[6/5, 8:53 PM] ρяσυ∂ℓу мє∂ι¢αℓ яє¢σя∂: SARKIN SARAKAI
Littafi Na Huɗu (4)
Part A.
.
Marubucin Littafin
Abdul Aziz sani M/Gini
AA Misau Ke Magana
.
Labari ya isowa AA Misau cewa
NAN TAKE BAWA HALUF YA GOYATA A BAYANSA SUKA TAFI INDA AKA KAMAR DA su Sarki Sahibul Hairi.
Kafin su karasa gurin sai suka ga wani kare wanda shi ma aka kamar da shi kamar yadda aka kamar da su Sarki Sahibul Hairi.
Bawa Haluf ya tsaya a dai-dai kan karen sannan ya sauke Alfila daga bayansa ya fito da wannan kana nan kwalabe masu ruwan sihiri a aljihunsa.
Kawai sai ya bude guda ya yunkura zai kwara akan wannan kare.
Cikin sauri Alfila ta ruke Hannunsa ta ce da shi a cikin rada.
"me kake shirin yi ne?"
Haluf ya ce, "so nake na jarraba wannan ruwan sihirin akan wannan karen ko ruhinsa zai dawo domin nayi amfani da shi wajan tashin 'yan uwana da Boka Shamzabul zwas ya mai da su gumaka."
Koda jin wannan batu sai Alfila tayi murmushi ta ce, "Ai inda ka zuba wannan shidin ruwa akan wannan karen da nan take zai rugurguje ya zama gari."
Cikin mamaki Haluf ya dubeta ya ce, "ya ya akayi ki ka san wannan?".
Alfila tayi murmushi ta ce, "Ai mahaifina yana da duk irin wadannan ruwan sihirin guda dari ba daya ne kuma ko wanne na san amfaninsa".
Koda jin haka sai murna ta kama Bawa Haluf ya ce, "To yanzu wanne ne zan zubawa 'yan uwana ruhinsu ya dawo?".
Alfila ta ce, "ba zan gaya maka ba face kayi mini alkawari guda."
Haluf ya ce, "fadi duk irin abinda ki ke son nayi miki, lallai zan zama mai ciki alkawari a gareki".
Alfila ta ce, "ina son ka yi mini alkawari cewa zaka mayar da ni kasarmu wajen mahaifina, domin na tabbatar da cewa a halin yanzu yana can cikin tsananin damuwa da taahin hankali bisa rashin ganina.
Tabbas inda yana da ikon zuwa nan ya kar6eni da tuni ya zo."
Bawa Haluf ya ce, "kwantar da hankalinki ya ke Alfila kiyi sani cewa ni da maigidana mun san komao bisa al'amarinki, kuma akan hakan ne ma muka zo nan fadar Shmzabul Azwas domin mu sace ki mu kaiki gida ga abbanki domin muma munada muhimmiyar bukata wacce muka son ya biya mana".
Koda jin wannan batu sai Alfila tayi murmushi ta ce, "shin maigidanaka shi ne sarki Sahibul Hairu na Birnin Misra?".
Cikin mamaki Bawa Haluf ya ce, "kwarai kuwa shi ne, ya ya aki yi kika sani?".
Alfila ta ce, "Ai tuntuni mahaifina ya bani labarinsa da irin matsalar da ta addabi rayuwarsa cewa bashi da wani buri wanda yafi ya ga yafi gaba dayan sarakunan duniya arzuki, daukaka da yawan mata sabo da gorin da sauran sarakina suke yi masa akan cewa shine mafi talauci da kaskanci a cikin sarakuna.
Lallai yanzu na aminta da kai don haka sai ka fito da wadannan kwalabe na nuna maka wadda za kayi amfani da shi."
Cikin murna da hanzari Bawa Haluf ya fito da sauran kwalaban daga cikin aljihunsa. Nan take Alfila ta dauki kwalba da ke dauke da shudin ruwa ta karasa in da su sarki Sahibul Hairi suke a tsaye jikam cikin suffar gumaka.
Da zuwan ta sai ta bude kwalbar sai ta digawa kowannensu.
Faruwar haka ke da wuya sai Sarki Sahibul Hairi ya fara motsawa.
Idanunsa ne suka fara budewa, sannan 'yan yatsunsa na hannu da na kafafunsa, sannan ragowar jikinsa. Faruwar haka ke da wuya sai jikin gimbiya Humaira ya motsa gaba daya.
Koda Humaira ta bude idanun ta sai ta rafka salati. Al'amarin da ya janyo gaba daya gidan ya kama girgiza yana rugurgujewa ke nan.
Kwatsam! Sai ga aljani Shamzabul Azwas ya kara bayyana a gabansu cikin firgici da tsananin mamaki. Ita kuwa gimbiya Humaira sai ta lazamci karanta wadansu addu'o'i na musammam bata yadda ta daina ambatonsu.
Ya yin da Shamzabul Azwas ya yi arba da Bawa Haluf sai ya ciji yatsa cikin tsananin takaici domin ya san cewa mantuwar da ya yi da shi ita ce babban kuskurensa.
Ita kuwa Alfila sai ta ruga bayan sarki Sahibul Hairi ta 6uya tana mau cewa da shi, "ya kai wannan sadaukin sarki kada ka bari azzalumi Shamzabul Azwas ya maidani cikin kwalbarsa ta tsafi, domin kuwa idan hakan ta faru kaima har abada burinka ba zai ta6a ciki ba."
Koda wannan batu sai Sarki Sahibul Hairi dada kankame Alfila a bayansa sannan ya zare takobinsa yana mai fuskantar Shamzabul Azwas.
Shamzabul Azwas ya dubi sarki Sahibul Hairi ya dubi gimbiya Humaira kawai sai ya bushe da mahaukaciyar dariya sannan kuma ya murtuke fuskarsa tamkar wnda aka aikowa da sakon mutuwa ya daka musu tsawa wadda ta sa suka ji hantar cikinsu ta kada kamar zata fito waje.
Ya ce, "ku kananan sadaukai ku yi sani cewa hakika ku tsokano tsuliyar dodo, dan haka yau zakuga bala'i da masifa irin wadda baku ta6a gani ba a rayuwarku. Kun katse mini aikina a karo na farko alhali na kusa idashi, nakamaku na sanyaku a cikin tarkona wanda babu wani mahaluki da ya isa ya ketareshi ya kai labari amma sai gashi ku yanzu kun tarwatsa tarkon nawa, har ma kun katse mini aikin nawa a karo na biyu. To ku sani cewa wannan karon ba wai zan sanyaku a cikin tarko bane sai dai na zaremuku ruhin numfashinku gaba daya tunda kun zamo dan hakin da ka raina maitsokane mini ido".
Kafin Shamzabul Azwas ya gama rufe bakinsa sai gimbiya Humaira ta daka masa tsawa ta ce, "ya kai tsohon munafikin Allah wanda ya gaji cin amanar Allah da bayinsa, ka sani cewa kai kana kan hanyar 6ata mabayyani, ni kuwa ina kanhanyar shiriya kuma a ko yaushe Allah na tare da bayinsa masu tsoransa da bin dokokinsa, don haka nasan cewa komai wuya, komai gumu sai na sami nasara akan ka, don haka sai ka shirya ga MACE MAI KAMAR MAZA nan bisa kan ka".
Kafin Shamzabul Azwas ya kara mai da martani tuni Humaira ta falfala da azababban gudu izuwa gareshe, kawai sai gani ya yi ta daka tsalle guda daya tayi sama ta dure a gabansa tana mai kawo masa mummunan sara da nufin ta zarga masa kafada gida biyu. Shamzabul Azwas ya goce cikin zafin nama, amma duk da haka sai da takobinta ta zabtare rabin gashin kansa, shi kuwa ya hantsila gefe daya.
Koda Sha,zabul Azwas ya g rabin gashin kansa a kas, sai hankalins ya dugunzuma domin tunda ya mallaki wannan damara ta kugunsa bai ta6a haduwa da wani jarumi ba wanda ya iya kai masa wannan mugun hari ba face Humaira.
Cikin tsananin rudewa ya daga rigarsa ya shafa damarar kugun nasa don yaji wai shin yana tare da ita kuwa.
Ai kuwa sai yaga damarar na nan.
Al'amarin da ya kara furgitardashi kenan ya mie tsaye zumbur! Ya ja da baya ya gyara tsayiwa sannan ya zare takobinsa sannan ya fuskanci Humaira.
Koda ganin haka sau Humaira tayi murmushi ta ce, "ya kai tsohon munafikin Allah kai sani cewa komai na da lokacinsa.
Tabbas Allah ya ara maka lokaci a baya kayi budurinka ta hanyar amfani da wannan damara da ke kugunka wacce ke dauke da sunayansa tsarkaka, to ka sani cewa lokaci ya kare a yanzu.
A yau sai na hallakaka na rabaka da wannan damara ta zama tawa domin shi kansa Ubangiji yana kishin Addininsa da bayinsa, don haka nayi imani cewa sai ya bani nasara a kanka.
Lallai zai bani karfin da ya fi wanda kake amfani da shi wajan zaluntar bayinsa, burinka na son ka mallaki duniyar nan gaba dayanta ba zai taba cika ba."
Koda gama fadin haka sai Humaira ta sake daka taalle irin na baya ta dire gaban Shamzabul Azwas suka sake ruguntsimewa da azababban yaki suna masu kaiwa juna sara da suka cikin mutukar zafin nama, juriya da bajinta gami da nuna kwarewa.
A duk sa'adda takobin suka sai kaga tartsatsin wuta na tashi gami da tsawa da walkiya.
Duk wanda aka kaiwa sara ya goce, to fa duk abin da takobin ta sara sai abin ya dare gida biyu kuma ya kama da wuta. Nan da nan suka hargitsa fadar gaba daya suka dugunzuma hankalin duk wani abu mai rai da ke cikinta.
Su kansu su sarki Sahibul Hairi daka tsaye suna kallon artabun da ake sai da kallon ya gagresu suka kama guje-guje suna neman ma6uya domin ginin ya ci gaba da rushewa yana fadowa kasa zai dannesu.
Sai da Shanzabul Azwas da Humaira suka shafe sa'a uku cur! Suna wannan gumurzu ya zamana cewa gini fadar fadar ya ruguje ya zama fili fetal har ma 6angorin sun danne sarki Sahibul Hairi da Bawa Haluf da yarinya Alfila sun kasa tashi, kuma suna ihu suna kiran sunan Humaira ta kawo musu dauki domin rayuwarsu tana cikin tsaka mai wuya.
A wannan lokaci Huamaira da Shamzabul Azwas babu wanda ya sami rauni ko daya a jikinsu, kuma babu mai nuna almar gajiya a tare da shi, tamkar ma a sannan suka fara gumurzun.
Koda Humaira ta hango hali da su sarki Sahibul Hairi suke ciki sai ta fusata ainun ta ci gaba da karanta addu'o'i da ta fara yi a dazu, sannan ta afkawa Shamzabul Azwas da dukkan karfinta tana mai kai masa mugun sara da suka.
Wannan karon sai labari yasha banbandomin karfin saran nata da nauyinsa sai ya ninka na Shamzabul Azwas sau uku har ta kai cewa baya iya mai da martani kuma da kyar yake iya kare harin.
