iya sanar dani ba I felt like you didn't trust me as your wife."
"Ba haka bane Nazeefah of course I do trust you."
"Toh yaya ne Ya Rouhi ai idan da ka yarda dani komi naka zaka iya sanar dani nasan da Amal ce ta tambaya da tuni ka sanar da ita."
"No please don't ever say that again kaman yadda Amal take matata kema haka ne so ki daina tada hankalinki kina ganin kaman nafi sonta fiye da ke, I love you both okay?"
"Okay Ya Rouhi kayi hak'uri idan magana na ya 6ata maka rai."
"Ba komai ya wuce."
"So zaka iya fad'a mun?" Nauyayyan ajiyan zuciya ya sauk'e "I'm very sorry Nazeefah amma Amal ce sababin ciwon nawa, rashinta a kusani dani shi yake haddisa mun ciwon nawa."
"Amal?" Ta tambaya cike da mamaki bil adad "Rashin Amal Ya Rouhi?"
"Yes Nazeefah, Amal."
"Wow!" Ta numfasa yanzu akan Amal Mummy ta mareta ranan a fuska? Yanzu akan Amal tsakaninsu da Ummi ya kusan 6aci? Wow! Ai dama seda jikinta ya bata haka amma tak'i amincewa ashe gaskiya ne in bahaka ba kanta ya mugun d'aurewa yadda ciwon nasa be sake tashi ba tun da ya kusan aure.
"Amma ban fahimce ka ba Ya Rouhi shin ba auran soyayya kukayi da ita Amal d'in bane dama har kake tsoron rasata haka?"
"It's a long story Nazeefah."
"Will it be okay if you tell me?" Numfasa yayi sannan ya fara kaman haka;
"I've known Amal for three years now tun kafin muyi aure muke tare da ita amma ba a matsayin saurayi da budurwa ba don daga baya ne nayi developing feelings mata lokacin kuma ita har sunyi nisa da wani saurayinta Abdul kin gane sababin ciwon nawa?"
"Anytime ka gansu tare se ciwon naka ya tashi kai kuma ka kasa sanar da ita kana sonta?" Kai ya gyad'a zalla.
"Toh ina shi saurayin nata yanzu?"
"Yana Canada."
"Ya sadaukar maka da soyayyanta kenan?"
"Yes Nazeefah."
"Allah sarki gaskiya na ji ma wannan masoya guda biyu Allah sa hakan shi yafi alkhairi a gareku duka."
"Ameen Rabba'atul Bait I hope I've answered your question."
"Yes you did Ya Rouhi muje ka watsa ruwa mu kwanta gobe office ko?"
*****
Haka kwanaki suka ta shud'ewa yayinda shak'uwa da soyayya keta dad'uwa tsakanin Afzal da Amal, a yau jirginsu na zuwa Saudi ya tashi kad'an ya rage Amal batayi kuka ba sanda jirginsu yazo tashi tsabaragen tsoro.
Da zuwansu yau sun samu sati kenan lafiya k'alau suke zaune, kullum suna cikin fita shopping da wajajen shak'atawa, tsaraba da dama Afzal ya sai wa Nazeefah wasu ababen ma Amal ce ke cewa ya saya mata, sosai yake jin dad'in yadda Amal ta d'au Nazeefah da zuciya d'aya.
Yau a d'aki sukayi deciding su yini Amal na mik'e akan gado tana latsa wayarta yayinda Afzal ke tsaye gaban mirror ko mey yakeyi oho.
"Arghh!" ya saki k'ara bisa yankewan da yayi da reza.
"Subhanallahi lafiya?" Amal ta tambaya. Ba shiri ta mik'e lokacin da taga jini na bulbula daga yatsn nasa.
"Innalillahi! Habib Albi!" Tissue taja da wuri gaban mirron ta shiga tare mai jinin "Omg I'm so sorry sannu" tace dashi a rikice tamkar zatayi kuka da mamaki Afzal ya tsaya yana kallonta shi da ya yanken ma hankalinsa be tashi ba kaman yadda nata ya tashi. Iska take hura masa tana ce mai sannu ba makawa.
"Kitten calm down yanka nefa kawai."
"But yankam ai deep ne Habib Albi sannu" iska ta cigaba da hura masa sannan tajasa izuwa bayi, spirit ta bud'e "Ka rufe idonka zeyi zafi" dariya sosai ta basa "Ce miki akayi rago ne ni?" A hankali ta shiga bulbula masa akan ciwon, wincing kad'an yayi Amal kam sekace ita aka sawa akan ciwo se tashi tsikan jikinta yake. Cike da lalashi tana hura mai iska tana ce mishi sannu ta mishi dressing ciwon ta tasa bandage. Se kallonta yake yayinda wani irin wutan sonsa yake ruruwa a zuciyansa.
"Kitten it's okay."
"It's not Habib Albi baka ga yadda yata jini bane?" hannun nasa ya zame daga nata had'e da rik'o k'aramar kunkuminta seda ya matso da ita kusa da shi "Bade kuka kike shirin yi ba Kitten?"
"No" ta amsa ciki-ciki mik'awa yayi had'e da kissing soft lips nata, sun d'au tsawon lokaci suna abu d'aya sannan a hankali tayi pulling out. "Thank you Kitten" ya furta yana maida gashin ta baya.
"What for Habib Albi?" Ta amsa tana zagaye hannayenta a wuyansa.
"For everything sweetheart, I can't imagine life without you, Allah yayi miki albarka I love you so much."
"Ameen Habib Albi I love you most" peck ta masa placing a kumatu "Muje ka huta" d'akin suka koma ta mik'e akan gado tana duba messages nata yayinda ya canza kayan jikinsa da jini yad'an 6ata. Hankalinta gabad'aya ya duk'ufa akan chatting da takeyi da Maamah kawai taji Afzal ya k'wace wayan kafin tace ya bata ya mik'e a jikinta had'e da kwantar da kansa a saitin k'irjinta wane d'an wani yaro.
"Habib Albi-"
"Lets sleep Kitten bacci nakeji."
"Toh ka tsaya in gyara kaji?"
"Ni haka nakeso" murmusawa tayi sannan tayi placing mai light kiss acikin gashin kansa yayinda take shafashi a hankali. A haka har bacci ya d'aukesu duka.
Sati biyu sukayi sannan suka dawo Nigeria, a ranan da suka dawo Nazeefah ta shirya musu abinci da dama ta kai musu haka Ummi da ma Mami, washegari sukayi sorting out tsaraban kowa suka kai musu, da yammacib ranan ya wuce gidan Nazeefah. Bayan sun k'are dinner sun dawo d'aki ta zaune gefensa akan gado inda take sanar da shi batun makaranta akan cewa in a week time zasu bud'e.
"Yes haka Amal tace kekam final semester d'inki kenan ai ko?"
"Yes Ya Rouhi."
"Toh Allah nuna mana graduation nakun."
"Ameen thank you nace ba.." se kuma tayi shiru.
"Yes what is it?"
"Ya Rouhi are you okay with it in d'auko mey aiki? Kaga semester'n nan na neman concentration sosai bazan zo in iya da aiki da shara d'innan ba shine nace idan ka amince na riga nayi magana da wata mata yaranta are ready to work for me and Amal."
"Itama Amal tace tana buk'atan mey aikin ne?"
"Bata fad'a ba amma nasan zata buk'ata ai Ya Rouhi ita da course nata yafi nawa wuya ma ai kaga zata fini buk'ata ma."
"Hakane kam so masu aikin kwana ne ko na jeka ka dawo?"
"Na kwana ne saboda daga k'auye za'a kawo su bawai anan suke da zama ba."
"Masu aikin kwana kuma Rabba'atul Bait?"
"Ya Rouhi nasan me kake gudu karka damu yara ne fah Khaleefah ma ya girmesu d'ayar 16 d'ayar kuma 14 kaga ai baza a samu wata matsala ba in shaa Allahu."
"Toh zanyi ma Amal magana."
"Yauwa duk abinda akwai seka sanar da ni muyi making arrangements ya zammana de sun fara aikin tun yanzu ba se an bud'e makaranta ba."
"Jazakillahu khair Rabba'atul Bait yadda kikeso wa Amal abinda kikeso wa kanki."
"Ameen Ya Rouhi an zamo d'aya ai yanzu zamu kwanta ko?"
"Wallahi kaman kin sani a gaje nake."
"Akwai gajiya ai ko nayi maka tausa tukun?"
"Baki gaji ba?"
"Ai bana gajiya when it comes to you" mik'ewa yayi kan gadon ta shiga yimai tausan a hankali tana relieving mai tension.
*****
Kwana biyu yayi mata sannan ya dawo gun Amal.
Amal fa ba wasa kitso taje aka rangad'a mata k'anana sannan ta sha lalle ja a tafin hannu ta baya kuma akayi mata bak'i irin na zamanin nan mey kyau. Kafin Afzal yazo ta gama girkinta ta bi gidan da turare se k'amshi zallah ke tashi.
"Oyoyo Habib Albi" taje tayi hugging nasa da gudu.
"Oyoyo my Kitten" sun d'au kusan minti d'aya manne a jikin juna sannan ya d'agota a hankali "Masha Allah kin ganki kuwa?"
"Nayi kyau?" Ta tambayesa tana wasa da yatsun hannunsa.
"Yes Kitten yakamata in biya kud'in wankan nan."
"Awwn thank you Habib Albi" ciki suka k'arisa suka nufi d'akinsu inda ya rage kayan jikinsa suka haye kan gado "Yau mey aka girka mun Baby?"
"Your favorite!" Ta sanar da shi.
"Spaghetti?
"Uhumm."
"Wow! Ya kike toh?"
"Lafiya k'alau ka baro Nazeefah lafiya?"
"Lafiya k'alau tace in gaisheki."
"Ayya ina amsawa jiya ma Mami tana nan ai tazo muka yini mun."
"Allah sarki ya take?"
"She's fine" ta amsa se kuma taga yadda Afzal keta kallonta tun d'azu da fari ma tsarguwa tayi kode jan bakinta ya hau kan fuskanta ne?
"Habib Albi lafiya?"
"Matso kiji" matsowa tayi kusa da shi hakan be masa ba seda ya aza ta kan cinyansa "Kitten?"
"Yes?"
"Anya kuwa?"
"Anya kuwa mey Habib Albib? Wani abun ne?"
"Anya babu ajiya na anan?" Ya tambayeta had'e da aza hannunsa kan cikinta wani kunya maras misaltuwa taji ya rufeta "Kai Yaya" nan ta shiga kare fuskanta.
"Seriously naga kin k'ara freshness ne ai skin naki se wani glowing yake."
"Toh Yaya naje k'asa me tsarki ba dole ba ko ka manta kwanana na hud'u kacal daga dawowa daga Saudiyya?"
"Ina sane kawai de ina tambaya ne."
"Toh ka kwantar da hankalinka ba komi anan" ta fad'a tare da aza hannunta akan nasa dake manne da cikinta.
"Kai Kitten kode 6oye mun kike ne?"
"A dalilin mey zan 6oye maka Habib Albi?"
"Toh yaushe rabon ki da kiga period naki."
"Ni bana son tambaya" ta fad'a tana neman mik'ewa hannunta yayi saurin ja "Ai sai kin amsani."
"Yaya mana hannu na" saketa yayi a hankali "So answer me."
"Yaya jiya fa nayi wankan sallah."
"Kitten k'arya kike mun ko?"
"Yaya na ta6a maka k'arya ne?" Ta maraice fuska.
"Toh shikenan very soon nasan seed d'ina zeyi germinating."
"Muje kaci abinci toh."
"Yauwa Nazeefah tace in fad'a miki ta sama muku masu aiki tunda kun kusa komawa school kar aikin gida yayi interfering muku da school."
"Mey aiki kuma Habib Albi?"
"Yes haka tace."
"Na mey? Ni bana buk'atan mey aiki da safe kafin in fita school zan iya kammala aiki na, ranan da nake da lectures 7 kuma idan na dawo gida se inyi abu na."
"Gajiyan baze zo ya miki yawa ba Kitten I think shawaran Nazeefah fa yayi mey aikin zata taimaka miki kinga kafin ki dawo daga school ta gama miki komai kika dawo girki kawai zakiyi ki huta."
"Habib Albi ni gaskiya bana so."
"Toh yanzu ya kenan? Ince wa Nazeefah bakiya so? Ai bazata ji dad'i ba tunda har tayi wa mutanen magana kuma tun daga k'auye tace za'a kawo su."
"Kyansa dama ta tambayeni ko kai kafin tayi musu maganan."
"Hakane amma ai ita bata d'au zaki k'i taimako ba."
"Ba wani nak'i bane Yaya kawai ina ganin bana buk'ata ne."
"Zaki buk'ata fa Kitten keda kike yin tough course aikin gidan zezo yayi miki yawa."
"Toh shikenan tunda kaima ka goyi bayan hakan."
"I'm sorry if I'm forcing you into this kinsan halin Nazeefah ba sena fad'a miki ba kina k'i yanzu zata ce bakiya appreciating effort nata ne ta fara k'ananun suratai kawai kiyi hak'uri ki amince shine kwanciyan hankalinmu duka. Bazan 6oye miki ba ko ni banji dad'in yadda seda ta gama komai sannan ta sanar dani ba amma haka nima nayi hak'uri."
"Hakane kam ba komai zan kirata inyi mata godiya."
"That's by Babeh let's go eat toh I'm craving for your delicious already." Hannunta acikin nasa suka nufi dining suka ci abinci ba da dad'ewa ba Maghrib ya shiga ita kad'ai tayi nata kasancewar Afzal ya soma fita Masallaci yanzu.
Washegari***
"Ya Babe shiru har yanzu? Cewan Rumaysa daga d'ayan 6angaren.
"Wallahi layin Ya Afzal nake ta gwadawa amma bai d'auka nakega suna meeting ne so nike in tambayesa izini kamin in fito."
"Toh ina jiranki." Kashe wayan tayi 10 minutes later ta sake trying numban Afzal amma still baya d'agawa. Se chan k'arfe uku taga call nasa na shigowa da hanzari ta d'aga.
"Babe ina ka ajiye wayanka?"
"I'm sorry meeting muke se yanzu muka fito ya akayi?"
"Izini nake son nema zani gidan k'awata."
"Toh bismillah go ahead you're permitted."
"Thank you Ya Rouhi."
"Aha bye." Dama ashirye take key'n motarta ta d'auka kawai ta fice chan gidansu Rumaysa ta wuce inda ta nuna mata 'yan matan. Bayan sun gaisa Rumy ke tambayarta "So wacce zaki d'auka?"
"K'aramar kai ai babban zata fi mana harka da kyau senu kaiwa Amal babban."
"Toh Hindu ga Aunty'nki Nazeefah ita zata d'aukeki aiki ke kuma Safiyya zamu kaiki wa amaryarta" kai duka suka gyad'a "kina iya tafiya ko Hindu na?" Cewar Nazeefah "Bari muyi magana da yarki" ba musu ta mik'e ta fice.
"Yauwa kaman yadda na fad'a miki wannan itace Aunty Nazeefar itace wacce mukeso ki bamu had'in kai dan fitar da shegiyar da ta aure mata miji."
"Duk abinda kukace shi za ayi Aunty."
"Yauwa Sofin gaye ga waya nan Aunty Nazeefah ce tace a sai miki za kuna waya da ita ta ciki koda wasa kuma kar kiyi saving lambarta saboda ba'a san yadda abu ze zo ya kasance ba da kinga lamba me 08102 toh nata ne kin gane?"
"Na gane."
"Good kuma kina yi mata ladabi da biyayya kinji?" Nazeefah ta kar6e Rumaysa "Sunanta Amal amma Aunty zaki na ce mata duk aikin da takeso a gidan kinayi mata shi ba ruwanki da yi mata sata, duk abinda kikeso ki kirani zan baki kina ji na ai?"
"Eh Aunty."
"Yauwa zuwa gobe zan zo in d'aukeki da 'yar uwarki in kaiki gidan nata."
"Toh Aunty."
"Rumy ta fad'a muku albashinku ko?"
"Eh dubu goma."
"Yes sannan naki zanna k'ara miki extra dubu goma akai ko wani k'arshen wata idan har zakiyi mun aiki me kyau zuwa lokacin da zan samu in cimma burina."
"Toh Aunty godiya nake."
"Yauwa bayan nan kuma ko k'anwarki ce karki sanar da ita, wannan magana ya rage sirri a tsakanin mu kin gane?"
"Na gane Aunty."
"Toh Babe barin koma." Har waje Rumy ta rakata sannan ta dawo ciki.
Washegari kaman yadda suka tsara Nazeefah tazo ta d'aukesu gidan Amal suka fara wucewa lokacin Afzal ma bai gida ya fita office. Sannu da zuwa Amal tayi musu ta shigo dasu "Bari in d'auko muku ruwa."
"A'a 'yar uwa (yadda take kiran Amal) karki damu ai daga gida nake wannan ne masu aikin zan d'au k'aramar in baki babban tunda daman ke yayata ce."
"Kai Nazeefah ai kece babba a gidan nan."
"Toh nide zan d'au k'aramar Hindu ke kuma babban Safiyya."
"Toh Safiyya sannu da zuwa:"
"Yauwa Aunty nagode."
"Safiyya ban da rashin kunya kinji ko? Yi kinyi bari kin bari."
"In shaa Allah Aunty."
"Toh bari zamu wuce gida muma."
"Toh kin shigo da kayakin ki duka ko?" Amal ta tambayi Safiyya.
"Eh Aunty" ta amsa.
"Toh bari mu raka ku" nan suka rakasu har gun mota bayan sun dawo ciki Amal ta kai Safiyya d'akin data bata wanda zata na kwana aciki. D'aki ne harda bayi aciki ga gado da drawer harda dressing mirror. Yadda ake kunna shower da kuma yadda ake flushing ta nuna mata sannan ta bata waje ta watsa ruwa.
Bayan Afzal ya dawo daga aiki ya watsa ruwa ya d'an huta take sanar da shi akan cewa Nazeefah ta kawo mata mey aiki d'azu "Bari inyi mata magana ku gaisa."
"Ko gobe ma baza mu gaisa bane Kitten?"
"Toh ai kana fita office da wuri bari de ku gaisa yanzun lemmi speak with her" Nan ta mik'e, tare suka taho da Safiyya tana binta a baya daga baki bakin parlourn ta tsuguna ta gaishe da Afzal cike da ladabi da biyayya, shima ba yabo ba fallasa ya amsa.
Washegari bayan Amal ta shirya Afzal office ta dawo ciki ta koma bacci se wajajen goma ta tashi, wanka tayi tasa kaya sannan ta fito da mamaki ta tsaya tana bin parlourn nata da kallo yadda Safiyya ta share tayi mopping, dining ta zarce nan ma ko ina sparkling yake. "Wow!" Ta furta wai ita da take shirin koya mata yadda zata na yin aikin?
"Safiyya!" Ta k'wala mata kira.
"Safiyya!"
"Na'am Aunty" ta amsa tana shigowa ta k'ofar kitchen. "Ina kwana?" ta tsuguna ta gaisheta.
"Lafiya kin tashi lafiya?"
"Lafiya k'alau Aunty."
"Sannu da aiki ga ko ina yayi kyau."
"Nagode Aunty Tv'n ne banso in goge ba kar in ta6a wani abun."
"That's so thoughtful of you, zan gwada miki da kaina amma kafin nan kin karya?"
"A'a tukuna."
"Toh bari in shirya mana breakfast" nan da nan suka shiga kitchen d'in Safiyya tana tayata, bayan sun gama tayi wanke-wanke sannan Amal ta nuna mata yadda zata na goge TV da stand d'insa. Bayan sun gama Amal ta sallameta ta wuce d'akinta. Tana cikin buga game a wayarta Nazeefah ta sa mata kira nan ta d'aga tare da kashe muryarta yadda ba waje baze jita ba.
"Assalamu Alaikum Aunty."
"Wa'alaikumus salam Safiyya ya kike?"
"Lafiya Aunty ina kwana?"
"Lafiya k'alau ya wajen aikin naki? Ba wata matsala ko?"
"Babu komai."
"Ta baki abun karin kumallo?"
"Eh flask d'in ma ta ajiye mun a gaba na wai in d'iba da kaina."
"Mak'ira kawai, ke kika shirya wa Ya Afzal breakfast ko ita da kanta?"
"Ita da kanta nace zan tayata tace zatayi da kanta inje in kwanta."
"Mak'ira mey ta girka masa?"
"Dafaffen dankali ne da sauc da wani abu kaman nama nama aciki."
"Lallai aikin ki na kyau kwanan nan zamu fara aikinmu akanta kede ki tabbata kina mata duk wani ladabin da ya kamata."
"Toh Aunty."
"Yauwa karki manta kina goge lamba na daga call logs naki duk sanda muka gama waya."
"Toh Aunty ki gaishe mun da Hindu."
"Tana bacci idan ta tashi zan sanar da ita sai anjima."
"Yauwa nagode" da haka sukayi sallama.
RANA D'AYA!
#RD
Love... King Miemiebee👄✨
[13/08, 09:37] +234 907 483 8352: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
August, 2018
beeenovels.blogspot.com
_Written by Miemiebee👄_
*PAGE 3⃣1⃣*
Nazeefah de bata da aikin da yafi kiran Safiyya kullum tana tambayarta mey Amal ta girka wa Afzal, shin idan ya dawo daga aiki mey sukeyi, suna yawan fita ne ko kuwa zama suke a gida suna wasa? Komai so take tana ji haka kawai tayita tada wa kanta hankali.
Kwana bibbiyu Afzal ya cigaba da yima kowaccensu, bada dad'ewa ba aka bud'e makaranta. Ranan da kwanan Amal ne kuma tana da early morning lectures tare suke shiri su fita se yayi dropping nata kafin ya wuce office haka ma idan kwanan Nazeefah.
Yau Amal da Afzal suka cika wata d'aya da aure se kuma Allah yayi ranan ya fad'o a kwananta se rawa jikinsa yake he can't wait to go back home. Itama Amal bata mance da wannan muhimmiyar rana ba, morning lectures nata na k'arewa wajajen sha d'aya driver'n da Afzal ya mata hiring ya dawo gida ta shiga kitchen yayinda Safiyya ke tayata aiki. Abinci kala-kala suka had'a da juices abin se wanda ya gani ga fruit salad ba abinda babu dam suka cika kan dining table d'in da kayan abinci. Dab ta fito daga wanka around three kenan Afzal ya buga mata waya.
"Halo my adorable Kitten?" Ya fad'a bayan da ta d'aga.
"Yes Habib Albi ya kake ya office?" Ta amsa.
"I'm soo missing you Baby" ya sanar da ita.
"I miss you too Habib Albi ai ka kusa dawowa."
"Wani kusa? Kina ji wai muna da meeting."
"Meeting kuma? Se goma zaka dawo kenan?" Ta tambayesa tamkar zatayi kuka.
"Ai nima ba iya jira zan ba I miss you so much Babe."
"I miss you even more darling amma ya zamuyi?"
"K'arya nayi nace musu bakida lafiya zan kaiki asibiti so I'll be back in a jiffy."
"Awwwn Habib Albi se kazo toh Allah ya kare."
"Ameen Kitten I love you."
