*♡...  MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*1*

"Na rantse da Allah yau sai an biyani ni babu ruwana"
rik'e take da kunkuru tana marmaɗen ido da murguɗa baki jikinta sai rawa yake wai ita ga matsifaffeya.
yaron dake gabanta ya risina har k'asa yana bata hak'uri
"dan Allah Mairo ki yafe min wlh ba zan kara ba ni naga kinje wani gurin ne shiyasa na cika miki ban san ba kyaso ba"
sai a lokacin ta kalleshi cikin matsifa tace "saka nayi cewa nayi na cika min kai mai hegen salo yau ko saika busar dashi ko na maka hegen duka"

wata dattijuwa take wanki gefen kogin ta kalleta tace "ke Mairo wai miyasa baki jin magana ne yanzu miye laifin yaron nan dan ya cika miki tulu?"
harara ta watsa mata ta murguda mata baki "ke kuma tsohuwa ina ruwanki dake nake yi ne da zaki samun baki ko sashi nayi da zai cika min tulu wannan ai rainine"
"ke fa baki da kirki Mairo daga magan zaki wani taso min kamar wata warinki"
"mtsssss yau daman kin san ba warinki nake ba kika samin baki a magana dan neman tsokana"

daidai nan Almu ya iso da jakinsa da jalkunan ɗinba ruwa.
yana kallon Mairo yasan matsifa ce take ganin yadda take marmaɗen ido tana rawar jiki
murmushi kawai yayi ya gaida dattijuwar

"inna ina kwana?"

"lafiya kalau Almu an tashi lafiya?"

"Alhamdulillah inna"

kallon mairo yayi "ke lafiyarki kike wannan harare2?"

banza ta masa ta cigaba da karkada jiki.
inna ta taɓe baki

"ai haka take indai rashin kunya ne ta iya ga yar banzar matsifa"

juyowa mairo tayi kanta "wai ke ina ruwanki dani kinga ban hega saggarki ba ki fita tawa bana son shinshigi"

da marmaɗe2 ta ksrasa maganar tana murguda mata baki.
      mari Almu ya kai mata ya fizgota ya jefar
"ke wai miyasa rashin kunya yayi miki yawa kamar inna zaki tsaya kina faɗawa irin wannan maganar sa'arki ce?"
wani ihu mairo ta saki ta shiga murk'ususu cikin kasa tana jan gashin kanta
"wayyo na shiga uku ya kashe ni wayyo Allah ya kare ni wayyo gwaggo"

tsoro Almu yaji ganin yadda take ihu duk'awa yayi ya rikota "tashi mu gani?"
wani mugun cizo ta kai masa a hannu saida ya saki kara ya saketa da sauri.
inna ta rike baki "oh ni hajjo wannan wace irin masifaffiyar yarinya ce haka?"
Almu dai shiru yayi yana murzar hannun dan ba karamin cizo tayi masa ba,
ya dade a haka kamin ya nufi kogin ya shiga cika jalkunansa.
       ihunta ta cigaba dayi tana murje2 daga Almu har inna babu wadda ya sake bi ta kanta.
Almu na daf da cika kayansa halilu ya iso gurin yana ganin mairo yayi saurin ta data "ke lafiya miya faru?"
langaɓe masa tayi ta cigaba da kukan
nan ya kalli inna da Almu ya shiga tambayar su ba'asi "wai miya sameta ne haka?"
inna tace "babu kawai rashin kunya tayi min Almu ya ɗan zungureta shikenan fa ta faɗi ta shiga koke2"
cikin kuka Mairo ta ɗago "wlh karya suke itace ta fasa kuka tace masa na zageta shi kuma ya ɗaga ni sama ya jefar na kare"
tana kaiwa nan ta saki wata kara kamar wadda aka sokawa wuka.
rik'e baki inna tayi jin irin karyar da Mairo ta zagga
Halilu ya kalli Almu "haba Almu ya zaka mata haka kamar wata warinka ko namiji"
Almu yayi murmushi "haba dai Halilu sai kace bakasan halin Mairo ba wlh karya take"
Halilu yace  "wai minene mafarin wannan masifa?"
inna tace "ɗiban ruwa tazo fa saita eje tulun ta tafi yawonta shine haruna ya dauka ya cika mata shine data dawo tace sai ya biyata shine ya zubar da ruwan daya zuba kuma duk da haka tace wai saiya busar tulun yadda yake shine ya shiga bata hak'uri taki hak'ura wai ita saita dake sai natibmata magana shine fa ta shiga fada min magagganu har Almu saida tayi masa rashin kunyar"
Halilu yace "daman shine kawai take yiwa wannan kuka?"
"shine kawai babu wani abun da akayi mata"
cewar inna.
kai halilu ya kaɗa ya Nufi ecen dogon yaro ya k'allo ya juyo gurin mairo cikin zafin nama ya watsa mata ita,
mairo najin saukar bulala ta tashi da gudu ta nufi gida tana uhu.

***   ***   ***

da ihu ta isa gida tana murxa gurin da Halilu ya buga mata bulalar.
da sauri gwaggo ta tare ta "lafiya Mairo miya sameki?"
rumgumeta tayi "wayyo gwaggo zasu kasheni gwaggo basa sona sun min taro suna ta duka na"
gwaggo ta dagota "su waye Mairo faɗa min uban wa ya taba ki cikin garin nan?"
cikin kuka ta shiga yima gwaggo k'arya data saba "tsohuwar gidansu hajara ce tace wa Almu wai na zageta shine shi kuma ya daga ni sama ya jefar gwaggo ya k'arya ni na bani mutuwa zanyi"
da sauri gwaggo ta zaunar da ita ta shiga duba ta tana matsifa "wannan wace irin k 'etace haka wlh duk suka karyaki sai munyi shari'ah dasu mugayen mutane azzalumai"
gwaggo na taɓa mata k'afa ta saki wani mahaukacin ihu "wayyo na shiga uku gwaggo nan gurin Halilu ya buga min ecce"
gwaggo tayo waje da ido "ecce kuma yaushe mi kika masa?"
"ban masa komai ba daga zuwansa suka fada masa k'arya shine ya dauko k'aton ecce ya buga min gwaggo basu sona na shiga uku"
tashi gwaggo tayi ta shiga ɗaki ta ɗauko mayafinta ta nufi kofa.

  
        '''
NOTE'''
*_Assalamu Alaikum ina bawa fans ɗina hak'uri bisa ga rashin ganin cigaban novel ɗina mai suna LAMARIN DUNIYA na k'are novel ɗin gaba ɗaya kamin na fara posting sai phone ɗina ya samu matsala kuma wadda nayi publishing a blog ɗina blog ɗin ya samu matsa. ta dalilin matsalar da phone ɗina ya samu amman ana kan gyara blog ɗin da zarar an kare zanyi muku C & P Insha Allah ko kuma na baku blog address ku karanta bayan haka dan Allah ina rokon duk mai novels ɗina ko wane iri ya turo min ta wannan number_*
+2348036126660
*_taku har kullum Khadeeja Candy_*

© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:37 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*2*

gwaggo na k'ok'arin fita halilu na k'ok'arin  shigowa sukaci karo nan taci kwalarsa ta k'asara shigowa dashi tana masifa "ashe baka da hankali halilu dan kana magu zaka sa ecce ka bugawa Mairo bancin bugun da Almu yayi mata wai mi ta tare maka ne?"
kai ya girgiza "haba gwaggo wai miyasa duk tazo tayi miki k'arya saiki yarda ya za'aiyi na buga mata ecce fisabilillahi?"
"ai halinka na sani ba sonta kake ba zaka iya mata komai"
kallon mairo yayi da tayi shiru tana kallonsu kamar wata munafuka yace "ke dukanki nayi?"
kai ta daga ta turo baki tana matsar kwallah.
"eh gurin da Almu ya karyani ka buga min ecce"
gwaggo ta kara ciyo kwalarsa "mugu yanzu abunda kake ya kamata kenan a gaban idonka ka bari Almu yayi mata wannan illar wai miyasa baka son yarinyar nan ne halilu?"
"ohhh gwaggo haba haba wane irin illa Almu zaiyi mata rashin kunya fa tayiwa tsohuwar mutane shine ya dan zingureta fa"
gwaggo tace "tho ina ruwansa ya zingureta haihuwarta yayi kuma karya kake karyata yayi"
"haba gwaggo yarinyar da aka karya zata iya kawo kanta gida har ta iya faɗa miki an karya ta ai saidai a kawo miki ita"
saki kwalarsa gwaggo tayi ta nufi Mairo ta shiga duba k'afar.
aiko nan mairo ta k'ara marairaicewa tana "wayyoh k'afata" gwaggo ta duba bata ga alamun kariya a k'afarta ba ko alamun jimuwa babu barre karaya ta data gwaggo tayi tsaye "tashi kiyi tafiya na gani"
nan ta lak'e kafar "wayyo bazan iya takata ba gwaggo ta riga ta karye"
cikin dabara halilu ya cire takalminsa ya jefa mata iya karfinsa aiko da gudu ta faɗa ɗaki tana ihu.
matsowa yayi kusa da gwaggo ya ɗauki takamin yana faɗin "yanzu wadda aka karya zata iya wannan gudun?"

shiru gwaggo tayi halilu yace "gwaggo wata rana saita saki kunya matukar duk abunda tazo ta faɗa miki kina yarda dashi tho ko zaki ɓata da kowa"
tsaki gwaggo taja "mtsss tho sai mi dan na ɓata da kowa akanta so kake na zuba ido ina kallon ana cin amanarta? ko kai ka taɓa ta saina taɓa ka bare wani can"
halilu bai kara cewa komai ba banda kan da ya girgiza ya fice ya barta tana masifarta.
saida Mairo taji fitarsa sannan ta fito tana kukan munafurci.
nan gwaggo tayi cikinta ta masifa "Allah mairo in kina zuwa kina min karya saina ɓata miki rai kuma na ɓata dake na fita harkarki"
    kwantowa tayi jikinta tana kukan shgwaɓa "tho ai ba karya nake ba Almu ya dakeni kuma Halilu ya zaggamin bulala"
tureta gwaggo tayi "amman ai cemin kikayi shiya buga miki ecce Almu kuma ya karyaki"
turo baki tayi
"eh karya nake amman dai sun dakeni dukansu"
"tho miyasa kika min karya kuma halilu yace ai tsohuwa kikayiwa rashin kunya"
"tho gwaggo ai itace ta samin baki a magana kuma tace min masifaffiya"
"amman ai kinsan na hanaki rashin kunya da karya ko ni daga yau babu ruwana dake"
kuka ta shiga rerawa "na daina gwaggo dan Allah kar kiyi fushi dani ba zan kara ba"
gwaggo bata so kuka mairo ko kaɗan janyota tayi jikinta "shi kenan bazanyi fushi dake ba amman ki daina kinji ba kyau kuma bana so"
"na daina daga yau ni ko kallon mutane bazan sakeyi ba"
gwaggo tayi dariya tace "rufe da ido zaki rika yawo kenan?"
"eh bazan sake kallon mutane ba bare suce nayi musu rashin kunya"
gwaggo ta shafa kanta "a'a kawai ki rika jin magana kibar rashin kunya yayi basai kim rufe idoba"
dariya mairo tayi "ai wasa nake miki gwaggo ya za'ayi na rufe ido kina son na fada rijiyane ko rame?"
dundu gwaggo ta kaimata a baya tana dariya "oh baki daina karyar ba kenan ko?"
"na daina Allah yanzu ko zanyi kaɗan zanyi"
gwaggo ta girgiza kai "a,a ki daina gaba ɗaya dai wai ina kika baro min tulu?"
"yana can kogi ni gaskiya gwaggo daga yau bazan kara zuwa ɗiban ruwa ba kullum ni nake zuwa kuma yar k'ank'anuwa dani shi halilu da yake k'ato bazai jeba sai ni shiyasa suke dukana sunga ni banida girma"
cike da shagwaɓa take maganar tana son yin kuka.
gwaggo ta shafa bayanta "shikenan bazaki sake zuwa ba halilu ne zai rik'a ɗebowa"
rumgumeta mairo tayi tana murna.

'''        * * *'''

_2:13pm..._
gwaggo ta kare dahuwar giɗar ta ta zuba a gwango.
ta kwalawa Mairo kira da sauri ta fito tana ɗaurin ɗankwali rabin fuskarta duk fodace da bata shafu ba.
"na'am gwaggo kin kare?"
saida ta kare lisafin sannan ta ɗago ta kalleta tace "ta ɗari biu da arba'ince"
ɓata fuska mairo tayi "gaskiya gwaggo saidai ace ta ɗari biu da talatin dai dan gaskiya zan ɗauki ɗaya"
gwaggo tace "ɗauki ko nawa kike so mairo waya isa ya hanaki?"
murmushi tayi ta duka ta ɗauki turen tana faɗin "yau duka zan siyar"
"tho Allah bada sa'ah amman dai hodarki bata shafu ba mairo"
turo baki tayi "nidai gwaggo bana son haka bani na shafa ba nidai haka zanje"
hannu gwaggo ta ɗaga mata "jeki jeki Allah bada sa'ah inda yanzu kuma ban faɗa miki ba ki hauni da masifa"
batace komai ba ta ɗora turen samsn kai ta nufi kofa.
gwaggo ido ta sakar mata a ranta tana _Allah ya shirya minke mairo ya tsare_

© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:39 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*3*

tafe Mairo take ɗauke da turenta na giɗa saman kai tana yan wakewakenta.
saida tayi nisa da tafiya sannan ta tuno da ɓanɓaramar da tayi jiya da sauri ta chaja hanya harda haɗawa da ɗan gudu tana waigen bayanta.
saida taga ta shanye kwana sannan hankalinta ya kwanta tafiya ta rik'ayi a hankali tana kwanɗalar giɗar tana ci.

kashe kunne tayi tayi gefen dashi tana son ta tabbatarda abunda kunnuwanta suke jiyo mata.
wak'ar india ce _ghajiniguzarish_ ke tashi cikin wani kiɗan taushi mai daɗi
taɓe baki tayi "tho wai wayasa wannan kiɗan mai ɗaɗi cikin ɗaji kodai buki ake?" magana take tana kallon giɗar dake hannunta kamar wata taɓaɓɓiya.
kara kasa kunne tayi har ta gano gefen da sautin ke tashi dariya tayi "Allah buki ne ake bari na leka na gani amman ba zan daɗe ba sai na dawo"
haka ta kunna kai daga wani ɓangare na hanyar ta rika tafiya tana bin inda taji sautin wakar na tashi harta iso wani guri mai kamada lambu.
tsayawa tayi tana kallon etacen dake gurin "lahhh ashe ma haka gurin yake ni kan ban taba zuwa ba sai yau"
rabon ido ta shigayi saida ta kare kallon gurin sannan ta cigaba da tafiya.
a hankali ta fara hango wasu mutane sanye da wani yadi kala ɗaya.
da sauri ta laɓe gefen ecce tana lekensu ,

duk kansu sanye suke da yadi kala ɗaya mai ja da kore (red and green) kana gani kasan fadawa ne in banda mutun biu dake zaune saman wani k'aton carpet na alfarma ɗayan sanye yake da riga da waddo na turawa ɗayan kuma sanye yake da riga doguwa mai kamada jalabiyar fakistan _golden color_ Mai kyau sai kyali take.
ya dora wani ɗan kyale saman wuyansa daya sauko har saman rigarsa.
gashin kansa ya kwanta lum kamar balarabe ya lankwashe kafafunsa wata rekoda na gefensa tana bada sauti shi kuma yana fuskarta ɗayan suna karta ko wannensu kuɗi yake azawa in aka cinye ya kara wasu.

        sosai abunda suke ya burge Mairo aje turen giɗar tayi tayi zaune tana kallonsu tana dariya amman baki rufe dan kar suji
ta daɗe a haka can dai taji bazata iya jurewa ba ta ɗauki turenta ta nufosu tana Murmushi.
"Assalamu alaikum"
sallama tayi musu tana k'ok'arin k'arisawa kusa dasu
   da sauri suka tare wadda ke zaune saman carpet ɗin wasu kuma suka nufota rik'e da takobi.
tsaye tayi tana kallonsu kamar hoto har suka karaso kusa da ita,
wani zarare cikinsu ya ɗaga takobi zai sara mata ɗayan yayi saurin  rikewa yana faɗin "Yarima yace a dakata"
da sauri ya janye takobin yayi baya.
ɗaya daga cikin fadawan ya fisgota da karfi har giɗar dake saman kanta ta watse ya nufi gurin yarima da ita.
yana tsaye yana kallonsu har suka iso da ita kallo ɗaya yayi mata ya gane bata cikin hayyacinta ganin yadda idonta suka k'afe kuma bata motsi.
    ido ya ɗan tsura mata sannan ya bada umarnin a zuba mata ruwa,

da sauri bafaden ya dauki ruwan gora ya watsa mata
sai a lokacin ta matsa alamar ta dawo hayyacinta zubewa tayi zaune ta ɗaga kai tana kallonsu
suma ita suke kallo har yarima saida ta kare kallonsu ɗaya bayan ɗaya sannan ta saki wata irin kara iya karfinta mai shiga cikin kwakwalwa faɗuwa yarima yayi zaune ya dafe kunnunwansa shida wadda ke kusa dashi.
mari daya daga cikin fadawan ya watsa mata saida ta faɗi can gefe ta fashe da kuka
     ɗagowa yarima yayi ya watsa masa wata mugunyar harara da sauri bafaden ya faɗi kasa "Allah ya huci zuciyarka Yarima banyi dan ranka ya bace ba"
kawarda kai yayi yana sauraren sautin kukanta dake tashi tare da sautin waka

ya daɗe a haka sannan ya ɗago cike da isa yace "kashe sautin nan" da sauri ya tashi ya nufi rikodar sa hannu ya kashe ya dawo ya risina gaban Yarima yana faɗin "Allah karawa Yarima martaba na kashe"
ba tare daya kalleshi ba yace
"jeki ka rarrasheta"
"am gama Yarima" tashi yayi da sauri ya nufi gurin Mairo.

tirgewa Mairo ta karayi tana kuka tana kiran gwaggo tana murza hannayenta da kafafunta cikin kasa,
yayita rarrashinta har ya gaji tak'i tayi shiru sai ma karawa take.
ganin tak'iyin shiru yasa Yarima yayi mata alamar tazo da hannun tashi tayi ta share hawayenta ta nufoshi tana murmushi kamar ba ita ba.
kallonta yake harta karaso kusa dashi tun kamin yayi mata magana ta zauna saman carpet ɗin kusa dashi.
       da sauri ɗaya daga cikin bafaden ya unkuro zai mata magana Yarima ya ɗaga masa hannu nan dukansu suka ja baya kowa ya shiga harkar gabansa.
kallonta yayi a natse cikin isa yace

"ya sunanki?"
washe masa hauru tayi
"Mairo"

"Mairo?"

"eh sunana Maryam amman Mairo ake cemin kaifa ya sunaka?"

bai amsa mata ba ya jefa mata wata tambayar "an garin kike?"
"eh kai amman dai ɗan birni ne ko?"
nan ma wata tambayar ya sake jefa mata batare daya amsa mata ba
"mi kikazo yi nan?"
"talla nake zan wuce sai naji kiɗi na ɗauka bukine ake shine nace bari nazo na gani saina koma shine na ganku sai na taɓe"
shiru ya ɗanyi yaɓa kallonta sannan yace
"tho miyasa kika fito?"
abunda ke gabansa ta ɗauka ta nuna masa "wasan da kuoe da wannan abun ya burgeni shiyasa na fito"
bai sake ce mata komai ba ya janyo wayarsa ya shiga danne2

sai a lokacin Mairo ta tuno da giɗarta
hannu ta ɗora saman kai ta fasa kuka
"wayyo na shiga uku giɗata"
wani mugun tsaki wadda ke kusa da Yarinan yaja yana hararta.
a hankali Yarima ya ɗago kai ya kalleta
"ina giɗar take?"
"nima ban saniba ɗazu dai kamin nayi bachi nasan tana saman kaina"
kallon rashin fahimta yayi mata "bachi kikayi?"
"eh ɗazu da suka nufoni da takobi ba sai naji bachi dana farka sai naganni nan kuma banga giɗar ba"
murmushi yayi dan ya gane suma take nufi da bachi.
ɗaya daga cikin fadawansa ya kira da sauri yazo gabansa ya risina cikin isa Yarima yace
"ina giɗar Yarinyar nan?"
"gata can kusa da ecce ta zubar"
"jeki ka ɗauko mata"
tashi yayi da sauri ya nufi gurin yana faɗin "am gama Yarima"
kallon Yarima tayi tana dariya "na gode"
kai kawai ya ɗaga mata
ta sakar masa murmushi tace
"kai baka fada min sunanka ba?"
yi yayi kamar bai jita ba ya mai yarda idonsa wani gefen
nan mairo ta ɓata fuska ta buro baki
"ni inna tambayeka saika kyaleni nima amsar da na baka ban yafe ba lafira saika biyani"
cikiciki take maganar amman hakan bai hanashi ji ba
dariya ce tazo masa da sauri ya mayarda ita murmushi ya kara kawarda fuskarsa.

*© Khadeeja Candy*
[11/5, 9:39 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*4*

suna haka nafaden ya kawo mata turen giɗarta ya aje yana faɗin "gashi Yarima Allah ya kara maka daraja"
hannu ya ɗaga masa bafaɗen ya tashi.
kallonsa Mairo tayi "na gode"
banza yayi mata kamar bai jita ba sun daɗe a haka sannan ya juya ya kalleta yace "amsar da kika bani zan biyaki lahira?"
shru tayi tana kallonshi dan batayi zaton yaji ba can tace "eh mana tunda kai baka banu amsar tambaya ta ba"
shiru ya ɗanyi sannan yace "mi kike tambayeni?"
"ba nace ka faɗa min sunanka ba"
ya ɗan daɗe kamin ya bata amsa "sunana Yusuf Usaini"
dariya tayi harda sa hannun baki "lahhhh shiyasa kake da kyau daman masu suna Yusuf suna da kyau"
murmusawa ya ɗanyi ya ɗauki enabi yakai bakinshi.
yatsa ɗaya Mairo ta ɗaga masa "sauran tambaya ɗaya" 
kai ya ɗaga mata yana tsusar enabi kamar mai shan minti.
tsaki kawai na kusa dashi keja haushi ya isheshi
harara Mairo ta watsa masa ta kalli Yarima tace "amman dai ɗan bunni ne ko?"
murmushin gefe yayi ya ɗaga mata kai alamar 'eh' waje tayo da ido ta shiga shafa mishi riga "lahhh nikan daman nace dan bunni ne kai inason yan bunni kuma..."
"ke! mahaukaciya"
bata karasa maganar ba na kusa dashi ya katsa mata tsawa saida ta razana
hmda sauri Yarima ya ɗaga mishi hannu yana kallon fuskar Mairo data k'ara rik'e masa riga tana kallon mutunen.
tsaki ya k'ara ja ya kalli Yarima "haba Yarima ya zaka..."
dakatar dashi Yarima yayi ba tare daya kalleshi ba yace "enough yahuza plz excuse us"
tashi yayi cike da bachin rai ya nufi wta bishiya ya zauna.

sai lokacin Mairo ta turo baki tayi kwafa "tho an taɓa shi zo kayi abunda zakayi mai k'aton kai"
murmushi Yarima yayi yace "baki tsoron ya dakeki?"
kai ta kaɗa "ni wlh bana tsoron duka nifa ko sheɗan bai kaini masifa ba"
faɗaɗa murmushinsa yayi "gaskiya ne tho tashi zaune"
tashi tayi zaune ta ɗauki ruwan dake gansa "insha ruwan bunni?"
kai ya ɗaga mata yana kakkaɓe rigarsa data bata da k'asar hannunta.
saida ta shanye ruwan kofin gaba ɗaya sannan ta dire kofin tana dariya tana faɗin "wlh na sha ruwan bunni"
"birni ake cewa ba bunni ba"
ya gyara mata
washe hakora tayi ta sake cewa "bunni"
murmushi yayi yace "waya shafa miki hoda?"
"nice na shafa ɗazu da zanje tallah"
ta karasa maganar tana gyaran ɗankwalinta.

can ta ɗauki abunda ke gabanshi ta kalleshi tace "minene kuke da wannan abun ɗazu naga kuna wasa dashi?"
saida ya ɗan daɗe sannan yace "chachace muke zakiyi?"
da sauri ta matso kisa dashi tace "eh zanyi dan Allah"
"tho mi zaki aza?"
"kamar ya mi ake azawa"
"duk abun mutum kr so yana azawa bakiga yadda muke yi ba ni kuɗi nake azawa"
kalle2 ta shigayi tana neman abunda zata aza can ta kalli giɗar ta da sauri ta ɗauko k'waya ɗaya ta aza "to ga giɗa nan na aza"
shafa kansa yayi yayi murmushi ya sa hannunsa aljihu ya ciro dalar amerika ɗaya ya aza.
bata fuska Mairo tayi ta turo baki "ni dai bana son wannan takardar da kuke da ita saida ka aza kuɗi ko wani abu mai daɗi"
ta karasa maganar tana lek'en lemun dake bayansa.
ido ya tsura mata yana mamakin wayonta wato shi ya aza (ɗora) kudin data sani ko abu mai daɗi ita kuma ta aza kwaya ɗaya ta giɗa
cikiciki yayi murmushi yace "ai kuɗi ne ba takarda bace in kika chaja kuɗi da yawa za a baki"
lak'e kafaɗa tayi "ban yarda ba kuɗi bane ai da na sansu saidai ka aza kuɗin k'warai"
"ba nida wayan can kuɗin da kika sani wannan ne kawai in kuma ba zakiyi ba shi kenan"
shiru tayi tana son masa musu shima shirun yayi yana kallonta.
da taga babu sarki sai Allah yasa ta kalleshi tace "na amince"
kai ya kaɗa mata ya ɗan daɗe sannan ya gyara zamansa suka fara.
yin kawai suke tana masa shirme dan bata iyaba ci kusan 10 yayi mata sai haushi take ji dak'er ta samu tayi masa ci biu koshi danya nuna mata yadda zatayi ne.
aiko murna kamar ta kasheta sai dariya take kwasa harda hawaye.
shidai kallonta kawai yana shakkun hankalinta.

da taga ya kara mata ci biu ta ɓata fuska tace
"nidai na daina kuma saika bana giɗata"
shiru yayi yana kallonta kamar ba zaiyi magana ba saida yaga ta fara turo masa baki sannan yace
"ni kuma kuɗina dana baki fa?"
ɗaukar kuɗin tayi ta kikkiresu tayi musu guntu guntu baiyi unkurin hanata ba saida ta k'are  ta watsar  ta kalleshi tace "ni bana sonsu"
"mi yasa kikayi haka bakisan ba kyau yaga kuɗi ba?"
"ai ba kuɗi bane takardace nidai bani giɗata"
banza yayi mata ya ɗauke kansa saida yagata soma yi masa kuka sannan ya ɗauki giɗar ya mik'a mata ta da sauri ta karɓa tasa a ture ta tashi ta karkaɗe jikinta ta ɗora turan saman kai tayi masa murmushi ta kama hanya.

har tayi nisa sai kuma tayi juyo ta nufoshi.
kaɗan kaɗan take tafiya tana turo baki har ta karaso kusa dashi ta sauke turen ta aje masa ta fashe da kuka.
kallon kawai yake tun tana kuka ba hawaye harta fara hawayen tana shureshuren kafafunta cikin k'asa sai kallonshi take,
shima ita yaƙke kallo yana tsusar baki kamar mai mai shan minti.
sunfi karfin minti 30 a haka ita taki tayi maganar sai kuka take shina yaki yayi mata magana fadawansa sai satar kallonsu suke yahuza ko yasa earphone a kunne dan kar haushi ya kasheshi.

saida yaji ta kara buɗe baki tana kiran Gwaggo sannan ya matsa ya rik'o fuskarta ya sakar mata manya idonsa yace "mi kike yiwa kuka?"
cikin kukan tace "ba kaine ba ka jani da wasa har lokacin komawa gida yayi ban siyar da giɗa ba kuma Gwaggo bazata bani kuɗin sawa asusu ba"
murmushi yayi yasa wani bafaden sa ya kira masa yahuza.
haka ya iso gurin yana hararar Mairo.
Yarima ya kalleshi yace "kuɗin nageriya nake so"
hannu yasa aljihu ya ciro yan dubu dubu ya aje masa gabansa.
nan ne yaga kuɗin da Mairo ta yaga kallon Yarima yayi yace "wayayi wannan aikin?"
kallon Mairo Yarima yayi bai bashi amsa ba hakan ya tabbatar masa da itace 'uhmmm' kawai yace ya watsa mata harara ya koma gurin zamansa.

Yarima ya kalli Mairo yace "ɗauki ko nawa kike so"
da sauri tasa hannu ta dauki dubu uku tana dariya tace "na gode"
kai ya ɗaga mata "sun isheki?"
"eh na gode amman dan Allah ka bani wacan abun"
juyawa yayi yana kallon apple ɗin data nuna masa.
hannu yakai ya dauki ɗaya ya mika mata tana karɓa takai baki "lahhh daman haka goribar bunni take?"
murmushin gefe yayi ya girgiza mata kai "ba goriba bace apple ne"
"minene apple?"
"tuffa"
"minene tufa?"
shiru yayi dan yanzu kam baisan mi zai ce mata ba.
kamin yayi mata wata magana ta sake rokonsa
"dan Allah karamin ɗaya na kaiwa Gwaggo"
kara ɗauko ɗaya yayi ya mika mata dariya tayi ta kara rok'onsa "na gode amman ɗan Allah kara min ɗaya na kaiwa k'awata jummalo (MANIRA Lol.) da Halilu hannu yasa ya sake ɗaukowa ya mika mata.
bata bar gurin ba saida ta lisafa masa mutum takwas ya bata sannan ta tashi ta ɗora ture tana dariya tayi masa godiya tare da sallama ta nufi hanyar fita gurin tana waigensa tana ɗago masa hannu shidai kallo kawai ya bita dashi da murmushi harta fice.

© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:39 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*5*

tana tafe saman hanya tana cin apple ɗin tana ɗariya.
koda ta iso gida taci kusan guda 4 ɗayan ma da giɗa ta haɗashi ta ci a kofar gida ta tsaya ta karasa na biyar ɗin sannan ta shiga tana watsar hak'ora

Gwaggo na zaune k'ark'ashi ecce durumi taɓa jan carbi Mairo ta shigo
"fuwan (gafaran) kudai masu gida"
murmushi Gwaggo tayi jin yau abunda Mairo ta shigo dashi sabanin sallamar data saba.
kusa da ita Mairo ta zauna ta eje mata turen giɗar gabanta ta zuba mata ido.
Gwaggo saida ta kai karshen carbin ta shafa sannan ta kalli Mairo da fuskar damuwa tace "yanzu Mairo tun fitar da kikayi giɗa ɗaya kika siyar?"
ɗariya tayi ta ɗauki apple takai bakinta tace "ɗayar ma cinta nayi ba siyarwa ba"
kai Gwaggo ta girgiza "yayi miki kyau yanzu ai saiki ce na baki na sawa asusu ko na siyen wani abu"
fashewa tayi da dariya harda buga k'afa ta ɗauki apple ɗaya ta mikawa Gwaggo "Gwaggo karbi ki ci goribar bunni"
banza Gwaggo tayi mata ta kara hade fuska.
nan Mairo ta ciro  kuɗin dake lak'ame a k'ugunta ta ajewa Gwaggo
"nidai ga kuɗinki nan har ma sun ninka na giɗar"
buɗe baki Gwaggo tayi tayo waje da ido "Mairo ina kika samu wannan kuɗin mai yawa haka?"
"wani ɗan bunni ne ya bani harda wannan goribar shine ya bani kuma fa kuɗin da yawa ne nice na ɗebo kaɗan"
kallon tsoro Gwaggo tayi mata "ina kika haɗu dashi Mairo"
kwantayi tayi saman k'afafunta ta soma bata labari tun farkon fitarta.
      
Mairo na kaiwa karshe Gwaggo ta ɗora hanu bisa kai tana salati
"Hasbunallahu wa ni imal wakil innalillahi wa inna ilaihi raji'un Mairo mi ya kaike mi yasa bakisan ciyon kanki ba Mairo mun shiga uku da wannan 'ya mai ya kaiki shiga can?"

Tashi Mairo tayi zaune tana kallon Gwoggo gabanta soma faduwa.
“minene hala Gwaggo?”
“Mairo kinyi gamo miya kaiki Mairo”
baki Mairo ta saki “gamon me Gwaggo?”
kamin Gwaggo tayi magana sukaji sallamar Halilu da sauri Mairo ta shige cikin Gwaggo tana fad'in “Gwaggo karki fad'a masa”
koda ya karaso Mairo yake kallon ganin yadda ta ahige cikin Gwaggo dan yasan ruwa baya tsami banza gashi kuma Gwaggo na kuka.
“Lafiya Gwaggo miya faru kike kuka?”
da sauri Mairo tace “bata da lafiya ne shine take kuka”
risinawa yayi yana fad'in “Subhanallah mi yake damunki?”
Mairo tace “ciyon kai ne da ciki yake damunta ko Gwaggo?”
Kai Gwaggo ta girgiza Alamar 'ah ah' nan cikin Mairo ya duri ruwa hannu tasa ta toshe bakin Gwaggo tana fadin “dan Allah Gwaggo karki fada masa dan Allah”
tsawa Halilu ya katsa mata “jaye mata hannunki kona miki duka yanzu”
da sauri ta janye hannun idonta cike da hawaye.
hannu Gwaggo ya rike yana fadin “dan Allah Gwaggo ki fada min abunda ya faru”
cikin kuka ta soma fada masa abunda ya faru.
raku6ewa Mairo tayi gefe tana hawaye.

Halilu ya juyo yana harararta yace "ashe haukarki Mairo har takai kiyi wannan kasadar?"
Gwaggo tace "ni tsoro ma nake ji in basu shige mata ba"
Halilu yace "wane irin shige mata Gwaggo aini bako ta aljanu nake ba ya mutanen nan nake yan yankan kai ko yan iska tunda zamani yanzu ya chaja babu babba babu yaro inma aljanune ai da sauki"
sai a lokacin wannan tunanin ya zowa Gwaggo kallon Halilu tayi tace "kana da gaskiya Halilu tunda kaga harda goribar burni ya bata wata kila akwai abu a ciki"
Kallon apple ɗin dake saman ture Halilu ya kalla "ragowarce nan?"
"eh itace taci guda shida tace koma minene ai ta cinye shikenan"
da kuka ta karasa maganar.
Ayatul-kursiyu Halilu ya karanta sannan ya ɗauki sauran biu da suka rage ya jefar bayan gida ya juyo gurin ecce durumi ya kallo ya hau Mairo da duka.

ihu take tayi ko ina ana jinta babu wanda take kira sai Gwaggo tana faɗin kasheta zaiyi.
wannan karon kan Gwaggo ba tayi unkurin hanashi ba dan itama ta tsorata da lamarin Mairo
mak'ota ne suka shigo suka caceta koshi daker dan mugun rik'o Halilu yayi mata saida bulalar ta kwanta mata a jiki.
kowa tambayar yake dalilin dokan da akayi mata Halilu dai baice komai ba ya fice Gwaggo ce take cewa kuɗin tallah ta zubar kuma an sata aiki taki tayi
wasu dai basu yarda ba dan sunsan yadda Gwaggo take son Mairo duk abunda zaisa ayi mata wannan dukan ta kyale batayi magana ba ba karami bane.
haka suka fice kowa da abunda yake faɗa,

                 '''*   *   *'''
kuka kan Mairo ta shashi har ta gaji tun tana iya ɗaga murya har ta koma kiran baba.
tausayinta ne ya kama Gwaggo tana cikin ɗaki ta fito ta nufi ta tadata zaune tana kaɗe mata jiki "dan Allah Mairo ki rika jin magana ki gyara halinki ki daina wannan halin"
kai Mairo ta ɗaga mata tana shisshekar kuka kamar zuciyarta zata fito idonta sunyi mugun ja.
hannunta Gwaggo ta rik'a suka shiga banɗaki wannanka tayi mata sannan suka fito,
Mairo na shiga ɗaki ko kaya bata saba ta faɗa saman gado ta soma wahalallen bachi

_8:15pm..._
gwaggo ta tashe ta taci abinci.
da ciyon kai ta tashi saboda kukan da tasha gashi kuma tayi bachi hannunta Gwaggo ta riko suka fito.
saida ta wanke mata ido sannan ta nufo tabarma.
Halilu dai kallonsu kawai yake yan mamakin irin son da Gwaggo take yiwa Mairo
saida ta zauna sannan ta zaunar da ita saman cinanunta (cinyoyi) ta shiga bata abincin da hannunta.
kai Halilu ya girgaza yace "Gwaggo kinga irin wannan sagartar da kike nuna mata shi yasa take kara lalacewa tana rashin jin maganar nan"
tsaki Gwaggo taja ta watsa masa harara sai yanzu take jin haushin dukan da yayima Mairo.
bai sake ce mata komai ba harta kare bata abinci ta bata ruwa kamar wata jaririya ta zaunar da ita saman  tabarma tana k'ok'arin tashi Mairo ta rik'o hannunta tace "Gwaggo kin daina sona ko?"
dawowa tayi ta zauna tana shafa fuskarta tace "ina sonki Mairo inban so kiba wazan so  halinki ne bana so koshi kuma na rashin jin nan da kikene ina sonki Mairo"
saida ta kalli Halilu dake kallonta sannan ta sake kallon Gwaggo tace "tho miyasa kika bari Halilu ya dakeni ɗazin?"
"saboda abunda kikayi baki kyauta ba kuma inason ya zamo miki dalilin da zaisa bazaki sake irin abunda kikayi ba ko makamancinshi"
jikinta ta shiga nunawa Gwaggo da ko ina kwancin bulalane "amman Gwaggo ai kwarai dakeni dubi jikina kuma inata kiranki ki ceceni kika kyaleni"
"na daina Mairo daga yau babu wadda zai sake dukanki bazan bari ba kiyi hak'uri kinji"
kai ta ɗaga mata tana hawaye.
Gwaggo tace “amman fa ki rika jin magana kinji?”
“na daina daga yau bazan sake ba Gwaggo har na mutu”
tashi Halilu yayi ya nufi kofa yana faɗin “indai dukane tho yanxu kika fara shanshi har sai ranar da kikayi hankali” kukan shagwaɓa ta shigayi “Gwaggo ce ya kyaleni bana sonsa”
“a a ki daina cewa baki son sa amman dai dukakan bazan bari ya sake miki shi ba”
kai Mairo ta ɗaga mata tana share hawaye.

© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:39 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*6*

tun daga lokacin Gwaggo bata sake bari Mairo ta fita ba.
tallar da take ɗora mata ma bata sake ba kullum tana gida ko fita zatayi saida tare da Gwaggo,

tun abun baya damun Mairo har ya fara damunta
tunani take ko ta saci hanya ta fita in kuma ta tuna da dukan da Halilu yayi mata saita tsorata duk da yake tasan Gwaggo tace mata ba zata sake bari ya dake taba.
tana zaune ta raffka uban tagumi tana tunanin karyar da zatayiwa Gwaggo da zata sa ta kyaleta ta barta fita,
can wata dabara tazo mata
tashi tayi ta koma kofar ɗakin gwaggo ta fasa kuka tana murgemurge
da sauri Gwaggo ta fito tana tamabayarta “lafiya Mairo mi nene?”
“ni gidansu Jummala nake son zuwa ba tada lafiya”
shiru Gwaggo tayi tana kallonta dan tasan rigimar ce ta tashi
“nidai babu ruwana kinsan halin Halilu in yanxu yazo bai ganki ba faɗa zaiyi”
“tho ai ba daɗewa zanyi ba kuma ai ba zaki faɗa masa ba”
Gwaggo bata sake cewa komai ba ta nufi tabarma ta zauna.
Mairo na ganin haka takara ɗaga murya tana ihu
cikin faɗa Gwaggo tace “tashi kije kuma duk kika daɗe babu ruwa daga can kuma karki biya ko ina”
tashi tayi tana dariya daman kukan kawai take ba hawaye.
“amman dai zan biya giɗan tsoho ko tunda kusa ne”
“nidai ba ruwana keda Halilu”
“eh na yarda”
da gudu ta fita gidan

bata tsaya ko'ina ba sai gidansu jummala wuni sukayi suna shiririta basu can basu nan.
sai da bayan magariba sannan ko wannensu ya nufi gida
da fargaba ta shiga gidan tana lek'e2
bakin k'ofar ɗakin Gwaggo ta hango Halilu zaune farin wata na haskashi.
faɗuwa gabanta yayi ɗan tasan ita yake jira zagi ta shiga zabga masa cikin ransa.
_hege mai katon kai mai kamada zabarmawa ni dai wlh ka takuramin Allah kasa ma ya mutu mai idon mage (mussa) mai kan ɓera_
ta daɗe gurin tsaye tana kallonsa wai ko zai tashi amman sai kara gyara zama yake.
kamar ta fasa kuka ta shiga kwalawa Gwaggo kira _Gwaggo Gwaggo Gwaggo a dawo_
ɗagowa Halilu yayi yana kallon k'ofa yace “to shigo mana aike ake jira”
k'in shigowa tayi ta cigaba da kwalawa Gwaggo kira “Gwaggo ke ki taho mana gani”
ta daɗe tana kiranta sannan ta fito sanye da hijab da alama sallah ta k'are,
har kofar gida tazo ta kama hannunta suka shigo.
tashi Halilu yayi yana k'ok'arin rikota Gwaggo ta tare “kyaleta Halilu ni na aiketa”
“Gwaggo ki daina goya mata baya tana k'ara lalacewa”
“tho mi nayi da zakace na goya mata baya bana son raini fa Halilu”
“wane irin aikene zaki mata tun da maraice sai dare zata dawo”
Mairo ta turo baki tana watsa mata harara “ai bada maraice bane da rana ne”
buge mata baki Gwaggo tayi “ke yiwa mutane shiru dake ake ne”
kai Halilu ya girgiza “yayi miki kyau ai kamaki zanyi saiki faɗi wadda ya aikeke”
kuka Mairo tasa “Gwaggo kinji ko dukana zaiyi”
“ba zai dakeki ba bani na aikeki ba”
“hmmm Gwaggo ina miki tsoron wata rana ki daina goyawa Mairo”
“wai miyasa ka rai nanine Halilu karya zan maka kenan na faɗa maka aikenta nayi”
taɓe baki yayi ya girgiza kai ya fice.

kwafa tayi da taga ya fice “kai mugu bakin azzalumi to zo ka dakeni ɗin”
sakin hannunta Gwaggo tayi ta shiga mata masifa “ban rabaki da rashin kunya ba kuma kinsan saida mukayi dake bazaki daɗe ba kikaje kika zauna har dare”
turo baki tayi “to ba shine daren yayi saurin yi ba kuma kinsan na daɗe ban fita ba kuma...”
bata karasa maganar ba Gwaggo ta katsa mata tsawa “ke dan Allah rufe min baki 'yar rashin ji kuma ki wuce kije kiyi sallah kici abinci”
da ture2 ta nufi ɗaki tana gunguni.

_Washe gari..._
tun safe Mairo tasa Gwaggo gaba tana rokonta tayi mata giɗar siyarwa,
sai faman rantsuwa take mata wai bazata sake yin abunda tayi ba.
sam Gwaggo kin yarda tayi duk da magiyar da tayi ta mata
Mairo na ganin haka ta sawa Gwaggo kuka ba k'akkautawa harda su shak'ewa tana murje murje cikin kasa duk ta bata kayan jikinta.
banza Gwaggo tayi da ita duk da bata son kukanta amman ta daure.
haka ta wuni tana kuka ta kuma yi sa ah Halilu bai dawo gidan ba tun fitar da yayi da safe. 
          saida ta gaji dan kanta ta shi ta dawo kusa da Gwaggo dake tukin tuwo ta zauna tana ajiyar numfashi,

    Gwaggo saida ta gama kwashe tuwon ta kai ɗaki sannan ta riko hannunta suka shiga banɗaki tayi mata wanka.
har suka fito bata daina ajiyar zuciya ba idanuwanta duk sun kunbura sunyi ja
saman gado Gwaggo ta zaunar da ita ta ɗauko doguwar rigar atamfa tasa mata,
ta kwantar da ita saman jikinta tana shafa bayanta
lafewa Mairo tayi in banda ajiyar zuciya babu abunda take sauke
sun daɗe a haka Gwaggo sai buga mata baya take tana son tayi bachi ita kuma taki tayi bachin sai faman sauke wahalallen numfashi take.
kai Gwaggo ta girgiza tace “ni kan Mairo kina bani mamaki ace bakida aiki sai kuka sai ja magana sai masifa haka kawai ki wahallarda kanki dubi yadda kika wuni kina kuka”
nan sabon kuka ya zo mata “to bake bace kika ki yarda kimin giɗa ba kuma na faɗa mki bazan sake ba”
da in'in niyar kuka take maganar tana numfashi da karfi kamar zuciyar zata fito

bubbuga bayanta Gwaggo ta shigayi tana faɗin “halinki nake tsoro Mairo karkije ki sake yin wani abun kuma kina ganin yadda Halilu ya sa miki ido jira kawai yake kiyi wani abun bama hHlilu kaɗai ba harda makota jiraye suke dake Mairo ke kuma gaki baki jin magana”
ɗagowa tayi idonta cike da hawaye tace “wlh Gwaggo na daina na faɗa miki bazan sake ba in kuma na sake Allah yasa na mutu”
rufe mata baki Gwaggo tayi “Subhanallahi Mairo miye haka karki sake faɗan irin wannan maganar kinji”
kai ta ɗaga mata “na daina Gwagho zaki doramin ko gobe zakimin giɗar?”
shiru Gwaggo tayi tana tunani dan tasan Halin Mairo in kuma bata dora mata ba wata sabuwar masifa ce.
kallonta tayi tace “kinmun Alkawari bazaki sake ba bazaki yi abunda zaisa a dake kiba?”
da sauri tace “eh nayi”
“shikenan zn dora miki”
“gobe ko Gwaggo?”
“eh Allah ya kaimu”
“amin”
rumgumeta tayi “na gode Gwaggo”
“Allah yayi miki Albarka”
“amin gwaggo zaki sayamin hancin ligidi?”
“eh  shi kike so?”
“eh”
“to bari na bada a siyo miki”
kwantar da ita Gwaggo tayi ta nufi kafit (wadurup ta da tsohuwar yayi) ta bude fanteka (kwala) ta ɗauko kuɗi ta sa hijabinta ta fice.

© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:39 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*7*

_Washe gari..._
tun da asuba Mairo ta tashi tana yin sallah ta shiga karatun gajerun  surorin data iya inta kare ta sake maimaitawa har rana ta fito.

_8:14pm..._
Gwaggo na motsa kunu (koko) Halillu ya shigo gaishe ta har lokacin Mairo karatu take.
mamaki yayi sosai bayan sun gaisa da Gwaggo yace “yau yarki abun k'warai akeji?”
murmushi Gwaggo tayi “ai daman tana abun k'warai indai karatu ne ai kasan Mairo ba baya ba”
“a makarantan ba agida yaushe rabon da tayi irin wannan karatum tunfa da asuba nake jinyo ta ɗakina”
“to ai daman Mairo abunda take ai kuruciya ce data girma dainawa zatayi”
“ai da girmanta Gwaggo yanxu inta kara kaɗan ai aurarda ita za'ayi”

kuka Mairo ta fara wadda ba hawaye ta daina karantun “wlh Gwaggo bana son aure ba zanyi ba”
dariya Halilu yayi “au daman ba karatu kike ba kunnenki na kanmu ai daman nasan karatun munafirci ne”
kamar ta fasa kuka ta kalli Gwaggo “kice ya kyaleni ya tashi ya bar miki ɗakinki”
kofi Gwaggo ta janyo ta zubawa Halilu ta mika masa “karɓi ga kununka kosai na can gindin murhu a kwano”
dariya yayi bayan ya karɓa yace “dan tace ki koreni shine zaki koreni Gwaggo?”
“to naga fitina kake son jami muna zaman mu lafiya”
“ai ni gaskiya ce na faɗa kuma Mairo da kike gani aurene kawai zaiyi mata hankali ta daina abubuwan nan da take”
haɗashi da Allah Gwaggo ta shiga ganin Mairo nason yin kukan da gaske daker ta samu ya fita.
juyawa Mairo tayi zata cigaba da karatu Gwaggo ta shafa bayanta “taso haka yar Gwaggo ki karya (breakfast) ai kinyi karatun da yawa”
murmushi tayi “to gwaggo aI zaki mun giɗar ko?”
“sosai ma ai dole nayi miki bana miki alk'awari ba anjima kaɗan zanyi miki”
daɗi ne ya lumluɓe Mairo da sauri ta ɗauki kayan karatun ta aje gefe ta kwanto jikin Gwaggo ta soma bata kunun tana sha cike da jindaɗi.

_2:00pm....._
Mairo ta fita tallar giɗar k'inbi tayi hanyar da tabi ranar duk da zuciyarta na raya mata ta ɗan lek'a taga ko yana nan gashi har k'anshin goribar birni takeji tana tuna yadda take cinta.

haka dai ta daure ta nufi bakin kasuwa gurin data saba zama tana siyarda giɗar. wata yarinya na zaune a gurin tana ganin Mairo ta tashi da sauri ta koma gefe dan tasan halin Mairo indai matsifa ce saida ka barmata balle yau da fuskarta take a haɗe kamar anyi mata mutuwa.

koda la'asar tayi Mairo siyar da bakin rai ta nufo gida tana tureture baki kamar ta fasa kuka sai wata tafiya take kaɗan kaɗan.
haka ta ido gida ko sallama babu tun a bakin kofa tayi jifa da turen ta ta karaso idonta ciki da kwallah ta zauna kusa da Gwaggo dake Sallah,

tana sallamewa ta kalleta “lafiya Mairo waya taɓa ki?”
soshe soshe ta shiga yi tana tunano karyar da zatayi “ni..ni...ni....ɗan ta malele zan siya?”
shafa kanta Gwaggo tayi tana murmushi “haba Mairo sai kace wani abu harda su kwallah? ɗauki kuɗi kije ki siyo ki haɗa da kifi yadda zaki jidaɗin cinsa”
kai ta ɗaga “tho amman sai in zanje makaranta”
“tho inkin huta ki watsa ruwa sannan kije makaranta kinji”
kai ta ɗaga mata ta mika mata kuɗin giɗar.
“eyeee Mairo yau duka aka siyar gaske naji kin jefar da ture tun kofa”
murmushi Mairo tayi “yau nawa zaki ban?”
“hamsi zan baki ashiri kisa a susu talatin ki siye ɗan ta malele”
ta karasa maganar tare da mika mata 50 ɗin.,

da zumuɗi ta karɓa ta tashi ta nufi ɗaki da guɗu yau an sami abun sawa a susu mai tsoka.

    '''*** *** *** *** *** ***'''
     tun daga lokacin kullum sai Gwaggo tayiwa Mairo giɗa ita kuma bata fashin zuwa gurin siyarwa so ɗaya ta je gurinda aka bata goribar birni koda taje bata tararda kowa ba tsoro taji sosai babu abunda take rayawa a ranta sai aljani ne

“kai aljanine wannan mutunen da gaskiyar Gwaggo tunda gashi ban sake ganinshi ba kuma duk goriba karfine da ita amman tashi taushi ne da ita kuma na riga naci”
a fili take wannan maganar can ta tsaya tana tunani “inda ba aljani bane ai bazai zo cikin dajin nan ba har ya zauna kuma fa....”

bata karasa maganar ba ta watsa da gudu saboda motsin da taji cikin itacen dake gurin tana faɗin “karku biyoni na daina bazan sake zuwa ba wayyoh Gwaggo”
ihu take tayi da kuka tana gudu rabin giɗarta na zubewa,
har tabar gurin bata daina kuka ba dan gani take kamar sun biyota saida ta isa baki kasuwa sannan ta ɗan natsu ta soma numfasawa daidai,

tun daga lokacin bata kara tunanin zuwa gurin ba
duk ta ɗauko tallar giɗarta sai dai ta nufi bakin kasuwa inta siyar ta tayi ta shiririta ita da abokanin talla ko inta dawo ta biya gidansu jummala suyi gantalin da suka saba daman haka take so,

fagen neman magana da matsifa ba babba ba yaro kowa ta raina musamman inta ga ta girmeka ko kana tsoronta,
        Gwaggo in banda goya mata baya babu abunda take.
Halilu yayi faɗa harya gaji amman a banza kamar ma kara turata yake,

gashi Gwaggo ta hana ya daketa sai in ya faki idonta ko ya haɗu da ita can waje.
harta saba inta ganshi saita chanja hanya haka suka rika wasan ɓoya ita dashi.

*_3 months later....._*
yau da wuri Mairo ta siyarda giɗarta kuma yau bata jin wasa saboda dukan da Halilu yayi mata jiya dan yanzu har bakin kasuwa yake zuwa da ya tarar tana wasa ya fatattaketa da duka har gida,

duk yadda abokanin shashacinta sukaso ta tsaya kiyawa tayi dan tsan sai yazo gurin kuma Gwaggo tace mata da ta siyar ta dawo gida dan kar halilu ya daketa,
sallama tayi musu badan sunso ba dole suka kyaleta wasu kuma suka wuce gida dansu inba da Mairo ba basa jindaɗin wasa,

_Aysha adon gari ga Hajara adon gari ni Maryam adon gari inba ni ai ba gari Khadija Abubakar nake Candy kunji laqani gani tafe da'ayari yan mata a dandali_(MY UP COMING SONG INSHA ALLAH)
Mairo na tafe tana rera wak'a mak'ale da turenta na giɗa.

tunda kamin ta k'araso ta hango wata kafirar mota baqa mai shek'i fake kofar gidansu yara sun zagayeta sai shafa suke.

© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:39 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*8*

da gudu Mairo ta karaso gurin ta shiga korar yaran duk da bata san mai motarba ɗan kawai ta ganta kofar gidansu ne kuma taga yara sun zagayeta suna shafa ita yar neman masifa,

shafa motar itama ta shigayi tana dariya tana kallon kanta ta madubin motar harda zira halshe tana lasa glass tana tale idanunta (fitar da ido)
tafi kafin minti 3 ahaka sai fana dariya take kamar wata taɓaɓɓiya,

yaran sai kallonta suke suna son su kwakwayeta suna tsaron tayi musu masifa tunda taɓa motar ma ta hana su.

can ta juyo ta kallesu ta hade rai taja tsaki “mtssss ku dan Allah ku ba mutane guri kauyawan banza kawai kowa ya bar mana k'ofar gidan mu ko naa muku hegen duka”
maganar take tana wani ɗageɗage da marmaɗen ido.
          duk ja yaran sukayi da baya dan sunsan halin Mairo indai masifa ce ba baya ba
yarinya ɗaya aka bari tana watsawa Mairo harara harda kai hannu ta shafa motar tana faɗin “an shafa kema ai yar kauyece da hegen kanki”
kai Mairo ta girgiza tana dariya “hee ni kike faɗawa wannan maganar  zaki ko ci ubanki yanzu”
ɗankwalinta ta cire ta k'ulle kuɗin giɗar dake hannunta ta ɗaura ɗan kwalin a k'ugunta (kwankwaso) tayi cikin yarinyar suka hau faɗa da juna,

kaye huɗu yarinyar tayiwa Mairo dan ta fita girma kuma k'arfi ba ɗaya ba gashi  daman can  Mairo ba wani k'arfi ne da itaba sai yar banzar masifa.
ɗukan k'warai Mairo tasha a hannun yarinyar tun tana iya jurewa har takai ga fasa kuka tana faɗin “azzaluma wlh sai naci ubanki hegiya-”
Mairo bata rufe baki ba yarinyar ta kai mata wani mugun shuri.
nan Mairo ta faɗi ta fashe da kuka
da gudu yarinyar tabar gurin gudun kar Gwaggo ta ji ta fito.

kuka Mairo tayi tayi tana kallon kofar gidan ganin babu wadda ya fito yasa dole ta tashi rik'e da ɗankwalinta a hannu kanta kuma duk k'asa ta shiga gida,
da kuka ta shiga gidan ta nufi gurin Gwaggo dake bakin murhu tana eza wuta.
da sauri ta ɗago ta rikata “lafiya Mairo Halilu ne ko?”
kai ta girgiza mata ta shiga faɗa mata abunda ya faru,
ɗankwalinta Gwaggo tasa tana share mata hawaye “haba Mairo miye na wani korar yara dansun taɓa mota kuma in banda fitina inake ina faɗa da wannan yariyar?”
turo baki Mairo tayi ta ɓata fuska kamar ta fasa kuka

“shigar mata kikayi ko Gwaggo?”

“a'a wani nan na shigarwa wata na bar Mairo dukan da ta miki ne ban jidaɗiba”

“kuma harda wani mugun shuri tayi mun ina jin zafi har yanzu”

“barta da Allah kijin”
kai ta ɗaga “Gwaggo motar wace kofar gida?”

“yan birni ne suka zo ganin gida”

kusa da ita Mairo ta matso “yan bunni Gwaggo gurin wa sukazo ina suke”

“sun tafi ganin sauran dangi”
“lahh daman Gwaggo kina da yan uwa yan bunni?”

“eh kema ai en'uwanki ne tun kima karama marabinsu da nan”
risinawa Mairo tayi zatayi magana sukaji Sallama.

Gwaggo ce ta amsa masa Mairo kan ido ta sakar masa kamar bata taɓa ganin mutane ba,

harya karaso tsakar gidan shi take kallon tana masa dariya shidai kallon kawai yake kamin ya kalli  Gwaggo yace “Sannu da aiki Gwaggo”
“yauwa sannu qasin kai kaɗai ka dawo?”
“eh ina gabansu ne suna hanya suma”
tabarmar dake shinfiɗe k'arkashin ecce ya nufa ana k'ok'arin zaunawa yayiwa Mairo magana
“ke baki eya gaida mutane ba?”
tasowa tayi da gudu tazo kisa dashi ta zauna.

“na eya ina wuni?”
“lafiya kalau ya sunaki?"
saida tayi dariya sannan tace “Mairo sunana Mairo”
murmushi yayi ya kalli Gwaggo “Gwaggo ni bansan wannan yarinyar ba yar gidan nan ce?”
daga can Gwaggo ta amsa mishi “eh gidan nan take ear uwarka ce ai yar wajen margayi ce”
“wane margayi?”
“malam tanimu wadda koda kukazo gaisuwarsa bakayi aureba ita kuma tana k'arama”
shiru yayi yana kallon Mairo data washe masa hak'ora,

“na ganeta Gwaggo daman ke kike rik'onta?”
sallamar dasu Abbah sukayine ya hana Gwaggo amsa masa tambayarsa.
“amin wa'alaikassalam alhaji harku dawo?”
“eh wlh kinga kara mu kama hanya da wuri tunda munga dangi”
momi ce ta amsa mata.
bayan sun xaune Gwaggo ta nufosu tana faɗin

“ai nikan ban yaba miku ba ace mutum shekara ds shekaru rabonsa da gida amman yazo ɗai rana ai kamata yayi ace kuzo ko sati ɗaya kuyi ko biu”

ɗariya sukayi Abbah yace “har yanzu dai Jamila baki chaja ba halinki nanan na masifa”

“yau ni wani haline dani daga faɗar gaskiya”
momi tace

“karki damu jamila insha Allahu zamuzo muyi sati anan yanzu bamuzo.da shirin kwana ba kuma kinga sauran yara suna makaranta sai anyi hutu tukuna”

taɓe baki Gwaggo tayi “nidai nawa idone ai rana bata karya”
dariya suka sake yi har Mairo sai a lokacin ta gaishesu.
duk suka amsa Abbah ya shafa kanta “Maryam am girma ko?”

“ashe zaka iya gane ta ai ɗaukar ka manta”
cewar Gwaggo

murmushi yayi yace “haba dai yar tawa zan manta ko yanzu da mukaje gurin tsoho saida mukayi maganarta”
mansura ta kalleta tana murmushi tace “oh Abbah itace yarinyar da ake magana”

momi tace “eh itace yar marainiya”
“Allah sarki Allah ya jikan mahaifa”
duk suka amsa da Amin.

sun ɗan juma suna fira daga bisani Gwaggo ta kawo musu abinci.
gudun masifar Gwaggo yasa dole suka ci badan sunso ba koshi kaɗan sukaci dan tuwon dawane ba wani sonshi suke sosai ba.

kuɗi Abbah ya ciro aljihunsa masu ɗan ɗama ya ajewa Gwaggo “gashi ayi wata lalurar”
“haba Alhaji bancin abin alkharin da aka kawo?”
“babu komai jamila a daici da hak'uri”
godiya sosai Gwaggo tayi masa momi da mansura sukayi mata sallama.
suna shirin fita Mairo ta laqe kafaɗa ta bata fuska ita saita bisu.

Gwaggo ce ta shiga lallasarta “haba Mairo wane irin binsu kuma bunni fa zasuje”
“eh ina son zuwa bunni nidai saina bisu”
“kinason ki daina ganina?”
“a a ai dawowa zanyi”
Abbah ne ya dafata “kiyi hakuri Mairo kinga Jamila bata so kije ki bari har wani lokacin inmun dawo sai muje dake kinji?”
kuka ta fasa “a a ni saina biku yanzu”
Qasin ya kalli Gwaggo yace “Gwaggo ki bari aje da ita tunda tana son zuwa”
faɗa Gwaggo ta soma “babu inda zataje ita kenan ina ganinta ina jindaɗi saiku ɗauke ta to baza taje ba”
juyowa Gwaggo tayi gurin Mairo ana lallasarta ba

aiko.kamar tana kara turata sai uhu take kaar wadda aka yiwa wani abu.
Abbah tsaye yayi yana lallaɓata shima
duk yadda Momi taso su tafi kiyawa yayi dan bayason barin Mairo tana kuka gashi Gwaggo ta hana aje da ita.

suna Halilu ya shigo aiko da gudu Mairo ta tashi tayi bayan Gwaggo tana kuka,
nan ya shiga tambayar abunda akayi mata momi ce ta faɗa masa,

nan ya hau Mairo da masifa “Allah in baki yiwa mutane  shiru ba saina miki shegen duka yar iskar yarinya”
kara buɗe baki Mairo tayi tana kuka kamar wata karamar yarinya,

Gwaggo ta kalli Halilu “kaga ko ana neman tayi shiru kaxo kana mata masifa ko”

“to Gwaggo in tana son xuwa ki barta taje mana in kuma ba zataje ba su su kama hanya kar dare yayi musu”

“to waya hanasu tafiya ai sune suka hure mata kunne tace saita bisu”

Qasin yace “a a Gwaggo karkiyi zargin kowa itace kawai dan kanta tace saita bimu”
momi dai haushine yasa ta fice ita da mansura suka bar Abbah da Qasin.

Halilu yace “ni wlh da kina yarda da kinbarta taje su da kansu zasu dawo da ita dan mugun halinta”

kin yarda Gwaggo tayi saida taga su Abbah zasu wuce gashi Mairo na kuka kamar ranta ya fita sannan ta amince.
aiko Mairo kamar ta zuba ruwa k'asa tasha da gudu ta nufi ɗaki ta shiga haɗa kayanta cikin bakko (ghana most go).


© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:39 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*9*

bayan Amimcewar Gwaggo saida akaje gurin tsoho tare da Mairo aka faɗa masa shima kin amincewa yayi saida yaga abun na Mairo bana wasa bane sannan ya yarda sosai Abbah ya jidaɗi daman tun rasuwar kanensa yaso a bashi ita Gwaggo ta hana,

sai goshin magariba (kusan magariba) suka kama hanya
so huɗu ana tsayawa Mairo nayin amai jikinta sai rawa sanyi yake nan da nan zazzaɓi ya rifeta saida aka kashe ac ɗin motar,

*_9:37pm....._*
suka isa Sokoto koda Qasin yayi farkin Mairo na rungume jikin momi tana bachi.
saida kowa ya fita sannan momi ta tasheta
a firgice ta fito motar tana ɗaga kanta hankes ya cika mata ido,
gidan sama ne mai hawa ɗaya ko ina an manna gulof murza ido Mairo ta shigayi dan gani take kamar mafarki take.

bayan momi ta fito Qasin ya rufe motar shida Mansura suka nufi part ɗinsu daman Abbah tuni ya wuce nashi part ɗin,

Mairo na tsaye tana kalle2 momi ta rik'a hannunta zasu shiga ciki Mairo tayi tsaye tana kallon kofar farlon da alama tsoro take ji,

faɗuwa gaban momi yayi tana tsoron kar kuma tace bazata shiga ba.
“lafiya zomu shiga ciki mana”
shiru Mairo tayi ta lakkafe kafaɗa
saida Momi ta maimaita sannan tace “nan ne gidan?”
“eh nan ne zo mu shiga ciki”
tsaye tayi kamar bazata shiga ba
momi bata bi ta kanta ba taja hannunta suka cigaba da tafiya.
jiki a sanyaye Mairo ta shiga farlon tayiwa hannun momi mugun rik'o Usman na kwance saman doguwar kujera yana bachi siraj kuma na kallo,

shine ya taso ya tari momi da far'ah “sannu da zuwa momi”

“yauwa sannu siraj baka kwanta ba?”

kayan dake hannunta ya k'arɓa yana faɗin “eh ban kwanta ba wacece wannan momi?”

kallon Mairo momi tayi “qanwarka ce”

“daga can aka zo da ita?”

“eh bari na shiga ciki”

Up stairs momi ta nufa Mairo na rik'e da  hannun Momi,
suna shiga bedroom Momi ta faɗi zaune saman bed ita da Mairo,
har lokacin tana  rike da hannunta

bayan sun ɗan huta Momi ta nunawa Mairo tawel “jeki ki ɗauki ga tawul can ki ɗaura sai kiyi wanka kici abinci ki kwanta”
kai Mairo ta girgiza “a'a nidai Gwaggo wanke min kafafu kawai take in zan kwanta bata min wanka”
“to mu wanka muke in zamu kwanta tashi ki cire kayanki”
tashi Mairo tayi ta nufi gurin da Momi ta nuna mata.
itama Momi tashi tayi ta shiga cire kayanta

saida ta gama wanka sannan ta kira Mairo tayi mata
tare suka fito  Mairo bata tsaya jiran komai ba ta faɗa saman bed
Momi kuma ta nufi waduraf tasa kayan bachi ta ɗaura zane sama bayan tasa hijab ta kabbarta sallah.

koda Momi ta gama sallah Mairo tayi bachi.
tana cire hijab ɗinta ta nufi down stairs.
bata daɗe ba ta shigo ɗakin da plate din abinci a hankali ta shiga tada Mairo amman hakan bai hanata farkawa a firgice ba.
“k'arɓi ga abinci kici saiki kwanta”
kin k'arɓa tayi ta tsurawa Momi ido can kuma ta mayarda su gurin abinci.

sakwarace da miyar agutsi da namomi hannun tasa ta k'arɓa “ni bazan iya cinyewa duka ba”
“ci kibar saura”
kusa da ita Momi ta zauna tana amsa waya.

saukowa Mairo tayi kasa ta hau cin abinci
cikin yan mintuna ta kare ta tashi tana suɗar miyar dake plate ɗin duk ta ɓata gurin da miya kamar mai ɓararen baki.
nunawa Momi hannunta tayi “na kare ina zan wanke hannuna?”
toilet Momi ta nuna mata
tana gyaran ɗaurin tawul ta shiga toilet ɗin

koda ta fito Momi ta gyara gurin tana mopping
tsaye tayi har momi ta kare ta nuna mata gado “hau ki kwanta”
ba musu ta hau Momi taja zanen rufa ta lulluɓa mata.
ta kashe wutar ɗakin ta kunna ta bedside lamp ta nufi kofa,
Mairo na ganin zata fita ta tashi da sauri “ni kaɗai zaki bari nan?”
Momi daga gurin da take tsaye tace “tsoro kike jine?”
“eh bazan iya kwana ni kaɗai ba”
“babu abunda zai sameki ki kwantar warki kiji?”
“aa ni bazan yarda ba”
saukowa tayi ta nufo Momi.
Momi tace “to bari na kunna miki wutar saiki kwanta kamin nazo yanzu zan dawo jeki kwanta”
lake kafaɗa tayi “a a ni bazan yarda ba”
tsawa momi ta katsa mata “wuce kije ki wanta nace”
jiki na ràwa Mairo ta faɗa saman gado ta ɗanne fuskarta cikin katifa,
Momi na ganin haka ta taja kofa ta fice

kuka Mairo tayi tayi kaɗankaɗan kuma ta kasa ɗago kan dan tsoron kar taga wani abu har bachi ya ɗauketa.

*_washe gari....._*
tunda asuba Momi ta tada Mairo
a firgice ta farka jikinta sai rawa yake hannun momi ta rika suka shiga banɗaki tare sukayi alwala.
bayan sun fito Mairo ta nufi yar zakarta ta zazzage ta ɗauki wata atamfar kauye tasa tare da hijab ta fara sallah,

tana sallamewa komai bata tsaya yiba  ta koma bachi.
sai 8 da minta ta farka koshi dan siraj ya tada tane.
da murje murjen ido ta tashi tana mik'a idonta a lumshe tana soma kiran gwaggo.
“ke tashi momi na kiranki nace”
‘to’ tace tana turo baki kamar ta fasa kuka
shidai bai tsaya jiranta ba ya fice,

saida ta gama gunguninta sannan ta tashi ta nufi kowa duk jin take bata son gidan,
tana fitowa ta hango farlo down stairs.
wani irin ihu ta saki saboda juwa data gani tayi bayabaya tana kiran “na shiga uku wayyo Gwaggo na bani mutuwa zanyi”

duk kai suka ɗago sun Kallonta daga dining area siraj ne ya fara tambaya “lafiya?”
cikin kuka tace “na bani bazan iya saukowa ba na shiga uku Gwaggo”
duk fashewa sukayi da dariya banda siraj da yaja tsaki sai kuma Momi data hau mata faɗa “ke wai wane irin iskancine dake haka haka kawai zaki rika yiwa mutane uhu”
Qasin dake tsaye ya kalli Momi yana murmushi “tsorone taji momi kinsan yar kauye ce”
“to dan taji tsoro sai tayiwa mutane ihu iskancin da takeyi can kauye nan bazan ɗauke shiba”
tea cup ɗin dake hannunshi ya aje ya nufi up stairs.

hannunta ya riko ta rumgumeshi iya karfinta ta kulle ido gam sannan suka sauko.
har suka isa dining bata buɗe idon ba saida taji an zauner da ita sannan ta buɗe ido tana kare musu kallo,

da Qasin ta fara sannan Usman, Siraj sai kuma ta juyo gun Nura.
kofin tea Momi ta aje mata idonta cike da hawaye ta ɗauka ta kai baki
bata ajeba saida tasha rabin kofin Siraj da Nura da Usman sai dariyarta suke Qasin Murmushi yayi ya kalli agogon hannunsa yace “Momi ni bari na wuce gurin aiki”
“to Allah ya tsare”
“Amin”
saida ya kara kurɓa tea ɗin sannan ya fice.

Usman ya kalli Mairo yana driya yace “bakison bredin hala?”
banza ta masa har Momi ta kare cin abincinta da Usman suka tashi.
sannan ta ɗauki bredin tana hawaye ta rika somawa kamar turo da miya tana ci.

© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:39 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*10*

Siraj dai sai kallonta yake can yaji bazai iya zurewa ba yace “wai mi kike yiwa kuka?”
cikin kukan tace
“ni gida nake so”
dariya yayi “gida?”
“eh”
“mi aka miki to?”
“bana son gidan nan bana son gida a sama kuma mumi faɗa take min”
fashewa sukayi da dariya Nura yace “hala baki taɓa ganin gidan sama ba?”
“eh nidai bana sansa”
tashi nura yayi yana faɗin “amman gaskiya kauyancinki yayi yawa”
k'ara turo baki tayi kuka nason fito mata fili Siraj dai kallonta kawai yake har ya kare cin abinci ya tashi,

Mairo tasowa tayi ta dawo kusa da doguwar kujera dake parlour ta zauna har lokacin hawaye take.
jin tafiyar momi yasa ta ɗago kai tana kallon up stairs “lafiya kike kuka?”
fuskar momi a haɗe take mata tambayar
“gida nake so gurin Gwaggo”
murmushi momi tayi “karya kike yi ai ke kika dage saikin biyomu jiya jiya muxo yau kice a kaiki gida babu yadda bayiba akan ki zauna kika ki”
hannayenta ta haɗe tana rokon momi
“na daina mumi bazan sake cewa a zo dani ba”
“uhmm tashi muje kicin kiyi wanke wanke”
lake kafaɗa tayi “ni ban iya wanke wanke ba”
kunneta momi ta kamo “ke bari kiji na faɗa miki iskancin da kike can kauye nan bazaki min shiba”
kuka Mairo tasa sai kiran Gwaggo take.

haka momi taja hannunta suka nufi kicin.
gurin wankewanke momi ta nuna mata ta “oya sa hannu ki wanke” kallon momi tayi idonta cike da hawaye tace “wlh ban iya wanke wanke ba”
“dukanki dai kikeso nayi kamar zakice baki iya wanke wanke ba kuma rikon kauye ba birnin ba koki wanke shi ko na miki dukan tsiya” momi na kaiwa nan ta juya tabar kicin ɗin,

haka Mairo ta hau wankewanke tana kuka
sama take wankewa dan har ga Allah bata iya ba tunda Gwaggo bata sata aikin komai inba sharaba koshi inta ga damane take yi.
haka ta wankesu samasama kofukan da akasha tea ma ɗaurayisu kawai tayi ta aje,
koda ta kare ta fashe tea cup ɗaya kuma duk ta ɓata gurin da ruwa ɗan kwalinta tasa ta goge ruwan ta jefashi bayan firjin.
jikinta a sanyaye ta nufo parlour tsaye tayi tana kallon momi dake zaune saman kujera.
ganin bata kula taba yasa ta karaso kusa da ita “na kare”
sai lokacin momi ta kalleta “to wuce kiyi wanka”
“ina?”
“inda kika ga na miki jiya”
lake kafaɗa tayi tayi baya baya “ni bazan hau sama ba gaskiya”
taɓe baki Momi tayi ta cigaba da kallon tv.

*****
ranar Mairo wuni tayi tana kuka saboda faɗan da momi tayi mata kuma ta hana mata abincin rana saboda takiyin wanka.

da magariba Mairo na gefen kujera zaune Momi ta nufi kofa da sauri Mairo ta tareta tana “ni ki bani abincina yunwa nake ji”
tureta momi tayi saida ta faɗi wani mahaukacin ihu ta saki momi saida ta rufe kunnuwanta ta hau shurenta.
“lafiya?”
Qasin na shigowa abunda ya fara tambaya kenan

momi ta nunata da yatsa “rainin wayo ne da ita so nake na gyara mata zama”
karasawa yayi ya tada ta “mi tayi momi?”
“iskancin da take can kauye ne take son tamun”
kallon Mairo yayi “mi kika mata?”
cikin kuka Mairo tace “ban mata komai ba muguwace azzaluma ƙk'atuwar banza kuma ban yafe miki b-”
da sauri Qasin ya rufe mata baki “ke karna sake ji ba mamanki bace”
kai ta girgiza tana hawaye “ni ban sonta ba mamana bace”
kwafa momi tayi “aiko kashinki ya bushe cikin gidan nan”
“wai minene mafarin wannan abun ne momi?”
momi tace “rantsuwa nayi duk batayi wanka ba bazan bata abinci ba”
kallon Mairo yayi “ke mi ya hana miki wanka maryam kin fi son ki zaina da k'azanta?”
“a a itace tace saina hau saman sama sannan nayi wanka ni kuma tsoro nake ji”
kallon momi yayi yana murmushi “kinji momi tsoro take ji kinsan ko ɗaxun saida aka saukarda ita”
“ba wani tsoro iskancine kawai”
“ba iskanci bane ko?”
ya tambayi Mairo kai ta ɗaga yace “bata hakuri sai kuje tayi miki wanka kuma karki kara rashin kunya kinji”
saida ta daɗe sannan ta kalli momi kasa2 tace “yi hakuri bazan sake ba”
da ita da dashi duk tsurawa momi ido sukayi sunajiran abunda zatace

saida ta watsa masu harara sannan ta fixgi hannun Mairo suka nufi up stairs.
kankame momi Mairo tayi ta rumtse ido nan momi ta sakar mata hannu “wuce da kanki”
kuka tasa nan momi ta katsa Mata tsawa dole ta rike karfen ta rika hawa da rumtsen ido har ta haye.
momi ce tayi mata wanka Mairo kan ana mata wanka tana tunanin yadda za ayi ta tsera ta gudu ta bar gida,
bayan sun fito momi ta wulgo mara kayanta ta sauka downstairs ta ɗebo mata abinci.

*_washe gari....._*
tun asuba momi ta tada Mairo bayan sunyi sallah bata barta ta koma bachi ba suka nufi kicin.
tare suka haɗa komai na breakfast ranar momi batayi mata faɗa ba dan tare sukayi komai duk da ba wani iyawa tayi ba daman momi abunda bata so ta saka aiki kaki da kuma kuka.

*_8:30am....._*
suka kare hada komai momi ta nunawa Mairo gurin da zata jera.
ba musu ta rika jera abinci badan ranta yaso ba sai dan gudun matsifar momi aranta kan ɗebima momi albarka kawai take tana aiban ta'ta.
Mairo ce ta fara zama bayan ta jere breakfast ɗin sannan momi,
Usman da Nura dake zaune saman kukera suka nufo dining.
Siraj sai janta yake ita kuma ta wani haɗe fuska kamar ta fasa kuka .
momi da kanta ta zubawa Mairo breakfast su kuma suka shiga zubawa kansu.
Nura ya kalli Momi yace “yau yaya ba zai karya nanba ?”
momi tana k'ok'arin zuba ma kanta tace “zaizo mana ai kasan nan yake karyawa kila bai tashi bachi bane”

kamar daga sama sukaji an banko kofar parlour duk juyawa sukayi suna kallon Qasin daya shigo fuska a haɗe.
yana karasowa momi tace “lafiya?”
takardun dake hannunsa ya nunawa momi cikin zafin rai yace “kwangila ce Yarima yakai a kanfaninmu”
murmushi momi tayi “wow...-”
tare numfashinta yayi ya juyarda fuska “haba momi kamar bakisan Yarima ba he just want to ruin my life kuma deal ne between me and him saina gani tsakanin ni da shi who is going to be loser”
tashi momi tayi ta daga hannunta da niyar yi masa magana sai kuma ta kasa jefarda takardun yayi ya fice cike da bacin rai.

*HAPPY JUMMA'AT MUBARAK.*
_i Really Need Your Prayers fans Ina Ciyon Zuciya_

© *Khadeeja Candy*
[11/10, 2:12 PM] ‪+234 806 053 5947‬: © *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:39 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*11*

sanyi jikin momi yayi ta kasa kai komi bakinta Nura da Usman ne kawai suke cin abinci shima Siraj ya damu sai kallon momi yake,

tashi momi tayi ta nufi gurin daya watsarda takardun ta shiga haɗawa.
saida ta haɗesu guri ɗaya sannan ta kalli Siraj daya juyo yana kallonta tace “Siraj jeka kiran min yayanku”
kai kawai ya ɗaga mata ya tashi ya fice.
Mairo dai sai satar kallonsu take tana tsomen beredi,

guri momi ta samu ta zauna dafe da kai kamar mai mata ciyo.
tana haka Qasin da Siraj suka shigo dining Siraj ya nufa Qasin kuma ya nufota yana faɗin “gani momi”
kujera momi ta nuna masa har lokacin tana ɗafe da kai.
bayan ya zauna ta kalleshi tace “Qasin ka rika hakuri kasan da wadda kake zama Qasin ni bana tunanin saboda ɓata maka suna ko karyarda kai Yarima ya ɗauki kwangila ya baka”

kawar da kai yayi alamar bai jidaɗin maganar ba.
ganin haka yasa momi ta taso ta dawo kusa dashi ta zauna “Qasin ni a ganina kamar ma Yarima yana son ɗaukaka kanfaninku ne”
juyowa yayi ya kalleta “a a momi so yake ya karya ni kawai kuma bazan taɓa yarda da wannan kwagilar ba ba zai taɓa cinma burinsa a kaina ba”

dafashi momi tayi “ban sanka da zuciya haka ba bana son ka runtse ido ka yanke hukuncin da zai zamar maka nadama nafison ka yanke hukunci ido a buɗe
bana son abunda zai saka cikin matsala Qasin”

kallon momi yayi yana nazarin kalamanta can ya lumshe ido ya sauke ajiyar zuciya ya sake buɗe idon yace “momi banida mafita sai wannan momi bana son Yarima yayi nasara a kaina momi ki duba min plz”
itama Momi ajiyar zuciya ta sauke tace “baka ganin mayarda kwangilar zai zame maka matsala?”

“zai iya zama kan dan lokacin da zai bada kwangilar tare da yan jarida yazo”
“to karka kuskura ka mayarda kwangilar zai zubar muku da mutuncin kanfani”
“momi ba nida wata mafita sai wannan”
“haba Qasin sai kace kai ba namiji ba kai bakasan yadda zaka sarrafashiba ka bashi kunya ka taka abunda ya taka Qasin ka zama gawurtaccen namiji ba rago ba”

Siraj da tunda ake maganar hankalinsa na gurin tasowa yayi yana faɗin “yes yaya kaima namijine ka ya k'eshi ks kara ɗags martabar kanfaninka kabi shawarar momi plz”

ajiyar zuciya Qasin ya sauke a karo na uku ya kalli momi “momi ba hannuna da nasa ya bani kwangilar ba PA ɗina yaba kuma banida tambas dan zai iya haɗa kai dashi ya cutar dani”
Siraj yace “ka chanja PA kawai”

“haba Siraj how many PA I have to change just because of him? PA 4 na chanja akanshi bazan sake chanja wani ba not anymore”
cikin faɗa yake maganar jijiyar wuyansa na tashi da sauri Usman da Nura suka juyo suna kallon su, Mairo kara sakin baki tayi tana kallonsu daman hankalinta yana gurin,

dafashi momi tayi “ga wata shawara Qasin”
kai ya ɗaga mata ba tare daya kalletaba ‘uhmm’
“mi zai hana ka karɓi kwangilar kayi da kanka?”

murmushi yayi mai cike da jin haushi “haba momi ai zubarda kai ne daɗi zaiji na k'arɓi kwangila da hannuna masa”
“ba faɗuwa kayi ba Qasin cigabane a gareka da kuma ɗaga darajar kanfaninku”
kai ya girgiza “momi ba zaki gane ba”

“kaine baxa ka gane ba Qasin idan kayi haka mutane zasu yaɓeka suce bakada girman kai sannan kodan kwangilar tayi ya kamata kayi haka kuma idan tayi kyau zaka jawowa kanka customers ayaba maka ka kara samun ɗaukaka”
Siraj yace “gaskiya ne yaya ka ɗauki shawarar momi”

ya daɗe zaune gurin kamin ya ɗago kai ya kalleta “shi kenan momi zanyi yadda kikace”

murmushin jidaɗi Momi tayi ta shafa kansa “Allah ya maka albarka ya shige maka gaba”
shida Siraj suka amsa da ‘amin’
tashi yayi ya nufi kofa yana sauke ajiyar zuciya,

da gudu Mairo ta taso ta nufo shi tana faɗin “dan Allah ka je dani yawo inson fita”
fuska a haɗe ya shafa kanta yace “ba yanzu ba” ɓata fuska tayi idonta suka cika da hawaye shirinta na guduwa ya rushe .
juya tayi  tana kallonsa har ya fice.

tashi momi tayi ta nufi up stairs tana faɗin “Maryam in kuka k'are ki haɗa kayan ki kai kicin ki wanke kuma ki share parlour nan ki goge”
kara ɓata fuska Mairo tayi abunda ta rsana kenan hawayen dake makale a idonta suka zubo.





© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:39 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*12*

bachi Mairo take saman kujera ta wani turo baki sai numfashi take da k'arfi,

Momi na saukowa ta tadata “ke ke ke Maryam”
a firgice ta farka ta kara turo baki fuskartar momi ta rik'o “kinyi wanke2?”
kai ta ɗaga tana murza ido momi tace “tashi kije kiyi wanka”
tashi tayi kamar ta fasa kuka ta nufi up stairs zuciyarta cike da tsoro,
rik'e k'arfin tayi ta rumtse ido tana tafiya a hankali har ta haye.

        '''*  *  *'''
Momi na kicin tana girki taji uhun Mairo da sauri ta aje robar dake hannunta ta nufi up stairs.
tsakiyar ɗaki ta tararda Mairo sai juye2 take tana kuka jikinta ba kaya kikata momi tayi “ke lafiya miya faru?”
kasa magana tayi sai toilet take nunawa momi tana tuma,

da sauri momi ta nufi toilet ɗin,
kalle2 ta shiga ta rasa dalilin dayasa Mairo kuka hankalinta bai kai gurin shower da take kunne ba sai gab da zata fita sannan idonta suka kai gurin juyowa tayi ta nufi shower da niyar kashewa,
nan hannunta ya taɓo ruwan dake zuba da sauri tayi baya baya da yar k'ara saboda ta fasasshin ruwan da suka taɓa mata hannun,

ta daɗe tsaye cikin toilet ɗin tana duba hannunta,
sannan tasa hannun hagu ta kashe shower.
koda ta fito duk'e ta tararda Mairo sai faman kuka take tana kiran ta bani ta shiga uku ta data momi tayi tana faɗin “sannu Mairo ni wlh na manta da yadda shower take mantawa ma nayi na haɗa miki ruwan da kai na yi hakuri kinji”
kai ta ɗaga tana kuka tace “ni a kaini gida gurin Gwaggo”
hakuri momi tayi ta bata daker tayi hakuri momi ta haɗa mata wasu ruwan tayi mata wanka ranar har kanta saida momi ta wanke,

da suka fito momi ta rasa kayan da zata saka mata dan ita bata ga wasu kayan kwarai da zata sa mata ba haka dai momi ta ɗauko wata tsohuwar a tamfa tasa mata,
momi ta kalleta tace “hau gado ki kwanta”
da sauri ta nufi gadon ta faɗa rub da ciki,

momi na gab da wucewa Mairo ta ɗago da jajayen idanunta ta kalli momi “mumo ko zaki aikeni?”
juyowa momi tayi “aike kuma Maryam kamar ya?”
tashi tayi zaune “in siyo miki wani abu ko aike”
murmushi momi tayi tace “a a ni babu abunda za'asiyo min koma abu zan siya saidai na aiki direba ko yara su siyo”
komawa tayi ta kwanta tana zubarda hawaye.
kai kawai momi ta girgiza ta fice.

Mairo tunda ta kwanta take wahalallen bachi sai uku da rabi ta farka koshi dan momi ta tadata ne.
hannunta Momi ta riko ta suka nufi bathroom kin shiga tayi ta lak'e kafaɗa “ni bazan shiga ba”
“yi hakuri ni zan haɗa miki ruwan ba zakiji zafi ba”
daker momi ta lallaɓata ta yarda suka shiga,

brush momi tasa tayi tare da alwala sannan suka fito,
tsareta momi tayi saida tayi sallah sannan ta riko hannunta suka nufo downstairs.

zaune suka tararda Qasin yana cin abinci laptop na gefensa yana aikin danne2.
tsaki momi taja bayan ya jama Mairo kujera ta zauna,
ɗagowa yayi yana kallon Momi “lafiya dai momi?”
saida ta zauna sannan tace “hala baka ci abincin ba?”
sosa kai ya ɗanyi yayi murmushi “indomi ce ta ɗafa”
taɓe baki momi tayi “to Allah ya kyauta ya sawwake”
kasa amsawa yayi saima kallon Mairo da yayi yace “bakida lafiya ne hala?”
kin masa magana tayi saima faman cin abincinta da take tana sauke ajiyar zuciya,

momi ce ta kalleshi tace “k'onewa tayi da ruwan zafi shine take fushi”
“ayyah sorry kijin injin bata jimu ba?”
“bata jimuba zafin daine ya raɓeta”
kanta ya shafa “sannu kinji?”
kai ta ɗaga masa tana aika lomomi,

suna haka Usman ya fito ɗakinsa ya nufi kofa.
kiransa momi tayi “Usman”
“na'am Momi”
“dan Allah jeka ɗaki ka ɗauki ATM ɗina kaje nan Damary plaza ka siyo ma Maryam kayan sawa”
“owk momi”
da sauri ya nufi upstairs.

tashi Mairo tayi jikinta na rawa tace “zan bishi mumo ina zuwa”
momi kamar tasan plan ɗinta ta zauner da ita “a a ba yanzu ba ba kasuwa zaije kuma ba daɗewa zaiyi ba”

da kuka tace “thom”
ta sunkuyarda kanta tana hawaye.
Qasin ya shafa kanta yana murmushi “yi hakuri bari ranar da nake free sai muje yawo ko ki zaga gari?”

kai ta ɗaga mishi ba tare data kalleshi.
murmushi momi tayi ta kalli Qasin tace “Qasin ya akayi da batun kwangilar?”
“na karɓa ni da kaina zanyi kuma baza a samu matsala ba insha Allah”
daɗi sosai momi taji “Allah ya taimaka ya shige maka gaba”

tashi Qasin yayi ysns faɗin “Amin momi bari naje part ɗina nayi wani aiki”
kai kawai momi ta ɗaga mishi ya fice rik'e da laptop.



© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:39 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*13*

da ɗare Usman ya kawoma Momi kayan (tufafi) data aikeshi ya siyo,
aiko murna gurin Mairo ba'a magana sai tsalle take tana wani shafar tufafin tana jefasu sama tana rawa.
duk wani bachin rai dake ranta ranar gushewa yayi sai faman godiya take yima momi.
tun abun naba Momi dariya har ya koma bata tsoro ganin irin murnar da take kamar zata haukace sai faman uhu take, tana daredare harda hawaye,

momi dai da taga ba kanta baro mata ɗakin tayi ta sauko k'asa,
nan ta tararda Qasin yana aikin rubuce2,
guri ta samu ta zauna suka soma fira.