Ana cikin haka ne da ta kawo masa wannan sara a ka ya kare da takobinsa sai da ya durkuahe kasa bisa gwiwoyinsa. Take takobinsa da tata suka rabe gida bibiyu. Karfin saran ya sa Shamzabul Azwas ya fadi kasa ya mirgina baya sau uku, sannan ya mike zaune zumbur! A lokaci guda duk su biyun suka dubi gutsiran takobin da ke hannunsu suka yi jifa da su. Kawai sai Shamzabul Azwas ya mike tsaye yana murmushin mugunta sannan ya dunkule yatsun hannunsa yana shirin a fara gumurzuwa da hannu. A tunaninsa ya tabbatar da cewa ya fi Humaira karfin dantse, don haka dolene wannan karan ya gama da ita.
Koda Humaira ta gane nufin Shamzabul Azwas sai ita ma ta dunkule yatsun hannunta ta daga hannayen sama tayi shirin fara dambe, kuma ta ci gaba da karanta Addu'o'i a cikin zuciyarta. Shamzabul Azwas ya falfalo da gudun tsiya irin nasu na aljanu tamkar walkiya izuwa gareta ya kawo mata wawan naushi a fuska kawai sai yaga ta kare naushin da hannunta. Koda hannunsa da nata suka hadu sai yaji kamar nasa hannayan za su rugurguje, ba shiri ya juya da baya zai kare amma sai ta damko wuyansa da hannun daya ta daga shi sama tamkar ta dau jariri ta fyada da kasa sannan ta kuma dau kansa da hannu biyu ta cillashi sama kamar takarada. Shamzabul Azwas ya fado kan rusassun tubalin gini a galabaice. Kafin ya sami damar mikewa Humaira ta bayyana tsulum a gabansa ta tallafo kansa da hannunta na hagu sannan ta dinga gabza masa lugude naushi a fuskarsa da hannunta na dama. Nan da nan ta hada masa jini da majina ta sauyawa fuakarsa kamanni. Nan take Shamzabul Azwas ya sume, Humaira ta sakeshi sai ya baje a kas tamkar gawa.
Kawai sai ta sunkuya tana mai karanta Bismillah, ta kwance wannan damara daga kugunsa mai dauke da sunayen Allah tsarkaka ta daura a kugunta. Gama hakan ke da wuya sai ta ruga wajan su Sarki Sahibul Hairi domin ta ceci rayuwarsu.
Gunguma-gunguman tobalin dutse ne ya danne su sarki Sahibul Hairi wanda inda karti goma za su taru baza su iya dagashi ba, amma sai ga Humaira tana dauke tubalan duwatsun tana wurgi da su can gefe daya. Cikin dakika kadan ta zaro sarki Sahibul Hairi, Alfila da Bawa Haluf sai suka tsandara ihu sabo da abin da suka hango a bayanta. Kafin Humaira ta juya taga abin da yake tahowa tuni Shamzabul Azwas ya soka mata wani dogon mashi a gadon bayanta. Mashin ya faso ta cikinta. Bisa mamaki sai Humaira ta ga babu ko digon jini da ya zuba daga jikinta sakamakon wannan mashin da ya tsira ma ta. Humaira ta juya tafuskanci Shamzabul Azwas ta ga ya tsaya cak! Yana kallonta cikin tsananin mamaki, nan take Humaira ta sa hannunta ta zare mashin daga cikinta sai gashi sai gashi ramin da mashin ya yi a jikinta sai gashi ya 6ace 6at! Ko alamar rauni babu a wajan.
Humaira tasa hannunta biyu ta lankwasa mashin duk da cewa an yishi da karfe mai kwari da kauri, amma sai gashi ta kanannadeshi ta cureshi waje daya tamkar an daka fura a turmi, sannan tayi jifa da shi.
Koda ganin wannan abin al'ajabi sai Shamzabul Azwas ya juya da sauri da nufin ya gudu amma sai Humaira ta sake cafo wuyansa. Wannan karon da ta daga shi sama sai da ta yi filfilwa da shi sannan ta fyadashi da kasa ta sa kafarta guda ta take wuyansa sai gashi yana kakarin mutuwa, jini na zuba ta hancinsa da bakinsa.
Allah sarkin iko, yanzu in ba Allah ba wazai iya bawa Bil'adama irin wannan gagarumin karfi wanda zai iya yin fada da aljani har ya sami nasara akansa.
Lokacin da aljani Shamzabul Azwas ya fara wannan kakarin mutuwa sai ya dubi humaira cikin karfin hali sannan ya bushe da dariya. Al'amarin da ya mutukar bata mamaki ke nan ta daga kafarta daga kan wuyansa sabo da tasan bashi da wani kuzarin da zai iya yin komai.
Koda Shamzabul Azwas ya yi tari sai ga gudan jini ya fado daga bakinsa mai kauri tamkar hantar cikinsa ce ta fado. A wannan lokaci idanunsa sunyi jawaur babu kyan gani tamkar wutace ke ruri a cikinsa.
Shamzabul Azwas ya bude baki dakar ya dubi Humaira ya ce, ya ke wannan 'yar sarki, ki sani cewa koda kin sami nasarar hallakani to fa baku isa ku fita daga cikin gidan nan ba a raye, idan ma kum fita har abada burin dayanku ba zai ta6a cika ba. Ke na sani cewa so kike addinin musulinci ya bazu ko ina a duniya ya danne sauran addinai? To ki sani cewa munyi mummunar 6arna a boron kasa, kadan ne daga cikin mutane da aljanu za su baka goyan baya.
Kai kuma sarki Sahibul Hairi kayi sani cewa burinka bazai ta6a cika ba na shahara da daukaka feye da sauran sarakunan duniya face ka auri wadannan 'yan mata uku da aka yi maka da aka yi mka bayanin su tun da farko. Idan kuwa kana tare da wannan ma 'abociyar addinin musulincin har abada bazaka ta6a haduwa da wadannan 'yammata ba koda kuwa ka kai Alfila wajan mahaifinta ya tai maka maka ku tafi neman 'yan matan. Shawarar da zan baka ita ce duk yadda zakai kayi ka rabu da ita domin burinka ya cika, ina ba haka ba kuqa duk wahalar da ka sha a baya zata zamo ta banza.
Koda gama fadin haka sai Humaira ta fusata ta sake take wuyan Shamzabul Azwas ya ci gada da kakarin mutuwa. Kafin cikar dakika dari ya daina motse, komai na jikinsa ya sandare.
Faruwar hakan ke da wuya sai gidan gaba daya ya fara nutsewa izuwa karkashin kasa.
Cikin tsananin zafin nama Humaira ta goya Alfila ta kama hannun Sarki Sahibul Hairi da Bawa Haluf tana mai kiran sunayan Allah tsarkaka. Kawai sai ji tayi an yi sama da ita, a lokacin da gidan ya ci gaba da nutsewa izuwa cikin kasa.
Hakika abin al'ajabi baya karewa a duniya. Humaira na dauke da su Sarki Sahibul Hairi a cikin iska sai su kaji an tsai da su cak! Don haka sai suka kallo kas suna ganin yadda fadar Shamzabul Azwas ke ci gaba da nutsewa izuwa cikin kasa. sai da fadar ta gama nutsewa kaf sannan kasar wajen ta koma ta hade tayi lebur tamkkar wani abu bai ta6a faruwa ba a wajen.
A sannan ne su Humaira suka ji an sakko da su kas a hankali sun dire bisa turba. Nan take Humaira ta yi wa Allah godiya bisa wannan tai mako da ya bata ta sami nasara akan azzalumi Shamzabul Azwas wanda ya dade yana cutar da musulmi a doran kasa. Bayan ta kammala wannan godiya ga Allah sai ta juya ta dubi Sarki Sahibul Hairi, da Bawa Haluf da yarinya Alfila ta ce, "to yanzu ku ganau ne ba hiyau ba, hakika kunga iko da isa irin na Ubangijina bisa yadda ya bani gagarumin karfi na hallaka boka Shamzabul Azwas, kuma sannan ya tserar da rayuwarmu daga cikin fadarsa.
Wannan ya isa hujja a gareku wacce za ta sa kuyi imani cewa babu wani sarki da ya cann canta a bauta masa face Ubangijin Musulinci kuma shi ne kadai mai yin dud abin da ya so. Arziki da Talauci duk nasa ne. Rayuwa da mutuwa na hannunsa, shi ne mai mayar da sarki ya zama bawa, kuma ya daukaka bawa ya zama sarki. Idan har kun gamsu da bayanina ina son a yanzu take ku kar6i addinina mai daraja.
Koda jin wannan batu sai hankalin Sarki Sahibul Hairi ya dugunzuma ainun yana tunowa da wasiyar da Boka Shamzabul Azwas ya yi masa kafin Humaira ta hallakashi cewar muddin yana tare da Humaira har adaba burinsa ba zai cika ba.
Sarki Sahibul Hairi da Bawa Haluf da Yarinya Alfila suka kurawa Humaira idanu aka rasa wanda zai ce da ita kala. Koda ganin haka sai Humaira tayi murmushi sannan ta dubi Sarki Sahibul Hairi ta ce, "ya kai wannan sarki mai babban buri, kayi sani cewa musannan sabo da kai na baro kasata na yia wannan tafiya bisa umarnin mahaifina dan na sanyaka bisa tafarkin gaskiya, don ha lallai sai ka ce wani abu a yanzu in a haka ba kuwa zan datse maka dukkan shirinka bisa neman biyana bukatarka".
Lokacin da Humaira tazo nan a zancenta sai sarki Sahibul Hairi ya yi ajiyar zuciya gami da gyaran murya sannan ya dubeta ya ce, "ya ke wannan jaruma mai abin mamaki, kiyi sani cewa hakika akwai dumbin abin al'ajabi a cikin lamarun Ubangijinki, to amma duk da haka ina bukatar dan lokaci ka domin na yanke hukunci a cikin zuciyata. Ina son son ki bani dama mu isa birnin su Alfila domin in dankata a hannun mahaifinta. Na yi miki alkawari lallai a sannan ne zan kar6i addininki. To amma wane alkawari za ki yi mini cewa nima nawa burin zai ciki?.
Sa'adda Gimbya Humaira taji wannan tambaya sai tayi murmushi ta ce, "ya kai wannan sarki kayi sani cewa, duniya, mulki da mata da kake son ka mallaka fiye da kowa ba komai bane a wajen Ubangijin musulinci, domin da ya so zai iya baka kamarsu cikin duniya sau ba adadi domin da duniyar da duk abin da ke cikinta da wanda ke wajanta shi ke da ikonsa.
Na yarda na amince da duk sharadin da ka zo dashi, kuma kuma zan yi hakuri mu isa har garin su Alfila. Ina mai sanar maka da cewa ko a yanzu ka kar6i addini musulinci to zamu roki Ubangijin musulunci da ya cika maka birinka cikin gaggawa ba tare da ka sha wata wahala ba.
Ina gargadarka da kada ka dauki Shawarar wannan fandararran Boka Shamzabul Azwas gafalalle, domin bazata kai ka ko ina ba face izuwa ga halaka. Lallai kayi tunani kuma kayi hattara. Ka sani cewa tsalle daya mutun yake ya fada rijiya."koda gama wannan jawabi sai Gimbiya Humaira ta juya baya ta ci gaba da tafiya tana mai cewa, "ku biyoni mu tafi, domin akwai dogon zango a gabanmu".
Ba tare da gardamar ko mai ba kuwa su ukun suka bita a baya suka nufi inda suke tsammanin cewa za su ga aljanin da yya kawosu wannan wuri.