"I love you too darling" ta fad'a had'e da katse wayar. Nan da nan ta ciro wata had'ad'd'iyar purple blouse ta sanya da wani bak'in straight skirt ba k'aramin amsan ta skirt d'in yayi ba yadda yabi perfect curves nata. Zama tayi gaban mirror ta rangad'a kwalya yau harda yin lining saman idonta tasa mascara ta taje dogayen eye lashes nata sannan tasa maroon janbaki ba k'aramin kyau tayi ba gashinta da tayi stretching jiya a salon ta jik'a da mai sannan ta taje ta kwantar a jikinta ta feffeshe da turare tana cikin sanya d'ankunne se taji k'aran motan Afzal da hanzari ta k'arasa tasa bracelets nata ta d'aura agogo ta fita taransa. Dai-dai bakin k'ofan ta tsaya yadda yana bud'e k'ofan ze fara cin karo da ita.
Hannunsa a cike ya fito daga motan d'aya rik'e bouquet na flower d'aya kuma da ledan da ya yo mata shopping aciki. Yana bud'e k'ofan sega Damsel tasa tsaye tana mar murmushi.
"Dayyummm!" Ya furta yayin da yakasa koda kyafta ido se kallonta yake kaman ze hambuleta tsabagen kyan da tayi.
"Happy one month anniversary Habib Albi" ta sanar da shi ledan ya ajiye a kan wani stool dake kusa da bakin k'ofan sannan ya mik'a mata flower'n "Happy anniversary to you too Baby I love you" amsa tayi sannan yayi hugging nata yana mey shak'an daddad'an k'amshin turaran jikinta, sun dad'e a haka sannan ta raba hug d'in a hankali.
"You're looking.. you're looking fabulous Kitten, gosh you're so beautiful" ya sanar da ita tun daga k'ark'ashin zuciyansa wani sa'in har mamakin kalan kyawawan yaran da Amal zata haifa masa yake tabbas idan zasu bi ta ba k'aramin kyau zasuyi ba.
"Thank you Habib Albi thank you for the roses too."
"Don't mention Darling" jakarsa ta amsa ya d'aga ledan suka k'arasa d'aki inda ya rage kayan jikinsa yabar nickers zalla.
"Baka ci abinci ai bako?" Ta tanbayesa tana zaune a gefensa.
"Bayan kince kar naci se kuma in ci Kitten? Yunwa nakeji kaman zan mutu."
"Kar ka mutu kaji? Taho muje kaci abinci."
"Wow" kawai yake furtawa lokacin da suka isa kan dining d'in kuloli sekace fiest za'ayi se sallama suke masa ga wani chocolate cake babba da aka rubuta caption na "Happy Anniversary Habib Albi" akai ajiye a gaban sa.
"Duka wannan kika girka Kitten?"
"Yes Habib Albi nida Safiyya."
"Wow I'm impressed the cake is so beautiful."
"Thank you Habib Albi shi catering nayi" ta fad'a had'e da yankan kad'an tayi feeding nasa da shi. "Mmnm" ya furta yana santi "Chocolate cake."
"Your favorite right?" Kai ya gyad'a eagerly "Shin mey da mey da mey Kitten d'ina ta tanada mun haka?" Ya tambaya se tsinkewa miyaun sa yake.
"Kai de bud'e kaga" flasks d'in ya shiga bubbud'ewa daga na pepper soup na kifi sena ganda se fried rice da coleslaw ga su samosa dasu spring rolls da ta sa akayi mata bayan nan ga apple juice da su aldeb da zo6o abun de se wanda ya gani.
"Kitten isn't this too much?"
"Ka manta kai d'an gata na ne?" bi tayi one-by-one tana d'iba mai a plate sannan tayi serving nasa. Yaci wai sam shi seda ita haka tayi joining nasa. A kan cinyarsa ya zaunar da ita haka ya bata yaci har suka cinye inda ta kira Safiyya da ta tattare wajen seta d'iba duk abinda ya mata itama taci idan ta gama se tayi wanke-wanke. Safiyya se washe baki take taga pepper soup har kala biyu ga cake.
D'aki su Afzal suka dawo inda da k'yar Amal ta sanya sa ya watsa ruwa wai sam shi seda ita zeyi, ita kuwa tace bazata goge wannan kwalyan nan duka ba. Bayan ya fito ya sanya nickers nasa sannan ya iso ya zauna a gefenta "Here this is for you Wifey" ya fad'a yana mik'a mata ledan d'azu cike da jin dad'i ta amsa ta shiga fiddo da kayakin da suke ciki. Waya taga sabuwa pil k'irar Iphone X aciki, seda wasu shoes and bags kala biyu da wani purple doguwar riga voile me combination na colors a jiki wanda ko ba a tambaya ba ansan mey d'ankaren tsada ne k'arshe kuma seda wani photo album wanda ciki hotunansu ne da dama wanda suka d'ad'd'auka a waya yakai aka wanke masa.
"Omg Habib Albi this's too much" ta d'ago kai tana kallonsa yayinda idanunta suka ciko da hawaye tsan-tsan farin ciki.
"Oh Kitten not again" yayi maganan yana matse ta a jikinsa, kukan farin ciki ta shiga yi yayinda ta kasa 6oye farin cikinta. "Please don't ruin this beautiful moment Love" ya buk'aceta yana shafa gashin kanta sannan a hankali ya d'ago ta daga jikinsa yana share mata hawayen nata da babban yatsansa.
"I'm sorry I just don't know how to react Habib Albi banida bakin yi maka godiya, wallahi ban san ta ina zan fara ba, I know thank you won't compensate for this but thank you so much Habib Albi, Allah saka da alkhairi ya k'ara maka bud'i I love you soo much."
"Masha Allah Kitten ameen kuma nagode, I love you even more. I don't think I can survive without you, in fact my life has no subtle in the absence of your love Amal, duk yadda nakeso in nuna miki how deeply in love I am with you bazan iya ba because no words can describe the love I have for you, not even feelings could show Kitten, one thing I'm sure is that there's no ME without a YOU" ya k'arisa yana mey rik'o k'ananun hannayenta cikin nasa tare da placing gentle kiss akai.
Hawaye sosai Amal take dan farin ciki sau dayawa takan zauna ta tambayi kanta shin mey ta ta6ayi wa Allah da ya bata miji mey kyautatawa kaman Afzal, mijin da burinsa bai fi yaga ya sanya ta farin ciki, mijin da be ta6a k'untata mata ba a iya zaman da sukayi, mijin da se abinda take so yakeyi mata. Gani take kaman bata cancanci mutum kamansa ba, shin anya zata iya rayuwa idan ba shi?
"I can't leave without you Habib Albi wallahi I can't" ta rushe da kuka rungumarta yayi yana shafa gashinta a hankali sun d'au tsawon lokaci a haka sannan a hankali ya d'agota bayan da kukan nata ya lafa "Cry nomore okay? I love you so much" Kai ta gyad'a tare da kwantar da kanta a k'irjinsa "I love you more Habib Albi."
****
Bayan sallan Isha suka shirya tsaf suka fice wajen shan ice cream se hoto Afzal yake tayi mata tun tana ce mai ya bari bata so chan itama da abin ya isheta ta d'au sabuwar wayarta ta shiga d'aukansa tana mai video, shak'atawa suka tayi abinsu suka bar Safiyya kad'ai a gida. Ita kam ta samu TV se fata take kada su dawo ita bata k'i ma su kwana a waje ba saboda tayita kallon series abinta. Haka har wayanta ya gama ringing bata ji ba se a karo na biyu tsabagen yadda hankalinta ya duk'ufa kan kallon.
"Assalamu Alaikum Aunty ina yini?"
"Ina kika ajiye wayanki ina kiranki Safiyya?" Nazeefah ta kurareta.
"Kiyi hak'uri kallo nakeyi."
"Ya uwar d'akin naki? Meya faru yau?"
"Hmm Aunty baki san meya faru ba."
"Gayan mey?" Ta tambaya cike da rashin hak'uri.
"Kinga abincin da Aunty ta girka wa Uncle kuwa? Wallahi sunyi kala ashirin pepper soup babu irin wanda batayi ba ga juice d'innan da su meat pie."
"Kai! Wai meke faruwa?"
"Wallahi wai ani.. ani-- ani wallahi na mance sunan abun amma tace wai yau ani wani abinsu ne shiyasa ta mai wannan girke-girken kuma baki ji yadda komi yayi dad'i ba."
'"Yar k'auye anniversary? Yau anniversary'nsu?"
"Yauwa wallahi shi! Anibasari haka tace."
"Innalillahi!" Ta furta cike da tashin hankali yayinda wani irin kishi da haushin Amal taji ya rufeta kup, shekaranta uku a gidan Afzal amma bata ta6a celebrating anniversarin su ba sega Amal da ta shigo na wata d'aya tayi hakan taya Amal zata fita kaifin tunani? Inaaaa baze yuwu baa! "Yanzu ina suke?"
"Sun fita tun d'azu tun bayan sallan Isha."
"Basu dawo ba har yanzun?" Ta tambaya had'e da zaro ido tana duban agogon bangon d'akinta.
"Eh."
"K'arfe goma fa! Ina sukaje ta fad'a miki?"
"Cemun kawai tayi zasu fita."
"Innalillahi wallahi hawan jini ya kusan kamani 'yar nan zata sace mun miji, na shiga uku ke wawiya meyasa baki k'ok'k'ona mata girkin nata ba?"
"Bata bari na ko kusa da cookan nata iyaka in yanka mata su albasa ko in daka mata maggi."
"Wawiya ki bud'e kunnenki ki saurareni kina jina?"
"Eh Aunty."
"Anytime ta sake saki yi mata jajjage ko kuwa daka maggi kiyi excess ki k'ara naki akai yadda abincin zeyi rad'au yayi yaji ya rud'awa Ya Afzal ciki ya kasa ci kinji? Haka ne kawai zesa abincinta ya fita masa a rai."
"Aunty toh ai zata gane."
"Banza ce mata zakiyi bakiji adadin da tace ki d'iba ba."
"Amma fa ita take d'iba ni kawai bani take in daka ko in yanka."
"Ki jini, nan gaba idan kuka shiga kitchen tun kafin ta d'iba mikin kice zaki d'iba da kanki seki tambayeta nawa, anan seki k'ara da naki akai idan ta tambayeki kice baki ji da kyau bane kinji?"
"Toh Aunty an gama."
"Yauwa bayan nan se meya sake faruwa kingan shi ya saya mata wani abun?"
"Toh wallahi ban san wannan ba dake ina cikin d'aki ya taho."
"Bance kullum kina jin k'aran motansa ki fito ba kiga meya shigo da shi?"
"Aunty na shiga ba ne."
Aikin kenan kullum mstww wallahi ina da tabbacin ya mata sayayya shima soko d'aya ya cigaba se 'yar shuwan nan ta tsiyatar da shi tukuna yanzu kinsan mey nakeso dake?"
"Sekin fad'a."
"D'akinsu zaki shiga ki duba mun kiga koya sai mata wani abun."
"Aunty-"
"Bade tsoro kikeji ba?"
"Aunty idan suka dawo ina cikin d'akin fah?"
"Wawiya idan baki cire tsoron nan ba ya zaki yi mun aiki toh? Ko bakison extra dubu goma akan albashinki k'arshen watan nan?"
"Ina so."
"Good jeki lek'a mun d'akin nasu."
Mik'ewa tayi ta nufi d'akinsu Amal cike da fargaba ta gwada bud'e k'ofar sede a kulle ta tarar. Koda wasa Amal bata ta6a fita bata kulle musu d'aki ba not that tana zargin Safiyya na sata se don gudun abinda shaitan ze iya raya wa mutum wataran. "Aunty a rufe" ta sanar da ita.
"A rufe de!"
"Eh wallahi."
"Amma 'yar nan shegiya ce wallahi barta watan cin ubanta ya kusa kamawa wallahi da ikon Allah sena koreta daga gidan nan Ya Afzal is mine alone." Nan ta kashe wayan cike da takaici, safa da marwa ta shiga yi a d'akin nata yayinda hankalinta ya mugun tashi ji take kaman zatayi hauka. Wai taya ma shawaran celebrating anniversary be ta6a bugo mata akai ba? Shin hakan na nufin Amal ta fita iya tarerayan miji? Mstw! Wayanta ta bud'e ta shiga date tana neman yaushe 25th zeyi itama anniversary'n ta ya kewayo, dubawa tayi taga next week ne, nan ta shiga irgawa tana fatan Allah yasa ranan ya fad'o a kwanan ta, da ikon Allah kuwa se ya fad'a a kwanan nata. Toh ma auren nasu shekara uku da wata nawa ne? Ana March yanzu sun yi auren a December that is 3 years three months, perfect!
Jira tayi har ranan da anniversay'n nasu ya kewayo itama ta shirya gaggarumin girki, ba abinda bata had'a ba sauran abubuwan ma catering tayi dam ta cika kan dining itama. Tasha lalle da kitso ba dama ta sanya sabon d'inki. K'arfe biyar da rabi Afzal ya baro gidan Amal zuwa na Nazeefah, tun daga bakin gate k'amshin turare ya ke tashi gashi tunda ya gwada mata yadda ake sa turaren wutan ta koya takeyi itama. Tun daga gun parking lot taje ta taresa.
"Welcome home Ya Rouhi" tace da shi had'e da pecking nasa a kumatu.
"Wannan kwalya fa Rabba'atul Bait?" ya tambaya yana kallonta admiringly ba k'arya tayi kyau gashi unlike Amal da bata yin heavy makeup Nazeefah idan ta tashi yin kwalya yi take wane makeup artist ce ta zana mata fuska.
"Naka mana Ya Rouhi" ta amsa tana amshe mai jakansa.
"You look awesome Babe."
"Thanks Baby" nan suka k'arisa ciki "Wai wai wai kulolin nan fah daga ina?" Ya tambaya yana bin dining table d'in da kallo.
"Happy anniversary Babe."
"Wow!" Kawai ya iya furtawa yayinda kansa ya rud'e "Happy anniversary Dear" ya miyar mata had'e da brushing light kiss a lips nata "But wait I thought a December mukayi aure yau kuma March ko ba haka ba?"
"Yes Ya Rouhi yau 25th march which marks 3 years 3 months of our marriage ko ka manta?"
"Yeahh right" yayi reasoning da ita "Thank you Babes."
"Muje ka watsa ruwa se mu ci abinci ko? Ina ba a k'oshe kake ba?"
"Ai ko a k'oshe nake ya zama dole inyi creating space wa delicious d'in Rabba'atul Bait d'ina" sosai taji dad'in amsansa. A tare suka k'arisa d'akin nan da nan ta had'a mishi ruwa ya shiga ya watsa fitowansa ya nufi wardrobe dan ciro wandon da ze sanya se cin karo yayi da wani k'aramin pack da akayi wrapping da wrapping sheet cike da mamaki ya d'aga ya bud'e wani had'ad'd'en designer agogo ya tarar mey d'ankaren tsada aciki, gefensa kuwa wani happy anniversary card ne daya sha k'amshin turare. Da murmushi kwance a fuskansa ya karance, a ko da yaushe godiya yake yi wa Allah da ya shiryar mar da Nazeefar sa har sukayi sorting out differences nasu suke zaman lafiya yanzu. Baya jin ze iya rayuwa ba ita, a hankali soyayyarta ya ginu a zuciyansa. A da be ta6a kawowa koda kusa da mafarki cewa wataran ze auri mata biyu ya zauna da su kuma ya sosu duka ba se yanzu da hakan yake faruwa. Ya sani son Amal daban yake a zuciyansa amma kuma Nazeefah na da wani gur6in da ta mamaye a zuciyansa, gur6in da ba me iya mamayewa se ita.
"Rabba'atul Bait?" Ya kewayo yana kallonta cike da soyayya.
"Yes Ya Rouhi" ta amsa had'e da takowa zuwa inda yake.
"Is this for me?"
"Yes Ya Rouhi Happy 3 years anniversary I love you so much" 'yar kunkuminta ya kama had'e da matso da ita kusa dashi sannan yayi owning lips nata kissing her so gently with thousands of emotions and gratefulness. A hankali yayi pulling out "Thank you Nazeefah, this means alot to me Allah miki albarka."
"Ameen Ya Rouhi you deserve alot morethan this."
"Kin san ina sonki ko?" Kai ta gyad'a masa a hankali tana mai murmushi "Ko zaka sake sanar dani?"
Murmushin ya miyar mata sannan yace, "I love you Nazeefah ni kaina mamakin kalan soyayyan da nake miki nake ban ta6a kawowa kusa da raina that I'll one day love you like I'm doing, Allah ne kad'ai sheda akan kalan soyayyan da nake miki, I just pray it continues to grow and never fades away, Allah bar min ke Rabba'atul Bait ya miki albarka kuma."
"Ameen Ya Rouhi I love you even more gani nake kaman idan ba kai bazan iya rayuwa ba. Ka sani ka riga ka zama 6angare daga jikina wanda idan aka cire bazan iya rayuwa ba, please never leave my side."
"We'll forever remain together Nazeefah in shaa Allah har mu mutu sannan kuma mu cigaba da soyyayar namu achan Jannah where we'll reunite."
"In shaa Allah Ya Rouhi. I'll choose you a million times if I were given the chance to, muje kaci abinci ko?" Kai ya gyad'a mata sannan ya zaro wandonsa ya sanya dining d'in suka k'arisa inda tayi serving nasa sannan ta zauna gefensa tana masa hirar soyayya har ya gama ci. Sosai ya yabawa girkin nata ranan. Washegari tun k'arfe sha biyu ya dawo daga office ya watsa ruwa se wajajen uku Nazeefah ta dawo daga school sannu da zuwa yayi mata ya sirka mata ruwa ta watsa sannan yajata dining da taci abinci. Bud'e flask da zatayi kawai ta tarar da kwalin waya ciki k'irar Iphone X sak irin na Amal fari itama.
"Omg! Ya Rouhi!" Tayi exclaiming had'e da d'agowa "Ya Rouhi an iX!"
"Yes Rabba'atul Bait this's my anniversary gift to you I hope it's not too late?"
"It's never too late Ya Rouhi thank you soo much Allah k'ara bud'i I love you endlessly."
"I love you too darling so ki shirya muje muci abinci nima yunwa nakeji." Nan da nan suka shirya suka fice Nazeefah dad'i kaman ze kasheta sede jikinta se bata yake Afzal ya sai wa Amal itama iphone X d'in, da ta tuna da hakan se ranta ya 6aci she can't wait ta fitar da ita daga gidan. Washegari bayan Afzal ya dawo daga office ya shiga tattara wasu documents nasa da ze buk'ata idan ya tafi gun Amal kasancewar yau kwanan Nazeefah ya k'are. Tunda Nazeefah ta shigo d'akin ya karanci mood nata sam ba walwala a tattare da ita.
"Rabba'atul Bait?" Ya kirata.
"Uhmm?" Ta amsa had'e da d'ago kai tana kallonsa a maraice.
"Lafiya?" Ya tambeyeta kai zalla ta gyad'a mar sede be yarda ba yana gama tattara documents nasan ya sanyasu cikin briefcase nasa ya k'arisa gefenta ya zauna. "What's going Dear?"
"Ya Rouhi..." kawai seta rushe da kuka cike da tashin hankali ya rungumeta a jikinsa yana shafa bayanta a hankali yana bata hak'uri kukan ta cigaba da yi chan da kukan nata ya lafa ya d'agota yana share mata hawayen nata. "Ya isa kinji?" Kai ta gyad'a masa a hankali sannan ya tambayeta meya faru a cewan shi gabad'aya mutuwa akayi mata.
"Ya Rouhi I can't do this anymore."
"Talk to me Nazeefah I'm here."
"Ya Rouhi muje asibiti."
"Why? Meya faru? Bakida lafiya ne?" Yayi saurin jero mata tambayoyi.
"Ya Rouhi shin baka tunanin ko ina da wata matsala?"
"Matsala kaman ya kenan Nazeefah?"
"I don't think I can conceive (bana jin zan iya haihuwa.)"
"Subhanallahi meyasa kika ce haka?"
"Ya Rouhi it's been three years."
"Se mey? Meya kawo maganan nan?"
"Ya Rouhi k'awayena da akayi auransu bayan namu duk sun haihu wasu kuma suna hanya amma ni shiru ko miscarriage ban ta6a yi ba, yanzu Asma'u ta kirani wai she's pregnant Asma'u da last two months mukayi bikinta" se ta fashe da wani kukan. Hugging nata yayi a hankali yana mey cigaba da bata hak'uri, sosai ta basa tausayi be saketa ba seda ya tabbata kukan nata ya lafa.
Fuskanta ya rik'o cikin hannayensa a hankali ya fara ce mata, "It doesn't matter Rabba'atul Bait it doesn't matter saboda wanda kika rigasu yin aure sun riga haihuwa ko makamancin hakan remember kowa da lokacinsa a duniyan nan, we weren't born together, we shall die alone and so shall live our lives differently. Kisa a ranki kema naki lokacin na nan zuwa kuma koda ma baki haihu mun bama ni banida matsala da hakan, dai-dai da RANA D'AYA Ummi bata ta6a cemun meyasa taji shiru ba har yanzu saboda tasan shi haihuwa yin Allah ne yau shekaranta nawa ita da Abba amma ta ta6a haihuwa ne?" Kai ta kad'a a hankali "Good kuma Abba yak'i ta don hakan ne? Har yanzu suna tare and deeply in love so ki kwantar da hankalinki bazan ta6a k'in ki ba wai don baki haihu mun ba a gidan nan kuma duk wanda ya goranta miki da hakan zan tabbata na mishi ba dad'i ke bakisan matsalar ma ze iya yuwuwa daga ni bane?"
"Ai kaima kasan ba daga kai bane Ya Rouhi ba haka ranan wata tace mun wai dan bana haihuwa ne ka k'ara aure ba, I'm very sure kwanan nan zamuji Amal tana d'auke da cikinka."
"Subhanallahi! Don't you ever say that Rabba'atul Bait kin de ji rantsuwa ko? Wallahil azeem ban auri Amal wai saboda ke bakiya haihuwa ba, Nazeefah ban ta6a d'aukan rashin haihuwan mu a matsayin damuwa ko matsala a zamantakewan auren mu ba kuma bazan ta6a ba saboda nasani haihuwa yin Allah ne. Kuma da kike maganan kwanan nan za aji Amal na d'auke da juna biyu se mey? Ai d'an Amal kaman d'anki ne kaman yadda kema d'anki yake matsayin nata. Ke baki san duk mun zama abu d'aya ba yanzu? Kuma ki sani dan Amal ta haihu kafin ke doesn't mean anything, it won't change the fact that kece Rabba'atul Bait d'ina and that I love you so much. Saboda haka nakeson ki kwantar da hankalinki mu cigaba da addu'a Allah kawo mana nagari masu albarka ko bakisan sometimes Allah yana hana bawa haihuwa bane saboda ya ga yaron ze zo ya zame mai matsala?"
"Na sani Ya Rouhi."
"Toh sekiyi aiki da hakan kisa a ranki koda baki haihu ba bawai Allah ya k'i ki bane inda haihuwa wani abu ne da duk duniya ba wanda ze kai Aisha R.A yawan yara amma kuma mey? Ko miscarriage bamu ta6a jin tayi ba haka kad'ai ya isa ya kwantar miki da hankali Rabba'atul Bait."
"Thank you so much Ya Rouhi I'm so lost without you, wallahi bansan ya rayuwata zata kasance idan ba kai ba, ban ta6a neman abu na rasa a k'ark'ashinka ba please forgive me if I've every wronged you." Ta fad'a jikinsa tana kuka, rungumarta yayi yana shafa bayanta a hankali.
"It's okay Darling kibar kukan haka kinji? Ita kuma Asma'au Allah ya inganta ya raba lafiya."
"Ameen Ya Rouhi."
"Smile toh in san ranki ba a 6ace yake ba." Ya fad'a had'e da d'ago ta. Murmushin ta sakar masa kad'an "That's my girl bari in gama shiri toh."
"Zaka koma gun Amal ko?"