Mairo na jin muryarsa ta kwaso tufafin ta nufo downstairs da gugu tana faɗin “Qasin kaga tufafina da-”
kasa karasa maganar tayi saboda wani mugun kaye da tasha saman tile aiko nan kuka ya chaja salo ta koma yin na gaske,

dariyace tazo ma Qasin haka ya matseta ya nufeta ya tadata tsaye yana bata hak'uri yana murza mata gurin data gimu.

momi kan faɗa ta hau yi mata “yarinya ba kai sai bak'ar hauka tun ɗazu take murnar tufafin nan kamar mahaukaciya kekan kauyenciki yayi yawa Maryam”
Qasin na dariya yace “haba momi koni ai murna zanyi inna samu sabon tufafi zuwa fa tayi ta gwada min ko?”
kai ta ɗaga masa tana kuka, handkerchief ɗinsa ya ciro yana share mata hawaye.
“ya isa haka jeki gwada tufafin mugani suna miki kyau”
da ininniyar kuka tace “thom”
ta nufi ɗaki.

tana shiga ta cire kayan jikinta ta ɗauki wata diguwar riga tasa da gudu ta fito ta nufo parlour.
bata tararda shiba sai momi dake zaune saman kujera tana kallon tv,
gurinta ta nufa tana nuna mata kayan, koɗata momi tayi tana yaba yadda kayan suka karɓeta nan dariyarta ta dawo ta rik'a tsalle tana mulmula a k'asa saida momi ta soma yi mata faɗa sannan ta tashi ta nufi ɗaki.

       ''' *   *   *'''
tun daga lokacin Mairo bata k'ara saka tufafinta na kauye ba saidai wayanda momi ta siya mata,
kuma ba laifi Usaman ya iya zaɓi dan duk tufafin data saka saisun yi mata kyau sun k'arɓi jikin ta,
kyau ta ma ba laifi da farinta sai kara fitowa yake ga gashin kanta kullum sai momi ta gyara mata shi,

taci maikyau tasha maikyau tasa maikyau wasa wasa cikin wata 2 tayi bulbul kamar ba itaba,
aiki kan yanzu Mairo ta ɗan fara sabawa dan kullum tare da momi suke haɗa breakfast kuma duk wani karamin aiki ita momi take sawa tayi tun tana fushi har ta gaji ta daina sai in taje ɗaki ta rika kuka tana zagin momi da cire mata albarka,

zancen guduwa yanzu ta daina tunda taga momi bata bari a fita da ita kuma in zata fita bata zuwa da ita babu yadda batayi ba momi tak'i yarda duk wata dabara ta ta saita rushe ta daina ma yima momi zancen ta hakura,


*_3 months later....._*
yau da far'ah Mairo ta tashi saboda tayi markin Gwaggo,
koda Momi ta shigo ta tasheta zaune ta tararda ita harma tayi alwala tana sanye da hijab,
da mamaki momi ta shiga bathroom bayan ta ɗoro alwala ta fito ta nufi waduraf tana faɗin “Maryam ya akayi yau kika rigani tashi?”
carbi ta nunawa momi tana wani gyaran murya kamar wata babbar mace wai ita mai tasbihi ba a magana,

“hmm Maryam manya”
momi ke faɗar haka tana k'ok'arin ɗaura zane,
hijab tasa ta shimfiɗa carpet ta rik'a carbin tana salati har aka tada sallah sannan suka bi zan'in masallacin dake kusa dasu,
suna karewa bayan suyi yan addu'o'e suka nufi kicin.

*_8:45am_......*
Mairo ta shiga jera breakfast a dining sai tsaki take tana faɗin “mumo yau munyi rana”
tsayawa tayi tana kallon agogn dake manne gefen gurin tana tunani yadda momi ta koya mata,

ta daɗe a tsaye tana kallon agogon ganin bata tuna ba yasa ta shiga shirmen ta “kinga fa mumi har wannan mai laulaye tayi (8) da mai k'afa ɗaya (4) da mai kai sama (9) gaskiya munyi rana yau”
da dariya momi ta fito kincin ta nufo dining tana faɗin “waike Maryam yaushe zaki daina wannan shirmen naki ne? ke kullum ana koya miki abu amman kamar kara toshe miki k'wak'walwa ake”
turo baki tayi ta nufi kujerar data saba zama ta zauna,
momi bata sake cewa komai ba ta shiga zuba mata abincin harsu Usman da Nura da Siraj suka fito suka nufo dining,

bayan sun zauna kowannensu ya shiga zubama kansa,
har suka fara ci Mairo bata ci nata ba sai kunbure2 take tana harararsu duk da momi ce take son ta harara amman ba dama.
babu wadda ya tanka mata sai Siraj dake k'ok'arin zaunawa,
“waike lafiya kike hararar mutane?”
saida tayi kwafa sannan ta kalleshi tace “ina ruwanka dani”
tashi yayi da niyar ya doketa momi ta tareshi “ai tace maka ina ruwanka da ita bai isaba?”
“tho momi baki ganin yadda take hararar mutane”
“ba da kai take ba ni take son harara bata da dama saboda nace bata gane agogo”
komawa yayi ya zauna yana dariya “LOL yarinya aike kullum liki minandak'u ce kulli yaumin ɗifɗif”
kifa kanta tayi da dining tana kuka,

momi ta kalleshi da siffar masifa “wai Siraj mi yasa kake wasa da ita ne bafa tabashiyarka bace mahaifinta da naku uwa ɗaya uba ɗaya suke”
hannu ya ɗaga “tho momi kice ta daina wasa dani”
“ai kai ka soma wasa da ita gashi har sauran suna son yi”
jan zib yayi a bakinsa alamar bazai kara cewa komai ba,




© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:39 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*14*

sai a lokacin Mairo ta ɗago kai ta soma cin abinci,

_GOOD MORNING EVERYONE_
yau da abunda Qasin ya shigo dashi kenan fuskarsa ɗauke da murmushi ya ware hannayensa hannunsa ɗaya rike da wasu file.
duk juyowa sukayi suna kallonsa rabon da suji muryar irin wannan ta farinciki daga gareshi harsun manta,
wani sanyi ne ya ziyarci zuciyar momi dan tasan duk yadda akwai abun farincikin daya faru,

yana karaso ya mika ma momi file ɗin yana faɗin “lafiya kuke kallona hakane?”
murmushi sukayi suka ci gaba da cin abincisu dan sun san ko minene dole a fasa kwai suji,

a rikice momi take karanta har tana tsalleke wasu saboda daɗi tana kare karantawa ta mike tsaye ta rumgumeshi idonta cike da hawaye
“ai daman na faɗa maka Qasin duk ka ɗauki hawarana bazaja taɓa jin kunya ba kuma ka gani”
rumgumeta yayi yana dariya “haka ne momi na”
ko wannensu kasa cin abincin yayi sai murna suke suna yaba masa suna rumgumarsa,

Mairo kan ido ta sakar musu kamar tana cin abincinta dan ita mahaukata ta ɗaukesu tunda bata gane abunda suke yiwa murna,

saida tayi tsaki sannan suka tuna da tana gurin
ɗagata momi tayi saboda murna ta tsayar da ita saman dining tana faɗin “me kike yiwa tsaki yata? yau ranar farinciki cefa”
“to ba duk kunata murna ba kuma kunk'i ku faɗa min dalili”
“ayyah to yi hakuri bari na faɗa miki yayanku ne yaci nasara akan kwangilar da aks bashi har mutumen ya yaba masa da kalamai masu daɗi”
“to minene kwangila?”
“sashi akayi yayi gini sai kuma yayi sa'ah shine muke murna”
fashewa tayi da dariya “hahaha nima Qasin nayi murna”
“to ai ba haka akeba uhu ake ana tuma”
aiko kamar jira take ta soma yin sama tana yin kasa saman dining,

juyawa momi tayi tana kallon Usman da yayi maganar “kasanfa bana son iskanci dan ba hankaline da ita ba”
juyowa tayi ta sauke Mairo tana faɗin “ke kuma kinsan na rabaki da kiran sa Qasin ko to daga yau karna sake ji”
bata fuska Mairo tayi ta soma kuka,

dafata Qasin yayi “haba momi miyasa zaki sata kuka yaufa ranar farinciki ce”
share mata hawaye ya shiga yi yana faɗin “yi hakuri yi shiru kinji?”
makkale kafaɗa tayi “ni bazanyi shiru ba”
“aiko in bakiyi shiru ba ba zanje dake yawo ba kindai san kinfi kowa son yawo ko kina so naje dake?”
kai ta ɗaga tana share hawaye.
Qasin yace “good to ysu zanje dake kodan farinciki danake”
da far'ah tace “yanzu ko?”
“a'a sai an jima inna shirya harda tufafi ma xan saiya miki kiyita tsalle”
wata irin dariya ta saki tana tunowa da momi yasa ta karasa ba ta rufe baki,

ɗagowa yayi yana murmushi ya kalli momi “thank you more. momi”
“ur welcome Qasin nafika farinciki”
“momi ai har a tv aka nuno dan da yan jarida yaje dan yayi zaton zan to zarta”
“kwata2 yau bamu kunna tv ba bamu gani ba”
“ai tun jiya ne da dare ai”
hannu momi ta daga “oh nidai Alhamdulillah ai tunda anyi nasara”

     ''' *   *   *'''
ranar wuni sukayi suna farinciki momi harda rabon kuɗi ta rikayi ko abincin rana ma kasa ci tayi saboda farinciki,

*_2:30pm......_*
Qasin ya shigo sanye da kananan kaya,
zaune ya tararda Mairo tasha doguwar rigar fakistan momi ta mata farkin ɗin kanta kamar wata balara sai ɗan gyale na abayar da take rike dashi,
ta wani hakinci kamar wata princess ga bakinta yasha mai yar girace kawai momi batayi mata ba,

tsayawa yayi yana kallonta kamin ya kai hannu yaja hannunta su taɓe “eyye yarinya haka momi ta gyara ki?”
da sauri ta tashi tsaye “eh daman kai nake jira tun ɗazu”
murmushi yayi “to yayi kyau bari naga momi sai muje kinji?”
kai ta ɗaga masa ya nufi stairs.

bai daɗe ba ya fito ba mairo ta mika masa hannu ya rika suka fice yana yaba kwaliyarta,
suna kaiwa parking space ya buɗe mata giɗan gaba ta zauna shi kuma ya shiga driver seat. yayima motar key suka fice,

wuni sukayi suna yawo duk gurinda suka ga wani abun kwadayi sai ya tsaya ya siya,
Qasin yasha dariya saboda Mairo take murna kamar wata taɓɓabiya.

*_4:52pm....._*
suka nufo gida Mairo sai surutu take masa shidai tun yana dariya harya koma murmushi,

daf ta zasu shiga gida ta tuno da Alkawarin da yayi mata na siya mata kaya,
aiko nan tasa mai kuka dole ya juya ya nufi Dubai mall. suna isa ta shiga k'ok'arin rigansa fita amman ta kasa dan bata san yadda ake buɗewa ba,

saida ya fita sannan ys buɗe mata kofar ta fito sai dariya take tana yaba kyaun gurin,
suna shiga ta nufi wani gurin saida ya riko hannunta suka nufi sashen yara,
sannan ya saketa ya ɗauki basket ya mika mata ya riko kunnenta “karki kuskura wuce ɗauko kala uku uku kawai zaki ɗauko kinji ni ai?”
kai kawai ta ɗaga mishi badan ta fahimci mi yake nufi ba dan hankalinta nacan gurin kayan data gani,

haka ta nufi kayan tana wani leko harshe kamar karya tana shafa kayan.
tafi karfin minti 20 tana duba kayan sannan ta ɗauko kala biyar ta nufoshi tana dariya “duba kaga suna da kyau sosai”
ɗaya bayan ɗaya ya rika dubasu “haba Maryam har huɗu keda nacewa uku?”
“nidai su nake so”
“a rage kinji?”
lake kafaɗa tayi “a a nidai duka”

bai sake cewa komai ba ya nuna mata gurin biyan kuɗi “ɗauki ki kai can”
da sauri ta ɗauki kayan ta rigashi isa,
ana cikin lissafi ta ɗauko wata riga ta ɗora “harda wannan inaso”
bakin baki Qasin yayi yana kallonta can dai yaji tsoron ta sake ɗauko wani abun ya nuna mata kofa “Maryam jeki gurin mota ki tsaya harna fito kinji?”
ba musu ta fice ta barshi,

tsaye tayi jikin motar tana wasa da hannayenta duk wadda zai shiga saita faɗa masa akwai kaya masu kyau a ciki,
wasu basa kulata wasu kuma suyi ta dariyarta,
tana haka Yarima yazo shiga cikin wasu tufafi na alfarma fadawansa na take masa baya,
nunashi Mairo tayi tana faɗin “kai ma kayi sa'ar zuwa nan kayan suna da kyau”
kwatakwata bai lura da itaba sai a lokacin ya juyo ya kalleta a ransa yana _wani sabon tsari suka samune nasa yara sunayiwa mutane welcome_
suna haɗa ido Mairo tayi waje da ido “lahhhh kaine”
kayanshi ta shiga shafawa tana ɗaga masa gira.
can ta shaa nata kayan tana juyi tana rawar kai “ni ka gani yanzu kaya masu kyau nake sawa”

shikan kallonta kawai yake yana tunanin gurin daya santa. dan jikinshi yana bashi ya santa,
saidai ta ɗan kwanta masa lumshe ido yayi yana tsusar hot pink lips ɗinsa faɗawansa dai sai kallonsa suke da k'warorin mutanen dake guri

bai buɗe idon ba sai da ya tuna da murmushi ya rika fuskarta “ya akyi kikayi kyau haka? waya kawoki nan?”
saida tayi dariya sannan tace “yaya kuma momi ce tamun kwaliya”
“wane yaya?”
kamin ta bashi amsa Qasin ya fito ya nufosu fuskarsa ɗauke da mamaki.

nunashi Mairo tayi “gama shi nan”
kai ya ɗaga mata yana wani shu'umin murmushi.
Qasin na karasowa Yarima ya mika masa hannu “thanks to yhu once again My Men for the contract”
kallon hannun kawai Qasin yayi fuskarsa babu yabo ba fallasa ba tare daya amsa ba yace “ur welcome the perfect one”
murmushin fuskar Yarima ne ya kara faɗaɗa,
Qasin bai saje kylashi ba buɗewa Mairo mota “ke shiga muje”
da sauri ta shiga tana ɗagawa Yarima hannutana sama byebye.

da wani irin karfi Qasin yaja motar har saida Mairo taji tsoro,
Yarima yayi tsaye yana kallon motar har suka bace masa.



© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:40 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*15*

tunda suka shiga motar Mairo kasa magana tayi saboda tsoro saima rike bel ɗin motar da tayi,
shima bai tanka mata ba saida suka kusa isa gida sannan ya soma magana ba tareda ya kalleta ba “ina kika sanshi Maryam?”
shiru tayi kamar ba zata amsa ba saida ya sake maimai tawa sannan tace “can gida na sanshi harda kuɗi yake bani da goribar bunni ba na taba faɗa maka wani yaban goriban bunni ba?”
kai ya ɗaga mata “eh ina ya haɗu dake?”
“can gida”
“gida ina?”
daidai nan suka iso gida yana yin parking ta yinkura zata taji bazata iya buɗewa ta juyo ta kalleshe “buɗe min zan fita”
yana kallon kallon fulawoyin gidan yace “sai kin faɗa min gurin da kika sanshi?”
kamar ta fasa kuka tace “bana ce maka can gida ba”
sai a lokacin ya kalleta “to ai baki min bayani yadda zan gane ba”
ganin babu sarki sai Allah dole tasa ta faɗa masa tun farkon haɗuwarsu,

“to tun daga lokacin baki sake ganin shi ba sai yanzu?”
“eh nidai buɗe min na fita”
“to ya akayi ya ganeki?”
“nidai ba shine ya ganeni ba ni ban saniba”
bai sake ce mata komai ba ya buɗe motar ya fita,
ya zagayo gefenta ya buɗe mata ta fito da guɗu ta nufi parlour. bayan ya rufe motar ya rufa mata baya,

parlour suka tararda momi da gudu Mairo ta faɗa jikinta “kinga yaya ya simin mai kyau”
dubawa Momi ta shigayi tana yabawa “eyyye yar yayanta duk ke kadai?”
“eh ni kuma na zaɓo kuma mukaje yawo”
“amman gaskiya yana ji dake to injin kin masa godiya?”
“eh na masa ko yaya?”
kai ya ɗaga mata yana murmushi
“eh kinyi bama iyaka”
“naji je ɗaki ki aje”
“to”
tashi tayi tana dariya ta nufi ɗakin.

momi ta kalli Qasin tace “magana nake son muyi dakai Qasin mai muhimmanci”
agogonsa ya kalla “owk momi amman fa kamar lokacin Sallah yayi”
agogon ɗakin momi ta kalla “inaga ma an soma sallar wani gurin jeka masallaci kawai nima bari na tashi nayi sallah gobe mayi maganar”
‘to’
kawai yace ya tashi ya fice jiki yake baya son maganar duk da bashi da masaniya akan abunda zasu tautauna,

*_washe gari....._*
da safe Qasin bai lek'a part ɗin momi ba ya wuce gurin aiki,
bai shigo gidan ba sai dare part ɗinsa ya fara wucewa saida yayi wanka ya sauke gajiya sannan ya nufo part ɗinta,
zaune ya tararda momi tana hamma Mairo na kasan carpet tana bachi Usman da Nura ma duk bachi suke saman kujera,
ta dasu Qasin yayi yana faɗa “momi sai ki rika barinsu suna miki bachi saman kujera manya dasu kuma maza”
“ai nasha musu magana har na gaji”
masifa Qasin yayits musu da suka farka basu dai ce masa uffan ba daya kare suka tashi kowane ya nufi ɗakinsa,

tsaki yaja ya zauna yana faɗin “shi yasa Siraj yake burgeni wlh shi halinsa da ban yake”
momi tace “ai Siraj yasan kansa gadai wata nan da take son biye musu”
kallon Mairo yayi “gaskiya momi ya kamata asa maryam makaranta dan inaga Gwaggo ba k'arɓarta zatayi ba”
“eh ai inaso ma maka maganar daman jira nake naga yadda zaman zai kasance dan kar asata daga baya tace abata yarta amman kaga yanxu tunda bata tambaya ba ai sai a sakata”
“ina gafa Gwaggo fushi ne tayi kinga ai ko waya bata kira duk da son da take yiwa Maryam”
“fushi kan ai da gani”

momi na yunkurin tashi Qasin yace “momi wace magana ce kikace zamuyi jiya?”
da idon bachi momi ta kalleshi “bachi zanyi ba wani magana yanzu yau ma ko leko nan bakayi ba bakayi breakfast ba ka fita”
“eh kirana akayi shiyasa kuma tunda naje nake aiki sai da magriba na samu kaina”
“to nidai bachi zanyi kuma ko gobe bani da time dan gobe abbanku zai dawo”
tashi yayi yasa hannayensa aljihu yana faɗin “Allah kawoshi lafiya ni bari naje na kwanta”
“to saida safe ta damun maryam kamin ka wuce”
ɗaki momi ta nufa tana hamma,

a hankali Qasin ya shiga data ita ganin bata motsaba yasa shi girgiza ta. ciki magagin bachi ta rika faɗin “mumi kinga Siraj ko”
“ba Siraj bane nine tashi kije ɗaki ki kwanta”
sake komawa tayi bachi haka yasashi data ita tsaye yana girgizawa “ke momi tace kije ɗaki ki kwanta”
“aa barni ni nan zan kwanta”
girgizata ya rikayi da karfi daker ya samu ta buɗe ido aiko tana ganin shine ta kara zube masa, dole ya ɗauketa ya kaita ɗakin yayiwa momi saida safe ya fuce.

*_4:21pm....._*
momi na zaune ita da Siraj suna fira sukaji an buga k'ofa. kofar momi ta kalla tace “waye?”
shiru akayi ba amsa nan ta kalli Siraj “jeka duba”
tashi yayi ya nufi kofar yana buɗewa yaga Yarima tsaye cikin kananan kaya yasa hannayensa ciki aljihu sai kanshin turare yake fuskarsa na kallon wani gurin.
kasa masa magana Siraj yayi shima kin juyo fuskar yayi ya kalleshi,
juyowa Siraj yayi ya nufi ɗakinsa tambayarsa momi ta shiga “lafiya wanene?”
yana gaf da shiga ɗakin yace “gashi nan waje nima ban sanshi ba”
tashi momi tayi ta nufi kofar, yadda Siraj haka ita ta tararda shi tsaye murmushi momi tayi tace “Yarima ne yau a gidan?”
sai a lokacin ya juyo ya kalleta shima fuskarsa ɗauke da murmushin “nine Momi”
“kuma ka tsaya a waje”
“to ai ba amin iso bane”
kai momi ta girgiza “Yarima ai naga gidan ba bakonka bane gidan nan ai gidanku ne tunda kai ɗana ne”
momi na cewa haka ta juyo ta dawo cikin parlour.
kai ya ɗaga yana karewa bakin kofar kallo kamar sannan ya taka kafarsa ya shiga cike da takama,

yana zaunawa momi ta dire mishi drinks.
“yau Yarima an tuna damu? kodai wani abun ne ya kawoka?”
da kanshi ya shiga zuba drinks ɗin yana faɗin “ziyara ce na kawo muku momi”
momi tayi dariya “aiko ka kyauta ya aiki to ya kuma gida?”
saida ya kurɓa drinks ɗin kusan so uku sannan yace “Alhamdulillah”
kallon parlour yake ta ko ina kamar mai neman wani abu.
can ya kalli momi yace “gaskiya momi Siraj bashi da tarbiya”
ko kaɗan momi bata jidaɗin maganar ba amman haka ta haɗiye tayi murmushi “yayan zamanine sai hakuri kannen naka”
taɓe baki yayi ya juyarda fuskar wani gefe.
momi zatayi magana Mairo ta fito kicin rike da abu a hannu tana faɗin “mumi kinga ni duk na wanke shuwakar kuma ta fita” maganar take tana kallon kujerar da Yarima yake zaune dan bata gane ko wanene ba,
momi tace “thom naji jiki gani nan zuwa”

yana juyowa suka hada ido murmushi ya sakar mata.
waje Mairo tayo da ido ta buɗe baki ta nufoshi da gudu rike da shiwakar da sauri momi ta tashi tsaye kamin ta rikota ta rumgumeshi har cup ɗin dake hannunshi ya faɗi.
[11/10, 2:12 PM] ‪+234 806 053 5947‬: . MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*16*

fisgota momi tayi ta jefar k'asan carpet “lallai Maryam baki da hankali daga ganin mutun baki san inda ya fito ba ki wani rumgumeshi dubi yadda kika bata masa riga”
momi ta kalli yarima “dan Allah Yarima kayi hakuri hankaline bata da”
cikin kuka Mairo tace “nida hankalina niba mahaukaciya bace”
hannu momi ta ɗaga zata ɗaketa Yarima ya rik'e “no momi plz”
hannu yasa ya ɗago Mairo yana bata hakuri,

kuka Mairo tace yanzu ta fara daman mai nema a duhu balle an yada duk yadda yaso tayi shiru k'iyawa tayi.
fuskarta ya kama da hannayensa biu ya rik'e iya karfinsa ta kasa juya fuskarta shi kawai take kallo.
“yi shiru kinji in kina son na baki apple da abu mai daɗi”
kai ta ɗaga “to na daina”
“good girl”
handkerchief ya ciro ya share mata hawaye ya cire mata majina,

juyawa tayi tana hararar momi k'asak'asa ta gefe Yarima yayi murmushi ya rika hannunta ya “muje ki raka ni”
lakkame masa hannun tayi “ba kace zaka bani abun daɗi ba”
baice mata komai ba ya kalli momi yana murmushi yace “ni ban wuce momi in Qasin yazo ki gaishe shi”
fuska a sake momi ta amsa mishi “to zan faɗa miki mun gode a gaida gida”
kuɗi ya ciro masu ɗan dama ya aje mata sannan ya fice rike da hannun Mairo.

motarsa ya nufa harya buɗe rike yake da hannunta yana zaunawa ya kama ɗayan hannum ya rike “faɗa min miye dan gantakarki da gidan nan?”
turo masa baki tayi “to ni nasan mi kake nufi ne”
shiru yayi yana tunanin yadda zai mata ta gane “faɗa min momi mamar suwa ce?”
kai ta ɗaga sama “maman yaya da Siraj da Usman da Nura su kenan”
“good ke kuma ina mamanki?”
“mu bamuda mama sai dai Gwaggo tana can gida”
“yauwa to faɗa min ya akayi kika zo nan gidan?”
“da sukaje can suka zo dani nan gidan”
“to faɗa min Qasin yace miki wani abu da ya gamu tare?”
“a a baice komai ba”
banɗir ɗin 500 ya ciro ya dora mata saman hannu yana faɗin “karki faɗawa kowa munyi wannan maganar dake kinji”
da karfi tace “to bazan faɗa ba” tana wani kallon kuɗi tana dariya.
har kasa ta duka tana masa godiya,
kunnenta ya kamo yana faɗin “duk kika faɗawa wani saina ɓata dake kuma bazan sake miki komai ba”
ɗagowa tayi tana kallonsa “wlh ba zan faɗa ba ko za a kasheni”
murmushi yayi “yauwa jeki kar moni taga kin daɗe”
tashi tayi da gudu ta nufi cikin gida.

saida yaga shigewarta sannan yayi ma motarsa key.
kaura suka tashi yi da Qasin daya kunno kai cikin gidan shi kuma yana k'ok'arin fita da sauri Qasin ya bashi hanya dan yasan shi ba jaye mishi zaiyi ba, saida ya fita sannan Qasin ya karaso parking space a ransa yana mamakin abunda ya kawo Yarima yanzu,

da sallama ya shigo parlour momi ta amsa masa Mairo ta nufeshi da gudu tana nuna masa kuɗin “yaya ka gani Yarima ya bani duka kuma ni kadai”
kuɗin ya karɓa ya duba yana kokarin zaunawa yace “momi miya kawoshi yanzu kuma”
“jiyara ta kawoshi kuma yace a gaishe ka”
“a gaishe ni? yanzu fa kasa bari yayi na shigo saida na kauce masa”
momi tace “to ai kasan halin kayan ka”
Mairo ta riko hannunsa “yaya kuma harda mumi yaba kuɗi masu yawa”
lakatar mata hanci yayi “ke wai ba ance miki momi ake cewa ba ki daina cewa mumi”
turo baki tayi tana kallon momi “to kuma yaya momi tace mun banida hankali”
kamin Qasin yayi magana momi tace “ai ba kida hankaline Maryam”
kara ɓata fuska Mairo tayi “kaji ko?”
Qasin yayi dariya yace “haba momi Maryam fa nada hankalinta komai na hankali take dan Allah ki daina ce mata mahaukaci”
“Allah ni bana mata ɗaukar masu hankali kaga abunda tayiwa Yarima yanzu?”
“mi ta masa?”
“bata fa sanshi ba daga ganinshi ta tazo a guje ta rumgumeshi ga hannayenta ba kyau har cup ɗin hannunshi ya faɗi”
Qasin ya kalleta “amman ya dakeki ko?”
momi tace “bai mata komai ba dama zan daketa hanani yayi inajin yan k'aurai ne bisan kai harda fa kuɗi ya bata”
murmushi Qasin yayi ya shafa kan Mairo.
yace “ya santa ne shiyasa”
“ina ya santa?”
nan ya bata labari kamar yadda Mairo ta faɗa masa da kuma haduwar da sukayi Dubai Mall,
Momi tace “shiyasa kika rumgumeshi ni ai nayi mamaki yadda naga ya sakar mata fuska harda share mata hawaye”
uhum kawai Qasin yace yana kallon siraj dake saukowa downstairs.

“Maryam faɗa min mi Yarima yake ce miki daya rike miki hannu?”
wani irin ɓata fuska tati ta ɗago tana kallonshi “ni baice min komai ba kawai yace yace yace yana siyomin kayan daɗi kuma kuma yana in yana gaida momi”
taɓe baki yayi “aikin banza”
momi tace “kaga halin nan naks Siraj sam bana sonsa ai kodan girmanka da yayi yaci ake ka gaisheshi amman kaki”
“wlh momi matukar bai sauke wannan girman kan dake tare dashi ba to baza mu taɓa haɗa hanya ba”
cikinsa momi tayi da faɗa “bana fason shashanci Siraj bai girmeka miye abun girman kai a ciki mutun ya tako kafarsa har nan cikin parlour nan ka kasa yi masa magana kaifa da kanka ka buɗe masa kofa ina ruwanka da girman kansa”
murmushi yayi ya nufi kofa “Siraj”
kiran Qasin ne ya juyo dashi “na'am yaya”
“nasan bai fika da komai ba amman ka rika masa magana tunda momi bata so”
kai ɗaga masa ya fice.

candynovels.wordpress.com

© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*17*

tsaki momi taja “da gaskiya Yarima da yace Siraj bashi tarbiya”
kallonta Qasin yayi “shi yace haka?”
“eh”
“shi Yarima har ya iya buɗe baki yace Siraj bashi da tarbiya”
momi tace “ai da gaskiyarsa ace murun ya shigo ka kasa masa mana dama fa na tambayeshi cemun yayi baisan ko wanene ba jifa”
“haba momi duk abunda Siraj ai baici ace gaban idonki ya furta bashi da tarbiya ba shi har ya isa yayi miki wannan maganar gaban idonki duk fa wadda ya aibanta maka abu kaiya aibanta babu wadda zai buɗe baki kaf duniyar nan yace yayan gidan nan basu da tarbiya”
cikin faɗa yake magana cike da jin zafin maganar.

momi tace “miye na wani tada jijiyar wuya akan wannan maganar”
tashi yayi tsaye yana faɗin “hmm iskancin Yarima yayi yawa sai yayi nadamar furta wannan kalamin”
tashi ita momi tayi tsaye “Qasin bance kayi rigima da shiba wannan maganar kuma ta wuce karka kuskura ka masa wani akan wannan maganar kaji na faɗa maka”
tana kawai nan ta nufi upstairs.

Mairo tayi war da ido ta rufe baki “tho momi tayi fushi kuma kaine”
murmushi yayi ya shafa kanta ya fice.

saida momi taji ficewarsa sannan ta fito tun kamin ta karasa saukowa Mairo tace “momi yaya yasa kinyi fushi ko?”
momi ta karasa saukowa tana faɗin “a a ni banyi fushi ba”
“to mi yasa kika masa faɗa kuma kika shige ɗaki saida ya fice kika fito?”
basarda maganar momi tayi “muje cikin mu karasa girki kar babanku ya dawo bamu kare ba”
da sauri ts nufi kicin momi ta rufa mata baya,

*_washe gari....._*
tara saura Qasin ya shigo part ɗin momi zaune ya tararda ita tana kallon aljazeera news saida yaɗan kalleta sannan ya zaina kusa da ita yana gaisheta,
juyowa tayi ta kalleshi fuskarsata ba yabo ba fallasa bayan ta amsa tace “ga abun breakfast ɗinka can inka kare zamuyi magana”
faduwa gabansa ya ɗanyi jin harsun karya basu jirashi ba,
su jiki a sanyaye ya kalli momi yace “ke har kun karya ne?”
“eh yau tea kawai nayi su Usman da Nura sunci nasu sun tafi makaranta”
“ke fa momi?”
“ni tun part ɗin babanku na karya nida Siraj maryam ce kawai bata tashi bachi ba”
bai sake cewa komai ba ya tashi ya nufi dining.

ruwan tea kawai ya zuɓo ya dawo kusa da momi ya zauna “momi wace magana ce?”
shiru momi tayi na ɗan wani lokacin kamin ta kalleshi tace “akan maganar matarka ne”
faduwa gabansa ya ɗanyi “momi wani abun ne?”
“a a ba wani sabon abu bane kawai dai na gaji da dafa maka abinci kana ci,
matarka na kwance tana yadda taga dama da aurenka ace kullum sai kazo nan kaci abinci kaci na rana kaci na dare banda na safe  tu na maka wannan lokacin da baka da aure yanzu kan bazan maka gaka ba”
Qasin jim ya ɗanyi sannan ya kalli momi yace “momi bata saba bane kota girka ba wani daɗi yake ba”
“to ta rika girka maka haka nan ko ruwa ne ta rika dafa maka kana sha daga yau dai bazan sake aje maka abinci ba kodai kayiwa kanka abun kunya kaci na kasuwa ko kuma ka cilasta mata ta girka maka”

“to momi a bamu maryam saita ri..-”
hannu momi ta ɗaga mishi “dan Allah karka soma na baka maryam ita da bata san zafin gikinta ba ko? kai da ka iya kare mata in anyi magana ka iya kareta ita yar masu kuɗi yar boko bata iya komai ba sai hutu ko to nadai faɗa maka kuma bazan bada maryam ba in yar aiki zaka ɗauko ya rage naka”
kansa na kasa har momi takai aya,
ko kaɗan bai jidaɗin maganar ba.
       “shikenan momi zan san abun yi shine kawai matsalar?”

kai ta ɗaga mishi tana kallon Mairo dake saukowa sanye da kayan bachi.
murmushi ya sakar mata “maryam kin tashi?”
“eh momi ina kwana yaya ina kwana”
“lafiya kalau kin tashi lafiya?”
kusa da momi ta zauna tana “kalau momi yau ba ayi kari ba?”
“anyi kinga naki can kan dining”
zata tashi Qasin yace “momi nafa nema wa Maryam makaranta”
sai lokacin momi ta ɗan sakar masa fuska “amman kuwa daka kyauta gaskiya a ina?”
“nan tudun wada Alex international school makarantar nada kyau kuma suna karatu sosai”
wani daɗi Mairo taji ta riko hannunshi “yaya da gaske?”
“da gaske mana ina miki karyane?”
“a a kuma zanje?”
“eh yau zamuje su tantanceki in aka shirya komai saiki fara zuwa”
tashi tayi ta shiga rawa tana taɓi da hannu momi tayi dariya “yau fa abun nema ya samu sai a dage ayi karatu in yaso sai a samu wadda zai rika miki lesin kina ɗan karawa”
Qasin ya tashi yana faɗin “nima haka nake sonyi yadda zatayi ssurin fahimta da kuma islamiya sai a nema mata ta na kusa kidai shirya mata kamin 11 sai muje ayi komai”
“to saika fito”
Mairo ta kalleshi “yanzu zamuje?”
“a a saikin karya kinci abinci”
“to bari nayi sauri”
da gudu ta nufi dining shi kuma ya fice yana murmushi,

'''   *    *    *   '''
tunda suka fita sai basu dawo ba sai dare Qasin na rike da hannunta suka shigo parlour.
Siraj ne ya taresu yana zolayar Mairo “eyye yar kauye an sata makaranta eyye aiko za a ga kauyanci kai”
murguda masa baki tayi “eh naji koma minene naji mai k'aton kai”
momi tayi dariya “a a maryam kan yar birni ce ko?”
nan Mairo ta nufeta “eh momi kuma karantar nada kyau kuma gidan sama ce har sun bani kayan makarata kuma momi wlh suna ta turanci harda yan yara”
Siraj yace “ke kan harki kare bazaki gani komai ba sai shinkafa”
ɓats fuska tayi “momi kin jishi ko?”
momi ta shafi fuskarta “ke kyaleshi xuwazuwa kema zaki iya ai da tambaya akan zama malami”
dariya tayi ta kwanta jikin momi tana rufe ido,

momi tana kallon Qasin tace “an kare komai ko?”
“eh anyi komai sunce monday zata iya fara zuwa ga uniform nan sun bata na biya kuɗin scul bos zata rika zuwa 7:30am tana ɗaukar ta in kuma suka tashi zata kawo ta”
“to Allah ya taimaka abbanku ma ya jidaɗi sosai”
murmushi yayi ya tashi “bari naga abbah naje na kwanta”
kai momi ta ɗaga mishi Mairo ta ɗago tana kallonsa “baza kaci abinci ba?”
kallon momi yayi dake kallonsa,
can ya ɗauke kai yace “bana jin yunwa”
ya sun kuyarda kai ya fice.

candynovels.wordpress.com

© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*18*

wasawasa Mairo ta fara karatu a'na mata lesin a gida na makaranta ma Qasin ya sakata.
in kuma lokacin islamiya yayi momi ta tura bata samun zama inba weekend ba da dare ma Siraj ne yake tisa mata ko Usman,

*_2:30pm..._*
schools bus ta sauke Mairo.
da gudu ta shigo parlour tana faɗin “momi yau”
bata karasa magabar tayi shiru ganin Yarima zaune saman kujera.

ware mata hannaye yayi yana murmushi kaɗan kaɗan ta karaso tana kallon upstairs.
saida ya mata kiss a goshi sannan ya rumgumeta,

da sauri ta ɗago tana masa magana kamar mai raɗa “ina momi?”
schoolbag ɗinta ya shiga cirewa “bata nan nima ban tararda ita ba”
“tana ɗaki ko tana kicin”
kai girgiza mata “bata nan ta fita”
“a a bari dai na duba”
kicin ta nufa ta fara duba bata ga kowa ba nan ta nufi ɗakin momi nan ma bata nan haka ta fito ta nufoshi hannu a baki ta ɓata fuska,
hannu ya mika mata yana murmushi “zo nan bana faɗa miki bata nan ba”
ba musu tazo kusa dashi ta zauna hannu yasa ya cire mata takalmin makaranta da safa ya kara janta kimusa dashi ya riko mata fuska,
“pretty gal wani sirrin zanyi dake”
shiru tayi sannan tace “na minene?”
“bazaki faɗawa kowa ba?”
“wlh Allah ni bazan faɗa ba kofa wannan da kace karna faɗa har yanzu ban faɗawa kowa ba”
hannunsa yasa yana taɓa lips ɗinta “da gaske kodai kin faɗa?”
“wlh ban faɗa ba”
“yauwa haka nake so wannan ma karki faɗawa kowa kuma karki bari kowa ya gani kinji zan baki abun daɗi da kuɗi kinji”
“tho amman ka xaka kawo min kayan daɗi da gaske harda ice cream da madara kuma kaje dani yawo”
hannunsa yasa yana shafa gefen fuskarta “zan miki duk abunda kike so matukar zaki mun abunda na saki”
da sauri tace  “zanyi minene?”
“zan fada miki zaki daiyi ko?”
war tayi da ido “eh da gudu ma”
murmushi yayi ya shiga mata chakulkuli tana dariya saida tayi mai isarta ya jata jikinshi ya rumgumeta yana shafa bayanta,

“Maryam....”
kamar daga sama taji muryar Qasin da sauri ta ɗago tana ganinshi jikinta ya shiga rawa Yarima kuna bai fasa shafa bayanta da yake ba koma ɗagowa baiyi ya kalli Qasin ba saima haɗe fuska da yayi yana wani tsusar baki da yake na salon iskancin.

tsawa Qasin ya katsa mata “mi kike nan?”
tashi tayi tsaye cikin rawar murya tace “momi bata nan”
“bashi na tambayeki ba?”
razana tayi sosai tayi bayabaya tana son yin kuka zatayi magana Yarima ya tari numfashinta ba tare daya kalli gurin da Qasin yake ba “ba komai take ba miye matsalarka?”

kara haɗe fuska Qasin yayi yace “I thought da ita nake Magana”
tashi Yarima yayi tsaye yasa hannayensa Aljihu ya nufi Qasin cikin wata tafiya ta isa da tak'ama,

saida ya isa daf da fuskar Qasin ya sakar masa wani shu'umin murmushi yace “don’t put words into my mouth. I have got plenty to say”
wani kallo ya watsa masa tun daga samansa har kasa ya ɗauke kai ya fice.

wani kallo Qasin ya bishi dashi cike da jin haushi can ya juyo ya watsama Mairo wata muguwar harara,
aiko jikinta ya kara shiga rawa kamar mai jin sanyi.

cikin tsawa Qasin yace “baki san wanene Yarima ba ko miya tsayarda ke gurinshi?”

kasa masa magana tayi babu abunda zuciyarta take nuna mata saita shige cikin ɗaki ta kulle karya ɗaketa duk da bai taɓa dukanta ba amman haka zuciyarta take nunama ganin yadda yake harararta,

hankalinta bai kara tashi ba saida taga ya nufo gurinda take,
sakar masa ido tayi saida ya kisa kawowa kusa da ita ta watsa da gudu,
cikin zafin nama ya kaɗe mata k'afa ta faɗi.

gashinta ya riko ƴya tada ita tsaye “ina zaki ba tambayarki nake ba?”
fashewa tayi da kuka tana rokonsa “dan Allah kayi hakuri ka yafe min bazan kara ba wayyo Gwaggo momi”
saida ta kira momi ya tuna da ita da sauri yaja hannunta suka nufi kofa.
tana masa ihu ya buge mata baki yana mata alamar tayi shiru ba shiri ta rufe baki tana son mayarda kukan,

part ɗinsa ya nufa da ita wani emptyroom ya nufa da ita.
saida suka shiga sannan ya sake mata hannu ya kulle ɗakin ya zare bel ɗinsa ya buɗe mata ido “mi ya kaiki kwanta masa a jiki?”
baya tayi tana kuka ta kasa mace masa komai,
matsowa yayi yana faɗin “duk na sake ganin kin rumgumeshi saina miki shegen duka na rufeki cikin ɗakin nan babu wadda ya isa ya ceceki”

sai a lokacin ta soma magana “dan Allah yaya kayi hakuri bazan sake ba wayyo momi”
bel ɗin ya ɗaga sama kamar zai buga mata wani irin ihu ta saki tayi cikinshi ta rumgume mishi kafafu tana kuka,

“lafiya Qasin miya faru?”
mansura ce take masa tambayar tana jijjigar kofa.
nan Mairo ta koma kiranta “anty mansura zoki ceceni”
ɗagota “aya rufe min baki”
da sauri tasa hannu ta toshe baki tana ɗaga masa kai.
juyawa yayi ya buɗe kofar ya dawo parlour bel ɗin dake hannunshi mansura ta rika kallo kamin ta kunno kai cikin ɗakin tana duɓe duɓe,

bata ga komai ba sai Mairo take tsaye rufe da baki tana shawaye.
rikota mansura tayi suka fito gurin Qasin ta nufo tun kamin ta karaso ta jefa masa tambaya “mi kayi mata Qasin?”
ba tare daya kalleta ba yace “mi kike tunanin zanyi mata?”
“ka bani amsa ta kawai Qasin ya zaka saka ta cikin ɗaki harda zare bel zaka ɗaketa mi tayi maka?”
wani dogon tsaki yaja ya tashi fuska a haɗe ya fisgi hannun Mairo suka fice.

tunda suka fito Mairo take masa magiyar karya daketa,
yana shigowa parlour ya jefarda ita saman kujera yana kiran momi.
jin shiru yasa ya nufi upstairs. bai jima ba ya fito ya nufi kicin nan ma bai jima ba ya fito ya nufi gurin Mairo dake kuka,

da sauri ta tashi zaune tana share hawaye sai wani numfashi take kamar zai ɗauke,
“ina momi?”
“ta fita koda na dawo ban ganta ba Yarima kawai na isko”
cikin rawar muryar kuka take masa maganar,

ido ya tsura mata tayi kasa da kanta hawayen na zuba.

candynovels.wordpress.com

© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*19*

ajiyar zuciya ya sauke ya ciro handkerchief ya kama fuskarta yana share mata hawayen “yi hakuri kinji bazan sake ba daina kuka”
kai ta ɗaga masa tana wani wahalallen numfashi,
kwantarda ita yayi saman kujera “wanta kiyi bachi?”
harta kwanta sai kuma ta ɗago ta kalleshi “yaya karka faɗawa momi kaji?”
kai ya ɗaga mata ya tashi ya fice.

takura kanta tayi saman kujera ta matse guri ɗaya kamar wadda aka cilasta tana matsar kwallah har bachi ya ɗauke ta,

'''   *   *   *   '''

*_2 hours letter..._*
can cikin bachi taji muryar momi da Siraj,
    da sauri ta tashi tana soshe2.
Momi na kallonta taja wani dogon tsaki “haba Maryam ace mutum kana girma kana cin k'asa kamar ki ace inkin dawo makaranta ba kisan ki cire uniform ba saidai ki samu guri ki kwanta dubi kiga har lokacin islamiya ya wuce kuma baki san ki saka uniform kije ba”

ɓata fuska tayi “to momi ba fita kikayi ba kika barni”
nan momi kasa ce mata komai tayi dan takaici in banda tsakin data sakeyi ta nufi kicin,

momi na shigewa Siraj yaja mata kunne “ba wani daman baki son makaranta yar kauye”
fashe masa tayi kuka ta tashi tana aika masa mugayen duduna tana son huce haushinta akansa.

tsawa momi ta katsa mata “wuce ki cire uniform ɗin nan kiyi wanka kila ma ko abinci baki ciba?”
kai ta ɗaga
Momi tace “Allah ya shiryaki maryam wuce kije kiyi wanka duk kika sake yin abunda kikayi yau saina miki shegen duka”
kamar ta fasa kuka ta nufi stairs Siraj na zolayarta,

ta kusan minti 30 toilet ɗin tana wasa ruwa saida taji motsin momi a bedroom sannan ta fara wanka,
koda ta fito momi na zaune saman kujera tana duba wasu matirial da atanfofi.
     kallonta kawai Mairo tayi ta nufi waduraf ta ɗauko wata atamfa red colour riga da saket tasa ko mai bata shafa ba ta janyo k'aton hijab ɗin momi tasa ta shimfiɗa carpet ta soma sallah,

momi na kalle da ita saida ta rama azahar sannan tayi la'asar.
bayan ta sallame ta cire hijab ɗin ta jefar saman bed ta nufi kusa da momi ta zauna,

    “momi kayan waye?”
kyaleta momi tayi saida ta kare danne2 wayar da take sannan ta kalleta “na siyarwane”
shafa kayan ta shigayi “wlh momi suna da kyau suma siyarwa zakiyi?”
momi bata amsa ba ta kama hannunta ta kira sunanta a natse “Maryam”
dariya tayi “na'am momi”
“magana zamuyi ki bani hankalinki kinji banason kisa wasa ki daina dariya kinji?”

wani haɗe fuska tayi saida tasa momi murmushi sai kace wani cartoon ta wani tada kafaɗu “thom ina jinki?”
a natse  momi ta soma mata magana yadda zata fahimta “maryam ki daina abunda kikeyi kinji ba kyau kinga kara girma kike ba ragewa ba ya kamata ki rika sanin ciyon kanki ki daina abunda kike”

“tho ni kuma momi mi nayi?”
ajiyar zuciya momi ta sauke “yanzu fa saida kika rama azahar sannan kikayi la'asar kina ganin kin kyauta?”
kai ta girgiza alamar a a momi tace “tho kingani wadda fa yake haɗa salloli azaba ake masa ba kyau ki daina kinji?”
nan ta ɗaga kai “kuma kinga in kika dawo makaranta maryam basai nace ki cire uniform ba ki rika cirewa duk abunda kika san aikin kine ki rikayi basai nace kiyi ba kinji? ki zama yarinyar kirki”
wata dariya ta rikayi tana kallon momi tana tsutsar leɓenta na kasa,
can dai ta kawarda fuska tace “tho momi na gane koma minene kike nufi”
shafata momi tayi “yauwa yata haka nake so kuma ki dage ki rika karatu ba wasa banda faɗa ko jan magana kinji?”
nan ma kan ta ɗaga ta tashi tsaye “nidai bari naje naci abincin yunwa nake ji”
bata ko tsaya jiran abunda momi za taceba ta fice.

tana saukowa downstairs Qasin na shigowa.
suna haɗa ido ta juya da sauri zata koma hannu yakai ya rikota “ya haka ina zaki?”
upstairs ta rika nunawa “ɗaki zan kwanta ne”
murmushi yayi yaja ta suka nufi kujera bayan ya zauna ya zaunarda ita “baki san ba kyau bachin maraice ba?”
“eh ni ban saniba”
“tho ba kyau ki daina karki sake bachi da maraice”
“tho na daina bazan sake ba”
idonta a kasa take amsa masa dan tsoron kallonsa take.
lura da hakan yasa ya sakar mata hannu yace “tsorona kike ko maryam?”
shiru tayi tana wasa da hannayenta fuskarta ya riko “faɗa min mana tsorona kike ne?”
ɓata fuska tayi ta soma magana “nidai bana son duka in mutun yana dukana tsoronsa nake sosai”

murmushi yayi “tho na daina bazan sake ba ai ban dakekiba”
“eh amman ai kaso ka dakeni dan dai anty mansura tazo ne ka kyaleni”
tana maganar tana wani langwashe langwashen kai da turo baki,

dariya yayi tace “ai ba mansura ce ta ceceki ba daman ba dukanki zanyi ba”
harara ta watsa mishi “kai wlh karya ne tho miyasa ka ɗaga dankon zaka buga min?”
“minene sanki?”
rufe ido tayi tace “wannan wadda kaso ka dakeni dashi”
“bel?”
kai ta ɗaga tana kara matse ido dariya yayi yace “ki yarda maryam bazan iya dukanki ba kawai dai horaki nayi”
kwanta masa tayi saman jiki tana dariya,

“wlh karya ne dukana kaso kayi”
kunnenta riko ya rika murɗawa “ni nake karya?”
dariya ta rikayi tana faɗin “na daina ba kaiba”
haka ya rika wasa da ita soma masa kuka sannan ya saketa ta nufi kicin shi kuma ya fice.

washe gari tunda safe Mairo ta shirya kanta duk abunda momi ta saba mata ita tayiwa kanta,
sosai momi ta jidaɗi da schoolbus ɗinsu tazo har bakin gate momi ta rakata ta buɗe mata motar ta shiga.
hannu ta rika ɗagoma momi har suka fice,

*_2:30pm..._*
ta shigo gidan da sallama ta shiga parlour momi ta amsa mata da fa'ah “wa'alaikissalam yar mama an dawo?”
kai ta ɗaga mata tana cire takalmin makaranta,

daga gurin da take zaune ta jefasu gurin da aka tana da dan ajeye takalmin tana faɗin “momi yau Yarima ya kai mana ziyara a makaranta”
Usman dake zaune kisa da momi yace “da gaske?”
“eh wlh harda chocolate ya raba mana”
momi tace “gurinki yaje ko makaranta gaba ɗaya”
“a a makaranta dai kofa jiya yaje kuma yazo gidan na-”
shiru tayi ta kasa karasawa sai rabon ido take. momi tace “jiya ya zo nan? bayan fitana ko?”
wata dariya tayi “ke momi na tuna mafarkine nayi ba gaske bane”
tashi tayi da sauri ta nufi upstairs “bari naje nayi sallah nayi shirin islamiya”
  tanayi tana waigo momi harta shige.
momi kan daɗine ya isheta tana gani ta fara samun kan Mairo.

© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*20*

washe gari ma Mairo ita ta shirya ma kanta komai bayan ta saka safa ta riko schoolbag ɗinta ta nufo downstairs.

da dariya ta sarasa saukowa ta rumgume Qasin dake zaune saman kujera rike da laptop,
aje laptop ɗin yayi yana murmushi ya zaunar da ita saman kafafunsa “maryam har kin shirya?”
ɗagowa tayi tana murmushi “eh kuma ni na shirya kaina”
saukar da ita yayi jin motar makarantarsu ya karɓi jikar hannunta yasa mata,
da sauri momi ta fito kicin rike da kular abincinta tana faɗin “oya karɓi ga abincin ki naji motar ku”
da gudu ta karɓa ta nufi gurin da takalminta suke ta saka harta fice sai kuma ta dawo ta tsaya bakin kofa “momi ba zaki bani komai ba?”
“mi zan baki?”
shiru tayi tana bugun kofar parlour.
hannu Qasin yasa aljihu yana cirowa ya mika mata ɗari biyar,
wata dariya ta saki jikina na rawa ta karɓa tana masa godiya “na gode yaya” kai ya ɗaga mata ta fice da gudu.

ɓata fuska momi tayi tace “Qasin bana so karka sake ka ɗauki kuɗi har ɗari 500 ka bata”
hannu ya ɗaga “shi kenan na daina amman naga kamar bada yawa bane”
cikin faɗa momi tace “tho na dai faɗa maka bana so duk kyautar da ita karta wuce 100 zuwa k'asa”
tana kaiwa nan ta nufi kicin,
da sauri Qasin yace “owk momi yi hakuri ai ya wuce zo kiga wani abu?”
yi tayi kamar bata jishi ba shige kicin ɗin saida ta kare abunda take sannan ta fito.
har lokacin yana zaune ƴyana danne2 sa,
kujerar dake kusa dashi ta zauna “gani ya akayi?”
ɗagowa yayi ya kalleta “momi ɗan ruwan tea ma bazan samu ba?”
taɓe baki momi tayi “au daman jiran kake na ɗauko maka breakfast? inma shine dalilin zamanka nan tho tashi ka koma part ɗinka dan kasan munyi ba'ada dakai tun farko”
dariya yayi “a'a momi bashine ba abu zan nuna miki”
laptop ɗin ya ɗauko ya ɗora saman jikinta “kinga wani design ɗin wata kwangila da za'ah ba kanfaninmu”
duba momi ta shigayi tana faɗin “amman kan abun da girma sosai mi za a gina haka?”
“wani kanfani suke so a gina musu na sarrafa motoci _JAMES GLOBAL AUTOMOBILES_ sunan kanfanin shine na farko da zai kafa branch a Nigeria”
momi tace “aiko dasun kyauta muma mu ɗan samu cigaba kuma matasan mu su samu aiki”
“sosai ma momi kinga in aka ginashi mutun kusan ɗari biyar zasuyi aiki karkashin su kinga ai an ɗan rage kuma kanfanin sun iya motoci ana son motocinsu sosai sune zakiga J.G.A mutunin ɗan amerika ne”
momi tace “amman naji daɗi to kai zaka gina musu gurin ne?”
“tho haka ake tunani amman dai ba ni kaɗai bane mu uku aka kaimusu zasu zaɓa ne saisu bada kwangilar ga wadda suka yarda da aikinsa amman dai mutane da yawa ni suke cewa saboda kanfanin fitaccen kanfanine kuma muna aiki babu kissa ciki”
murmushi momi tayi “tho ai haka ake so Allah ya taimaka yasa ka samu”
“amin momi dan gaskiya zamu samu kuɗi masu yawa”
“to Allah ya yarda ya taimaka”
“amin”

tashi yayi rike da laptop ɗin yana kallon “bari naje can na karya”
kai momi ta ɗaga mishi “da yafi”
murmushi yayi ya fice.

*_7pm..._*
Mairo na zaune parlour kasan carpet ita da Siraj yana duba littafanta na makaranta sai zolayarta yake tana masa kuka yana sa ta karanta gurinda bata iyaba yayi mata dariya ita kuma ta buga masa fillo. suna haka sukaji an taɓa kofa duk juyawa sukayi suna kallon kofar,

cike da takama Yarima ya shigo ba tare da yayi sallama ba ya nufo gurinda suke,
wani irin haɗe fuska Siraj yayi kamar bai taɓa dariya ba,
wannan karon Mairo batayi unkurin tarboshi ba ido kawai ta sakar masa tana dariya.
da murmushi ya karaso kusa da ita tashi Siraj yayi tsaye da niyar tafiya tunowa da magagganun momi yasa ya kalli yarima yace “sannu da zuwa”

banza ya masa yana tsutsar lips ɗinsa.
juyawa Siraj yayi cike da bachin rai ya fice,
            hannu Mairo ya riko yana murmushi ya nufi kujera suka zauna tare.
     
kallonsa tayi tace “ba kaji Siraj yana mska magana ba?”
lakatar mata hanci yayi “na jishi bana jin amsa masa ne”
murmushi tayi gyaɗa masa kai,
wasa ya shigayi da hannayensa yana faɗin
“pretty gal ya maranta?”

“lafiya kalau”

“ina momi?”

“tana ɗaki na kirata?”

hannu yasa yana taɓa lips ɗinta “a a karki kirata”
saida ya ɗaga kansa ya kalli upstairs sannan ya kalleta yace “gurinki nazo kinsan munyi dake zan saki abu ko?”
kai ta ɗaga “eh kuma kace zaka bani kuɗi kuna kace zak-”
rufe mata baki yayi da sauri jin motse saukowar mutun downstairs,
saida yayi mata alama da tayi shiru sannan ya juya da murnushi yana kallon momi.
“Yarima yanzu ake tafe?”
“eh momi ya wunin gidan?”
taka kokarin zaunawa tace “lafiya kalau maryam baki ɗauko masa abun sha ba?”

war tayi da ido tace “lahh mantawa nayi bari na ɗauko”
tana sauka ya riko hannunta ya tashi tsaye “a a momi barshi kawai yanzu zan wuce”
“da wuri haka?”
“eh kinga an kira sallar isha kuma daman biyowa kawai nayi naga Maryam”
da ɗan mamaki momi tace “owk tho a gaida gida”
hannu yasa aljihu ya ciro dubu 20 ya aje mata “ayi hakuri da wannan momi”
murmushi momi tayi “Yarima kenan Allah dai ya amfana”
baice komai ba yaja hannun Maryam suka fice,

motarsa ya buɗe mata ta shiga bayan ya rufe ya zagayo shima ya shiga.
“ina zamu?”
tambayar data fara jefa masa kenan tana kallonshi,

baice mata komai ba yasa hannu baya ya ɗauko laptop ya ɗora mata saman jiki “kinga wannan abun?”
“eh”
“kin taɓa ganinta?”
“eh sunanta kwanfuta”
mirmushin jindaɗi yayi “good wa kika taɓa gani da irinta?”
“malamin makarantarmu da yaya”
“tho kinsan mi nake ao dake?”
kai ta girgiza “a a”
“ta yaya nake son ki ɗauko min”

da sauri tayi waje da ido ta rufe baki “kaikai nidai babu ruwana baya so fa ina taɓa mishi kaya”
“ke mayarwa zanyi kawai inason na arane na ɗanyi wani abu sai na baki ki mayar”
lake kafaɗa tayi “a a gaskiya saidai nace ya aro maka”
haɗe mata fuska yayi “a a karki kuskura kice masa haka bazai bayar ba kuma inma yaji dukanki zaiyi kuma nima na ɓata dake”

hannu yasa ya ɗauko wata leda dake bayan ya mika mata “kinga kayan daɗi nan na siyo miki kuma gobe zan karo miki wasu kullum zan rika siyo miki kuma na baki kuɗi amman fa sai in kin aikata abunda nace”

shiru tayi tana tunani kamar ta fasa kuka ta kalleshi tace “amman inna ɗauko cewa zaiyi mi zanyi da ita”
“no ai bazaki bari ya gani ba a boye zaki ɗauko karki yarda kowa ya gani koda kuda ne”
“tho inna ɗauko ina zan ɓoye?”
shiru yayi yana kallonta kamin yace

“ke bakisan gurin da zaki ɓoye ba?”

“eh duk gurinda zan ɓoye gani za ayi”

“tho ki kaɗa rijiya”
“kai rijiya?”

“eh koki jefar wani gurin innazo sai ki faɗamin na ɗauko”

“ba zai lalace ba?”

“ba zaiyi komai ba kinji”
kai ta ɗaga mishi sosai yaji daɗi ya shafa kanta “good pretty gal”
“amman mi zakayi da ita”
idonsa ya shiga susa kamar wadda abu ya faɗawa “am zan ɗan ɗauki wani abune a ciki na cofa sai na baki ki mayar kinga bazai gane ba ko?”
da mirmushi ya karasa maganar itama tayi masa murmishin karfin hali,
kuɗi ya ciro masu yawa ya mika mata “gashi ki siye duk abunda kike so amman kinsan bazaki faɗawa kowa munyi wannan maganar dake ba ko”
“eh bazan faɗa ba”
“good kuma tsakanin gobe sa jibi nake son ki ɗauko min ita”
kai ta ɗaga mishi,

daga nan ya mika hannu ya buɗe mata motar shima ya buɗe suka fito tare.
Qasin na tsaye bakin kofa yana kallonsu yana rumgume da hannayensa fuskarsa a haɗe,
faɗuwa gaban Mairo yayi da sauri ta juya ta riko hannun Yarima ta soma kuka “nidai bazan iya zuwa ba ga yaya can yana kallona”
mirmushi yayi yaja hannunta suka nufi kofar parlour.

har suka isa Yarima bai kalli gefen da Qasin yake ba,
ita kadaice ke masa kallon tsoro jikinta har wani ɓari yake, da kansa ya buɗe mata kofar data shiga yayi mata byebye yana murmushi hannu itama ta ɗago mishi sannan ya rufe kofar,

yana juyowa Qasin yace “ka bani kunya ka kuma zubar da girmaka momi bata taɓa yiwa yayanta gurɓatacciyar tarbiya ba kuma bana tunanin za'a samu matsala a maryam dan haka ta banbanta da sauran matan da kake gani.
maryam karamar yarinya ce in zakayi sama kayi kasa ba za ah aura maka itaba balle baka daman lalata mata rayuwa dan haka banga abunda zai haɗaku ba”
yana kaiwa nan ya juya ya shigewarsa parlour.

kasa tafiya Yarima yayi sosai maganganun suka ɓata masa rai sai wani busar da iskar baki yake,
_ɗan iskane ni Qasin na karshe har yanzu baka gama sanina ba zan nuna masa true color na_
a zuci yake wannan zancen yana wani kashe ido.

candynovels.wordpress.com
[11/10, 2:12 PM] ‪+234 806 053 5947‬: © *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

_na gode Sosai da k'auna yan *perfect women's*👌🏻 Allah barmu tare 😍 kaina a kasa maman husna & mrs tijjani much love😘_

*21*

Mairo na zaune kusa da momi tana nuna mata kuɗin,
Qasin na shigowa ta tashi tsaye da sauri tana masa kallon tsoro gabanta sai faɗuwa yake ganin yadda ya haɗe fuska,

yana karasowa kusa da ita ya fisgota ya jefar kasan carpet ya cire bel ɗinsa ya watsa mata,
wani ihu mairo ta saki ta durkushe guri ɗaya,
da sauri momi ta tashi ta rik'e "lafiya Qasin miya faru?"
kallon momi yayi rai a bace yace "bata jin magana ne momi so nake nayi mata dukan da in taga Yarima ko kallonsa ba zata sake yiba"
bel ɗin momi ta karɓe "miya faru wani abu tayiwa Yarima?"
"ba wani abu tayi masa ba shi daine yake son yayi mata illah"
kallon mamaki momi tayi masa "wani abun yayi mata ne?"

"momi kinfi kowa sanin halin Yarima ba mutunin kirki bane taya zaki rika barinshi yana keɓanta da maryam?"
sai a lsokacin moni ta gane inda ya dosa kallon maryam "Ke Tashi Kije ɗaki"
tashi maryam tayi ta gudu ta nufi stairs tana kuka.

saida ta shige sannan momi ta kalli Qasin tace "mi yasa kake da zafin zuciya haka ne Qasin?"
"ba zafin zuciya bane momi ina tsoron abunda zaije ya dawo ne kinfi kowa sanin halin Yarima saboda mi zaki barta ta keɓanta dashi ba ɗan'uwanta bane ba wani nata bane hasalima bashida wata alaka da ita ta dalilin mi zai rika bata kuɗi haka masu yawa kuma ki zuba ido kina kallo keda kanki kika ce bakison ina bata kuɗi mai yawa saboda karta lalace to akanmi zaki barta da Yarima?"

cikin faɗa yake maganar har jijiyar wuyansa na tashi,
kai momi ta girgiza tace "bana tunanin haka Qasin nasan waye Yarima"
wani murmushin jin haishi Qasin yayi ya fice,

a hankali momi ta kai zaune saman kujera tana nazarin kalamansa.
sai a lokacin wani tunanin ya soma bijiro mata,
ta kusan awa biu a haka sannan ta tashi ta shiga ɗaki.

*_washe gari..._*
Qasin na zaune garden ya wani aiki a computer yaji an dafashi,
a hankali ya ɗago suka haɗa ido da mairo da gefen fuskarsa ya kunbure,
murmishi ta ɗan sakar masa tace "yaya"
shima murmushin yayi mata yaja mata kujera ta zauna a kusa dashi "maryam kin tashi?"
"eh tun ɗazu"
"eh kaima kaci?"
kai ya ɗaga mata yana yana taɓa gurin daya kunɓurar mata "dukan da nayi miki jiya ne?"
taɓa gurin tayi "eh shine yaya karkayi fushi dani"
laptop ɗinsa ya matsar gefe ya kara matso da kujera kusa da ita "ba zanyi fushi dake ba maryam dukan jiya ma rai nane ya bace kiyi hakuri kinji?"

hawaye ne suka zuɓo mata "yaya ni banma ce ya bani kuɗi ba shine ya bani kuma bance ya sani mutarshi ba shine ya sani"
cikin kuka ta karasa maganar,

tausayinta Qasin yaji duk sai yaji ba daɗi hannunsa yasa yana share mata hawayen "ya isa daina kukan haka kinji bazan sake dukanki ba"
ɗagowa tayi ta kalleshi "kayi alk'awari?"
"eh nayi"
saida taja majina tace "malamin mu yace ba kyau saɓa alk'awari"

dariya yayi yace "maryam kwan wayo na yarda amman sai in kin min alkawari nima kin yarda"
"eh minene?"
ido ya tsura mata yayi shiru yana mata murmushi,

ganin haka yasa tace "yaya lafiya?"
ajiyar zuciya ya sauke yace "kalau kesan mi nake so dake?"
"a a saika faɗa"
"so nake karki sake kula Yarima duk abunda ya baki karki sake karɓa"
shiru tayi "koda kuɗi ne yaya"
"eh koma minene"
kai ta ɗaga mishi "tho bazan sake ba"
murmushi yayi ya rumgumeta yana faɗin "yauwa maryam ɗina"

"yaya mi yasa baka shiri da Yarima?"
daidai kunnensa tayi masa tambayar.
ɗagota yayi yana murmushi ya tashi ya rufe laptop ɗin ya mika mata "jeki ki kaimun ɗaki"
tashi tayi tsaye jikinta na rawa ta karɓi laptop ɗin tana kallonsa,
juyawa yayi ya nufi part ɗin momi ya barta nan tsaye.

laptop ɗin ta tsurawa ido tana shafawa maganganun Yarima suka rika mata yawo akai tunawa zuciyarta ta shiga mata zance biu akai akai takan kai duba gurin rijiyar dake gefen gurin sai faman haɗeye yawu take,
dukan da Qasin yayi matane ya faɗo mata rai nan da nan sai tsoro ya shigeta,
da sauri ta juya ta nufi part ɗinshi.

''' ***************** '''
*_6:15pm..._*
Qasin ya shigo part ɗin momi da sallama yana murmushi,
Nura da Usman suka amsa masa Maryam kuma ta tashi da gudu ta tarɓoshi "oyoyo yaya"
shafa kanta yayi "maryam oyoyo bita kikeyi?"
sakinshi tayi tana faɗin "eh kuma yaya iya"
zaunawa yayi yana sauke gajiya "yayi kyau haka nake so ina momi?"
"tana ɗaki bari na kirata"
da gudu ta nufi ɗakin tana kwalawa momi kira,

tare suka fito tana rike da hannun Mairo da murmushi ta zauna tana kallon Qasin "injin anyi nasara?"
dariya yayi yace "anyi momi saidai fa akwai yar matsala"
nan da nan yanayin fuskar momi ya chanja "wace irin matsala kuma?"
"wai sunce zasu min interview gobe bance wadda suka min yau"
"daman abun harda interview akeyi sai kace ɗaukar aiki"
ajiyar zuciya ya sauke "nima abunda yaban mamaki kenan momi kuma kinsan wani abu?"
"a a minene?"
"Yarima ne zai min interview ɗin kuma wai sai nazo da laptop ɗina sunga irin aikin da nayi"

lumshe ido momi tayi "oh ni har ka faɗarmun da gaba wannan tho ai ba wani abun ɗaga hankali bane sai kaje da ita ka nuna musu kuma duk abunda suka tambayeka ka basu amsa"
"momi bakiji mi nace ba Yarima fa zai mun"
"tho minene a ciki ai baka kirsa cikin aikinka ko kaɗan bana fargaba akan aikin da za'ayi maka"
"momi tsoron nake kar Yarima yayimin wani abun kinsan halinsa"
"karka taɓa saka wannan a ranka ka yarda da kanka Qasin karka bari damar nan ta wuce ka kaifa kmda kanka ka faɗa min kuɗine masu yawa"
kai ya ɗaga mata yana kallon maryam,

Usman yace "yaya ya akayi Yarima ya zama shine zaiyi maka interview ɗin"
Qasin yace "nima ban saniba amman dai kasan yana hulda da motocin kasashen waje kuma kasan tunda Illustrator ne inajin shiyasa"
"Allah dai ya baka nasara yaya"
duk suka amsa da 'amin'
sun ɗan jima suna fira saida aka kira sallar magriba sannan kowannensu ya tashi momi da maryam kuma suka nufi ɗaki dan sallah.

*_Monday @10:30am..._*
cikin nasara akayiwa Qasin interview duk yadda Yarima yaso ya samu matsala Allah bai yarda ba duk abubuwan da suka bukata saida ya nuna masu Yarima yayi mamaki sosai ganin laptop ɗin,
bayan fitarsa akayiwa mutun 3 duk basuji sun gamsu dasu ba kamar yadda sukaji da Qasin sun daɗe suna ttaunawa kamin su yanke hukunci sosai Yarima yaso a bawa wani ba Qasin ba amman suka ki yarda dan sun lura da gwarewarsa nesa ba kusa ba,

*_2 hours letter..._*
suka aika aka kira Qasin daya shigo suka sake yi masa wasu tambayoyi,
ya amsa musu fiye da yadda suke tunani nan suka kara jindaɗi Yarima suka bawa files ɗin cike da jin haushi ya mika masa,
Qasin na murmushi ya karɓa yayi sign fuskarsa a sake ya mikawaƳYarima files ɗin yana murmushi yace "thank you"
murmushi Yarima wadda bai kai zuci ba "ur welcome Men"
hannu suka rika mikawa Qasin sunna masa congrats,

'''**********************'''
cike da jindaɗi Qasin ya shigo gida kai tsaye part ɗin momi ya nufa tun daga sallamarsa ta gane haka bata masa magana ba saida ya zauna "an daiyi nasara ko?"
dariya yayi ya mika mata jakar dake hannunshi "anyi momi sun bani"
ba karamin daɗi momi taji ba saida ta gama duba laptop ɗin sannan tayi ma Allah godiya "Alhamdulillah Allah mun gode maka haka nake so Alhamdulillah Yarima yaje?"
"eh tare dashi akayi komai shima ya bani files ɗin nasa hannu"

"masha Allah Allah ya tayaka riko"
"amin momi kinga fa ko breakfast banyi ba"
maganar yake yana wani sosa kai,
taɓe baki momi tayi tace "zakaci albakacin wannan ranar zan baka na yau"
murmushi yayi "aiko momi da kin kyauta"
tashi yayi ya nufi dining yana faɗin "yau momi gidan sit ba kowa"
"to ai kasan yau monday wazai zauna nima anjima kaɗan fita zanyi"
"tho bari na daukeki dan nima fitar zanyi"
taahi momi tayi ta nufi upstairs,
"bari na shirya wani abin kamin ka kare"
"owk momi"

kujera yaja ya zauna ya hau cin abincin har wani sauri yake yana lumshe ido raban da yaci abinci mai daɗi haka har ya manta kullum cikin siyen takeaway yake gashi abinci inba na momi ba baya jindaɗinshi,

kusan plate biu yaci yasha zoɓon da momi ta haɗa ya tashi yana hamdallah,
part ɗinsa ya nufa bai daɗe ba ya fito ya sake nufo part ɗin momi bayan ya ɗan watsa ruwa ya chanja kaya, zaune ya tararda ita tana jiranshi,
"momi har kin shirya?"
"eh so nake nayi saurin dawowa kar maryam ta dawo gidan ba kowa"
agogon hannunsa ya duba "gashi ko sun kisa dan 12 ta kusa"
tashi momi tayi ya ɗaukar mata jekar dake gabanta suka fice.

*_2:34pm..._*
Mairo ta shigo gida kamar ta fasa kuka ta nufo parlour dan tun gate maigadi ya faɗa mata momi bata nan,
jefa tayi da jakarta tsakiyar parlour ta nufi upstairs,
tana shiga ta cire uniform ɗinta ta ɗauki tawul ta ɗaura ta shiga bathroom wanka tayi tare da alwala sannan ta fito sai wani tureturen baki take tana matsar kwallah,
wadurof ta nufa tana buɗewa taji an kira amsawa tayi duk da bata san mai kiran ba ta rufe wadurof ɗin da sauri ta nufi kofa.

candynovels.wordpress.com

© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*22*

da sauri ta sauko stairs tana rabon ido dan bata ga kowa ba har ta nufi kofa taji an rikota,
juyowa tayi da sauri suka haɗa ido da Yarima sosai ta razana ganin fuskarsa a haɗe gashi batayi tsamaninsa,
kokuwa ta shigayi dàshi tana son kwace kanta jikinta har wani rawa yake.
iya karfinsa yayi wurgi da ita saman kujera cikin jar fuska yace "mi yasa kika karya alkawarin?"
tashi tayi zaune tana kuka tace "yi hakuri dan Allah karka dakeni"
risinawa ya shafa gefen fuskarta "baki son na dake ki miyasa kika ki aikata abunda na saki? mi yasa maryam?"
shiru tayi tana kallonsa hawaye na mata zuba.
hannu yasa yana share mata wayarsa tayi ringing,
saida ta kusan katsewa sannan ya ɗauka banji mi akace masa ba saidai naji nace "Gret mun faɗi sai dai mu tari gaba... owk sai na ganka"
yana aje wayar ya tashi tsaye yana tafiya bayabaya fuskarsa ɗauki ke da murmushi saida ya kai kofa sannan ya juya ya fice,

ajiyar zuciya ta sauke ta kawanta saman kujera dafe da zuciya.
ta kusan minti 20 a haka sannan ta tashi ta nufi ɗaki,
cikin kankanen lokacin tayi shirin islamiya ta ɗauki littafanta ta nufo downstairs.

cike da tsoro ta sauko sai leke2 take har ta samu ta fita parlour,
har ta isa harabar gidan bata daina jin tsoro tana kisan isa gate motarsu momi ta kunno kai,
Qasin nayin parking mairo ta nufi momi ta rumgumeta idonta cike da hawaye.
murmushi momi tayi ta rumgumeta "maryam kin dawo?"
kamar tayi kuka tace "eh momi ki daina fita kina barina"
"tho na daina maryam jeki islamiyar karkiyi latti"
kin ɗagowa tayi saida taji an ja mata kunne sannan ta juyo da fuskar ta kalli Qasin,
murmushi ya sakar mata ya buɗe mata mota "shiga na kaiki"
ba musu ta shiga bayan ya rufe ya shiga mazaunin direba yayi ribas suka juya momi kuma ta nufi cikin gida.

tukin yake yana kallonta ita kuma kanta na kasa sai murza yatsunta take tana haɗiyar yawu,
A'hankali ya rage gudun da yake ganin haka yasa ta ɗago ta kalleshi suna haɗa ido yace "mi yake damunki maryam?"
shiru ta ɗanyi sannan tace "babu komai"
Qasin yace "kinsan ba kyau karya ko?"
kai ta ɗaga mishi
"tho faɗa min miya ke damunki?"
"nace maka babu komai"
"Yarima yazo?"
batace masa komai ba har yayi parking daidai gate ɗin makarantar saida ta buɗe motar zata fita sannan tace "eh yazo"
da sauri ta rufo motar ta nufi cikin makarantar,

saida ya daina hangota sannan yayima motar key da sakesake ya iso gida yana tuna yadda mairo ta rumgume momi,
har ya nufi part ɗinshi wani tunanin ya dawo dashi gurin maigadi ya soma masa tambayoyi bayan sun gaisa "Sadiqu bayan fitarmu waya shigo?"
"babu wadda ya shigo inba Yarima ba"
"ya jima nan?"
"a'a bai jimaba ya fita"
kai Qasin ya ɗaga mishi "owk na goɗe"
ya juyo ya nufi part ɗin momi,
da sallama ya shigo saidai bai samu mai amsa masa ba dan babu kowa parlour.
guri ya samu ya zauna yana sauke ajiyar zuciya sai kallon parlour yake ta ko ina kamar wani bako,
ya daɗe haka sannan ya tashi ya nufi part ɗinshi.

*_washe gari..._*
*7am* Qasin ya shigo part ɗin momi,
momi na kicin tana aiki taji shigowar mutum hakan yasa ta nufo parlour,
Qasin na ganinta yace "an tashi lafiya momi?"
"lafiya kalau"
"masha Allah maryam tqa tashi?"
da ɗan mamaki momi tace "eh tana ciki shirin makaranta take yi lafiya dai"
murmushi yayi ya nufi stairs "lafiya kalau momi abu zan bata"

a hankali ya tura kofar ya shiga tana zaune tana saka safa tana ganinshi ta saki murmushi "yaya ina kwana?"
"lafiya kalau maryam kin tashi lafiya?"
"lafiya kalau"
zaunawa yayi kusa da ita yana faɗin "shirin makaranta kikeyi?"
"eh"
"yayi kyau"
kafarta ɗaya rika yana saka mata safar "maryam jiya da Yarima yazo mi yayi miki?"
ɓata fuska tayi "nidai ba nace maka bai min komai ba bai min komai ba"
"tho miya yace miki?"
"nidai baice komai ba kawai yace gurin momi yazo kuma bata nan harda kuɗi ya bani amman ban karɓa ba sai yayi tafiyarsa"
tana maganar tana wani ɓalɓal da ido karya gano karya take.
daɗi Qasin yaji sosai da kanshi ya saka mata jikar makarantar yana murmushi yace "yauwa maryam daɗina dake jin magana kin kyauta da baki karɓi kuɗin nan ba"
rufe ido tayi ta fashe da dariya da gudu tabar ɗakin,

'''***********************'''
tafiya yake yana shewa (fito) hannayennsa na lakkame a bayansa.
duk gurin da yabi sai sun gaisheshi jiki na rawa amman ko kulasu ba yayi bare ya amsa gaisuwar sai wani rangashi yake har ya iso maidaidaicin parlour,

guri ya samu ya zauna bayan ya gaisheta ya ɗora kafa ɗaya saman ɗaya yana wani lumshe ido,
tsakin da yaji tayi ne ya sashi ɗago kai ya kalleta yana kalkatar dariya "haushi nake baki ko hajiya?"
taɓe baki tayi "Yusuf na gaji da maka magana na gaji da saka maka ido haba Yusuf sai kace wani yaro karami kullum ayita faɗar abu ɗaya ana maimai tawa"

rufe baki yayi kamar wani mai jin hamma "sorry hajiya komai ya kusa zuwa karshe na samu wadda nake so jira kawai nake ta karasa girma"
kallon rashin fahimta Haiyar tayi mishi "ban gane ba?"
murmushi yayi "na samu wadda nake so saidai karamace amman idona na kanta data girma zan ɗauke abunta"
maganar yake yana wani ɗaga hannu sama yana taɓe baki kamar wadda yasha wani abu,
kai Hajiya ta girgiza "Yusuf lafiyarka kuwa ban sanka da wannan halin ba"
dariya yayi yace "nayi miki kama da yan shaye2 ko kinfi kowa sanin bana shaye2"
"tho mi yasaka cikin wannan halin?"
"tsabar bakin ciki ne kawai"
"bakinciki kamar ya?"
kafaɗunsa ya ɗaga ya tashi tsaye yana faɗin "barshi kawai hajiya kona faɗa miki bashi da rana"
cikin rashin jindaɗi tace "Allah ya sauwake"
dariya yayi yace "amin bari naje ciki"
kofa ya nufa yana saida ya kusa fita sai kuma ya juyo ya kalleta yace "wlh hajiya bana shaye2 kuma ba wani abun na shaba karki saka wannan a ranki kinji dai na rantse wannan abun da nake tsabar bakincikine da kuma yunwa"
a jiyar zuciya ta sauke iya Tabbacci tana dashi akan Yarima baya shaye2 ko babu komai yakan yi mata irin haka wani lokacin saidai ba kamar na yau ba.
a kasale ta kalleshi tace "na yarda dakai Yusuf baka taɓa aikata irin wannan amman mi yasa ka bakinciki haka?"
yana rike da kofa yace "wani abin na sawa gaba kuma ban cima masara ba shiya ɓata min rai har na kasa cin abinci tun jiya amman karki damu yanzu zan koma daidai dan na hari gaba"
"Allah ya yaye maka ko minene Yusuf na yarda da kai"
murmushi ya sakar mata "good mother"
saida ta masa murmushin sannan ya fice.

*©Khadeeja Candy*

candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*23*

yanzu hankalin mairo a kwance yake dan ta daina ganin Yarima ba tada wata matsala inba ta jarabawar da suke ba dan momi bata barinta ta zauna data dawo gida kullum ciki karatu take banda wadda ake mata a makaranta da kuma wanda Siraj yake tisa mata Qasin ma wani lokacin yakan mata,

'''*********'''
yau Mairo da far'ah ta tashi ita ta da shi kowa na gidan tare suka shiga kicin da momi aikin komai tare sukayi,
bayan sun kare ta shiga jerawa a dining tana wakewake momi na zuba mata abinci a kula tace "maryam yau far'ah me kike haka?"
fashewa tayi da dariya "oh momi kin manta yau muke kare jarabawa shikenan sai hutu"
momi ta rufe kular tana faɗin "o na ganoki shiyasa kika tashi tun safe haka tho Allah yasa a kara muku wata har 8"
da fuskar zolaya momibta karasa maganar
mairo ta marairaice fuskar "Allahumma a'a Allah karka amsa momi wlh bana son haka"
dariya momi tayi tace "tho na daina amman dai kinsan ta ɗaya zaki ɗauko mana ko?"
dariya tayi ta rufe ido "momi dan kinga ban iya ba ko?"
"a a kin iya maryam Allah dai ya bada sa ah"
"amin momi kin san kince in an mana hutu zaki kaini gurin Gwaggo ko?"
"eh anyi haka tho bari a muku hutun"
rumgume momi tayi cike da jindaɗi kamin ta sake ta ta ɗauki kular makarantar ta fice dan tuni motar makarantar ta iso,

*_2:37pm..._*
ta shigo gida uniform ɗinta duk ya bace da k'asa tafarta ma babu kyau gani,
tafiya ta rikayi laɓalaɓa har ta isa kofar parlour ta shiga leke.
cikin rashin sa'ah ta hango momi zaune ita da Siraj da sauri ta koma baya,
can kuma ta sake lekowa momi kamar wadda aka tsikara ta waigo suka haɗa ido.
"lafiya maryam kike laɓe?"
kara laɓewa tayi ta yadda fuskarta kawai ake gani tace "momi uniform ɗina duk yara sun lalashi"
"kamar ya? shigo mana"
"kasa suka samin kuma nidai banma yi qasan kasa ba sune suka samin"
"tho shigo"
"bazaki dakeni ba?"
"eh shigo"
daker ta shigo parlour tana wani kakkaɓen2 muna furci.

ɓata fuska Siraj yayi "yanzu maryam da girmanki zakiyi wasan kasa haka?"
harara ta watsa masa "ina ruwanka nida momi nake magana bada yara kananuba"
dariya Siraj yayi momi kuma tayi murmushi hakan yasa ts ɗan saki jiki ta matso kusa da momi "momi ni yarane suka ɓata uniform ɗin harda kular suka fasa marfin kawai suka barmin"
sai a lokacin momi ta lura da murfin kular dake hannunta,
Siraj yace "karya kike kedai kika fasa da kanki ai nasan halinki"
kamin mairo tayi magana momi ta tari numfashinsa "tho ai babu komai sai a siya mata wata aini tunda tana karatu komai zan iya yimata"
gwalu tayiwa Suraj tana daddalomai ido "yaee an bashi red card"
shikan inbanda dariya babu abunda yake ganin abun nata ba mai karewa bane yasa momi ta riko tace "kyaleshi haka jeki wanka kiyi sallah sai muci abinci"
saida ta kara masa gwalon sannan ta nufi stairs.

da dare mairo na zaune parlour ita da Qasin suna game Siraj ya shigo,
aiko daman neman tsokana yake haka yasha mur yace "ke tashi muje kiyi karatu"
juyowa tayi ta kalleshi tayi mai fari da ido "kai dan Allah ja can yaro ba sauran karatu mun kare jarabawa hune kawai zayi mana yaro"
dariyace ta suɓucewa Siraj Qasin ya kalleta yace "Siraj ɗin ne yaro?"
"eh yaro ne man baka ga ka girme shiba"
"tho ai shekara kaɗan na bashi"
"eh duk da haka dai yaro ne"
maganar take tana wani war da ido tana jujjuya baki,
fashewa Qasin yayi da dariya Siraj ma da dariyar ya nufi dining.

game ɗin Qasin ya kashe ya rika hannunta "tashi muje muci abinci"
ɓata fuska tayi ta taɓe baki "yaya bamu gama game ɗin ba fa kuma momi bata zoba barre muci abincin"
hancinta ya lakkata "momi yau ba nan zata ci abinci ba kisan abbah yana nan g(me kuma gobe zamuyi tunda ba makaranta tashi muje"
tashi tayi yana rike da hannunta suka nufo dining saida yaja mata kujera ta zauna sannan shima ya zauna ya soma zuba mata abincin"
Siraj dai kallonsu kawai yakeyana cin abincinsa yana murmushi saida suka fara cin abincin sannan yace "yaya kasan momi tace ka daina ci mata abinci fa"
harara Qasin ya watsa mishi "tho momi ka gani nan ne"
rufe baki mairo tayi tana dariya "lahh yaya Allah sai na faɗa mata"
dariya Siraj yayi Qasin ya haɗe fuska
"kaga bana son iskancin nan fa Siraj ina ruwanka"
Siraj yace "gaskiya ce ai ace mutum da matarsa amman kullum sai yazo gurin momi yaci abinci"
banza Qasin yayi mishi ya cigaba da cin abincinshi,
Mairo kan dariya kawai take tana kallon Qasin.

can ta dafe ciki ta koma kuka kamar ba ita ba "na bani cikina ciyo yake"
duk suka kalleta Qasin yace "ciki kodan kinyi dariya ne?"
"a a tun safe yake min ciyo kuma sosai"
Siraj yace "kinsha magani?"
"a-"
waje tayo da ido tunowa da bata son magani da sauri tace "eh na sha momi ta bani magani mai shegen ɗaci"
wani ya mutse fuska tayi kamar da gaske
Qasin yace "tho ci abincin sai kije ki kwanta"
kuka tasa masa
"ni bazan iya ciba Allah ciyo yake sosai"
"owk jeki ki kwanta"
tashi tayi da sauri tana yiwa Siraj ɗageɗage,
har ta kama hanya sai kuma ta dawo ta nunashi da yatsa ta maida baki gefe tace "kai kuma yaro kayi sauri ka cinyeshi duka"
juyawa tayi ta cigaba da tafiyarta tana wani rausaya kamar wata tsohuwar karuwa,
Siraj kai ya girgiza yana dariya,
murmushi Qasin yayi ya bita da kallon har shige.

*©Khadeeja Candy*

candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*24*

*_washe gari..._*
9 da yan mintuna mairo ta nufo downstairs sanye da kayan bachi fuskarta babu annuri,
duk ɗagowa sukayi suna kallonta harta zauna momi nakai wainar kwai tace "maryam lafiyarki kuwa?"
kara ɓata fuska tayi "momi cikina ne yake ciyo sosai tun jiya"
Siraj ne ya gwaleta "dan Allah can ji kanta"
"kai yaro wlh ka kyaleni"
dariya yayi "Allah momi in bata daina cemun yaro ba dukan gwarai zanyi mata"
momi na mika mata cup ɗin tea tace "karma ka soma ka daketa bakai ka fara wasa da itaba"
gwalo mairo tayi mishi "ance yaro yaro yaro yaro yaro yaroooooo"
Usman yace "ba cikinki ke ciyo ba kenan?"
nan ta rike cikin ta langwashe "momi ni ko tea nan bazan iya shaba ciyo yake sosai"
momi tace "wani abun kika cine?"
"a a ni banci komai ba"
Qasin na kurɓa tea yace "bakince kinsha magani ba ko karya kike?"
soshe2 ta shigayi yana son kawarda maganar "uhm momi kinsan kince yaya bazai kara ci miki abinci ba ko jiya yaci kuma yau yana ci"
kallonshi momi tayi "tho yana iya da abunda yafi k'arfin wuta inji kishiyar k'onanna"
dariya yayi yace "Allah momi abinci inba naki ba bana jindaɗinshi"
momi zatayi magana Siraj yace "nidai duk ba wannan ba dan Allah momi karki barta taje ki hanata"

mairo da Qasin suka kalli momi mairo ce ta riga tambaya "minene momi wa za a hana?"
da fork Siraj ya nuna ta "ke mana ke za a hana"
"ina zataje?"
Qasin ya tambaya,
momi badan taso ba ta soma masa bayani "jiya ne bayan fitarka Yarima yazo wai yana son maryam ta rakashi wani taro da za ayi na buɗe wata kungiya ta taimakon yara"
ɓata fuska Qasin yayi ya taɓe baki "tho saboda mie sai ita zata rakashi miye haɗin ta ta kungiyar?"
Siraj ne ya karɓa mishi "wai shine zai kaddamar da abun kuma yana son yaje da yarinya da zatayi jawabi a maimakonsa jifa"
momi tace "tsarin ne yazo da haka dan haka aka tsara komai har ma abunda maryam zata faɗa a rubuce yake"
tsaki Qasin yaja "aikin banza maryam ce kawai yarinya ai yana da kanne mata da maza yaje dasu mana babu inda zata je"
momi tace "yafa riga ya bada abunda zata karanta har kayan da zata saka ya kawo"
tashi Qasin yayi tsaya yana faɗin "tho a mayar masa da kayansa momi dan Allah karki barta taje"
momi bata ce mishi komai ba sai maryam take kallo data ɓata fuska kamar ta fasa kuka,

tana ganin ya fice tace "momi nidai zanje inason nayi jawabi"
Usman da Nura dai kallonta kawai suke basu ce komai ba
kai momi ta ɗaga mata "ai zaki je inma kike kare zan baki takarɗar kiyita bita kamin assabar kin iya"
daɗi sosai mairo taji za a rika Microphone ayi jawabi.
baki sake Siraj yace "momi kina nufin barinta zakiyi taje duk magangganun nan da akayi"
shima banza momi tayi dashi mairo nata watsa masa harara harya kare cin abincin ya fice.