Wannan shi ne abin da ya faru ga su Sarki Sahibul Hairi bayan san sami nasarar shiga fadar Boka Shamzabul Azwas sun hallakashu kuma sun dauko yarinya Alfila.
.
Zan dakata a nan saikuma Allah yakaimu gobe zamu cigaba
Admin
AA Misau Ke Magana
[6/5, 8:54 PM] ρяσυ∂ℓу мє∂ι¢αℓ яє¢σя∂: SARKIN SARAKAIA
Littafi Na Huɗu (4)
Part B.
.
Marubucin Littafin
Abdul Aziz sani M/Gini
AA Misau Ke Magana
.
Labari ya isowa AA Misau cewa
A CAN BIRNIN MISRA KUWA, LOKACIN DA SU WAZIRI SUKA ISA WAJAN ABINDOGARONSU kuwa, wato boka suka sanar da shi duk irin abin da ya faru tsakaninsu da dokin Aminul Has sai ya cika da tsananin mamaki yai shiru ya shiga tunani.
Daga can kawai sai ya runtse idanunsa ya shiga karanta wadansu dalasiman tsafi. Yana cikin haka ne awani irin turaren hayaki ya fara fitowa ta ckin kunnuwansa, nana take ya kwala ihu ya daina karanta dalasiman tsafin. Al'amarin da ya mutukar furgita su Waziri ke nan su kaji kamar su tashi su ruga da gudu amma sai suka yi ta maza.
A sannan ne bokan ya dubi Waziri ya ce, "ya shugabana ai babu yadda za a yi ka sami nasarar hallaka Aminul Has face anyi abu guda. Dole ne ka tura a sato awannan takalmi da yake sanyawa kullum a kafarsa wanda ko barci zai yi baya cireshi, sannan a sato tsohuwar Alkebbassa wadda ya ke sawa kullum a jikinsa da kuma sanda da yake dogarawa kullum.
Ku sani cewa irin sihirin da yake jikin wannan Doki nasa da ya gagareku kamuwa shi ne a jokin wadannan abubuwan uku nasa. Da zarar kun sani nasarar rabashi da wadannan abubuwa uku tolallai zaku iya hallakashi a kowane lokaci".
Sa'adda su Waziri suka gama jin wannan jawabi sai Hanlalinsu ya dugunzuma suka rasa abin da ke musu dadi domin sun san cewa sato wadannan abubuwa uku dai-dai yake da tafiya ne man jiki mai kaho tun da de dare da rana sarki Aminul Has na tare da su sannan kuma akwai kyakkyawan tsaro na dakaru a cikin gidan sarautar don haka basu san yadda za a yi ba a shiga har cikin turakar Aminul Has a sato abubuwan uku.
Bayan su Waziri sun yi nazarin maganar boka sun yi tunani akan al'amarin sai dukkaninsu suka rasa abin cewa. Daga can sai Waziri ya dubi bola ya ce, "ya kai abin dogaranmu kayi sani cewa mu kammu ba mu ga mahalukin da zai iya sato wadannan abubuwa uku ba sabo da haka wannnan bukata tafi karfimmu sai dai mu hakura gaba daya, in ya so mu yi hijira mu bar garin domin ba zamu iya ci gaba da zama ba muna ganin abin takaici".
Ya yin da boka yaji wannan batu sai ya bushe da dariya. Al'amarin da ya baiwa su Waziri mamaki ke nan. Daga can kuma sai bokan ya hada rai ya ce, "ya ku wadannan sarakai kuyi sani cewa akwai mani shahararran kungurmin 6arawo a birnin kisra wanda zai iya wannan aiki ana kiransa da suna Baruzul Damsus.
Ina tabbatar muku da cewa wannan 6arawon yana da karfin Sihiri mutuka kuma a halin yanzu duk duniya babu wani 6arawo da da ya fishi kwarewa da sa'a kan sata, domin yafi shekaru arba'in yana sata amma ko sau daya bai ta6a haduwa ba da 6acin rana ko rashin sa'a.
Ina mai shawartarku da ku gaggauta zuwa can Birnin Kisra ku gana da wannan 6arawo. Amma ku tabbata kun tafi da Durhami mai ya wan gaske, domin aikinsa na da mutukar tsada, idan attajiri bai bunkasa ba farat! Daya yake talautashi. Asalin Baruzul Damsus baya harka da kananan Attajirai da kananan sarakai sai wandanda suka gawurta a duniya".
Lokacin da Boka ya zo nan a zancensa sai Waziri ya bushe da dariyar farin ciki ya ce, "ai wannan abu ne mai sauki, domin idan so yake na shimfida Durhami a ko ina a cikin 8irni Kisra ya zamo abin takawar jama'a zan iya yin hakan".
Nan take Waziri ya yiwa boka sallama sannan ya kawo zinare guda dari ya bashi suka tafi suka barshi.
Kashegari kuwa tun da duku-dukun safiya Waziri tare da magoya bayansa mutum biyu suka ya shirin kama hanya suka nufi birnin Kisra
Lokacin da suka isa birnin suna tambayar gidan 6arawo Baruzul Damsus aka sa su akan hanya domin gidan ba 6oyayye bane amma a karshen gari yake. Tafiyar rabin sa'a suka yi kacal suka isa kofar gidan. Da zuwa sai suka iske gaba daya kofofin gidan a bude suke kuma babu masu gadi a kofar gidan, sannan duk inda suka duba basa ganin komai face buhunhuna cike da lu'u-lu'u, da zinare, jahurma da sauransu. Kai har a kasa ma an zubar da wannan dukiya ga ta nan birjik! Ga ta nan birjik ba adadi sai mutun ya takata da kafafuwansa sannan zai iya shiga gidan. Al'amarin da ya baiwa su Waziri mamaki ke nan suka tambayi kansu a cikin zuciyoyinsu cewa Baruzul Damsus ba ya tsoran wasu 6arayin su zo su yashe shi ne? Amsar da suka baiwa kansu ita ce, "ai kura ta san gidan mai babbar sanda."
Nan dai su Waziri suka ja linzamin dawakansu suka tsaya cak! A kofar gidan kamar masu jiran a basu umarni. Kwatsam! Sai suka ji an bushe da mahaukaciyar dariya amma kuma ba su ga mai yin dariyar ba. Daga can kuma sai aka daina yin dariyar aka ce, "lale marhaban da manyan sarakai daga birnin Misra, ku yi sani cewa na dade ina jiran wannan rana da zaku kawo mini wannan babbar ziyara sabo da haka ku manyan baki ne masu mutukar mahimmanci a gareni.
Na umarceku da ku shiga gidan nawa, domin mu gana".
Koda ji wannan batu sai farin ciki ya lullube su Waziri suka sauko daga kan dawakansu suka dauresu, sanna suka kunna kai izuwa cikin gidan. Sai da suka yi 'yar doguwar tafiya sannan suka isa wata kasaitacciyar fada ta gaban kwatance wadda ko fadar sarkin birnin Kisran bata kai ta ba a kyau da tsaruwa. Kuyangi da barori na tai kawo a cikin fadar suna ta hidima. Can kuma ga wani mutunnan zaune akan wata kasaitacciyar karagar mulki ta kasita 6arawo Baruzul Damsus ne fuskarsa cike da annuri, a gabansa an ajiye wani tebur cikie da kayan abinci da na sha iri-iri.
Koda shi gowar su Waziri sai Baruzul Damsus ya mike tsaye da kansa ya tarbesu yana mai rungume Waziri cikin mutukar farin ciki kamar wanda ya ga babban amininsa, bayan dan lokaci sai ya janye jikinsa daga cikin na Waziri, sannan ya jasu inda karagar mulkin tasa take ya zaunar da su kuma ya yi musu tayi abincin da ke gabansu. Ba tare da gardamar komai ba suka hau kintsawa har sai da suka ji sun gamsu amma basu cinye kaso daya ba cikin kaso goma na abincin da ke gabansu. 
Lokacin da 6arawo Baruzul Damsus ya ga su Waziri sun sami nutsuwa sai yai gyaran murya sannan ya dubi Waziri ya ce, "na san cewa baku zo gareni domin komai ba sai domin na yi muku gagarumin aiki na sato takalmi da Alkebba da sanda na Sarki Aminul Has, ko ba haka bane? 
Cikin tsananin mamaki duk su ukun suka bude baki suka ce, "tabbas maganarka dutse ce".
Damsus ya yi murmushi sannan ya ce, "hakika wannan aiki da kuka zo min dashi na san dashi fiye da shekara goma baya kuma na san cewa duk ranar da Sarki Sahibul Hairi ya bar ksarsa za ku zo gareni, domin aikin, inaso ku sani cewa wannan aikin yana da mutukar hadari, dole ne cikin biyu ayi daya. Ko dai ayi nasara ko dai na rasa rayuwata. Lallai zanyu wannan aiki, amma bisa sharadi guda.
Shadin kuwa shi ne, idan har na sami nasara kammala aikin da zarar kun hau kan karagar mulki zaku raba dukiyar birnin Misra kaf biyu ku bani kaso guda. Wannan shi ne babban burina a duniya."
Koda jin haka sai su Waziri suka yi tsuru-tsuru da idanu suka cika da tsananin mamaki. 
Daga can sai waziri yayi ajiyar zuciya ya ce, "ya kai wannan kungurmin 6arawo, kayi sani cewa kazo mana da babban al'amari sabo da haka akwai bukatar muyi shawara."
Koda jin haka sai Baruzul Damsus ya yi murmushi ya ce, "na baku kwana biyu kuyi shawara. Yanzu zan sa a kaiku masaukinku dan ku huta sosai".
Gama fadin haka ke da wuya sai Damsus ya kira wata kuyanga ya umarceta da ta kai su Waziri masauki.
Nan take su Waziri suka mike tsaye suka wanke hannayansu da ruwa sakamakon abincin da suka ci. Sannan suka bi bayan kuyangar izuwa masauki.
Da shigarsu cikin wannan katon daki wanda aka kawatashi da gadaje da shinfidu na alfarma sai suka cika da tsananin mamaki, suka tabbatar da cewa ba a cikin karamar daula suke ba.
Cikin su6utar baki daya daga cikin su ya ce, "hakika kai gidannan ba karamin attajiri bane. Ai ko a gidan sarautar birnin Hindu bana jin akwai dakin da yakawatu kamar wannan".
Koda jin wannan batu sai kuyangar tai murmushi ta ce, "ai in ba dan matarsa ta ci amanarsa ba ta gudu da rabin dukiyarsa da sai in ce da ku bana tsammaninza a sami wani mutun guda daya mai karfin arziki tamkarsa a duniya".
Koda jin wannan batu sai Waziri ya dubi kuyangar cikin kaduwa ya ce, "ya ke wannan kuyanga mai zai hana ki zauna ki bamu wannan labari yadda akayi har matar Baruzul Damsus ta yaudareshi ta sace rabin dukiyarsa alhalin yana kan matsayin sarkin 6arayi na duniya mai karfin sihirin tsafi?"
Kuyangar ta sake murmushi a karo na biyu ta ce, "hakika kuna wasa da kaidi irin namu na mata, domin inda ka ji kaidin da matar Baruzul Damsus ta kulla ta sami nasarar sace dukiyar kuma ta tsira da ita da kun sallamawa mata.
Ku yi sani cewa dokace babba akan duk hadiman gidan nan na baku wannan labari, domin labarin ya kunshi sirrin Baruzul Damsus. Wata kila nan gana bayan bukatarku ta biya shi da kansa ya iya baku labarin da bakinsa.