"Eh."
"Akwai abinda kake so in tayaka da shi?"
"Kawai ki daina damun kanki bana son in sake jin kina maganan rashin haihuwar ki a gidan nan kinji?"
"In shaa Allah Ya Rouhi yauwa se kud'in fees na Islamiyya na kasan mun shiga sabon term dukda yanzu ba kullum zanna samu ina zuwa ba saboda boko."
"Alright zan miki transferring shikenan ko akwai wata matsalar?"
"Babu bayan nan thank you."
"Don't mention" tayasa gama shiri tayi sannan ta rakasa har waje ta dawo ciki bayan ya sallameta.
***
Kasancewar Nazeefah ta cika masa ciki da abinci koda ya isa gidan Amal be buk'aci abinci ba se chan wajajen tara, serving nasa tayi ta zauna a gefe kasancewar macaronin be gameta ba yau. Cokali d'aya ya kai baki ya harar take.
"Subhanallah Habib Albi!" Tayi exclaiming a rud'e. Goran ruwan dake gefensa kawai ya bud'e ya shiga kwankwad'a seda ya kusan shanye duka ya cire. "Habib Albi lafiya?"
"Kitten mey kikasa a abincin nan haka?"
"Kaman ya mey nasa kuma Habib Albi? Wani abu ne?"
"Kinji gishiri da barkonon da yake ciki? Baki san bana son yaji bane?"
"Barkono da gishiri kuma Habib Albi?" Ta tambayesa da mamaki a iya saninta attarugu biyu tasa gishiri kuwa kad'an maggi ma tafi bawa k'arfi a girkin, mey Afzal yake cewa toh?
"Yes" ya jaddada mata tare da k'arar da ruwan goran plate d'in taja don d'anawa sede be barta ba yayi sauri yaja "Don't mind bazaki iya tasting ba."
"Wallahi attarugu biyu kacal nasa."
"Maybe yana da zafi ne."
"Toh gishirin fah? Har dana kusan sauk'ewa ma fa na d'ana kuma banji yayi rad'au ba please ka bani in ta6a inji." Plate d'in ya tura mata spoon d'aya takai itama ta harar gora ya mik'a mata da wuri nan ta kur6e itama. "Kinji?"
Mamaki ne ya cikata shin ya akayi haka? Abincin se kace an d'ibo ledan gishiri ne aka juye a ciki ga wani d'an banzan borkono "Habib Albi I'm so sorry wallahi ban san ya hakan ya faru ba believe me har dana kusan sauk'ewa ma na d'ana and everything was okay ka kira Safiyya ka tambayeta kaji."
"Haba Kitten me yayi zafi harda tambayan Safiyya? It's okay kinji? Karki damu ina Safiyya kirata tazo ta zubar da abincin don ko almajirai ban jin ya dace a basu abincan."
"Habib Albi dan Allah kayi hak'uri I'm very sorry."
"Ohh Kitten" yayi maganan had'e da dafe hannunta dake ajiye kan table d'in "It's really okay just be careful next time okay?" Kai ta gyad'a hankali har cikin ranta bata ji dad'in hakan ba, sam ta rasa ya akayi hakan ya faru koda wasa kuma bata kawo a ranta wai Safiya zata iya zuba mata borkono da gishiri cikin girki ba.
"In dafa maka indomie toh?"
"Karki damu."
"Habib Albi kayi fushi dani ne?" Ta tambayesa tamkar zatayi kuka.
"Meyasa zanyi fushi dake Kitten kinsan mey?" Kai zalla ta kad'a mar. "Sanya hijabinki muje muci abinci a waje."
"Hab-"
"Shhh not a word" da kansa ya kira Safiyya ta zubar da abincin sannan ya sanar da ita zasu fita. Suna fita ta d'au wayanta ta kira Nazeefah a karo na farko ta d'aga. "Aunty ina yini?"
"Lafiya ya kike?"
"Lafiya k'alau Aunty yau baki san meya faru ba."
"Meneh?"
"Hmmm abinci Aunty ta ke girkawa da ta shiga d'aki na saci idonta na shiga kitchen d'in na barbad'a borkono da gishiri akai gashi yanzu Uncle ya dawo ya kasa cin abincin k'arshe ma cemin yayi in zubar."
"Kai Safiyya!" Tayi exclaiming cike da jin dad'i.
"Wallahi Aunty."
"Wow kinci kyauta, aikinki yayi kyau yanzu ina suke?"
"Naga sun fita amma de kam beji dad'i ba da be tarar da girki mey kyau ba har a fuskansa naga hakan."
"Haka nakeso ki cigaba da gashi Sofin gaye niko na miki alk'awain sabon atamfa harda d'inki."
"Godiya nake Aunty."
"Yauwa se anjima aikinki na kyau" da haka sukayi sallama.
*****
Haka tun daga ranan sede Amal batayi girki ba se Safiyya ta zagaya ta zabga mata gishiri ko yaji aciki gashi koda wasa Amal bata ta6a zarginta ba saboda yadda ta amince da Safiyya ta rik'eta da zuciya d'aya bayan nan ga yadda it Safiyyan da kanta take nuna mata girmamawa da k'auna. Gashi kaman dagaske duk sanda girkin ya 6aci ta rink'a nuna damuwa. Abun daya sake d'aurewa Amal kai shine se idan Afzal ze zo mata ne girkin yake tashi 6aci idan ba haka ba girkinta me kyau takeyi idan baya nan amma da zaran ya dawo se gishiri da borkono su fara zarcewa. Abu kaman wasa seda Afzal ya ya tattare borkono da gishirin ya kulle a storeroom, attarugu kuwa ya kyautar don kar girkin nata yana 6aci sede aikin banza yayi. Muddin Amal tayi mai girki toh se gishiri da borkono yayi yawa. Sosai abun ya d'aure masa kai. Amal kam har kaman ta fara samun ta6in hankali ne tsan-tsan tashin hankali. Ba aikinta se kuka a gidan, ace wai yanzu Afzal nata baze iya cin girkinta ba? Hakan ba k'aramin k'ona mata rai yake ba. Gabad'aya ta fita daga hayyacinta barin ma yanzu da Afzal ya fara zancen hanata yin girki kwata-kwata don tun baya nuna damuwa abun ya fara damunsa. Ya rasa gane meke faruwa. Tunani ya fara kode iskokai ne suke mata wasa da hankali? Sede be san ta ina ze fara sanar da ita hakan ba, shi kansa ba wai ya amince da hakan bane, be ta6a ganin mace mey son addini kaman Amal tasa ba har taya iskokai zasu ci nasara akanta? Kullum suka fita seta tuna masa yayi addu'an barin gida haka idan suka dawo, na shiga bayin nan bata wasa da shi ko ruwan d'umi zata zubar setayi istihaza toh tayaya aljanu zasuyi nasara akanta? Sede kuma ba wanda yafi k'arfin jarawaba.
Kuka take sosai tana rantse mishi akan cewa lallai-lallai bata sa gishiri da attarugu ko d'igo ba cikin girkin amma ga abincin nan rad'au da uban borkono. Yau kusan sati biyu kenan suna abu d'aya.
"Kitten it's okay kibar kukan haka."
"Habib Albi please believe me."
"I do believe you Kitten I do" ya amsa yana share mata hawayenta amma ina se zuba sabi suke.
"Wallahi ban bud'e storeroom d'in na ciro gishirin ba kana iya zuwa muje ka gani ko kuwa ka tambayi Safiyya, a kulle d'akin yake wallahi ban bud'e ba" hannunsa ta kama da niyyan jansa storeroom d'in akan yaje ya gani sede yayi saurin tsayar da ita ta hanyan rik'e ta.
"Shhhh it's okay it's okay" ya fad'a yana k'ok'arin calming nata. "Calm down okay? I believe you, I do believe you Kitten nasan baki bud'e d'akin ba amma ai kinji amount na gishirin da yake cikin abincin ko?"
"Wallahi ban sa gishiri ba Yaya."
"I know Kitten and I do believe you, kinsan mey nake so da ke? Ki huta na kwana biyun nan kar ki sakeyin girki duk abinda kikeso zan siya miki ko kuwa Safiyya ta girka miki amma ke karki sake aza tukunya a gidan nan hala stress na school ne yake damunki you need to rest."
"Har zuwa yaushe Habib Albi? I don't need to rest ba hauka nake da shi ba wallahi ban sa gishiri cikin girkin nan ba you have to believe me tunda ka tattare gishirin ka rufe a store ban sake yin girki da shi ba, taya zakace kar in sake aza tukunya a gidan nan Habib Albi?"
"It's just for some time Kitten please stop crying" Ya amsa yana share mata rushing tears nata had'e da rungumarta "Kiyi hak'uri kibar girkin na kwana biyu until everything is okay kinji?" Jikinta ta janye daga nasa "Kai kuma fa Yaya? Wa ze na maka girki? Wa ze na dafa maka abinci? Shikenan bazaka sake cin girki na ba?"
"Wayace bazan sake cin girkin ki ba Kitten? It's just for the mean time okay? Zan na ci a restaurant kafin nan kin huta kema I'm sure stress ne ya miki yawa."
"Yaya wani irin stress? Wallahi ba wani stress dan Allah kar ka hanani yi maka girki I beg you please Yaya" kuka take sosai tana rok'ansa. Hannayensa ya kama acikin nata.
"Kitten dan Allah kibar kukan nan haka bawai hanaki yi mun girki nake shirin yi ba its just for the meantime."
"Yaya please I beg you, I promise daga yanzu zanna sa hankali maggi baze sake zarce mun ba please kar ka hanani yi maka girki."
Kuka take sosai shi kansa ya rasa mey yake ciki shin ya kira malami a yi mata ruk'iya ne? Kokuwa likitan mahaukata ze nema? Shin meyake damun Kitten tasa? He don't want to believe ta6in hankali ne ke shirin kamata, he can't afford to lose her. Taya zata na rantsuwa bata sa gishiri da barkono a girki ba amma kuma ga abinci rad'au? Meke faruwa? Hugging nata yayi gam a jikinsa yana shafa bayanta har suka sauk'a k'asa akan gado. Be saketa ba seda ya tabbata bacci ya d'auketa. A hankali ya shimfid'ar da ita akan gadon ya rufeta da bargo sannan ya fito. D'akin Safiyya ya nufa yayi knocking bisa k'ofan take ta amsa ta fito.
"Sannu Uncle."
"Safiyya?" Ya kirata "Na'am?" ta amsa tana kallon k'asa. "Meyake faruwa idan na tafi office?"
"Kaman ya Uncle?"
"Meyake samun Auntin ki? Meyasa girkinta kullum gishiri yake zarcewa bayan na tattare gishirin na kullesu a d'aki ke kike d'auko mata?"
"Wallahi ba ni bace Uncle kuma kaman yadda baka sani ba wallahi nima banida masaniya game da abinda yake faruwa ni kaina mamaki abun yake bani a ido na tayi girkin d'azun nan maggi da tattasai zalla tasa kuma har da ta kusan sauk'ewa seda muka d'ana mata amma da zaran ansa a flask se abincin ya 6aci."
"Are you sure?"
"Na'am?"
"Nace kin tabbata?"
"Eh Uncle."
"Bake kike yin gwaninta ki k'ara mata a bayan idonta ba?"
"Meyasa zanyi hakan Uncle? Allah ma shaidana ne."
"Huhhh" nauyayyan ajiyan zuciya ya sauk'e.
"Ban so inyi maganan ba d'azu a gabanta sede ranan naga Aunty tana wani abin al'ajabi."
"Abin al'ajabi?" Ya tambayeta cike da rashin fahimta.
"Eh uncle a kitchen ranan naganta tana magana da kanta haka jiya ma."
"Tana magana da kanta kuma?"
"Eh Uncle ita kad'ai sekaga tana suratai dama Aunty tana da aljanu ne?"
"Aljanu kuma? Kina ganin aljanu ne suke mata wasa da hankali?"
"Toh ban sani ba amma da abun tambaya dan akwai wata k'anwar mamar mu a k'auye da aljanu suka tak'ura mata. Itama amarya take kaman Aunty amma sai dai bata d'aura girki ba baya nuna. Ko kwana kwanon zeyi akan murhu baze ta6a nuna ba daga k'arshe seda aka kaita gun Malami akayi mata ruk'iya sannan ta samu sauk'i."
"Subhanallah" ya furta yana shafa sajensa "I'll figure out what to do dan ko ni na fara zaton aljanun ne nima gashi de kema kince bata sa gishiri toh taya abincin yakeyin rad'au haka?"
"A gwada nemo malami yayi mata ruk'iyan ni kaina tausayi Aunty take bani wallahi se kaga kukan da takeyi d'azu."
"Kiga koda wasa kar ki nuna mata munyi maganan nan kinji ai ko? Bana son kowa yaji maganan daga ni sai ke, kin gane?"
"In shaa Allah Uncle Allah ya bata lafiya."
"Ameen" da haka ya koma d'akin nasu ya zauna a gefenta hannunta ya rik'o cikin nasa a hankali yana murzawa "Kitten what's really going on? Meyake faruwa? Why is this happening to you?" Sosai ya tausaya mata he can't believe aljanu na son haukatar masa da ita.
Kuka sosai Amal ta sha washegari da Afzal ya hanata yi masa breakfast yasa Safiyya. Ko makaranta tak'i fita ranan tun fitan Afzal ta rufe kanta a d'aki tana kuka, se hak'uri Safiyya ke bata kaman dagaske chan tace zata shiga bayi tana ficewa taje ta kulle kanta a d'aki ta d'au paper'n da Nazeefah ta rubuta mata lambarta ta zuba tare da danna mata kira.
RANA D'AYA!
#RD
Love... King Miemiebee👄✨
[13/08, 09:37] +234 907 483 8352: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
August, 2018
beeenovels.blogspot.com
_Written by Miemiebee👄_
*PAGE 3⃣2⃣*
"Assalamu Alaikum Aunty ina kwana?"
"Sofin gaye ya kike?"
"Lafiya k'alau Aunty ya Hindu?"
"Hindu tana gida ni na fita school ya uwar d'akinki?"
"Hmmm Aunty ina da labari mey dad'i miki."
"Kai Sofin gaye har ta gama haukacewan ne?"
"Gashi Uncle jiya yazo d'akina yana tambayata ko meke faruwa na tsara mishi labari kaman yadda kikace inyi yanzu haka yace ze nemo malami ayi mata ruk'iya don shima ya fara zargin ko aljanun ne."
"Kin min dau-dai shin ta sake yi masa girki?"
"Ai hanata yayi yau gata chan a d'akinta se kuka take."
"Bravo alaiki Sofin gaye tsaraban ki na nan na tanadar miki."
"Toh amma Aunty yanzu idan aka kira Malamin ya duba ta yace lafiya fah? Za a iya gano ni ke k'ara mata gishirin fah."
"Inji wa? Taya za a gane ki bayan duk malaman ruk'iyan nan kud'i kawai suke so? Da mutum nada ciwo da bashida shi muddin an kaisa gun su se sun bada magani dan abasu kud'i in return saboda haka ki kwantar da hankalinki in shaa Allah baza a kama ki ba kede ki cigaba da gashi."
"Toh Aunty."
"Mission number one complete muddin akayi mata maganin kar ki sake 6ata mata girki mu barta nan haka se idan an kwana biyu se mu fara mission number two."
"Ohh kar in sake sa mata gishirin?"
"Eh mana baya riga ya hanata yi mai girki ba yanzu?"
"Eh."
"Toh kinga idan akayi mata maganin seya zammana kaman dama akwai matsalar amma an samu an magance yanzu."
"Nagane."
"Yauwa jeki sameta kiyita bata hak'uri idan Ya Afzal ya dawo kice d'azu ma kin ganta ita kad'ai tana suratai."
"Toh Aunty" da haka sukayi sallama. Wani irin dad'i maras misaltuwa Nazeefah taji burinta ya cika ta haukatar da Amal ta sa Afzal ya daina cin girkinta, ita taso ace ta6in hankali ma Afzal ya soma zarginta da shi bama aljanu ba yadda za a d'auketa akaita chaan asibitin mahaukata ta fara rayuwarta ta bar mata Afzal nata amma hakan ma be 6aci ba.
****
Da Azahar Afzal ya wuce restaurant yaci abinci daga chan ya biya gida gun Ummi kallo d'aya tayi masa ta gano akwai matsala.
"Prince?"
"Ummi" ya amsa a ksalance.
"Meke faruwa?" ta tambayesa.
"Ummi it's Amal."
"Subhanallah lafiya dai ko?"
"Ummi I don't know na rasa gane ta6in hankali ne yake neman kamata ko kuwa aljanu ne suke mata wasa da hankali."
"Subhanallahi meya faru? Wani abun tayi ne?" Labarin komi ya kwashe ya bata batare da ya skipping komai ba.
"Shine baka ta6a bud'an baki ka fad'a mun ba Prince? Allah sarki Amal gata mahadacciyar Qur'ani oh! kowa da tasa jarabawan amma anya kuwa aljanu ne? Ba ta6in hankali ba?"
"Ummi I don't know I'm totally clueless kuka take yau seta yimun breakfast amma na hanata saboda ko tayi ba iya chi zan ba banda gishiri da borkono ba abinda yake cikin girkinta yanzu."
"Kuma ba ita take sawa ba?"
"Gashi na tambayi Safiyya tace a gabanta Amal tayi girkin bata sa gishiri ba shiyasa nake zaton ko aljanu ne."
"Kuma gashi yarinyan tace tana ganinta tana magana ita d'ai?"
"Har sau biyu ma tace."
"Ikon Allah kode aljanun ne toh?"
"Shine nima ban sani ba mu fara kaita psychiatric hospital (asibitin mahaukata) ne su duba ta ko mu fara dana gargajiyan?"
"Toh nide gani nake kaman aljanu ne amma a fara kaita asibitin idan sun kasa gane kan abun se mu dawo na gargajiyan, akwai sanannen malamin dana sani yana ruk'iya sosai zan nemesa."
"Toh yanzu ya zan fara sanar da ita zan kaita asibitin mahaukata Ummi? Wallahi bazata amince ba bayan nan kuma gani zatayi kaman naci amanarta ne ina danganta mata ciwon hauka kuma bana son su Mami suji maganan nan se idan abu ya gagara tukun zamu sanar dasu ko ba haka ba?"
"Tabbas kayi tunani Prince tunda de yanzu Amal responsibility'n muce."
"Toh kinga..."
"Ka san yadda zaka sanar da ita Prince ai matarka ce zata fahimce ka in shaa Allahu."
"Toh Ummi I'll try, please karki manta kiyi wa Malamin magana."
"In shaa Allah Prince kuma duk abinda akwai ka kira ka sanar dani Allah ya bata lafiya."
"Ameen bari zan koma" rakiya tayi masa sannan ta dawo ciki. Yana isa gida Safiyya tayi mishi sannu da zuwa sannan ya k'arisa d'aki inda Amal ke mik'e akan gado amma ba bacci take ba ko da taji shigowansa bata juya ta kallesa ba Sallama yayi ta amsa ciki-ciki ba tare da ta kewayo ba. Kayan jikinsa ya rage sannan ya k'arisa gefen gadon ya zauna a gefenta.
"Kitten?" Ya kirata sede bata amsa ba. "I called you twice baki d'aga ba why?"
"Ban san inda na jefar da wayan ba" ta amsa ba tare da ta kallesa ba. Hannu ya mik'a ya mik'ar da ita zaune "How're you feeling?" Ya tambayeta.
"Kaci abinci?" Ta mayar masa tunanin da take tayi tun d'azu kenan, shin yaci abinci, mey yaci? Ya k'oshi? It pains her alot idan ta tuna Afzal baze sake cin girkinta ba yanzu, sosai zuciyarta keyi mata k'ona.
Allah sarki sosai ta basa tausayi, bata ma damu da lafiyarta ba, ita burinta kawai taji yaci abinci ne, "Kefa kin ci?" Ya tambayeta.
"Yaya I really want to cook for you koda sau d'aya ne ka barni in sake yi maka girki please Yaya I miss feeding you" ta rok'esa yayin da idanunta suka shiga cikowa da hawaye.
"Kitten please cut it out, kibar kukan haka."
"Then allow me cook for you and feed you one last time."
"Baby" ya ambaci sunanta had'e da rik'o hannunta cikin nasa yana murzawa a hankali "Ba kida lafiya ki bari se in kin samu sauk'i kinji? I myself miss your cooking kinsan kece best cook d'ina ko?"
"Yaya can't you see? I'm perfectly okay wallahi lafiyata k'alau ba abinda yake damu na" kwantar da ita yayi a jikinsa yana shafa bayanta a hankali "Zamu kaiki asibiti gobe su duba ki in shaa Allah idan kika samu sauk'i se kiyi resuming normal duties naki ki cigaba da yimun girki kinji?" cike da rashin fahimta ta d'ago kanta tana kallonsa "Asibiti Habib Albi?"
"Kitten I'm so sorry-"
"No" ta furta cike da tashin hankali tare da janye jikinta daga nasa.
"Kitten please understand me-"
"No Yaya" da sauri ta janye hannunta da yake k'ok'arin rik'ewa "Mey kake nufi da hakan? Ina da hauka?" Ta tambayesa cike da d'umbun mamaki.
"No Kitten ba haka nake nufi ba" ya amsa a rud'e shima, a rayuwa ba abinda yafi tayar masa da hankali kaman yaga Amal tana kuka, da zaran yace ze rik'e hannunta se ta ja da baya.
"Ni Mahaukaciya?" Ta ambata da mamaki yayinda hawaye ke bin k'uncinta.
"Kallon mahaukaciya kake mun Yaya?"
"Kitten please-"
"Yaya.." kasa cewa komi tayi kawai ta rushe da wani irin masifaffen kuka yayinda ta mik'e da hanzari dan bar mai d'akin. Hannunta ya cafko ya kwantar da ita a jikinsa had'e da matse ta gagam wane wani na shirin k'watar masa ita. Kokowa take sosai ya saketa amma yak'i hak'uri ya ta bata yana shafa bayanta a hankali har seda ya sauk'ar da temper'nta. A hankali ya d'agota yana share mata hawayen nata "Kitten please understand me bawai cewa nayi kina da hauka ba, bazan ta6a kwatanta ki da mahaukaciya ba but contrary to abubuwan da suke faruwa bakiya tunanin ko akwai wata matsala?"
"Yaya ashe Allah ze kawo ranan da zaka yi mun kallon mahaukaciya?" Ta tambayesa hawaye na bin k'uncinta.
"Kitten I will never refer to you as that kema kin sani I love you and I only want the best for you, dan za ki ga psychiatrist doctor (likitan mahaukata) bawai hakan na nufin kinada hauka bane, ze iya yuwuwa wani matsalan ne daban yake damun ki psychologically ko stress ko makamancin hakan."
"There is no stress Yaya and I'm not losing my mind ni ba mahaukaciya bace kana tsammanin zansa gishiri acikin girki ba tare da na san nayi hakan bane? I told you ni bani kesa gishiri da attarugu ba, ba ni bace!" Sosai ranta ya 6aci taya upon all people Afzal baze yarda da ita ba? Taya za'a ce mijinta tilo yana yi mata kallon mak'aryaciya kuma mahaukaciya? Cikin tsananin kuka tace, "I thought you love me Yaya, I thought you trust and believe in me."
"Of course I do Darling, I love you with every burning fiber in my soul and I do trust and believe in you than I do myself."
"No Yaya inda har kana nufin abinda ka fad'a da baza ka fara tunanin kaini gun likitan mahaukata ba, da zaka yarda dani idan nace maka bani kesa gishiri da borkono cikin girkin ka ba."