'''***'''
koda 12 tayi mairo na zaune ɗaki tana karanta takardar da taji motsi ta ɓoye dan kar Siraj ko Qasin ya shigo ya gani,
haik'an ta ɗauki abun ta rika tarewa a ɗaki duk abunda da bata gane ba ta tambayi momi,
islamiya ce kawai take tasa ta aje idan ta dawo ta cigaba,

a waya Yarima yake kiran momi tabawa mairo yana jin yadda take karantawa dan yasan zuwa gidan ba zai masa daɗiba kuma daman momi tayi dashi akan komai zasuyi ayi a waya karya zo gidan inba weekend ba ranar da zasu tafi,

kullum Qasin da Siraj cikin nanatawa momi suke akan karta barta taje. a fili momi nuna musu take bazata barta ba dan karsu dameta,
mairo har zumuɗi take taga assabar ɗin tayi duk wani ciyo da take ji daina faɗawa momi tayi dan karta hana ta zuwa,
cikin kwana biu mairo ta haddace abunda yake fefar kasancewar ba wani jawabi ne mai yawa ba,

*©Khadeeja Candy*

candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*25*

*_Saturday morning..._*
_8:24am_ Qasin ya shigo part ɗin momi cikin kananan kaya,
parlour ya tararda su suna karyawa.
momi na ganinshi gabanta ya faɗi a haka ta ɗaure ta amsa gaisuwar da yayi mata "lafiya kalau ya naganka cikin shiri haka?"
yan duba agogon hannunsa yace "wlh meeting ne wai zamuyi da wasu kuma basu faɗa min ba sai jiya da maraice gashi anjima zasu wuce balle nayi cancle ɗinshi"
wani daɗine ya jiyarci zuciyar mairo da momi mairo kasa jurewa tayi saida tayi dariya,
cup ɗin tea momi ta aje mishi "xauna ka karya mana"
ɗaukar tea yayi a tsaye yana sha "bani da time ɗin tsayawa ina Siraj ne?"
"yaje birnin kebbi"
fuskar mamaki yayi birnin kabbi gurin mie?"
"nima ban saniba baba hajara ce ta aiko tana nemansa tun da 7 ya tafi"
iskar bakinsa ya busar "owk maryam tashi ki chanja kaya ki rakani"
da sauri momi ta kalleshi "gurin meeting ɗin zata rakaka?"
"eh momi ban yarda da barinta cikin gidan nan ba"
faɗa momi ta taso masa dashi "tho bazata ba in baka yarda da magana naba sai kayi abunda zakayi nifa na haifeka Qasin ba ni ka haifa ba"
kasa yayi da kansa yana sauke ajiyar zuciya,
duk sai yaji ba daɗi ganin yadda ranta ya bace haka ya juya jiki ba kwari ya fice.

*_9:41am..._*
motar Yarima tayi parking,
ya kusan minti uku ciki motar sannan ya fito ya nufi parlour.
da sallama ya shigo mairo ta amsa masa tana murmushi,

tsaye yayi yana kare mata kallo ganin yadda tayi masa mugun kyau doguwar rigace jikinta golden colour sai ɗan karamin bakin hijab da momi ta saka mata da da jan janbaki sosai tayi kyau,
a hankali ya karaso kusa da ita ya risina ya kai hannu ya taɓa gefen fuskarta yana haɗiye yawu,
murmushi ta sakar masa "ina kwana"
bai amsa mata ba
ya mayar mata da murmushin yana mata wani kallo,

jin an taɓa kofa ya sashi tashi ta sauri ya matsa baya yana kallon momi data nufo downstairs.
"Yarima ka iso?"
"eh momi naga har kin shiryata"
"eh kasan kace mun 9:30 zaka zo"
agogon hannunsa ya kalla "bari muje momi kar muyi african time"
"owk tho Allah ya kiyaye"
hannunta ya rika suka fice tana yiwa momi byebye.

murmushi momi ta bita dashi har ta fice ko kaɗan momi bata son tafiyarta dan dai babu yadda zatayine tunda tana ganin inta hana mairo zuwa bata kyautawa Yarima ba,

'''*************'''
Qasin ne tsaye tsakiyar ɗaki yana kai da kawo kana ganin yanayin fuskarsa kasan ransa a bache yake.

momi ma zaune take saman kujera dafe da kai lokaci lokaci takan kai dubanta gurin agogon dake parlour.
wannan karon *9:21pm* ya nuna hankalinta ne ya kara tashi,
da sauri ta janyo wayar dake hannunta tana kiran number Yarima duk sakamoko ɗaya ake bata kamar ɗazun wayar a kashe,
juyowa Qasin yayi ya kalleta "kinga ni ko momi saida nace miki karki barta taje kika ki yarda da magana na gashi yanxu abunda ake yiwa gudu"
numfashinsa momi ta tara "babu abunda zai samesu insha Allah kawai dai bana son sukai 10 ne"
magana take kamar abun bai dameta ba saɓanin cikin ranta dake cike da tashin hankali,
kai Qasin ya girgiza "hmm ace tun safe mutun ya fita har yanzu babu labarinsa"

da karfi Mairo ta turo kofar parlour ta shigo idonta zurun zurun.
duk juyowa sukayi suna kallonta babu wadda ya iya taɓuka komai harta karaso kusa dasu,
lumshe ido Qasin yayi yana sauke ajiyar zuciya.

da fata momi tayi tana kallon bayanta "ina Yarima?"
"yana can basan inda yake ba sawa yayi a kawoni"
magana take muryarta na rawa kana gani kasan tsoro take ji sai waiga bayanta take,

juyowa Qasin yayi da ita "maryam mi yasa kuka daɗe?"
shiru tayi tana haɗiyar yawu "ba ba babu komai"
tsawa Qasin ya katsa mata yana girgiza ta "faɗamin min gaskiya tun safe ku fita sai yanzu ki dawo kice mun babu komai faɗa min miya faru?"
matsawa tayi ta rike momi tana kuka "yace duk na faɗa sai ya kasheni"
sanyi jikin Qasin yayi momi kuma tsigar jikinta ta tashi,
a hankali momi ta rika zata zaunarda ita kin zama mairo tayi ta ɗan ɗaga rigarta cike da tsoro tace "momi kayana duk ya ɓata dubi jini na min zuba"
da sauri Qasin da Momi suka kalli jinin dake bin k'afarta.

*©Khadeeja Candy*

candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*26*

waje Qasin yayi da ido cikin rawar murya yace "maryam..-"
da sauri ta kalleshi itama idon nata a tsaye.
zai rikata momi tayi saurin rika hannunta "muje ciki"
janta momi tayi suka nufi stairs jikinta babu karfin,
Qasin ma haka yake kallonsu jiki ba kwari har suka shige sannan ya faɗin zaune yana kallon gurin da jinin ya zuba,

sai kusan 10 da wani abu ya tashi ya nufi part ɗinshi tafiya yake kafafunsa na masa nauyi zuciyarsa sai bugawa take da karfi,
baiyi sallama ba ya shigo parlour.
har ya zauna bai lura da mansura dake zaune saman kujera ba
dafe kanshi yayi ya kulle idonsa gam yana cizon baki,
jin an dafashi yasashi ɗago kai ya kalleta.
tashi hankalinta yayi yanayin yadda taga idonsa yayi ja tasan ba lafiya ba,
tana shafa gefen fuskarsa tace "Qasin lafiya na ganka haka?"
janye mata hannun yayi "babu komai jeki kwanta"
"kamar ya naje na kwanta bayan kai hankalinka ba-"
cikin tsawa ya tari numfashinta "nace miki kije ki kwanta babu komai"
tashi tayi tana masa wani kallo kamin ta juya ta nufi ɗaki,

dafe kai yayi ya sake rumtse idon abunda ya faru ɗazu ne ya rika dawo masa,
jin yayi bashi da natsuwa yaji wani irin abu ya tsaya masa a zuciya da sauri ya tashi ya nufi firij yana buɗewa ya ɗauki gorar ruwa ya kafa a baki,
kaɗan yasha ya ɗire ta saman firij ɗin yana maida numfashin,
ya daɗe tsaye a gurin sannan ya juya ya nufi kofa.

part ɗin momi ya sake nufowa yadda yabar parlour haka ya tarardashi kai tsaye upstairs ya nufa,

tun kamin ya karasa hawa yayi tsaye jin shinshikar kukan momi wani abu yaji ya tsikareshi tun daga ɗan yatsan kafarsa har tsakiyar kansa karfen stairs ɗin ya rike da karfi ya matse hannunsa ciki yana dantsar hakora,

jin bazai iya jure tsayinba yasashi zaunawa a gurin,
lumashe ido yayi saida yaji abunda ke zuciyarsa ya ɗan kwanta sannan ya tashi ya nufi ɗakin momi,

a hankali yakai hannu ya tura kofar ɗakin.
tsaye yayi yana kallon mairo dake saman gado kwance tana bachi kamar gawa.
ɓachin ransa dake ransa ya karu saurin ɗauke idonsa yayi ya mayar gurin momi dake zaune kusa da ita hana sharar kwallah,
cikin dakisasshiyar murya yace "momi kuka kikeyi?"
ba tare data kalleshi ba ta girgiza masa kai alamar a'a,
kai ya ɗaga "itama naji kukanta ɗazu"
sai a lokacin momi tayi gyaran murya tace "eh ina tambayar tane ko yayi mata wanin abun ne shine nace zan daketa inbata faɗa ba shine take yiwa kuka"

saida ya ɗanyi jimmm sannan yace "mi tace momi?"
ita shirun ta ɗanyi kamin ta bashi amsa "ina jin menstruation ne Qasin dan banga wata alama data nuna yayi mata wani abun ba kuma ita bata faɗa ba"
sai a lokacin ta kalleshi

murmushi yayi "yes momi menstruation ne saida safe"
bai tsaya jiran mi zata ce ba yayi baya baya yaja mata kofa daman can bai karasa shiga cikin ɗakin ba,

cikin wani yanayi ya nufo downstairs yana tafe hawaye na masa zuba har sauko.
saman kujera ya zauna saida yaji hawayen sun tsaya masa sannan ya tashi a kasale ya nufi part ɗinshi,

*_washe gari..._*
Mairo na zaune saman gado tana wasa da kafafunta Qasin ya turo kofa ya shigo fuskarsa ɗauke da murmushi,
tana ɗago kai suka haɗa ido murmushin da ta gani a fuskarsa ya hanata jin tsoronsa tun kamin ya karaso tace "yaya ina kwana?"
saida ya risina kisa da ita sannan ya amsa mata murya kasakasa "lafiya kalau kin tashi lafiya?"
"lafiya kalau"
"ina momi?"
"tana kicin"
hannayenta ya riko "faɗa min maryam mi Yarima yayi miki?"
"ni bai min komai ba yaya"
shiru yayi ya soke kai

can ya ɗago kai ya kalleta "jinin dake miki zuba har yanzu yanayi ko ya daina?"
"a'a ya daina koda na tashi da safe bai min zuba ba"
da sauri ya lumshe ido bugun zuciyarsa ya karu.

"ba abunda kake zargi bane Qasin jikina bai bani haka ba kuma na bincike ta banga haka ba"
momi ce take maganar lokacin da ta karaso kusa dashi.
sakin hannunayen nata yayi suka tashi tsaye tare shida Mairo,

wani irin faɗuwa gabansa yayi lokacin da ya juyo suka haɗa ido da mansura dake tsaye bakin kofa rike da kofar ɗakin.
cikin rashin ta karasa shigowa tana faɗin "miya faru da maryam?"
da sauri momi ta tari numfashinta "babu abunda ya faru da ita gimuwa ne tayi da kuma ciyon kai"
karasowa tayi kusa da mairo "gimuwa a ina?"
nan mairo ta soma mata bayana "a a jiya ne da-"
tassssss Qasin ya wanke mata fuska da mari saida ta faɗi tun bata kai ko ina a zancen ba,
da sauri mansura ta kalleshi "Qasin mi-"
marin itama ya watsa mata saida tayi baya ta dafe kunci.

*©Khadeeja Candy*

candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

_dedicated this page to maama Hajiya Zainab Kano kakar yan biu 🙈 LOL_

*27*

da sauri momi ta riko Qasin da fuskarsa ke ɗauke da bachin rai tace "mi yake damunka Qasin mi suka maka?"
kallon kawai ya rikayi ba tare daya amsa mata ba,
sun minti 10 haka ɗakin tsit sai shehsekar kukan Mairo ke tashi.
mansura ce tayi karfin halin sake yin magana "momi mi yake damunsa ne tun jiya na kasa gane kansa?"
nan momi ta saki Qasin ta matsa kisa da mansura "abunda ya kawo ki kenan? daman nasan baki taɓa leko part ɗina ba sai a wata bukatar kanki ta taso"
kasa tayi da kanta har alokacin tana dafe da kuncinta hawaye na mata zuba,
"indai har abunda ya kawo ki kenan tho ki juya ki barmin ɗakinki ai mijinki ne kinfini sanin hanyoyin da zakibi ki fahimcin abunda yake damunsa"
kamar *HAWAINIYA* ta soma tafiya kanta a kasa har ta fice,

juyawa momi tayi ta nufi mairo ta tashe'ta tana share mata hawaye cikin sanyayyeyar murya momi ta soma magana da Qasin ba tare data kalleshi ba "bana son kowa yasan da maganar nan Qasin koda Siraj ne"
nan ma baice komai ba ya kaɗa kai ya fice,

mairo sai taga ya fice sannan ta kalli momi cikin muryar kuka tace "momi minayi masa?"
"baki masa komai ba maryam"
"amman momi ya mareni haka da zafi"
murmushi momi tayi "baya son idan manya na magana yara su saka baki"
shiru mairo tayi tana shafa gurin,
momi ta kwanto ta ita jikinta "maryam"
cikiciki ta amsa "na'am"
"duk wadda ya tambayeki mi akayi miki kice komai karki kuskura kice Yarima yace in kika faɗa sai ya kasheki ko kice ranar jini yayi miki zuba kinji?"
"tho momi"
"koda fa can ne kauye karki faɗawa kowa kinji?"
"tho bazan faɗa ba"
"yauwa Maryam ɗina yar albarka tashi muje muyi breakfast"
"tho"
da sauri ta tashi momi ta rika hannunta suka fice,

parlour suka tararda Qasin zaune saman tree-setter rike da cup din tea.
da kallo ya bisu yana kurɓa tea a hankali har suka zauna sannan ya tashi ya nufi kofa,
"yaya yau ba dakai za ah karya ba?"
Siraj ne yake masa maganar yana kokarin saka T-shirt ɗin dake hannunsa ya nufi dining.
kai kawai ya ɗaga masa ya fice,

haɗe gira yayi ya kalli momi "lafiyarsa kuwa?"
momi tace "lafiyarsa kalau saidai ko in wani gurin aka taɓoshi"
kafaɗunsa ya ɗaga alamar bai damu ba yaja kujera ya zauna yana tsokanar mairo,
"miya kunbura miki fuska haka yar kauye?"
turo baki tayi ta kalli momi "momi kingan shi ko?"
kai momi ta girgiza "oh Siraj dan Allah ka rabu da ita bana son fitinar nan dan Allah"
murmushi yayi ya noce kansa ya soma cin abincin.
lokaci lokacin ya kan ɗago dasun haɗa iɗo da mairo yayi mata gwalo ita kuma ta murguɗa masa baki,
daga ita har momi ba suyi wani cin abincin kirkiba suka tashi daman ita Siraj ya tsangwameta

*_2:55pm..._*
Qasin ya shigo part ɗin momi saida ya karewa kujerun parlour kallo sannan ya kalli momi dake tsaye dining yace "Yarima yazo?"
kallon mamaki momi tayi masa "Yarima? mi zaya maka?"
jijiyar kansa ce ta tashi jin yayi kamar ya ɓalɓalowa momi masifa amman ba dama dan mahaifiya ce. dole tasa ya tausasa harshensa "magana nake son miyi dashi momi na ɗauka ta shigo ne"
"tho bai zoba kuma in har akan maryam ne karka kuskura masa magana kaji na faɗa maka"
kallon rashin fahimta yayi mata "momi karfa ayi masa magana kikace"
kallonshi tayi ido cikin ido "eh nima mahaifiyarta ce ina tunanin ko ni kaɗai nayi magana dashi ya isa"
wani murmushin ban haushi Qasin yayi ya juya ya fice,

Gardem ya nufa yana tafe yana tunanin hali irin na momi,
wakewaken Mairo ne suka ɗago da hankalinsa yakai gareta
tana zaune karkarshin bushiyar mangoro rike da gwallon gwaiba tana ci,

sai a lokacin ya soma jin tausayinta nn d nn idansa suka cika da kwallah wata irin tsanar Yarima yaji ta taso masa a ɗayan ɓangaren kuma yana son ganin laifin momi,
ya daɗe yana kallonta zuciyarsa sai wani tunani take kawo masa saida ya fisgi kansa sannan ya samu karasa kusa da ita,

da sauri ta tashi tsaye ta jefarda gwaibar tana masa kallon tsoro.
risinowa yayi ya ɗan sakar mata murmushi "maryam..."
da sauri ta amsa "na'am yaya"
hannu yakai ya shafa gefen fuskarta kamin ya jata jikinshi ya rumgume,
_'ya lalata miki rayuwa Maryam ya cutar dani yayi miki taɓon ds zakiyi bakinciki nan gaba amman zan nuna masa kuskurensa sai yayi nadamar abunda ya aikata'_
a zuciyarsa yake wannan maganar yana cige da lips.

kalamanta ne suka dawo dashi daga tunanin da yake,
"wlh yaya kaci arziki yanzu na daina fitsara na shiryu da baka isa ka mareni na kyale kaba"
hannu yasa ya ciro handkerchief ya share hawaye da suka zubo masa ya ɗago yana murmushi yace "da gaske?"
"Allah wlh kai hmm"
gefen fuskarta ya lakata "ashe ke matsifaffiya'ce ko?"
dariya tayi ta rufe ido "a'a ni mai lafiya ce"
dariyar yayi shima "mai lafiya ai sunan wani ne"
wannan karon rumfumeshi tayi tana dariyar
"yaya zaka bimu kauye?"
"yaushe zaku je?"
"da anyi hutu ranar juma ah za ayi mana hutu"
saida ya sauke ajiyar zuciya sannan yace "zanje Allah ya kaimu"
rawa ta rika masa "yauwa yaya na gode ina sonka sosai"
murmushi kawai ya shafa bayanta,
can ta ɗago "bari naje nayi shirin islamiya kar momi tayi faɗa"
kai ya ɗaga mata ta masa byebye ta nufi cikin gida da sauri.

*©Khadeeja Candy*

candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*28*

Mairo na zaune parlour gaban tv tana buga game Siraj ya shigo,
da far ah ya karaso kusa da ita yana ya zauna,
kallonshi tayi taja tsaki ta matsa nesa dashi tana harararsa.
hannu ya kai ya kashe game ɗin ya ja mata hanci,
tashi tayi tsaye ta ɗauki fillon kujera ta rika buga mishi iyakar karfinta.

rikota yayi ya fisge fillon yayi ya jefar ya shiga kokuwar zaunar da ita,
daker ta zauna koshi dan ya rike mata hannayene haka ta rika kokuwar kuncewa ganin bazata iya bane yasa dole ta hakura ta zauna kurum,

bakinsa ya ɗora daidai kunneta yace
"plz maryam magana nake son muyi dake ta fahimta ba faɗa"
banza tayi masa ta kara turo baki ta ɗauke fuska.
murmushi yayi "haba my sis plz"
"tho ka faɗa mana ai kunne ne yake ji kuma ka sakeni"
sakinta yayi ta zauna daidai tana fuskartarsa "maryam kinga yau aka muku hutu kuma momi tace kauye zata kaiki dan Allah in kukaje karki yarda a baro ki kice ke bazaki zauna ba"
wani kallo tayi masa ta ɗaga baki sama "saboda mie?"
"kinga can ba daɗi kuma ba abinci mai kyau irin wannan ba gurin bachi mai kyau ba daɗi kinsan ai kauye ba daɗine dashi ba"
"nikan inaso a haks zan zauna har hutun mu ya kare inason naga gwaggo da tsoho da kawayena da kowa da kowa"
"oh maryam bazaki gane ba yanxu fa in kikaje can bazaki sake ganinmu ba sai anyi hutu"
tashi tayi tsaye "eh naji nidai ka kyaleni"
kallo ya bita dashi har ta haye stairs tana masa gunguni.

*_6:30pm..._*
momi na zaune ita da Usman,Nura da Mairo Qasin ya shigo da sallama,
da gudu mairo ta rumgumeshi tana murna momi bata kulashi ba Nura da Usman ne suka rika kallonsa har ya zauna,
gefensa Mairo ta zauna tana rike da hannunsa "yaya mi yasa ka daina zuwa nan gurin momi?"
shiru yayi yana kallon fuskar momi data ki ta kalleshi,
nan mairo ta sake jefa masa wata tambayar "kuma yaya ka daina cin abinci nn?"
sai a lokacin ya kalleta yana murmushi yace "aiki ne ya mun yawa bani da time ɗin kaina shiyasa kika daina ganina"
kai ta girgirza tana dariya,

juyawa yayi ya kalli momi "momi an wuni lafiya?"
amsa mishi tayi still bata kalleshi ba "lafiya kalau Qasin ya aiki?"
"Alhamdulillah"

bai sake cewa komai ba in banda wasa da yake da yatsun mairo momi ma ko kallonsa batayi ba barre ta sake ce masa wani abu,
suna haka aka kira sallar magariba haka ya sashi tashi yana kallon momi "bari naje nayi sallah an kira magariba"
sai a lokacin ta kalleshi "ka shirya ranar assabar zamuje kauye"
kai ya ɗaga "owk momi har da mansura"
"a a daga ni sai kai sai maryam zamuje"
"owk Allah ya kaimu"
"amin"
kallon su Usman yayi "ku ba zakuyi sallar bane?"
tashi sukayi ko wane na sosa kai suka nufi kofa, nn ya juyo gurin mairo "kema je kiyi sallah"
"tho"
da sauri ta tashi ta nufi stairs saida ta shige sannan ya maso kusa da momi ya risina hakan yasa momi ta kalleahi cikin sanyayyiyar murya yace "momi fushi kike dani ko?"
"mi zai sa nayi fushi dakai Qasin mi kayi min?"
shiru yayi yana kallonta kamar mai tunanon abunda zaice,
tashi momi tayi "nikan bari na shiga ciki nayi sallah"
bata tsaya jiran mi zai ceba ta nufi stairs saida yaga shigewarta sannan ya tashi ya fice.

*_washe gari..._*
tun 7am Qasin ya shigo part ɗin momi ya tare a parlour murna gurin mairo ba a magana haka ya sake jikinshi kamar ba shiba momi dai sai kallonshi take.
tare sukayi breakfast sai kusan 10am ya koma part ɗinsa bai daɗe ba ya fito cikin shiri ya yabar gidan.

da dare ma nan ya ci abinci ya rika jan momi da fira tun tana shareshi har ta gaji ta sake jiki, saida dare ya raba sannan yayi mata sallama ya nufi part ɗinshi,

haka Qasin ya rikayi duk wani bachin rai dake ransa dannesa yayi ya barshi a ranshi saidai duk lokacin daya kalli mairo sai yaji ba daɗi,

da sallama ya shigo kaya nuki nuki a hannunsa banci wa yanda Siraj da Usman suka riko,
gaban momi suka ɗire kayan nn da nn mairo ta shiga budewa "momi kayan waye?"
ɗan kwalin dake kanta Siraj ya cire yaja mata gashi saida tayi uhu,
da sauri Qasin ya kalleshi "kai mi yasa kake son mata keta haka ne?"
mairo ta watsa masa harara "mugune shi mai katon kai ai gobe ba zaka gannin ba"
murmushi yayi ya kalli momi yace "dan Allah momi karki baro ta"
shafa kanta momi tayi "a a can zan barota sai taga gari sannan a dawo da ita"
gwalo tayi masa tana masa rawar kai,
dariya Qasin yayi yace "gobe mirna gurin Gwaggo ba a magana"
momi tace "lallaikan an kwana biu ba a ga mairo ba"
rufe baki Siraj yayi "momi mairo kike ce fa"
"eh ai haka suke ce mata can kauye"
aiko nan ya hau kiran suna nata yana fashewa da dariya tun bata kulaba har ta soma tsarguwa ta tsuke baki "tho sai miye dan kace Mairo ai sunane haka ake kirana"
gwalo yayi mata "ai ba mairo yake ba mero yar kauye"
fashewa duk sukayi da dariya haka yasa ta haɗe fuska kamar ta fasa ta turo baki,
nn Qasin ya sake fashewa da wata dariyar yace "Siraj shi yasa ta raina ka ka cika mata shinshigi da yawa"
"ba shinshigi bane Allah mero ne sunan"
da fata momi tayi "ke kyalesu tashi kije ki kwanta kinsan gobe sammako zamuyi"
tasgi tayi kamar ta fasa kuka ta nufi daki.


*©Khadeeja Candy*

candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*29*

*_washe gari..._*
koda 8am tayi mairo tayi shirin tafiya kasa yin breakfast tayi saboda murna ruwan tea kawai tasha ta tare saman kujera tana kallon su momi dake karyawa,

can taja tsaki ta kalli agogon dake hannunta "mts momi duk kun ɓata min lokaci har 9tayi"
juyowa Siraj yayi ya kalleta "eyye yar kauye an waye yanzu kin iya agogo ko mero?"
kawarda fuska tayi ta masa banza momi ta tashi tana faɗin "bari naje na shirya muje na kaiki gurin Gwaggo ki huta da matsalar Siraj"
kallonta Siraj yayi "momi dan Allah karki baro mana Maryam wlh miss ɗinta zamuyi"
kallonta kawai Qasin yayi ya kara kurɓa tea dake gabansa ya tashi ya fice,

mairo ta kalli momi "nidai kije ki shirya momi kar ki daɗe"
Usman yayi dariya yace "yau Maryam har gudun mu akayi ne dan zakije kauye"
Siraj kamar mai tsira ya hau tsokanarta "kaji fa wai kauye babu ma daɗin faɗin"
taɓe baki mairo tayi ta kalli momi "momi kije dan Allah ki shirya muje"
stairs momi ta nufa tana faɗin "tho yar gidan Gwaggo"
itama tashi tayi tana rufawa momi baya tana hararar Siraj,

*✧*

sha ɗaya da yan mintuna suka kama hanya,
mairo na front-seat Qasin na driving momi kuma a gidan baya surutu kan mairo shi tasawa gaba inta ɗauko wannan ya ɗauko wannan momi dai saurarenta kawai take inta kai gana dariya ba ta tamata saɓanin Qasin da fuskarsa take haɗe hankalinsa ma a wani gurin yake,

hannu Mairo takai ta taɓoshi da sauri ya kalleta "ya maryam mi kikace ne?"
murmushi tayi masa "bance komai ba naga dai kayi shirune baka magana kuma ka ɓata fuska"
sakin fuskar yayi "ina tunanin wani business nawa ne"
"tho ka ka daina haɗe fuska"
murmushi yayi yace "na daina Auntie"
dariya tayi ta kwanta tana kallon t-t,
motocin dake wucewa ta rika lisafawa har bachi ya ɗauketa.

'''*************'''
tsayawar da motar tayi da karfine yasa ta farka a figice tana rabon ido,
rana ne zagaye dasu sai tsalle suke suna ambatar mairo.
da sauri ta fita motar tana uhu suka shiga rumgumar juna ita dasu suna tsalle² ta gina wasu matan aure suka rika lekenta,

tuni momi da Qasin suka kunna kai cikin gidan,
ita kan saida suka gama ɓata mata kaya da kasa sannan ta shiga cikin gidan. da gudun ta karasa ta rumgume Gwaggo dake zaune saman tabarma tare dasu momi, idon Gwaggo cike da hawaye ta soma ture mairo "ni ɗagani ai guduwa kikayi kika barni"
kara rumgume tayi "Gwaggo ni ba guduwa nayi ba ai daman nace miki zan dawo kuma ba gashi na dawo ba ni babu inda zanje"
momi tayi murmushi tace "haba aiko duk kika kori mairo baki mata adalci ba dan kullum zancenki take ita dai Gwaggo ta dai"
Qasin yace "Gwaggo yar matsifa ke kullum matsifarki karuwa take ba raguwa ba"
nn Gwggo ta dawo kansa "eh ai daman kaine ka hure mata kunne tunda kazo taki ta samu matsuwa sai ta biku"
dariya yayi "tho Gwaggo ba gata yanxu mun dawo da ita ba da nan fa da can duk ɗaya ne tunda duk abu ɗaya ne"
momi ta karɓa masa "duɓe ta ki gani na gyare miki ita ta zama yar zamani"
gaban Gwaggo mairo ta dawo tana jujjuyawa kamin ta fashe da dariya ta faɗa jikinta ta rumgumeta,

*_two hours letter..._*
"kingani ko Gwaggo mairo ta sami lafiya ai daman nasan cikin biu sai anyi ɗaya kodai a maidota dan mugun halinta ko kuma ta chanja hali"
Halilu ne ke maganar yana kai lomomin shinkafs da wake bakinsa,
taɓe bag Gwaggo tayi "ai daman ba wani mugun haline da ita ba kaine dai ka bi ka matsa mata"
halilu yayi dariya yace "Allah Gwaggo in zaki faɗi gaskiya kema kinsan mairo ta chanja jifa har take bari yaran na su taɓa ta inda ne ai basu isaba ballan tana ma ta dawo daga birni"
"gaskiya kan ya gashi yanzu har girma maryam tayi kuma tayi hankali"
maganar momi take tana kallon fuskar Gwaggo,

Gwaggo ta taɓe baki "ai dole tun Allah kaɗai yasan hawalar da kuke gwada mata ai duk abunda zai sa mairo ta zama haka ba karamin abu bane"
Halilu ya tashi yana faɗin "Gwaggo ai ba zasu dai yi mata abunda kike nufi ba"
momi tace "ai muna zuwa duk wani abu da tasan bana Gwarai bane zubarwa tayi kuma muka saka ta a makaranta"
juyowa Halilu yayi da far'ah "harda makaranta kuka saka ta momi gaske dai ta kara chanja wa tayi kyau yanzu"
dariya momi tayi "kaji Halilu shi boko har sawa yake mutun yayi kyau?"
"Allah kuwa momi kinga ai yanzu ta natsu kuma ta waye ba kamar daba daman burina kenan naga mairo a makaranta kuma cikin rayuwar jindaɗi"
harara Gwaggo ta watsa masa "kuma can da kake dukanta?"
"yau ai saboda bata jin maganane shiyasa kuma kinga dan ta dainane ake mata haka"
"hmm tho chanjawa tayi ne ai babu irin dukan da bata a hannunka ba"
dariya yayi ya aje kwanon dake hannunsa "ai ba zaki gane ba Gwaggo ni dai bari naje Qasin na jirana mu zaga gari"
momi ta kalleshi "kar kuyi nisa halilu yanzu zamu je gidan tsoho mu koma gida dan ba daɗewa zamuyi ba"
"tho momi bari na faɗa masa"
hannunsa ya ɗauraye bayan yasha ruwa ya kurkure baki ya fice.

*©Khadeeja Candy*

candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*30*

momi ta kalli Gwaggo tace "wai halilu ya daina karantun da yaje ne"
"wane karatu?"
"ba nasan da yana zuwa can sokoto gurin karatu ba"
Gwaggo ta taɓe baki "karatu kan ai yasha kashi tunda babu kuɗin karasawa"
"ayyah haba nijan kasan yana karatu a da digiri yake ne ko mie?"
"karki tambayeni ni sanin nayi yadda abun yake ne can dai su suka sani"
dariya momi tayi tana gyara ɗaurin ɗan kwalinta,

abincin dake gaban momi Gwaggo ta kalla tace "kema bazaki ci abincin ba ko Qasin ma yace ba zai ciba ku yan birni baza kuci na kauye ba"
"a a aini kinfi kowa sanin ba haka nake ba tun kamin mu baro gida saida muka ci abinci kuma ni bama abincin ne a gaba na ba"
"ko a siyo miki wani abun ne kici?"
"a'a ai inason shinkafa da wake ni wata magana nake son muyi dake Gwaggo"
kara juyowa Gwaggo tayi tana fuskarta "wace magana ce hauwa?"
"cewa nayi wai mi zai hana ayi haɗin gida"
"haɗin gida kamar ya kiɓfito kiyi magana tunda ba kunyata kike jiba kuma ba bakuwarki nake ba"
dariya momi tayi ta matso kusa da Gwaggo "ina nufi auren gida a haɗa Maryam da Qasin"
faɗaɗa fuskar Gwaggo tayi da far'ah "masha Allahu hauwa kin kawo magana daman abunda aketa magana kena a gari wai mun bayarda mairo can birni dan kwaɗayi mamakon muyi mata aure ai kara lalacewa zatayi magagganu kalakala babu daɗin ji
shekaran jiya fa tsoho yake cewa shidai cewa zaiyi a maido da mairo ya huta har nace nidai ba zanyi magana ba indai ba garin kukazo"
dariya momi ta girgiza kai "ai koda man munce fushine kikeyi"
"ai babu yadda halilu bai yiba kan yaje ya ganota na hana amman gaskiya naji daɗin maganar nan kin kawo shawara tho amman kunyi magana da Alhaji?"
"da haɗin bakinsa nake wannan maganar saida muka tattauna komai dashi kuma ya aminci shi da kanshi yace in nazo nayi miki magana ke kuma kiyiwa tsoho magana kinga duk yadda kukayi in muka dawo sai muji"
"tho insha Allah haka za'ayi abu mai sauki"
sosai momi ta jidaɗi dan batayi zaton zata samu goyon bayan Gwaggo ba,
abincin taja ta fara ci suna fira da Gwaggo, daf da zata kare Qasin ya shigo tare halilu.
zaunawa yayi kusa da ita yana kallon agogon hannunasa yace "momi tashi muje gurin tsoho so nake muje gida da wuri mansura tace nayi baki"
banza momi ta masa saida ta gama cin abincin sannan ta tashi suka nufi gidan tsoho,

''' * * * '''
sai bayan la'asar suka dawo gidan Gwaggo har lokacin mairo bata dawo gida ba,
sosai momi taso ta ganin mairo kamin su wuce.
amman ba dama dan halilu yayi nemanta har ya gaji baiga inda ta shiga ba, haka yasa dole momi tayiwa Gwaggo sallama. godiya Gwaggo tayi ta musu ita da halilu suna ɗsgs musu hannu har suka daina hango su,
sannan suka koma cikin gida.
kuɗi halilu ya ciro aljigunsa ya mikawa Gwaggo "ga naki kason"
da far'ah ta karɓa "yayi ɗan albarka abun ya samu"
yana dariya yace "Qasin ne ya bani ɗazun da muka fita"
zaunawa Gwaggo tayi tana faɗin "ai yaron nan yana da albarka wlh shiyasa ni na jidaɗi sosai da haɗin auren na da za'ayi shida mairo"
faɗuwa gaban halilu yayi nn da nn yanayin fuskarsa ya chanja tsigar jikinshi ta tashi a kasali ya kalli Gwaggo yace "aure za a haɗa mairo da Qasin?"
"eh abunda muka tattins da hauwa kenan kuma alhaji ne ya aikota yace a faɗawa tsoho kuma ni wlh nafi kowa farinciki wannan abun da za ayi ksgs ms mun huta da tsegumin mutane-"
da karfi halilu ya haɗeye yawu duk sai yaji maganar ta cika masa kunne, ya juya jiki ba gwari ya nufi kofa, kallo Gwaggo ts bishi dashi baki sake har ya fice,
tsaki taja ta taɓe baki "ai daman kai bason mairo kake ba kafison ka rika gwada mata azaba kamar haihuwarta"

'''***************'''
cikin dare su momi suka shiga sokoto _Rahama Restaurant_ momi tasa Qasin ya biya sukayo takeaway sannan suka iso gida,
Qasin nayin parking ya nufi part ɗinsa, momi ma a gajiye ta nufi nata part ɗin,

*_washe gari..._*
sai kusan 10 momi ta kare haɗa breakfast saboda gajiyan tafiyar jiya gashi kuma mairo maitaimaka mata bata nan,
Nura ne ya taimaka mata gurin jera abincin a dining, Usman yayi dariya "ayyoh Allah momi har nayi miss ɗin mairo"
momi na shirin zaunawa tace "ai nice nayi miss ɗinta yanzu haka ita nake tunani aikin nan duk sai naga yayi min wata kala"
Qasin yayi murmushi "ai momi ko ita sai tayi miss ɗinki balle ma can da nan ai ba ɗaya ba"
Siraj ya kalli momi "Allah momi da ba dan wani abu ba dasai nace Allah ya kara ai saida nace karki barota kika ki ɗaukar shawara ta"
"ai dole na barota wata nawa bata ga gida ba sai yanzu bamabfa shi kaɗai ya kaini ba"
Siraj yace "tho miya kaiki momi?"
tana buɗe marfin filas tace "auren maryam naje nemawa Qasin..."
kamar daga ssma sukaji maganar da sauri Qasin ya tashi tsaye yana kallonta
Usman da Nura ma duk ita suke kallo Siraj baisan lokacin daya saki tea cup ɗin dake hannunshi ba.

*©Khadeeja Candy*
[11/10, 2:13 PM] ‪+234 806 053 5947‬: candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*31*

"aure fa kika ce momi?"
Siraj ne yake maganar yana mata wani kallon rashin fahimta,
murmushi momi tayi "aure mana miye abun tada hankali a ciki?"
Qasin da tun ɗaxu ya kasa fahimtar ta yace "kamar ya momi nifa naji kin anbata?"
ɗago kai momi tayi ta kalleshi "eh kai na nemawa inason ka auri Maryam ne"
a hankali ya zauna yana kallonta "saboda mi momi nifa ban fahimta ba?"
"bari mu gama cin abinci sai muyi magana"
juyawa tayi gurin Siraj "zauna mana Siraj"
zaunawa yayi yana kallon wainar kwan dake gabansa momi ta sake haɗa masa wani tea ta mika masa,

Qasin kasa cin komai yayi shidai moni kawai yake kallo zuciyarsa cike da tambayoyi,
Siraj ma cin abinci kawai ba dan yana jidaɗinsa ba
wayarsa nayin ringing kamar mai jira yayi sauri tashi tsaye ya ciro ta a jihu ya kara a kunne ya fice,

momi saida ta kare cin abincin tsaf sannan ta tashi ta nufi stairs ko minti uku ba tayi ba Qasin ya rufa mata baya,
gefen gado ya samu ya zauna yana kallon momi dake tsaye gaban madubi yace "momi kefa nake saurare nama kasa fahimtar abun kike nufi?"
zaman kujerar mirrow momi ta zauna "kasan me nake nufi Qasin auren maryam nake so kayi"
"saboda mie momi?"
"saboda inason ka kara aure"
"ban gane na kara aure ba mansura fa momi?"
"mansura ba mata bace Qasin so nake ka auri matar da zaka san kayi aure kasan waye kai"
kai ya girgiza "momi ni ban shirya kara aure yanzu ba haba momi ni bazan iya zama da mata sama da ɗaya ba"
leme baki momi tayi
"soboda mi baka san macce hudu Allah ya halitta maka aure ba?"
"na sani momi amman gaskiya ni ban shirya kara aure yanzu ba"
momi tace "ban fahimceka ba Qasin baza iya ba kamar ya?"
shiru yayi ya maida dubansa wani gurin fuskarsa ɗauke da damuwa,
ido momi ta tsura masa tana jiran amsar da zai bata.
ganin bashida niyar magana yasa tace "ina saurarenka faɗamin dalilinka?"
juyowa yayi ya kalleta "momi da wane ido zan kalli mansura bama zata fahimta ba momi inma gwadanine kike dan Allah ki daina"
"mansura..." momi ta faɗa "itace ta faɗo maka a rai ko baka kada wata matsala sai ita. kar dai ranta ya bache kana gudun bachin ranta amman ita bata gudun naka"
kallon mamaki yayi mata "momi muna zaine lafiya da ita fa ba muda wata matsala"

a hankaɗe momi ta kalleshi "na faɗa maka mansura ba mace bace Qasin har yaushe zaka san waye kai ne tunda mansura tazo gidan nan bata taɓa girka maka na safe da rana da dare kaci ba saidai ka siye takeaway koka zo nan kaci, wata hidima ta dangi bata taɓa tashi ta wanke kafarta taje ba bata taba shiga familinmu ba wani daga familinmu bai taɓa zuwa gurinta tayi masa kyakyawar tarba ba bata taɓa tako kafarta tazo nan part ɗina da sunan tazo gaidani ba matarka bata son haihuwa duk wannan bai taɓa damunka ba bai taɓa bata maka rai ba?"
da karfi momi take masa faɗan saida ya rumtse ido,
"mi yasa son mansura ya rufe maka ido haka Qasin? miyasa baka ganin laifinta baka son bachin ranta wanyannan abubuwan dana lissafa nasan suna damunka amman ka ɓoye saboda kar ranta ya bachi thobin kai ka jure ni bazan iya jurewa ba umarnine nake baka ba neman shawara ba kuma mun riga mu yanke shawara da babanka maryam zaka aura"
kallonta yayi da raunanniyar fuska "momi naji amman fisabilillahi a rasa wadda za a ce na aura sai maryam"
"kamar ya sai maryam
maryam ba mutum bace?"
kamar ya fasa kuka yace "momi kankanuwar yarinya ai kowa ma yaji dariya zai mun"
"kwarai za'a maka dariya kan tunda ka auro dodo ko aljana kamar maryam kake cewa kankanuwar yarinya shekara goma sha?"
tashi yayi tsaye yana kallonta yace "momi am more than 30 now taya kike ganin zan auri yarinyar da bata kai shekara ashirin ba?"
"tho abun kunya kayi ko saɓawa addini kayi Annabi (S.A.W) ya auri nana Aysha tana da shekara 6 aka kaita gidansa tana yar shekara 9 auren duk kuma abunda Annabi ya aikata Sunna ce ba akanka aka fara ba barre a kare kanka dan haka ni maryam nake son ka aura"

lumshe ido yayi ya buɗe "amman momi kona sureta hankalina ba zai taɓa kwanciya da ita ba ba zan taɓa samun natsuwa ba"
momi tace "saboda mi Qasin baka son tane?"
ya daɗe kansa a kasa kamin ya bata amsa "inason ta momi ina sonta sosai amman-"
shiru yayi ya kasa karasawa,

tashi momi tayi tana murmushi tace "ka zamo min ɗa Qasin bana son ka bani kunya mun riga mun kate magana da babanka kuma na sanar a kauye amincewarsu kawai muke jira mansura zaɓinka ce Qasin kasan ko kaɗan bana son aurenta amman na hakura saboda ka samu farinciki dan na fahimci kana sonta sosai tho nima inson ka farantamin ka auri maryam"
baice mata komai ba ya sauke ajiyar zuciya ya fice.