Da wannan furuci nake yi muku sallama, ku huta lafiya".
Koda fadin haka sai kuyangar ta juya ta fita daga cikin dakin, ta janyo musu kofa ta rufe.
Nan da nan kuwannansu ya hau kan gado guda suka bararraje suna more lahinsa da ni'imarsa domin su yi barci. Amma sai barcin ya gagara, domin hirace ta sarke a tsakaninsu.
Da farko dai Waziri ne ya dubesu ya ce, "hakoka duniyar nan da fadi take, kuma abin cikinta yawa gareshi. Ni kam na fuskanci cewa in dai da rai da nuntashi to har abada buri ba zai yi karshe ba.
Ku tsaya kuyi tunanin irin dukiyar da wannan 6arawo ya tara ku dubi irin daular da yake ciki, amma duk basu ishe shi ba yana hankoran ya sami wata. Wai shin me zai yi da dukiya ne? Gashi dai bashi da mata a yanzu, kuma bashi da 'ya'ya, shin baya tunanin cewa komai dadewa sai mutuwa ta riskeshi. A yau idan ya fadi ya mutu waye zai gaji gidan da dukiyar da ke cikinsa?".
Sa'adda Waziri ya zo nan a zancensa sai ya ran nasa biyu guda biya sai suka yi ajiyar zuciya. Daya daga ciki mai suna shumar ya ce, "ya shugabana ai baka san sirrin da ke zuciyarsa ba, sabo da haka bai kamata kayi mana wannan tambaya ba. Tabbas akwai wani abun da yake shiryawa rayuwarsa da dukiyarsa.
Itkanta wannan rabin dukiya ta birninmu da yake son ya mallaka akwai wani burin da yake son ya cika da ita. Ni dai kawai abinda ya daure min i kai da al'amarinsa shi ne batun matarsa wadda ta shammaceshi ta gudu da rabin dukiyarsa".
Koda jin wannan batu sai Waziri ya yi murmushi ya ce, "ai inda ka san matsayin kaidin mata a duniya da baka fadi haka ba. Ina tabbatr maka da cewa duk wani tashin hankali da ke faruwa a duniya babu mai haddasa shi face mata. Idan mata suka so za ai zaman lafiya, idan kuma basu so ba sai dai ayi ta tashin hankali.
Shin ka ta6a jin labarin sarkin Rum shi ne mutumin da yake kaunar 'yarsa fiye da kansa, wanda a sabo da haka ya shiga duniya neman wadansu gagaruman abubuwa don ta daukaka a duniya, ya yin da matansa suka dauki aniyar ruguza wannan shiri nasa tare da kawar da yarinyar daga doron kasa?".
Waziri ya ce, "ai kuwa ban ta6a jin wannan labarin ba, kuma zan so in ji shi".
Sumar yai murmushi ya ce, "ai kuwa labarin yana rubuce a cikin wani littafi wai shi DAKAKKIYAR ZUCIYA amma zan datsi labarin ne na ci maka gaba soda yawansa.
"Sarkin Rum ya co gaba da keta gudu a cikin daji tamkar bazai tsaya ba har duhun dare ya fara shigowa. Bisa sole ya ja linzamin dokinsa ya tsaya, ba don ya gajo ba, kuma ba don ya so ba face sai domin dokinsa ya dan huta ya yi kiwo, shima ya ci daga guzurinsa, ya sha ruwa, ya dan kishingida yana hutawa. Bayan kimanin sa'a data ya tashi ya ci gaba da tafiya.
Bayan ya shafe tsawon sati guda yana tafiya a cikin mugwayan dazuzzukan da ke nahiyar ba tare da ya sake haduwa da wani mugun abu ba tun daga muyagun arnan dajin nan masu karfin sihiri da suka kwabza azababban yaki da su, face namun daji wadanda ko damuwa da su baiyi ba, domin ya raina jarumtakarsu. Amma a zuciyarsa yana fata ya sake haduwa da wani mugun abun wanda yafi arnan dajin, domin shi yana ganin a haka zai ci gaba da baiwa kansa horon yaki da miyagun abubuwan da suke cikin wadannan dazuzzuka.
Yana tsaka da tafiya sai ya zo bakin wata sahara mai tsananin zafi da nisan tsiya, ko ina ka kai dubawarka saharace, ba za ka ta6a hango karshenta ba. Kuma sau tari zazzafar iska kan buso daga cikin saharar ta yanyame sagarar sai ka daina ganin komai, wanda ko wacce halitta indai tana wajen.
Sa'adda ya zo dai-dai bakin saharar ne, ba tare da wata shawara ba, ko kuma tunanin abin da zai biyo baya ba, ya banna kansa kawai cikin saharar ya fara tafiya tinkis-tinkis bisa dokinsa yana kallon gefe da gefensa. Bai yi nisa da fara tafiya ba wata kishirwa mai tsanani ta soma addabassa, dan haka ya dakko silkassa ta ruwa ya kafa a bakinsa ya shanye ruwan cikinta. Koda ya sake ci gaba da tafiya sai ya sake jin wata kishirwar wadda ta fi ta farko a karo na biyu. Ya sake dakko silkar ruwan nasa ya sha ruwa. A takaice dai bai yi nisa da tafiya a cikin saharar ba ya shanye gaba daya ruwan guzurinsa. Haka ma dokinsa ya gaza tafiya a cikin saharar. A fusace ya tsaya cak, ya dire daga kan dokin, kafarsa ta nutse a cikin saharar, wata kura ta tashi.
A dai-dai lokacin ya ji wata kakkarfar iska a saman kansa. A nutse ya daga kansa ba tare da fargaba ba. Wani jibgegen mummunan aljani ya gani mai suffar mikiya ya yi masa rumfa.
Fuskar aljanin irin ta biri ce, wadda take dauke da wani ta6a66an hanci, tare da katon baki masu dauke da manya-manyan hakora kamar kashin guiwa. Haka idanunsa jajawur kamar wuta ce ke ruri a cikinsu. Haka kuma fuskar duk a dabai baye take da wani bakin gashi. Kan aljanin dan karami ne kamar na karamin biri, sai dai akwau wadansu kahuhhuna guda hudu a jere akai. Yana da manya-manyan fuka-fukai guda takwas.
Aljanin ya tsuke fuka-fukansa ya dire kasa. Wani tsamurraran dattijo wanda a kalla ya yi rubda ciki akan shekaru dari biyu da 'yan kai ya sauko daga kan tsauntsun tamkar ya sauka daga kan doki, yana fadada mummunar fuskarsa da wani kodaddan murmushi wanda shi a ganinsa shi ne murmushin kure adaka, murmushin da ba kowa zai iya yiwa irinsa ba. Abin da bai sani ba da ya yi irin wannan murmushin gwara ya fashe da kuka, domin da kuka da murmushin basu da maraba, musamman ganin yadda fatar kumatunsa ta tatta6e tamkar ana nannade Tabarmar karauni.
Jarumin sarkin baiyi wani yunkurin komai ba balle ta kai da ya yi shirin ko ta kwana, ya dai kurawa halattar tsamurarran tsohon yana dubansa, yana jiran ya karaso gareshi dan jin da wacce ya zo.
Ya yin da tsohon ya kusanto gareshi, sai ya ce da shi da muryarsa da take satar kwaikwayo da kukan dan marakin saniya.
" An gai da mai shirin zama gwarzo. Na zo na taimaka maka a wajen cimma burin rayuwar ka."
"bana bukatar temakonka. ! Ka yi gaggawar 6ace mini da gano!!" ya yi mai tsawa a fusace yana da karkarfar murya yana nunashi da dan yatsa.
"Ba a sannu dan samari. Ba'a yi min tsawa kuma ba'a nunani da hannu. Idan na fadi magana ta zauna, dole a amince da ita. Kuma kaima dole ka kar6i taimakona."
Tsohon ya ce dashi da karkarfar murya.
"karyarka tasha karya gafalallan banza! Baka isa ba, ba ka kai matsayin da zaka tai maka min bz. Kai! Ba ai wani da namiji ba, akan burin rayuwata. Zan iya sada zai iya sada kuntuwar rayuwarka da ajalinta mutukar baka 6ace mini da gano ba." A fusace yake gaya masa maganar cikin kunfar baki.
Ya tuntsure da wata karkarfar tsawa. 
"Lallai yaro baia san wuta ba sai ya taka! Na san baka san koni waye ba shi yasa kake gaya min gafalallun maganganunka kai tsaye ba tare da fargaba ko sha yi ba. Dan haka zan yi maka afuwa, na san kayi ne bisa kuskure."
"Bana bukatar a tarihina ace wani ya yi min afuwa bisa wani kuskure da na yi masa, zan bukaci ya dauki fansa mutukar zai iya. Ka sani cewa na girmi in yaki karkarfan sadauki shi kadai, balle gafalallan tsoho da jikinsa ya gama kasalantuwa, babu kuzari da karfin jiki a tare da shi. Sadaukantakata ta girmi in kai hannu jikinka da nufin yaki. Dan haka kaje ga wani sarki ka nemi alfarmagareshi ya ara maka gayyar rundunonin yaki a kalla mutum sama da dubu daya ku taho gareni tare da gyara a kai, anan ne na san zan iya sauraronka da nufin yaki.
Yana gama maganganunsa ya haye dokinsa, ya yi gaba ba tare da ya dubi tsohon ba. Taku daya, biyu uku, ya yi ya ga tsohon a gabansa yana masa murmushin mugunta ya ce, "Dan samari na girmi tunaninkagigin yarinta ya daina dibanka ga furta gafalallun furci ga maigidanka. Koda ka ganni tsoho ka yi tunani ka fini tsagwaran sadaukantaka ko jarumtaka. Ka daina tunanin kana karar da adadin ragwaye har kana tutiya da alfahariba maza a gabanka, ba za ka yaki mutun daya ba sai mutun dubu. Da sannu zan nuna maka yadda tsoho yake dakawa karamin sadauki gumba a hannu, ya sanya shi yin dana sanin zuwa duniya, ya sanya shi yin ihun azaba.
Ko kallonsa bai yi ba, ya kada kan dokinsa ya ratse shi zai wuce. Ya ce da shi, "Ba zan yarda da ka cika kai cikakaen ne ba sai kazo da adadin runduna da na gaya maka, su doraka a matsayin gyara, in ya so a nan sai ka nina min ko kai waye".
Kai yaro ne. Ban zo gareka da nufin na yake ka ko na hallakar da kai ba, na zo ne domin na taimaka maka bisa abinda ba zaka iya ta6awa iyawa ba mutukar ban taimaka maka ba. Domin miliyoyonka sun gaza. Amma kafin nan zan nuna maka matsyina da na kai. Na shallake tunaninka da hangenka. Idan ka saduda zan baiyana gareka na sanar da kai sunana da irin taimakon da zan yi maka."
Ba tare da ya ko kalleshi ba ya kada ya yi gaba tsohon ya bishi da kallo cikin murmushin mugunta yana girgiza kai.
Sarki Jurhama ya ci gaba da tafiya ba tare da waigo ba. Ya ma manta da batun wannan tsoho. Saharar da yake tafiya a kanta ta dau zafi sosai, kishirwa ta dameshi daga shi har dokinsa, babu ruwa, kuma babu wani tsiro a kan saharar. Dan haka ya sauka daga kan dokin ya rike linzamin dokin suka kama tafiya a hankali-a hankali.