"I know Kitten nasan ba ke kike sawa ba shiyasa na fara zargin ko aljanu ne suke miki wasa da hankali."
"Aljanu? Yanzu kuma mey kallon iskokai kake mun Yaya? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" juyawa tayi da niyyan bar mai d'akin bata ma jin zata iya yi masa magana. Da sauri ya sha gabanta "Kitten please ki fahimceni ki sani lafiya nake nema miki wallahi na gaji da ganinki haka cikin k'unci da kuka kullum, kiyi hak'uri ki bari a magance miki wannan matsala please."
"Ni bana tattare da aljanu I know how I feel saboda haka ba wanda zeyi mun ruk'iya, nasan kaina kuma na dogara da addu'o'in da nakeyi."
"Kitten bawai ina jayayya da hakan bane ni kaina sheda ne game da yadda bakiya wasa da addu'o'in kariyan nan I'm aware of everything."
"Toh mey kake nufi Yaya? Kallon mey iskokai da ta6in hankali fa kake mun how do you expect me to feel and react?"
"Darling I'm sorry but I'm just worried, ke da bakinki kika ce bake ke sa gishiri da borkonon nan ba kuma na amince da hakan I trust you Kitten amma toh wa yake sawa? Bakiya tunanin akwai wata 6oyayyan al'amari? Kuma baza mu ta6a iya gano inda matsalar take ba bale a magance miki se har idan kin amince kin bada had'in kai Kitten. I promise no harm will come to you, I've got you Baby, ba wanda yace kina da ta6in hankali I just need to find out what's really going on. Please calm down everything is going to be alright in shaa Allah okay?" Ya k'are yana matso da ita kusa da shi. Cike da dabara ya kwantar da kanta a k'irjinsa yana shafa kanta "I love you so much" ya furta mata, a hankali yaji hannayenta a bayansa tana hugging nasa back "I love you too" ta furta. Washegari Afzal be fita office ba, wanka sukayi tsaf tare suka shirya, da kansa ya had'a musu breakfast sannan suka wuce psychiatric hospital inda aka duba Amal akayi mata gwaji da dama akan washegari su dawo su kar6i sakamako.
Washegari Afzal ya koma ya amshi results d'in shi kad'ai kasancewar daga office ya biya wajen sede da mamaki sakamakon ya nuna ba abinda yake damun Amal, hankalinta dai-dai yake dana mutane ba wata matsala. Hakan ba k'aramin d'aure wa Afzal kai yayi ba don haka kawai ya yanke hukuncin aljanu ne toh sukeyi mata wasa da hankali nan take ya kira Ummi yayi mata bayani dama ta riga tayi magana da Malamin yace koda yaushe suka shirya suje yana jiransu. Address kawai ta tura masa.
Gida gun Amal ya koma yaci ace ya koma gun Nazeefah dake kwanan Amal ya k'are amma baze iya barin Amal cikin wannan yanayi da iska suke wasa da hankalinta haka ba har se idan ya samo mata lafiya. Nazeefar yayi niyyan kira ya sanar da ita halin da ake ciki se ya sha'afa. Itako chan a gidanta ta gama girki ta gama komi jiran zuwansa kawai take amma shiru gashi har shida da rabi yayi. Jin shirun yayi yawa gashi be kirata ya sanar da ita dalilin hakan ba ta d'au waya kawai ta kirasa a karo na farko ya d'aga suka gaisa.
"Kin jini shiru ko?"
"Eh Ya Rouhi lafiya?"
"Amal ce bataji dad'i ba I'm afraid I can't make it today ina fatan hakan ba matsala."
"Allah sarki meke damunta?"
"Ermm... ermmm zazza6i ce" yayi mata k'arya haka kawai yaji baya son ya fayyace mata gaskiyan al'amarin. Amal na kwance kan cinyansa tana sauraransu.
"Ayyah ka gaisheta da jiki da Allah, Allah k'ara mata lafiya zan kirata in gaisheta."
"Ameen in shaa Allah ba wata matsala ko?"
"Ba komai."
"Toh seda safe I'll call you tomorrow."
"Alright take care" wata mak'irar murmushi ta sakar yayin da ta katse wayar. "Ai kad'an ka ga se zaman gidan chan ya gagareka you'll see."
"Nazeefah na gaisheki" ya sanar da Amal had'e da sanya hannunsa cikin gashin kanta yana massaging mata cikin kai a hankali, kai zalla ta gyad'a masa. "Kina jin yunwa?" Nan ma kai ta kad'a a hankali.
"I called Ummi earlier batun Malamin tace ta riga tayi mai magana so she sent me his address gobe zamu kaiki baki da wani test a school ai ko?"
"Babu" ta amsa ciki-ciki. Wace irin msuiba ce wannan? Tana ji tana gani ana dangata mata ciwon aljanu ciwon da tasan ba ta da shi. Kan nata ya cigaba da massaging mata chan ya dafa musu indomie bayan sun gama ci sukayi wanka sukayi sallah suka tofe addu'an bacci sannan suka kwanta. Washegari da yamma bayan sallan La'asar suka wuce gidan Malamin. A mota ya barota ya k'arisa ciki bayan sun gaisa yayi wa Malamin bayanin abinda yake damunta ciki harda ce masa da Safiyya tayi akan Amal ita kad'ai tana magana ya kuma buk'acesa da koda ya shigo da Amal d'in kar yayi maganan komai a gabanta. Bayan Malamin ya fahimce shi ya koma ya shigo da Amal karatu Malamin ya shiga yi mata amma ba alamun komai a tattare da ita, bayan ya k'are karatun yayi mata hayak'i nan ma ko alaman aljanu babu.
"Gaskiya bata tattare da iska sede ze iya yuwuwa shafanta sukeyi su barta amma bawai sun shiga jikinta ba."
"Toh yanzu ya kenan Malam?" Afzal ya tambaya.
"Sede ince ta dage da addu'a ta kuma rage kalle-kalle da fita da kai a bud'e. Zan baku turaren almisky tana amfani da shi tana kuma shan man hul6a ta na karatun Al~Qur'ani sosai in shaa Allahu iskokan zasuyi nesa da ita."
"Tana yi sosai wallahi Malam mun gode in shaa Allah zata kiyaye duka ababen da ka irgon."
Almiskin ya d'iba musu da man hul6an Afzal ya biya kud'in. Tun shigansu mota har suka dawo gida Amal bata mai magana ba. Waje ya fita ya kira Ummi ya sanar da ita abinda Malamin yace.
"Ai Malamin ya iya aiki da ikon Allah zata samu sauk'i kuma shi ba ta kud'i yake ba kaga idan wani ne yanzu ya rink'a raina mana wayo kenan yana mana k'arya akan lallai akwai aljanun a jikinta ayita ruk'iya ana kashe kud'i ana bata wuya."
"Hakane kam wallahi thank you so much Ummi."
"Ya Amal d'in toh?"
"Lafiyarta."
"Tana kusa ne ka had'amu?"
"Eh toh" nan ya bud'e k'ofan ya dawo ciki ya k'arisa ciki. "Kitten?" Ya kirata.
"Uhmm?" Ta kewayo tana kallonsa
"Ga Ummi tana son ku gaisa" ba gardama ta amsa suka gaisa sannan ta miyar masa. Ya so ya sake kwana mata amma baya son ya shiga hak'k'in Nazeefah dayawa dan haka ya shiga tattare abubuwan da ze buk'ata. Yana gamawa ya kewayo kan Amal dake mik'e kan gado "Kitten zan koma wajen Nazeefah" ya sanar da ita yana takowa inda take hannunsa ya mik'a mata kamar wacce bazata kama ba tasa nata ciki a nitse ya mik'ar da ita yana shafa fuskanta a hankali.
"Kina amfani da turaren kinji? Man hul6an kuma kina sha safe da yamma kaman yadda Malamin ya fad'a nasan kina karatun Al~Qur'ani sosai ba sena ce kiyi ba Allah baki lafiya Sweetheart I love you so much." Kai ta gyad'a masa a hankali "Muje in raka ka" da sauri ya rik'o ta kafin ta ku6uta daga hannunsa yana mey zagaye hannayensa a 'yar kunkuminta.
"Where's my cheerful and loving Kitten please tell her I miss her so much and that I want her back" yayi maganan yana shafa kan lips nata a hankali da babban yatsansa. "Allah baki lafiya Kitten I can't wait for you to get better, I love you so much."
"I love you too Habib Albi" ta sanar da shi a hankali ya mik'a yayi owning lips nata kissing her gently and taking her fears away seda nishinta ya kusan d'aukewa ya saketa ya shiga shafa fuskanta a hankali "Take care of yourself okay? Duk abinda kike buk'ata ki fad'awa drivernki yaje ya siya miki idan kuma Safiyya zata iya seta girka miki amma kar ki sakeyin girki se kin samu sauk'i kinji?" kai zalla ta gyad'a masa. "Na ajiye miki kud'inki a gaban mirror ki kwanta ki d'an huta kafin Maghrib Sena dawo."
"Thank you bara in raka ka."
"A'a kiyi zaman ki I can manage" peck ya sauk'e mata akan goshi sannan ya fice. Koda ya koma gun Nazeefah hankalinsa gabad'aya na akan Amal ne minti minti yake d'aukan waya yana kirarta yana tambayarta ko lafiya se yanzu yake regretting meya hanasa amsan lamban Safiyya da ita zena kira yana tambaya ko lafiya baya son abin da tak'urawa Amal tasa, sosai yake missing nata ji yake shima kaman ba shida lafiya. He can't explain how much he's missing her giggles, laughs and smiles. Suna zaune a d'aki Nazeefah na masa tausa tayi gyaran murya "Ya Rouni?" ta kirasa cikin wani irin salo.
"Yes Rabba'atul Bait?"
"What's wrong tun shigowanka jiya na ganka wani iri meke damunka?"
Be 6oye mata ba ya sanar da ita gaskiyan al'amarin "It's Amal Rabba'atul Bait I'm worried about her."
"Allah sarki zata samu sauk'i in shaa Allah muna kan mata addu'a."
"Thank you Rabba'atul Bait."
"Don't mention love amma ciwon nata zazza6i ne kawai?"
"Wani abu ne?"
"A'a d'azu dana kirata ne take cemun wai abun nata harda iska-iska haka."
"Ita da bakinta?"
"Eh" ta jaddada masa dukda kuwa tasan k'arya takeyi basu ma yi waya da Amal ba yau bale har wai Amal ya sanar da ita akan iskokai ne suke damunta.
"Malamin yace basu shige ta ba kawai sun shafeta ne amma ya bamu magani in shaa Allah zata samu sauk'i."
"Allah sarki Amal, shin bata karatun Al~Qur'ani ne? Kasan ance aljanu basa kama me yawaita karatun Al~Qur'ani."
"Tana yi kinsan shi jarabawa kowa da irin nasa, Amal mahaddaciyar Al~Qur'ani ce kullum seta d'au Qur'ani tayi karatu I guess wannan itace jarabawarta." Haushi taji sosai Amal na da haddan izu sittin akanta ita tana nan tana fama da izu goman k'asa. Taya bazata tsani Amal ba bayan ta ko ina seta nuna tana son ta k'ureta.
"Allah sarki Allah bata lafiya toh" ta fad'a ba don tana so ba tana k'wak'ulo murmushin dole.
"Ameen" ya amsa.
****
Duk da kwanan Nazeefah ne hakan bai hana Afzal zuwa duban Amal da safe kullum kafin ya wuce office, da kwanan ta ya zagayo kuwa komi shi yake k'ok'arin yi mata, ba k'aramin kula da ita yake ba. Da yamma idan ya dawo daga office zasu d'au Qur'ani suyita karatu har zuwa Magriba. Tun ranan da suka dawo daga gun Malamin Afzal be sake gane kan Amal ba. Gabad'aya yanayinta ya canza a gidan sa6anin yadda suke zama suyi hira suyi dariya yanzu kam jugum sede shine ma yayita zuba ita befi tana amsa sa da eh ko a'a ba. Hakan ba k'aramin damun Afzal yake ba he can't explain how much he's missing her.
Yau sati biyu kenan tun dawowansu daga gun Malamin, cikin ikon Allah ta shiga sake sakewa da Afzal ta fara yi mai hira har suka koma zama yadda suke da. A hankali a hankali suka fara shiga kitchen tare suna yin girki har yazo ya fara barinta tanayi ita kad'ai. Afzal baze iya kwatanta irin murna da farin cikin da ya tsinta kansa aciki ba da Amal ta soma yin girki ba matsala yanzu, Ummi ya soma kira ya sanar da ita. A kullum son Amal dad'a k'aruwa yake a birnin zuciyansa, tabbas baze iya rayuwa ba ita ba.
Yau ya na tashi daga office ya wuce gida straight he can't wait ya iso gida ya samu Kitten tasa. Fresh flowers ya tsaya ya saya mata a florist shop sannan ya k'arisa gida. Sede sa6anin kullum yau Kitten tasa bata fito ta tare sa ba k'arisawa ciki yayi amma Safiyya kad'ai ya tarar bayan ta mai sannu da zuwa ya tambayeta ko ina Amal take ta ce mai tana d'aki. D'akin nasu ya k'arisa sede be ganta ciki ba, kasa kunnen da zeyi yaji splashes na ruwa a bayan gidan don haka yayi knocking bisa k'ofan "Kitten I'm home."
"Welcome home Habib Albi."
"Mey kikeyi wanka?"
"Eh" ta amsa.
"In shigo?"
"Ka shigo Habib Albi" ta amsa tana murmushi, kayan jikinsa ya rage ya d'aura towel sannan ya d'au flower'n ya shiga bayin. "Here this's for my adorable Kitten."
"Awwn thank you Habib Albi" tace tare da amsa "I love orchids" ta sanar da shi "Don't mention Love, matsa min toh in shiga" batayi gardama ba ta gyara masa ya shiga ya zauna had'e da riginginar da ita a jikinsa. Wasa suka tayi cikin tub d'in k'arshe suka wanke jikinsu suka d'aura alwala sannan suka fito. Sosai yaji dad'in kwana biyun da sukayi tare ba k'arya yayi missing delicious nata baze fasa yima Allah godiya ba da ya bawa Kitten nasa lafiya. Musamman ya koma gun Malamin da yayi musu maganin ya mishi kyautan kud'i. Kaman kar ya tafi yau da kwanansa ya k'are, yadda ta saba raka sa haka tayi ta kaisa har gun mota inda ya shiga kissing nata awajen be saketa ba seda ya tand'e jan bakin data shafan tas sannan ya sallameta ta dawo ciki. Yana isa gidan Nazeefah ta taresa da wani hot kiss nata itama bayan sun k'arisa d'aki seya karanci yanayinta ya sauya a lokaci guda.
"Rabba'atul Bait lafiya?"
"Ai kai zan tambaya Ya Rouhi" ta amsa tana turo baki
"Da nayi me Sweetheart?"
"Ba wani Sweetheart d'innan ai nasan inda ka ajiye ni."
"Haba Darling meya faru haka?" tasowa yayi daga gaban mirron ya k'arisa inda take had'e da zauna a gefenta.
"Gaya mun waya ta6a mun Rabba'atul Bait d'ina."
"Ba amaryarka bace."
"Amal?" Kai ta gyad'a cike da shagwa6a.
"Me kuma tayi?"
"Cemin tayi kullm ka fita seka taho mata da flower ni dai-dai da RANA D'AYA ko yashi baka ta6a ibowa kace gashi Rabba'atul Bait wannan naki ne shin kana ma sona kuwa Ya Rouhi?" Mamaki da kunya yaji duka a lokaci d'aya. Be ta6a tsammanin hakan daga gun Amal ba. Wani irin abin kunya take shirin yi masa haka? Taya zata na fad'awa Nazeefah abinda yake mata? Meye riban hakan?
"Bayan nan kuma tace sede baka je gida mata ba baka bari ta zauna a ko ina se a kan cinyanka, ko abinci akan plate d'aya kuke ci ni duk baka mun ko d'aya Ya Rouhi" ta sanar da shi kar kusha mamaki komi nan Safiyya ne ke fad'a mata. Afzal baze iya kwatanta irin tsananin kunyan da yaji ba yayinda ya kasa daina mamakin dalilin da zai sa Amal tayi masa haka, shin mey ya buga mata kai? So take ta 6ata tsakaninsa da Nazeefah?
"Rabba'atul Bait I'm really sorry" ya furta cike da disappointment, a hankali ya d'agata ya zaunar da ita kan cinyoyinsa.
"Ba komai dama nasan kafi son Amal akaina ai."
"Please don't you ever say that nasan nayi kuskure amma kiyi hak'uri I'll make it up to you in shaa Allah I promise." Hannayenta ta zagaye a wuyansa "Can I count on you?"
"In shaa Allah Rabba'atul Bait, I love you so very much."
"I love you more Baby" ta amsa fuskanta ya shiga bi yana kissing har seda ya kai kan lips nata.
***
Bayan sallan isha ya d'auketa a mota suka je suka ci abinci a waje daga chan suka wuce 3G inda ta kwashi jakukkuna guda uku masu kyau, tana jiran taji yace bari ya d'auka wa Amal kaman yadda ya saba fad'a ta ji yayi shiru yau kud'in kawai ya biya suka fito. Ai kuwa idan haka ne plan nata ya fara aiki kenan, da alama bai ji dad'in abinda tace masa Amal tayi bane shiyasa ko jakar ma yak'i sai mata, ai ko idan haka ne ta ringa 6ata Amal a gabansa kenan se tasa ta fita masa a rai gabad'aya. Zata sa Safiyya ta musu ido sosai tana d'auko mata rahoto.
***
Kamar yadda ta d'au alk'awari hakan ta cigaba da 6ata Amal gaban Afzal, duk abinda yayi ma Amal se Safiyya ta kwashe ta fad'a mata itako idan kwanan ta ya zagayo seta maraice fuska tace ai gashi-gashi abinda Amal ta kirata ta fad'a mata. Sosai abun yake k'ona ma Afzal rai be ta6a sanin Amal da halin nan ba se yanzu shin meye ribanta na fad'awa Nazeefah abubuwn da yakeyi mata? Sabida ta 6ata tsakaninsu ne take hakan kokuwa dan ta nuna wa Nazeefah a fili baya adalci a tsakaninsu? A kullum 6aci ransa yake idan Nazeefah ta irga masa abubuwan da yayi ma Amal wanda beyi mata ba amma dai-dai da RANA D'AYA be ta6a tunkarar Amal da maganan ba. A tunaninsa da kanta zata gano abinda takeyi ba dai-dai bane ta daina amma ina abun se worse yakeyi ko bathroom slippers ya sai mata be sai wa Nazeefah ba seya ji a bakin Nazeefah sosai abin ya isheshi har ya zamma ko tsinke ya daina saiwa Amal yana kai mata idan har ya sai mata abu to ya sai wa Nazeefah ne amma special treatment kam ya daina bata.
****
Yau ranan ya kewayo kwanan Amal wanka tayi tasha kwalya tasa sabon d'inki ba k'aramin kyau tayi ba sannan tayi zaman jiransa se after six ya iso shida kullum 5:30 ya shigo. Tun daga bakin parking lot taje ta taresa sede kaman zuwansa na biyu da suka wuce yau d'inma haka ya shigo fuskansa a d'aure, d'aure fuskan yau d'inma yafi na kowanne, ko attempting kissing nasa da ta gwada yi se taga yayi dodging abinda be ta6ayi ba shin meke faruwa? Jakansa ta gwada amsa nan ma ya hanata ya wuce gaba, cike da mamaki ta bi bayansa suka k'arisa ciki.
"Ya office?" ta tambayesa bayan sun shigo d'akinsu.
"Lafiya" ya amsa sama-sama ko kallonta beyi ba. Toh me tayi yake shasshareta haka?
"In sirka maka ruwa ko?" Ta tambayesa.
"Yanzun na yi a chan gida karki damu."
"Toh muyi tare" ta sake fad'a duk don ya amince. "Maybe next time" ya amsa nan ma ko kallonta beyi ba. Wow! Shin meke faruwa? Ta tambayi kanta.
"Toh abinci fah?" Ta sake tambayansa a hankali, sosai jikinta ya mutu da irin short-short answers da yake bata.
"Nazeefah ta bani" ya amsata, amsan da a iya zamansu be ta6a bata ba.
"Habib Albi amma kullum fa kana ci idan ka dawo."
"Bana jin yunwa Amal" taji ya kirata gatsau da sunanta. Tirk'ashi! Bata sake yi masa magana ba se chan wajajen k'arfe tara. A tunaninta wai ko stress ne daga office yake sanya sa yin abinda yake yi bari ta barsa ya huta. Bayan ta k'are karatun Al~Qur'ani ta d'an ta6a na bokon ta fito ta sami Afzal dake zaune a parlour yana kan tattara documents nasa yana sanya su cikin briefcase. K'arisawa tayi ta zauna akan cinyansa.
"Sekin yi hak'uri kin tashi na buge k'afa na d'azu zafi yake mun" yayi mata k'arya.
"Subhanallahi! Sannu shine baka sanar dani ba? Mu shafa maka man zafi ne?"
"Karki damu I'll be fine" da haka ya sauk'eta.
"Baka ci abinci ba Habib Albi."
"Bana jin yunwa."
"Kana nufin yau abinci na zeyi kwante kenan?"
"I'm sorry but I guess yes excuse me" yana kaiwa nan ya d'aga briefcase nasa ya koma d'aki. Mamaki ne sosai ya cika Amal shin mey tayi wa Afzal yake shareta haka? A iya saninta de bata mai komai ba meyasa yake shareta haka toh? Safiyya ta kira ta tayata suka juye abincin suka sa a fridge sannan ta bi Afzal ta koma d'akin inda ta tarar da shi yana tu6e kaya da alama wanka zeyi. "Habib Albi wanka zakayi?" Ta tambayesa inda ya gyad'a mata kai zalla.
"Muyi tare?"
"Bacci nakeji Amal ki bari ko gobe" har cikin ranta taji zafin yadda yayi rejecting nata, ta rasa mey tayi yake yi mata haka amma tabbas tasan da akwai abu a k'asa amma bazata masa magana nan take ba zata yi masa uzuri halan wani abun ne yake damunsa. Haka tana ganinsa ya wuce bayin ya watsa ruwan ya fito ya sanya boxers nasa, bata ce da shi komai ba ta mik'e ta shiga itama fitowan da zatayi ta gansa da coke da cookies yana ci so ashe yana jin yunwa amma yayi mata k'arya wai baya ji don kar ya ci girkin ta. Mey tayi masa yanzu da baze ci girkinta ba? Hmm duk yadda ranta ya 6aci da kuma yadda taso tambayan sa dalilin da yasa yakeyi mata haka kwana biyu ta danne zuciyarta ta fasa. Wani shara-sharan rigan baccinta ta sanya tana ta zirga-zirga a d'akin duk don ta karkatar mai da hankali amma ko d'aga ido ya kalleta beyi ba bale yasan tana yi. Yana gama cinye cookies nasa yayi disposing goran da ledan ya haye gado ya kwanta had'e da juya mata baya. Addu'o'in baccinta ta tofe sannan ta samesa akan gadon ta gangaro da pillonta kusa da nasa inda yayi shiru kaman be jita ba.
"Habib Albi?" Ta kirasa shiru yayi kaman baya jinta. "Habib Albi I miss you" ta sanar da shi. "Please turn around" ta buk'acesa amma ko ya motsa bale tasan yanayi. A rayuwa baya son munafikin mutum mey yayi zafi da zata na kiran Nazeefah tana yi mata gulman abubuwan da yakeyi mata se yazo nan kuma ta tsaya tana maraice fuska tana acting kaman wata salihar k'warai.