*©Khadeeja Candy*

candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*32*

*_K'auye..._*
taliya ɗaya ɗaya Mairo take ɗauka tana kaiwa baki tana kallon Halilu Da Shima Taliyar Yake Ci Tana Dariya,
"wai lafiyarki mairo mikike dariya haka?"
Gwaggo ta tambaya cikin dariyar Mairo tace "Halilu ne yake bani dariya"
ɗagowa yayi ya kalleta "dariyar mie nake baki mairo?"
nan ta ɓata fuska "ni dan Allah ku daina cemun mairo nan a birni fa maryam ake cewa yafi daɗi"
Gwaggo tayo dariya "lallai mairo yanzu fa an waye ko ɗan zuwan nan da kikayi tho ai nan k'auye duk mai suna maryam mairo ake ce masa"
"ni dai gaskiya ku daina cemun mairo haka fa jiya su hawwa damary suka rika cemun mairo duk naji haushi"
Gwaggo tace "lallai xuwa birni yayi miki daɗi mairo an fara chanjawa ga kiba ga fari ni har maganarki naji ta fara chanjawa"
"ai dole Gwaggo kullum fa da nama muke karya wa da rana ma muci da dare ma haka ga kwai ga madara ga komai na daɗi ai dole nayi kiba"
wani guntun tsaki Halilu yaja "Gwaggo sai kace marar ido yanxu dan Allah ina kibar da mairo tayi nan daman can ai tanada ɗan jikinta saida kice tayi fari da ɗan girma koshi ba sosai ba"
leme baki Gwaggo tayi "ai kai daman ba son kake a ambaci abun alkharin taba"
murmushi yayi ya ɗauke kai
Mairo ta watsa masa harara tace "aiko Halilu duk wadda ya gannin sai yace nayi kyau nayi fari nayi kiba"
Gwaggo tace "ke fita harkarsa ai shi haka yake baya kaunar a ambaceki da alkhari saidai abunds zaisa ya rika dukanki yana shuri kamar an aiko shi"
mairo tace "aiko Gwaggo kinga ɗana je can ba duka ba komai"
ta karasa maganar tana yiwa Halilu gwalo,
hartatarar ta yayi "dan Allah gafara can ai bazaki koma ba"
"ai wlh sai na koma da hutun mu ya kare zan koma birni na barka nan dan yaro"
kwafa yayi "gani kike kamar wasa nake ko tho bari ki gani bazaki koma ba kowa yayi miki tsaye"
ganin da gaske yake yasa Gwaggo ta kallonshi tace "kamar ya bazata koma ba?"
"babu komai kawai dai bazata koma ba"
"koma warta aiko yanzu ma take dan mai dalilice za'ayi sai in abunda ake son k'ullawa bai yiyu ba kuma bama fatar haka"
ɓata fuska Halilu yayi "tho karma ku soma Gwaggo wannan haɗin da kuke son yi ba zaifa haɗu ba"
Gwaggo ta leme baki "sannu baba ba zai yiyu ba tunda kai ka haifeta wai miyasa baka son mairo ne Halilu? mita tare maka?"
"Gwaggo ba wai bana son cigaban mairo bane ko kaɗan babu wannan a zuciyata hasalima nafi kowa son cigabanta amman Gwaggo ina son ki duba wannan lamarin da kuke son haɗawa kwata² bashi da wata ma'ana"
rike baki Gwaggo tayi "bashi da ma'ana kamar ya nifa ban gane inda ka dosa ba?"
matsowa yayi kusa da ita ya sassauta murya "dan Allah Gwaggo karki yarda da abun nan dasu momi suke son hadawa wata kila ma wata cutace zasuyi ya za ace kamar mairo Qasin ya aure ta haba Gwaggo ki duba fa"
Gwaggo tace "ban fa gane maka ba Halilu ka fito fili kamun bayani yadda zan fahimta mana mi kake nufi ne?"
"Gwaggo taya za ace kamar Qasin yace yana son mairo? mairo tashin yaushe ce kuma yar kauye yaushe mairo tayi wayewar da har zaice yana sonta shifa digirine dashi kuma mai kuɗi ɗan birni.
kuma fa har yana da mata haba Gwaggo ki duba fa"
"tho in banda abunka Halilu minene aciki Qasin ɗan'uwanta ne ka kuma san inda wani abun cutane babu yadda za ayi babansa da mamarsa su amince har suzo tambayar in an basu kuma fa muma abunda muke nemane ya samu tunda kafi kowa sanin abunda uan garinnan suke cewa anki ayiwa mairo aure an kaita birin minene² kananan maganganu anyi kara anyi ice tho yanxu dan an bashi aurenta ai ba wani abun bane tunda ko ba shiba dole ne ai ne ayi mata aure"
"th tunda har haka ne ai kinga kara ma a aura mata wani ɗin ko ɗan gujewa masu cewa dan kwaɗayi aka kaita birni kinga yanxu ai sai su kara cewa wani abun in aka haɗa auren"
Gwaggo tace "babu fa abunda zai sa mu fasa haɗa auren nan duk kuma uban da bai zagemu ba bai haihuba dan an zagemu zagin lake mana zaiyine maganar banza"
da tsaki Gwaggo ta karasa maganar cike da bachin rai.
Mairo ta aje kwanon abincin ta matsa kusa dasu tana musu kallon rashin fahimta tace "mi kuke yiwa faɗa Gwaggo?"
tashi halilu yayi tsaye fuskarsa babu yabo ba fallasa yace "aure za'ayi miki mairo Qasin za'a aura miki"
da sauri ta nuna kanta tana kallon Gwaggo "ni?"
"eh ke aure za ayi miki mairo ai kinsan kin kai munzalin aure ai"
kamar ta fasa kuka tace "ni wlh Gwaggo bana son aure ni yar k'ank'anuwa dani za'ayi mun aure ga yan mata nan a birni manya dasu ba ayi musu aure ba sai ni"
hannunta Gwaggo ta riko ta zaunar da ita kusa da ita "mairo nan kauye ne ba birni ba kuma kinga mutane sai gulma suke suna faɗin anki yi miki aure"
"tho ni ina ruwana dasu nidai ma bana son hutun na fasa a mayarda ni gurin momi"
halilu yace "momi itace ta kawo wannan shawarar tace a aura miki Qasin"
shiru mairo tayi tana tunani, Gwaggo tace "karki ji komai mairo alkharine ake nema miki ba sharri ba kinga ma sai kiyi ta zamanki can birni kina yin yadda kike so, ko bakyaso?"
kai ta ɗaga "ina so Gwaggo amman nidai ina jin tsoro"
idonta cike da hawaye ta ke maganar.
nan Gwaggo ta shiga tallaɓata tana kwantar mata da hankali
ido halilu ya tsura mata kamin ya sauke ajiyar zuciya ya fice.

'''*****'''
"dan Allah Momi ku nemawa Nura admission a A.B.U Zaria nidai ganibnake kamar can yafi"
Usaman ne ke maganar yana kallon Momi dake zaune saman tree-setter tana cin abinci,
Momi saida tasha ruwa sannan tace "ni bana ra'ayin A B U nan nafi son State University nan da aka buɗa ance ana karatu sosai kuma kaga nan garin ne hankalina yafi kwanciya iddan yayana suna kusa dani"
dariya yayi yace "momi ni da nake ɗan fodio fa?"
"eh tho ai duka ɗaya ne tun cikin sokoto take nidai bana son ayi nesa ne kawai irin gari haka ko wata kasa"
"amman momi ai kinga yaya ba nan yayi karatu ba shi har kasar ma ya bari"
kafin momi ta bashi amsa aka turo kofar parlour,
juyowa sukayi suna kallon Yarima daya shigo cikin wata bugaggiyar shadda sky blue.
ba tare da yayi sallama ba ya nufo gurinda suke zauna hannayensa sanye cikin aljihu yana tsosar baki kamar mai shan sweet.

*©Khadeeja Candy*

candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*33*

Saida ya kusa kawowa kusa dasu sannan yayi sallama Momi ta amsa mishi da Usman,
kujerar dake kusa da Momi ya zauna yana yiwa Usman wani kallon raini ciki² Usman ya gaisheshi, ba tare daya amsa ba ya kalli Momi yace "sannu Momi an wuni lafiya?"
da far'ah Momi ta amsa masa "lafiya kalau Yarima kana nan?"
"no shekaran jiya na dawo dan naje Uk ne tun ranar da muka fita da Maryam"
"Allah sarki tho ya gida ya da kowa²?"
shiru ya ɗanyi kamin ya bata "Lafiya kalau kowa yake"
juyarda fuskarsa yayi gurin tv, Momi ta cigaba da cin abincinta Usman ya tashi ya fice,
daf da zata cinye ya juyo ya kalleta "Momi ina Maryam?"
"Maryam ta tafi Kauye kasan anyi hutu ta tafi ganin gida"
shiru yayi ya ɗan ɓata fuska "yau kwananta 6 tun ranar asabar taje sai kuma hutu ya kare"
gefen fuskarsa ya shafa "oh Momi nako yi mata tsaba na ɗauka tana nan"
"da yake baka cikin garin shiyasa baka sani ba"
tashi yayi tsaye yana murzar zabban hannunsa "ni zan wuce kuma Hajiya tace na faɗa miki tana son ganinki"
Momi ta kalleshi "lafiya dai ko?" wani murmushi yayi "yo ni momi ya za ayi na sani sai dai kinje zakiji"
"tho shikenan sai gobe zanzo insha Allahu ka gaisheta"
kai kawai ya ɗaga mata ya fice yana kallon upstairs,

*_7:12pm..._*
"Assalamu Alaikum"
a hankali momi ta ɗago kai ta kalleshi tare da amsawa ciki² "Amin wa'alaikassalam"
suku² ya nufi kujera ya zauna kansa a kasa yace "Momi an wuni lafiya?" momi fuska babu tabo ba fallasa tace "lafiya kalau ya iyali?"
saida ya haɗeye yawu sannan ya amsa mata "lafiya kalau Momi"
gyaran murya momi tayi tace "Qasin in baka aikin komai inason ka kaini gidansu Hajiya yanzu ta aiko tana nemana ɗazu naso na ɓari har gobe kuma dai hankalina bai kwantaba nafi son yanje naji koma minene"
"wace Hajiyar Momi?"
kallon mamaki momi tayi masa "Auntie Hasana mana"
"Yarima yazo nan ne?"
"eh shine ya faɗa min ai"
tashi yayi tsaye yana faɗin "bari na kiran Siraj sai ya kaiki akwai inda nake son zuwa"
haɗe fuska momi tayi cikin tsawa tace "babu wani gurin da zakaje Qasin kawai ka fito fili yace baka son zuwa gidan iya isa ba sai kayi min nuku² ba"
lumshe ido yayi ya dafa kai "oh Momi baki fahimceni ba-"
hannun Momi ta ɗaga mishi tana tari numfashinshi "na fahimceka Qasin na san abunda kake nufi amman karka amta wannan Yarima ɗan'uwanka ne kuma inason ka sani bazan taɓa yardar maka ba ka ɗauki kiyayyah ka ɗora masa babu wani dalili nayin haka koba ɗan uwanka bane ai ba abun kwaraine bane ballantana ɗan uwa mi yasa baka da tunanine in kaje gidansu Yarima faɗuwa kayi shi da yake tako kafarsa har nan gurina fa,
ya fika sanin muhimmancin yan'uwan taka Qasin ya fika iya siyasa dan ko kiyayyah ce Yarima bai taɓa fitowa fili ya nuna maka ba ballantana ni har a zuciyata nasan Yarima baya kiyayyah dakai"
komawa yayi ya zauna ya kama hannayen Momi ya rike cikin sanyayyiyar murya ya shiga mata magana "bana kishin Yarima ko kaɗan Momi bana kishinsa kawai dai halayensa ne banaso kuma momi bazan taɓa yarda na faɗa a gadar zaren da yake kullamin ba momi kinfi kowa sannin waye Yarima kinsan duk inda ya ganni ko yaga wani dags cikin familinmu sai ya musguna masa kodai ya faɗa masa gana mara daɗi ko kuma yayi masa wani abun na bachin rai ni kuma na tsani haka momi saboda babu abunda Yarima zai nuna min
sannan momi kin hana na rama momi kince Yarima ɗan'uwana ne nasani shiyasa ma nake ɗaga masa kafa amman momi kinsan Maryam ma yar'uwata ce ko kuma duk abunda ya sameta ya sameni bazan taɓa mantawa ba"
lumshe ido momi tayi ta sauke ajiyar zuciya a ranta tana _...ba zaka taɓa ganewa ba Qasin..._
can ta buɗe idon ta kalleshi tace "naji zaka iya tafiya"
"momi ki shirya na kaiki mana"
"a'a sai goben kafin ka fita"
"momi kar kimun rashin fahimta bana nuf-"
numfashinsa ta tara tare da tashi tsaye "a a Qasin na fahimtace ka karka damu gobe zaka kaini"
bata tsaya jiran mi zai ce mata ba ta nufi stairs,
Momi na shiga ta tararda wayarta saman madubi tana ringing da sauri ta karasa ta ɗauka Hajiya ta gani a screen kamin ta ɗanna picking ta kara a kunne,
_"Amin wa'alaikissalam Hajiya ya gida?"_
banji mi akace mata ba na daiji tace _"eh ina gida lafiya dai?"_
_"tho sakin iso"_
sauke wayar tayi gabanta na ɗan faɗuwa tana mamakin abunda yasa Hajiya take son ganinta haka.

*_© Khadeeja Candy_*
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*34*

*_9:35pm..._*
Hajiya ta iso gidan tun kamin ta fito mota momi ta fito ta tareta cike da far'ah, rumgume juna sukayi kowane na dariya suka shigo parlour,
momi bata barta ta zauna ba suka nufi bedroom drinks kala² momi ta jere mata da kayan ciye² bayan ta zauna suka ɗauko firar yaushe gamo,
can momi ta kalli Hajiya tace "nifa Hajiya ina mamakin zuwan nan naki haka kawai"
murmushi Hajiya tayi "ba zuwan haka kawai bane maman Nura ɗazu ai nayiwa Yusuf sako ya faɗa min kince sai gobe zaki zo shiyasa ni kuma na kasa hakura har goben nace bari nazo yau"
"nima ai na tashi zuwa ɗazun bayan magriba sai kuma nace bari dai na bari har goben lafiya dai ko?"
Hajiya ta dafa momi "lafiya kalau ɗanki ne yaga wata yarinya yace yana so"
farincikine ya bayayyana a fuskar momi duk da faɗuwar da gaban ta yake "masha Allahu ba dai Yarima ba?"
"shifa ai nima farinciki kasa ɓuyiwa yayi a gareni kuma yace nazo na tambaya masa shine fa nace tho ya kira min daya faɗa min kince sai gobe ni kuma na kasa hakuri"
momi tace "ai dole abunda aka ta jira shekara da shekaru nima ai na jidaɗi sosai"
Hajiya tace "yace yarinyar tana nan gidan ke kike rikonta yace mun sunanta maryam"
wani irin gaɗuwa gaban momi ya karayi shiru momi ta ɗanyi kamin ta haɗe yawu tace "maryam Hajiya?"
yanayn yadda tayi maganar yasa Hajiya ta kalleta "eh ita koda matsala ne?"
"a'a ba wata matsala kawai dai naga yarinyar karama ce dan bazata wuce 13 ba"
murmushi Hajiya tayi "kar wannan ya dameki ys faɗa min daman karamar yarinyace har yake cemin kiyonta yake sai ta girma tukuna tho shekaran jiya nida Mai Martaba muka sashi gaba muna masa faɗa mishine fa yake faɗa min shi babu yarinyar da yakeso inba ita ba sai kinga yadda mahaifinshi yayi murna"
momi jiki ba kwari tayi murmushi tace "ai dole kan abunda kowa yske mafarki nimaai nayi farinciki"
Hajiya tace "ina kika sani nima daɗin nake ji kamar me shine babbah yanzu kingaya kamata ace yanzu yayo aure kanensa na biu fa yanzu za ayiwa aure shi yasa ma ai abun ya damu mai martaba yasa yayi masa haka dan cewa yayi im bashi wadda yake so tho shi zai mema masa duk wadda yaga dama shine fa sai ya faɗa mana ita kaɗai kawai yake so dafa duk akayi magana sai yace shi bai samu wadda yake so ba kinga sai yanxu Allah yayi"
ajiyar zuciya Momi tace "kinsan komai yana da lokaci wata kila sai yanzu Allah ya kaddaro za ayi saida fs hajiya wani hanzari ba gudu ba"
kallonta Hajiya tayi "ina jinki minene?"
"its maryam ɗin yar kauye ce kuma ba tsyi wani karatu ba dan zuwannan ma da nayi da ita Qasin ya sata makaranta"
"kar wannan ya dameki duk ba matsala bace tho da dai har yace yana so ai duka ɗsys muke gurin Allah babu wadda yafi wani"
lumshe ido momi tayi ta buɗe ta kallii hajiya tace "shikenan zanje kauye sai nayi masa magana dan yarinyar ma tana can hutun na da akayi sai na kaita ganin gida"
"wai yar insce?"
"wlh kanwar su Qasin ce yar kanne mahaifinsu da mukaje kauye sai muka zo da ita......"
"tho yanzu dai kije kauyen ki nema masa"
cikin karfin hali momi tace "insha Allah haka za ayi"
hajiya tace "ki faɗawa mai gidanki dan ni cikin satin nan nake son aje inma ta kama har dani duk sai muje koda da Mai Martaba ne"
"a a ni ma ai ns isa na nema masa ba sai kunjeba inma dolene kuje ai sai na faɗa muku amman sai in babansu ya dawo dan yayi tafiya"
murmushin jindaɗi Hajiya tayi "ai ba matsala bace Allah ya dawo dashi lafiya ana nan anata harkokin business ɗin ko? ba hutu"
"eh ai shi koyaushe baya samum zama gida neman kuɗi kawai aka sawa gaba ba a nan ba a can zamansa gida kaɗsƙan ne kuma a koma"
"tho mai sa akan ai daman bai gaji zamaba musamman in akwai iyali"

haka momi tayi ta smsa mata firarda suke kamar marar lafiya sai kusan 11 da wani abu ta bar gidan,
daren momi kasa bachi tayi tana tunsnin yadda zata billowa lamarin, har a ranta Qasin take son maryam ta aura sai kuma yanzu dabo biu ziciyarta take mata akan maganar da hajiya tazo da ita dan Hajiya ba tada wani farinciki sai na yarima taya zata yarda Qasin ya aureta ga yarima in kuma ta yarda Yarima ya aureta rigima ce ba yar kaɗan,
kai ta dake ta zauna gefen gado _...oh ni mi yasa ban faɗawa hajiya anyiwa maryam miji ba..._ sai yanzu take jin haushin,
_...amman kuma in har taji Qasin ne ai zata iya cewa ya barwa Yarima kuma gashi har na rig na faɗa a kauye Qasin yana sonta yanzu kums si sai su ga ɓayi musu magana biu..._ busarda iskar bakinta tayi ta lumshe ido.

*_© Khadeeja Candy_*
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*35*

*_washe gari..._*
_10:47am_ Qasin ya shigo part ďin momi zauna ya tararda ita a dining area,
a kujerar daya saba zama ya zauna yana kallonta "momi ina kwana?"
a hankali ta kalleshi kana ganin fuskarsa kasam tana ďauke da damuwa "lafiya kalau ka tashi?"
"eh momi ke kaďai kike karyawa?"
"a a duk sun karya sun tafi makaranta ne kai ka daina karyawa nan ko?"
ďauke fuska yayi ya ďauko wani zancen "momi ya maganar tafiyar so nake na kaiki sannan na wuce dan yau zan wuni busy"
tea momi ta k'urɓa tace "ai tazo tun jiya"
kallon mamaki yayi mata "nan gidan laifiya dai ko?"
"lafiya kalau wata magana mukayi"
"tame momi?"
"sirrice"
"kamarbya momi nasan duk abunda zai sa Hajiya tazo gidanna ba karami bane dan Allah ki faɗa min minene kodai wani abun aka cene?"
momi bata ce masa komai ba ta tsura masa har tsargu ya tashi dan kanshi ya nufi kofa da tunane²
"Qasin..." murya kasa² momi ta kirashi da sairi ya juyo ya dawo "gani momi"
"ka faɗawa matar maganar aurenka?"
kasa yayi da kansa ya daɗe kamin ya bata amsa "a a momi ina tsoron abunda zai biyo baya ne kinsan ba fahimta zatayi ba"
ajiyar zuciya momi ta saike tace "yayi kyau zaka iya tafiya"
kallonta yayi kamar yace wani abu sai kuma ya juya ya fice,
dafe kai momi tayi tana nemawa kanta mafita sa kusan minti 30 haka sannan ta tashi ta nufi stairs,


''' * * * '''
kusan isha'i Siraj ya shigo part ďin momi ganin ba kowa parlour yasa kai tsaye ya wuce ďakinta, zaune ya tararda ita ta rafka uban tagumi tana kallon windo,
"lafiya momi?"
a sanyaye ta kalleshi da murmushin karfin hali "lafiya kalau Siraj ka shigo"
yana k'ok'arin zaunawa kusa da ita yace "momi gaskiya ba lafiya ba dan tunda safe naga damuwa a fuskarki akwai abunda yake damunki momi"
batace komai ba ta sauke ajiyar zuciya ganin haka yasa yace "barin kashi a ciki baya maganin yunwa momi babu kuma wadda ya dace ki fafawsa sirrinki irina hankalina bazai taɓa kwanciya ba momi matukar naki bai kwanta ba dan Allah ki faɗamin abunda ƴake damunki"
kallonshi tayi "kona faɗa maka Siraj ba magani zaka mun ba"
"naji nidai dan Allah ki faɗamin momi indai ba so kike nima na shiga damuwa ba"
momi ba dan taso ba ta fayyace masa komai,
Siraj ya daďe yana jinjina al'amarin kamin ya kalleta yace "yanzu momi mi kike gani shine fita?"
"nima ban saniba Siraj ita nake ta nema na kuma kasa samu"
Siraj yace "tho momi ga wata shawara..."
kallonshi momi tayi "ina jinka"
"momi mi zai hana kik'i yarda Qasin ko Yarima ya aureta"
"saboda mi?"
juyo yayi yadda zata fuskanceshi da kyau yace "kinga yanzu in kika bari Qasin ya aureta Yarima zai yita ganin laifinki shida mahaifiyarshi kuma otama zata taga kin mata cin fuska kinki bari Yarima ya aure kika bawa Qasin ya yaje ɗanki kimsan Hajiya bata tada wani Farinciki sai na Yarima tunda shi kaɗai ta haifa zata iya ɓatawala da kowa akansa kinga in kika mata haka ba zata taɓa mantawa dake ba kuma kinga zata ga baki tashi aurawa Qasin ita ba har saida Yarima ya ganeta yace yana so tunda baki riga kin faɗa mata kin nema masa ita ba kuma itama ba ganewa zata yiba sannan kinga shima yaya sai naga kamar bayason maryam sosai kuma kinga yana kaunar matarsa ko auren maryam yayi za suyita samun matsala,
in kuma kika yarda Yarima ya aureta nan ma baki tsira ba dan kinsan yaya bazai taɓa yarda ba kuma nima bazan yarda ki aura masa ita ba dan zai iya musguna mata kodam ganin daga falinmu take kuma kodan muji haushi zai iya yi mata hakan koda yana sonta dan kinsan halin Yarima ishesshen kanshine ko yanzu baki san dalilin da yasa yace sai ita kaɗai yake so ba tunda akwai yan mata da yawa a garinnna kuma suna sonsa dan babu wadda zaice yana so ta kishi kodan dukiyarsa balle ga mulki ga kyau amman ya nace shi sai maryam bakisan abunda yake shiryawa ba kuma kinga duk ya cuceta mudai ba kyalewa zamuyiba kauye kuma dake za suyi kuka dan haka ni abunda nake ganin mafita shine kawai ki bari can kauye ayi mata aurenta duk wadda suka ga damar haɗa shi da ita sai su aura mata"
gyara zama momi tayi tana nazarin kalamansa,
"ka kawo shawara Siraj amman kuma har yanzu da saura in har haka ta faru ita hajiya mi zan ce mata suma kauye dana riga nace Qasin na sonta ya zance musu har yanzu da sauran rina a kaba"
murmushi yayi "no momi kawai ki samu baba ku tattauna sai a warwar zancen auren Qasin ni da kaina zan kaiki kauye in yaso sai kice musu daman bakiyi shawara da Qasin ba kuma yanzu yaji bai amintaba kuma matarsa yar matsiface dan haka kina tsoron abunda zaije ya dawo dan haka a bar zancen aure kawai duk wadda suka dama su aura mata ita kuma hajiya in kika dawo saiki faɗa mata an riga anyiwa maryam miji alkawarine tun tana karama dan haka iyaye sunce bazasu tada ba koda tace ki kaita kauyen karki yarda kikaita dan zata iya zuwa ta rokesu ta nuna musu kuɗin koma shi Yarima da kanshi dan a yarda a aura mishi kuma kinga ko aura mishi ita akayi wahala zata sha dan kinga karamar yarinya ce sannan ba wani tsayawa zai kikayi yana bata hakkinta ba kuma zai iya ganinta tankar kaunarsa koma yarsa da ta masa abu ya daketa koma karki faɗa masu har sai an ɗaura aure, kawai momi wannan shine abunda nafa ya dace kiyi"
murmushin jindaďi momi tayi ta shafa kansa "ka kawo shawara Siraj haka zanyi Allah yayi maka Albarka"
shima murmushin yayi yace "amin momi shikenan damuwa ta wuce ko?"
kai momi ta ɗaga masa ya tashi tsaye yana faɗin "tho muje kici abinci dan nasan bakici abincin dare ba"
"jeka gani na zuwa"
"owk"
juyawa yayi ya fice cike da farinciki.

*_©Khadeeja Candy_*

candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*36*

A waya Momi ta kira Abbah sukayi magana dan kasa hak'uri tayi ganin ta samu mafita sosai yaso ta bari har ya dawo suje tare amman tak'i dan yadda Hajiya ta matsa mata kullum cikin kiran wayarta take,
ranar alhamis tun da safe Siraj ya fitarda motar da zasu shiga suna karyawa suka kama hanya,

*_K'auye..._*
ajiyar zuciya Gwaggo ta sauke tace "wannan magana ai kamar anyi sara akan gaɓa ne"
Momi tayi mata kallon rashin fahimta "mi kike nufi wani abun ne?"
Gwaggo tace "akan maganar nan ne wai Halilu yanzu ya fito wai sonta yake bai tashi magana ba saida yaga anyi wannan maganar kiji mun rainin hankali"
Momi ta rik'e baki "yanzu Halilun ne yace haka?"
Gwaggo tace "ai kuma baki san wani abun haushi ba wlh tsoho yayi tsaye shi sai Halilu zai aurawa"
"amman tsoho yaji da Qasin ne ake son haɗa auren?"
"wlh yaji kinsan matsalar da aka samu? ya rigani zuwa yayi magana dan ni a yadda na yanke sai an ɗan kwana biu kusan zata koma sannan nsyi maganar kinga koma minene amsar in kukaje sai kuji aiko yana jin haka sai kawai yaje ya faɗawa tsoho wai shi sonta yake ni kuma da naji haka sai naje nima nace ga abunda kike ce aiko tsoho k'in yarda yayi ya dinga ganin laifi yace nice nake son juyarda abun haka ai da kunso shi zaku samu kuyiwa magana ba niba wai shi daman yana son ya haɗasu amman yana tsoho amman yanzu tunda har haka ta faru shikena ta kwana gidan sauki shi Halilu zai bawa babu yadda banyi ba amman yayi tsaye shi lallai sai Halilu balle nasan ya kwashi k'arya da gaskiya ya faɗa masa"
Momi tace "tho injin ita Maryam ɗin tana sonshi?"
"uhmmm aifa kinji inda matsalar take nan itakan tayi tsaye wlh bata sonshi yanxu haka in kikayi mata maganar kuka zatayi"
"dank'ari aiko akwai matsala tho ba'a faɗawa tsoho bata soba?"
"hmm ai sai kiyi abunda tsoho yake nema ai shine ya tsaya kai da fata wai ko bata so sai anyi shi daman ya yanke shawarar aurarda ita dan ya gaji da tsegunmi mutane"
Momi tace "amman kuma Gwaggo ai naga kamar shi Halilun bashi da wata matsala"
"aiko shine da matsa nifa na rik'ashi tun yana k'arami yanzu haka ganin da kike masa baya noma tho ɗsn k'auye in baiyi noma ba mi zaiyi sannan babu sana'ah babu aikin fari babu ma bak'i in kinmai magana yace shi karatu zai bazai iya rayuwar k'auye ba kuma karatun nan bai wani yi zurfi ba balle ace aiki kuma ance aikin nan fa ko a can birni wahala yake tho ina wani abun k'aurai tunda babu abun ci da mata"
Momi ta jinjina kai zatayi magana taji an rumgumeta da karfi,
dariya tayi jin Mairo ce tace "tun ɗazu mukazo ban ganki kiba kina can gurin yawo ko?"
dariya Mairo tayi ta k'ara rumgume Momi "a'a Momi tunda kukazo naga Siraj yaje dani yawo sai yanzu muka dawo Momi nayi mesage ɗinki"
"missed ake cewa yar boko"
Gwaggo tayi dariya tace "haka muke da ita abu kaɗan sai turanci ita yar boko"
Momi ta juyo da ita ta zauna daidai "ina kukaje yawo wato kings shigowa amman da kiks gs Siraj sai kiks shareni ko?"
"a'a Momi yawo fa mukaje da mota ko'ina sai kallonmu ake"
ta karasa maganar tana wani marmarɗen ido,
Gwaggo tace "kin samu abunda kikeso ko kiyiwa mutane kuri tho ina kika baroshi ko ya sake fitane?"
"a'a waya yake yi yanzu zai shigo"
kallon Momi tayi "Momi kinci abinci?"
da murmushi Momi tace "a'a Gwaggo ki bata bamu ba amarya"
nan da nan Mairo ta ɓata fuska kamar ta fasa kuka "Momi bana so ki daina"
Momi ta dafata "ai dole kiso kedai tashi ki ɗauko mana abincin"
matsawa tayi gefen ta takure kanta ta haɗe rai, Siraj na shigowa ta rushe da kuka.
da sauri ya karaso kusa da ita "lafiya mi akayi mata"
Momi tace "wai dan nace mata amarya shine take kuka"
"kamar ya auren za'ayi mata ne?"
"eh Halilu za'a aura mata wai ita kuma bata sonshi"
murmushi yayi ya shiga tallaɓata yana bata hak'uri, daker ya samu tayi shiru ta tashi ta nufi ɗaki,
gurinsu Momi ya nufo yana faɗin "wai yanxu daga yin magana har anjuyarda abun zuwa ga Halilu?"
kamin ya zauna Momi tace "a'a daman rigimar da aketayi kenan wai shi sonta yake...................."
nan Momi ta labarta masa komai,
Sosai Siraj yayi mamaki ya kalli Gwaggo yace "mi yasa bakison auren Gwaggo? Halilu bashida hallin k'waraine hala?"
Gwaggo tace "a' wlh yana dashi nina rik'ashi tun yana k'arami gaskiya bashi da wani mugun hali"
Siraj yace "tho mi yasa bakison ya auri Maryam ni aganina ba wani abu bane kinga shima ai ɗan'uwane kuma duk duniya bana ganin akwai wadda ya dace ya aureta sama da shi kefa kika reneshi Gwaggo ya tashi a hannunki yanzu dan yace yana son Maryam in kikak'i baki ganin xai iya shiga damuwa? ni aganina koda ahi baiyi magana ba kema ya kamata ki haɗasu ballantana har yayi gaskiya Gwaggo in kikak'i goya masa baya baki masa adalciba kuma kin nuna masa ke bake kka hafeshi ba"
shiru Gwaggo tayi tana nazarin maganar.
"amman fa Sirajo ita Mairo bata sonshi fa"
"karma ki kawo wannan Gwaggo Maryam k'aramar yarinyace bata san soba ko a birni ksmar Maryam za'a iya aura mata wadda akaga dama balle k'auye kune kuke k'ara sa tana cewa bata sonshi kawai kibar ma wannan zancen inta girma gidansa a babu zance k'i"
dariya Gwaggo tayi "kuma fa haka ne Sirajo da maganar ka Allah dai ya zaɓa mana abunda yafi zama alkhari"
duk sukace 'amin'
Siraj yace "amman dai Gwaggo ba zaku raba ta da karantunta ba ko?"
Gwaggo ta leme baki "karatu kan ai yasha kashi tunda in an mata aure ai tarewa zatayi kaga ko babu zancen karatu"
"amman gaskiya Gwaggo ku barta tayi makarantar ta koda anyi auren ne inta k'are sai ta cigaba da zamanta na aure"
ido Gwaggo ta nuna masa "kaga nawa ni yanzu kuma fa ako auren akayi nan zatayi ta zama dan bashida gurin ajeta sai yayi gina"
shiru Siraj yayi ya nuce kai bai sake magana ba,
can Momi tace "wai ins wadda taje ɗauko mana abinci?"
Gwaggo tace "aifa sai kiyi bafa zata ɗauko ba da nan fushine take dake"
Momi tayi dariya "in banda abinki Maryam daga faɗar gaskiya sai cibi ya zama k'ari"
Gwaggo ta tashi ta nufi ɗaki tana faɗin "bari na ɗauko miki indai wannan ce saiki shekara"
tashi Siraj yayi "ni bari naje bakin kasuwa kamin ki k'are cin abinci"
"kai ba zaka ciba?"
"kai Momi kinsan ni kan bazan iya cin abincin nan ba bari dai naje can ko zan samu abunda zanci"
kai Momi ta ɗaga mishi ya saka hannayensa aljihu ya fice.

*_©Khadeeja Candy_*

candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*37*

kai tsaye Siraj bakin kasuwa ya nufa daman ɗazu da suka wuce ya hango gurinda Halilu yake zaune,
Halilu na hangoshi ya ɓata fuska aransa yana _babu wani magiya da zaka mun na barma ku ita wlh boko dai nima nayi dan haka baka fini wayeba_,
Siraj ya k'arasowa kusa dashi yayi masa sallama tare da mik'a masa hannu, ciki² ya karɓa ya juyarda fuska,
murmushi Siraj yayi ya zauna saman teburin da yake zaune yana faɗin "kai kaɗai kake zaune?"
"eh ina hutawane"
Siraj ya kalleshi "Halilu ka saki jikinka dani bana nufin cutarda kai ko cilas taka yin abunda baka tashi ba ni shawara nazo na baka kuma inason kayi nazari ka ɗauki shawarar karka kalleni a matsayen ɗan'uwan Qasin inason ka kalleni a matsayin ɗan'uwanka"
juyowa Halilu yayi ya kalleshi "wace shawarace?"
dafashi Siraj yayi yace "naji ance ka fito kana son Maryam ita kuma bata sonka kuma kaga yayana ma yana sonta banci shi kuma akwai wadda yake sonta can birni sannan naji ance baka kada sana'ah ba kama da gurin ajeta tho kuma yanzu naji tana zance sai ta bimu birni tho abunda nake so da kai shine kayi sauri ka matsa a ɗaura muku aure koda baka da gurin ajeta ɗin dan in kayi sake tho rasata zakayi kaga in ka aureta koda tace sai taje birrin kana iya kyaleta taje tayi karatunta amman fa da aurenka kaga kamin ta k'are kai kuma ka samu aiki kayi gidan ajeta ni zan iya taimaka maka ka cigaba da karatunka amman karka yarda wani sati yayi ba'a ɗaura maka aure da ita ba"
ido Halilu ya tsurawa Siraj yana son tantance abunda yake faɗa,
_ta yaya zai yi masa wannan shawarar bayan shi ɗan'uwan Qasin ne miyasa yake son shi ya aureta sama da Qasin can wata zuciyar tace amman kuma fa gaskiya ya faɗa min tunda banida gurin ajeta balle abun ciyarda ita kuma nasan yanzu Mairo bazata yarda ta zauna k'auyen nan ba tunda nama ji ta fara zancen sai ta bisu kuma gashi har yace zai taimaka min na k'arasa karatuna inhar da gaske yake kuma fa inna aureta na huta koda taje can birrin wani ya ganta yana so na dai riga na aureta......_
dafashi da Siraj yayi yasashi dawowa daga duniyar tunanin daya tafi,
Siraj yace "ka yarda da shawarata Halilu shine kawai mafita a gareka"
ajiyar zuciyar Halilu ya sauke yace "maganganunka abun dubawa ne Siraj saidai na kasa ganewa taya zaka goya mun baya na auri Mairo bayan yayanka ma yana sonta?"
murmushi Siraj yayi yace "shiyasa tun farko nace karka ɗaukeni a'matsayen ɗan'uwan Siraj ka ɗaukeni a'matsayin ɗan'uwanka Halilu bana nufi cuta a gareka nayi haka ne saboda shi Qasin yana da mata sannan kuma zuwan da Maryam tayi birni ne ya ganta yace yana so saɓanin kai da tun tana k'arama kake sonta ko ɗazu na faɗawa Gwaggo babu wadda ya dace da Maryam irinka,
Halilu nifa bance dole ka ɗauki shawarta ba kawai in tayi maka shikenan in kuma batayi maka ba duk ɗaya ne"
ya karasa maganar tare da tashi tsaye. Hannu halilu ya mik'a masa "na gode sosai Siraj zanyi tunani a kai"
"nima na gode da bani lokacinka da kayi Allah ya shige mana gaba"
nan sukayi sallama Siraj ya nufo gida,

''' * * * '''
bakin k'ofa ya tararda Mairo zaune rik'e da ɗan karenta tana zane a k'asa,
da murmushi ya fito motar ya nufota, saida ya kusa kawowa kusa da ita sannan ta ɗago ta kalleshi ta wani turo baki wai ita gamai fushi,
sai da ya zauna kusa da ita sannan yace "fushin mi kike Maryam?"
"wai Momi ce tace bazata je dani birni ba"
"tho ai hutunku bai k'areba kuma kinga aure za'ayi miki babu ma zancen komawa birni gaba ɗaya rayuwarki ta dawo nan kenan"
da sauri ta kalleshi "ni wlh ba zan zauna ba kuma ni bana son aure wlh bana son halilu"
da kuka ta k'arasa maganar,
saida Siraj ya duba yaga babu mai kallonsu sannan yace "in baki shawara?"
kai ta ɗaga mishi
yace "karki yarda a aura miki Halilu kinga ɗan k'auyene kuma duk wani abun daɗi da kikasan kinaci da kin aureshi kin daina cinsa kenan kuma kings babu ke babu karatu babu zuwa birni nan zakiyi ta zama kina daka da zuwa daji kina ɗebo kara shikenan kinyi bankwana da jindaɗi muma ba zaki sake ganinmu ba har Momi"
k'ara fashewa tayi da kuka da sauri ya rufe mata baki yana kallon k'ofa "shinnnnn kar sujiki kina son na baki wata shawara?"
nan ma kan ta ɗaga yace "koda an ɗaura miki aure da Halilu karki yarda ki zauna kice ke gurin mu kikeso kiyi ta musu kuka kice kesai an barki kinyi karatu in kikayi haka nasan za'a iya barinki ki bimu amman inba haka ba shikenan ba zaki k'ara jindaɗi ba kinji"
cikin muryar kuka tace "tho Gwaggo zanyiwa ko tsoho?"
"dukansu har Halilu kice indai yana sonki yabarki kije kiyi ta musu kuka kina murje² in kikaga sunk'i yarda sai kice ke sai kin kashe kanki...."
maganar yake yana wani kalle² kamar wani munafiki,
ita ko sai kai take ɗaga mishi, hannunta ya rik'o "Maryam kimin alk'awari komai akayi bazaki faɗa ni nace kiyi haka ba"
"nayi wlh bazan faɗa ba"
murmushi yayi "yauwa ai inma kika faɗa ɓatawa zanyi dake dan haka karki faɗawa kowa kinji share hawayenki"
hannu tasa tana share hawaye yana tayata saida ya goge mata fuska sannan ya rika hannunta suka shiga cikin gidan,

*_©Khadeeja Candy_*

candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*38*

biye² Momi tayi dan duk inda wasu ɗangi suke na kusa saida takai Siraj,
da shine bai san dangi sosai ba sai kusan magariba suka dawo gidan Gwaggo danyi mata sallama, tana zaune tana tuki tuwo suka shigo Mairo na genta,
"Assalamu alaikum" Momi ce tayi sallamar Gwaggo ta amsa mata "amin wa'alaikumussalam ku wayannan sai yanzu?"
momi tace "tho ya muka iya Siraj ne ai ya tsayarda mu yanzu kan ai sai kama hanya"
"a'a zaku tsaya kuci abinci kan"
Siraj yace "a'a Gwaggo k'ara mu wuce kawai bason tuk'in nan na dare nake ba koma can ai munci abinci"
tashi Gwaggo tayi tana faɗin "kai ai da yayanka daman bason cin abincina kuke ba Allah dai ya kiyaye hanya"
dariya yayi ya ciro kuɗi aljihunshi ya mik'a mata "ga daishi a siye goro"
karɓa tayi tana godiya nan ya sake sa hannu ya ciro dubi kusan 5 ya mikawa Mairo, k'in karɓa tayi idonta suka ciko da kwallah "a'a nidai zan biku bama son nan"
hannun Momi ta rike ta fashe da kuka,
lallasarta Momi ta shigayi "haba Maryam ki bari har hutunku ya k'are sannan kinji kinga ko yanzu tsoho saida yayi ta mana masifa akanki kinga in mukaje dake faɗa zaiyi"
"nidai kije dani haka inaso Momi dan Allah karki bari"
risinawa Momi tayi ta dafata "tho ya isa daina kukan haka kinji ki tambaye Halilu in ya yarda sai na aiko a ɗaukeki amman fa sai inya yarda da zarar ya yarda kisa a bugamin waya kawai zam aiko mota aje dake?"
lak'e kafaɗa tayi "a'a nidai kije dani yanzu dan Allah Momi"
kuka ta ringa rusawa tana k'asa tana sama duk sai Momi taji ba daɗi babu irin lallaɓar da basuyi mata ba amman ta k'iyin shiru,
har bakin k'ofa ta biyosu tana jan gyalen Momi, nan Siraj ya shiga lallaɓata shida Gwaggo ganin abun nata na gaskene, k'in daina kukan tayi nan idanuwan Momi suka koma kwallah. daker ta samu tayi musu sallama suka kama hanya,

'''*****'''
cikin dare suka iso gida bayan Siraj yayi parking Momi ta fito rai ba daďi ta nufi part ďinta
palour ta tararda Qasin zaune yana kallon k'ofar data shigo, gyara zamansa yayi yana faďin "sannu da zuwa Momi"
wani irin haushinshi Momi taji ciki² ta amsa mishi "yauwa sannu"
saman kujera ta zauna tana sauke gajiya, Qasin ya kalleta yace "Momi yau ina kukaje haka tun safe naga kun fita kuma sai yanzu ka kuka dawo lafiya dai ko?"
"lafiya kalau k'auye mukaje"
Siraj ne ya bashi amsa yana k'ok'arin zaunawa kusa,
Qasin yadda yaji gabanshi ya faɗi yaji bazai iya k'ara tambayasu wani abu ba tashi yayi yasa hannayensa aljihu yace "sleep tight Momi saida safe" bai tsaya jiran amsarta ba ya nufi k'ofa,
saida ya fice Siraj ya kalli Momi yace "gaskiya Momi Maryam taban tausayi sosai banji daďin da muka barota ba"
wani guntun numfashi Momi taja tace "tho ya muka iya tunda haka suka zaɓa mata kuma kasan indai ba Halilu ya aminceba ba zasu bari muzo da ita ba"
"eh ai naga haka amman ya kamata a masa magana ya barta ta dawo nan kamin ya kammala shirye² kinga ta ɗan k'ara samu illimi"
"tho ai sai yaga dama tunda yanzu shi zai aureta"
taɓe baki yayi ya tashi yana faɗin "saida safe Momi"
"Allah ya tashemu lafiya nima ai bari na shiga ciki nayi sallah"
har zai fice Momi tace "amm.. Siraj gobe ma ka shirya muje gurin hajiya na mayar mata da amsa"
murmushi yayi yace "In'sha Allah" ya juya ya fice,

'''*** *** ***'''
*_3:47pm..._*
wani uban ta gumi Hajiya ta rafka wadda ya rufe mata fuska da kuma hanci,
cikin yanayin damuwa Momi tace "Hajiya babu yadda zanyi ne na buga na buga sukace ina su sam bazasu chanja zaɓin ds sukayi mata ba babu yadda banyi ba amman suka k'i aminta wai tun tana k'arama mahaifinta yayi wannan alk'awarin na haɗasu aure dan haka su bazasu tada ba"
saida Hajiya ta sauke ajiyar a'zuciya sannan ta kalli Momi tace "kin kuwa faɗa musu wanene yake sonta?"
"hmm Hajiya babu abunda ban faɗa musu ba inma baki yarda ba sai ki kira Siraj kiji komai dan tare mukaje ke in takaice miki labari magagganu babu daɗin ji nima ai kamar kar naje sai kin gani"
kai Hajiya ta girgiza "ni yanzu bansan yadda zan cewa Yarima ba ba fahimta zaiyi ba kuma yanzu yana iya cewa inba ita ba saidai ya fasa aure"
Momi tace "ni wlh dama zaki ɗauki shawarata a nema masa wata tunda yan'matan ne gasu nan kuma kyawawa"
Hajiya tace "ai inda matsalar take yace yana so ɗin"
dafata Momi tayi "ki yarda dani Hajiya In'sha Allah wannan sai yace yana so dan babu abunda akeso ga ‛ya mace wadda Allah bai bata ba babu wadda zai ganta yace baya sonta 'yar k'awata ce kawai ki bari mu haɗa shi da ita muga kuma abunda Allah zaiyi"
shiru Hajiya tayi kamin tace "tho yanxu mi kike ganin zance sa game da wannan yarinyar ta k'auye?"
"karki faɗa masa anyi mata miji dan inyaji haushin haka zai iya rufe mishi ido yak'i son wannan kawai ki bari inna kirata yaje ya ganta kinga in yace yana so sannan ki faɗa masa Maryam anyi mata miji kinga babu wani shan wahala nasan zai amince da wannan"
sosai Hajiya ta jidaɗin shawara daman mafita take ta nema,
da fira Momi ta jata sai kusan biyar ta baro gidan,

*_©Khadeeja Candy_*

candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*39*

*_K'AUYE..._*
tun tafiyar Momi Mairo bata kara walwalah ba duk tabi ta takura kanta kullum cikin kuka take tana kiran Momi duk tabi ta rame dan bata cin abinci ga ɗan banzan ciyon kai da take fama dashi wadda ya sakar mata zazzaɓi sanaɗin kukan da take, Gwaggo babu irin rarrashin da batayi mata ba har ta gaji ta zura mata ido,
yau ma kamar kullum tana zaune saman ta barma tana rusa kukanta data saba Halilu ya shigo,
tana ganinshi ta juyarda fuska ta k'ara fashewa da kuka,
saman tabarmar ya zauna yana bata hakuri. maimako tayi shiru sai abun ya k'aru Gwaggo ta tabe baki tace "aifa sai kayi ai duk kasan matsalar yarinyar nan ka barta taje birni kak'i ka dai riga kasan halin Mairo tun ba yau ba ba daina kukan nan zatayi ba dubi yadda duk tabi ta rame dan Allah ko abincin kirki bata ci amman baka tausayinta shiyasa mani nake tsoron auren nan naku wlh kar kaje can kayi ta gallaza mata daman ka saba"
Ajiyar zuciya ya sauke ya dafe kanshi,
_ba nida wata mafita sai wannan inhar na barta taje birni tho na rasata kenan dole ne na ɗauki shawarar Siraj dan itace kawai mafita agareni_
kallon Gwaggo yayi dake ta masa masifa yace "shikenan zan barta taje birnin amman sai in an ďaura mana aure ta tafi da aurena inma karatun zatayi taje tayi in yaso daga baya sai ta tare"
kafin Gwaggo tayi magana Mairo tace "da gaske halilu?"
kai ya ɗaga mata yana murmushin da baikai zuci ba "da gaske Mairo tunda naga kina son zuwa birnin"
k'ara matsowa tayi kusa dashi "yanzu ka yarda gobe naje?"
"a a sai an ɗaura aure"
"tho a ɗaura mana ni na ƴyarda a ɗaura sai naje"
bakinta Gwaggo ta buge ta kalli Halalu tace "indai har da gaske kake tho kaje ka sanarda tsoho duk abunda yace shikenan"
kai ya ɗaga "In'sha Allah haka za'ayi anjima zan sameshi mu tattauna"
da sauri Mairo ta rumgimeshi tana masa godiya,
fisgeta Gwaggo tayi ta jefar tana mata faɗa wai bata da kunya, Halilu kan daɗi yaji dan gani yake yanzu Mairo na sonshi tunda ta daina kukan aurenshi sai na a barta taje birni,

'''*** *** *** *** ***'''
cikin satin nan aka saka ranar ɗaurin auren, murna gurin Mairo ba'ah magana ko yar kunyar nan da yan matan k'auye suke yi ita batayi ba,
duk wadda yagani sai yayi zaton son Halilu take itakan bata ma kulaba murnar zuwa birni take, a'waya aka sanarwa da su Momi dama duk wasu dangi da suke nesa,
duk wannan abun da ake Qasin bai saniba dan ya daina zuwa part ďin Momi indai ba wani abun zaiyi ba Momi kuma ta fita sabgasar,
ana gobe ɗaurin aure Abbah ya dawo dan Momi ta faɗa masa ranar laraba za'a ɗaura,
*_2:45pm..._*
Momi na shirye² kaima Abbah abinci Qasin ya shigo rike da wata leda a hannu,
saman kujera ya dire kayan yana faɗin "gashi inji Abbah yace na kawo miki"
ba tare data kalleshi ba tace "shaddodin ne?"
"eh sune"
"ok barsu harna tashi amm ka shirya gobe zamuje ɗauri aure k'auye"
haka yaji maganar kamar wadda aka jefowa abu daga sama da k'arfi ya haɗeye yawu ya kalleta yace "auren wa Momi waza'ayima aure?"
tsayawa Momi tayi ta kalleshi "Maryam za a ɗaurawa aure amman bada kai ba da ɗan'uwanta Halilu"
a hankali ya kai zaune saman kujera "Momi ban gane abunda kike nufi ba?"
kusa dashi Momi ta dawo ta zauna tace "Qasin na fahimci baka son Maryam kuma kana tsoron matarka dan haka nake ganin inna aura maka ita na cilas maka na kuma shiga tsakaninka da matarka shiyasa nace musu ka yanje zancen nemanta su kuma sukace koda kai ko ba da kai ba su daman aire zasuyi mata dan haka suka zaɓa mata Halilu a matsayen miji gobe ne ɗaurin aurensu na sani ko ba yau ba wata rana kai da kanka zaka nemi k'ara auren"
kai ya girgiza baki na rawa yace "wlh Momi ina sonta Momi na shirya bin umarninki kodan na faranta miki miyasa kika yi haka ba tare da kinyi shawara dani ba haba Momi"
"aikin gama ya riga ya gama Qasin sannan banida tabbacin kana sonta ko a'a bazan iya kai Maryam gurinda nasan zata cutu ba inason ka shirya gobe ka halarci ɗaurin aurenta"
kasa ce mata kamai yayi ya tashi idonsa cike da hawaye jiki ba gwari ya fice.
da dare Qasin kasa bachi yayi haka yasa ya dawo parlour,
_tunani fal a ransa jin yake bai kyautawa Momi ba da kuma zuciyarsa dan harga Allah yana son Mairo saidai natsuwace bayaji a tare da ita haka yasa sai kuma yaji daďin yadda Momi tayi dan yana ganin hakan kamar mafitane a gareshi tunda yanzu tayi aure ai dole ya daina sonta_ juyawa yayi daga kwancen da yake, ya lumshe ido.