Can bai ankara ba sai ji ya yi an fincike linzamin dokin daga hannunsa. Ya jiyo bayansa a fusace dan ganin wane mai tsautsayin ne ya aikata wannan babban lefi a gareshi?
Wadansu irin halittu ya ga ni kimanin goma sha biyu masu mutukar girma tamkar tsauni. Sai gani ya yi guda ya jefa dokinsa a baki ya yi masa tauna daya ya hadiye, tamkar dan adama ya sa tsokar nama guda ya lunkuma a bakinsa, haka halittar nan ta dauki dokin ta lamushe.
A dai-dai lokacin ne ya jiyo dariyar wannan tsohon nan da ya bayyana a gareshi dazu. Bayan daukewar dariyar tasa sai ya ce da shi, "ga wani dan abu daga cikin matsayina sai ka zuba ka gani, su kansu nafi karfinsu shiyasa nake sarrafasu, wabda ina da tabbacin kaima sun fi karfinka. Ba ma kai ba, daya daga cikinsu zai iya kifar da kasa a cikin sa'a daya. Don haka a bada homma mai burin zama gwarzo". Ya kima budlshe da dariya, saharar ta kuma amsa amon sautin muryar daryarsa.
Daukewar tasa ta yi dai-dai da surarsa da akai aka gwarashi a jikon wani abu mai kama da tsini. Aka gara gwarashi da tsauni a karo na biyu. Anan yaji numfashinsa ya dauke, bai kuma sanin halin da yake cikin ba.".
Shumar ya bakata a dai-dai nan sakamakon kwankwasa kofar da yaji ana yi. Nan take shumar ya mike yaje ya bude kofar sai ga saikon Harayi Baruzul Damsus ya shigo fuskarsa cike da annuri yana murmushi. Al'amarin da ya mutukar basu mamaki ke nan gaba dayansu.
Baruzul Damsus ya ce, "kuyi hukuri na katse muku hanzari, amma naga kun manta da abin da ya kamata ku fara yi mafi mahimmanci a gareku. Bawani abu bane face yanke shawara bisa sharadin da na gindaya muku akan bukatar da kuke son na biya muku. Ku rabu da baiwa junanku labari ko kuma son jin labarin yadda matata ta ci amanata. Lallai ina son ku yanke wannan shawara a tsakanin yau zuwa gobe domin 6ata lokaci a tsakaninmu na da hadari, saboda nayi bincike na gano cewa saura kwanaki kadan Sarki Sahibul Hairi ya sami nasarar abin da ya tafi nema ya dawo gida. Kun ga kuwa idan kuka yi sakaki har ya dawo baku kawar da Aminul Has ba har abada burinku ba zai cika ba".
Koda gama fadin haka sai Baruzul Damsus ya nufi jikin bango ya shafa shi da hannunsa na hagu. Take bangon ya tsage ya wuce kamar yadda danshi ke tsatstsafowa daga cikin kasa, ya fice fit daga cikin dakin.
Koda ganin haka sai su Waziri suka sake tsorata da al'amarin Baruzul Damsus suka shiga sabon tunani domin sun san cewa abin da ya fada musu gaskiya ne.
Bisa wannan dalili ne daya daga cikinsu cikin tsananin damuwa ya ce, "Ya kai shugabana mene ne abin yi, shi zamu aminta da sharadin Baruzul Damsus ne ko kuwa zamu hakura da bukatar tamu ne gaba daya?."
koda jin wannan tambaya sai Waziri ya yi ajiyar zuciya ya ce, "Ai tun da muka kawo izuwa wannan matsayi ina ganin cewa bamu da wani za6i na Baruzul Damsus
Ku tuna cewa matsoraci baya zama gwani har abada. Haka kuma ita duniya ba'a samunta a banza, shi kuwa nema kugiya ne ba'a san abin da zai janyo ba sai an jarraba. Kawai mu karfafi zukatammu mu mika wuya mu jira muga abin da zai faru".
Gama fadin haka ke da wuya sai farin ciki ya lullu6esu suka ce, "Tabbas mun gamsu da wannan jawabi naka bamu da wani haufi a kansa.
Kashe gari da sassafe bayan su Waziri sun yi kalaci sai Baruzul Damsus ya sa ala sake kai su fadarsa. Da zuwa sai suka iskeshi cikin mutukar farin ciki tamkar wanda ya gama cika burinsa na duniya. Ko zama su Waziri ba su yi ba sai ya dubesu cikin murmushi ya ce, "Na yi murna da naji kun yanke shawara akan cewa kun amince da sharadina sabo da haka na urmarceku da ku kama hanya ku koma birninku na Misra ni kuma zan biyo bayanku zuwa gobe, ina mai tabbatar muku da cewa a cikin kwana uku rak! Zan sato Takalmi, Alkyabba da Sandar Aminul Has na kawo muku. Lallai ku kasance masu cika alkawari a gareni, odan kuwa ku ka sa6a, ina tabbatar muku da cewa dayanku ba zai tsira da rayuwarsa ba. Yanzu sai ku tashi ku yi haramar tafiya na sallameku".
Dajin wannan sai su Waziri suka yi sallama da Baruzul Damsus cikin murna suka fice daga fadar sannan suka hau dawakansu suka durfafi birnin Misra.
¤¤¤¤¤¤
A can birnin Misra kuwa, a ranar da wannan al'amari ya faru ne Aminul Has ya yi wani mummunan mafarki mai ban tsoro.
A cikin mafarkin nasa an nuna masa wani bakin jaki ya take mutum ya kashe shi. Faruwar haka ke da wuya sai jini ya kama zuba daga jikin mutumin ya yi ta kwarara yana jika gonakai. Nan take duk shukar garin ta kone kurmus, sakamakon wannan jinin da ya jika kasa.
Cikin rusa ihu da firgicewa Aminul Has ya farka daga wannan mafarki ya mike zaune zumbur!
Karar da ya yi ne yasa matarsa ta farka, dama tare suke kwance bisa gado a wannan lokaci. Cikin firgici itama ta farka. Koda ta fahimci cewa Aminul Hasa ne ya yi mafarki na ban tsoro sai ta rungumeshi tana shafarsa ta ce, "Ya kai mijina bani labarin irin mafarkin da kayi".
Ba tare da 6oye komai ba Aminul Has ya zaiyane mata duk abin da ya gani a cikon mafarkin nasa.
Koda jin haka sai hankalinta ya dugunzuma ainun, tayi shiru tana tunani da nazari. Daga can sai tai ajiyar zuciya ta daga kai ta dubeshi ta ce, "Ya kai mijina kayi sani cewa kakana ya sanar da ni ilimon fassarar mafarki, tabbas wannan mafarki naka yana nuni da cewa makiyanka suna nan suna dana maka tarkon yadda za su sami nasarar hallakaka.
Wannan bakin jaki da ka gani a cikin mafarkin shi ne makiyinka. Mutumin da ya danne kuma kaine. Wannan jini da ka gani ya malala gonakai ba komai bane face zaluncin makiyanka akan jama'ar gari. Shukoki da ka ga sun kone yana nuna cewa makiyanka za su kwashe duk arzikin wannan birni su tsiyatar da kowa".
Lokacin da matar Aminul Has ta zo nan a jawabinta sai hankalinsa ya dugunzuma fiye da ko yaushe har tausayin jama'a yasa idanunsa suka ciko da kwalla.
Cikin alamun karayar zuciya ya dubeta ya ce, "Ya ke matata kin sani cewa nayi imani da ke dari bisa dari domin in ba don taimakon da kika bani ba da tuni yanzu na dade da mutuwa. Yanzu wacce shawara za ki bani domin na tsira daga muggan tarkon da wadannan makiya nawa suka dana mini, ko don sabo da na ceci rayuwar jama'a da dukiyoyinsu?".
Koda jin wannan magana sai matar Aminul Has tayi shiru tana tunani har izuwa lokaci mai dan tsaho, sannan ta ce da shi, "abin da za a yi shi ne, duk abin da ka ga na yi kada ka tambayeni dalili. Kuma abin da na umarceka da yi ka yi shi kawai koda kuwa cewa na ce ka shiga cikin wuta
Aminul Has ya kyada kai ya ce, "ai ko cewa za ki yi na cakawa kaina wuka a ciki ba zan ki ba".
Daga wannan rana Aminul Has ya zuba ido kuma ya kasa kunne yaji ko matarsa za ta umarceshi da yin wani abu sa6anin wanda ya saba yi kullum ko kuma ita da kanta za ta yi wani abun wanda bata saba yi ba, amma shiru, kamar maye ya ci shirwa har izuwa tsawon kwana uku.
A safiyar kwana na uku ne bayan sarki Aminul Has ya gama shiri tsaf zai tafi fada sai matarsa ta zo gareshi rike da wata katuwar jakar fata. Kawai sai ta mika masa jakar fatar ya kar6i, sannan ta ce da shi, "ya kai mijina kayi sani cewa ba komai bane a cikin wannan jaka ba face takalmi, alkyabba da sanda iri daya sak da wanda ke jikinka yanzu tamkar an tsaga kara babu digon bambanci. Ina son ka tafi da wannan jaka a sirrince, kafin ka isa fada ka sami ka6a66en waje ka 6oye jakar inda babu wanda zai gani. Kada ka taso daga fada sai dare ya soma sannan ka biyo ta inda ka 6oye wannan jaka ka sauya takalminka, alkyabbarka da andarka, ma'ana ka sanya na gaskiyar a jakar ka 6oyesu ka dawo gida sanye da na karyar ka kwana da su a jikinka".
Koda jon wannan umarni sai Aminul Has ya cika da mamaki. Har ya bude baki zai tambayi dalilin bashi wannan umarni sai ya tuno da sharadin da ta kafa masa, sabo da haka sai yai shiru bai ce komai ba ya kar6i jakar kawai ya juya ya tafi.
Kamar yadda matar tasa ta umarceshi ya yi hakan ya yi bai karya ka'ida ba. Wato sarki Aminul Has bai baro fada ba sai da dare ya yi, kuma ya 6oye ta inda ya 6oye wannan jaka ya sauya takalminsa, alkyabbarsa da sandarsa ya nufi gida kai tsaye cikin tsananin tsoro da fargaba. Gani yake a ko yaushe za a iya hallakashi tun da baya tare da abubuwa uku da ya gamsu cewa su ne suka kareshi daga dukkan masifa.
Lokacin da Aminul Has ya shigo cikin turakarsa ya iske matarsa a zaune akan gado tana jiransa, hankalinta a tashe sakamakon ganin cewa ya dade da yawa bai dawo ba.
Koda ta hangoshi sai ta ruga gareshi ta rungumeshi cikim matukar farin ciki, sannan ya sa bakinta dai-dai kunnensa tayi masa magana cikin rada ta ce, "idan mun kwanta muna barci karufe idanun ka kamar kana barcin, amma kada kayi barcin, kuma kanutsu kaji abinda zai faru a jikinka. Kai za ma ka iya byde idanunnka kadan domin ka ga abin da zai faru, amma kada ka kuskura kayi ido biyu da abin da ya shigo".
Koda gama fadin haka sai ta jashi izuwa kan gado suka kwanta. Dama kafin su kwanta din ta kashe fitilun turakar, turakar ya yi duhu dumdum! Ko tafin hannu mutun ba zai iya gani ba. Nan fa suka yi lamo tamkar suna barci har ma jan munsharin karya auke yi.