Amal ta kasa bacci ranan se tunanin dalilin da zaisa Afzal yana shareta haka ta kwana tana yi, be ta6a dawowa be nemeta ba se wannan karan gashi ko da ta gwada nemansan ma yak'i ya kulata kuma sarai tasan ba bacci yakeyi ba lokacin.
Washegari ko da ta gaishesa sama-sama ya amsa, yana shiga bayi don yin wanka ta wuce kitchen ta shiga had'a masa breakfast sede da ya fito ko kallon kulolin nata beyi ba bale yayi tunanin ci. Yana cikin had'a black tea se gata ta fito don serving nasa.
"Karki damu bazan ci ba."
"Bazaka ci ba kuma Habib Albi?"
"Eh" ya jaddada mata.
"Toh mey kakeso in girka maka?"
"Karki damu ina Safiyya? Safiyya!" Ya k'wala mata kira nan da nan ta fito daga d'akinta ta gaishesa sannan Amal.
"Zo ki soya mun k'wai biyu kiyi sauri I'm already late" Sandarewa Amal tayi wajen ko k'ala ta kasa cewa yayinda zuciyanta yakeyi mata k'ona sosai wato ya gwammace Safiyya ta soya masa k'wai da yaci girkinta? Hmm. Haka ba yadda iya ta koma d'aki ji take kaman tayi kuka.
Gashi tun da ya fita office ranan be dawo gida ba har wajajen tara na dare. Ba irin kiran duniyan da Amal batayi masa ba amma yana ganin calls d'in yak'i d'agawa a rayuwa baya son munafikin mutum taya zata na d'iban duk abinda sukayi tana kai wa Nazeefah kuma ya tabbata ba k'arya Nazeefah takeyi ba idan ba a bakinta ba a ina Nazeefah zata na jin dukkan abubuwan da suke faruwa idan yaje mata kwana? Ace wai har kayan abincin da ya siya ya kaiwa su Papi seda ta kira Nazeefah ta fad'a mata, dan kawai yana kyautata mata da iyayenta shikenan seta shiga neman 6ata tsakaninsa da uwar gidansa tana sanya sa looking maras adalci a fili, yanzu mey ze faru idan Nazeefah taje ta fad'awa iyayenta har magana ya kai kunnen Abba? Sam be santa da wannan munafikin hali ba kode k'awaye ne suke zigata? Toh ta cigaba shi de baze yi mata magana ba.
Amal na zaune a parlour tana jiran dawowan Afzal se taji k'aran gate. Agogo ta duba taga ana neman goma ko meya rik'esa se war haka yake zuwa gida? Yet she's still grateful Allah ya dawo mata da shi gida lafiya. Da hanzari ta mik'e Afzal na bud'e k'ofar ta ruga taje tayi hugging nasa.
"Habib Albi where've you been? I've been trying your number but you weren't picking up wallahi hankalina ya matuk'ar tashi." Cike da tak'ura ya janyeta daga jikinsa "Meeting muka yi se yanzu muka tashi ni kuma ban sake duba waya na ba" yayi mata k'arya bayan gidansu Sultan yaje ya yini throughout.
"Bakada lafiya ne?" Ta tambaya tana shafa fuskansa.
"I'm just stressed out lemmi take a shower" yayi maganan yana sauk'e hannunta daga fuskansa.
"Kawo jakan naka in rik'e maka."
"Bari karki damu" nan ya wuce ta ya k'arasa d'akin ji tayi tamkar tayi kuka bata ma iya ta bisa d'akin ba a parlourn ta cigaba da zama yayinda tunani ya mamaye mata k'wak'walwa ji take kaman tayi kuka ta rasa mey tayi masa yake bata wannan attitude. Se chan ta iya ta mik'e ta bisa d'akin. A kwance ta tarar da shi yana jin motsinta ya 6oye wayansa da yake ta faman chatting da Nazeefah k'ark'ashin pillow yana pretending kaman yana bacci. "Habib Albi?" Ta kirasa shiru yayi yak'i amsawa a hankali yakejin takunta har lokacin da ta k'ariso kan gadon ta zaune gefensa.
"Habib Albi bazaka ci abinci ba?" Nan ma shiru yayi mata sarai kuma tasan ba bacci yake ba. Hijabinta ta cire ta kwanta a d'an space dake gabansa had'e da kwantar da kanta a k'irjinsa tana mey zagaye hannunta kan cikinsa sannan ta ja musu bargo ta rufesu. "Goodnight Habib Albi I love you" ta furta a hankali bacci me wuya ya d'auketa chan tukuna shima Afzal baccin ya d'aukesa.
Kasancewar tana da morning lectures washegari se suka gama shiri kusan a tare, dukda cewan se shareta Afzal yake. Yau kwata-kwata ma k'in karyawa yayi wai ze fita da azumi. Gano itama school zata se yayi mata k'arya wai bazeyi ya kaita ba yana da meeting driver ya kaita kawai. Kud'in makarantar ta ya ajye mata ya fice ko kiss daya saba yi mata beyi ba yau haka ma jiya. Na matuk'a hankalin Amal ya tashi ta rasa mey tayi Afzal yake yi mata haka, Maamah ce ta karanci yanayinta a makaranta ta tambayeta ko lafiya.
"Babu" ta amsa.
"Taya zakice babu Amal? Tun d'azu fa na lura banda tunani ba a inda kike tayi mey ne?"
"Maamah it's Yaya."
"What about him."
"Wallahi ni kaina ban sani ba, na rasa gane meke damunsa kusan sati kenan yau idan yazo baya sakewa dani seda yata d'aura mun fuska ko girki na baya son chi d'an tsaraban daya saba siyo mun idan ze dawo gida ma ya daina I don't know why."
"Subhanallahi Ya Afzal d'in?"
"Wallahi aka ce mun Yaya zemin haka wataran bazan yarda ba kinga tun da ya fita office jiya be dawo ba se kusan goman dare nasan sarai ba wani meeting da sukayi k'arya yake mun gashi ba kiran duniyan da ban masa ba haka yata ignoring calls d'ina maganan da nake miki haka yanzu ko nema na bayayi."
"Ikon Allah this's serious toh ke mey kikayi masa? Am very sure Ya Afzal baze fara shareki haka kawai ba dole da akwai sila."
"Wallahi ban yi masa komai ba Maamah I can't take this anymore bana jin dad'in yadda Yaya yake fushi da ni haka wallahi ko karatu na kasa yi jiya gashi muna da test gobe I can't stop thinking about him, I miss him so much bazan iya rayuwa ba shi ba" ta k'are maganan idanunta na cikowa da hawaye.
"Ke kuwa kar kiyi kuka mana" Maamah tayi maganan tana kwantar da ita a jikinta "Yi hak'uri don't cry komi mey wuce wa ne."
"Har zuwa yaushe toh Maamah?"
"Kiga toh kiyi confronting nasa mana ki tambayesa mey kikayi yake shareki haka talk to him Amal silence is never a solution."
"Maamah bana son hakan ya 6ata masa rai."
"Toh haka zaku cigaba da zama ne? Har zuwa yaushe? Kiyi masa magana dole da akwai abu a k'asa tunda shi yak'i yayi confronting naki ai ke se kiyi hala wani laifin kikayi masa baki sani ba."
"Bazan iya ba mey zan fara ce masa? Bana son yaga kaman rashin kunya nake shirin yi masa I respect him alot."
"Ai ba rashin kunya aka ce kiyi masa ba Amal cike da kissa zaki tambayesa idan laifi kikayi masa ya yafe miki da haka har ze sanar dake abinda kikayi masa seku daidaita tsakaninku."
"Okay I'll try."
"Yauwa yanzu tashi muje muyi karatu nasan idan kika je gida ba iyawa zakiyi ba in shaa Allah everything will be fine."
RANA D'AYA!
#RD
Love... King Miemiebee👄✨
[13/08, 09:38] +234 907 483 8352: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
August, 2018
beeenovels.blogspot.com
_Written by Miemiebee👄_
*PAGE 3⃣3⃣*
Se yamma Amal ta dawo gida bayan sun k'are karatu da Maamah. Driver na sauk'eta ta zarce d'akinsu inda ta tarar da Afzal yana shirin komawa gun Nazeefah ko sannu da zuwa beyi mata ba hasali yi ma yayi tamkar be ganta ba. Itace tayi gyaran murya ta gaishesa tukun ya amsa sama-sama.
"Zan koma gida gun Nazeefah ga kud'inki ajiye a gaban mirror" ya sanar da ita.
"Habib Albi tun yanzu zaka tafi?" Ta tambayesa tana mey duban agogo dududu 5:17 ne amma yake zancen nan bayan se pass 6 yake tafiya kullum.
"Eh wani abu ne?"
"Habib Albi ko ka mance da alk'awarin da kayi mun?"
"Na mey fa?"
"Kace kafin ka tafi zamuyi wanka tare I miss bathing with you Habib Albi, I really do" tayi admitting abun tausayi. Kau da kansa yayi gudun kar tausayinta ya kama sa.
"Nata jiranki baki dawo ba Amal ni kuma sauri nake maybe next time."
"Abinci fa kaci? Nasa Safiyya ta maka microwaving sauce d'in ta dafa maka white rice tayi?"
"A k'oshe nake karki damu na wuce."
"Yaya" ta kira sunansa da sauri lokacinda ya shiga takawa chak ya tsaya had'e da kewayowa.
"Wani abu ne?" So take tayi masa magana kaman yadda Maamah tace da ita amma inaa bata jin zata iya, mugun nauyinsa takeji bata son a sanadin hakan yaga kaman rashin kunya take son yi masa don haka kawai tayi shiru. "Sauri nake" ya sanar da ita.
"Ermm nace Allah dawo da kai lafiya ka gaishe da Nazeefah idan ka isa."
"Kaman dagaske" ya furta chan ciki-ciki.
"Na'am?" Ta tambaya kasancewar bata jisa da kyau ba.
"Nace naji" da haka ya fice Allah kare Safiyya dake sharan parlour tayi mishi sannan ya k'arisa.
Safiyya na ganin fitansa tayi hanzari ta kammala sharan nata da wuri ta wuce d'akinta inda tasa key ta danna wa Nazeefah kira bayan sun gaisa take ce mata, "Aunty bazaki amince da abinda nake shirin fad'a miki ba."
"Mene meya faru?"
"Hmm yanzun Uncle ya bar gida toh kafin ya fito ina cikin share corridon d'akinsu naji su suna magana da Aunty."
"Wai mey suke cewa?"
"Nide ban gane kan zancen nasu ba amma naji tana ce masa wai yayi mata alk'awarin zasuyi wanka tare se gashi kafin ta dawo daga makaranta har yayi wankansa ya gama shiri."
"Wanka tare?!" Nazeefah ta tambaya da d'umbun mamaki "Wanka tare de?" Ta sake nanatawa yayinda ta kasa amincewa da hakan.
"Wallahi Aunty."
"Kaiiii inaaaa! Baki ji su da kyau ba, wannan k'arya ne."
"Wallahi na jisu da kyau Aunty kuma daman tun ba yau ba ina zaton hakan dan akwai ranan da abokin Uncle yazo Uncle Sultan se yace inje inyi ma Uncle magana toh dana k'arisa d'akin nasu sena tarar da k'ofan a bud'e nayita sallama amman shiru chan dana kasa kunne najiyo hayaniyansu acikin bayin."
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un wallahi Amal mak'ira ce, shegiya 'yar asiri toh dan ubanta bazeyi wankan ba kiji mun karuwanci fah! Wato har wanka ma sukeyi tare? Chab!"
"Hmm wallahi ko amma kuma kinsan tun dawowan Uncle wannan karan ko fita sau d'aya basuyi ba? Jiya kanma da tayi masa breakfast k'in ci yayi yace wai nice zan yi masa baya son nata. Bayan nan zama da sukeyi a parlour suyi kallo ma basuyi yanzu gashi banda d'ad'd'aure mata fuska ba abinda yakeyi yau tana da makaranta da safe amma yak'i kaita sa6anin kullum yace se de driver ya kaita shi yana da gun da zasa. Maganan da nake miki yanzu ko tsinke ban ga ya siyo mata ba tun zuwan sannan."
"Ai kibari kad'an ta gani da izinin Allah se Ya Afzal ya tsani taka k'afa acikin gidanta kede kiyi k'ok'ari ki sato min littafin makarantar ta guda d'aya mu samu copy na handwriting nata, zata gani ba har wanka sukeyi ba? Allah kawo shi gida."
"Zanyi k'ok'ari in samo miki bari in gudu ina kan aiki."
"Jeki Safiyya aikin ki na kyau se anjima."
"Toh se anjima" da haka sukayi sallama.
Fresh flowers Afzal ya tsaya ya amsa mata a florist shop sannan ya k'arisa sede har ya shigo parlourn bata mik'e tayi masa sannu da zuwa ba ko sallamansa ma k'in amsawa tayi. Da mamaki kwance a fuskansa ya k'arisa kan kujerar da take zaune ya zauna daga gefe.
"Rabba'atul Bait I'm home" ya sanar da ita.
"Sannu da zuwa" tace da shi zalla ba walwala tattare da ita.
"Rabba'atul Bait what's wrong?" Hannunta ya gwada rik'ewa wanda tayi saurin wabcewa "Sweetheart please talk to me keda nake marmarin in dawo wajenki saboda ki cire min bak'in cikin da 'yar uwarki ta cusa mun kuma kike haka? What have I done this time?"
"Ai mey hali bai ta6a fasawa amma nagode." Cike da rashin fahimta ya tambayeta "Mey kike nufi Rabba'atul Bait please talk to me."
"Ni de wallahi na gaji bazan iya ba da rashin mutuncin nan da tokari tunda baka sona kawai ka sallameni in tafi gida gun Mummy yaso ka cigaba da sha'aninka da amaryarka."
"Wani irin magana kuma kike haka Rabba'atul Bait sanin kanki ne ina sonki kuma bazan iya rayuwa ba ke ba."
"Wallahi baka sona Ya Rouhi" ta fad'a tana cika idonta da hawayen munafirci.
"Please don't cry darling."
"Ka daina kira na darling tunda ba sona har zuciya kake ba, idan da har ka d'auke ni da muhimmanci kaman yadda na d'auke ka da Amal baza tana kirana tana mun gori ba."
"Amal?"
"Eh ita."
"Oh Dear! Mey wancan ta kira kuma ta sake ce miki? Wallahi we're not on good terms with her girkinta haka ban d'ana ba tun zuwa na, mey tace miki?" Ya tambayeta ransa na 6aci.
"Ni baza ka ji komai daga bakina ba har ga Allah bazan so in had'a kanku ba amma de ka cigaba wallahi ranan da komi ya isheni tattara kayakina zanyi in koma gida inyi ma Daddy magana asan ya za'ayi tunda gashi a fili ka nuna baka sona kuma baza ka iya yin adalci a tsakanin mu ba. Ka nunawa Amal ni ba kowa bace banida daraja a idonka idan ba haka ba taya zata na kira na tana gaya mun magana iya son ranta?"
"Nazeefah please calm down ke kanki kinsan I'll never do this to you, I love and respect you alot, dan Allah ki daina magana haka kiyi hak'uri mey yayi zafi da zakice zaki koma gida? Believe me duk abinda Amal ta kira tace miki nayi mata wallahi k'arya take don ko tsinke ban sai na bata ma tun komawa na."
"Ai idan da har ba kayi mata abubuwan dagaske da koda wasa bazata kira tace mun gashi ba nasan ba k'arya take mun ba."
"Ni ke miki miki k'aryan kenan Rabba'atul Bait? Please tell me what is it that Amal told you."
"Ka kirata ka tambayeta da kanka ni bazan had'a kanku ba."
"Ita d'in ba so take ta had'a kanmu ba take kiran ki take miki k'arerayi a waya? Please tell me."
"Dan tamun haka nima senayi mata? Ai ko addini cewa yayi karka sak'a wa mutumin da yayi maka sharri da sharri Allah ma shaida ne ni da zuciya d'aya na d'auki Amal amma ita kam ba haka bane."
"Rabba'atul Bait wallahi ba k'arya nake miki ba I and Amal aren't even speaking to each other ko tamun magana shareta nake saboda na gaji da kalan abubuwan da take yi miki, I'm tired."
"I'm not buying any of your lies again Ya Rouhi zaka ce mun bakuwa magana da Amal bayan d'azun nan na kirata dan mu gaisa take ce min kana jiranta a tub zakuyi wanka tare."
"Amal d'in?"
"K'arya zanyi maka ne?" wayanta ta janyo ta shiga call logs ta nuna mai wayan da sukayi da Amal d'in. Kuma tabbas ta kirata d'azu sun gaisa amma bawai Amal tayi mata magana makamancin haka ba.
"Innalillahi!" Ya furta cike da tashin hankali "Wallahi tallahi k'arya take yi miki Nazeefah-"
"A'a Ya Afzal" tayi saurin katsesa "Karka 6ata lokacinka, ba seka mun bayanin komai ba na riga na fahimceka na sani kafi son Amal akai na dama idan ba ni da shashanci bama taya zan had'a soyayyan da kake mun da wacce kake yima Amal ita da take matar so a gareka bayan ni auran had'i akayi mana? Ni abu d'aya nake buk'ata kawai ka sawwak'e mun in koma gida bazan iya ba da wannan walak'anci da cin fuska" ta k'are tare da rushewa da kuka. Sosai ransa ya mugun 6aci yayinda wutan tsanan Amal ke sake ruruwa a zuciyarsa. Gabad'aya ji yayi ta fita masa a rai, amma ko tana tattare da babban asara.
"Rabba'atul Bait" ya kira sunanta cike da tausayi yana mey k'ok'arin rungumarta sede tayi saurin janye jikinta yayinda ta cigaba da kuka.
"Nazeefah dan Allah kiyi hak'uri kibar kukan haka I'm dearly sorry."
"Ka rik'e hak'urinka Ya Afzal ba laifinka bane don zuciyarka ta fi kwanciya da Amal akai na, ni kawai ka sawwak'e mun zey fiye mun kwanciyan hankali idan ina gida gun iyayena."
"Please don't talk like this wallahi k'arya Amal take yi miki you have to believe me" a hankali ya janyota jikinsa yana hugging nata "Idan kika tafi wa ze zame Rabba'atul Bait d'ina? Please stop crying I love you and you know it isn't that all that matters Sweetheart? By Allah duk abinda Amal ta ce miki nayi mata k'arya ne ki yarda da ni" be d'agota ba seda tabar kukan munafircin nata. Hak'uri yayi ta bata ranan throughout chan dare da yazo yin wanka yace suyi tare Nazeefah tana so tana kaiwa kasuwa wai ita baza tayi ba. Lalashinta yata yi har seda ta amince suka shiga bayin wasa suka yita yi sannan sukayi wanka a k'arshe ya sanyata sukayi alwalan bacci kaman yadda Amal ke tunasar masa kullum. Da kansa ya sanya mata kayan baccinta sannan suka kwanta inda yata tattalinta yana mata wasu irin abubuwan da tuni yasa ta fita daga hayyacinta. Wani irin so na musamman Afzal ya shiga nunawa Nazeefah na d'an kwana biyun da sukayi, ji yayi kaman kada ya tafi da kwanansa ya k'are sam baya sha'awan komawa gun Amal gabad'aya ta fita akansa da abubuwan da takeyi.
"Ya Rouhi har six baka fara shirin tafiya ba ka manta yau kwanan ka ya k'are anan?"
"Ba se gobe ba?"
"Gobe kuma? Da Allah ka tashi ka shirya kar mu shiga hak'k'in Amal."
"She can wait se bayan Maghrib zan tafi."
"Ni baza ayi rashin adalcin nan da ni ba gaskiya."
"Tashi ka shirya Ya Rouhi."
"Zo ki d'agani toh."
"Ni da kai wa ze d'aga wani?"
"We wouldn't know until you give it a try so zo ki d'agani" bata sake musu ba ta k'arisa kan gadon. Hannun sa ta kama ta shiga ja sede ko motsawa baiyi a lokaci d'aya ya jata bata sauk'a ako ina ba se akan jikinsa inda sukayi gware.
"Awch!" Ta furta tana murza goshin nata "Ya Rouhi!" Tayi exclaiming.
"Toh ai na fiki jin zafi."
"Tayaya?"
"Ba goshinki yafi nawa tudu ba."
"Wallahi k'arya ne banida goshi" ta fad'a had'e da kai masa bugin wasa a k'irji.
"Mu gwada ne?" Yace yana mata dariya.
"Ban sanin ba ni ka sakeni" ta fad'a tana k'ok'arin mik'ewa, kankameta ya sakeyi a jikinsa tare da placing mata kiss a gefen baki hannu tasa ta dirje ita a dole tayi zuciya yace mata mey goshi at once yayi flipping position nasu ya zammana shi a sama ita a k'asa.
"Babe you're the most beautiful girl I've ever seen."
"Ba wanin nan nice mey goshi ba? Tashi ka barmun gida jeka samu amaryarka."
"Haba Rabba'atul Bait idan kika koreni gun wa zanje?"
"Amal mana of course."
"Nifa nace ki daina kawo mun magananta."
"Nide d'agani."
"Haba my beautiful Rabba'atul Bait" yayi maganan had'e da matso da fuskansa gab da nata yayinda ta zagaye hannayenta a wuyansa "I love you Babe" ya sanar da ita.
"I love you too Darling" a hankali ya sauk'e lips nasa akan nata ya shiga kissing nata yayinda take miyar masa da martani kaman wasa suka fara wuce gona da iri kafin su hankara har sun wula wani duniyan daban. Bayan sun gamsar da juna suka yi wanka tare Nazeefah na mik'e akan gado tana kallon Afzal cike da adoration da soyayya yayinda yake faman neman kayan da ze sa a wardrobe. Wayansa dake kan gado ne ya shiga ruri ko motsawa Nazeefah dake kan gadon batayi ba ina irin ita ba ruwanta da yi mai shisshigi d'innan shi da kansa yace "Who's calling?"
"I don't know" ta mayar masa tana gyara d'aurin towel nata.
"Duba" ya umarceta. Lek'awa tayi taga Kitten❤💍🔐 na flashing akai ga picture'nsu da yayi saving contact natan dashi wani selfie'nsu ba hassada sunyi kyau.
"Amal ce" ta amsa tana k'ok'arin 6oye kishin daya rufeta lokaci guda "Ayya taji shiru."
"D'aga kice mata idan nayi sallah zan shigo."
"Ya Rouhi kana ganin yin hakan ya dace?"
"Toh ki bari seta ga shigowa na kawai" ya amsa tare da juyawa yana mey cigaba da neman abinda ze sa. Bada dad'ewa ba sega Amal na sake kira wayan ta d'aga tayi answering had'e da yin shiru.
"Halo Habib Albi?"
'"Yar uwa Nazeefah ce" ta sanar da ita.
"Oh Nazeefah, ina yini?"
"Lafiya k'alau, kinji Ya Afzal shiru ko? Yana hanya abu ne ya rik'esa."
"Ayya ba komai seya shigo toh."
"Aha seda safe" da haka sukayi sallama sauk'e wayan tayi tana ma Afzal murmushi yayinda shima ya miyar mata yana mey mamakin hali irin na Amal ace duk yadda Nazeefah ke sonta har take kirarta da 'yar uwa amma se tana kiranta tana irga mata ababen da tasan zasu 6ata mata rai. Seda sukayi sallan Maghrib sannan Afzal ya tafi yau har doubling kud'in daya saba ajiye musu yayi wa Nazeefah ita kam dad'i kasheta she can't wait ta gama aikin ta akan Amal ta fiddata daga gidan finally.