*_WASHE GARI..._*
tun 6 na safe Qasin yabar gidan, kuma ya kama duk wayoyinsa ya kashe,
haka su Momi da Abbah suka Kama hanya ba dashi ba Siraj dai inbanda dariya babu abunda yake yana faɗin wai Qasin kishi yake.

*_©Khadeeja Candy_*

candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*40*

*_K'ARFE 2:30PM..._*
aka ɗaura auren Mairo da Halilu babu laifi anyi taro saidai wasu yan'uwa na nesa basu samu halarta ba ango kan baki har kunne sai murna yake,
gudumuwa kan ya samu sosai musamman gurin Abbah.
ɓangaren Mairo ma farincikin ba baya ba dan ita zuwanta birni ne kawai a gabanta, da su Momi zasu dawo lak'ewa tayi sai ta biyosu daker aka samu aka lallaɓata bayan an aje ranar da Momi zata aiko a'je da ita.

'''*** *** *** ***'''
"miya hana ka zuwa ɗaurin auren nan Qasin?"
zaune yake saman kujera kansa a k'asa Momi kuma na tsaye kansa tana masa magana, a hankali ya ɗago kai ya kalleta yace "wani meeting ne mukayi da wasu chenis shiyasa na fita da wuri"
taɓe baki Momi tayi tace "tho Allah ya kyauta daman zancen karatun Nura ne inason ka nema masa admission a state University tun kamin lokaci ya k'ure"
"abun yana raina Momi nayi magana ai kuma In'sha Allah gobe zanje makarantar ma"
"Allah ya kaimu"
"Amin"
haka ya tashi ransa a jagule ya fice,

*_4 DAYS LETTER..._*
ruwan sama ake kamada bakin k'waya harda k'ank'anra,
Qasin na zaune parlour sanye da k'ananan, laptop na gabansa yana yan danne² sai cup ɗin drink dake gefen laptop ɗin. a hankali yaji ana shafashi ɗagowa yayi suka sakarwa juna murmushi "daman ba bachi kike ba?"
"a a idanuna huɗu baka jin sanyi dear kake zaune parlour?"
murmishi ya sake sakar mata "tho ya na iya so nake na k'are aikin nan kamin gobe dan-"
ihun daji yasashi kasa k'arasa maganar ya tashi da sauri ya nufi windo,
yana ɗaga labulen gabansa yayi wani dakan uku² ganin Mairo na gudu cikin ruwa tana son kama lema. kasa tantance abunda yake gani yayi mamaki ya rik'ayi yana tunanin abunɗa zai kawo Mairo gidan cikin wannan lokacin haka ya rik'a k'acce² wai ko idonsa ne suke masa gizo,
gani haka yasa Mansura ta karasa kusa dashi tana kallon windom tana ganin Mairo ta ɓata fuska ta taɓe baki "mts miye abun kallo gurin wannan mahaukaciyar ai daman ni nasan sonta kake"
juyowa yayi yana kallonta fuskarsa ɗauke da mamaki kwata² baya jin abunda take faɗi dan hankalinsa na can wani guri har ta k'are surutanta ta shige ko ɗaya kunnensa bai ɗauka ba,

*****
"gaskiya ni har yanzu sanyi nake ji sosai"
Mairo ce take maganar tana sanye da atamfa red colour da hijab tana saukowa downstairs,
Siraj dake zaune saman kujera ya kalleta yace "ai dole duk fa ruwan nan da akayi saman kaki suka k'are"
"tho ba lema naje kawowa ba sai suka jik'ani" "tho dan kinje kama lema sai akace ki tsaya cikin ruwa kiyi wanka?"
dariya tayi ta zauna saman kujera tana k'ank'anme jiki "kai kuma Siraj ba murna nake nazo birni ba saida fa nayi ta kuka sannan aka barni nazo"
rigar sanyin dake jikinsa ya cire ya mik'a mata yana faďin "ai naga duk kin rame k'arɓi wannan rigar ki saka"
saida ta k'arɓa sannan tace "kaifa?"
tashi yayi ya nufi stairs "bari na ɗauko wata"
kai ta ɗaga mishi ta shiga saka rigar,
takan mata yawa sosai saida kuma ta fitar mata da kyaunta sosai tana jan zip taji an buga k'ofa, da sauri ta nufi kofar tana buɗewa ta sako idanu "lahh Yarima"
"na'am pretty gal"
da murmushi ya amsa ya kai hannu ya shafa gefen fuskarta, sannan ya shigo.
hannunta ya rika suka nufi kujera Siraj na tsaye yana kallonsu da murmushi har suka zauna, sannan yace "ke Maryam tashi daga nan yanzu ba kamar da bane"
da sauri ta koma a ɗayar kujerar Yarima ya ɗago yana masa wani wulakantaccen kallo, can kuma ya ɗauke kai yana kallon Momi dake saukowa dwnstairs,
saida ta zauna sannan suka soma gaisawa "Yarima yau kaine a gidan namu da maraice haka?"
saida ya daɗe kamin ya bata amsa
"eh an faɗa min Maryam tazo ne"
mamaki ne fal a fuskar Momi "waya faɗa maka?"
"mutum..."
a takaice ya bata amsa yana kallon zoben hannunsa,
murmushi Momi tayi zatayi magana Siraj yace "Momi ya kamata yasan halin da Maryam take ciki yanzu Level ďinta ya chanja ba"
kallon Momi Yarima yayi alamar bai fahimci abunda Siraj ke faďi ba,
cike da tsoro Momi tace "Yarima...Marya...m fa yanzu ..matar..aurece.. satin da ya wuce aka ɗaura mata aure"
wani kyakkyawan murmushi ya saki wadda ya kara fitar da kyauwunsa yace "kidding me it's funny Momi"
Siraj yace "ba wasa ake maka ba yanzu Maryam igiya uku ce a kanta in kuma kana shakku kaje ka tambayi Hajiya ko kuma ita Maryam ɗin gata nan"
kallon Maryam yayi dake kallonshi tana dariya da rufe fuska, ya sake kallon Momi kai Momi da gyaɗa mishi tace "wlh an ɗaura mata aure Yarima kaji kuma na rantse"
tashi yayi tsaye ya wani yarfarda hannu "ohhh Momi inma gwadani ne kike tho ki daina bazai taɓa saɓuwa ba bindiga a ruwa bari kiji na faɗa miki tunda hajiya ta haifeni ban taɓa neman abu na rasaba wht ever I luff is my nd my only inason ki rubuta ki aje Maryam tawa ce no mttr wht dan haka in so kike ki gwadani k'ara ma ki daina in kuma so kike ki aura mata wani tho ki janye wannan tunanin..."
yana kaiwa nan ya karkaɗe rigarsa ya fice,
lumshe ido Siraj yayi yana _k'arya kake Maryan tawa ce duk wannan plan ɗin nawa ne tunda har yayana baya sonta tho mine mijina ba kaina she s my_ a zuciyar yake wannan zancen yana wani lafiyayyen murmushi.
[11/10, 2:13 PM] ‪+234 806 053 5947‬: *_©Khadeeja Candy_*

candynovels.wordpress.com
[11:27PM, 3/17/2017] Khadeeja Candy: ​*♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

Candynovels.wordpress.com

_How can I begin to say I am sorry akan rashin ganin post's d'ina akan Lokacin I didn't mean to upset you hakan yafaru ne akan wasu yan dalilai I didn't mean to do what I did,_ _Naga sak'wanninku da kuma calls d'in_ _wasu daga cikinku na gode da jajanta min wayanda ban samu damar yima reply ba my apologies please, and thanks to you all kuma KHADEEJA CANDY na alfahari daku and to my Cooperate writers na gode sosai da irin kulawar ku agareni Allah bar zumunci._

'''I DEDICATED THIS EPISODE TO ALL MAIRO FANS AND READERS.'''😘

_CIGABA...................._

*41*

Kallon Siraj mummy tayi cike da tsoro tace "kaga abunda nake gudu ko?" cikin mamaki Siraj yace "bansan abunda yasa kike tsoron Yarima ba Momi kina gudun 6acin ransa sama dana kowa kuma fa dolene a fad'a masa gaskiya dan ita matar aurece yanzu kuma dolene ya d'aga mata k'afa"
ajiyar zuciya Momi ta sauke tace "Bashi nake nufi ba bakaga yadda ya fita ba rai a 6ace inafa gudun abunda zaije ya dawo"
kai Siraj ya girgiza "babu abunda zai faru ki kwantarda hankalinki babu abunda zai iya yi"
Momi ba dan ta gamsu ba tace "Allah yasa haka"
Siraj ya amsa da "amin"
nan Mairo ta kalli Momi tace "nifa duk ban gane abunda yake faruwa ba" k'arasowa Siraj yayi kusa da ita yace "ai bazaki ganeba maganar manya ce jeki upstairs"
lak'e kafad'a tayi "ni bazani ba kasan ďazun kace zaka siya min ice cream in an ďauke ruwa"
murmushi yayi "yanzu da sanyin nan zan siya miki ice cream Maryam gashi ma duk sanyi ya kamaki ki bari har gobe saina siya miki chocolate" kai ta girgixa tana masa kallon rashin yarda "a'a Ni bazan yarda ba saika siya min kuma ice cream nake s-"
Bata k'arasa ba Momi ta katsa mata tsawa "Ke dan Allah rufema mutane baki wuce kije ďaki"
razana Mairo tayi da sauri ta nufi upstairs
da kallo Siraj ya bita saida ta shige ďaki Sannan ya kalli Momi yace "Momi kin razana ta sosai ki daina mata tsawa haka yau² fa tazo gidan nan"
Tsaki Momi taja "mtwwss aikin banza in yau tazo gidan nn yau ta fara zuwane? ai tasan halina sarai danni bazan ďaukar mata abunda Gwaggo take mata ba kuma faďa ai yanzu ya dace ayi mata shi dan tasan ciyon kanta yanzu fa babbar macce take k'okarin zama tunda aure ne da ita"
                dariya Siraj yayi "gaskiyarki Momi banga laifinki ba"
harara kawai Momi ta watsa mishi ta shige kitchen shi kuma ya fice yana dariya,

'''******'''
da dare Momi da Mairo na zaune parlor Qasin ya shigo,
Mairo na ganin shi ta tashi da sauri zata tare shi tana dariya "oyoyo yaya tun ɗazun na zo ban ganka ba"
Murmushi yayi ya ɗaga mata hannu alamar karta k'arso kusa dashi ya zauna a kujerar dake facing ɗin ta Momi yana faɗin "baki je part ɗina ba ai da kin ganni"
komawa tayi ta zauna tana faɗin "ai Momi ce ta hanani zuwa can kuma kasan yau anyi ruwa sosai"
kai ya ɗaga mata
"thom yayi kyau ya hanya dasu Gwaggo"?
"lafiya kalau suke duk sunce suna gaida ku"
"thom muna amsawa ina mijin ki?" dariya tayi ta shigar da kanta jikin Momi alamar kunya,
                Kallon ta Siraj yayi yana dariya yace "ni wallahi abun nan ni har dariya yake bani wai kamar Maryam Ace anyi mata aure"
Kallon rainin wayo Momi tayi masa "au kama ce ma? ai Maryam ta isa aure koda a nan birni ballantana k'auye shekarar ta fa goma sha 13 fa yanzu musulunci ma ai da shekara 9 ya halitta ayi macce aure baka ga ta kusan kamo kafaɗa ta ba?"
Kai Siraj Ya jinjina yace "lailai Momi kema kina cikin masu ra'ayin yan da"
Momi tace "sosai ma aini da ace yaya mata Allah ya bani bazan bari suyi wani girma ba zan aurarsu dan bazan yarda mu haďa kafaďa dasu ba a'rasa gane uwar sai kace yayan yahudawa"
dariya Siraj yayi shida Mairo banda Qasin daya maida hankalinsa gurin tv,
sun daďe suna fira amma ko uffan bai ceba sai can ya kalli Momi yace "Momi me Maryam tazo yi?"
"cigaba zatayi da karatu"
Siraj ne ya bashi amsa
fuskar mamaki Qasin yayi yace "ba'a mata auren bane?"
murmishi Siraj yayi ya jefa masa tambaya ba tare daya amsa masa tasa tambayar ba "kamar ya ba'ayi mata auren ba?"
Qasin yace "tho ya za'a ďaukota a rabota da mijin azo nan da ita ace wani karatu zatayi sai in daman can ba'ayi mata auren ba"
Sai a lokacin Momi tasa baki "da izinin mijinta tazo nan"
gyara zama Qasin yayi yana murmushi mai ďauke da mamaki yace "nifa ban gane inda zancen nan ya dosa ba ya za'ace an ďauko yarinya daga k'auye a kawota birni tayi karatu kuma karama kamar Maryam"
Siraj ne ya tari numfashinsa "tho ai da yarda su Gwaggo tazo nan kuma shima mijin nata ya aminta ni banga wani abu a ciki ba"
kallon Mairo Qasin yayi ta wani marairaice jikin Momi kamar ba itaba kafaďunsa ya ďaga ya tashi tare da sa hannunsa aljihu ya fice,

Har ya isa part ďinsa tunani yake abunda yasa Momi take son yin haka sam zuciyarsa k'in yarda tayi da anyi mata aure,
_thom amman su Abbah sunje ďaurin aure kwanakin baya sai in ba nata bane in har kuma ba nata bane thom na wane_
Haka zuciyarsa ta rik'a masa sak'e² har ya shiga cikin parlour.
Zaune ya tararda Mansura ta wani sha kunu tana wani kunbure² murmushi yayi ya k'arasa kusa da ita yakai hannu ya shafa gefen fuskarta "my heart ya naga fuskarki haka?"
ture masa hannu tayi ta juyarda fuskarta, hannunta ya kama "wai mi yake damunki ne waya ta6a min zuciya?"
cikin fushi tace "ina kaje?"
"gurin Momi"
"mi kayi?"
"kamar ya mi nayi?"
cike da mamaki ya mayar mata da tambayar,
juyowa tayi ta kalleshi "gurin Maryam kaje Qasin"
fashewa yayi da dariya "kina bani mamaki Mansura bansan abunda yasa damun kanki akan Maryam ba yarinya da yanzu ta riga ta zama matar aure"
"thom mi tazo yi nan in har da gaske an ďaura mata auren?"
ta6e baki yayi "Momi tace karatu zata cigaba dayi kuma mijinta ya yarda"
shiru tayi alamar tunani ganin haka yasa ya janyota ta kwanto saman k'irginsa yana faďin "minene na wani tsayawa tunani dear baki yarda da mijinki bane?"
kallonshi kawai tayi ta zare hannunta daga nashi ta tashi ta shige bedroom,
da kallo ya bita harta shige sannan ya sauke ajiyar zuciya yana _"oh ni Qasin kuma yanxu wace rigimar ce Momi zata janyo min da Mansura"_
tsaki ya ďanja ya tashi ya sake nufo part ďin Momi,

tun kamin ya k'araso ya hango Mairo tsaye bak'in k'ofar tana kallon part ɗinsa,
shima ita yake kallo zuciyar na bugawa har ya k'araso fuska a ɗaure yace "min kike yi a nan?"
hannu tasa a baki tayi k'asa da kaita "Siraj nake jira Momi ta aike shi"
"shine zaki zo nan kiyama mutane tsaye da dare haka wuce ki shiga ciki"
da ɗan faɗa yayi mata maganar hakan yasa bata masa musu ba ta juya ta shiga shi kuma ya rufa mata baya,
tsaye tayi tsakiya parlor tana kallon shi har ya zauna "yaya....."
ciki² ta kira sunan shi yana kallonta tace "abinci zaka ci?"
Shiru yayi kamar ba zai amsa mata ba can kuma ya girgiza mata kai alamar a'a yace "ina Momi?"
da sauri ta bashi amsa "tana ɗaki bari na kirata" bata jira mi zaiceba ta nufi stairs da gudu,

_3 Minutes Later_
ta fito rike da hannun Momi k'asa Qasin yayi da kansa har suka sauko,
Zaunawa Momi tayi tana kallonshi "lafiya Qasin?"
ɗagowa yayi ya kalleta "Momi akan Maryam ne yanzu wannan abun da aka yi ba zai haifar da wata matsala ba?"
Kamin Momi tayi magana suka ji parking ɗin mota da sauri Mairo ta tashi ta nufi k'ofa dan a zaton ta Siraj ne,
juyowa tayi da sauri tana faɗin "Momi ga Yarima nan da wata mata"
da sauri Momi ta tashi tsaye "Yarima?" Momi ta tambaya nan Qasin ya tashi ya lek'a ta window cikin mamaki yace "Hajiya ce tare da Yarima miya kawo ta da dare haka?"
Kai Momi ta girgiza "daman nasan za'a rina" kallonta Qasin yayi "wani abun ne ya faru Momi?"
bata bashi amsa ba ta kalli Mairo tace "ke jeki ɗaki"
da gudu Mairo ta nufi upstairs.



*One heart One luff ❤*
*for my fan's*😍

*_©KHADEEJA CANDY_*
[11:27PM, 3/17/2017] Khadeeja Candy: ​*♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

Candynovel.wordpress.com

*42*

Da sallama Hajiya ta shigo parlor fuskantar ba yabo ba fallasa,
Momi da Qasin suka amsa mata guri ta samu ta zauna tana amsa gaisuwar da Qasin yake mata saida Hajiya ta gama gaisawa da Momi sannan Yarima ya shigo hannaye sa sanye cikin aljihu kansa a ɗage yana kallon ceiling,
kallo ɗaya Qasin yayi masa ya ɗauke kai dan yasan babu komai a tattare dashi sai rainin wayyo da wulakanci, zaunawa Yarima yayi yana ya mutsar fuska can ya kalli Momi yace "Momi ya dare? "
da far'ah ta amsa masa "lafiya kalau Yarima ya harkokin"
saida ya ɗan daɗe sannan ya amsa mata ciki² "Alhamdulillahi"
Murmushi Momi tayi ta kalli Hajiya tace "lafiya dai Hajiya na ganki da dare haka?"
Nisawa Hajiya tayi tace "lafiya kalau wata magana ce Yusuf yazo min da ita ɗazun shine nace bari na zo da kaina naji yadda abun yake"
da ɗan fargaba Momi tace "wani abun ne?"
Hajiya tace "ce mun yayi yaga yarinya da yake so a nan gidan wadda muka yi magana dake har nake ce masa kodai ba ita bace yace itace ni kuma nace bari na zo da kaina naji"
Momi saida tayi murmushi sannan tace "wai Maryam kike magana ta dawo ne dan zata cigaba da karatu ne kamin mijin nata ya ɗan kintsa"
da mamaki Hajiya tace "ya ďan kintsa kamar yaya nifa kwata² ban gane inda kika dosa ba Maman Nura yarinyar daman mijin bai shirya ba aka aura masa ita?"
Momi tace "Hajiya kinsan auren k'auye sai a han-"
bata k'arisaba Yarima ya katse ta "wait! wait!! wait!!! ni ban gane inda kuka dosa ba wai kuna nufin da gaske anyi mata aure?"
Momi ce ta riga bashi amsa "anyi mata aure Yarima ai kasan ba zanyi maka k'aryaba....... "
sai a lokacin yaji wani mummunan faɗuwar gaba tashi yayi tsaye yana kallon Hajiya yace "baki faɗa mata inason Maryam ba?"
ajiyar zuciya Hajiya ta sauke cikin sanyin jiki tace "na faɗa mata Yusuf na tambaya maka aurenta sai dai a lokacin ka riga kayi latti dan anyi mata engaged da wani har ma ansa ranar aure su ni kuma sai naji tsaron faɗa maka saboda gudun ɓacin ranka na yanke shawarar nema maka wata ba tare da ka sani ba"
tana kaiwa nan Yarima ya girgiza kai yana murmushin da za'a iya banbancewa shin na bak'in cikin ne ko kuwa na ɓacin ran da Hajiya ke magana,
rumtse ido yayi ya buɗe ya kalle su yace "Maryam bata isa aure ba ballantana na yarda da anyi mata auren da gaske, nima kaina raino ta zanyi har sai ta mallaki hankali kanta sannan na aure ta kuma ni babu ruwana da wani plan naku ko anyi mata aure ko bayi mata ba ni aurenta zanyi in'ma har anyi mata auren thom ku warware shi dan duk abunda nake so nawa ne ban taba son abunda ba nawa ba"
cikin wani irin ɓacin rai ya k'arasa maganar,
nan Qasin ya kalleshi a hankaɗe yace "su warware aure saboda kai ka haife su ko kuma dan kana wawa? But banga laifinka ba cox If you are shameless, you would do as you wish"
hannu Yarima ya ɗaga mishi yana wani izgilanlen murmushi "wait please Mr Pest stay where you are"
nan zuciyar Qasin ta kawo ya tashi tsaye tare da nuna shi da ɗan yatsa "you are fool Yarima Koda ba'a ɗaurama Maryam aure ba bazan taɓa bari ta aureka ba dan kai baka dace da zama mijin Maryam ba"
tsawa Momi ta katsa masa "ya isa haka Qasin! wace irin magana ce wannan Yarima bai dace da zama mijin Maryam ba sai kace wani mugun mutum ya kamata ka rik'a tauna magana kamin ka furta ta"
cike da ɓacin rai Momi ta k'arasa maganar,
nan Qasin ya sassauta murya ya kalli Momi yace "Momi karki ɓata ranki akan abunda na faɗa kinfi kowa sanin wanene Yarima wata k'ila ma mugun halinsa baya rasa nasaba da abunda yasa kika hana masa Maryam"
hannu Hajiya ta kai ta dafa kafaɗar Qasin "Qasin ɗana kake aiban tawa haka har kake ik'irarin hana masa matar daya buɗe baki ya furta yana son ya aura kuma kake faďa masa wayan nan kalaman a gaban idona mi yayi maka haka Qasin?"
taɓe baki Yarima yayi yace "kin ga ɗaya daga cikin abunda nake faɗa miki kenan ai Qasin yafi gaban haka"
matsowa Qasin yayi kusa da shi yana faɗin "banyi maka k'age ba Yarima, mummunan halinka a bayyane yake kai-"
"Qasin............"
da k'arfi Momi ta kira shi hakan yasa ya kasa k'arasa maganarsa,
K'ofa Momi ta nuna masa "wuce kabar parlor nan"
Hajiya ce ta tari numfashinta "ki barshi kawai ya faɗi son ransa damace ya samu sabodaYusuf yaga jininku yace yana so shine kake son wulakanta shi ko?"
kai Qasin ya girgiza "ba haka nake nufi ba Hajiya koke kikaji abunda Yarima ya aikatawa Maryam ba zaki yarda ya aure ta ba ya lalata mata rayuwa ya mayar da ita babbar mace"
Wani irin sanyi jikin Momi yayi da sauri tace "kabar wannan maganar Qasin karka kuskura aikata abunda zai zame maka matsala"
k'asa yayi da kansa ganin yadda ran Momi ya ɓace,

tsaki Yarima yaja "mtssww aikin banza kara min mutum ai da ka faɗa ni duk a tafin hannu nake kallonku daga kai har Momi babu wani plan da zaku haďa da zaija kwakwalwata ni da kai kar tasan kar ne" har lokacin kan Qasin a kasa yake yana sauraren kalaman Yarima, gudun 6acin ran Momi yasa ya kasa ďagowa yace masa ko da uffan.
matsowa Hajiya tayi kusa da Qasin tace "me kuke nufi da wayannan kalaman Qasin me kake nufin Yusuf dashi me kake nufin ya aikata me kuke k'ok'arin yi haka? saboda ba Siraj bane ko shiyasa kake aibata shi har kake k'ok'arin yi masa k'age?"
nan Qasin ya ɗago kai ya kalleta a natse yace "shima ɗan uwana ne kamar Siraj Hajiya ba k'age nake masa ba shi kanshi ya sani na sani Momi ma gata a nan ta sani fyaďe yayi ma Maryam........"

tassssssssss!!!
Momi ta wanke fuskar Qasin da mari Hajiya kuma ta k'ura masa ido tana son tantance abunda ya faɗa,
fashewa Yarima yayi da dariya ya rik'a tafa hannayensa kamar wadda aka yima albishir,
matsowa yayi kusa da Qasin ya rik'a wuyar rigarsa da yatsu biu ya ɗan ja kamar mai wasa da yaro ya girgiza kai yana murmushi yace "ohhh brother why are you so stupid today? u knw wht da ace a film ne mukeyi a nan da ka zama super star cox it really works"
Sake masa wuyan rigar Yarima yayi ya ɗan matsa baya yana nuna shi da yatsa "bansan Wayyo ka iya nan ya tsaya ba i thought kai wani super hero ne ashe kai sakarene ai Kana da dama fel free 2 tll th wrld hw yuh hate mie ba sai kamin k'azafi ba"
Qasin cikin jan ido yace "in har nace bana sonka k'arya nake dan bansan ribar da zanci ba in'na tsaneka ba k'azafi nake maka ba Yarima abunda ka aikata ne na faɗa karka kuskura sake k'aryata ni"
wata dariyar Yarima ya sake yi ya shafa gashin kansa daya kwanta luf yace "I think ka manta wanene Yusuf bazan taɓa aikata abunda ka faɗa ba koda ga babbar mace ballantana ga k'aramar yarinya kamar Maryam pls tll mie nawa aka biya ka kayi min wannan k'azafin? nasan kai dan kwangila ne mai neman kuɗi ta kowace hanya kuma yima mutum irinna wannan k'azafin babbar hanyar samun kuɗine dan za'a baka million dollars go ahead tll mie waya saka wannan aikin?"
ya k'arasa maganar yana masa wani abu da hannu kamar mai wasa da maciji,
                        zauna Momi tayi dafe da kai dan bata jin akwai wani abun da zata iya cewa kota aikata dan Qasin ya riga ya chakuɗe komai iya ɓaci dai ranta ya gama yi,
Hajiya ma haka ta gama kamar yar kallo dan ta kasa furta komai gashi zuciyar ta tak'i yarda da abunda Qasin ya faɗa duk da tasan halin ɗan nata da yadda mutane ke yabonsa da mugun hali sai dai kuma ba ta taɓa jin anyi masa k'azafin zina ba,

                qat.qat..qat... Yarima ya rik'ayi kamar mai kiran akuya yana faɗin "ina jinka faɗa min mana karkaji tsoro ni ba wani abun zai maka ba"
sai a lokacin Qasin yayi murmushi yace "wh d yuh thnk yuh are da har za biyani nayi maka k'azafi let mie tll yuh somethng yuh are nthng bt pest in trash ita da kanta Maryam ɗin ita ta faɗa"
waje Yarima yayi da ido kamar wadda yaji tsoro da gaske "OMG really?" sai kuma ya fashe da dariya ya shiga k'walama Mairo kiran da saida muryarsa ta cika falon,

amsawa tayi daga can cikin ɗakin sannan ta fito tayi tsaye bakin k'ofa tana kallonsu,
Suna haɗa ido da Yarima ta sakar masa Murmushi shima murmushin ya mayar mata ya mik'a mata hannu alamar tazo da gudu ta nufo downstairs tana dariya,
can idon ta suka kai ga fuskar Qasin ganin yadda yake harararta yasa data k'araso bata rik'a hannun Yarima ba ta rungume hannayen nata far'ar dake fuskantar ta gushe tayi k'asa da kanta,
mamaki ne ya cika Hajiya a ranta tana _...daman wannan ce yarinyar da Yusuf yake so k'arama..._
tashi Momi tayi tsaye ta nuna ma Mairo upstairs "ke wuce ɗakin..."
harta juya Yarima ya rik'ota "no Momi barta akwai abunda zan tambaye ta......"
hannu Qasin yasa ya buge hannun Yarima "ɗauke hannun ka daga jikinta"
dago hannun Yarima yayi ya kalla ya taɓe baki yace "are yuh jealous my friend kodai kai ma sonta kake shiyasa kuke wannan drama?"
wata mugunyar harara Qasin ya watsa masa "in sonta nake kai ka isa ka hanane da har zamu tsaya yin wata drama?"
dariya Yarima yayi ya ɗaga hannayensa sama "no ai ni ban isa na hana zuciyar ka faɗawa son yarinyar da ta kusa ta zama matar wani ba" cike da isa ya k'arasa maganar,
Qasin zai sake yin magana Hajiya ta kalli Mairo tace "ke Maryam faɗamin abunda Yarima yayi miki?"
ɗagowa Mairo tayi da kanta ta kalli Hajiya tace "ni bai min komai ba"
tsawa Qasin ya katsa mata "ke...! faɗi abunda Yarima yayi miki ranar daya fita dake bai dawo dake ba sai dare kika shigo jini na miki zuba da muka tambaye ki abunda ya faru kika ce yace duk kika faɗa sai ya kashe ki"
nan da nan tsoro ya bayyana a fuskar Mairo da k'arfi ta haɗeye yawu ta kalli Yarima idanuwanta kamar zasu zazzago.


*_©KHADEEJA CANDY_*
[11:27PM, 3/17/2017] Khadeeja Candy: ​*♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

Candynovel.wordpress.com

*43*

Murmushi Yarima yayi mata ya kaɗa mata kai alamar ta faɗa ganin haka yasa ta kalli Momi da Qasin sannan ta sake kallon Yarima cike da tsoro tace "bai min komai ba"
cikin tsawa Qasin yace duk baki faɗa ba saina miki shegen duka na kakkaryaki"
nan wani sabon tsoro ya sake shigar ta ta fashe da kuka tana faɗin "dan Allah yaya Qasin kayi hak'uri Wallahi yace duk na kuskura na fada sai ya kashe ni"
nan Qasin ya kaɗa kai ya kalli Hajiya yace "good yanzu kinji da bakinki ko?"
Kallon Yarima Hajiya tayi cike da mamaki da kuma sanyin jiki.
Murmushi yayi ya risina daidai tsaron Mairo ya soma mata magana a hankali "karki ji tsoro Maryam ki faɗa mishi duk abunda ya faru ranar kinji?"
lak'e kafaɗa tayi "a'a ba kace duk na faɗa ba zaka kashe ni"
Kai ya girgiza mata "no na fasa yanzu ma in kika faɗa harda chocolate zan siyasa miki na baki kuɗi"
shiru tayi alamar tunani can tace "da gaske ba zaka min komai ba?"
"bazan miki komai ba ai ni nace ki faɗa"
"thom rantse sauka rantse ba zaka min komai ba"
sai da ya yarda ya rantse mata sannan ta sake kallo shi tace "kadai san ba'a wasa da Allah ko ka dai riga ka rantse ba zaka min komai ba"
Sai da ya ɗaga mata kai sannan ta kalli Qasin murya k'asa² ta soma magana,

"Daman ranar da muka fita wani guri mukaje gurin buki daga can sai muka shiga mota zamuje wani gurin sai wasu suka cin mana da mota suka tsayar da mu duk fa suna ɗauke da bindigogi manya sun ɗauke wani mutum da sarka sai Yarima yaje yayi magana dasu har ya mari wadda aka ɗauren ya bugar masa baki ni kuma duk naji tsoro kwarai shine yace duk na faɗa sai ya kashe ni shine yace wani ya kawo ni gidan......"
kai Qasin ya girgiza "karya kike Maryam wannan ba shine kaɗai abunda ya faru ba"
rantsuwa ta shiga masa da kuka "wallahi yaya shine abunda ya faru ba karya nake ba kuma ka tambayi Yarima gashi nan"
matsowa yayi kusa da ita ya watsa mata mari da sauri ta nufi gurin Momi dafe da kuncin tana kuka,
Yarima ya kalle shi yace "ina tunani ta faɗa maka komai maye na wani dukanta kuma?"
yana nuna ta da yatsa yace "sai ta faɗamin dalilin zubar wannan jinin data shigo dashi"
"menstruation ne Qasin"
Momi ce ta bashi amsar tana share hawayen da suka zubo a fuskarta,
da sauri Qasin ya kalleta haka ya rik'a jin maganar tana masa yawo a k'wak'walwa nan da nan yaji jikin sa ba k'arfi gumi ya shiga karyo masa​

murmushi Yarima yayi ya rik'a wuyan rigar Qasin da hannu biu yana gyara masa kwalar rigar yace " ba haka ake takara ba Qasin da ace kai ɗan siyasa ne da ka faɗi zaɓe dan baka iya siyasa ba i really believed da ace kai lauya ne thom da kaji kunya a gaban kotuna da dama"
sake masa rigar yayi harya juya sai kuma ya juyo ya kalleshi yana tsotsar baki yace "u knw wht my frnd we are all in th sme game bt dffrnt roads wannan karon ka faɗi bt it is a deal btwn us last rubuta Ka aje I wsh yuh a very gud luk nxt time swt drm...."
da wani shu'umin murmushi ya k'arasa maganar ya sara masa sannan ya kalli Momi yace "ki kwana lafiya Momi"
yana kaiwa nan ya nufi k'ofa,
Kiran shi Momi ta shigayi idon ta sai zubar da k'wala suke, yi yayi kamar bai ji taba yayi ficewarsa.
nan Hajiya ta matso kusa da Qasin ta kalli k'wayar idonsa cikin sanyayyiyar murya tace "ko a mafarki ban taɓa tsammanin wannan ranar ba ban taɓa tunanin zaka iya yima ɗan'uwanka abunda kayi masa yanzu ba ina saka layin masu hankali da tunani duk abunda Yusuf yake faɗa a kanka ban taɓa yarda ba sai yau ka chanja rayuwa Qasin dan Yusuf ɗan'uwankane ba abokin gaba ba"
juyowa tayi gurin Momi idonta cike da k'wallah tace "kin ɓata wayonki da kike biyewa ɗanki kuka aikata abunda ban taɓa tunani ba"
dubawa tayi ta ɗauki jakarta harta fice Momi bata ce mata uffan ba sai hawaye take,

darker Qasin ya iya ɗaga kai ya kalli Momi "Momi dan Allah kibar kukan nan wallah-"
bai k'areba ta ɗaga mishi hannu tana hannun Mairo suka nufi upstairs.

Da ido ya bisu itama Mairo ta sako masa nata idon har suka shige,
Ajiyar zuciya ya sauke ya lumshe ido iya ɓacin rai ya san Momi tayi shi shi sam bai ɗauka abun haka yake ba kuma gashi har yanzu zuciyarsa tak'i yarda da abunda Mairo ta faɗa dan shi gani yake kamar biye wa ne tayi wata ajiyar zuciyar ya sake saukewa sannan ya buɗe idon ya nufi part ɗinsa jiki ba kwari,
duk wannan abun daya faru a idon Siraj ya faru dan yana tsaye a windon baya yan kallon su baby komai a I donsa sai kwallah dukawa yayi a gurin ya dafe kai,

sululu ya shiga parlor harya zauna bai lura da Mansura ba dan kwata² hankalinsa baya jikin shi "sai yanzu ka dawo ai daman nasan haka zai rik'a faruwa tunda ta dawo"
maganarta ce ta dawo dashi daga dogon tunanin daya tafi kallon ta yayi cike da jin haushi yace "gurin ta naje ko zaka hana ne?"
da sauri ta tashi tsaye "Qasin ni kake faɗawa wannan maganar?"
"an faɗa miki ke wace irin macce ce haka damuwa mijinki bata dameki ba sai kishi tirrr da halinki sai yanzu na soma yarda da wayansu kalamai da Momi take faɗa a kanki ba kida tunani wlh"
idon ta cike da hawaye tace
" *HAKA NAMIJI YAKE* banyi mamakin jin wannan kalmar daga bakinka ba daman nasan Momi ba sona take ba daman nasan-"
tassssssssss ya wanke mata fuska da mari yana nuna ta da yatsa yace "iskancinki ya tsaya kaina karki kuskura saka Momi a ciki dan ba sa'arki bace"
Baya² tayi tana kallon shi wani tsoro ne ya kamata wadda ko faɗa baya son mata yau gashi harda mari juyawa tayi da gudu ta shige ɗaki tana kuka,
faɗawa yayi zaune saman kujera ya lumshe ido "oh ya Rabbi" abunda ya furta kenan yana cizon baki,

'''***         *    **            ***'''
cikin wani irin ɓacin Yarima ya isa gida yana sauke Hajiya ko motar bai fito ba ya nufi gidan sa,
        cikin yan mintuna ya isa sakamakon gudun da yake    ido a rufe yayi parking ya nufi k'ofar parlor da k'arfi ya tura k'ofar ya shiga yana wani irin numfashi da k'arfi.
zaunawa yayi yana murmushi mai cike da jin haushi yana kaɗa kai "lallai Qasin kana wasa ni zaka yima irin wannan siyasar hmmm yanzu ne ko zaka gane wanene ni dan saina aure ta"
        wayarka ya ciro ya shiga danna neman number sannan ya danna callin bara daɗe tana ringing ba aka ɗauka "clock ka sameni gida gobe" haka kawai yace ya kashe wayar,
a hankali yaji an kai hannun ana taɓa shi tun daga k'eyar kansa har zuwa kirjinsa k'ara haɗe fuska yayi ya ɗaga idanuwansa sama yana faɗin "don't Zil am not in the mood......"

*_©KHADEEJA CANDY_*
[11:27PM, 3/17/2017] Khadeeja Candy: ​*♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

Candynovel.wordpress.com

*44*

Yi tayi kamar bata jishi ba ta cigaba da shafa shi,
Hannun ta ya fisgo da karfi ya yarfar ya tashi tsaye yace "nace miki am not in the mood bakida hankaline?"
Da sauri ta Kalleshi tsantsar ɓacin rai ta gani a tare dashi "Yarima mi yake damunka waya ɓata maka rai?"
Sama yayi da kansa "Zil miya kawo ki nan?"
"wannan wace irin magana ce ai kasan banada gurin zuwa sai nan wai wane irin ɓacin rai ne ya rufe maka ido haka Yarima Kaga yadda ka koma kuwa?"
Fuskarsa ya shafa yana yak'unar hanci "u are right Ni kaina nasan na chanja na daɗe banga ɓacin rai irin wannan ba ban taɓa sanin inason Maryam ba sai yau kuma kota halin yaya sai na aure ta koda sama da k'asa zasu haɗe"
cikin rashin fahimta tace "ban gane ba Yarima wata kake so ne?"
Murmushi yayi "yes wata kyakkyawar yarinya ce mai k'ananan shekaru kuma yar k'auyen"
Kai ta girgiza "kasan da ni kake faɗawa wannan maganar ko dai wani abun kasha?"
tana kare maganar ya wanke mata fuska da mari biu ya nuna ta da yatsa "karki kuskuren faɗa min kalmar da zata daɗamin ɓacin rai ɓace ki bani guri"
yanayin fuskanta naga ya chanja cikin ɓacin rai tace "babu inda zanje kawai ka fada min aure zaka yi ko me?"
gira ya ɗaga mata "yes aure zanyi tsoronki nake jine"
"tho ni kuma kayi yaya dani?"
"ai nasha faɗa miki Zil bazan taɓa iya aure ki ba maybe bazaki yarda ba har sai kinga matata a cikin gidan nan"
kwalla ne suka cika mata ido cikin muryar tausayi tace "amman ka ɓata min rayuwa Yarima ka raba ni da karatuna kasa na watsarda samarina"
murmusawa yayi ya taso yazo daf da ita ya ɗora hannayensa saman kafaɗarta yace "kina da matsala Zil mi yasa kike ɗora min wayannan laifukan koda yaushe ni ban lalata miki rayuwa ba kuɗine suka ja hanalinki kikaga zaki iya kum gwargwado na kyautata miki tunda na baki mota na kai ki makka na mallaka miki gida na cia miki account ɗin ki and what else do you need?"
Hannunsa ta rika hawaye nabin fuskanta tace "duk abunda ka zana yanzu ba sune a gabana ba aurenka nake so shine cikar burina"
Kai ya girgiza ya janye hannunsa "am so sorry Zil dear bazan iya yi miki wannan ba"
Cikin ɗaga murya tace "ba a haifi matar da zaka aura ba Yarima ba ayika dan ko wace mace ba sai ni kuskure ne kasa son wata a ciki zuciyar ka matukar ina raye"
Fashewa yayi da wata mahaukaciyar dariya yasa kafarsa ya kaɗe mata kafafu ta faɗi da karfi sai da kashinta ya amsa (yayi kara) sannan ya sake kai mata wani mugun shuri ba shiri ta saki ihu ya nuna ta da yatsa yace "ba'a faɗa min irin wannan maganar be careful next time ɓace min da gani"
da sauri tayi baya² ta shige ɗaki da kuka,
shi kuma ya zauna saman kujera yana cikama bakinsa iska
bai bar parlor ba sai kusan 3 dare bayan y gama sake² ya nufi bedroom,
zaune ya tararda Zil babu abunda take sai kuka tana rike da kunkurota kamar mai shirin haihuwa, yana kallonta yaja tsaki ya shiga toilet ya watsa ruwa ya fito
yana cikin saka kayan bachi yace "baci zanyi malama ko kiyi shiru koki fita kije gidan ubanki" ba shiri ta hade bakinta ta matse haka rage hasken wutar ɗakin yayi kwanciyarsa ya barta zaune.