Bayan kamar rabin sa'a da kwanciyarsu sai suka ji wata irin iska mai sanyi ta buso cikin cikin turakar. Al'amarin da jefa matukar tsoro ke nan a cikin zukatansa. Amma sai sukadaure suka ki su motsa jikinsu.
Cikin mutukar karfin hali sarki Aminul Has ya bude idonsa guda kadan kawai sai ya ga wani abu kamar inuwa ya ratso bango ya shigo cikin turakar ya tsaya dai-dai kansa.
Koda abin ya dafa kafarsa sai yaji takalminsa ya cire, abin ya sake dafa jikinsa da hunnunsa, sai alkyabbarsa ta 6ace, sandarma da yake ruke da ita sai ta 6ace 6at.
Faruwar haka ke da wuya sai itama inuwar ta 6ace 6at! Bayan kamar dakika dari da ashirin sai Aminul Has ya ga matarsa ta mike zumbur! Taje ta kaunna fitilun turakar haske ya gauraye turakar. Sai gashi kuwa Aminul Has bayatare da abubuwa uku a jikinsa.
.
Zan dakata a nan saikuma Allah yakaimu gobe zamu cigaba
Admin
AA Misau Ke Magana
[6/5, 8:55 PM] ρяσυ∂ℓу мє∂ι¢αℓ яє¢σя∂: SARKIN SARAKAI
Littafi Na Hudu (4)
Part C.
.
Marubucin littafin
Abdul Aziz sani M/Gini
AA Misau Ke Magana
.
Labari ya isowa AA Misau cewa
NAN TAKE MATAR
TASA TA BUSHE DA DARIYA SANNAN TA RUNGUMESHI TA CE, "YA KAImijina, kayi sani cewa gobe kana da gagarumin yaki a fada, domin a gobe ne za ka ga makiyinka a fili wadanda suke son su yi maka juyin mulki su hallakaka.
Abin da na ke so da kai shi ne, ka tashi da duku-dukun safiya ka tafi izuwa inda ka boye wannan jaka ka sanya alkyabbar da takalmin, sandar ka wuce kai tsaye izuwa fada. Duk irin sauyin da za ka gani kada ka ji tsoron komai, kaje ka zauna a kan karagar mulkinka."
Koda gama jin wannan batu sai Aminul Has ya sumbaci goshin matarsa ya ce, "madallah da matar da take kaunar mijinta fiye da uwa take son danta. Hakika kina bina bashin da ban san yadda zan iya saka miki ba."
Nan take suka sake kashe fitilun tirakar kamar yadda suka saba kwanciya a kullum, har barci ya kwashe su basu sani ba.
Da asubar fari zakara ya baiwa Aminul Has sa'a ya tashi ya yi wanka ya kintsa, ya sanya tufafinsa wanda ya saba sawaa kullum, sannan ya sulale ya fice daga cikin gidan sarautar ba tare da kowa ya shaida shi ba.
Kai tsaye ya wuce can cikin wani lambu mai yawan dogayan bishiyoyi da dogayan ciyayi masu duhuwam inda ya hoye jakar.
Da shigar Aminul Has lambun sai ya wuce izuwa cikin wata duhuwa ya bankada ya dauko ajiyarsa. Cikim hanzari ya bide jakar ya fiddo da sandarsa, takalminsa da alkyabbarsa. Nan take ya sanya takalminsa da alkyabbarsa sannan ya dogara sandar ya fice da sauri ya nufi fada.
Da zuwan Aminul Has fada sai ya cika da mamaki, domin ya iske kofar cike makil da dakaru, dukkaninsu sun yi shigar yaki ta musamman, sunyi sahu-sahu biyu.
Aka'ida wadannan dakaru basa fitowa sai bayan sarki ya iso, amma yau gashi sun riga sarki fitowa.
Nan fa Aminul Has yaji a jikinsa cewa lallai akwai makarkashiyar da ka killawa amma sai ya dake ya ratsa ta tsakiyar dakarun ya wuce izuwa cikin fadar.
Koda ya yi nazzarin fiskokin dakarun sai ya gane cewa basu bane wadanda suka saba tsayawa ba a bakin kofar, lallai an sauyasu.
Da shigar Aminul Has cikin fadar kuma sai ya ga abin mamaki. Ba komai ya gani ba face Waziri da dukkanin mukarrabansa a tsaitsaye cikin shigar yaki sun yiwa fadar kawanya kimunin su dari daya.
Gaba daya sauran fadawa da barori wadanda suka saba hidima a fadar babu ko mutum daya daga cikinsu.
Da shigar Aminul Has sai aka yi sauri aka rufe gaba daya kofofin fadar ya zamana cewa babu ta inda mutun zai iya fita.
Faruwar hakan ke da wuya sai Waziri da mukarrabansa suka bushe da dariya gaba dayansu suka yi ta kyalkyalawa kamar ba za su daina ba.
A wannan lokaci Aminul Has ya tsaya cak! A tsakiyar fadar yana kallonsu kawai.
Daga can sai suka ga shima ya 6arke da dariyar yana tayasu. Al'amarin da ya sa suka tsuke nasu bakin ke nan suka kura masa idanu, domin da farko sun yi tsammanin ko ya sami ta6in kwakwalwane. 
Aminul Has ya daina dariyar sannan ya dubi Waziri cikin murmushi ya ce, "me kuke nufi dani?".
Koda jin wannan tambaya sai Waziro ya sake bushewa da dariya a karo na biyu domin ya gane cewa Aminul Has ba zautuwa ya yi ba
Waziri ya hada fuska sannan ya nuna Aminul Has da hannu ya ce, "Ya kaia wannan shashashan sarki kayi sani cewa mun gaji da walakancinka na banza da wofi, wanda mataccen sarkinmu ya bar maka domin ka takuremu ka hanamu walwala da jin dadi a cikin mulkinmu. Sabo da haka yanzun za mu yi maka kisan wulakanci na haye karagar mulkinka.
Kayi sani cewa tuntuni mun dade muna ta kokarin halaka ka amma mun kasa sabo da kana tare da abubuwan sihiri guda uku wadanda suke kareka. 
To ka sani cewa a jiya mun sa sarkin 6arayi Baruzul Damsus ya shiga har cikin turakarka ya sace wadannan abubuwa guda uku a jikinka kana barci baka sani ba har ma mun konasu a daren jiya.
Yanzu ta ya za ka iya kare kanka daga mugun kisan da zamu yi maka?".
Sa'adda Aminul Has yaji wannan batu sai yai murmushi, sannan dubi Waziri ya ce, "Shin kai makaho ne ko kuwa mai idanu? Ka dubeni da kyau ka gani, abubuwa ukun nawa da kuka sa aka sace irin su ne sak a tare da ni yanzu ko basu bane? Ga sandar a hannuna, da alkyabbata a jikina, kuma ga takalmina a kafata!
Ina mai sanar da kai cewa kayan da sarkin 6rayi ya sace mini a jiya da daddare ba su bane na gaskiya ba. Tun a jiya na cire na gaskiyar na 6oyesu a can lambuna na wajan gari, yau da duku-dukun safiya naje na daukosu na sanyasu a jikina, sannan na taho fada.
Ina mai tabbatar maka da cewa duk yawan nan naku na banza ne, domin ba za ku oya hallakni ba. Yanzu kun rufe kofofin fadae gaba daya babu wanda zai kawi mini dauki, kuma babu wanda zai kawo muku. Ni da ku kowa karfinsa da sihirinsa ya kwaceshi."
Koda gana fadin haka sai Aminul Has ya gyara tsayuwa ya ruke sandarsa da hannu biyu. 
Cikin tsananin firgita da taurin rai Waziri ya dakawa dakarunsa tsawa ya ce, "Su afkawa Aminul Has su yi gutsun-gutsun da sassan jikinsa".
Nan take kuwa dakarun suka yi ca! A kansa tamkar an ajiye kwayar dawa a tsakiyar gidan tururuwa.
Nan fa fadar ta hargitse da ihu mazaje, karafkiyar karafa, domin Aminul Has ya zamo tamkar shaidani a cikinsu. Duk inda ya kai duka da sandar hannunsa sai ka ga ya bazar da sama da dakaru biyar. Kuma take suke zama gawa ko shurawa basa yi.
Shi kuwa idan suka sari jikinsa sai kaji kara kal! Tamkar sun sari dutse. Wani lokacin idan suka yi masa rubdugu suka lullu6eshi suka danneshi kasa da ya yunkura sai ka ga ya taso sama ya tarwatsasu tamjar an jenyesu da kugiyoyi.
Koda dakarun suka ga Aminul Has baya jin sara da suka kuma sai bankesu yake tayi suna ta mutuwa, sai suka fara rugawa da gudu izuwa bakin kofofin fadar da nufin su bude su gudu.
Koda Aminul Has ya fahimci hakan sai ya kwaci kwari da baka a hannun wani Badakare ya rinka harbo wadanda suka ruga jikin kofofin suna fadowa kasa matattu.
Babu abinda zai baiwa mutun mamaki face irin tsananin zafin naman da Aminul Has ke amfani da shi wajen harbo dakarun, domin a cikin dakika biyu yana iya dana kibiyoyi arba'in cikin bakansa ya harbe mutum arba'in din.
Kafin a jima Aminul Has ya kashe sama da rabin Dakarun da ke cikin fadar.
Koda ganin wannan al'amari, sai cikin Waziri ya duri ruwa suka fara tunanin hanyar da za su bi su tsira da rayuwarsu.
Abin da ya fara fado musu a rai shi ne suma su shmmaci Aminul Has su ruga su bude kofa su fita. Amma kuma samun nasarar yin hakan abu ne mai hadari, domin zafin naman Aminul Has ya wuce tunaninsu.
A wannan lokaci Waziri da manyan mukarrabansa sun 6oye ne a bayan karagar mulkin.
Nan fa suka fara tattaunawa a tsakaninsu. Waziri ya dubi mukarraban nasa ya ce, "Hakika bokanmu ya yaudaremu kuma ya cucemu, ashe bai samu ikon sato ababan dogaron Aminul Has ba?".
Koda jin haka sai galadima ya ce, "ai ba yauda rarmu ya yi ba, shima an shammace shi ne. Ni kam a tawa shawarar kada mu ce zamu yi yunkurin gudu, kawai mu fito mu yakeshi da iyakar karfimmu da dai mu mutu ragwaye ai gwara mu mutu mazaje.
Ina tabbatar muku da cewa a yau dai dayanmu ba zai tsira da rayuwarsa ba.
Don haka dukkamu burinmu da shirinmu ya rushe, kawai mu fita mu yi kundumbala mu tari kaddararmu".
Koda jin wannan batu sai hawayen takaici da bakin ciki ya su6uto daga cikin idanun Waziri, kawai sai ya kurma ihu ya mike tsaye sannan ya zare takobinsa ya ruga izuwa kan Aminul Has. Koda Aminul Has ya hango Waziri ya durfafoshi gadan-gadan da mugun nufi, sai Aminul Has ya daka tsalle sama ya kai masa wawan duka da sandar aka. Take kan Waziri ya rabe goda biyu tamkar an 6are gyada, ya sulale kasa matacce.
Koda ragowr mukarrabansa suka ga abin da ya faru akan shugabansu, sai suka kara firgicewa, suka kasa fitowa dga bayan karagar har dai Aminul Has ya gama kashe dukkunin dakarun dake cikin fadar.