Yana isa gida Amal ta bud'e k'ofa tayi masa sannu da zuwa tana cewa bari tayi hugging nasa yaja da baya. Dama a cike take dam tunda ta kirasa taji Nazeefah ta d'aga wayansa gashi yau se bayan maghrib ya shigo abinda be ta6a yi ba. Kuka kawai ta rushe da sede da mamaki taga ko d'aga kai Afzal beyi ba bale yasan tanayi. "Excuse me" yace da ita yana neman wuceta hannu tasa ta dakatar da shi.
"Yaya mey nayi maka haka ka za6i kana shareni kana wulak'anta ni a gidan nan? Idan wani laifin nayi maka dan Allah ka fad'a mun a shirye nake da in baka hak'uri" ta sanar da shi cikin tsan-tsan kuka. Shi dariya ma ta basa bayan duk rashin hankalin da take tafkawa still tana da bakin da zata tambayesa mey tayi? Lallai she thinks she's smart. Kallonta kawai ya tsaya yi ko uffan bece mata ba.
"Yaya please talk to me I can't do this anymore yau kwana nawa idan ka shigo mun sede kayita d'aura mun fuska, ka daina cin girki na, d'an gifts da ka saba siyo mun ka daina, ka daina kwanciya da ni yanzu ko jikinka kana neman hanani ta6awa baka tunanin hukuncin nan da ka yanka yayi tsauri dayawa?"
"Yayi tsauri fa kikace Amal? I'm truly disgusted at you I never expected this from you how could you stoop this low? Tell me mey kikayi benefiting da wannan abun kunyan da kikayi mun kika kuma yi wa kanki?" Ya tambayeta cike da tsiwa. Hawaye take sosai yayinda kanta ya d'aure shin mey yake fad'i? Wani abun kunyan tayi masa?
"Yaya wani irin magana kakeyi? Wani abun kunya nayi maka please talk to me ban fahimce ka ba."
"Ai dama baza ki ta6a fahimta ta ba Amal you know what? I don't have time for this idan kinsan k'arya zaki tsaya kina mun just forget it."
"Yaya dan Allah kar kayi mun haka I beg of you wallahi ba k'arya nake maka ba" ta rok'esa cikin tsananin kuka.
"Ohhh itace take k'arya kenan?"
"Ita wa?"
"Seriously Amal? Har tambayana kike ita wa? Kin d'au magana baze zagayo kunne na bane? Kede ki cigaba."
"Wallahi ban fahimceka ba Yaya bansan akan mey kake magana ba kuma a iya sani na ban yi maka wani abun ba sede ban sani ba ko a bisa rashin sani yet still zan baka hak'uri dan Allah kayi hak'uri ka rage wannan hukunci wallahi yayi mun tsauri dayawa Yaya can't you see? I'm slowly losing my mind and going crazy fushinka a gareni ba k'aramin tashin hankali bane please kayi hak'uri ka gafirceni I'm dearly sorry."
"Idan ba kiya son ina fushi dake se ki iya bakinki ki koyi rik'e sirrin gidanki ki dena buga waya tako ina kina irga wa mutane abinda mijinki yake miki, how could you Amal? I thought kina da hankali kuma kinsan abinda ya kamata ashe ba haka bane, wallahi ba halin ki bane ban san ki da halin nan ba."
"Ni Yaya? Wa na kira na sanar dashi sirrin gidan nan? Wallahi ban buga wa kowa waya ba ko Mami."
"Kiji I don't have time to listen to your lies because a sane nake da komai don haka ba abinda zakice da zaisa in amince dake I've heard enough and I'm very disappointed with you ban ta6a sanin kina da wannan mumunan hali ba amma ki cigaba ni bazan miki baki ba sede inyi miki fatan shiryuwa idan ma k'awaye kike bi suke rud'anki suke d'aura ki akan gur6arcacciyar hanyan nan gara tun wuri kin rabu da su ina Safiyya!" Nan Safiyya dake lek'ansu ta koma cikin d'akinta a 360 seda ya sake kiranta a karo na biyu sannan ta fito tana wani hamma irin bacci takeyi ya kirata d'innan.
"Ina yini Uncle?" ta gaishesa.
"Lafiya ki dafa mun indomie biyu da k'wai biyu kiyi sauri I'm hungry."
"Akwai abinci fah Rice and Stew Aunty ta girka."
"Ina sane ai nace ki dafa mun indomin."
"Toh" da haka ta wuce kitchen d'in wani pathetic look ya bawa Amal ya wuceta ya shige d'akinsu. Har k'asa ta sauk'a tana kuka wajen gabad'aya ta rasa mey ke mata dad'i sam bata da masaniya ga abinda Afzal yake cewa mey yake nufi da ta daina kiran mutane tana yad'a musu sirrin aurenta a ina tayi hakan? Ita da ko da iskokai suka shafeta ma bata kira Mami ta sanar da ita ba wani sirri yake nufin tana yad'awa idan akwai mutumi d'ayan da ta mar maganan aurenta itace Maamah kuma ta yarda da Maamah tasan Maamah baza ta ta6a ci mata amana ba. Kuka tayita sha wajen har zuwa lokacinda Safiyya ta gama abincin Afzal ta ajiye masa kan dining gun Amal ta k'arisa ta durk'usa.
"Aunty kiyi hak'uri dan Allah ga abincin Uncle yayi."
"Kije kice mishi ya fito."
"Da kaina?" Kai zalla ta gyad'a mata nan ta wuce bayan tayi mar sallama ta sanar dashi ta gama godiya yayi mata sannan ta dawo kan Amal tana cigaba da bata hak'uri kaman dagaske.
"Kije d'akinki Safiyya ba komai" haka Afzal yazo ya tarar da ita zaune a wajen, ko kallonta beyi ba ya k'arisa dining. Da k'yar ta tattara kanta ta koma d'aki Qur'ani kawai ta d'auka ta shiga karancewa shi kad'ai take jin ze iya rage mata wannan k'unci da bak'in cikin da takeji. Bayan Afzal ya gama cin abinci yazo shiga d'akin yaji sautin karatunta na tashi, na d'an lokaci ya tsaya ya saurareta sannan ya koma parlourn ya cigaba da zama be sake kewayowa d'akin ba se da ya tabbata tayi bacci wajajen sha d'aya kenan. Tsince akan gado tana bacci ya tarar da ita da alama karatu take bacci ne ya d'auketa don ga handouts nata baje a gabanta, Jallabiyan jikinsa ya tu6e sannan ya tattare handouts d'in ya ajiye a gefe ya gyara mata kwanciyan nata ya haura ya kwanta daga chan gefe shima had'e da kashe musu wuta.
Haka ya cigaba da d'aga mata kai yana shareta, washegari Amal tayi kuka har ta godewa Allah test da ta rubutan ma dukda cewan tayi karatu batazo ta gane mey ta rubuta ba saboda gabad'aya ba hankalinta a jikinta.
"Amal kiyi hak'uri haka kukan nan ba shida amfani" fuskanta daya kumbura tim ta d'ago daga kan benchi tana share hawayenta "Maamah a rayuwa ba abinda na tsana kuma yafi k'ona mun rai kaman banyi abu ba ace nayi fisabilillahi ko ke na ta6a sanar dake sirrin gida na ne in ba wannan karan da matsaloli suka yi mun yawa ba?" Kai Maamah ta kad'a mata a hankali cike da tausayi "Amma cemin yayi wai ba aiki na se buga waya wa mutane ina sanar dasu sirrin gida na harda wai ya d'au ina da hankali ashe babu duk na munafirci ne Yaya fa Maamah, Yaya yake kwatantani da wannan munanan kalamu" ta sake rushewa da wani kukan.
"Amal ki kira Mami ki sanar da ita kawai taya Ya Afzal ze miki haka ina laifin ma ya sanar dake laifin da kika yin amma haka kawai ya barki acikin duhu ai ba yi bane hakan."
"So kike ya gama tsanata idan na sanar da su Mami? Ban kira kowa bana yace ina kiran waya ina yad'a sirrin gida na bale har in kira Mami? Hmm ashe ina tona kabari na da kaina kenan."
"Toh ya zakiyi Amal? Ni anya kuwa ba kishiyarki bace take neman had'a kanki da Ya Afzal?"
"Nazeefah wai?"
"Sosai ma kiyi tunani mana mey yake nufi da yace miki ita take k'aryar? Nazeefah yake nufi."
"Da wuya idan itace I trust Nazeefah bata da wani mugun hali kuma kinga ita bama zuwa gida na take ba bale ace taga wani abun taje tayi mai gulma."
"Don't get too confident trusting her Amal wallahi halin mutum se Allah idan ba haka ba waze shiga tsakaninki da Ya Afzal haka?"
"Maamah ban sani ba amma zan cigaba da addu'a har se idan Allah ya amsa kuka na."
"Toh Allah taimakeki ya shige miki gaba Amal shi kuma Ya Afzal Allah sa ya gano gaskiya ya sani cewa idan mutum yayi laifi confronting nasa ake bawai a rik'e shi a zuci ana k'untata mai ba."
**
Washegari kasancewar Amal tana iya kai har yanma a school ta yi girkin rananta tun da safe kafin ta fita. Abinda Safiyya zatayi kawai tayi wa Afzal microwaving ne idan ya dawo daga office that is idan ze ci ma kenan tunda yanzu ya k'aura daga cin girkinta. Tun k'arfe sha biyu ya dawo gida yana shiga ciki yaga cup da snacks haka akan table sekace anyi bak'o sallama yayi Safiyya ta fito tayi mai sannu da zuwa.
"Auntinki na gida ne?"
"A'a ta fita school."
"Wannan fah?" Ya nuna cup d'in "Kinyi bak'uwa ne?"
"A'a Aunty ne ta shigo bada dad'ewa ba ita da wani."
"Excuse me?!" Yayi exclaiming had'e da zaro idanunsa waje.
"Yanzu suka bar nan."
"Ita da wa?"
"Ita da wani na miji suka shigo ta d'au wasu takardu suka d'an zauna se suka sake fita tace tayi mantuwa ne."
"Amal ta kawo na miji gidan nan?" Sam ya kasa amincewa da hakan.
"Ni na d'au ma ko d'an uwanta ne yadda suka zauna a kujera d'aya."
"A kujera d'aya!?" Ya sake tambaya idanun nan kaman zasu fad'o a k'asa dan mamaki. Dan yadda zuciyarsa ta shiga k'ona ko k'ala be sake cewa da Safiyyan ba take idanunsa suka kad'a sukayi ja. Cikin wani irin taku ya k'arisa d'akin nasu kawai ji Safiyya tayi ya buga k'ofan wane yana neman 6allesa, d'aki ta koma jiki na rawa ta kira Nazeefah.
"Aunty na aikata, kuma wallahi ya amince."
"Kai haba!"
"Bakiga yadda yake ta nishi ba kaman zaki."
"Kinyi dai-dai ai in shaa Allahu kwanan Amal a gidan nan ya kusa k'arewa aikinki na kyau."
Amal baiwar Allah da tun fitanta k'arfe sha d'aya se biyar ta dawo bata san meyake jirarta ba a gida. A galabaice driver ya dawo da ita tana shiga parlour ta tarar da Afzal zaune kan kujera ko d'aga ido beyi ba bale yasan mutum ya shigo gidan se harkan gabansa kawai yake itama bata yi mai magana ba sanin ko tayi ba amsata zeyi ba. Da mamaki ya bita da kallo wato ma ko magana baza tayi masa ba lallai rainin har ya kai haka? Bayan ta kawo masa k'ato gida ta dawo kuma bazata iya ce mai sannu ba, wuyanta ya kai yanka. Da abinda zata sak'a masa kenan duk kalan halaccin da yayi mata a rayuwa? Wajajen goma ya koma d'akin kwance akan gado ya tarar da ita a galabaice.
"Kibar min d'akin nan kije ki kwana wani wajen" yace da ita zallah.
Da mamaki ta tsaya kallonsa ashe Allah ze kawo ranan da zeyi mata gori akan abubuwan da yayi mata a rayuwa? Ko k'ala bata ce da shi ba ta d'au pillonta da waya ta bar masa d'akin bayanta yabi yayi locking k'ofar sannan ya dawo ya kwanta yana mamakin wannan sabon d'abi'artan wato ma tsabagen tasan halinta ta kuma san mey takeyi shiyasa ko a bakin zaninta bale ta tambayesa dalilin da ze hanata kwana masa a d'aki ba. Toh ta cigaba.
Ta d'ayan fannin kuka Amal ta kwana tana yi bata jin zata iya da wannan walak'anci mey yayi zafi da ze koreta daga d'aki? Saboda bata kawo ko tsinke gidan ba? Da k'yar bacci yazo ya d'auketa. Kasancewar tana da morning lectures washegari bayan Asuba tayi wanka sannan ta wuce d'akin nasu dan d'auko kayan da zata sa sallama tayi jin shiru seta bud'e k'ofan amma bata gansa a ciki ba don haka kawai ta yanke hukuncin yana bayi ne. Wajen wardrobe ta nufa ta shiga fiddo da kayan da zata sa tana cikin hakan Afzal ya fito daga bayi ko juyawa ta kallesa batayi ba harkan gabanta ta cigaba da yi daga wajen wardrobe ta k'arisa gun mirror ta tattara man shafawanta da turare da sauran abubuwan da zata buk'ata ta fice. Binta da kallo yayi shima bece da ita ko k'ala ba. Tana gama shirinta tayi ma driver magana ko tambayan Afzal kud'in makaranta batayi ba sallama kawai tayiwa Safiyya ta fice. Yau ma kaman jiya Afzal ya riga Amal dawowa and thesame thing cup ya tarar a kan centre table da plate na abinci daya tambayi Safiyya still ta basa amsa irin na jiya akan Amal ce ta shigo da wani basu jima da tafiya ba. Na matuk'a ransa ya 6aci yau kam baya jin ze iya d'aukan rashin hankalin nata abun ya ishesa zama yayi a parlourn yana jiran dawowanta chan bada dad'ewa ba ta iso yau ma a galabaice. Kanta ta sunkuyar lokacinda ta shiga parlourn har ta kai ga wucesa ya kira sunanta chak ta tsaya had'e da kewayowa.
"Wa kika kawo mun gidan d'azu?"
"Mey kake fad'i Yaya?
"I'm not repeating myself Amal wa kika kawo mun gida d'azu?"
"Wa zan shigo maka dashi gida Yaya? A iya zama na da kai na ta6a shigo maka da na miji gidan nan ne? Why don't you believe me Yaya? Na d'au ko da an fad'a maka hakan bazaka amince ba saboda a tunani na kafi kowa sanin hali na, a tunani na kafi kowa sanin abinda zan iya aikatawa da abinda bazan iya ba I'm so disappointed with you Yaya" ta tsaya ta numfasa yayinda hawaye yake ciko mata a ido "Ina soyayyar da kake ikirarin kana mun? Ashe za a iya fad'a maka magana akaina ka hau ka zauna akai ba tare da kayi bincike akai ba?"
"Stop acting like you're the Amal I used to know saboda gabad'aya kin canza, I can't trust you anymore Amal yau komin ya girman laifi yake aka ce mun kin aikata zan amince saboda I've lost my trust in you since the day kika fara d'iban sirrin gidan ki kina yad'a wa jama'a."
"Allah ma shaida ne ban ta6a kwasan abinda kake mun a gidan nan na fad'awa kowa ba not even Mami" ta amsa tana share hawayenta.
"Ki bud'e kunnenki ki saurareni da kyau ban yafe ba idan kika sake kawo mun wani k'ato cikin gidan nan."
"Yaya please idan wani abun nayi maka ka fito fili ka fad'a mun amma ka daina cemun nayi abinda ban aikata ba, yaushe na shigo gidan nan tun fita na bale har in shigo da wani?"
"Da ace ban shigo na tarar da ragowan snacks da drink da kikayi serving nasa bane se ki gaya mun maganan banza."
"Drink? Wallahi ni ban kawo wani gidan nan ba ka kira driver ka tambayeshi ko ya dawo dani gida tun fita na da safe in ba yanzu ba."
"You're not as smart as you think you're Amal and ki cigaba."
"See Yaya idan gajiya dani ne kayi kawai ka fad'a mun I'll understand you it's too early for this, taya banyi abu ba ina ji ina gani zaka na mun sharri da fari kace ina kire-kiren waya ina baza sirrin gida na a waje yanzu kuma zargi na ka fara? Har kana tunanin kai na ya waye da zan fara kawo maka maza a gida? Wallahi a da koda wasa aka cemun zaka yi mun abinda kakeyi mun yanzu bazan amince ba amma ka cigaba dama nasani dole wataran zaka goranta mun tun da har ka iya ka koreni daga d'akinka jiya." Bata jira jin mey zece ba ta wuce d'akin data koma a guje. Kuka ta shigayi daga haka har ta fara yin amai, bata tsaya ba seda ta harar da abincin cikinta tas har jiri na neman d'ibanta. Da rarrafe ta k'arisa d'akin ta kwanta ahaka har wahalallen bacci ya d'auketa. Next da ta tashi Safiyya ke ce mata Afzal ya riga ya tafi kai kawai ta gyad'a mata har ta tashi zata tafi seta kira ta.
"Na'am Aunty?"
"Mey kika cewa Ya Afzal jiya da bana gida?"
"Game da mey Aunty?"
"Kinsan mey nake nufi ai."
"Wallahi ban fahimce ki ba dan ni magana ma be had'ani da Uncle ba."
"Waya ce mishi na shigo da na miji gidan nan?"
"Na miji? Wallahi bani bace Aunty dan meyasa zan miki sharri? Wallahi bani bace."
"Shikenan tashi ki tafi." Chan bayan sallan Isha ta fito kitchen dan had'a custards ta sha sanadin wani irin yunwan da ya dameta. Tana tsaye a kitchen tana jiran ruwan ya tafasa Safiyya ta shigo zata dafa indomie.
"Ki d'au k'wai biyu ki soya" tace da ita.
"Toh Aunty nagode" jiki na rawa ta bud'e fride d'in ko ya akayi kawai d'aya ya ku6uce daga hannunta ya fad'i ya fashe.
"Subhanallahi! Ya akayi haka Safiyya?" Amal tayi saurin tambaya tana neman toshe hancinta.
"Aunty dan Allah kiyi hak'uri wallahi ban sa ya akayi ba bari in goge da wuri ina tissue" kafin ace mey k'arnin ya mamaye kitchen d'in gabad'aya gas d'in Amal ta kashe da wuri sannan ta juya sink ta shiga kwararo amai, amai tayita yi wane zata harar da hanjinta yayinda Safiyya ke bata hak'uri. Bakinta ta wanke Safiyya ta taimaka ta jata izuwa d'aki.
"Sannu Aunty kina buk'atan wani abun?" Kakkarwa take sosai ta kad'a mata kai "Ki had'a mun black tea kawai."
"Toh ina zuwa" nan da nan ta had'o ta kawo mata.
"Shikenan kina iya tafiya."
"Ba wani abinda kike buk'ata?"
"Babu kar ki damu."
"Allah sawwak'e."
Da k'yar Amal ta samu ta sha rabin tea d'in taji ta k'oshi zazza6i ne ya rufeta a lokaci guda ko makaranta ta kasa fita washegari ga shi jikin nata ya d'au zafi. Maamah ce da ta jita shiru ta kira dan tambayan ko lafiya.
"Wallahi zazza6i Maamah kaman zan mutu."
"Allah sarki shafakillahu habibty Allah baki lafiya."
"Ameen nagode."
"Na yi miki assignment d'in na mana submitting."
"Allah sarki Maamah kaman kinsan ina ta bi a raina wallahi nagode sosai Allah ya bar zumunci."
"Ameen munyi waya da Ya Abdul ma yace in gaisheki."
"Allah sarki ina amsawa."
"Ya Afzal fah? Be kaiki asibiti bane?"
"Ya koma gun Nazeefah tun jiya ai."
"Baki kira kin sanar da shi bakida lafiya bane?"
"Ko nayi mey zai mun? Kin manta ba wanda ya tsana kaman ni ne a duniyan nan yanzu?"
"Allah sarki Amal do you need anything? Wallahi Ya Afzal bai kyautawa."
"Ba komai Nazeefah wataran se labari nagode" ta amsa hawaye na tsiyaya mata daga ido.
"Gobe zan shigo in duba ki in shaa Allah ki huta kinji? I love you."
"I love you too sekinzo."
****
Se wajajen sha biyu Amal ta samu k'arfin jiki a gida ta yini ranan ba inda taje, chan Maghrib nayi kuma zazza6in ya sake tashi ga amai idan ta fara kaman zata harar da kayan cikinta sosai Safiyya ta tausaya mata take kuma k'ok'arin kula da ita. Har anan Afzal be san mey ake ciki ba kaman yadda be kira Amal ba haka itama bata kirasa ta sanar da shi batun rashin lafiyarta ba ko Mami bata kira ba.
Bayan Safiyya ta tattare plate d'in ta fita dashi Amal ta janyo wayanta ta shiga calender tana counting yau kwana uku kenan da missing period nata anya kuwa lafiya? Kode? Subhanallahi it can't be possible Allah yasa ba abinda take zargi bane inde haka ne ya zamo dole gobe taje asibiti ta tabbatar da koma mey amma fatanta Allah yasa ba abinda take zargi bane. Se sha d'aya ta fita washegari bayan da zazza6in nata yad'an sauk'a. A wani private clinic Driver ya sauk'eta inda ta k'arasa ta bud'e file tukun ta shiga ganin doctor tayi mata bayanin yadda takeji. Murmushi likitan tayi mata tace "Amma Amarya ce ke ko?" Kai Amal ta gyad'a mata cike da rashin fahimta.
"Shiyasa ai."
"Ban fahimce ki ba Dr Sadiya."
"Congratulations you're pregnant Mrs Abdallah."
"Pregnant?" Amal ta nanata cike da k'in yarda "Taya bakiyi mun gwaji ba bakiyi komi ba kice ina da ciki?" Murmushi ta saki kad'an "ni da aiki na kuma Mrs Abdallah ai ko ban miki gwaji ba idanunki kad'ai ma shaida ce kina d'auke da juna biyu."
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" taji Amal ta furta.
"Lafiya?" Tayi saurin tambaya.
"Dan Allah kiyi mun tests d'in tukuna I can't be pregnant at least not when babu jituwa tsakani na da mijina, I can't be pregnant Dr please do something" ta fad'a cike da tashin hankali.
"Subhanallahi please calm down, taya zaki k'i kyauta daga Allah haka Mrs Abdallah?"
"Ba haka bane Dr matsaloli sunyi mun yawa and cikin nan will only add to it please help me."
"That's where you're wrong wannan ciki sede ya warware miki duk wani matsalan da keda mijinki kuke fuskanta, ki yarda dani mijinki na jin wannan news ze sauk'o daga kowani irin temper yake kai, kede ki godewa Allah kawai" ta sanar da ita ta na wani rubutu jikin wani paper "Ga wannan kije next room zasu yi miki scanning mu gano sati nawa ne duk abinda akwai zasu sanar dake kafin ki fara zuwa pre natals naki, congratulations once more." Jiki na k'yarma Amal ta amshi paper'n "Don't be afraid Mrs Abdallah in shaa Allahu juna biyun nan shi ze zame sanadin shirya tsakaninki da mijinki."
"Toh nagode Dr."
"Sey kuma ga wannan magunan basuda k'arfi in shaa Allah baza suyi komi wa cikin ba, zasu rage yawan jin jiri da kuma yawan yin amai da zazza6in duka, Allah inganta."