*WASHE GARI..........*
8:34am Qasin ya shigo part ɗin Momi bai iya yin sallama ba saboda bugun gaban daya sami kansa dashi har ya isa dining room,
Nura da Usman suna zaune suna karyawa Momi kuma ta tisa abincin a gaba tana kallon wani guri
Mairo ce ta Kalleshi tace "yaya ina kwana?" da murmushi ya amsa mata "lafiya kalau Maryam an tashi lafiya?"
Kaita ɗaga mishi ta na dariya nan suma suka shiga gaida shi bayan ya amsa ya kalli Momi yace "Momi an tashi lafiya?"
ba tare data ɗago ba ta amsa mishi "lafiya kalau"
cikin sanyi jiki yace "dan Allah Momi kiyi hak'uri wallahi banyi-"
kasa k'arasa maganar yayi sakamakon ɗagowar da tayi ta ɗaga mishi hannu "karka kuskura fitar da kalma ko ɗaya daga bakin ka matuk'ar ni zaka furtawa ita kawai ka fita kabar parlor nan"
Nan da nan yanayinsa ya kara chanjawa bugun zuciyarsa ya karu kamar ya fasa kuka yace "dan Allah Momi karkiya fushi dani dan adam ne ni ajizi wallahi banyi hakan dan na ɓata miki rai ba dan Allah ki gafarce ni"
Momi fuska a ɗaure tace "bana fushi da kai tun har na iya amsa s
gaisuwarka kawai dai ka ɓace min da gani nace"
tsayar da cin abinci Usman yayi ya kalli ta yace "Momi lafiya?"
"babu ruwan ka kuma karka kuskura sa min baki a magana kaima inka kare ka tashi ka fice"
k'asa yayi da kansa shida Nura suna mamakin abunda yasa ran Momi ya ɓace haka,

tsaye Qasin yayi yana kallonta kamar ba dashi take maganar ba sai son yake yayi magana kuma ya kasa
ganin haka yasa Momi ta tashi ta bar mishi parlor,
Jinginawa yayi da ginin dake gurin ya dafe kai yana cizon baki ya daɗe a haka sannan shima ya juya ya fice,
Nura da Usman ma suna ganin ya fita suka tashi suma suka fice aka bar Mairo ita kaɗai sai cin abincin ta take tana yan wake²,

                baifi 5 minutes da fitar su ba Siraj ya shigo fuskarsa babu yabo ba fallasa sallamar ma ciki² yayi ta Mairo ta amsa masa ta kaɗa kai "taf lallai ma kai wannan yaron sai yanzu kaga damar tashi har kowa ya gama breakfast? Kayi olo ma dan abincin ya k'are"
Murmushi ya ɗan yi "aini ba abinci zan ci ba"
gyara zama tayi "saboda me?"
shiru ya ɗanyi sannan yace "a zumi nakeyi"
taɓe baki tayi "thom kun zama ɗaya kai da Momi kenan"
"itama a zumin take ne?" ya tambaya saida ta girgiza kai sannan ta bashi amsa "a a bata dai ci abinci ba"
"miyasa?"
"Nima ban sani ba kila bata da lafiya dan tun jiya kuka take ko bachi bata yi ba"
da a sauri ya nufi upstairs jikinshi na rawa ya tura k'ofar ɗakin Momi,
da sallama ya shiga ta amsa masa da muryar kuka "wa'alaikassalam"
kusa da ita ya zauna yana faɗin" Momi kuka kike yi ne?"
bata iya ce masa a'a tunda yaga hawaye a idonta kawai sai kawarda fuska,
Hannun ta ya rik'a "dan Allah Momi kibar kukan nan Maryam tace tun jiya take kukan nan"
hannu tasa ta share hawayen tana faɗin "dole inyi kuka Siraj jiya Qasin a gaban Hajiya ya aibanta Yarima ɗan ta kwara ɗaya ɗan da tafi kowa sonsa ban taba ganin bacin ranta ba irin na na jiya wani abu bai taa haɗa ni da itaba sai jiya kuma nasan zata rika ɗaukar na hana ma ɗanta Maryam da nasan rikonta haka zai zamar min daban ɗauko ta ba tun farko"
Ajiyar zuciya Siraj ya sauke yace "har gobe Momi bazan basa faɗa miki ba Yarima bai dace da Maryam ba dan ba mutumin kwarai bane taya za a ɗauki karamar yarinya kamar Maryam a aura masa kada ki sake ɓata ranki akan wannan hukuncen da kika yi dan ni banga wata matsala ba"
Momi tace "akwai matsala Siraj dan yanzu ganin suke na hana Yarima auren Maryam na aura mata wani"
tashi yayi tsaye ya kalleta yace "Momi kina son Yarima sosai da badan wani abuba da nace kinfi sonshi sama da mu da muke yayanki"
Lumshe ido tayi ta sauke ajiyat zuciya shi kuma yasa hannayensa aljihu ya fice,

''' *** *** *** '''
duk inda yabi gaishe shi ake cikin girmamawa har ya isa parlor Hajiya zaune ya tararda ita tana cin apple wata baiwa na matsa mata kafafu Hajiya na ganinshi ta janye kafafun nata tayi mata alama data ta fice cikin sauri ta tashi ta gaida Yarima ta fice,
Karasowa yayi kusa da ita ya zauna ya ɗauki apple ɗin ya kai baki ganin bai yi mata magana ba yasa ta kalleshi yadda taga fuskarsa a ɗaure tasan akwai wata a kasa saida ta ɗanyi gyaran murya sannan tace "ɓacin ran jiya ne ko kuma na yau dn nasan Mai martaba yayi maka magana?"
ba tare da ya kalleta ba yace "saboda mi Mai martaba zaisa min baki a neman aure?"
"saboda bata dace da kaiba haba Yusuf koda basu wulakanta kaba ai kaima kasan bai dace ka auri wannan yarinyar ba ga yayan manyan mutane masu aji masu kyau wasu m har sun nuna suna sonka amman ka kai kank gunda za a wulakanta ka karama da ba ayi auren ba dan Mai martaba ya nuna baya so kamar yadda nima bana goyon baya"
kallonta yayi yana murmushi yace "nima zuciya tace take so ba ni ba kuma aure sai anyi shi no matter what dan haka kuso abunda ɗan ku yake so kawai"
fuskantar a haɗe ta kalleshi "saboda baka da zuciya ko shiyasa har yanzun kake son ta ina mamaki ka Yusuf kwata² ka chanja wai mi ka gani a jikin yarinyar nan ne.....?"
kamin ya bata amsa wayarsa tayi ringing ciro ta yayi ya danna picking ya kara a kunne,
banji mi akace masa ba murmushi kawai naga yayi yace "good job an samoshi kenan.........bani minti biyar"
da kallo Hajiya ta bishi har ya tashi tsaye sannan tace "waya kira ka a waya mi kake kokarin aikatawa?"
kallonta yayi fuskarsa ɗauke da far'ah ya rika hannunta yace "babu komai Ummi na ɗan ki ba zai aikata wani mummunan abu ba just trust him okey?"
bai jira cewarta ba ya sakarma hannun nata kiss ya fice yana murmushi.


*_©KHADEEJA CANDY_*
[11:27PM, 3/17/2017] Khadeeja Candy: ​*♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

Candynovel.wordpress.com

*45*

Haka Momi ta share kwana da kwanaki bata kula Qasin iyakarta dashi gaisuwa babu hanyar da bai biba na ganin ta dawo normal amman abun yaci tura dole tasa ya hakura ya kyaleta,

Wata ranar Asabar Momi na zaune parlor tana tunane² Siraj ya shigo guri ya samu kusa da ita ya zauna kasan carpet cike da ladabi ya kalleta yace "Momi wai miyasa yasa ba zaki ɗaga ma ya Qasin kafa ba Momi wadda fa kike abun nan danshi baima san kinayi ba dan me zaki rika fushi da ɗanki akan ɗan wata Momi"

Ajiyar zuciya Momi ta sauke irin nasu na manya sannan ta ɗan gyara zamata tace "bana daga cikin iyayen da suke fushi da y'ay'ayensu dan fushi iyaye yana tare da fushi Allah ko kaɗan ni bana fushi da Qasin kawai dai inason nuna masa kuskuren daya aikata babbane gaba karya sake aikata shi kuma wani gefen ma bana ganin laifinsa laifin kaina nake gani dana ɗauko Maryam riko har Yarima ya ganta ya nuna yana so kuma na hana shi ita wannan abun shine ya tsaya min a rai shiyasa yanxu na yanke shawarar ma yarda ita gurin Gwaggonta kusa da mijinta"

kallon rashin fahimta Siraj yayi mata "kina nufi ki ma yarda Maryam kauye kenan?"
"haka nake nufi kuma hakan shine kwanciyar hankali"
Amsar Da Momi ta bashi kenan a takaice

"amman Momi naga ai abunda na faru ya riga ya faru kuma kin riga kince yarinyar nan karatu zatayi mijinta yayi Na'am itama tana so Gwaggo ta amince dan me kuma yanzu zaki ce ki maida ta itama ai ba zata jidadi ba"

Motsa baki Momi tayi "ma yarda ita ya zama dole a gareni kodan suma na sama musu sukuni"
"ki sama musu sukuni su suwa?" Siraj ya tambaya

Momi saida ta nisa sannan tace "satin daya wuce Gwaggo ta kirani a wayar haruna tace mun wasu daga birni zunzo neman auren Maryam an faɗa musu tana da miji shine suka samu halilu sukace zasu bashi kuɗi mai yawa ya sake ta shi kuma ya k'i Aminta babu irin rarrashin da basu yi masa ba yak'i sun jera kwana da kwanaki suna zuwa har suka ce masa matukar bai rabu da itaba komai zai iya faruwa dashi"

keɓe baki Siraj yayi "ba kowa sai Yarima dan babu wadda zai aikata haka sai shi dan sheɗan kaɗa masa ganga yake yana rawa"

Momi tace "hakan yasa nake son maida ta kusa da mijin ta kar wani abun ya shiga kuma adawo ana ganin lafin juna"

"babu wani ganin laifi Momi kawai ki barta tayi karantunta shi kuma darasi yake son a koya masa"

kai Momi ta girgiza "a'a bana son wata fitina wacce na sha yanzu ta ishe ni kabar shi yayi duk abunda yake son aikatawa"

Da sauri ya kalleta fuskarsa da ayar tambaya "Momi wht are yhu tlkng abt abarshi ya kashe aure akan wani dalili na shi na banza?"

"abunda nayi ban kyauta masa ba Siraj na hana masa aurenta dan haka yanzu bazan hana shi rawar gaban hantsi ba na ganin ya kwatarwa zuciyarsa abunda take so"

wani kallo Siraj yayi mata kamar bai gane abunda ta faɗa ba can ya kawarsa kansa yana jinjina lamarin sannan ya sake kallonta yace "Momi yhu love Yarima a lot da ace ba ke kika haife ni ba da nace son da kike masa bana banza bane tunda banga wani abunda yake anfanarki dashi ba Amman ke kullum burinki ki faranta masa ko rantsuwa nayi ba zanyi kaffara ba kinfi mahaifiyarsa sonsa"

Sai a lokacin idanuwan Momi suka kawo kwallah magana ta soma yi cikin muryarsu ta manya "kai Da yayanka kun kasa fahimta ta akan Yarima da mahaifiyarsa Siraj yau inason faɗa maka wani abu da baka san da shiba dan ina ganin har yanzu baka wayi dangantakar dake tsakaninmu ba..."

lutse baki yayi ya tari numfashinta "na sani Momi bana nufin ɓata miki rai dan Allah karki zubar da hawayenki akan wannan maganar"

Momi ba tare da ta kalleshi ba tace "mu biyu kawai mahaifiyarmu ta haifa saida aka fara haihuwar Hajiya da shekara 6 sannan aka haife ni ina da shekara 15 mahaifiyarmu ta kwanta ciyon ajali a lokacin Hajiya tana gidan aure ni naje na kirata mukazo gaban gadon mahaifiyarmu muka zauna nan mahaifiyata ta rika hannuna tace nayi ma Hajiya biyayya na ɗauketa kamar uwa na guji ɓacin ranta duk kuma abunda zai sata farin ciki na tabbatar da na yi shi na sota kamar yadda nake son kaina sannan ta ɗauko hannun Hajiya ta ɗora saman hannuna tana faɗin ga kanwar ki nan ki riketa ki zamo mata uwa karkiyi mata abunda zai sata bakin ciki ki sota kamar yadda kike son kanki wannan itace wasiyar da mahaifiyarmu ta bar mana bayan rasuwarta Hajiya ta mayar dani gidan ta da zama wato gidan mahaifin Yarima tunda naje gidan bata taɓa koda hararata ba balle ta min tsawa bata taɓa ɓata min rai ba har ta aurardani ga mahaifinku lokaci ɗaya muka haihu da ita ita ta reni Qasin duk da irin son da take ma Yarima bai rufe mata ido ta nuna Qasin ba ɗanta bane karara take nunwa Yarima kiyayya ta karɓe abun hannunsa ta baiwa Qasin ko ta dake shi akan Qasin koda shine da gaskiyasa har kuka girma kuka kawo yanzu kuke ganin inayin abunda bai dace ba alhalin ni nasan abunda yake nan uwa ɗaya uba ɗaya ba wasa bane koda mahaifiyarmu bata mana wannan wasiyar ba......"

da kuka ta karasa maganar ta lumshe ido alamar tunawa da bacin cikin baya

Lakas jikin Siraj yayi sanyi a hankali ya sunkuyarda kansa cike da tausayi

Sun daɗe a haka parlor yayi tsit kamar ba kowa Momi dai in bada sharar hawaye babu abunda take,

Ganin hakan yasa dole Qasin ya ɗaga lalulen parlor ya shigo dan babu abunda ya tsana kamar zubar hawayen Momi.


*_©KHADEEJA CANDY_*
[11:27PM, 3/17/2017] Khadeeja Candy: ​*♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

Candynovel.wordpress.com

*46*

A kasan carpet shima ya zauna gefenta na dama yana faɗin "na fahimci dalilinki Momi ina neman yafiyarki akan abunda nayi"

"na yafe maka Allah ya yafe mana gaba ɗaya"
Shine abunda Momi ta furta suka amsa da amin

Sannan ta sake kallonsa tace "ka shirya gobe zamuje kauye"

Kai kawai ya ɗaga mata ya amsa da thom ya tashi ya fice

'''*** *** ***'''
Guraren biyar da rabi Mairo ta shigo ɗakin Momi kinik kinik da fuska kamar ta fasa kuka koda ta shigo ta tararda Momi na waya hakan yasa tayi kwance saman gado tana kallon fuskar Momi

Momi na sauke wayar ta kalleta "ke lafiya kike wani kumbure²?"

Tashi tayi zaune "Momi wai Siraj yace min wai kauye zaki maidani"

Shiru Momi ta ɗanyi kamin tace "Gwaggo ce tace a dawo dake amman...."

Mairo bata jira Momi ta karasa maganar ba ta faɗi kasan carpet ta shiga murje² tana kuka

Lallashinta Momi ta shigayi tana bata hakuri faifai taki yin shiru saima karawa take ganin haka yasa Momi ta tashi ta ɗauko wayar radio ta shiga duka ta dashi

Aiko nan ta soma kukan gwarai sai ihu take iya karfinta tana faɗin "na daina Momi dan Allah kiyi hakuri"

Momi bata saurara mata ba saida Siraj ya shigo ya karɓe bulalar ransa a ɓace yace "haba Momi ya zaki rika mata irin wannan dukan da wayar loba?"

Cikinsa Momi tayi da matsifa "an daketa ai kai ka jawo a daketa ɗin dan ance za mayar da ita kauye ta rika yima mutane kuka ba daga kauyen ta fito ba da rainin hankali"

tsaye ya tada ita yana faďin "amman Momi ai kinsan ta riga ta saba da nan ba jindaďin zama can zatayi ba"

Momi tace "ko taso ko karta so saina maidata inna kai ta karta zauna"

"tho amman Momi ai ba haka ya kamata kiyi mata ba lalla6ata ya kamats kiyi"

Kofa Momi ta nuna masa "kai fita ka bani guri"

Ba musu ya juya ya fice nan nan ta kalli Mairo ta nunata da yatsa "ke kuma in bakiyi min shiru ba yanzu saina dada miki wani dokan"

Da gudu ta tashi ta fice
Ranar Mairo wuni tayi kuka har dare Momi kan ido kawai ta samata

Washe gari ma daga inda ta tsaya da kukan ta tisa kamar wata karamar yarinya Momi dai bata bi ta kanta ba duk suna downstairs suna breakfast

Daf da zasu gama Siraj ya shigo bayan ya gaida Momi su Nura da Usman suka gaidashi yana kokarin zaunawa ya kalli kujerar Mairo yace "ina Maryam bata tashi bane?"

"ta tashi tana can ta tisa kukan daga inda ta tsaya ba shi kake son tayi ba?"

Momi ce ta bashi amsa tana ɗan hararasa
shi kuma yayi murmushi ya tashi ya nufi upstairs

Be dade sosai ba ya fito ɗakin Mairo na gaba yana bayanta murmushi shinfiɗe a fuskarta saidai ta ɗan kunbura saboda kukan da tayi

Kallon mamaki Momi ta ringa yi musu har suka kawo dining sannan ta kalli Siraj tace "me kace mata Siraj?"

Kallon Mairo yayi yana dariya "Momi kamar ya me nace mata me zan mata?"

"hmmm" Momi ta taɓe baki "ai kodan kai saina maida yarinyar dan kaima kanka sai ka hore mata kunne"

Fashewa yayi da dariya "hore mata kunne Momi akan mi mema akayi da har zaisa na hore mata kunne?"

Turo baki Mairo tayi "ke Momi kin cika matsala inda kuma kuka ga inayi kice kuma wani abu"

Tashi Momi tayi tana faɗin "kyaji dashi yau ne dai kawai kike garin nan anjima kaɗa kauye zakije"

A maimakon tayi kuka kota ɓata fuska sai kawai ta kalli Siraj ta fashe d dariya "naji Momi ai in a son kauyen"

Kallon Siraj Momi tayi shima ita yake kallo yana kokarin ɓuye murmushin dake son fito masa sai faman kware ido yake alamar marar gaskiya

Uffan Momi bata ce masa ba kwafa kawai tayi ta nufi upstairs

*@2:32pm*
Suka kama hanya Qasin ke driving Mairo na front seat Momi kuma na gidan baya

Akai² Mairo takan kalli Qasin tayi murmushi shi kuwa tuni ya tsargu daman ba son tafiyar yake ba duk yabi ya wani ɓata rai wannan karon tana kallonshi ya watsa mata harara

Taɓe baki Mairo tayi ta ɗan ja tsaki "mtw dan nan kalle ka zaka Harare ni"

Kasa² take maganar tana rama harar da yayi mata

Har yayi kamar yayi mata magana sai sai wata zuciyar ta hanashi wai a cewarsa matar aure ce

Bayan kamar minti 30 ta sake kallonshi wannan karon wsta magana ce tazo mata
"yaya wai mi yasa matarka bata dafa maka abunci saidai kaci na Momi koka siya kuma kullum ta rika bachi inna shiga part ɗinka ta rika hararata tana jan tsaki ni ko mi nayi mata oho"

Faduwa gabansa yayi sanin Momi na nan karta sa baki dan babu abunda ya tsana kamar maganar Mansura

Ta madubin gaba ya kalli Momi itama ta nan take kallonshi suna haɗa ido yayi sauri kawar da nashi idon
Bai iya cewa Mairo komai ba har suka isa

*☆ ☆ ☆*
Gwaggo tayi mamakin ganin su sosai dan sunyi mata tafiyar ba zata

Bayan sun ɗan huta Gwaggo ta kawo musu abinci Momi ce taja abincin tana ci daman shi Qasin al'adarsa ce duk akaje kauyen ba cin abinci yake ba sai dai ruwa ko k'walama Mairo kuma tuni ta nufi gidan tsoho

Bayan Momi ta kare ta sha ruwa ta wanke hannu tana hamdala

Murmushi Gwaggo tayi tace "nace Allah dai yasa lafiya naga kun mana zuwam rana tsaka kuma har da tufafin Mairo?"

"lafiya kalau gani nayi ya kamata a kawo ta taga gida tunda yanzu tana da aure kar a tauye ma mijin ta hakki"
Momi ta karasa tana gyatsa

Dariya Gwaggo tayi "a gaskiya kin kyauta ana son haka shekaran jiya ma halilu yake cewa shi wannan aure ya zame masa ala k'ak'ai matar daya aura tana gabas yana yamma amman an bi an takura shi"

Momi tayi murmushi "tho ya hutarda ranshi yanzu gata nan mun kawo sai ya gina ɗaki ya sakata ya huta"

Zunɗen baki Gwaggo tayi "ta ina zai iya gina ɗakin wannan ragon namiji ni wallahi sai yanzu nake jin haushi aura masa Mairo da akayi mutum ba sana ar komai sai zaman kashe wando"

Momi ta rike baki "to ai nema masa za'ayi ba za a kyale shi haka ba tunda yanzu har ya soma tasarma iyali"

Gwaggo ta taɓe baki "to wa zai nema masa shi ba zaije y nemaba si kace ba namiji ba ke nifa duk inda abun nan yakai ya kaimin na halilu kullum da anyi masa magana sai yace shi karatu yake son yi shidai ya cigaba da karatu koda uban me zaiyi karatun oho"

Sai a lokacin Qasin ya kalleta yayi dariya dan tunda suje maganar uffan baice ba har Gwaggo ta gama zaginsa da ɗebe masa albarka

'''*** *** *** '''
Sai kusan biyar na yamma su Momi suka kamo hanyar gida
har bakin mota Mairo ta rako su tana ɗaga musu hannu sosai Momi tayi mamakin ganin bata yi kuka ba saima murmushi da take kamar bata damu ba

Momi dai kallonta kawai take har suka ɓace

Juyowa Mairo tayi kamar kazar da kwai ya fashewa tana rike da hannun Gwaggo suka shiga gida

Koda suka zauna kwalla sun cika ma Mairo ido duk ta wani marairaice fuska cikin muryar tausayi ta kalli Gwaggo tace "Gwaggo kinga sun tafi sun barni"

Gwaggo ta janyota "tho ai in kika kwana biu sai ki je can kuma kinga ai kara kina zuwa ganin gida ko?"

"a a Gwaggo tace nan zata bar ni ba zan sake zuwa birni ba"

Yanayin fuskar Gwaggo naga ya chanja "tho me kika mata?"

Wannan karon har hawayen sun soma mata zuba "nima ban sani ba nidai haka kawai ta mayar dani kuma nata rokonta ta barni taki harda dukana tayi amman dai Siraj yace min kar nayi kuka gobe zai zo yaje dani"

Gwaggo ta shafa kanta "kedai faɗamin gaskiya yar Gwaggo kodai wani abun kikayi mata ne? "

ɗan kare ta ɗauka tana zanawa a kasa kanta na saman cinyoyin Gwaggo tace "wallahi ban mata komai ba ni duk ma na daina wannan rashin jin tunda naje can sai faman aiki da nake"

Gwaggo tace "tho me zai sa tayi miki haka ni daman zuwan nan naku ban yarda dashi ba dan ruwa baya tsami banza"

Cikin muryar kuka Mairo tace "kila dan taga suna da kuɗi ne sunga ina son zama gurin su dan ko wannan matar Qasin ɗin inna shiga gurinta sai ta rika hararana tana jamin tsaki shima yaya Qasin naga yana yimin bakin rai kuma ban masa komai ba Siraj ne kawai yake sake min fuska ina jindaɗi"

Shiru Gwaggo tayi alamar tunani kana ganin yanayin fuskarta kasan ranta ya ɓace.



*_©KHADEEJA CANDY_*
[11:27PM, 3/17/2017] Khadeeja Candy: ​*♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

Candynovel.wordpress.com

*_JINJINAR BAN GIRMA A GAREKI RUFAIDA OMAR_*😘👍🏻

*NA YABA DA SOYAYYARKI MARYAM ABDULKADIR (MAMAN AFFAN)*😍

*WANNAN SHAFIN NAKI NE DR. ZULAIHAT ISA (AUNTY NA)*😘

*47*

"Assalamu alaikum Assalamu alaikum Assalamu alaikum"
Halilu ne yake sallamar tun daga kan Gwaggo har Mairo aka rasa mai amsa masa.
Mairo dai in banda harara babu abunda take masa.
"wa'alaikassalam" saida ya kusa k'arasowa sannan Gwaggo ta amsa masa can k'asan mak'oshinta.
jiki ba k'wari ya zauna saman tabarmar ganin marhabar da Mairo take masa da harara ga kuma yanayin yadda Gwaggo ta amsa masa sallamar duk sai yasashi jin ba daɗi.
haka ya danne abunda ke zuciyarsa ya kalli Mairo da far'ah
"Yan birni saukar yaushe ?"
"D'azu ɗazun nan Hajiya ta kawota har ma take tambayarka"
Gwaggo ce ta bashi amsar bayan ta nisa
murmushi yayi
"Ayyah aiko ban jidaɗin da suka wuce ban samu ganinsu ba dan naso ganin Siraj sosai"
"Ai ba dashi aka zo ba da Ya Qasin aka zo kuma basu daɗe ba suka wuce"
Wannan karon Mairo ce ta amsa masa.
"Amman dai lafiya suka kawoki yanzu ko anfasa karatun ne ?".
Gwaggo ta taɓe baki "Toh ban sani ba amman dai sun kawota ne wai kar a tauye maka hakki"
Murmushin jindaɗi yayi "Aiko Hajiya ta kyauta kuma tayi abunda ya dace. daman jiya Tsohon yake cewa ya kamata a dawo da ita gida abar maganar karatun nan."
"Toh gata nan an kawo sai ta maka maganin da zatayi maka haka kawai ka ɓata rayuwarka kana son ɓata mata nata rayuwar." kallon Gwaggo yayi fuskarsa na nuna ɓacin ran dake zuciyar "Haba Gwaggo wannan wace irin magana ce haka.?"
Sake taɓe baki tayi a karo na biu "Eh mana toh in bashi ba miye na wani damuwa da a kawo ta alhalin ko ɗakin da zaka sakata baka ginaba gaka babu sana'ar yi barre aiki kai dai kamar ba namiji ba!"
a hankali ya sauke ajiyar zuciya "Gwaggo kada rashin aikina ya dame ki munyi magana da wani zanje neja zai nemin aiki kuma zai mayar dani makaranta yanzu haka ma na haɗa kuɗin mota nan da kwana biu zanje In'sha Allah"
cikin sanyayyiyar murya yake maganar cike da ladabi.
Gwaggo ta nisa "Toh Allah yasa ya kuma taimaka ai haka nake so jin"
Murmushin jindaɗi yayi ya amsa da 'amin' tare da tashi ya nufi k'ofar ɗakinsa.
daf da zai shiga Mairo ta tashi zaune ta kalleshi "Halilu zaka je dani ko ?"
juyowa yayi bakinsa ďauke da dariya
"A'a Mairo kinga nema zai kaini ba zama ba sai naga yadda abun zai kasance tukuna."
Gwaggo taja mata kunne "Wai mai yasa kike da shegen son yawo ne ?"
"Ni wallahi bana son zama a k'auyen nan."
cewar mairo tana wani yak'unar fuska kamar wacce taga wani abun k'azanta.
Murmushi. kawai halilu yayi ya shige ɗakinsa.
Gwaggo ma dariya tayi "Ai zama k'auye ya kamaki tun da nan kika tashi kuma nan kikayi aure. sai hak'uri"
ɓata fuska tayi ta sake komawa saman k'afafun Gwaggo kamar ta fasa kuka.

Washe gari k'iri k'iri Mairo tak'i ta ci dumame dak'er Gwaggo ta lallaɓata ta samu ta sha kunu da rana ma k'in cin abinci tayi haka ta wuni har dare wai ita ba zata ci tuwon dawa ba tuwon masara da Gwaggo ta tuk'a mata ma k'in cin tayi saida dare Halilu ya shigo mata da agashe mai tumatir da albasa.
da murna ta karɓa tayi zaman kirki taci tasha ruwa sannan ta kwanta.
Cikin kwana biu duk tabi ta chanja sai rama da take fama da ita na rashin cin abinci da kuma tunanin birni kullum cikin kuka. take da mafarkin ranar da Siraj zaizo yaje da ita,
Ranar wata laraba Gwaggo ta na zaune tsakar gida tana aiki Mairo ta fito daga cikin ɗaki ta zauna fuskarta a kunbure da a'lamar kuka tayi.
Kalllo ɗaya Gwaggo tayi mata ta ɗauke kai "Allah yayi miki saukin wannan halin rayuwa da kika saka kanki ciki Mairo wannan abu dame yayi kama daga zuwa birni shi kenan kin mayarda abu armun-azi'mun kin are kin yafe ke sai can ai toh k'ara da aka dawo dakw yanzu dan in kika kara jimawa k'ila koni bazaki so gani ba."
idonta ne suka k'ara cika da kwallah. da muryar kuka ta soma magana "Gwaggo nan fa babu daɗin zama kuma tunda na dawo babu halin na fita sai ace naje yawo Tsoho ya rik'a min faɗa ko k'awayene sun daina zuwa guna..."
Gwaggo ta rik'e baki "Oh ni yau kiji mani 'ya toh ba aurene dake yanzun ba yaya zamu saka miki ido kina yawo yanzu fa ba kamar da bane ke MATAR AURE ce yanzu"
fashewa tayi da kuka "har ga Allah ni bana son auren na dan kun mayardani k'ank'annu kuke min haka"
"Uhmmm. inma dan zuwanki birni ne yasa kike wannan abun gara tun wuri ki shafawa kanki lafiya ko babu komai dai kinga bason suke ki zauna a tare dasu ba."
cewar Gwaggo,
uffan Mairo bata sake cewa ba in banda kuka da ta shiga rusawa.
fitowa Halilu yayi daga cikin ɗakinsa ya nufo Gwaggo yana faɗin "Gwaggo ina ganin tafiya ta gobe ne in sha Allah"
wani irin faɗuwa gaban Mairo yayi zuciyar ta ta buga da k'arfi nan da nan hawayen dake mata zuba suka tsaya ta ɗaga kai tana kallon Halilu,
Gwaggo ta kalleshi "Gobe gobe Halilu ?"
"Eh kinsan nace miki ranar Alhamis za muje da naso ɗaga tafiyar toh wadanda zamuje tare ne suka k'i"
Gwaggo na dama garin dake gabanta tace "Shin wai yau wace ranace ni har Alhamis ɗin tazo ne ?"
Halilu yayi dariya "Eh mana Gwaggo gobe ne Alhamis fa ko kin manta yau Laraba kinsan shekanjiya ne matar Garba ha haihu yau kwana huɗu"
kai Gwaggo ta girgiza "Haka ne fa oh duniyar nan lokaci yana gudu dubi kaga haihuwar nan wai har an kwana huɗu Allah dai yasa mu cika da imani kwankinmu ne ke tafiya maganar nan yaushe muka yi ta amman wai har Alhamis ɗin tazo"
"Wallahi kuwa Gwaggo ai mai hankaline yasan wannan ga tsadar rayuwa saidai ace Alhamdulillahi"
yayi maganar yayin da yake k'ok'arin risinawa kusa da ita,
Gwaggo taja damun ta aje gefe ta sake kallon sa "Wai tafiyar nan dai babu wani abu ko nidai sai na rik'a ba daɗi karfa garin neman gira a rasa ido karka jefa kanka cikin wani halin daman dan neman abunyi, dama ace bakiyi nisa da muba ko nan kusa ai ka samu wani abun amman qce har neja"
Murmushi yayi "Babu komai Gwaggo sai alkhari kedai kiyi ta min addu'ah wannan abun da kikeji ba komai bane sai sabo in sha Allahu za ayi nasara."
Ajiyar zuciya ta sauke "Toh Allah yasa addu'ah ai kullum ciki yi muku ita nake Allah ya kaika lafiya ya tsare amman naso tafiyar nan ba yanzu ne da sai na karɓi a dashe na saina baka ka k'ara"
"Babu komai Gwaggo addu'ah kin ya fiye min komai inada yan kuɗin da zasu ishe ni kwana biu kuma kinga in naje ba zama zanyi ba aiki zamu rik'a yi"
"Toh Allah ya taimaka yasa ayi sa'ah ya tsare min kai ya raya ka ya cika maka burinka"
sosai ya jidaɗi addu'ah da Gwaggo tayi masa bayan ya amsa da 'amin' ya tashi tsaye yana faɗin "Bari na shiga gari na ɗanyi bankwana da wasu"
kai Gwaggo ta ɗaga masa "Toh aikan yafi Allah dai ya tsare."
tafiya ya somayi har yakai k'ofa Mairo ta kirashi
"Halilu..."
"Na'am"
juyowa yayi ya kalleta itama shi take kallo bakinta yayi mata nauyi ta kasa magana. ganin hakan yasa shi tambaya ta "Minene Mairo ko wani abun kike son a siyo miki ne ?"
kai ta girgiza alamar a'a "Toh minene faɗi naji ?"
cika idonta sukayi da kwallah "Halilu dan Allah karkaje neja ɗin nan kaji ko kuma kaje dani"
"Saboda mi ?" Gwaggo ta tambaya "Nidai bana son yaje bana so kawai"
cikin muryar tausayi ta bata amsar, hawayen dake idonta suka soma gudana.
dawowa Halilu yayi ya risina daidai gun da take zauna ya kalleta cikin muryar lallashi ya soma magana "Kar dai ace tafiya tace ta saki kuka ai ba daɗewa zanyi ba zan dawo dole naje dake dan haka kibar k'ararda hawayenki kinji ?"
"A'a nidai bana so kawai kar kaje bana son kaje ka bari har wani lokacin"
wannan karon muryarta na rawa tayi maganar.
iskan dake bakinsa ya busar sai zuciyar ta soma masa ba daɗi "Haba Mairo karfafa min gwuiwa ya kamata kiyi fa kinga nan ina zauna babu wani abunda zanyi amman can zan samu aikin yi nayi kuɗi na gina miki gida mai a birni da zaki zauna na rika baki kwai da daɗi kina ci amman kinga inna zauna nan haka zamuyi ta zama babu wani cigaba yanzu fa dana dawo birni zamu koma ko baki so ?"
"Ina so. mana"
Murmushi yayi "Yauwa toh ki zake ranki ki rik'a min addu'ah kinji ki daina kuka ?"
share hawayen tayi ta ɗaga mishi kai "Toh na daina amman dai in kaje karka daɗe"
"Ai bazan daɗe ba zan dawo na ɗaukeki"
Gwaggo daga gun da take tayi dariya tace "Oh Mairo kodai ya saki a jaka ne ya tafi dake ?"
fashewa tayi da dariya "Haba Gwaggo sai kace wata yar tsuntsuwa sai dai in Tsoho za asaka aje dashi"
wannan karon har Halilu saidai yayi dariya.
Gwaggo tasha mur "Wai Mairo mi yasa kika raina Tsoho ne naga dai ba sa'an ki bane ai ?"
"Amman dai kakana ne ko sai abarni dashi shima ai haka yake min"
"Toh shi kenan aiko zamu saka k'afar waddo ɗaya dake"
kai kawai Halilu ya kaɗa ya tashi ya fice.


*_©KHADEEJA CANDY_*
[11:27PM, 3/17/2017] Khadeeja Candy: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*
Candynovel.wordpress.com


*48*

Tunda Halilu ya dawo, sallar A'suba ya shiga kintsa sauran kayansa.
daf da zai gama Gwaggo ta shigo masa da kari "Halilu ana nan nata shirin ?"
juyowa yayi bayan ya aje jakarsa gefe. "Eh wallahi har kin tashi Gwaggo ?"
"Eh tunda nayi sallah na shiga haɗa maka abun kari naji kace da wuri zaka wuce."
kunun data aje gaban shi ya buɗe ya shiga motsawa "Toh ai kara tafiyar safen Gwaggo tun kinga garin nesa ne kara muje da wuri"
Ajiyar zuciya kawai Gwaggo ta sauke ta tsora masa ido.
biu da ludayi yayi ya aje Gwaggo ta kalleshi "Ba dai ka k'oshi ba ?"
"Gwaggo bazan iya sha da yawa ba ki cikina a ɗaure yake wannan ma dan kar naje babu komai a ciki nane"
Gwaggo ta tura masa dumame "Toh kaci tuwon mana ai bakaje da yunwa ba dai"
"Bazan iya ci ba Gwaggo inna ji yunwa zan siye wani abun ko a hanya ne"
"Toh Allah ya sauwake ko ni haka nake in zanyi tafiya bana iya cin abincin kirki"
kuɗi dake ɗaure a gefen zaninta ta ciro ta mika masa "Ga wannan jiya na aro gun Faɗime ka ɗan k'ara"
kamar bazai k'arɓa sai kuma yasa hannun ya karba yana godiya "Allah ya saka da Alheri amman dama baki wahalar da kanki ba Gwaggo na faɗa miki inada yan kuɗin da zasu ishe ni." "Babu komai Halilu in banyi maka ba wa zaiyi maka Allah dai ya raya mani kai ya tsare ya baka abunda kake buk'ata."
"Amin Gwaggo Mairo bata tashi bane ?"
saida yayi tambayar kunya ta zo masa da sauri ya sunkuyarda kansa.
murmushi Gwaggo tayi "Bata tashi ba daman bana son ta tashi dan in taga tafiyar ka zata iya fasa min kuka"
shima murmushi yayi "Mairo manya ana girma na cin k'asa Allah dai ya shirya"
kamin Gwaggo tace Amin sukaji an buga gida.
da sauri ya tashi ya fita, bayan kamar minti ɗaya ya dawo ya ɗauki jakar yana faɗin "Ga abokan tafiyar nan sun zo zamu wuce..."
ganin idonta sun cika da kwallah yashi risinawa ya kalleta "Haba Gwaggo kar kimin haka mana dan Allah karkiyi kuka bafa rabuwa mukayi ba tafiyace kuma in sha Allahu zan dawo"
sam Gwaggo kasa hak'uri tayi saida kukan nata ya fito fili,
nan shima nashi idon suka cika da kwallah amman bai yarda ya bari ta gani ba kasancewar shi namiji. tsit ɗakin yayi in banda shashekar kukan Gwaggo babu abunda kake ji.
saida hawayen suka ɗan tsaya mata sannan ta kalleshi da jajayen ido "Allah ya tsare ka Halilu ya kaika lafiya"
dak'er ya iya amsawa da Amin ya tashi ya nufi k'ofa nan ma ya daɗe tsaye sannan ya fice.
.                 Sai takwas da yan mintuna Mairo ta tashi da murjar ido ta fito ɗakin ta ɗauki buta ta shiga banɗaki., bayan ta fito ta nemi guri ta zauna zata fara alwala.
Gwaggo ta kalleta "Yau Mairo anyi ranar sallah."
"Wallahi Gwaggo jikin ne yayi min nauyi kuma duhu dubun nan da nake gani saina ɗauka ko safiya bata waye bane."
Gwaggo ta ɗan kalli gajimare "Eh da yake yau an tashi da hadari kuma yayi bak'i sosai ina ganin ruwa ake a wani garin kusa."
taɓe baki kawai tayi ta cigaba da alwala bayan ta k'are ta shiga ɗaki ta saka Hijab ta shinfiɗa ɗan kwali ta soma Sallar, tana k'arewa, ta fito ɗakin da sauri ta shiga ɗakin Halilu.
fitowa tayi kinit kinit da fuska kamar ta fasa kuka ta nufo Gwaggo,
tun kamin ta k'araso Gwaggo ta tare ta "Toh karki fara mani kukan nan naki ni ban iyawa"
"Miyasa baki tashe niba da zai tafi kuma kika barshi ya tafi"
da rawar murya tayi maganar alamar tana son yin kuka.
"Shine a yace karna tashe ki na kyaleki baya son kukan nan naki" aiko kamar jira take Gwaggo ta kai aya ta fara sana'ar ta ta "Ni wallahi Gwaggo sai na miki kukan tunda kika ki tashi na" abunda ta dinga faɗa kenan tana murjar kafafunta akasa kamar wata k'aramar yarinya,

*BIRNI.........*
Koda Momi ta sauko downstairs ta nufo dining room ta tararda Siraj zaune yana haɗa ma kansa tea.
"Kai kaɗaine a dining ?"
juyowa yayi ya kalle ta "Eh sun wuce makaranta tun dazu wai suna da lakca k'arfe takwas good morning Momi"
"Morning too yau kayi saurin tashi tunda A'suba fa na ganka parlor nan nama ɗauka ko aikin ne naku ya taso."
ta faɗa yayinda take k'ok'arin zaunawa.
dariya yayi "Haba Momi aiki tunda asuba ?"
"Eh mana in an kawo patient irin wannan lokacin kuma ace duty ɗinka ne ai dole kaje ba ɗaga k'afa dole a tashi da wuri"
shafa kanshi yayi "Taf ai kan ba amin haka ko patient ne wasu likitocin saji dashi sai goma ko sha ɗaya nake shiga office."
"Hmm. kaidai Allah ya kawarda ɓacin rana ai inta kama dole kayi toh yanzu wai miya tashi ka tun da safe. ?"
"Wani mummannan mafarki nayi..."
Momi ta tsayarda zuba madarar da take. "Mummannan mafarki kuma har kasa gabana yayi dakan uku uku ?"
dariya yayi "Kai Momi kin cika tsoro bafa akanki nayi ba akan Abbah ba akan kowa na gidan nan ba."
"Toh akan wa faɗa min gaskiya Siraj ?"
"Momi ai ance in anyi mafarkin daba na k'warai ba ba'afaɗa"
"Toh miya rage a kariga ka faɗa."
saida ya ɗan cije baki sannan yace "Mafarkin nayi wai Maryam ta Auri wani mutum..."
Ajiyar zuciya Momi ta sauke ta lumshe ido,
bayan ta buɗe ta ɗanja tsaki "Mtsss Siraj ka iya tada hankalin bawa ni Wallahi na ɗauka ko wani abun ne"
"Wani abun ne mana Momi kai Allah dai ya tsare."
kallon mamaki Momi tayi mashi "Ya tsare. mi abunda Allah ya kaddaro ai babu mahani in Allah ya rubuta saita Auri wani ai sai ta Aura"
tea dake gabansa ya kurɓa "Eh haka ne amman dai kada Allah ya kaddaro ta Auri wani bayan..."
sai kuma yayi shiru ya kasa karasawa.
kai Momi ta girgiza "Allah yayi muku saukin wannan rayuwa kun ɗauki kiyayyah kun ɗorawa Yariman nan na san ai danshi ne kake wannan abun"
hannayensa ya ɗaga sama "A'a Momi karfa ki lakamin laifi kedai kika amfato sweet son ɗin nan naki baki ji a baki na ba."
Momi ta soma shan tea tana faɗin "Ai ko baka faɗa ba na san haka kake nufi."
Murmushi yayi ya tashi tare da cup ɗin tea ya ɗauki jaridar dake gefensa ya fice.

''' *** *** *** '''
Kishingiɗe yake tsakar parlorshi sanye da wando pencil da riga yellow, idoshi a lumshe yana tsutsar minti yana mayarda numfa a hankali,
"Yes enter..."
shine abunda ya furta bayan mai bugun k'ofar ya dade tsaye.
wani wassgegen mutum ne naga ya kunnu kai cikin ɗaki da gamammiyar fuska kamar an masa mutuwa.
nesa dashi ya tsaya yace "Oga nazo maka da Albishir mai daɗi"
saida ya kusan minti uku da yin maganar sannan ya amsa masa har lokacin idon shi a lumshe suke. "Wane irin Albishir kazo dashi ?"
cike da isa yayi mashi tambayar shi ko jiki na rawa ya bashi amsa,
"Halilu ya mutu..... "
_Halilu ya mutu.! Halilu ya mutu..!! Halilu ya mutu...!!!_
haka maganar ta rik'a yima Yarima yawo a kwakwalwa sai a lokacin ya buɗe ido ya kalli Mutumin "Nace maka duk yadda zakayi kayi na ganin ka raba tsakanin su amman banyi da kai ka kashe shi ba."
da sauri ya bashi amsa "Oga ba kashe shi nayi ba accident ya samu a hanyarsa ta zuwa Neja neman aiki" wani tsire baki Yarima yayi "Ya a'kayi kasan ya samu accident ?"
"Oga idun mu yana kansa fa tunda ka bamu aikin nan ko ina yarana nake sawa su kula dashi a motar da sukayi accident ɗinma harda yaron mu"
Wani irin kyakkyawan murmushi ya shinfiɗe fuskar Yarima wadda na tabbatar har a zuciyarsa yake.
tashi yayi tsaye ya k'arasa kusa da mutumin ya dafashi fuskarsa ɗauke da annashuwa "Kazo min da albishir mafi daɗi kuma goron mai tsokane jeki waje ka jirani amman ka tabbatar mutuwa yayi ba dogon suma ba."


*©KHADEEJA CANDY*



Download Mairo Littafi Na Daya Complete HausaNovel