Lokacin da ake ta wannan gumurzu a cikin fadar, jara'ar gari sun yi cincirindo a kofar fada suna ta jiyo ihun daharu a ciki, gashikuma kofa a rufe take an ki budewa.
Al'amarin da ya tabbatar da cewa lallai akwai makarkashiyar da ake shiryawa a kan harkokin mulki.
Da yawa daga cikin jama'ar gari sai suka yi tsammmanin cewa ana ta kashe dakarun sarki Aminul Has ne makusanta a gareshi da kuma shi kansa Aminul Has din.
Abin da basu sani ba shi ne, kishiyar hakan ce take faruwa.
Bayan Aminul Has ya gama kashe dukkanin dakarun da ke cikin fadar ya zamana cewa duk inda ka duba ba abin da za ka gani face gawarwakin dakarun da kuma jinimale-male a kasa sai ya dubi 6angaren da kargar milki take ya ce, "ya ku makarraban Waziri, ku fito daga ma6oyarku ku yi mubaya'a gareni ku nemi gafara, idan har kuka yi alkawarin cewa ba za ku sake ha'intata ba ni kuwa zan yi muku rai, kuma na barku a cikin majalisata."
Koda jin wannan batu sai mukarraban Waziri sukai tsuru-tsuru suka kasa fitowa sabo da tsoro. Tunaninsu shi ne, suma zargin cewa Aminul Has so yake ya yaudaresu.
Cikim rada daya daga cikinsu ya ce, "mu amince da tayin Aminul Has, akwai abin da na shirya a zuciyata".
Koda jin haka sai gaba dayansu suka fito daga ma6oyar tasu suka nufi inda Aminul Has yake suka durkusa a gabansa.
Kawai sai suka kama tuba suna neaman gafara, harma suna kuka suna cewa, "ai Waziri ne ya yi musu dole suka bashi hadin kai".
Ya yin da Aminul yaga yadda suka marairaice sai tausayinsu ya kamashi ya ce da su, "su mike tsaye ya yafe musu."
Su duka suka mike tsaye suka kama murna da godiya. Aminul Has ya juya da baya ya nufi babbar kofa ta shigowa fadar da nufin ya budeta.
Cikin shammata daya daga cikinsu ya dauki mashi a kasa ya duge sandar da ke hannun Aminul Has ta fadi kasa can gefe daya. 
Koda ganin haka sai su duka suka afkawa Aminul Has da nufin su hallakashi, domin a zatansu idan daya tare da wannan sanda ta hannunsa ba zai iya tsinana komai ba.
Nan fa suka rufeshi da rubdugun sara da suka, har suka saishi kasa. Sai dai ko kadan makaman nasu basu yi tasiri a jikinsa ba, don fatar jikinsa ko kwarzanewa bata yi ba bare ya sami babban rauni.
Cikin tsananin fusata Aminul Has ya yunkura ya taso sama ya watsar da su su duka suka zube kasa, kafin su yunkura su sake afka masa tuni ya hausu da naushi da bugi hannu da kafa. Duk wanda ya yiwa naushi daya a fuska sai ka ga jini na tsartuwa a hancinsa da bakinsa, kuma nan take ya fadi kasa matacce, sabo da karfin naushin ya wuce misali.
Kafin cikin dakika dari da ashirin babu dayansu a tsaye ko a zaune rayayye.
Sarki Aminul Has ya tsaya cak! Ya dubi dukkanin gawarwakin da ke kwance a cikin fadar, ya ga cewa shi kadai ne fa ya kashe su sai takaici da bakin ciki ya lullu6eshi. Nan take idanunsa suka ciko da kwalla, ya fara zubar da hawaye.
Cikin sanyin jiki ya karasa bakin kofar fadar ya budeta da hannu daya alhalin sai karti Arba'in sun taru suke iya budeta.
Koda kofar ta wangame mutanan gari suka yi arba da sarki Aminul Has suka ga shi kadai ne a raye a cikin fadar si suka rude da shewa da jinjina. Suka hau yi masa kirari.
Aminul Has ya gadawa jama'a hannu suka yi tsit! Sannan ya ce, "ya ku jama'ar birnin Misra, ku yi sani cewa wadannan da na salwantar bada son raina ba ne, domin su ne wadanda suke son su kawar da mulkin Adalcin da ake yi muku su shimfida na zalumci. Ni kuwa na yiwa sarki Sahibul Hairi Alkawari cewa zan ci gaba da tafiyar da mulki kamar yadda ya saba tafiyar da shi, kuma zan tsare rayukan talakawa da dukiyoyinsu. Ina fata za ku gafarcene bisa wannan rayuka da na salwantar, domin da yawansu suna da nasaba da wasunku."
Koda jin wannan sai wani dattijo mafi tsuma a birnin ya matso daf! Da Aminul Has ya ce, "ya shugabana kayi sani cewa wadanda ka kashe ina farin ciki da hakan, domin mutun baya cika na gari face yana kaunar ci gaban Al'umarsa. Hakika muna Alfahari da mutane irinka da irin su sarki Sahibul hairi wadanda suke son talakawa kamar yadda suke son kansu."
Koda tsohon ya zo nan a jawabinsa sai mutane gari suka sake rudewa da shewa suka daga sarki Aminul Has sama suna masu ci gaba da yi masa kirari da jinjina. Duk wannan abu da ke
faruwa Bokan su Waziri na la6e a can gefe daya yana cizon yatsa cikin tsananin takaici da bakin ciki, domin yaga samu yaga rashi.
wannan shine abin da ya faru a birnin Misra bayan Sarki Aminul Has mai ruke da karagar mulki ya sami nasarar kawar da makiyansa.
¤¤¤¤¤¤¤¤
SARKI SAHIBUL HAIRI
Al'amarin su sarki Sahibul Hairi kuwa, lokacin da suka kama tafiya suka iso inda suka bar aljanin da ya kawo su fadar Boka Shamzabul Azwas sai suka iske wajan wayam babu wata haliita mai rai guda daya.
Al'amarin da ya mutukar dugunzuma hankalinsu ke nan suka yi cirko-cirko suna tunanin abin da ya kamata su ya. Daga can sai sarki Sahibul Hairi ya dubi gimbiya Humaira ya ce, "ya ke wannan Basadaukiya, yanzu ina dabara? Ta ya ya zamu yi wannan doguwar tafiya a kasa mu isa can garin su sadauki Awaisu mu kai masa 'yarsa Alfila domin ya yi mana jagora izuwa inda 'yan mata uku suke wadanda zan aura?"
ya yin da gimbiya Humaira taji wannan batu sai tayi murmushi sannan ta sami wuri ta dubi sarki Sahibul Hairi cikin untsuwa ta ce, "ni zan iya rokon Ubangijima ya kaimu can a cikin kwanaki kadan, ti amma yin hajan ba shi da wani amfani".
Koda jin wannan batu sai mamaki ya kama sarki Sahibul Hairi da Bawa Haluf da yarinya Alfila, har ma suka kurawa Humaira idanu.
Sarki Sahibul Hairi ya tambayeta ya ce, "mene ne dalilin da ya sa kika ce bashi da amfani yin hakan?"
Humaira ta sake yin murmushi a karo na biyu ta ce, "ya kai wannan jarumin sarki, ka ga dai da farko da muka zo nan kayi amfani da duk karfin damtsenka da kuma karfin sohirinka wajen shoga gidan nan amma ka kasa. Ni kuwa sai gashi na bide maka kofa da taimakon Ubangijina mun shiga.
Wannan abu da ya faru ya isa ishara a gareka kayi imani da Ubangijina ko ka rabauta, amma baka yi ba.
Bayan mun fafata kazamin yaki da Boka Shamzabul Azwas ya sami nasra a kammu ya tsafancemu muka zama gumaka daga baya kuma muka sake tashi, ni ce na sake yin gumurzu da Shamzabul Azwas har na sami nasarar hallakshi da taimakon Ubangijina. Gashi har na mallaki wannan damara da ke kugunsa.
Wannan abu da ya faru ahima ya isa ishara a gareka akan ka kar6i addinin musulinci, amma har yanzu baja kar6a ba.
Shin akan wanne dalili zan ci gaba da yin tafiyata tare da kai tun da na biyoka ne dama domin na ja hankalinka izuwa mikakkiyar hanyar da babu karkata a cikinta, hasken da babu duhu a cikinsa, tafarkin gaskiya, tafarkin da kau da karya, wato tafarkin addinin musulinci!
Ina tabbatar maka da cewa ni yanzu a nan zan rabu da ku na kama gabana, in ya so kowa tashi ta fishsheshi".
Koda jin wannan batu sai hankalin yarinya Alfila ya dugunzuma ainun, ta faka kuka.
Al'amarin da ya mutukar bawa Humaira da su sarki Sahibul Hairi mamaki ke nan.
Humaira ta durkusa gaban Alfila ta ruke kafunfunta ta shiga rarrashinta tayi shiru, sannan ta tambayeta ta ce, "ya ke Alfila mene ne dalilin da ya sa kike wannankuku?"
Alfila tayi ajiyar zauciya ta ce, "ba wani abu bane yasa kika ga ina wannan kuka ba face na san cewa idan kika tafi kika barni a nan su sarki Sahibul Hairi ba za su iya mayar dani kasarmu ba na sadu da mahaifina ba, domin daha nan zuwa kaarmu tafiya ce ta a kalla wata bakwai basa rakumi ko doki. Kuma akwai muggan abubuwan hadari a hanya wadanda ba za mu iya shallake hasarin su ba.
Ina rokonki da ki taimaka ki ci gaba da tafiyar nan tare da mu domin nawa burin ya cika".
Sa'adda gimbiya Humaira taji wannan batu, sai tai ajiyar zuciya sannan ta ce, "ya ke Alfila yanzu idan na kaiki kasarku kika sadu da mahaofinki za ki yi imani da addinina?"
koda jin wannan tambaya sai Alfila ta yi murmushi ta ce, "Ai tun da na ga ma kin sami nasara akan Shamzabul Azwas na ji na gamsu cewa tsafi karyane, addininki shi ne addinin gaskiya, yanzu take ina son ki shigar dani cikin addinin naki".
Da jin haka sai farin ciki ya lullu6e gimbiya humaira. Nan take ta biyawa Alfila kalmar shahada ta maimaita.
Humaira ta mike tsaye sannan ta dauki Alfila ta goyata a bayanta.
Humaira ta dubi yarinya Alfila da ke bayanta ta ce, "ya ke Alfila ki sani cewa daga yau kin zama 'yar uwata, duk rintsin da za ki shiga sai dai mu shiga tare".
Gimbiya Humaira ta sake juyowa ta dubi su Sarki Sahibul Hairi da Bawa Haluf ta ce, "ku kuma kun ci albarkacin wannan yarinya, sabo da haka ku zo mu ci gaba da tafiya".
Gama fadin haka ke da wuya, sai gimbiya Humaira ta ci gaba da tafiya dauke da yarinya Alfila, su sarki Sahibul Hairi suka biyo bayanta cikin jin kunya.
Gimbiya Humaira ta ci gaba da tafiya tana mai karanta wata addu'a ta musamman. Sarki Sahibul da Bawa Haluf kuwa suka rinka bin bayanta da sauri ba sa yarda ta basu sata.
Nan fa suja rinka ganin abin Al'ajabi, domin gani suka yi suna wuce dazuzzuka tamkar walkiya na giftawa.