"Ameen Dr nagode se anjima." Next room ta shiga inda akayi mata scanning cikin. Kwata-kwata ma cikin sati uku ne sede maimakon Amal tayi murna tun dawowanta gida take aikin kuka gabad'aya ta rasa meke mata dad'i bata ma san wa zata fara kira ta sanar da shi wannan labari ba abu d'aya da ta sani shine Afzal ne mutumi na k'arshe da zata kira ta sanar da shi. Tunda ya fara zarginta yanzu ai da k'yar ma idan ze amince cikinsa ne a jikinta, ya zatayi? Wannan musiba da mey yayi kama??
RANA D'AYA!
#RD
Love... King Miemiebee👄✨
[13/08, 09:39] +234 907 483 8352: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣
💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
August, 2018
beeenovels.blogspot.com
_Written by Miemiebee👄_
*PAGE 3⃣4⃣*
Ko makaranta Amal ta kasa fita washegari saboda yadda jikin nata ya tsananta, gashi de ta fara shan maganin amma ba sauk'i. Kaman yadda Maamah ta d'au alk'awari haka tazo ta duba Amal da soft drinks nata, Safiyya ce ta amsa ta sa a fridge sannan ta kai ta d'aki inda Amal ke kwance akan gado ta duk'unk'une kanta acikin bargo se kakkarawa take. K'arya ne mutum ya ganta be tausaya mata ba.
"Subhanallahi Amal!" Maamah tayi exclaiming cike da tashin hankali. "Amal dan Allah karki mutu" take idanunta suka ciko da hawaye tsan-tsan tausayi.
"Amal mey kike yima kanki haka? Meyasa baki kira Mami ba? Meke damunki dan Allah?"
"Maamah calm down ki kwantar da hankalinki."
"Ya jikin naki? How are you feeling?"
"Da sauk'i zuwa anjima zazza6in ze sauk'a morning fever ne."
"Subhanallahi sannu ai baki fad'a mun zazza6in yayi tsanani haka ba what's wrong?"
"Maamah I'm pregnant" ta sanar da ita.
"You're what?!" Tayi exclaiming had'e da zaro ido waje.
"Maamah ina d'auke da cikin Yaya" ta jaddada mata yayinda ta rushe da kuka. Hugging nata Maamah tayi tana kukan tare da ita sun dad'e a haka sannan ta janye Amal a hankali tana mey share mata hawayenta.
"Amal I'm so happy for you, Allah ya inganta idan lokacin yayi ya raba lafiya."
"Ameen" ta amsa chan ciki-ciki.
"Ya Afzal ya sani?"
"Ke na fara fad'awa ko Mami ban kira na sanar da ita ba."
"Amal why? Ai Ya Afzal ya kamata ya fara sani ke bakisan wannan news shi ze zame sanadin shirya tsakaninku ba?"
"Shirya tsakanin mu?" Ta tambayeta had'e da sakar da murmushin takaici "Maamah things just got worst kin san mey Yaya yamun?" Kai Maamah tayi saurin kad'awa.
"Korana yayi daga d'akinsa shiyasa kika ganni anan bayan nan jiya yake ja mun Allah ya isa idan har na sake shigo masa da na miji gida Maamah zargi na Yaya yake, gani yake kaman duk zaman mu cin amanan sa nake."
"Innalillahi wa inna ilai raji'un the fuck is wrong with Ya Afzal? Ya yake abu kaman wanda baida ilimi? Ai yaci ace yasan abinda zaki iya aikatawa da abinda bazaki iya ba daga gun wani d'an jakar uban yaji wannan batu? Waya gaya mishi kina shigo da maza gidan nan?"
"Wallahi ban sani ba Maamah kinsan zurfin cikin Yaya bayi ta6a fitowa fili ya fad'awa mutum abu."
"Amal dan Allah ki tattara kayakinki kibar mai gidan nan haka wannan walak'anci dame yayi kama? Se kikace mishi mey dayace kibar masa d'akin nasa?"
"Mey kuwa zance masa? Pillow na kawai na ja na fice mey zance masa?"
"Hmm wallahi munafukar mey aikin ki d'innan nake zargi da ganin yadda fuskanta yake bak'i k'irin d'innan haka zuciyarta take in ba haka ba ina Ya Afzal zeji batun nan? Bawai zama yake a gida koda yaushe ba dole gaya mishi akeyi."
"Na gwada mata magana tace ba ita bace banida lafiya ban so jan maganan ba nace kawai shikenan."
"Wallahi itace kinji rantsuwa ba kaffara ina gaya miki Nazeefah ba kishiryar arziki bace wallahi aiki suke tare da 'yar nan dalilin daya sa tun farko ta kawo miki ita kenan. Wallahi aiki suke tare."
"Nazeefah kuma?"
"Don't be fooled by her kind gestures makashinka na nan tare da kai duk inda kake, kiyi tunani ita munafukar Safiyyan ce take kai wa Nazeefah rahoton komi a gidan nan ita kuma mak'irar seta ce ke ce kika kira kika sanar da ita."
"Maamah ni bana son abu da tashin hankali da tada magana idan ma aiki suke tare wataran dubunsu ze cika dukda cewan ban yarda da hakan ba I know Nazeefah baza ta ta6a yimun haka ba."
"Hmm Amal kenan ki bud'e idonki kisani yadda ka d'auki mutum ba haka yake d'aukanka ba ko a jinki kowa ne keda zuciya d'aya kamanki? Wallahi ba haka bane, balle wai har kice kin aminta da kishiyarki? Kishiyan da ba wacce take gaba dashi a fad'in duniya kaman ka? Ki bani izini inyi questioning mey aikin kin nan kawai."
"Maamah please ki barta bana son k'ananun magana" Maamah bata saurareta ba ta mik'e "Maamah dan Allah ki dawo" ficewa tayi ta dawo da Safiyya biye a bayanta "Bani wayanki" ta buk'aceta.
"Waya na kuma?"
"Eh wayanki."
"Lafiya?"
"Wani abun kike 6oyewa ne?"
"Wani irin magana kuma kike Aunty? Mey zan 6oye?"
"Good then pass me your phone" hannu ta mik'a mata tana jiran ta sanya mata shi aciki bayan Saffiya ta d'au lokaci ta sanya wayan cikin hannun Maamah cike da fargaba.
"Amal ya numban Nazeefan yake?"
"Maamah dan Allah ki bata wayanta ni bana son matsala."
"Mstw" wayan Amal taja ta bud'e ta latsa numban Nazeefah had'e da zubawa cikin wayan Safiyya sede da mamaki taga babu numban a wayan Safiyya how can it be possible? Ta tambayi kanta.
"Babu ba?" Amal ta tambayeta kai zalla ta gyad'a "Ai na fad'a miki ba su bane dan Allah ki bata wayarta amshi Safiyya kiyi hak'uri."
Amsa tayi tace "Ba komai Aunty Allah k'ara miki lafiya" da haka ta fice.
"This can't be possible wallahi ina ji a jikina 'yar nan munafuka ce."
"Maamah please enough gashi de kin gani ko lamban Nazeefah bata dashi kuma bataje boko ba bale kice ta haddace lamban ne akanta ranan lamban ta na tambayeta amma bata sani ba, babu yadda za'ayi kuma ace ta haddace na Nazeefah, na gaya miki ba had'in Safiyya da Nazeefah."
"Hmm toh mey gadin kine? Wallahi dole akwai wanda yake fad'awa Ya Afzal abubuwan nan ko kina tsammanin shi yake zama yake shirya zancen?"
"I will not be surprised idan shi yake shirya komi Maamah saboda a fili yake nuna mun na fita a kansa baya sona ban ta6a tsammanin Yaya zemin haka ba watarana wallahi yanzu nake nadaman auransa da nayi nasan ko da wasa Ya Abdul baze ta6a yimun haka ba."
"Kar ki ce haka Amal Ya Afzal mijinki ne har yanzu."
"Maamah I miss Ya Abdul I miss him so much" hugging nata Maamah tayi yayinda ta cigaba da bata hak'uri.
"Amal be kamata mu nad'e hannu mu zubawa koma wa yake miki wannan aika-aika ido ba we have to do something."
"Mey zamuyi toh Maamah? Ba muda hujja bamuda komai."
"Ido ya kamata ki sawa mey aikin kin nan wallahi ina ji ajikina itace munafukar lamarin nan."
"Nace miki ki cire Safiyya daga lamarin nan."
"Hmm toh ke yanzu haka zaki cigaba da zama a gidan nan Ya Afzal na cusa miki bak'in ciki yana miki walak'anci har seya kasheki tukuna? Da wanne zakiji? Da laulayi ko kuwa da masifan miji?"
"Maamah tunda nasan ni banyi masa komai ba ya cigaba da koma mey yakeyi tabbas wataran Allah ze wanke ni kuma shi zeji kunya, zan cigaba da kai kuka na wa Allah ai shi ba azzalimin bawa bane."
"Haka wannan yake amma ki kira Mami ki sanar da ita wannan k'aruwan da kika samu."
"I'll amma ba yanzu ba saboda nasan one way or the other magana ze kai kunnen Yaya idan har na sanar da Mami abinda bana so kuma kenan bana son Yaya yasan ina da ciki."
"Amma ai ya kamata ya riga kowa sani tunda shine mahaifin abinda ke cikin naki, Amal you can't do this on your own."
"Ki yarda dani idan nace miki Yaya yana iya denying baby'n nan yace ba nashi bane tunda har ya iya bud'an baki yace mun ina kawo masa maza gida."
"Wallahi Ya Afzal na tattare da babban asara tunda de kome aka gaya mishi hawa yake ya zauna akai ba tare da yayi bincike ba, sannu kinji?"
****
Yini ranan Maamah tayi mata se wajajen biyar da rabi ta tafi. Seda Safiyya ta tabbata Amal tayi bacci ta dannawa Nazeefah kira lokacinda tasan Afzal bai gida ya fita masallaci.
"Hello Aunty?"
"Ya zaki kirani warhaka idan da Ya Afzal na gida fa?"
"Aunty naga kaman lokacin isha yayi ya fita sallah ne."
"Idan da kuma bai fita ba fah? Ba nace se ya fita office zaki na kirana ba?"
"Aunty kiran gaggawa ne."
"Meya faru?"
"Wallahi Aunty ciki take dashi."
"Ci mey!" Nazeefah tasa wani d'ankaren ihu.
"Wallahi ciki take dashi."
"Innalila..inna..innalila" dan rikicewa tama kasa k'arisa salatin yayinda cikinta ya d'au ruwa. Yau ga ranan da ta jima tana gudu. "Amal nada ciki kikace?"
"Eh Aunty."
"Wayyo na shiga uku na lalace ya kika gane? Kinsan ba a wasa da zancen ciki ko?"
"Wallahi ba wasa ba Aunty, tun rananda Uncle ya tafi ta ke zazza6i da amai d'azu wata k'awarta tazo sena ji suna tattauna wallahi ciki ne da ita."
"Yau na mutu na lalace taya Amal zatayi ciki gabani na? Wallahi baze yuwu ba koda sama da k'asa ne zasu had'u se na san yadda zanyi na zubar da cikin nan wallahi bazata haifesa ba."
"Aunty gashin be isa haka ba? Wallahi Aunty ta fara zargi na kokuma ince k'awarta, k'awarta ta fara zargi na d'azu harda amsan wayana ta zuba lamban ki aciki da ace nayi saving da shikenan sun kama mu."
"Wata mak'irar k'awarce take neman rusa mun plan bayan na kusan cimma burina?"
"Wata wai Maamah."
"Safiyya aikin mu ya koma baya be kamata ace Amal nada ciki ba nashiga uku amma Ya Afzal be sani bako?"
"Gaskiya da wuya kinsan basu magana."
"This's the only opportunity I have ya zama mun dole in zubar da cikin nan kafin su shirya dan muddin suka shirya shikenan nawa ya k'are ya zamuyi? Be kamata mu bari Ya Afzal ya gano Amal na d'auke da cikinsa ba."
"Toh ya zamuyi Aunty ni Wallahi tsoro nakeji kar a kama ni, ko a haka muka bar Aunty ta sha wuya, ya isa haka please."
"Wawiya ki saurareni gobe Afzal ze dawo mata inason ki taho mu had'u dake inda muka saba an gama rubutun zan baki seki je ki sa mun cikin wardrobe nasa ta k'ark'ashin kayakinsa kina jina?"
"Eh Aunty."
"In shaa Allahu daga gobe zaman Amal a gidan ya k'are na tabbata idan Ya Afzal ya karance rubutun nan se ciwon zuciyansa ya kusan tashi daga nan seya buga mata saki ta tattara tabar gidan mu samu mu zubar da cikin kowa ya huta."
***
Ba k'aramin rama Amal tayi ba acikin wannan kwana biyu sosai cikin yake bata wuya d'an kumatun da take da shi ma tuni suka zube ta kuma yi duhu. Yau da yamma ana neman shida Afzal ya dawo gida sannu da zuwa Safiyya tayi masa sannan ya wuce d'aki ya rage kayan jikinsa ya bud'e wardrobe nasa ya sanya wasu files aciki ya sake kullewa sannan ya fito parlour.
"Amal na gida ne?" Ya tambayi Safiyya.
"Eh tana d'akinta."
"Batun maganan da kikayi mun ranan shin dagaske ne Amal ta shigo da wani gidan nan?" Har yau zuciyarsa ta kasa aminta masa da hakan.
"Uncle meyasa zan fad'a maka abinda idanu na basu gane mun ba? Ni tasa na kawo masa drink da snacks wallahi ka yarda dani."
"In tambayi mey gadi? Kisani idan har sharri kikayi mata ina iya 6a6alla ki a gidan nan." Sosai cikin Safiyya ya d'au ruwa yadda Afzal yake maganan sam ba wasa tattare da shi.
"Kasan Malam Ahmad da zama a majalisa kuna fita shima yake fita se lokacin dawowanku ya ke shigowa da k'yar idan yana nan Aunty ta shigo in kuma baka yarda dani ba muje a gabanta ka tambayeni a idonta in shaa Allahu amsan dana baka zan sake nanatawa saboda ba k'arya nake yi maka ba."
Sajen fuskansa ya shafe cike da mamaki da kuma rashin sanin abunyi gabad'aya kansa ya d'aure. "Shikenan mey kuka girka?"
"Babu Aunty bata ji dad'i ba kwana biyu so bata girka komi ba nima batace in girka komi ba kuma."
"Bata da lafiya?"
"Eh."
"Meyake damunta?"
"Toh nima ban sani ba gaskiya."
"Ina take?"
"Tana kwance a d'akinta tana bacci nakega."
"Jeki ce mata ta shirya driver ya kaita asibiti."
"Toh" ta amsa ta fice sallama tayi bakin k'ofan Amal sannan ta shiga ta k'arisa ciki had'e da durk'usawa daga gefen gadon.
"Wani abu ne?" Amal ta tambaya.
"Uncle ne ya dawo."
"In yunwa yake ji seki dafa masa abinci kinsan banida lafiya ban iya nayi girki ba."
"Eh na sanar dashi."
"Rashin lafiyan nawa?"
"Eh."
"Meya kaiki? Ni na aike ki?"
"Kiyi hak'uri Aunty yanzu de yace ince miki ki shirya wai driver ya kaiki asibiti."
"Kice mishi nagode bana buk'ata."
Sak abinda Amal ta fad'a mata taje ta fad'awa Afzal a fusace yace, "Ki ce mata ta shirya ba wasa nake ba." Haka ta dawo ta fad'awa Amal inda Amal ta sake turata kice mishi "Nace bazan je ba."
"Uncle wai bazata je ba" a fusace ya k'arisa d'akin had'e da bankad'e k'ofan na sosai Amal ta tsorata.
"Ki tashi a kaiki asibiti nace."
"Nace bazan je ba nagode."
"In ta halin ki za a bi a jinki ko kallon ki zanyi ne a gidan nan? Karki 6ata mun rai Amal ki tashi driver ya kaiki asibiti."
"Nace bazan jeba Yaya ana dole ne?"
"Rashin kunya kuma zakiyi mun? Ki cigaba Amal zamuga inda wannan banzan d'abi'ar zata kaiki" bata sake ce masa komai ba har yaja k'ofan ya fice. Wani irin masifaffen kuka ta rushe da, maghrib nayi ta mik'e tayi niyya bayan sallan Isha ta sanya hijabi ta fito waje takawa take wane wacce k'wai ya fashewa aciki har ta wuce Afzal dake zaune a parlour yana aiki akan laptop nasa, be ce mata komi ba itama bata ce da shi ko k'ala ba. Chan bada dad'ewa ba yana zaune kawai ya fara jin sautin amai daga kitchen besan lokacinda yayi wulli da laptop nasa ba ya nufi kitchen d'in inda ya tarar da Amal tsugune jikin sink tana ta kwararo amai. Na matuk'a ta basa tausayi kad'an ya rage beje ya rungumeta ba amma ya dakatar da kansa. Kallonta ya cigaba dayi har tagama ta d'auraye bakinta zamewa k'asa tayi don yadda bata da k'arfin ko sisi sosai Afzal yake ji ajikinsa duk yadda yaso shareta hakan ya gagara besan a lokacinda ya k'arisa ciki ya shiga d'agata ba.
"Ka sauke'eni bana so I can take care of myself" ta fad'a a galabaice sede be saurareta ba ya d'agata sama chak be sauk'eta a ko ina ba se akan kujera a parlour "Safiyya!"
"Na'am Uncle" ta amsa had'e da fitowa daga d'akinta.
"Wuce ki d'auko mun key'n mota na."
"Ki dawo Safiyya nace maka bazan je asibiti ba" Amal ta fad'a a kasalance "Zo ki tayani in mik'e Safiyya" ta buka'ceta har Safiyya ta shiga takowa gun Amal Afzal ya dakatar da ita "Nace kije ki d'auko mun key'n mota na ko?"
"Uncl-"
"Bakiya ji ne?" Har ta shiga takawa zuwa d'akin nasu Amal ta tsayar da ita "Nace kizo ki tayani in mik'e baki jini bane?"
"Uncle dan Allah ka bari in taimaka mata kayi hak'uri" ta fad'a tana kakkarwa.
"Kije idan kika kashe kanki seki huta kowa ma ya huta" yace da Amal ko kallonsa batayi ba ta jira Safiyya ta taho ta taimaka mata ta kaita d'aki.
"Sannu ko Aunty?"
"Ki had'a mun black tea please."
"Toh Aunty" da haka ta fice nan da nan ta had'o mata tean tazo wucewa d'akinta Afzal ya kirata chak ta tsaya had'e da tsugunawa.
"Na'am Uncle?"
"Meyake damun Amal? Karki yi mun k'arya."
"Uncle wallahi ban sani ba zazza6i tace mun."
"Kin ganta taje asibiti?"
"Gaskiya a'a tunda ka tafi ko makaranta bata sake fita ba" ta mai k'arya gudun kar ya gano gaskiyan al'amarin.
"Ya jikin nata?"
"Tace in had'a mata tea."
"Shikenan kina iya tafiya." Yana kammala abinda yakeyi ya rufe laptop d'in ya koma d'akinsa towel yaja ya shiga bayi ya watsa ruwa fitowansa ya nufi wardrobe nasa yana neman shorts da ze sa k'ark'ashin wani wandon da yakeda niyyan sanyawa da fari Safiyya ta ajiye takardan da Nazeefah ta bata har ze janye wandon seya fasa ya hango wani a sama, zara yayi ya sanya sannan ya kwanta sede ya kasa yin bacci se tunanin Amal kawai yake tuna yadda take amai d'azu kaman wacce ke neman harar da hanjin cikinta. Shin meyake damunta? Ko da wasa k'wak'walwarsa be kawo masa ciki ne da ita ba.
Washegari Amal ta d'an samu sauk'i don haka ta shiga shirin makaranta koda ta fito ta tarar da Afzal zaune kan dining yana karyawa bata yimai magana ba harkan gabanta kawai ta cigaba da yi. Sosai ya sha mamakin yadda ya ganta back on her feet contrary to yadda take jiya kaman wacce zata mutu. Sosai yake son tambayarta ya jiki amma ya kasa har yanzun haushinta yake ji na abubuwan data ringa yi masa tana gama abinda zatayi tayi ma Safiyya sallama yana jiran ko zata tambayesa kud'in makarantar ta yaga kawai ta fice.
K'arfe biyu Afzal ya dawo daga office lokacin Amal ma har ta dawo tana zaune a d'akinta tana karatu, d'akinsa ya wuce bayan Safiyya tayi masa sannu da zuwa. Kayan jikinsa ya rage ya fad'a bayi ya watsa ruwa fitowansa ya nufi wardrobe nasa dan neman kayan da zaisa a garin haka takardan da Safiyya ta sanya a tsakankanin wandunansa ya fad'i hannu yasa ya d'aga tare da bud'ewa in da ya soma karancewa kaman haka;
_To my most beloved soul on earth (Ya Abdul) I write this with a very heavy heart. Darling words cannot describe how much I miss you, I miss you terribly I wish I hadn't sacrificed your love for Ya Afzal cause it's true he doesn't deserve my love, I regret the day I chose him over you, Ya Abdul I wish you were here to cry along with me and take my sorrows away, I wish you were here to fight for me and set me free from this miserable torture. If I were to be given another chance, I would choose you a thousand times over Ya Afzal. Ya Afzal is such a heartless demon now that I've thought of it I just realized it was never love he really felt for me but rather lust. All these while he's been after my body and now that he's gotten what he's wanted he treats me more like a maid than his wife, Ya Abdul you're the one I truly love and not Ya Afzal I'll never love a heartless demon like him, I so hate him and I hate destiny even the more for separating me from you. My love for you will never die Habibi it's still fresh like an open wound and I shall continue to hold onto it, I believe that one day you'll come back to me, I will forever love you Ya Abdul. Life without you is so dull and colourless I need you to brighten up my world and wake me up from this horrible nightmare-_
Afzal be k'arisa karancewa ba ya fad'i a k'asa bisa ga wani irin k'una da ciwon da zuciyansa ya shiga yi masa birgima ya shiga yi wajen yana rik'e dai-dai saitin zuciyansa yayinda idanunsa suka kad'a sukayi ja zir cike da wahala ya d'age carpet ya 6oye takardan aciki. Wayansa ya shiga lalima amman yayi masa nisa haka ya cigaba da birgima a wajen har seda ya sume chan Safiyya da ta gama had'a masa abincinsa tayi sallama bakin k'ofan.
"Uncle na gama" takai minti biyu tana magana bakin k'ofar amma shiru dan haka taje ta samu Amal.
"Lafiya?"
"Aunty uncle ne yace in dafa masa farar spaghetti ya taho da sauce gashi na gama naje kiransa ina ta sallama bakin k'ofar d'akinsa amman shiru."
"Hala wanka yake ki jira idan ya fito."
"Toh" da haka ta fice bayan minti kusan biyar amma bata ji hayaniyan Afzal ba ta koma bakin k'ofan inda ta cigaba da yin sallama amma ba response d'akin Amal ta koma ta sanar da ita shiru fa har yanzu.
"Safiyya kina damuna kije mana ki lek'a d'akin halan bacci yake." Da haka ta koma d'akin ta bud'e k'ofan wani irin rikicaccen ihu ta k'urma bisa ga sumammiyar jikin Afzal da ta tarar a k'asa.
"Auntyy!!!" ta k'urma wa Amal kira ba shiri Amal dake kwance ta zabura tana tambayan ko lafiya har ta iso bakin k'ofan inda Safiyya keyi mata nuni da cikin d'akin a rikice. Lek'a d'akin da Amal tace zatayi itama ta k'urma wani d'ankaren ihu had'e da k'arisasa da salati a guje tayi kan Afzal had'e da aza kansa akan cinyarta tana bubbuga fuskansa "Yaya? Yaya? Yaya please wake up" ba shiri ta shiga yin kuka "Yaya I'm terribly sorry dan Allah kayi hak'uri ka tashi na shiga uku Safiyya kije ki kirawo driver" a guje Safiyya ta fice Amal se kuka take a wajen yayinda take kakkarwa "Yaya dan Allah karka tafi ka barni I'm so sorry please don't go." Mik'ewa tayi ta janyo kayansa ta sanya masa sannan driver ya k'arisa ya cicci6esa sukayi mota duka har da Safiyya. Tunda aka shige da Afzal emergency room Amal keta safa da marwah bakin corridon gabad'aya ta rasa nutsuwarta tsabaragen yadda ta tsule ko Mami ta kasa kira bale su Ummi. Safiyya ce ta kira Nazefah ta sanar da ita, ita kanta Nazeefah bata d'au hakan ze tayar wa Afzal ciwonsa ba sosai ta rikice yanzu idan hakan kuma ya zame sanadiyan mutuwansa? Da ko itace da babban asara. Sarai tasan Afzal bayi so idan ciwonsa ya tashi iyayensa su sani amma da gan-gan dan aga laifin Amal ta kira Ummi ta sanar da ita akan Afzal ya samu attack ba shiri Ummi ta kira Abba ta sanar da shi.
Kaman daga sama kawai Amal taga Nazeefah na shigowa bada dad'ewa ba sega Ummi har ma da Abba. Yau nata ya k'are 'hasbunallahu wa ni'imal wakeel' kawai take ta nanatawa. Kanta suka yo duka suna tambayarta meya faru Amal ta kasa magana se hawaye kawai daga k'arshe suka koma kan Safiyya.
"Wallahi ban sani ba ya shigo gida yace in dafa masa spaghetti bayan da na gama naje nayi mai sallama amman shiru se nida Aunty mukayi zaton ko wanka yakeyi chan da shirun yayi yawa na sake duba shi bud'e k'ofan da zanyi kawai na tarar da sumemmiyar jikinsa a k'asa."
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Ummi ta furta cike da tashin hankali.
"Dole akwai abinda akayi masa" cewan Nazeefah dake ta faman kukan munafirci "Sanin mune nan duka ciwon Ya Afzal bai ta6a tashi kazai haka dole saida sanadi" Nan ta kewayo kan Amal da gaban hijabinta ya jik'e jak'ab da hawaye. "Amal mey kikayi wa Ya Afzal? Sanin kowa ne kece sanadin ciwon sannan mey kikayi masa?"
"Nazeefah wani irin magana kike haka? Har kina tunanin zanyi wa Yaya abinda ze tayar masa da ciwonsa da gan-gan? Wallahi banyi wa Yaya komai ba wallahi ban mishi komai ba Ummi" ta sanar dasu cikin tsan-tsan kuka.
"Taya zakice baki yi masa komai ba Amal bayan kinsan kece sanadin ciwon nasa? Bayan sarai kinsan da zaran kinyi masa abinda zuciyar bata so ciwon na iya tashi yet you still went ahead kika k'untata masa. Idan ban manta ba jiya kafin Ya Afzal yabar gidana seda yace kina yi masa abubuwan da baya jin dad'insu amma baze yi miki magana ba saboda yana gudun 6acin ranki meyasa ke bazaki mishi haka ba ki nisanci duk abinda ze 6ata masa rai?"
"Nazeefah ki yarda da ni Ummi, Abba wallahi ban yi wa Yaya komai ba."
"Ummi wallahi ita ce ita ta janyo komi koda rasa ransa Ya Afzal yayi kisani kece sanadi Amal kuma bazan ta6a yafe miki ba idan wani abun ya samesa" nan ta fad'a jikin Ummi tana kuka.
"Amal me kikayi wa d'ana? Mey kikayi wa Prince? A tunani na kece mace ta k'arshe da zata guji yi masa abinda zuciyarsa bata so meya faru Amal?"
"Hajiya Mariam ya isa haka please mu jira likitan su fito tukuna" da haka Abba ya samu ya toshe wa Nazeefah da Ummi baki koda kowa ya nemi waje ya zauna Amal ta kasa zama se safa da marwah take a wajen chan globe na bakin k'ofan da akeyi wa Afzal aiki aciki ya mutu nan suka duk'ufa suna jiran fitowan Dr. Kusan a tare duk suka jefa masa tambaya.
"Humm!" Dr'n ya sauk'e nauyayyan numfashi "Bazan 6oye muku ba ku sani by each attack da yake samu hakan na weakening rate and efficiency na heartbeat nasa ku magance masa matsala tun ba yau ba kun kasa kun zuba masa ido ranan da zuciyan ta buga gabad'aya shikenan se ku huta muma mu huta."
"Yanzu ya jikin nasa?" Abba ya tambaya.
"Munyi masa abinda zamu iya sauran ku jira ya farfad'o d'ayan ku ya biyoni ya amshi list na drugs da za'a sai mishi." Abba ne yabi bayansa ya rage su Ummi.
"Ummi dan Allah kibar kukan haka" cewan Nazeefah tana share mata hawaye. "Amal kin de ji abinda Dr'n Ya Afzal yace ko? Rayuwan Afzal yayi depending akan ki ne dan Allah ki kiyaye k'untata masa idan baki damu da shi ba mu nan we love and care about him."
"Nazeefah-"
Katse ta tayi da wuri "Ummi wallahi tun ba yau ba Ya Afzal yake mun complaining akanta gashi yanzu seda ta kwantar mana da shi."
"Nazeefah wallahi bani bace dan Allah ki yarda dani."
"Toh wa kikeso a zarga idan ba ke ba Amal? Ummi dan Allah ki sa baki."
"Amal dan Allah ba dan ni ba dan Allah nace kiyi hak'uri ki rufa mun asiri ki na yima Afzal abinda yakeso kin fi kowa sanin halin da yake ciki" Ummi ta rok'eta cikin kuka. "Na sani ba koda yaushe Afzal yake da dad'i ba amma dan Allah kina hak'uri da shi kina yi mishi abinda yakeso please Amal I can't afford to lose him shi kad'ai Allah ya bani."
"Ummi dan Allah kiyi hak'uri I'm so sorry, please forgive me."
"Shikenan bari in shiga in duba sa" ta kai kusan minti goma aciki sannan ta fito har anan Afzal be tashi ba tana fitowa sega Abba nan shima ya dawo da magunan Afzal wanda ya mik'a wa Ummi. Bayanta ya bi ya shiga ya duba Afzal shima bayan ya fito ya buk'aci Nazeefah next da ta shiga, k'arshe Amal ta shiga. A hankali ta k'arisa cikin d'akin ta zauna daga gefensa tare da sa hannunta cikin gashin kansa tana shafawa a hankali.
"Yaya I'm so sorry dan Allah ka tashi ka fad'a musu bani bace" kuka ta shiga yi sosai a wajen a hankaki ta kwantar da kanta a k'irjinsa yayinda kukan nata ya tsananta "Yaya please wake up wallahi ban aikata ko abu d'aya daga cikin ababen da kake tokari na dasu ba wallahi wasu ne suke neman shiga tsakanin mu Yaya bazan ta6a aikata abinda nasan ze 6ata maka rai ko zubar maka da mutunci ba you have to believe me and stop bothering yourself I beg of you please" a hankali ta d'ago da kanta tare da had'a hannunsu gu d'aya "I love you so much and no matter what I'll never leave your side" a hankali ta sauk'e light kiss akai. Har ta kai ga mik'ewa taga ya motsa yatsansa zamanta ta gyara ta shiga kiran sunansa har seda ya bud'e idonsa.
"Yaya you're back!" Tayi exclaiming ba shiri tayi hugging nasa sede ko ta6a jikinta beyi ba gabad'aya ji yayi ta haramta masa tunda har yanzu Abdul ne a zuciyarta. A hankali ta d'ago daga jikinsa "Yaya what happened?" ta tambayesa had'e da zira hannunta cikin gashin kansa. Kan nasa ya shiga girgizawa da nufin baya so a hankali ta maida hannun nata "I'm sorry" tayi apologizing.
"Su Ummi suna waje bari inyi musu magana su shigo" kansa taga ya kawar gabad'aya dan ko kallon ta baya sha'awan yi ko a mafarki akace masa Amal zatayi masa haka baze yarda ba kuma ba abinda yafi tsana kaman wannan munafikin halin hawainiyan nata, zatayi abu kuma ta zagayo kaman batayi komi ba tana proving innocence. Ko a ina yaci karo da rubutun chan yasan nata ne.
"Yaya har yanzu fushi kake dani? Yaya wallahi ban aikata ko d'aya daga cikin abubuwan da kake tokarina dasu ba Yaya sanin kanka ne ina sonka kuma bazan ta6a yin abinda ze 6ata maka rai ko zubar maka da mutunci ba you have to believe me."
"Ki kira mun Ummi da Nazeefah" yace da ita zalla ba tare da ya kalleta ba hawayenta ta share sannan ta mik'e "Allah baka lafiya" ko ta kanta beyi ba har ta fice
"Ya Afzal ya farfad'o Ummi."
"Ya farfad'o?" Ummi ta tambaya had'e da mik'ewa. Haushi Nazeefah taji wato seda Amal ta shiga ne ya ga daman tashi akan duk uban kalaman soyayyan da tayita fad'a masa? Duk su kwantar da hankalinsu soon enough ze saki Amal d'in.
"Yana buk'atan ganinki da Nazeefah."
"Alhamdulillah! Alhamdulillah" ta mik'a godiyar wa Allah.
"Abba fah?" Amal ta tambaya.
"Ya koma" Nazeefah ta amsa. Tana ganin shigewansu ta kira Safiyya suka koma gida tunda baya buk'atan ta na mey zata cigaba da zama?
"Prince!" Ummi ta kira sunansa had'e da hugging nasa "Prince dan Allah kayi a hankali wallahi likitanka na jiye maka."
"Ummi please it's okay I'll be fine."
"Welcome back Ya Afzal" Nazeefah dake tsaye akansa ta fad'a mai.
"Thank you Rabba'atul Bait" ya amsa yana mata murmushi.
"Prince meya faru? Mey Amal tayi maka?"
"Amal kuma?"
"Ka fara da zurfin cikin nan naka ko? Nazeefah ba ke kikace Amal ce bata kyautata masa ba?" Ido ya d'ago yana kallon Nazeefah da cikinta ya d'au ruwa tuni ta shiga rarraba ido.
"Haka nace miki?"
"Ya Afzal naga.. ermm... Toh ai sanin kanmu ne duka nan Amal ce sanadin ciwon naka Ya Afzal ko ba kai ka fad'a mun ba?"
"Se kuma nace miki Amal ce bata kyautata mun?"
"Toh waye ne?" Ummi ta tambayesa "Wayene idan ba Amal d'in ba?" Shiru yayi bece komai ba dan haka Ummi tayi tunanin ko bayi son yayi maganan a gaban Nazeefah ne. "Ermm nace mey kakeso kaci Prince Nazeefah ta girka ta kawo maka? Girkin waye ne acikinku?" Ta tambayi Nazeefah.
"Girkin Amal ne amma ba damuwa zan girka in kawo masa mey kakeso Ya Afzal?"
"Boiled potatoes da egg sauce" ya sanar da ita.
"Toh bari inje zan dawo yanzu in shaa Allah." Tana ficewa Ummi ta dawo da kallonta akan Afzal "Toh Nazeefar ta tafi gaya mun meke faruwa?"
"Ummi babu" mari me zafi ta kai masa akan cinya. "Ummi please! Kin fa san hannunki da zafi."
"Ina tambayanka abu kana kallon cikin idona kana mun k'arya? Nace meya faru? Wallahi ka kuskura kayi mun k'arya toh ni da kai."
"Ummi misunderstanding muka samu."
"Fad'a kukayi?" Kai ya gyad'a mata "Amma mun shirya shigowantan nan."
"Ka tabbata?"
"Eh Ummi."
"Ba senayi mata magana ba?"
"Babu amfani komi ya wuce."
"Toh koma meye ne de ka daina bin komi da zuciya haka kasan yadda zuciyar taka take da rauni please Prince Abbanka ma na nan ai d'azun ya tafi."
"Allah sarki ku daina tada hankalinku please I'll be fine."
"Zaka kwana ko zaka koma gida a yau?"
"Kwana kuma? Na samu sauk'i se in kwana a asibiti? Nazeefah na kawo mun abinci naci zan koma gida."
"Kana buk'atan wani abu toh?"
"A'a zaki iya tafiya Ummi thank you so much."
"Don't mention my boy Allah baka lafiya ko?" Kai ya gyad'a tare da amsawa yanayi mata murmushi. "Bari inyi ma Amal magana tazo ta tayaka zama kafin nan." Da mamaki ta nemi Amal bayan fitanta ta rasa ta dawowa ciki tayi tace, "Ban ganta ba fa, kode ta tafi ne?"
"Ohh ban fad'a miki ba ko? Na ce ta koma kinsan itama kwana biyu bata ji dad'i ba zazza6i ya sata a gaba."
"Haba! Shiyasa na ga ta rame Allah sarki Allah shi bata lafiya."
"Ameen Ummi." Zama ya cigaba dayi cikin d'akin har zuwa lokacinda Nazeefah ta kawo masa abincin ita da kanta ta basa bayan da ya gama tayi ma likitin nasa magana akayi discharging nasu. Kasancewar kwanan Amal ne har cikin gida Nazeefah ta kaisa sannan ta juya ta wuce nata gidan. Sannu da zuwa Safiyya tayi masa lokacinda ya shigo ciki.
"Ina Amal?" Ya tambayeta.
"Tana d'akinta" k'arisawa d'akinsa yayi ya zaro takardan d'azun had'e da ninkewa ya adana. Wayansa ya d'aga dan kiran Sultan inda ya tarar da missed call na Abba nan take ya kirasa back suka gaisa Abba yake mishi jaje. Suna k'are wayan ya kira Sultan.
"Maza yane?"
"Ba lafiya ba yanzu haka daga asibiti nake."
"Subhanallahi meya faru ciwon naka ne?"
"Yes and alot has happened Sultan ka shigo gobe kaji?"
"Toh sannu ya Amal ko gun Nazeefah kake?"
"Ni seka shigo kawai" tun daga amsan sa Sultan ya gane akwai matsala "Allah kaimu goben toh."
"Ameen" Afzal ya amsa had'e da katse wayan. Zama ya cigaba dayi a d'akin chan bayan sallan Maghrib Amal tayi sallama cikin d'akin nasa shiru yayi yak'i amsawa dan haka ta bud'e k'ofan ta shiga kansa yayi saurin kawarwa.
"Yaya-"
"Get out Amal bana k'aunan sake ganinki a cikin d'akin nan in shaa Allahu burin ki ya kusan cika kiban lokaci kad'an."
"Yaya mey kake nufi? Wani buri?"
"Just get out Amal in kuma fitan ne bazaki iya ba ina iya bar miki gidan gabad'aya."
"Allah huci zuciyanka" tace mishi zalla ta juya ta fice d'akinta ta koma inda ta kwanta kan gado ta shiga kuka sosai.
Washegari kaman yadda Sultan ya mar alk'awari haka yazarce gidan nasu daga office da Amal suka fara had'uwa lokacin tana zaune a dining tana cin abinci sannu da zuwa tayi masa tasa Safiyya ta kawo masa drink da snacks.
"Kinyi wuyan gani amarya."
"Ji Ya Sultan nice amaryar?"
"Amaryar amini na ma kuwa ke baki san yadda nake ji dake ba ko?"
"Uhm haka de kace amma ka barni da makaranta yana ta bani wuya."
"Karde shiya ramar dake haka? Har kun fara tests ne?"
"Ai mu kullum cikin tests muke Ya Sultan se a hankali."
"Allah sarki ba three kike ba yanzu? Kinyi mey wuyan ai Allah sa albarka."
"Ameen Ya Sultan yasu Umma?"
"Lafiyansu k'alau Afzal fa yana gida?"
"Eh ba motansa na waje ba?"
"Na sani koya fita strolling ya jikin nasa?"
"Toh Alhamdulillah de bari inyi mishi magana" nan ta mik'e ta nufi d'akin nasa sallama tayi amma be amsa ba dan haka ta bud'e ta shiga akan gado ta tsincesa yana bacci k'arisawa tayi had'e da tapping nasa a k'afa a hankali.
"Yaya? Yaya ka tashi Ya Sultan yazo" a hankali ya shiga bud'e idonsa har ya bud'e su duka ganin ita ne yayi saurin kawar da kansa "Bance kar in sake ganin ki acikin d'akin nan ba?"
"I'm sorry Ya Sultan ne yazo ya turo in kira ka" da haka ta juya ta fice. Brushing yayi ya wanke fuskansa sannan ya sanya shiry akan gajeren wandonsa ya fito ya sami Sultan. Bayan sun gaisa ya ce mishi su k'arisa ciki.
"Meya samu nan d'in? Ko so kake mu koro Amal waje ita da gidanta?"
"Bata d'akin come in" be sake musu ba ya mik'e suka k'arisa d'akin. Note na Amal ya d'au ya wulla wa Sultan akan cinya "Wannan fah?" Sultan yayi saurin tambaya.
"Ka bud'e kayi observing handwriting dake ciki" yadda aka ce da shi haka yayi bayan ya karance rubutun ya d'ago kai "Ehen?"
"Here take a look at this handwriting" yayi maganan yana zaro takardan d'azun daga inda ya 6oye "Handwriting na mutum d'aya ne ko kuwa?"
"Of course na mutum d'aya ne mana" Sultan ya amsa bayan yayi comparing handwriting d'in.
"Thank you ka zauna da kyau ka karanta content d'in." Hankali ya miyar kai ya shiga karancewa yayinda mamaki ya mamaye mai fuska da zuciya.
"Waya rubuta wannan maza?"
"Ka duba sunan dake jikin littafin" Afzal ya umarcesa.
"You don't mean this!" ya furta bayan daya duba yaga sunan Amal rubuce a bangon littafin.
"Yanzu zaka ga laifina idan na yanka mata ko wani irin hukunci?"
"Ban fahimce ka ba Triple A kana nufin Amal ce ta rubuta wannan?" Ya tambaya da d'umbun mamaki.
"Baka iya karatu bane?"
"I'm just confused Triple A, Amal de? Har Amal ce zata rubuta wannan abu? Kode kafin kuyi aure ne?"
"Kana ganin sabon paper sabon rubutu kana zancen kafin muyi aure?"
"Amma meya faru? Meyayi zafi da har Amal zata rubuta wannan abu a matsayinta na matarka?"
"Gata chan a chan d'akin kana iya zuwa ka tambayeta."
"Wow!" Ya numfasa totally speechless.
"Maza ban san meyake damun Amal ba yarinyar nan ta sauya gabad'aya ta koma wani abun daban banda munafurci da had'a kaina da Nazeefah ba abinda takeyi ko tsinke na sai mata seta buga waya wa Nazeefah ta fad'a mata knowing right ba duka abinda nakeyi mata nakeyi wa Nazeefah ba sedan kawai ta 6ata ni idon Nazeefah tasa Nazeefah tayi mun kallon maras adalci hakan be isheta ba har course mates nata maza ta fara kawo mun cikin gidan nan suna zama a kujera d'aya."
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un wacce Amal tukuna? Amal Amal naka da na sani?"
"Ita de Amal ta cikin gidan nan."
"Maza are you sure of what you're saying? Amal ce har zata shigo maka da gardawa cikin gidan nan?"
"In kira maka mey aikinta ne ka tambayeta?"
"Subhanallahi meya sameta?"
"Waya san mata ne?"
"Mey kake nufi kenan yanzu kana nufin kana zargin Amal kenan? Kana zargin tana ci maka amana?"
"Nooo not at all nasan Amal baza ta ta6a cin amanan aurena ba, ko tunanin yin hakan ma baza tayi ba I know that."
"Toh mey kake nufi da tana shigo maka da maza gida?"
"Yes ta daina shigo mun da coursemates nata saboda ba'a san abinda shaid'an ze iya raya musu ba wataran koba d'abi'arta bane wataran shi gardin ze iya kwad'aitar mata da hakan ko ba ka gane abinda nake nufi ba?"
"Sosai na fahimce ka amma Afzal I'm still shocked Amal da muka sani ce ta sauya haka take yin ababen nan da ka irgo? Innocent Amal taka?? Na tabbata haka kawai Amal bazata sauya halayanta ba sede idan kai kayi pushing nata don't you forget that for every reaction there's an action."
"Mey zanyi mata maza? Kafi kowa sanin irin son da nake yiwa yarinyar nan, Wallahi Amal bata ta6a neman abu a guna ta rasa ba komi ina yi mata da iyayenta amma ka kalli da abinda zata sak'a mun kuma abinda yafi bani haushi shine k'aryata komi da takeyi har yanzu ita bata amince da laifukanta ba bale ta nemi tuba mu sasanta tsakanin mu ni bazan iya ba, I can't do this anymore I'm tired of her sick behavior."
"Mey kake shirin yi?"
"Ba Abdul kowa take so ba? Seta je ta samesa."
"Wani irin magana kake haka Afzal? Da igiyan auranka akanta kake son taje ta auri wani?"
"Sawwak'e mata zanyi."
"Mey?? Kana da hankali kuwa Afzal? Wani irin zafin kishi ne da kai haka?"
"Toh mey kakeso inyi? Ba gara na sawwak'e mata ba taje ta samu shi wanda take son? Bazan iya zama da ita ba knowing zuciyarta na tare da wani gara na rasata gabad'aya dan idan har na cigaba da zama da ita toh zan cigaba da kallonta da abin ne wanda zuciya ta baza ta iya d'auka ba wataran sede ta har6a tabar aiki."
"Idan ka sawwak'e mata ta koma gun Abdul kai kuma fah?"
"Na sani sena fita shan wuya bayan rabuwan nan amma ka gaya mun mey riban ajiyeta a wajena idan zuciyarta na tare da wani daban Sultan? I love Amal kuma har duniya ta nad'e bazan fasa sonta ba but this is not reason enough to keep her with me tunda gashi da hannunta ta rubuta bata sona tayi nadaman aurena. Kaji fa har cewa take wai dama tun fari tasan jikinta kawai nake so yanzu da na samu abinda nake nema gashi ina walak'anta ta. Ni fa Maza? Ni d'in da ko hannunta ban ta6a sha'awan rik'ewa ba... excuse me" tari ya shiga yi yayinda zuciyansa ya fara tashi yana yi masa k'una tsan-tsan takaici da bak'in ciki da 6acin rai.
"Dan Allah kayi a hankali ba senun sake kaika asibiti ba it's okay ya isa."
Gyaran murya yayi ya cigaba "So I think it'll be better idan na barta taje ta samu shi wanda take so d'in ta huta kowa ma ya huta."
"Kai kuma fa Triple A? Ya zakayi da rayuwanka idan kuka rabu? Shin ka manta rayuwanka gabad'aya yana revolving ne a jikin na Amal? Shin ka manta idan ba soyayyarta zuciyarka bazata iya aiki ba? Shin ka manta idan ba ita a kusa da kai rayuwarka tana cikin gwagwarmaya? Ina ka mance da dukkan hakan Afzal har kake tunanin sawwak'ewa Amal? Besides ni ban yarda ma innocent Amal d'in da na sani zata iya aikata wannan munanan abubuwan da kake tokarinta da su ba. She's too innocent to do all these I know Amal kuma na yarda da ita."
RANA D'AYA!
#RD
Love... King Miemiebee👄✨
Download Rana Daya Littafi Na Ɗaya Complete Hausa Novel
0 Comments
Thank you for this comment