Tafiyar da ya kamata su yi ta a cikin sa'a guda sai gashi sun shafeta a cikin dakika sittin. 
Haka dai suka ci gaba da wannan tafiya har suka shafe tafiyar kwana arba'in a cikin sa'o'i kadan
A sannan ne dare ya riskesu a cikin wani dajo mai yawan manyan tsaunuka da duwatsu.
Kuma a dai-dai lokacin ne hadari ya gangamo, gari yai duhu, iska ta soma kadawa mai karfi alamar ruwa na shirin sauka. 
Kafin dakika goma karkarfan ruwa ya kece kamar da bakin kwarya.
Cikin gaggawa suka ruga izuwa cikin wani kogon dutse suka zauna. Zamansu ke da wuya sai Humaira ta dau wata karamar butar duma cike da ruwa tayi alwala sannan ta nunawa Alfila yadda itama za ta yi alwalar, sannan suka yi sallah tare.
Duk abin da ke faruwa sarki Sahibul Hairi da Bawa Haluf na daga can nesa kadan a zaune suna kallonsu.
Sarki Sahibul Hairi ya dubi Bawa Haluf ya ce, "ya kai Haluf kayi sani cewa ina ji a jikina cewa wannan addini na Humaira gaskiya ne, kuma kaima kanka shaidane bisa abubuwan da muka gani a zahiri na ban al'ajabi. To amma inda matsalar take shi ne, ina jin tsoron cewa idan na kar6i addinin shi ke nan har abada burina bazai cika ba".
Sa'adda Haluf ya ji wannan batu sai yai ajiyar zuciya sannan ya ce, "ya shugabana, amma ai idan baka manta ba Humaira ta gaya maka cewa idan har kayi imani da Ubangijinta dukkan burin ka zai cika, sabo da me ba za ka yi imani da shi ba idan har jikinka ya baka cewa addini ne na gaskiya?"
Koda jin wannan tambaya sai sarki Sahibul Hairi yai shiru yana sake-sake. Zuwa wani lokaci ya dago kai ya dubi Bawa Haluf ya kura masa ido na tsawan dakiku, sannan ya sunkuyar da kansa ya ci gaba da tunani ba tare da ya ce da Bawa Haluf komai ba.
Tabbas komai na duniya rabone, kuma komai yana da lokacinsa.
Gashi dai sarki Sahibul Hairi ya gamsu da cewa addinin Musulinci gaskiya ne, amma kuma ya kasa tankwara zuciyar tasa ta yarda ta kar6i addinin sabo da tsoron kada ya yi asarar abin da ya fito nema.
Lolacin da ruwan sama ya ci gaba da tsugewa, sai wata irin iska mai sanyi ta rinka busowa har cikin kogon da su Humaira ke ciki ta addabesu.
Ba shiri su sarki Sahibul Hairo suka mike suka kama karyo tsurarrun itatuwan da ke cikin kogon suka hada makamashi.
Bayan sun tare ice mai yawa sai suka fara kokarin kunna wuta ta hanyar goga dutse da dutse, amma sai wuta ta ki kamawa.
Lokacin da Humaira ta ga sarki Sahibul Hairi da Bawa Haluf sun jima suna fama amma sun kasa kuma wutar sai ta dubi Alfila cikin murmushi ta ce, "je ki ki kar6i duwatsun a hannunsu kiyi bisimilla ki ambaci sunan Ubangijin musulinci, da izininsa wutar za ta kama."
Ba tare da fargabar komai ba yarinya Alfila ta mike tsaye taje ta kar6i duwatsun biyu da ke hannun sarki Sahibul Hairi tare da yin bisimilla kamar yadda Humaira ta koyar da ita, ta ambaci sunan Ubangijin musulinci.
Gogawa daya tayi akan makamashin sai wuta ta tashi kamar an zuba mai.
Sarki Sahibul Hairi da Bawa Haluf suka cika da tsananin mamaki, jikinsu yao sanyi.
Nan dai suka gewaye wutar su hudun suna jin dumi. Alfila na zaune daf da Humaira, sarki Sahibul Hairi da Bawa Haluf na daga can 6angare guda suna fuskantar juna.
A duk sa'adda Humaira ta dago kai sai ta ga sarki Sahibul Hairi na satar kallonta, kawai sai ta mike tsaye tsam! Ta bar gaban wutar ta koma can gefe daya taa shimfida buzu ta zauna tana mai fuskantar gabas, sannan ta dauki casbaha ta kama lazumi.
Ba wani abu bane yasa sarki Sahibul Hairi ke satar kallon Gimbiya Humaira ba face tsananin kyawunta da ya ribaci zuciyarsa.
Tun ranar farko da ya fara ganinta yaji zuciyarsa ta buga da karfi, kuma ya rasa dalilin faruwar hakan.
Abin da sarki Sahibul Hairi bai sani ba ya kamu da tsananin kaunarta da begenta.
Haka dai su sarki Sahibul Hairi suka ci gaba da zama a cikin wannan kogon dutsen har dare ya yi sosai suka kama barci.
A duk sa'adda sarki Sahibul Hairi ya farka sai ya ga Alfila da Bawa Haluf na ta sharar barci abinsu. Ita kuma Humaira na nan a zaune bisa buzu tana ta lazumi. Wani lokacin kuma sai ya ga ta mike tsaye ta kama nafilfiloli.
Kai a takai ce dai Humaira bata gushe ba tana ibada har sai da ta gabatar da sallar Asuba ta jira Alfijir ya keto sannan ta kwanta ta lullu6e jikinta gaba daya tayi barci.
Lokacin da gari ya waye sosai sai sarki Sahibul Hairi da bawa Haluf suka farka daga barci suka ga Humaira da Alfila na ta barci abinsu.
Kawai sai sarki Sahibul Hairi ya dauki kwari da bakansa ya rataya sannan ya soke takobinsa a cikin gidanta da ke daure a kugunsa ya dubi Haluf ya ce, "zo mu tafo neman abin kalaci.
Koda jin haka sai shima Haluf yai sauri ya dauki nasa kayan yakin suka face daga cikin kogon dutsen suka nausa cikin daji.
Ba su yi wata doguwar tafiya ba suka hango wata barewa a can saman wani dogon tsauni da ke nesa da su.
Sarki Sahibul Hairi yai sauri ya dana kwari a cikin bakansa ya saita barewar, amma sai ya auna ya ga cewa ba zai sami nasara ba domin akwai tazara sosai a tsakaninsu da barewar, don haka sai ya yiwa Haluf inkiyar cewa su lalla6a ta bayan barewar su kusanci tsaunin da take kai. 
Cikin sanda suka rinka taku dai-dai a hankali har suka isa kan tsaunin suka hau a durkushe yadda za su iya hango barewar ta baya, amma ita ba ta hangosu ba.
Cikin hanzari sarki Sahibul Hairi ya sake dana kwari a cikin bakansa ya ta6eshi iya karfinsa ya saita barewar a ciki, sai ya saki harbi.
Kibiyar ta tafi cikin azababban gudu. Koda taje daf da barewar sai ta tsaya cak! A cikin iska ta kasa huda cikin barewar.
Ita kuwa barewar sai ta juyo tayi arba da su sarki Sahibul Hairi, ta kura musu ido kawai. Al'amarin da ya matukar baiwa su sarki Sahibul Hairi mamaki ke nan, suka mike tsaye jikinsu a sanyaye suka kasa juyawa da baya, kuma suka kasa karasawa inda barewar take.
Cikin tsananin tsoro Haluf ya dubi sarki Sahibul Hairi a lokacin da jikinsa ya kama karkarwa, ya ce, "ya shugabana waccan dabbar ba barewz bace aljanai ce, zai fi kyau mu hakura mu koma da baya domin na fuskanci cewa akwai muggan abubuwa a cikin wannan daji".
Koda jin wannan batu sai sarki Sahibul Hairi ya dakawa Bawa Haluf tsawa ya ce, "ai ni idan nayi gaba bana baya. Idan na za ka iya biyoni ba ka tsaya a nan ka ga abin da zai faru tsakanina da waccan barewar, idan kuma ba za ka iya tsayawa ba kayi kallo ba to ka koma inda muka fito".
Koda gama fadin haka sai sarki Sahibul Hairi ya zare takobinsa ya ci gaba da hawa kan tsaunin ya dufafi inda barewar take kai tsaye ba tare da shakkar komai ba.
Shi kuwa Bawa Haluf sai yaji kamar ya juya da baya a guje amma sai ya daure ya tsaya domin ya ga abin da zai faru.
Har sarki Sahibul Hairi ya isa daf da barewar wannan kibiyar ba ya harba mata tana nan a tsaye a cikin iska daf da barewar.
Da zuwan sarki Sahibul Hairi gaban barewar sai ya daga takobinsa sama ya kai ma ta wawan sara da nufin ya tsarge jikinta gida biyu.
Ba zato ba tsammani sai ya ga barewar ta rikida ta zama sarki Barusa rike da takobi yana mai kare saran.
A sannan ne wannan kibiya ta fadi kasa.
Koda sarki Sahibul Hairi ya ga sarki Barusa a gabansa sai ya ja da baya a tsorace cikin mutukar mamaki ya kasa ci gaba da kai masa hari.
Sarki Barusa ya bushe da dariyar mugunta ya ce, "shin kana tsammanin na mutu ne? To ka sani cewa kashe na mijin kwarai ba karamin aiki bane, duk abin da ke faruwa ina bie da ku baku sani ba. Yanzu gashi kun je kun sha bakar wahala kun dauko yarinya Alfila a cikin fadar Shamzabul Azwas ni kuma zan kwaceta a salim-alim a hannunku ba tare da na sha wahalar komai ba".
Koda jin wannan batu sai sarki Sahibul Hairi shima ya bushe da dariya ya ce, "ya akai wannan sarki kayi sani cewa wannnan mafarkin naka ba zai ta6a tabbata ba don haka ina mai baka shawara da ka janye wannan manufa taka ka koma kasarka ka ci gaba da mulki, ka hakura da iyakar abin da ka mallaka.
Idan kuwa ka zake ina tabbatar maka da cewa za ka iya rasa rayuwarka".
Ya yin da sarki Barusa yaji wannan batu sai ya sake kyakyatawa da Dariya a karo na biyu ya ce, "hakika iska na yawo da mai kayan kara. Tsaya kaji na gaya maka gaskiyar abin da duk yasa na kasa mallakar yarinya Alfila, shi ne zai sa kaima ka kasa mallakarta.
Yanzu zan kamaku nayi garkuwa da ku, domin gimbiya Humaira ta kawo yarinya Alfila, idan kuwa taki sai na hallaka ku. Sannan na bi sawunta itama na hallakata na dauke Alfila."
Sa'adda sarki Sahibul Hairi yaji hakan sai abin ya bashi dariya ya ce, "ya naji kana cewa za ka kama mu kayi garkuwa damu kamar wanda zai kama 'yan tsaki? Shin kana tsammanin kamani a hannunka abu ne mai sauki?".
Koda jin wannan tambaya sai Barusa yai murmushin mugunta ya ce, "yanzun nan kuwa za ka sha mamaki, domin sanin da ka yi mini na da ne, amma wannan karon na zama MURUCIN KAN DUTSU, ban tashi fitowa ba sai na shirya"
.
Zan dakata a nan saikuma Allah yakaimu gobe zamu cigaba



Download Sarkin Sarakai Complete Littafi Na Hudu